UMM ADIYYAH CHAPTER 86 BY AZIZA IDRIS GOMBE

UMM ADIYYAH CHAPTER 86 BY AZIZA IDRIS GOMBE

                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

gaza yarda za ta zo ta yi shi da TJ. Ne

suka ji sa makulli, sai ga sallamar Zaid ya

shigo.

Cikin fara’a suka yi musabaha da TJ. Sannan

ya ce “Madam, sannunku da zuwa.”

Jakar kwamfutarsa ya ajiye da kwat dinsa, san-

nan ya dawo ya zauna a kujerar da

Umm Adiyya take zaune da Minaal a han-

nunta, idan ka gansu sunyi dagwas dasu

kamar ka sace, take TJ. Ya ji wani abu ya

murda masa, amma ya yi murmushi

kawai.

Saboda ya san mutum baya taba wuce rabonsa,

kuma Umm Adiyya da Zaid an yi su

ne domin juna ko yadda suka dace, yadda koo

wane motsinta akan idanun Zaid,

yadda suke yiwa Minaal wasa, daga gani ba

abinda suke so irin yara dukansu biyu.

Suna da wani gamayya na jini da kai na gefe,

idan ka zauna da su dole ka ji abin ya

ratsa ka.

To mun gaisheku, za mu wuce, magariba ta

kawo jiki.” TJ. Ya fada yana yunkurin

tashi.
“Haba da wuri haka? Ku tsaya mu ci abincin
dare mana kawai a nan? Twinkle, ku
shiga ciki da Maman Minaal mana.”
Aa, da gaske ba komai za mu zo wani
lokacin yanzu kam mun zo mu ga wuri ne,
mu taya ku murna kuma.”
“Ah haba? Da gaske dai ba za ku zauna ba ke-
nan.”
“Wani lokacin za mu dawo Inshaa Allah.”
“To shi kenan. Za mu bi ku ba shi.”
Zaid ya mike da Minaal a hannunsa yayin da
Umm Adiyya ta shiga ciki ta dauko
turaren wuta ta hada da madaurin gashi na
yara mata, da takalma da wasu riguna
guda uku masu kyan gaske, wanda take ga za
su yi wa Minaal dai-dai, cikin
sayayyar da ta je yiwa Saudah ne ta ga wadan-
nan kayan su ka yi mata kyau ta
kwashesu.
Haka ta ciko leda da su, har mota suka rako su.
Zaid ya dauki kudì dubu goma ya
bawa Minaal lokacin da Rahma ta zo karbar ta.
Ita kuwa ta ce ai sun yi yawa.
“Ke na bawa ko ‘yata? Idan na ba ki, sai ki ce
ba kya so.”
To Minaal ta gode. Allah ya biya.”
Cikin dadin rai dai aka rabu, duk da Umm
Adiyya ta kula da yadda kamar jikin Uncle
TJ ya yi sanyi kadan ba yadda ta san shi da
yawan far-far da surutu ba. Sun fita
daga gate ne ta ji muryar Zaid daf kunnenta har
tsikar jikinta ya tashi.
“Me ki ke tunani?”
“Me? Ba komai.”
“Hmm.” Hannunta ya rike cikin nasa ya sar-
gafe yatsunsu suka jera suna tafiya cikin
gida, cikin tsanaki.
“Tun yaushe ku ka zama abokai da Uncle T.J?
“Ina ruwanki?’
“A’a wai dai na ga, to ba dama na yi tambaya?”
“Muna gaisawa a waya, ya kira ya ce za su zo
da Madam.”
“Hmm!
“Meye?”
“Babu, kawai dai.. tsorona kar su zo (Dinner)
ka kone ne, yau har tafasa na ga ka
ke yi.” Tana fada tana matsawa gefe.
“Yarinyar nan kin yi baki da yawa fa.”
Ta tsunture da dariya, “Jinka kawai na ke yi,
wai su tsaya cin abinci bayan ka ki ka
matsa ko canja kaya ka je ka yi. Duk abinsa dai
ba zai mun magana ba a gaban
matarsa, don haka ka kwantar da hankalinka
kai ke da ni.”
Hannu ya sa ya zagaye kafadarta, daya han-
nunsa a cikin aljihun wandon Suit dinsa,
suna tafe har kusan Stairs din cikin falon.
“Na san da hakan Twinkle. Amma zumunci na
da kyau, ko ba komai saboda Yaya Isma’il za ayi
zumunci bare kuma… Wanda ya so Twinkle dina
ya wuce ai masa
wulakanci ko ba haka ba?”
“Koda ka na jin kamar ka shake shi, ka ji
dalilin da zai sa ya zo kusa da Twinkle din
naka ko?”
Dukawa ya yi ya sumbaceta a hankali. “Ina
sonki Twinkle.”
“Wannan fa na meye?”
“Saboda na ga zan iya. Ki na da matsala?” Gir-
giza kai ta yi, ta san kawai ya yi ne
don ya boye kishinsa, ta tabo shi da kala-
manta. “Ni ma ina sonka da yawaaaaa.” Ta
fada hade da makale masa wuya, kafafunta
suka bar Kasa.
Yana dariya ya ce, “Za ki kadamu fa.”
Dariya ta yi ta ce, “Ba na jin yin tafiya.”
Hannu ya sa ya tallafota jikin sa suka karasa a
haka, suna zuwa sama ya kwanta a
kasan kafet yana. “Wash! Da gaske za ki karya
min baya, kin kara nauyi, me ki ke
durawa ne idan na tafi ofis?”
“Kayan dadi.”
“Bakinki ne kayan dadin ai.”
“Ehm! Yaushe za mu tafi Bauchi?”
“Akwai tafiyar da zan yi, na fi son sai na dawo
sai mu je.”
“Tafiya?”
“Uhm! Za ki min rakiya ne?”
“Ya danganta da abubuwa biyu.”
Juyi da fuskarsa ya yi yana kallon fararen ida-
nunta. “Me da me?”
“Idan an min tayi, sannan idan na ji wurin
Zuwan.”
Tsuke idanunsa ya yi, “Oh! Ba ki damu da
wanda za ki tafi da shi din ba, koda jeji zai
kai ki?”
“Hmm! Zan iya dan lallabawa, amma dai a
fada min dai na ji tukun.”
“An ki a fada din, na fasa zuwa da ke ma.”
Ware idanu ta yi ta tashi ta zauna. “Wa ka ke
da shi da ta fi ni, kafarka ma kafata,
bari ma ka ji, dama na fara shirin komawa
Bauchi, don haka ka fadi, ina ne kawai na
je na karasa shiri.”
Dariya ya yi, ya jawota jikin sa, “Ga tsoro ga
baki. Hmm! Za ki gani.”

**************

Bayan kwana biyu ne ya zo ya dauketa saboda su

tafi yin VISA (Biza), sai a lokacin

ta fahimci inda za su je. kasar Jamus ne.

Daga nan kuma suka fara shirin tafiya, ba

kama hannun yaro. Wani aikin ne zai kai

shi daga nan kuma za su dan zagaya, sai su

dawo, tafiyar ta kwana goma ce.

Nan da nan ko Umm Adiyya ta yi masu shiri,

ana gobe za su tafi, ya kai ta gidan Anti

A’isha da gidan Abba ta yi masu sallama, san-

nan suka kama hanya. Aikin sa a cikin

Hamburg ne. Don haka nan suka fara yada

zango, har ma suka kaiwa Masdook da

Mihjanaa ziyara, sai da ya kammala abinda ya

kawo shi. Sannan ya wuce da ita

garin Göttingen.

*************

Tun safe ta gaza zaune ta gaza tsaye, ga shi Zaid

ya fita, duk ta rasa abinda ya ke

mata dadi, tana ta sake-sake a ranta. Ji take yi

kamar abubuwa suna mata yawo a

jikinta. Ga kuma wani tashin hankalin da ta
fuskanta a safiyar ranar.
Awowi biyu ya ce mata zai yi ya dawo su fita.
Amma yanzu ta ma daina kirga
awannin. Bandaki ta shige ta sauke (Toilet),
seat ta hau kai ta zauna hade da nade
kafafunta akai ta rungumesu a jikinta.
Sanyi take ji, amma ta gwammaci zaman
bandakin akan komai. Tun tana girgiza ita
kadai, ba ta san lokacin da ta fashe da
kuka ba.
Kuka ta rinka yi sosai, ba ta san iya lokacin da
ta dauka a haka ba.
Tunda Zaid ya shigo masaukinsu ya ji shiru, ya
yi tunanin bandaki ta shiga, tunda ga
mayafinta da su jakarta alamar ba ta fita daga
dakin ba, amma ya fi minti ashirin da
shigowa, wannan ya sa ya sa hannu ya buga
kofar bandakin a hankali.
“Twinkle..” Daskarewa ta yi da ta ji muryarsa.
Twinkle, lafiya dai ko? Me ke
faruwa?”
Jin shiru ba ta amsa shi ba, sai wani sauti da ya
ji kamar sheshsheka ya sa cikin
daga murya hankalinsa a tashe ya ce, “Zan
shigo yanzu.” Duk da haka, bai ji ta
amsa ba, hakan ya sa ya murda hannun kofar.
“Umm Adiyyah!” Da sauri ya isa gareta, han-
kali a tashe ganin irin yadda ta hautsine,
fuskarta ta yi ja, hawaye a bushe a fuskarta
gashinta biji-biji, tattarota ya yi a jikin sa
ya rikota.
“Twinkle dina me ya faru?”
Kuka ta sake saka masa har da diri da
shesheka. “Shhh. Ya isa. Shi kenan.Taho
nan.” A hankali ya sauketa daga inda take, ya
rikota suka fita daga bandakin.
Kan gado ya kwantar da ita, ya kwanta a
bayanta ya rikota jikin sa yana shafa kanta,
ko kayansa bai canza ba, blazer dinsa kawai ya
cire, ya rage linen Shirt dinsa da
wandon Jeans.
Jin tana ajiyar zuciya ya san cewa barci ne ya
dauketa. Amma duk da haka ya kira
sunanta don ya ji. “Umm Adiyyah?”
Jin shiru ba ta amsa ba, ya sa ya fahimci hakan
ne barci ne ya dauketa. Nan kuma
zuciyarsa ta cika da damuwa, me zai sa ta irin
wannan kukan da tashin hankalin?
Lokacin da Umm Adiyya ta yi juyi ta bude
idanu, idanunta akan Zaid suka sauka
yana zaune a kan kujerar dakin yana duba
wata mujalla. Da sauri ya rufe ya isa inda
take.
“Yaya ki ke ji yanzu?”
Wani numfahsi ta zuka, sai kuma idanunta
suka yi narai-narai! Za ta sake sa masa
kuka.
“Look, Adiyya ba za ki ci-gaba da rufeni ba,
Ya zamo lallai ki min magana, na san
me yake damunki, na fita na bar ki lafiya, na zo
na same ki a haka, hankalina dole
zai tashi. Sannan kin tsaya sai kuka ki ke yi,
kin ki ki yi magana. Talk to me, now.”
“Yaya Zaid…”
Daskarewa ya yi da ya ji ta ambaci sunansa,
domin muddin su biyu ne tunda suka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *