SANNU SANNU BATA HANA ZUWA COMPLETE

 SANNU SANNU BATA HANA ZUWA COMPLETE

[6/15, 11:34 PM] My S Nomba: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎+ _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___3💎 Murmushin da bai kai ciki ba shurahbil yayi masa yana kallon yaran da suka duqufa suna kallo abunsu hankali kwance, bud’e gambun motarsa yayi yafito tare da miqa masa hannu suka gaisa, fuskar shurahbil a d’aure yace “ammm…….kamar naso nawayi fuskarnan, waye kai? ya tambayeshi Kai tsaye batare da wani shayi ba. “Ni ba kowa bane” shima ya bashi amsa atak’aice, “Ok meya kai yarannan acikin motarka bawan ALLAH?” Yasake jefa masa wata tambayar batare daya dubi girman saba, Yana tunanin wane daliline zaisa daga ganin yara ya d’aukesu yatura cikin motarsa, ko dai so yakeyi ya sace sune, muryarsa yajiyo yana cewa, “Ganin yanda kabar motarka abud’e sun fito batare da sanin inda zasu nufa ba shine dalilin da yasa nayi tunanin tsayawa na taimakeka ta hanyar tsaidasu har sai kadawo, yakamata kasan cewa wannan abun da kayi sakaci ne babba kuma kuskurene? qananan yarane su dake buqatar cikakkiyar kulawa, don haka yakamata akula dasu sosai” bai jira me zai ceba ya sake bud’e gambun motar yace dasu, “Yawwa yaran baba, kuzo ga baba nan yadawo kunji ko?.” Maqale kafad’a sukayi sunaci gaba da kallonsa yayi murmushi tare da cewa, “yatafiyarsa kenan kun fasa zuwa wajen dady da ummie ko?” “Laa..a’a nidai zanje.” hassana tafad’a, hakan yasa itama hussaina ta taso tana fad’in, “nima zanje wajen dady da ummie.” Fiddosu ya dingayi d’aya bayan d’aya daga cikin motar ya diresu qasa had’e da juyowa yana kallon shurahbil daya saki baki yana kallonsu yace, “ga yaranka nan, amma don ALLAH yakamata adinga kulawa” sannan ya shiga motarsa ya tayar yaran na d’aga masa hannu suna yimasa byebye, yana qoqarin barin wajen da sauri shurahbil ya iskosa tare da duqowa ta saiti jikin glass d’insa yace “afuwa alhaji, dama kasan yaran nan ne?” Girgiza kai mutumen yayi don yafahimci gaba d’aya shurahbil qurciya na damunsa, girmane kawai ya rigayi hankali saboda yanayin yanda yake magana, abun nasa kamar rashin iya magana kamar kuma isa da jijji da kai a tattare dashi, kallonsa yayi sannan yace, “Ban sansu ba kuma ban san ko suwaye su ba, Amma abu d’aya nasani shine tun wajen da sukayi accident dana ganesu jikina yabani cewa kamar akwai wata alaqa tsakanin ni dasu kuma araina naji ina sonsu har acikin zuciyata hakan yasa nabiyo bayanku lokacin da kuka taho dasu, ina fatar jikin iyayen nasu da sauqi saboda tsaurin tambayoyinka d’azun sun kasa barina na tambayi hakan tun farko” sinne kai qasa yayi yana sosa qeyar kansa had’e da cewa “kayi hak’uri Alhaji naji tsorone araina saboda yanda duniyar tamu ta koma.” “Babu komai in sha ALLAH ka gaida iyayen nasu, in sha ALLAH gobe zanzo nadubasu saboda marece yayi yanzu.” “Shikenan Alhaji Amma shi mahaifin nasu ALLAH yayi masa cikawa, mahaifiyarsu kuma anyi nasarar yimata tiyata anciro wasu ‘yan biyun” da motar na slow amma alhaji najin haka ya kashe motar yana sallallami kai kace wani shaqiqin sane, yajima yana jajanta abun aransa tare dayi masa addu’a sannan yabar wajen bayan ya bashi complement card d’insa. Yana barin wajen yanufi inda twins d’in suke zaune agaban motar suna wasarsu hankali kwance yaje yaja hannuwansu ya nufi inda su Abba suke riqe dasu… Suna isa Abba ya miqa masu hannuwa alamar suje wajensa, da gudu suka isa tamkar sun sanshi ya rungumesu yana kallonsu d’aya bayan d’aya yana jin wani irin sonsu da k’aunarsu nashiga zuciyarsa, kallo d’aya zakayi masu kasan kamarsu sak da mahifinsu tamkar an tsaga kara hasken fatar mahaifiyarsu ne kad’ai suka d’auko, hawaye ne suka zubo masa a idanuwa yagoge had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “ALLAH sarki batool, Ashe rabon wu ‘yannan jikokin nawa yasa kika iya jurewa rabuwa dani bayan kinsan irin tsantsar so da k’aunar da nanuna maki acikin ‘ya’yana, wacce har takasa b’oyuwa azuciyata, har kikayi nesa dani ban dena jin wannan qaunar taki araina ba, ubangiji ALLAH ya tashi kafad’unki, ALLAH yabaki lafiya kiga yanda soyayyarki ta dinga lunkuwa a kowace rana cikin shekarunnan da bakya tare dani.” Haka Abba yayita suruttansa tamkar wanda yafara zarewa yayinda yaran daya d’ora saman qafafuwansa suke jan d’an farin gashin dake shimfid’e a fuskarsa. Tuni su uncle h suka kira matansu suka sanar dasu halin da ake ciki wanda nan take family da suka had’u don walimar tarbarsu da Abba ya shirya suka fara koke koke, baran mahaifiyar batool da kad’an yarage itama arasata saboda matsananciyar fad’uwar da tayi a some, tajima kafin asamu ta farfad’o, kuka takeyi sosai tana roqon ALLAH ya sassautawa ‘yar tata kuma yajiqan mijinta, nan take duk aka watse jikin kowa a sanyaye, asibitin wasu suka nufa wasu kuma suka wuce gidajensu saboda basu sanar da mazansu ba, kafin kace me tuni asibitin tafara samun halartar ‘yan uwa da abokanan arziqin Abba da ‘yan uwansa tako ina, duk wanda yaji labarin abunda yafaru saiya zuddarwa da yaran hawaye domin har zuwa lokacin ita batool d’in bata farfad’oba, Dr sadeeq ne yadawo wajensu uncle akan zancen gawar Abu sumayya da suka buqaci abasu akace sai zuwa gobe idan police d’in da suka tsaya sunzo sunsa hannu, hakan yamatuqar qonawa Uncle Hassan rai da yasa yanata fad’a har saida Abba yabashi haquri shida Dr sadeeq sannan yayi shiru. Ita dai mahaifiyar batool hajia salmah abu yakashe mata biyu, nafarko damuwar halin da ‘yarta ke ciki na biyu kuma maraicin da wud’annan qananan yara har su hud’u zasu fuskanta, tayi farincikin kyauta da kuma ni’imar da Allah yayiwa ‘yar tata amma sam damuwa takasa barin haka ya bayyana a fuskarta, ita da mahaifiyar shurahbil ne suka zauna zaman jinyar batool da kuma kula jariranta, yayinda Abba yace matar uncle hussain da kuma abokiyar zaman hajia salmah wacce ake kira da Rabi’atu su zauna gida sukula da yara da hidimar abinci, Tun daga Abba har su uncle h babu wanda yakoma sakama bakinsa wani abun tun safe, hakan yasa bayan sallar magrib hajia salmah da suke kira da hajia mama ta kallesu had’e da cewa, “ya kamata ace damu daku duka mun fawwalawa ALLAH komai, mudangana da tsarin da yayo mana domin bamusan dalilinsa nayin haka ba, don ALLAH ku daure ku zauna kuci abinci kada kuma wani abun ya sameku.” Wata qatuwar kula tajawo ta mik’awa shurahbil da isowarsa kenan shima yadawo daga masallaci tace, “ungo nan shurahbil je kazubawa iyayenka abincinan suci kuma kaima don ALLAH ka tabbatar ka zauna kaci naka” “To hajia mama, Ina yarana suke?.” “Kagansu nan har sunyi bacci.” Tafad’a tana miqa masa plates da spoons, karb’a yayi had’e da cewa, “yakamata hajia akirawo zainab tawuce dasu gida ta watsa masu ruwa, yau sun matuqar jigata sosai, donma yaro yana yaro ai da sai jikinsu yafad’a masu, amma kingansu nan yau sau uku suna barci suna tashi wannan shine na hud’u.” “Hmmmm! Shurahbil kenan!, ai dolene suyishi, baccin rashine ALLAH dai yajiqan mahaifinsu.” ya amsa da amin sannan ya wuce inda ya hangosu acan cikin wata runfa da aka tanada domin patient relatives. Gaida iyayen nashi yayi tare da qoqarin bud’e kular bayan ya ajiye uncle hussain ya dakatar dashi, “kaje dashi can cikin mota saboda bazan iya ci anan ba sai dai kosu alhaji idan zasu iya su.” kallonsa Abba yayi sannan yace, “Kana tunanin abunda duk baibar kaba zai barmune mu?, Aje dashi duka cikin motar gamunan zuwa.” Haka shurahbil ya sake kinkimar kular abincin da plates yakai cikin mota ya d’ibi nasa a plate ya rufe da wani plate d’in sannan yabaro wajen, masallaci yakoma yaci nasa duk da bawani ci yayi ba d’an tsakurane kawai yayi saboda hajia mama data had’asa da ALLAH, badon haka ba bazai iya cin abinci acikin asibiti ba. Saida ya kwatanta sun kammala ci suma sannan yaje ya d’auko masu lemu da ruwan da a kazo dasu na gora ya kai masu ya kwaso kayan da suka gama cin abincin ya maido wajensu hajia mama. STORY CONTINUES BELOW  Sosai Abba yaso yaji takamammen bayani akan lafiyar batool amma hakan ya cutara saboda tsoron yanayin da zai iya shiga, tamatuqar wahala saboda ana gama mata tiyata lumfashinta ya d’auke, kusan likitoci bakwaine suka taru akanta kafin su samo da taimakon ALLAH lumfashin ya dawo, shima d’in da qyar take fiddashi wanda sanadiyar hakanne ake shiga da Oxygen aguje saboda ya taimaka mata, daga lokacin da akayi mata aikin zuwa dare ta shanye tukunya hud’u na oxygen, sai bayan sunga lumfashin nata ya daidaita ne kuma suka fara qoqarin treatment d’in raunin da taji a fuska duk da dai and’an bata emergency care kafin akawota nan. taji rauni sosai sabod duk glass d’in mota ya yanke mata fuska har saida aka ciccire mata wani da ya shige, idanuwanta kad’aine ALLAH ya kare basu samu wata matsala ta sokewa a xahiri ba ko kuma wani internal injury aciki ba, Amma hatta kanta ya bugu sosai wanda Dr odugun ya sanarwa dasu uncle h sai ta farka za’a iya gano cewa bata samu wata matsala acikinsa ba idan anyi gwaje gwaje, kallo d’aya zaka yimata kasan tanajin jiki saboda yanda aka nannad’e mata fuska da bandage ba’a bari kowa yashiga d’akin sai nurses da kuma masu jinyarta suma d’in saida dalili. Jariran kuwa tunda aka cirosu Dr imaan ta karasu ga nonon mahaifiyarsu suka d’an tsots-tsotsa har yanzu ba’a basu komai ba, sunyi kukan har sun gaji amma Dr tace kawai asa masu drip zuwa gobe tunda har lokacin mahaifiyarsu bata farko ba, Abba dasu uncle basu bar asibitin ba sai misalin qarfe sha biyu da rabi na dare bayan shurahbil yaje gida ya watso ruwa ya dawo shi da zainab sister d’insa ta d’auki su hassana sannan su Abba suka wuce da ita gida saboda anan shurahbil zai kwana Koda za’a buqaci wani abun…. _*ALLAH KAJIK’AN IYAYEN MU*_👏🏻😭 [6/15, 11:34 PM] My S Nomba: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKIN KINE SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO (OUM AFFAN)*❤️ _ALHAMDULILLAH INA GODIYA GA RABBIL IZZATI WAL JABARUD DAYA BANI IKON SAKE DAWO MAKU DA WANNAN SABON LITTAFI NAWA DAKE CIKE DA ‘DIMBIN DARUSSA DA NAKE FATAN SUZAMO TSANEN DA ZAMU IYA TAKAWA WAJEN GYARA KURA-KURANMU, WANNAN LITTAFI GABA ‘DAYA QIRQIRARSA NAYI BISA LA’AKARI DA WASU ABUBUWAN DAKE FARUWA ACIKIN RAYUWARMU TA YAU DA KULLUM DON HAKA IDAN KAGA YAYI KAMA DA RAYUWAR KA/KI TO AKASINE KAWAI, SAI MUYI QOQARIN GYARAWA, FATANA ALLAH YA YAFEMUN KURAKURAN DA ZASUZO DAGA CIKINSA KUMA YASA DANI DAKU MUYI TARAYYA ACIKIN LADAR DA ZATAZO ACIKI👏🏻, HAR ILA YAU BAZAN MANTA DA ADDU’AR FATAN ALKHAIRI AGAREKU BA *YA HAJJA CE* DA KUMA TAWAN *SALMA ABALI (LITTLE PRINCESS)* INA ROK’ON ALLAH DA YATABBATAR MAKU DA ALKHAIRANSA KUDA AHALINKU ADUK INDA KUKE, *MLF*_💋👏🏻 Page___1💎 Tafe suke cikin wata kyakkyawar mota k’irar BMW da kallo d’aya zakayi mata kasan cewa sabuwace dal da ba’a dad’e da fiddota acikin ledar taba saboda yanda take faman sheqi da qyalli, cikin natsuwa matuqin motar ke tuqinsa yayin da wacce ke zaune agefensa da tsohon cikinta dake nuna alamar ko meye aciki neman fitowa yakeyi akoda yaushe, muskutawa tayi sannan tajuyo cikin zaquwa had’e da kallonsa tana cewa, “Abu sumayya wai wannan wace irin tafiya ce kakeyi haka?, Don ALLAH kataka motar nan da sauri, wlh namatsu naganeni agaban Abbana da kuma ummata.” yanayin yanda take maganar kad’ai tana faman kashe murya shi zai tabbatar da cewa ita d’in matarsa ce, cikin k’warewa da iya tuqi ya juya sitarin motarsa ya shiga kwanar dake gabansa tare da d’an qara gudun motar kad’an sannan yace, “Gimbiya! haka yayi maki?.” Yafad’i hakan batare daya d’auke idanuwansa daga kan titin da yake kallo ba “kad’an qara mana.” tafad’a tare da juyawa ta sit d’in bayansu tana kallon yaransu ‘yan mata su biyu dake kwance bacci ya d’aukesu, kallo d’aya zakayiwa yaran katabbatar da cewa ‘yan biyune saboda tsantsar kamar da sukeyi da junansu, wata kyakkyawar ajiyar zuciya tayi had’e da shafa tulelen cikin dake jikinta tace, STORY CONTINUES BELOW  “Alhamdulillah, Abu sumayya namatsu mu isa gida naga farincikin da zai bayyana a fuskar Abbana idan yaganeni tare da wud’annan kyawawan jikoki da ALLAH ya albarkacesa dasu bayan rabuwarmu dashi na tsawon shekaru bakwai, ga kuma wata kyautar agefe tare dani wacce nake fatar Allah yasa takwaransa ne aciki, natabbata hakan zai qara sakasa cikin farinciki sosai, Kuma yasake gusar masa da abun da nayi Masa azuciya” “To ALLAH ya saukeki lafiya gimbiya kuma yabamu abunda muke fata don cikar burinmu da kuma tabbatuwar farincikin Abban da kike hasashe.” “Amin Abu sumayya.” tafad’a tare da d’ora kanta saman kafad’arsa, shirune yabiyo baya na tsawon mintuna biyar kafin tasake cewa, “Wlh gani nakeyi kamar bama tafiya, hanyar tamkar ana qaramata tsawo, wataqil don na jima ban bita neba?.” murmushi yayi had’e da cewa “Kai gimbiya d’oki dai ne kikeyi, Amma ai ba laifi ina tafiya sosai, kiyi hak’uri, ai sannu a hankali zamu isa in sha ALLAH kilometers biyar ne yarage mana, kinji hausawa nacewa SANNU SANNU bata hana zuwa….” Kafin yarufe baki yaji tace, “Sai dai adad’e ba’a kai ba, kuma ni shine bana so.” taqarasa maganar tana turo baki had’e da mik’ewa zaune daidai, “Abu sumayya naji marata tad’an murd’a.” Rage gudun yayi had’e da cewa, “Subhanallah Gimbiya ko abun yazo ne?.” Yafad’a tare da juyowa yana kallonta a d’an firgice, yatsina fuska tayi sannan tace, “Bana tsammanin hakan, saboda idd na sai next month on 13 yanzu kuwa kaga muna 25 ne dis month.” Tana rufe baki wata qatuwar mota tayo cikinsu aguje tare da gittawa agabansu, ji kakeyi qiiiiiiiiii…gigigigif..karaf, tabugi motarsu tafad’a jikin wata motar dake tafe bayansu itama tana k’ok’arin kaucewa ta d’ayan gefen, sosai yake qoqarin juyar da staring motar da dukkanin k’arfinsa da kuma gwanewarsa amma da yake duk qaddarar da ALLAH yatsaro akan bayinsa ko suna so ko basa so sai wannan alqalamin da aka dad’e da rubuta qaddarsa ya tabbatar da ita agaresa, duk iya qoqarinsa kasa iya sarrafa motar yayi balle ya samu nasarar tsaida ita waje d’aya, ganin haka yasashi qoqarin riqo matarsa da tuni kanta ya bugi glass d’in motar yafita tacan waje yayin da gangar jikinta na acikin motar, cikin yanayin fad’uwar gaba da kuma firgici yafara k’ok’arin jawota sai ji yayi sun bugi wani abu da yasa motar tasu tsayawa cak, daidai lokacin shi kuma kansa yabugi dashboard d’in motar da k’arfi wanda yasa nan take yaji gaba d’aya na’urorin dake aiki a sassan jikinsa sun tsaya cak, hatta jinsa da ganinsa ji yayi suma sun d’auke alokaci d’aya, cikin tashin hankali mutanen da suka tsaitsaya akan titin suna salati ganin yanda wannan tashin hankalin ke faruwa sukayo kansu ganin motar ta tsaya don kawo masu d’auki, gaba d’aya motar ta nad’e waje d’aya sanadiyar wani makeken dutsi da suka buga, kallo d’aya zaka yiwa motar ka rantse baza’a samu rayuwar ko d’aya daga cikin mutanen dake cikin taba, ganin jini na malalowa tak’ark’ashin motar ya sanya mutanen himmatuwa wajen b’alla gambun motar ta kowane gefe, shi suka fara jawowa kafin suyi nasarar fiddo da matarsa fuskarta gaba d’aya jini ya wanketa ta yanda bazaka iya gane ko wace itaba, cikin tashin hankali suka ida fiddo da ita daga cikin motar tamkar gawa saboda ko motsi ba tayi, hankalinsu bai tashi ba sai lokacin da suka lura da tulelen cikin dake jikinta sai faman motsi abunda ke ciki yake ga kuma jini d’aya b’alle mata na faman kwararowa daga k’asanta, cikin rud’ewa wani daga cikinsu ya d’ago kai yana kallon wud’anda ke kan mijin nata yace, “Matarnan tana buqatar taimakon gaggawa.” Bai rufe baki ba mijin nata da tun d’azu ake faman yayyafa masa ruwa ya farfad’o tare da bud’e ido, ko kad’an babu alamar k’warzane ajikinsa da zai nuna yaji ciwo wanda hakan yaja hankalin mutanen akan doguwar sumace yayi suka fara yayyafa masa ruwa, k’ok’arin bud’e baki yayi yayi magana amma yakasa saboda lumfashinsa da yakejin yana qoqarin fin qarfins, yana gani aka tallabi matarsa aka nufi cikin wata motar da ita don ceto rayuwar abunda ke cikinta don gaba d’aya alokacin bata rayuwarta suke ba saboda ganin yanda cikin nata ke motsi kamar zai fasa cikin ya fito, sake yunqurawa yayi zaiyi magana idanuwansa na hawaye yana kallon yanda cikin nata ke motsi amma yakasa, kamar wanda aka tsikara da qarfi yajuyo ya maido kallonsa awajen motar tare da d’aga hannu yana nuna masu, da k’yar yabud’e baki yace, “‘ya’yana…” Bai k’ara saba jini yafara fitar masa abaki tare da sakin hannunsa ya fad’i qasa, da gudu wasu suka d’aukesa suka nufi motar da akasa matarsa aciki lokacin har ana qoqarin barin wajen aka sakashi shima cikin motar tabar wajen dasu aguje, yayin da wasu suka nufi wajen motar suka fara qoqarin b’alla gambunanta na baya, koda sukayi nasarar b’alle gambunan motar basu ga komaiba a saman sit d’in sai da suka leqa a k’arqashin motar sannan suka hango qananan yara a qarqashi, gashi motar ta molak’e waje d’aya babu isasshen wajen da za’a iya jawosu hakan ya matuqar tayarwa da mutanen wajen hankali saboda rashin sanin makomar yaran da kuma sanin ko awane hali suke ciki awajen. STORY CONTINUES BELOW  Anan sukayi cirko cirko suna shawarar yanda za’ayi a fiddo yaran, wani mutumne daga cikinsu yabada shawarar tunda akwai wani gari dake nan gaba kad’an aje asamo k’wararrun masu gyaran mota da suka iya kwanceta da had’ewa suzo su kwance motar gaba d’aya a fiddo yaran ko nawane shi zai biyasu, haka kuwa akayi cikin mintuna ashirin wane yaje yazo dasu su biyu d’auke da kayan aiki, nan take suka fara aikinsu cikin k’warewa wanda cikin minti 30 sai gashi sun raba body d’in motar da shimfid’ar qasanta, da sauri aka ciro yaran har lokacin gaba d’ayansu bacci sukeyi, bazaka tab’a cewa daga cikin motar aka fiddosu ba saboda ba wadda tayi ko qwarzane acikinsu inba d’ayar data d’an karce agefen kuncinta ba wanda ga alama wani qarfene ya karjeta, “ALLAHU AKBAR” wud’an ke wajen suka fad’a cikin mamaki da kuma tsoron ALLAH da gasgata ikonsa don gaba d’aya babu wanda yasa ran za’a fiddosu da rayuwa saboda la’akari da yanda motar ta mokad’e waje d’aya, ana hakane suka jiyo qarar waya acikin motar a gefen da aka ciro matar, d’aya daga cikin sune yaje yana bin sautin qarar wayar dake cikin jikkar ya d’auko tare da ciro wayar ya d’aga. “Assalamu alaikum.” Shine abunda yafad’a kafin yaji an amsa masa ta d’aya b’angaren da, “wa’alaikassalam.” Cire wayar yayi a kunnensa ya duba sunan dake yawo a screen d’in wayar yaga ansa _ABBANA_ hakan yasa yayi saurin maida wayar a kunnensa yana kallon sauran mutanen dake wajen tare dashi sannan yayiwa mutumen da tun d’azu sai faman tambaya yakeyi ina mai wayar bayanin abunda ke faruwa, Nan take yarud’e yafara tambayarsa adaidai wane wajene abun yafaru, cikakken bayanin yayi masa don akwai buqatar yazo yakarb’i yaran dake wajensu kafin yasan da komai sannan ya kashe wayar, Kallon wud’anda suka kwance motar mutumen da yasa aka kirawosu yayi had’e da cewa, “bayin ALLAH nawane za’a biyaku?.” Gaba d’aya suka amsa masa da “A’a alhaji, kabar kud’inka don ALLAH mukayi, ubangiji ALLAH yatsare kuma yatashi kafad’un iyayen yaran nan,” suna gama fad’ar haka suka d’auki kayan aikinsu fuskokinsu cike da tausayin halin da akace masu iyayen yaran na ciki sannan suka wuce, duk mutanen dake wajen godiya tare da addu’ar fatan alkhairi suka yimasu saboda karamci da ‘yan uwantakar addini da suka nuna. Kasan cewar kilometers biyar ne yarage a tsakanin inda akayi had’arin da kuma cikin garin kano inda iyayen wud’annan yaran suka nufa yasa Abban nata d’aukar dogon lokaci kafin ya iso wajen, hakan yasa mutanen duk suka fara watsewa d’aya bayan d’aya lokacin har yaran sun farka sun fara kukan ina iyayensu suke, A b’an garen sauran motocin da akayi had’arin dasu kuwa dama shi drivern babbar motar daya bugi motarsu tafad’a can gefe koda aka fiddosa yarasu, haka itama qaramar motar dake gefensu da yake irin golb d’innan ce ta haya mutum hud’u sun rasu, uku kuma sunyi rauni sosai ciki hadda drivern motar suma anwuce dasu assibiti tun d’azu, Sosai yaran ke kuka anyi rarrashi har angaji amma sunqiyin shiru har saida wannan mutumen yaje yabud’e cikin motarsa ya d’auko gorar ruwa yadawo da ita riqe ga hannunsa ya nunama d’ayar yace, “Zaki sha ruwa?” Batayi magana ba amma yanda take kallon gorar ruwan shizai tabbatar maka da tanada buqatarsu, bud’e murfin gorar yayi sannan ya azamata abaki ba musu tafara sha, saida tasha sosai sannan ta jaye bakinta daga gorar tana sauke ajiyar zuciya, ‘yar uwarta ya nufa da gorar Amma ga mamakinsa sai yaga ta sake fashewa da kuka sosai fiye da wanda takeyi farko tare da kauda kanta gefe, hakan yasa ya janye gorar, yamiqa hannu tana shessheka ya karb’eta, ajiyar zuciya ya sauke don ko kad’an baya son kukan yara, kallonta yayi ya sake kallon ‘yar uwarta da itama sai faman ajiyar zuciya takeyi tasa hannunta cikin baki tana tsutsa yaji inama ace wud’annan yaran nasa ne, kamarsu d’aya babu inda suka banbanta inba yanzu da d’ayar ta karce a gefen kuncinta ba bazaka tab’a iya banbancesu ba, wanda hakan zai tabbatar maka da cewa su d’in ‘yan biyune, ‘yan biyunma irin wud’anda ake kira da (identical twins), gaba d’aya shekarunsu bazasu wuce 3 ba aduniya Amma kana ganinsu zakasan suna da d’an banzar wayau sosai, yana wannan tunanin ne wayar da aka ciro acikin motar dake hannun wanda ke riqe da d’ayar tayi qara, d’agawa yayi yaji Abban yace, “bawan ALLAH gani na iso wajen.” Yafad’a muryarsa na rawa tare da yin parking motarsa daidai inda yaga babbar motar tafad’i da d’ai d’ai kun mutane a tsaitsaye awajen, wani kyakkyawan dattijo ne fari tas yafito daga cikin motar riqe da sanda qafafuwansa na rawa ko d’aukarsa basayi sai wani saurayi daya fito daga mazaunin driver da alama shiya tuqo motar tare da wasu maza su biyu kamarsu d’aya da alama suma tagwayene ko kuma wa da qane suka fito daga cikin bayan motar suma dai d’in sun manyanta amma ba kamar tsohon daya fara fitowa ba da gaba d’aya gashin dake kansa da fuskarsa farine tas ya cika da furfura, har lokacin wayar na akunnensa suna magana da mutumen, juyawa yayi ya hangosu tare da d’aga masu hannu da sauri duk suka nufo wajen in banda d’an saurayin daya tsaya yana tattakawa tare da tsohon, bayan sun iso wajen duk aka mimmik’a hannuwa aka gaggaisa ya nuna d’ayansu yace, STORY CONTINUES BELOW  “Ranka ya dad’e kaine Abba ko wannan?.” Da sauri duk suka juya suna kallon tsohon dake takowa riqe da sandarsa sukace “wancan shine Abba kuma yayanmu, Ina bayin ALLAHn da kukace sunyi had’ari suke?.” Saida ya qaraso aka sake gaisawa sannan yace, “kuyi haquri anwuce asibiti dasu, Amma ga wannan itace wayar da aka gani acikin motar tare da wud’annan yaran” yaqarasa maganar tare da miqa masu wayar sannan suka ajiye yaran agabansu shida d’ayan mutumen dake riqe da d’ayar yarinyar.” Sai alokacin suka lura da qananan yaran ‘yan mata dake wajen, cike da mamki suka bisu da kallo saboda tsantsar kamar da sukeyi da mahaifinsu tare da girmama ikon ALLAH ganin yadda motar tayi amma yafidda yaran lafiya klw batare da sunji ciwo ba, kad’an ya rage tsohon da ake kira da Abba yafad’i saboda tsantsar kamar yaran da mijin ‘yar tasa daya gani, da sauri suka riqesa cikin kuka yace, “Ina ‘yata da kuma mijin nata suke?.” “Haba Yaya kabi ahankali mana kada kafad’i, suna assibiti wud’an yaransu ne akace” “Innalillahi wainna ilaihirrajiun, nagani hussaini ga kamar yaron nan sak atare dasu, don ALLAH ku kaini asibitin inga halin da ‘yata take ciki, shekara bakwai kenan ina son ganinta Ina mararin had’a idanuwa da ita, ku kaini kona samu inroqi yafiyarta” yaqarasa maganar yana kuka jikinsa na rawa, Ganin haka yasa suka nemi da akaisu asibitin da aka nufa dasu ko kuma afad’a masu suje saboda yanda tsohon ke neman birkice masu awajen duk su kace basuda masaniya akan kowace asibiti ce amma suna da tabbacin kano aka nufa dasu. Wani daga cikin wud’anda ke can gefe tsayene yace abari yakira d’an uwansa yaji ko wace assibiti ce saboda da motarsu ce aka d’aukesu, bayan yakira sane ya sanar masa da cewa suna Aminu kano teaching hospital sannan yafad’a masu, godiya suka yimasu sosai tare da fiddo da kud’ad’en da basusan ko nawa bane suka basu sannan suka d’auki yaran da sauran abubuwan da aka basu da aka gani cikin motar suka kama hanyar kano kowanensu hankalinsa atashe, Banda kukan Abba babu abunda kakeji acikin motar hatta yaran ana shiga mota suka koma bacci, Shikuwa mutumen daya d’aukowa yaran ruwa daga cikin motarsa ji yayi bazai iya tafiyaba saboda wata irin soyayyar yaran da yaji tashiga ransa, ji yayi yana kwad’ayin sanin ko suwaye su da kuma halin da iyayensu ke ciki hakan yasa shima yaja motarsa yabi bayansu… _Hmmmm….! tirqashi!💔 Shin kuna so kuji yanda cigaban wannan labarin zai kasance? Shin ko zaku iya bani had’in kai tare da guntun lokacinku da kuma qarfafamun guiwa wajen warware maku bakin zaren wannan labarin cikin sauqi kuma daki daki yanda zaku fahimta? Comment d’inku shine amsar tambayoyina kuma shine zai tabbatar mun da cewa eh kuna buqata kuma kuna tare dani😍, shiiiii🤫 nasan zukatanku cike suke da tarin tambayoyi acikin wannan labarin kamar haka_ *WAYE ABU SUMAYYA DA GIMBIYARSA?*😅 *MEYE ALAQAR ABBA DA GIMBIYAR ABU SUMAYYA?*😡 *MEYA RABA GIMBIYAR ABU SUMAYYA DA IYAYENTA NA TSAWON SHEKARA BAKWAI?*😱 *AWANE HALI ABU SUMAYYA DA GIMBIYARSA KE CIKI?*😰 *MEYE TUSHEN WANNAN LABARIN?*🙇🏻‍♀️ *SHIN WANENE MUTUMEN DA YABI BAYANSU ABBA DA MOTA?*🚙 _Relax! kubiyoni sannu a hankali zaku samu duka amsoshin wud’annan tambayoyin acikin wannan sabon labari nawa dake cike da sabon salo mai suna *SANNU SANNU* Bata hana zuwa…🚶‍♀️🚶‍♀️🚶‍♀️_ *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏🏻😭_* [6/15, 11:34 PM] My S Nomba: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  _Jinjina agareku masoyana, fatan alkhairi da kuma fatan tabbatuwa cikin amincin ALLAH da yardarsa akoda yaushe Kuma cikin kowane hali shine addu’ata agareku, tabbas naga karamci, halacci, yarda da kuma zallar soyayya agareku, nayi farinciki da kuma murna ganin irin kyakkyawar tarba dana samu daga wajenku akowane group wanda hakan yatabbatar mani da cewa nid’in takuce akoda yaushe, ngd ngd ngd sosai ALLAH yadubi zuciyar kowanenku yabiya masa da buqatunsa na alkhairi👏🏻 Ina farinciki da kuka nuna mani cewa yanda nake ikirarin cewa ina sonku FILLAH kuma kuna so na FILLAH😍 in sha ALLAH zan zage damtse wajen ganin kun ilmantu kuma kun nishad’antu da wannan littafi,😅fatana shine ku juri bina daki daki tare da qarfafamun guiwa, ni kuma in sha ALLAH nayi maku alqawarin da *SANNU SANNU* Zaku samu tarin fad’akarwa da kuma farinciki marar misaltuwa acikin wannan labarin🥰MUCH LUV FILLAH na wajena😘❤️_ Page___2💎 Aguje matashin saurayin ke tafiya saboda yanda Abba ke faman reren kuka tare da azazzalarsa akan yayi sauri, kusan minti ishirin da biyar suka d’auka kafin su isa cikin garin kano, Hanyar asibitin suka nufa zuciyoyinsu cike da fargabar abunda zasu riska, suna isa ko daidaita parking basuyi ba Abba yafara kiciniyar bud’e gambun motar da sauri saurayin ya danna lock d’in motar had’e da cewa, “Haba Abba! Me kake shirin yi hakanne, karka manta babu abunda muke iya canzawa daga qaddarar da ALLAH yatsaro agaremu da kuma sauran bayinsa, kabi ahankali in Sha ALLAH babu abunda ya samesu.” ko jin abunda yake fad’a Abba ba yayi sai faman kica niyar bud’e motar yafita kawai yakeyi amma yakasa saboda lock d’in daya saka mata, ganin haka yasa wanda d’azu Abba yakira da hussaini ya dafa kafad’ar matashin had’e da cewa, “Shurahbil bud’e masa kaji ko!.” “Amma uncle h….” Bai qarasa ba yayi saurin d’aga masa hannu da sauri shurahbil yacire lock d’in ba tare daya sake cewa komai ba suka fito tare da bud’ewa Abba da tuni yakai maqurar b’acin rai da hasala kawai yanayin da yake jin kansa acikine yasa bai tsaya bi takan saba, fitowa yayi har yana neman fad’uwa sukayi saurin riqesa ba tare da sunce dashi komai ba suka nufi emergency ward, girgiza kai shurahbil yayi tare da bin bayansu hannunsa na riqe da ‘yan biyun da tunda sukaji tsayawar motar suka tashi daga baccin da sukeyi atare, Har sun kusa shiga emergency d’an uwan uncle hussain wanda shine hassan Kuma mahaifin shurahbil ya juyo yace, “katsaya daga waje kafin muji halin da suke ciki, idan zai yuyu ma ka koma cikin mota da yaran nan, idan akwai buqatar kazo zamu nemeka.” Babu musu yakoma cikin motar shida yaran tare da ciro wayarsa yajawo game d’in race na motoci yanayi, dama aikinsa kenan aduk lokacin daya kad’aita shi kad’ai, yaran na ganin haka duk suka dawo daga inda suke zaune baya zuwa gaba inda yake zaune suka haye masa jiki suna kallo shi kuma mahaifinsa ya ida qarasawa can cikin emergency ward d’in tare dasu Abba suna tambayar mutanen da sukazo daga k’auyen da accident d’in yafaru, sunfi minti goma shabiyar kafin su samu su had’u da d’aya daga cikin wud’anda suka kawo su Abu sumayya d’in wanda shikad’aine ya tsaya awajen, sauran kuwa tuni suka wuce bayan sunga likitocin sun karb’esu, shima d’in saida wannan bawan ALLAHn yaje yakirawo police tukuna suka amshesu. Hannu yabasu suka gaisa kafin yace, “kune iyayen bayin ALLAHn da mukazo dasu?.” Cikin rawar murya Abba ya amsa masa da “eh bawan ALLAH mune, Ina zamu ganesu ne, suna ina?.” Shiru mutumen yayi kafin ya d’an nisa fuskarsa cike da damuwa yace, “likitoci nakan duba su amma suna buqatar addu’ah sosai, shi namijin sun wuce da shi ICU (internatal care unit) ita kuma macen suntafi da ita gyni emergency.” Shiru yayi tare da ciro gilashin idanuwansa yasa gefen babbar rigarsa ya goge k’wallan da suka zubo masa sannan yaci gaba da cewa, “dukkaninsu suna cikin wani mawuyacin halin da addu’armu kawai suke buqata, amma har yanzu ina kallon yanayin da naga baiwar ALLAHn nan aciki kafin suwuce da ita, abun gwanin ban tausayi yanda abun dake cikinta ke faman motsi Yana neman taimako yayin da ita d’in takasa d’aga ko d’an yatsanta da zaya iya bashi koda k’warin guiwa ne na second d’aya, Ina addu’a ubangiji yadubi karamci da tausayi irin na uwa alokacin da rauni yasa takasa bawa d’an dake cikinta taimako da yakawo masu tallafi da kuma agajinsa domin ceto duka rayuwarsu.” STORY CONTINUES BELOW  Wani irin jirine ya d’ibi su uncle hussain jin yanayin da ‘yar d’an uwan nasu ke ciki daya sasu ja da baya tare da fad’awa zaune saman kujerun dake bayansu saboda tsananin tashin hankali suna furta kalmar, “innalillahi wainna ilaihirrajiun.” dama shi Abba tunda sukazo suka samu suka lallab’asa ya zauna saboda bawata lafiyar qafafune keda shiba balle yajuri iya tsayuwa na tsawon lokaci, lokacin da yaji wannan labarin sai kawai ya sake fashewa da wani sabon kukan da dama tun d’azu yake yin abunsa saboda rashin sanin awane hali gudan jinin tasa take ciki, kalmar shahadar shima ya Fara maimaitawa had’e da cewa, “Amantu billahi, qadarallahu wama sha’a fa’ala.” cikin tausayawa mutumen ke kallonsu kafin yace, “hak’uri zakuyi tare da addu’a kuma kusamu ku matsa inda suke nasan gab ake da anemi ‘yan uwansu, ni ina kan hanya tane ta zuwana garin minna, dama tsammanin jiran isowarku anan kamar yanda d’an uwana ya sanar mun awaya shine dalilin daya tsaidani anan saboda nasan kuna isowa dole direct nan (emergency) zaku zo, don haka ni zan wuce, ga wud’annan takardun acikin aljihun namijin aka tsincesu” yaqarasa maganar tare da miqawa Uncle Hassan takardun, har zai tafi saiga wani Dr da shine suka karb’i case d’in anan emergency ya iso wajen had’e da kallonsa yace “Ahhhh, ranka ya dad’e baka wuce bane?” “Eh Dr sadeeq Amma yanzunnan zan tafi in Sha ALLAH, wud’annan sune patient relatives na mutanen da muka kawo” yabashi amsa tare da nuna masa su Abba dake zaune kamar ruwa yacisu. “Masha Allah, ranka ya dad’e to ALLAH ya kiyaye ya kuma saka da alkhairi” “Amin ya rabbhi” yafad’a tare da bashi hannu sukayi musa baha, kallon su uncle h yayi tare da cewa “duk wani abu daya kamata wannan Dr zai taimaka maku insha ALLAH, aminina ne sosai don haka ku kwantar da hankalinku, pls Dr you should consider…” har lokacin suna riqe da hannuwan juna. “I will in sha ALLAH” yabashi amsa sannan suka yimasa godiya ya wuce, Dr yace sutashi yayi masu jagora zuwa can ICU d’in sannan suje gyni emergency, juyowar da zasuyi wajen Abba sukaga wayam babu kowa a mazauninsa, hankalinsu tashe saboda sanin yanayin da yake ciki suka fara duddu basa acikin wajen basu ganesa ba, cikin tashin hankali suka yiwa Dr bayanin ko wayeshi da matsayinsa ga patient d’in yace, “karku damu, inaga yakasa jurewane yanufi can, kuzo mutafi can d’in.” A b’angaren Abba kuwa kamar yanda Dr yafad’a kasa jure zama awajen yayi hakan yasa yamiqe lokacin da suke magana ba tare da sun lura ba yakamo hanyar gyni emergency jikinsa na rawa sai faman had’a hanya yakeyi, babu abunda yake buqata alokacin irin yaga ‘yarsa kuma yasan ko awane hali take ciki, kasancewar dole sai yafito tacikin emergency ward d’in zai iya isa gyani emergency dake can gefe dasu yasa shurahbil ya hangosa yana harhad’a hanya tare da neman fad’uwa, da gudu yafita cikin motar ba tare da ya tsaya kula yaran dake tare dashi ba yanufi inda yake, da sauri ya qarasa wajen tare dasa duka hannayensa biyu ya rungu mosa yana fad’in, “Abba ina kuma zakaje haka kai kad’ai, Ina su uncle ne?.” ‘Dago kai yayi ya kallesa ba tare daya iya furta masa komai ba sai dai ya nuna masa gefen da gyni emergency take da yake ana iya hangota daga nan inda suke, jujjuyawa shurahbil yayi yana kallon ta gefe gefensu ko zai hango su uncle h amma ko alamarsu babu, hakan yasa yariqasa suka nufi wajen, sukuwa ‘yan biyun ganin yabar gambun motar abud’e yasa suka fito suma suna ‘yan dube dube ta gefen, dai dai lokacin mutumen daya biyo bayansu Abba da mota shima yayi parking motarsa wajen tare da fitowa da sauri, cike da mamaki ya nufo wajensu tare da kamo hannun d’ayar yace, “Ina zakuje ne?” “Baba zamuje yabamu game.” Tafad’a tana tsalle tsalle, tashi yayi ya leqa cikin motar yaga babu kowa aciki gashi kuma anbarta abud’e, gefe da gefe yakalla kuma baiga su uncle ba, hakan yasa ya rufe motar tare da ce masu, “to ina baban naku yaje?.” hanyar da shurahbil yabi suka nuna masa. Kallonsu yayi yaga yanda suka jigata yace “Zakuci abinci?” “Eh zamuci dama yunwa mukeji” suka fad’a atare “To kuzo muje” yafad’a tare da riqo hannuwansu, d’ayar ce ta wafce hannunta had’e da cewa, “ni bazan jeba.” Itama d’ayar ta wafce hannunta had’e da cewa “nima bazan jeba” haddasu maqale kafad’a, tsaye yayi yana kallon su cike da burgewa kafin yace, STORY CONTINUES BELOW  “To zaku zauna anan inje inkawo maku abinci?.” “Mu baba zamu bi.” “Haba yaran baba ai bakusan inda zaku ganesa ba tunda yayi nisa, ku zauna anan karkuje ko ina bari naje nakawo maku abinci kuci kunji ko?” “A’a sai dai ka kaimu wajen dady da ummie zasu bamu abinci muci ko hassana!” d’ayar tafad’a tana kallon ‘yar uwarta, “Eh, ke ummie ke baki ni kuma dadynah take bani abaki ko” Tsayawa yayi yana kallonsu cike da jin wani farinciki aransa wanda baisan dalilin saba, yanayin surutunsu na matuqar burgesa wanda yanzune ya gano wacce taqi karb’ar ruwa a hannunsa d’azu itace hassana kuma itace tafara cewa baza take ba, d’ayar kuma itace hussaina wacce ta d’an karce a gefen kuncinta na dama, wani irin tausayinsu ne yaji ya rufesa tunawo da halin da iyayen nasu keciki yayi tare da addu’ar ALLAH yatashe masu da kafad’unsu, juyawa bayansa yayi ya hango d’aya daga cikin security d’in asibitin yamik’e tare da isa wajensa yabashi hannu suka gaisa sannan yace “Don ALLAH ko zaka iya kula mani da yaran can kafin inje indawo?.” Ganinsa babban mutum yasa yayi saurin cewa, “Babu damuwa Alhaji indai zasu zauna.” Don yasan dole za’a shafa masa wani abun, komawa wajensu yayi yariqo hannunsu yace, “Yawwa yaran baba, kuzauna anan kafin babanku yadawo zanje nakawo maku abinci kunji ko?.” Da sauri yabar wajen yanufi wani waje da ake saida abinci cikin asibitin aransa yana addua’ar yana saqa wasu abubuwa. Cikin mintuna biyar yaje ya siyo abincin ya dawo ya taddasu tare da security d’in sai faman surutu suke yimasa tamkar sun sanshi, murmushi yayi sannan ya bud’e bayan motarsa ya d’auko wata carpet mai girma ya shinfid’a cikin inuwar tare da aje abincin hannunsa sannan ya jawosu ya zaunar dasu ya bud’e masu abincin ya tura masu a gabansu, d’aya daga cikin take away d’in da yayo ya sake d’auka ya miqawa security d’in dama donsa ya siya tare da gorar ruwa d’aya da kuma lemu yanata godiya. Kallonsa sukeyi sana kallon abincin batare da kowacensu tasa hannu ba yace, “kuci mana.” Girgiza masa kai sukayi alamun bazasu ciba yace “Meyasa” atare sukace “dady yake bani idan zanci” itama d’ayar tace, “ummie take bani abaki.” Shiru yayi kafin yajawo gorar ruwan d’aya ya wanke hannunsa tare da d’ibar abincin yafara basu abaki ahankali, idan yaba wannan yaba wannan yana jin wani irin farinciki ya mamaye masa zuciya. Shurahbil kuwa suna isa gyani emergency sukaga wasu nurses aguje sun wuce da oxygen cikin theater room d’in dake laqe da wajen, bayan kamar mintuna bayar suka wasu sun sake wucewa da wani aguje, tsaye sukayi tare da rashin sanin abunyi data inda zasu fara, sunyi minti uku a tsaye kafin suga wata docter tafito daga cikin wani office dake kallon d’akin theater d’in da sauri shurahbil ya tareta had’e da cewa, “Assalamu alaikum, don ALLAH Dr ko nanne aka kawo wata patient da suka samu accident mai juna biyu?” Don kallo d’aya zakayiwa matar katabbatar da cewa ita d’in cikakkiyar likita ce, “Eh nanne, yanzu haka ita aka gama yiwa tiyata, ko kune relatives nata?.” Ta tambayesa atak’aice “Eh mune Dr yafad’a tare da gyara tsayuwarsa da alama yana son jin qarin bayanine daga bakinta, amma ga mamakinsa sai yaga tawuce cikin d’akin ba tare data sake cewa komai ba, Dr sadeeq kuwa koda sukaje ICU d’in yashiga d’akin da ake duba Abu sumayya ya tarar ana k’ok’arin gyarasa saboda mai kowa mai komai ya amshi abunsa wato dai ALLAH yayi masa rasuwa, rufe idanuwa yayi cikin jimami tare da girgiza kai sannan yanufi wajen wani dr dake tsaye akan gawarsa yana qoqarin had’a bayanan tabbatar da mutuwarsa bayan dogon bincike da suka gudanar akanta, kallonsa yayi yace “Ahh..Dr sadeeq kadawo? Kadai ga yanda ALLAH yayi ikonsa akan wannan bawa nasa ko, ya samu internal injury ne cikin k’wak’walwarsa haka kuma zuciyarsa tabuga a sanadiyar tsoro da kuma fargabar daya ziyarcesa a lokaci d’aya Kuma sai akaci sa’a yana d’auke da hawan jini wanda shine ya qara tasiri wajen bugawar zuciyar tasa har tafashe” girgiza kai Dr sadeeq yayi had’e da cewa, STORY CONTINUES BELOW  “ALLAH sarki, ALLAH yajiqansa yayi Masa rahama, dama relatives d’insa ne suka iso” “Ok zaka iya sanar dasu.” “Nooo..bazan iya ba Dr naseer i feel their pain.” “Ba damuwa, bari naqarasa had’e bayanan sai naje na sanar dasu, hak’uri zasuyi don dukkaninmu ita muke jira” Sai bayan kusan mintuna biyar sannan suka fito tare da Dr naseer d’in suka nufi wajen da su uncle h suke tsaye, gaisawa suka farayi dashi sannan yayi masu bayanin ALLAH yayiwa patient d’insu wato Abu sumayya rasuwa…salati suka farayi tare da jinjina al’amarin, tabbas sunji ba dad’i rasa nagartaccen mutum irin Abu sumayya adaidai wannan lokacin da suke tunanin shine cikar burinsa da kuma farincikinsa don uncle hussain ahadda hawayensa, haquri suka basu sosai tare da addu’ar ALLAH ya gafarta masa sannan Dr sadeeq yace suwuce gyni saboda ga alama Abba baizo nan ba, Jikinsu a sanyaye suka bar wajen suna tuna irin muqabalar daya fuskanta kafin su bashi auren ‘yar tasu. Suna isa Dr da d’azu suka magantu da shurahbil nafitowa wasu nurses su biyu na biye da ita abaya d’auke da jarirai guda biyu a hannunsu, kallonsu tayi tace “A’ah Dr sadeeq barka da Rana, yau kaine a ward d’inmu?” “Barka Dr imaan, ya zamuyi nabiyo patient d’inmu da muka kawo anan wacce tasamu accident, so dama d’azu da mukazo ake fad’amun kece on duty keda su Dr odugun da Dr na’eem hop anyi nasara wajen aiki” “Yeah upcouse, Ashe kaine Dr na’eem ke kwatantamun, ya aiki?” “Alhamdulilah Dr.” Tafad’a tare da kallonsu uncle h dasu Abba dake tsaye suka gaisa sannan tace “Ok Dr wud’annan sune relatives d’in patient d’inka” “Eh Dr imaan” “Ok congratulation Alhaji anyi nasarar ciro mata ‘yan biyu macce da namiji amma..” kafin ta iyar Abba yafashe da kuka yace, “Shikenan dama nasan hakan zata faru, ya ALLAH kayafemun, yau gashi nayi sanadiyar jefa kaina cikin huznu dalilin nisanta kaina da ita da nayi, ta tafi tabarni da mikin da har lokacin da za’a karb’i tawa rayuwar bazai warkemun ba.” Dafa kafad’arsa Dr imaan tayi had’e da cewa “Haba baba! Waya fad’a maka ‘yarka tarasu, ‘yarka na a raye saidai ba wannan kukan naka take buqata ba, kayi hak’uri addu’arka ita take so yanzu kaji” wani irin sanyi yaji azuciyarsa wanda saida hakan ya bayyana qarara a fuskarsa ya juya gabas yayi sujudush shukur had’e da kallonsu uncle h da fuskokinsu suka kasa bayyana farinciki ko kuma damuwar da suke ciki yace, “Alhamdulilah, Hassan hussaini ‘yarku naraye bata mutu ba, kuzo kuyiwa ALLAH godiya kunji ko.” ganin yanda fuskokinsu suke yasa hankalinshi ya koma akan mijinnata da sauri ya qarasa inda Dr sadeeq yake yace, “Dr ya jikin mai gidan nata?” “Sai hak’uri Alhaji shikam ALLAH yayi masa cikawa” “Innalillahi wainna ilaihirrajiun” Abba yafad’a da k’arfi tare da fad’uwa zaune, duk wanda ke wajwn jikinsa yayi sanyi jin cewa Abu sumayya ya rasu, hatta Dr imaan saida taji shock atare da ita saboda tunowa da halin da matar ke ciki, “ALLAH yajiqansa tafurta tare da juyawa ta koma cikin d’akin tiyata” Su uncle h suka karb’i yaran suna kallo tubarkallah masha ALLAH dasu, kyawawa dasu sak kamar mahaifiyarsu gasu da girma sosai, hud’uba suka yimasu sannan sukaba nurses d’in su aka koma dasu ciki saboda ga alama basuda lafiya don gaba d’aya hannuwansu saye suke da calular irinta qarin ruwa, Shurahbil kuwa jiyayi tamkar kar arabashi da jaririyar dake hannunsa wacce itace hussaina d’an namijin kuma shine hassan yana ta kallonsu har suka shige dasu ciki, hakan ne yasa ya tuno da yabaro ‘yan uwansu a mota d’azu kuma bai rufeba, ai da sauri ya juya yamik’i hanyar inda suka ajiye motar, STORY CONTINUES BELOW  Yana zuwa ya tarar basu cikin motar, nan take duk hankalinsa yatashi yafara dube dube harda qarqashin mota, kamar ance ya juyo ya hangosu cikin motar mutumen ya kunna masu laptop suna kallo hankali kwance, zaro idanuwa shurahbil yayi tare da qarasowa wajen yafara bubbuga glass d’in motar saboda duka a kukkulle suke saboda a.c da aka kunna, a hankali mutumen yafara sauke glass d’in motar tare da juyowa yana kallon shurahbil… *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏🏻😭_* [6/15, 11:34 PM] My S Nomba: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___4💎 Suna isa gida zainab tawuce dasu part d’insu yayinda uncle hussain ya ciro wayar batool da aka basu da kuma takardun da alhajin daya kawo su Abu sumayya asibiti ya basu ya mik’awa Abba yana fad’in, “Alhaji ga wud’annan takardun da wayar fatima” “Karik’esu hannunka hussain, Amma yakamata ace antuntub’i iyayen yaron nan an sanar dasu halin da ake ciki koba haka ba?”, “Eh hakane gaskiya, dama tun d’azu ake kiran wayar narasa qwarin guiwar d’agawa, bari naba yaya sai ya lalabo lambar wanda yakamata.” Mik’a masa wayar yayi ya karb’a tare da fara duba sunayen missed call d’in da yagani saboda yanada tabbaci akan nakusa da su d’inne suka kira, lamba uku ya gani, tafarko ansa gwoggwo, ta biyun kuma sister, sai ta ukun barrister kamal, shuru yayi yana nazarin wacce yakamata ace yakira Abba yace, “malan Hassan lafiya kuwa?.” “Lafiya klw alhaji. Kawai Ina nazarin lambar kdaya kamata inkira cikin ukunnnan da aka yimata missed call dasu, wannan ta farkon Ina tunanin qilan mahaifiyar sace wato surukar ita fatima ta biyun kuma qilan qanwar sace, sai ta ukun wacce nakasa fahimtar waye shi!, gashi dare yayi kada a d’aga masu hankali” “Malan Hassan kenan! d’aga hankali kuma har na nawa agaresu?, ai tunda suka kirawo wayarsu sukaji basu same suba dole hankulansu su tashi, Ina tabbatar maka da cewa dakyar daga cikinsu in akwai wanda zai iya bacci matuqar Basu samu wani labari akansu ba, ya zamuyi tunda mai faruwa tariga da tafaru, ko ance abari sai gone babu abunda zamu iya canzawa don haka ka kira a sanar dasu shine daidai domin hakan zai sama masu natsuwa koda kad’ance, kaga at least tunda akwai ‘yar tazara a tsakaninmu (kano da borno) idan aka sanar dasu tun yau zasu samu tasowa da wuri gobe” Abba yafad’a cike da damuwa, ganin shima gaskiya yafad’a yasa ya danna lambar barrister kamal kasancewar shine namiji aciki kuma shi zaifi iya karb’ar abun cikin kwanciyar hankali duk da dai bai san kowaye shiba, ringing d’in farko bai ida shiga ba yaji yad’aga Kiran da alama jiraye yake da hakan, lokacin shikuma yana part d’insu Abu sumayya don agida d’aya suke amininsa ne sosai wani aikine yakawosa agarin borno shida iyalinsa shine Abu sumayya yabashi wani b’angare daga cikin gidansa ya zauna har zuwa lokacin da zai gama, tunda rana mahaifiyarsa tayi masa waya hankalinta atashe tasanar dashi halin da ake ciki akan rashin samun lambar aminin nasa da takeyi ita kuma ta matarsa idan takira ba’a d’agawa, Nan shima yakira lambarsa bai samesa ba hakan yasa yakira ta batool ita Kuma bata d’aga ba, yanda hankalin mahaifiyar aminin nasa ya tashi tanata kuka yasa d’aya dawo sallar isha’i yawuce wajenta yana rarrashi tare da kwantar mata da hankali amma har tsawon wannan lokacin takasa dena kukan wanda hakanne yasa shikuma yakasa komawa part d’insa wajen iyalinsa, “Assalamu alaikum” Yaya hassan yafad’a ya amsa masa cikin natsuwa tare da fargabar abunda kunnuwansa zasu jiyo masa, runtse idanuwa yayi cike da rashin sanin ta inda zai fara sanar dashi wannan mummunan awannan lokacin, karb’ar wayar Abba yayi ahannunsa tare da duba lambar sannan yakara a kunnensa had’e da cewa, “da barrister kamal nake magana?.” cikin i’ina yace, STORY CONTINUES BELOW  “E..e…eh shine.” “Kana magana da mahaifin batool ne wato alhaji Umar fari” wata irin ajiyar zuciya yaji ya sauke had’e da cewa, “Alhamdulilah!.” sannan yace dashi, “Masha Allah, Abba ya gidan anwuni lafiya?.” “Lafiya klw barrister kamal, ya..” kafin ya ida abunda zaice cikin zaquwa barrister kamal yace “Alhaji yasu batool suke!, sun dai iso lafiya ko, saboda tun d’azu muke nemansu awaya bamu samu gaba d’aya hankulanmu sun tashi.” Gwaggo najin cewa da mutanen kano ne yake waya ta dakata da kukan da takeyi had’e da kashe kunnuwa tana sauraren yagama waya taji halin da ake ciki, Abba kuwa sai daya nisa sannan yace “To alhamdulilah don aduk halin da bawa ya tsinci kansa dole yayiwa ALLAH godiya.” Wani irin fad’uwar gaba barrister kamal yaji kafin cikin sanyin murya da sarewa yace, “Hakane Abba injin dai lafiya?.” “Lafiya barrister saidai ALLAH ya jarabcesu dayin hatsari gab da hanyarsu ta shigowa kano, wannan shine dalilin da yasa kika nemesu awaya kuka rasa, wayar batool kuma da muka samu bama cikin kwanciyar hankali tun lokacin shiyasa kukaji ba’a d’aga ba, yanzu haka duk suna asibiti wanda ALLAH mai kyauta da dad’i ya qaddara ita batool d’in saboda yanayin da take ciki anyi mata tiyata don ceto rayuwar abunda ke cikinta anfiddo mata da ‘yan biyu macce da namiji, amma shi nuruddin (Abu sumayya) saidai muyi hak’uri domin ALLAHn daya haliccesa kuma yafimu sonsa ya karb’i abunsa.” Cikin tashin hankali da kuma razana saboda yanda barrister kamal yaji dirar maganar kamar sakin aradu yasa ya saki wayar tafad’i k’asa yana fad’in “innalillahi wainna ilaihirrajiun, innalillahi wainna ilaihirrajiun” haka yayita maimai tawa na tsawon sakanni kafin ya lura da yanda hankalin gwaggo yatashi cikin rud’ewa tana tambayarsa, “lafiya kamal, meyake faruwa ne, meyasa mu ‘ya’yana da kuma jikokina, ka amsa mun kamal meya samesu ne nace?” Sai as lokacin ya tuna da yaran cikin sauri ya daidaita kansa tare da goge hawayen da suka zubo masa yace, “Kikwantar da hankalinki gwaggo ba wani abu bane.” Tare da duqawa ya d’auko wayar tasa da harta mutu, “Karka yimun qarya kamal kafad’amun halin da suke ciki, dama tunda naji wannan kiran awannan lokaci jikina yabani da akwai matsala, baranma da naji cewa da abbanta kake waya” tafad’a tare da sake fashewa da wani kukan. Kamo hannunta yayi ya zaunar da ita akan kujera tare da riqo hannuwanta biyu yana kallonta cikin tausayawa yace, “kiyi hak’uri gwaggo bazan b’oye maki komai ba domin waji bine agareni na sanar dake.” shuru yayi sannan yaci gaba da cewa “mahaifin batool ne yakira yake sanar dani cewa gab dasu nuradden su shiga kano sun samu accident yanzu haka suna asibiti Kuma a sanadiyar hakan ita batool anyi mata tiyata anciro mata ‘yan biyu macce da namiji, don haka suna buqatar addu’ar mu saboda sun d’anji rauni.” Sai yab’oye mata zancen rasuwar Abu sumayya saboda tsoron yanayin da zata shiga kafin safe, gashi kuma babu kowa atare da ita sai jidda qanwar nuradden ‘yar kimanin shekara goma sha shidda wacce itace batool ke kira da sister, sallallami gwaggo tashigayi tana kuka tana fad’in “Saida nace su haqura da tafiyarnan har sai bayan ALLAH ya sauketa lafiya Amma shauqi da soyayyar mahaifin yarinyar nan yasa suka kasa hak’ura, hazbunallahu wani’imal wakeel, ya Allah ka rangwanta masu halin da suke ciki.” Kuka tayi sosai yayinda tunanin halin da zata shiga idan tasan gaskiyar al’amarin yasa barrister kamal Fara zagayen d’akin, message yaga yashigo awayarsa yayi saurin dubawa, still no batool d’ince uncle hussain da yaga Abba yajaye akunnensa shima yana kukan ya karb’a ya sake kira amma yajita switch shine yaturo message kamar haka, _muyi hak’uri da rashin nuruddin domin dukkaninmu ita muke jira, kuma mugodewa Allah daya bashi wud’anda zasu bishi da addu’ah yaransa duka nanan cikin k’oshin lafiya hadda wud’anda ya bashi ayau bayan shi ankarb’i tashi rayuwar, mahaifiyarsu ce kawai kejin jiki itama rai ahannun ALLAH, da fatar zaka sanarda wannan sak’on ga sauran ahalinsa Kuma sunce gobe in sha ALLAH zasu bada gawar tasa, ALLAH ubangiji yajik’ansa kuma ya gafarta masa_ STORY CONTINUES BELOW  Awannan karon hatta shi kansa barrister kamal zaune yayi yana sharar k’wallah tare da jinjina girman izza da kuma iyawar ubangiji, yakarb’i rayuwar Abu sumayya alokacin da yabawa ‘ya’yansa rayuwar zuwa duniya, ya tsara al-amarinsa tayanda ajalinsa ya riskesa adaidai inda yake so bayan shekaru bakwai, wasu zafafan hawayene suka zubo masa aransa yana cewa, “Tabbas ALLAH baya barin wani don wani kuma duniya ba abakin komai take ba, wanda ya d’auka da zafi zai b’ata lokacinsa batare daya ankara ba mutuwa tazo tayi gaba dashi, kana naka ALLAH yariga daya gama tashi tuntuni, kayita hauka kana qirgawa kanka shekaru batare da kasan mutuwa na gab da d’aukarka ba, kayita hauka kana kumfar baki akan qanqanen abu daga qarshe ALLAH yasa azo azare ranka, lallai duk wanda ya shiryawa zaman duniya to tabbas yayi ganganci domin duk tsawon sjekarun da ALLAH ya ibar masa to da sannu zasu qare mutuwa ta riskesa saboda duk nisan abu da SANNU SANNU yake qarewa, girman iko na ALLAH zakaga yanzune zaka rabu da mutum sai kaji ba zato ba tsammani ance maka yamutu, don haka duk musulmin k’warai dole ya farka yasan cewa ita mutuwa gaskiya ce kuma idan lokacinka yayi duk gimanka, duk matsayinka ko mulkinka zata riskeka aduk inda kake kuma aduk akowane lokaci, babu ruwan Allah da cancantar ka wa’adinka nayi za’a zare maka rai.” _ubangiji Allah yakarb’i rayukanmu Muna musulmi kuma mumunai na k’warai, yajiqan wud’anda suka rigamu gidan gaskiya👏🏻😭_ Yajima awajen zaune har gwaggo ta gama kukanta taje ta d’auro arwala tadawo, kallon agogo tayi taga har k’arfe 1:25 na dare yayi tace “Kamal katashi kaje ka kwanta iyalinka najira, hak’uri zamuyi murok’i ALLAH da yabasu lafiya kaji ko?” Nisawa yayi tare da cewa, “to gwaggo.” Sannan ya tashi zai fita jiki a sanyaye, har yakusa fita ta sake cewa, “Kamal basu yimaka zancen ko awane hali yaran nasu suke ba?.” “Sunan lafiya gwaggo sunce babu abunda ya samesu” “Alhamdulillah, to saida safe” tafad’a tare da saka hijabinta sannan ta shimfid’a abun sallah ta tayar… A yanayin da barrister kamal yashiga wajen iyalinsa dake zaune a babban falon dake tsakiyar d’akunansu suna fira ya tabbatar masu da cewa akwai matsala, hakan yasa amaryarsa meenatu dake d’auke da tsohon ciki wata takwas miqewa da nufin barin wajen saboda ‘yar uwar tata sajida da yake d’akinta tasamu damar rarrashinsa da kuma kwantar masa da hankali, kirawota yayi cikin sanyin murya yace+ “Ina kuma zakije?.” “Zanje na kwanta dama muna jiran dawowar kane munji shiru.” “Shine kuma zaki tafi baki jira jin dalilin daya dad’ar dani ba?.” “Kayi hak’uri, baccin ne yariga yazo kuma kasan yanayin jikin nawa” tak’arasa maganar tana faman lumshe idanuwa irin na masujin baccinnan, hannunta yariqa tare da rakata har cikin d’akinta yasa taje tayo arwalar bacci sannan ta kwanta ya lullub’amata bargo tare da kashe mata fitala sannan yafito. Zaune ya isko sajida takawo masa abinci da ruwa don gaba d’aya yau ko lunch besamu yayi ba saboda tashin hankali tana jiransa, qarasaw yayi tare da zaunawa k’asan kujera ya mik’e k’afafuwansa sannan yace, STORY CONTINUES BELOW  “Sannu nabarki kina jirana ko, kinsan halin ‘yar uwar taki…” “Ba komai.” tafad’a batare da tabari ya iyar ba ta tsiyaya masa ruwa masu sanyi a cup ta miqa masa, karb’a yayi ya kurb’a ruwan sannan ya ajiye agefe, k’ok’arin rik’e hannunta yayi lokacin da takai hannuwanta saman kular abincin yace, “Kibarshi wifey, bazan iya ciba.” “Subhanallahi! Kayi hak’uri kaci kad’an kada yunwa ta kamaka” “Bana cikin yanayin da abinci zai iya shiga cikina sajida…” Nan ya sanar da ita abunda kefaruwa da kuma rasuwar Abu sumayya. Hannu biyu biyu tad’ora abaki tana qoqarin danne sautin kukan daya zo mata saboda ba b.kamal kad’ai ba hatta su da suke matansa sunsan da karamci da kuma kyautatawa irin ta abu sumayya, mutumne Mai mutunci da kuma tausayi da sanin haqqin musulmi d’an uwansa, rungumota yayi yana rarrashinta tare da cewa, “Nayi rashin aminin qwarai daga cikin aminaina, yanzu babu abunda yarage awajena tsakanina dashi kamar inbisa da addu’a, haka kuma, domin shine zai tabbatar da soyayyarmu agaresa bisa kyautatawarsa agaremu.” Addu’a tayi masa sosai tana kuka kafin yatayar da ita suwuce d’aki, har zasu shiga yaja hannunta suka shiga d’ayan d’akin da yaransu ke ciki ya kunna fitila yaga duk suna lafiya sannan ya sake gyara masu kwanciyarsu suka yimasu addu’a sannan suka wuce d’akinsu, kamar yanda yayiwa meenatu haka yayiwa sajida itama sannan yadawo falo ya zauna tare da rafka tagumi yana tunano hirarsu taqarshe kafin sutafi da kalar dariyar shaqiyancin da yatayi masa akan yanda yaga yana nan nan dasu meenatu saboda kada ran kowacensu ya b’aci, maganarsa zancensa na qarshe shine. _ni dai Gimbiya ta isheni anan duniya babuni babu yimata kishiya balle inyi tunanin raba mata soyayyata da kuma kalaman bakina da zuciyata ita da wata, nayarda da ita da kuma nagartacciyar soyayyarta agareni, Ina fatar kuma ALLAH ya yarda da ita kuma ya sota, nine noora amma azahiri batool itace wannan sunan hasken da ake kirana dashi, wlh badon ALLAH yatsaro a aljannah dolene za’a bamu wasu matanba da ni Abu sumayya nace ALLAH yabarni da gimbiyata ta isheni, ALLAH kasa gaba d’aya matan hurul ayni da za’a bani kamanninsu da komai nasu irin na gimbiyata ne._ Girgiza kai yayi had’e da cewa, “ALLAHU akabar, duniya kennan, ya ALLAH ka amintar dashi ga dukkanin muradansa na alkhairi.” Sannan yamik’e shima yayo arwala ya tayar da sallah, haka shima Abba kasa kwana yayi banda tunanin abubuwan da suka faru a shekarun baya da kuma tunanin halin da ‘yarsa take ciki Babu abunda yakeyi, hakan yasa yayo arwala ya fuskanci gabas don samun sassauci, a b’angaren hajia mama ma dake asibiti itama d’in hakan tayi don samun sasauci acikin yanayin da suke ciki. Daren ranar kam gaba d’aya wud’annan ahali guda biyu kasa bacci sukayi musamman Abba da gwaggo da hajia mama da kuma barrister kamal cikakken aboki managarci awajen Abu sumayya, kwana sukayi bisa abun sallolinsu suna addu’ah ALLAH yagafartawa Abu sumayya kuma yaba iyalinsa lafiya ya albarkaci abunda yabari, banda gwaggo da addu’arta ta tafi wajen ALLAH yaba yaronta lafiya ya tashi kafad’unsa shima yasamu cikar farincikinsa kuma yaraya masa abunda tahaifa yabata lafiya. Tun da asubar fari ya kirawo abokanansu na kusa dana nesa ya sanar dasu rasuwar aminin nasu tare da tabbatar masu da cewa yanzu haka suna shirin tafiya can kano saboda acan yarasu kuma yanasa ran acan za’ayi jana’izarsa, rana nafitowa ya iske gwaggo bayan sun gaisa yace yakamata tashirya suje kano, hakan kuwa ya matuqar yimata dad’i saboda jiya zaune takwana ana nuno mata fuskar d’anta tare da hakaito mata yanayin da yake ciki, duk hankalinta yabi ya tashi taga nawar safiya tawaye, saboda yanayin da meenatu ke ciki yasa yace sajida tayi hak’uri tazauna gida Idan sun dawo shida gwaggo sai yakaita tayowa batool gaisuwa kafin itama meenatu ALLAH ya sauketa lafiya. Haka kuwa akayi sajida ta gyara masa kayansa meenatu nata kuka don sai alokacin yasanar da ita abunda kefaruwa suka kama hanya shida gwaggo da wani mak’wabcinsu babban mutumne sosai tare da matar da kuma zainab da itama kukan takeyi jin d’an uwanta na kwance aadon asibiti shida autynta da take matuk’ar k’auna, abunda bata sani ba shi gaba d’ayama yabar duniya. STORY CONTINUES BELOW  Koda k’arfe d’aya na rana tayi har sun isa garin kano dama yakira yasanar dasu Abba suna kan hanya, suna isa ambulance na ajiye gawar Abu sumayya a k’ofar gidansu Abba, tsayawa fad’ar halin da gwaggo tashiga ciki abun zubarwa hawayene sosai amma daga qarshe ta dangana tabarwa Allah, Bayan kwana uku Abba yasa aka kirawota ya bata takardun da aka samu acikin aljihun Abu sumayya bayan ya sake bata hak’uri da kuma yimata gaisuwa akan rashin da sukayi, karb’a tayi taduba takardun ta farko takar dace data qunshi address d’in data bashi daren da zasu zo, dake d’auke da sunan malan NURADDEN IDRIS ALIYU, tare da address d’insa ak’auyen bebeji, tabiyu kuma takardun wata makaranta ce daya siya ahannun wani mutum acan borno d’auke dasa hannunshi da kuma na mutumen, ranar da zasuzo ya tsaya ya karb’i takardun wajensa wanda shine dalilin da yasa ya sanyosu aljihu suka wucikke. Kallon Abba tayi had’e da cewa, “Wannan takardar adreshin qauyen da nake tunanin zai iya gano mahaifinsa ne daka dad’e kana tambayar waye ubansa har kana jifarsa da cewa shi shegene, na qyalene alokacin saboda yanda naga qarfin soyayyar d’ana a idanuwan ‘yarka shiyasa banyi yunqurin sanar dashi inda zai iya nemo saba idan har yana raye, shine awannan karon nayi tunanin fad’a masa inda zai iya nemosa don in tabbatar maka da cewa shid’in d’an halak ne gaba da baya, Amma cikin ikon ALLAH Sai gashi hakan bai faruba ya karb’i abunsa” ta qarasa maganar tana kuka. Shiru Abba yayi kamar wanda aka zarewa lakka yana mai nadama da baqin cikin abunda yayi, saida tayi kukan mai isarta sannan taci gaba da cewa, “wannan kuma bansan kota meye ba, a ajiye har zuwa lokacin da ALLAH zaiba iyalinsa lafiya mai yuyuwa ne ita tasan kota meye.” Hak’uri su uncle Hassan dake gefenta suka shiga bata tare da ban magana tace, “Aini ku bakuyi mani komai ba tunda kuka nunawa d’ana gata aduniya kuma banida bakin da zanyi maku godiya saidai ALLAH yasaka da alkhairi, shima d’in daya yimana bawai nariqesa araine ba, kawai ina tuna masane.” Da haka dai suka samu suka sake bata hak’uri tare da tausarta sannan ta ajiye masu takardun tawuce tabar d’akin tana sharar k’wallah. Tun ranar da aka yiwa batool aiki har zuwa yau kimanin kwanahud’ubata farfad’o ba, tun anasa ran yau zata tashi gobene har iyayen sun fara sarewa akan al’amarin tare da fargabar abunda kan iya zuwa ya dawo, ana gobe gwaggo zata wuce gida sunje asibitin ita da barrister kamal da kuma zainab suna zazzaune cikin d’akin da aka kwantar da batool riqe da jariran da aka faraba madara yanzu sukaga ga hannunta yafara motsi, cikin farinciki duk sukayo kanta yayinda tafara bud’e idanuwa ahankali tana kallonsu d’aya bayan d’aya tamkar wud’anda bata tab’a gani ba, wani irin farinciki ne ya rufe gwaggo da hajia mama suka rungume juna suna hawaye tare da yima ALLAH godiya, barrister kamal ne yayi saurin fita sai gashi yadawo tare da likita, matsawa yayi kusa da ita yana duddubata sannan yace su tayar da ita zaune, ahankali yafara kiran sunanta kanta na duqe a k’asa, “batool, batool, batool” yakira sunan har sau uku, anan ukunne ta d’ago kai tare da kafesa da idanuwa, biron dake hannunsa yafara nuna mata saiti idanuwanta yana yawo dashi a fuskarta. Ahankali take bin biron da idanuwa aduk inda yayi dashi kafin likitan ya maidashi cikin aljihu yana murmushi had’e da juyowa yana kallon barrister kamal da shurahbil dake gefe a tsaye yace “Alhamdulilah, ansamu tafarfad’o kuma in Sha ALLAH babu wata sauran matsala, yanzu abunda ya kamata ahad’a mata ruwan tea abata tasha.” sannan ya rubuta wasu magunguna yabasu yace aje asiyo akawo idan tagama shan ruwan tea sai akirasa, juyowa yayi yasake kallonta har lokacin idanuwanta na saman aljihunsa da taga yasa biron aciki yayi murmushi sannan yafita. “Sannu maman twins” barrister yafad’a sannan ta maido idanuwanta akansa daga kallon likita da takeyi shima tanata kallonsa harda karkace kai, K’ok’arin had’a ruwan tea d’in hajia mama tafarayi yayin da gwaggo dake rik’e da maccen tamatso kusa da ita cike da tausayawa tace, STORY CONTINUES BELOW  “Sannu uwar biyu, ubangiji ALLAH ya baki lafiya” kamar da gaske batool ta d’ago kai tace “Amin.” tare da mik’a mata hannuwa, hakan yasa gwaggo ta mik’a mata jaririyar had’e da cewa zainab ta kawo mata d’ayan jaririn aka aza matasu saman jikinta tabisu da kallo d’aya bayan d’aya, so takeyi ta tuna kosu waye atare da ita amma takasa, hakan yasa taji kanta yafara jujjuyawa kamar ana yawo da ita cikin wata duniyar, dariya dariya kuka kuka tafarayi kafin can tasaki wata irin qara had’e da ture yaran daga jikinta tana wani ihu wanda nan take hankalinsu ya tashi, badon zainab tayi sauri taro yarinyar ba da tuni tafad’a akan k’arfen dake gefenta na qarin ruwa yayinda shikuma d’ayan tuni yafad’o k’asa tare da tsanyara ihun kuka da sauri gwaggo ta d’aukesa tayi waje tana k’walawa nurses kira ita kuma banda buge buge da takeyi tana sakin wata irin qara da duk wanda yaji sai tsikar jikinsa ta tashi, hajia mama na kuka tafara qoqarin riqota saboda kada tajima kanta takaimata wani irin cizo da yaga amma hakan bai hanata takamata tariqeta sosai tana maimaita kalmar “innalillahi wainna ilaihirrajiun, allahumma ajirni fi musi bati wa ahlifni khairan minha, ya ALLAH muntuba kayafe mana kada kajarabcemu da abunda bazamu iyaba.” Dukanta takeyi da dukkanin qarfinta amma taqi sakinta saima sake rungumeta da tayi sosai tana kuka, itama zainab d’in kuka takeyi tana riqe da jaririyar agefe, saiga shurahbil da barrister kamal da sukaje wajen sayo magani sun dawo, da gudu suka ida qarasowa wajen suka kamama hajia kaka ita suka rirriqeta tana kucce kucce saiga wasu likitoci harsu uku sun shigo gwaggo na biye dasu abaya tana sharar k’walla saboda nurses sun karb’i jaririn yana can suna dubashi. Nan take sukayi mata allurar bacci sannan sukace su saketa sufito, taimakon gaggawa suka fara bata tare da yimata binciken daya kamata, sannan suma suka fito fuskokinsu cike da damuwa, da sauri hajima mama tanufi inda suke tace, “Don ALLAH likita awane hali ‘yata take ciki” gaba d’aya kasa tanka mata sukayi suka shige cikin wani office, turowa sukayi aka kira masu shurahbil alokacin Abba da uncle Hassan sun iso saboda wayar da shurahbil yayi masu ya sanar dasu halin da ake ciki hakan yasa uncle hassan ya dakatar da shurahbil d’in suka shiga shida Abba, wata takarda suka mik’o masu bayan cikin natsuwa Dr na’eem wanda yana d’aya daga cikin likitocin da sukayi mata operation yayi masu bayanin cewa, “Alhaji kuyi hak’uri akan abunda zan sanar daku amma patient d’inku tana cikin wani mawuyacin hali sakamakon buguwar da tayi ga kai, bincikenmu ya tabbar mana da cewa tasamu matsala a kwakwalwarta, dama tuni wannan muke tsoro ga farkawar tata tun lokacin da aka gama mata aiki but alhamdulilah tiyatar tata tawarke sai d’an abunda ba’a rasa, don haka yanzu wannan takardar zakuje kubiya kud’in wani scanning ne da za’ayi mata zuwa anjima. Yanda abun ya matuqar girgza Abba yasa daga nan inda yake zaune sukaga ya b’ingire sanadiyar hawan jinin da yake dashi, dole shima nan take aka bashi gado kafin kaceme ‘yan uwa sun taru a asibitin cike da jimamin wannan irin jarabawa da Allah ya aikowa familyn nasu acikin wannan lokacin. Little Hassan kam babu abunda ya sameshi don anyi masa checkup sosai, haka Abba shima yasamu sauqi duk da dai har yanzu yana qarqashin kulawar liikitocin, gwaggo kam fasa tafiya tayi saidai tace barrister kamal yawuce ita zata jira har nan da kwana biyu, al’amarin batool kam ya tsananta, hauka tuburan takeyi wanda likitocin suka tabbar masu da basusan iya adadin lokacin da zata iya warkewa ba sai dai kawai suci gaba da addu’a da kuma nemar mata magani, yanzu haka dalilin daya hana suyi deparing nasu zuwa asibitin mahaukata saboda sauran raunukan dake jikinta ne da kuma tiyatar dake jikinta da suke treating badon haka ba ayqnayin da take bai kamata ace an ajiyeta nan ba, shiyasa kullum cikin yimata allurar bacci suke kuma tahakanne kad’ai yaran kesamu suna shan nono awajenta. Rayuwar batool tazama abun tausayi musamman idan ka kalli jariran dake gabanta da kuma yanayin da take ciki, su hassana kam tuni sun samu sababbin iyaye saboda kulawar da zainab ita da d’an uwanta shurahbil ke basu, abunka da yaro rayuwarsu sukeyi cike da farinciki cikin sauran ‘yan uwansu yara sai baka rasa bane zakaga sun aza rigama suna kuka sai ankaisu wajen dady da ummiensu, musamman cikin dare ko kuma lokutan da zasuci abinci sai kaji suna rigima waisu bazasu ciba sai I idan dady da ummie ne zasu basu, Abba kuma yasamu sauqi sosai har anbashi sallama amma yanda yayi rama saboda tsananin baqinciki da damuwar da yake ciki kallo d’aya zaka yimasa ka zubar masa da hawaye, yayi kuka, yayi nadama tare dayin tir da zuciya irin tasa, tabbas yayi dana sani abu adadi alokacin da SANNU SANNU yafara karb’a sakamakon abunda yayi, dama anfad’a masa cewa but khairan da sharran wanda duk ka aikata da SANNU SANNU zai riskeka, dama SANNU SANNU bata hana zuwa…..gashi yanzu anzo wajen da abunda ya aikata ya riskesa. A ‘bangaren mutumen dake iqirarin soyayyarsu hassana da hussaina kuwa tun ranar da yaji kalaman da suka fito abakin shurahbil yadena bayyana agaresu amma hakan bai hanashi bibiyar rayuwarsu ba akoda yaushe hatta rasuwar Abu sumayya dashi akayi jana’iza saidai ko kad’an bai bari sukayi arba da shurahbil ba saboda tsoron kada wancan tunanin ya zauna aransa, haka kuma yakanzo asibiti duba jikin batool saidai baya zuwa sai lokutan daya tabbatar su shurahbil basa wajen ko sun shiga sallah tukuna, hajia mama na lura dashi Idan yashigo amma bata tab’a kawo komai aranta ba,saboda aduk sadda yashigo sai yafara zuwa ya dudduba marasa lafiyar dake ward d’in tare da yimasu alkhairi sannan yake zuwa wajensu hakan yasa tunaninta yatafi akan qila irin mutanen nanne dake zuwa dudduba marasa lafiya suna yimasu alkhairi don suma duk sadda yashigo dubo goma yake ajiye masu, har ta tab’a nunawa Abba dasu Uncle h shi, Amma ALLAH bai tab’asa suka gane saba ko kuma suka had’u da shurahbil ba sai yau, shurahbil na shigowa da motarsa asibitin ya d’auko su gwaggo da matar uncle hussain yaga shikuma yafito, hakan ya matuqar d’aure masa kai har yafara tunanin ko waye wannan mutumen, tunowa da compliment card d’in daya basa ranar yayi da sauri ya ajiyesu gwaggo yajuya motarsa yakoma gida, yana zuwa yanufi wajen daya sargafe kayan dayasa ranar ga hanger yafara laluben aljihun rigar, cikin sa’a yanasa hannunsa cikin aljihun rigar na gefe yaci karo da compliment card d’in, Wata irin ajiyar zuciya yayi don dama tuntuni ALLAH ALLAH yakeyi inbai yadda shiba, rubutun da akayi jikinsa yafara karantawa kamar haka, [6/15, 11:34 PM] +234 703 729 2170: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___6💎 Rubutun dake jikin compliment card d’in shurahbil yaqurawa idanuwa kafin yafara k’ok’arin karantosa cike da mamaki, ” _DR. N.I.ALIYU (PSYCHATRIC DR.)_” ya sake maimaitawa aransa, sannan yabi sauran address d’in dake rubuce da kuma numbobin waya har guda biyu da kallo, jujjuya card d’in yafarayi yana son tunano inda ya tab’a jin wannan sunan, Nan take yatuna cewa ai babban likitan da yasha ji ana zance agarine akan k’warewarsa wajen iya kula da mararsa lafiya musamman masu fama da matsalar k’wak’walwa ya matuqar sanin aikinsa tare da tausayawa mararsa lafiya sosai wanda wannan dalilinne yasa nan take yasamu d’aukaka cikin qanqanen lokaci, shekararsa hud’u kenan da yasa akayo masa transfer daga minna zuwa kano, kuma cikin ikon ALLAH yanzu babu inda labarinsa bai kaiba acikin garin saboda tausayi, kamanta gaskiya da kuma taimako acikin aikinsa, ajiyar zuciya yayi tare da cewa “tabbas babu ko shakka wannan mutumen shine likitan da naji ana zance agari, idan kuwa hakane yazama dole na samesa har gida saboda matsalar auntynah tunda ance shi mutumne mai sauqin kai wataqil zai iya bamu wani taimako kodon saboda soyayyar da yake yiwa yaranta” haka yaqarashi zancensa shikad’ai yana safa da marwa acikin d’akinsa kafin ya kad’a katin a aljihu yabar d’akin, yana fitowa yaci karo da zainab tafito ita da twinse zasuji wajen bukin wata qawarta, da gudu suka nufi wajensa kowacensu na Kiran “oyoyo uncle” tare da bud’e hannuwa, shima bud’e nasa yayi suka shige Yana dariya yace,+ “Iyyeee ‘yan matan aunty Ina zuwa akaci wannan gayu haka?.” “Party zamuje” hussaina tafad’a tana kallon zainab data qaraso wajen, duka hassana ta kaimata had’e da cewa “ke kuma bikine zamuje ba party ba ko aunty zee” tafad’a itama tana kallonta. Dariya zainab tayi sannan tace “Gaskiya kam hassana fad’amata mu biki zamuje ba party ba, haba hussaina wane party ana zaune lafiya, ai sai kija uncle hussain ya kakkarya mu idan yaji haka!.” Kallon shurahbil da shima dariyar yakeyi tayi sannan tace “don ALLAH ya shurahbil Ina zakajene?.” “Ya akayi ne?” Ya amsa mata atak’aice tare da mik’ewa tsaye daga duqen da yake zai wuce don yasan halinta, yanzunnan me zatace ya ajiyeta, bai qarasa fitaba ta biyoshi da sauri tana fad’in. “Emm.emm dama cewa nayi ko zaka rage mana hanya pls” “Ok, dama nasan shine zancen” yafad’a tare da ficewarsa, da sauri ta dawo baya tariqa hannuwansu sukabi bayansa suna yimata ‘yan tsalle tsalle. Bayan sun shiga mota shurahbil ya tayar suka bar gidan ya juyo Yana kallon zee da tasha kwalliya qamshin turare na tashi ajikinta tako ina yace, “Zainab kinji fitinannen qamshin da kikeyi kuwa?” “Eh ya shurahbil turaren yayima dad’i ko?.” Saida yamere baki tare da yin kwana ya hau titi daidai sannan yace “Wane dad’i, turare na hawan kai haka?, Meyasa Wai ku bakwa fahimtar cewa annabi yafaku, fisabilillahi wannan qamshin turaren da kikeyi yayi yawa, zai iya jawo hankalin maza akanki, ga wannan baqar kwalliyar da kika b’ata fuskanki da ita, gaba d’aya ta maidaki wata irin halitta daban sai kace dodo ko kuma aljana. dubi d’inkin dake jikinki zainab inada tabbaci akan ko lumfashi maikyau baya barinki gashi kin d’auko mayafi sai kace abun tatar k’ullu kin d’ora akai, gaba d’aya kincika duk wasu sharudd’an da zasu iya jefe rayuwarki cikin halaka” turo baki tayi ranta ab’ace saboda jin yanda take faman kushe mata kwalliya da kafin tace, STORY CONTINUES BELOW  “Haba ya shurahbil meye aibun turaren dana saka?, meye laifin kwalliyata da zakace haka?, ALLAH a zamaninnan da kake gani wlh mace idan bata gayu tana gyara jikinta da iya d’aukar dress to ALLAH yasani sai miji yayi mata wuya, saboda yanda idanuwan mazan suka bud’e yanzu” “ALLAH?.” “Eh mana, kaima kasan hakan!” “Hmmm nikam bansan komai ba inba kuskuren da nake ganin ‘yan mata ire irenki na tabkawa ba, turare da kike gani manzon ALLAH sallalahu alaihi wasallam ya haramta mace ta sakashi idan zata fita domin yin hakan daidai yake da tayi zina, wasu matan na kuskuren fahimtar cewai wai sai ga matar aure wanda shi manzon ALLAH bai banbace matar aure ko budurwa ba, jam’ine na duka mata yayi, ita kuma wannan kwalliyar da kukeyi wlh da kunsan yanda take maida wasunku to da kun hutar da kanku domin asalin kamanninku sunfi sha’awa da burgewa akanta, ni anawa ra’ayin nafiso naga mace tayi kwalliyar da bazata canza mata kamanni daga yanda take ba wannan shike tabbatar mani da cikar hankalinta, banace kuskure ne yin kwalliyar ba, Amma yakamata kudinga yin mai ma’ana, zancen d’inki kuwa a yanda ya matseki d’innan kuma kika fito haka to ina tabbatar maki da cewa kin sake shiga jerin matan da annabi ya tsine masu wato kasiyatun, ariyatun, ma’ilatun, mumilatun….har dai zuwa qarshe akan sakin tsiraicinsu da sauransu, don haka tun wuri kiyiwa kanki fad’a, wannan d’abi’ar ba zata baki mijin aure ba sai shashasha kamarki, ammadai wanda yasan ciwon kansa bazai d’aukeki ba da duk wasu masu irin d’abi’arki domin shike yawan haifar da zinace zinace, bayan ALLAH da kansa yace _’wala taqrabuzzina…’_ kada ku kuskura ku kusanci zina domin takasance alfasha ce, wlh wannan sakin jikin da kukeyi baya haifar maku da kima awajen maza asalima shikesa namiji yaga arharku yaga sauqin fuskantarku da maganganun banza da kuma na fasiqanci, kujurewa rufe jikinku kamar yanda ALLAH ya umurci annabinmu daya sanar da matansa da ‘ya’yansa da kuma mata muminai cewa _’yudnina alaihinna min jalabibihinna’_ surufe dukkanin jikinsu da jilbab (hijab) hakan zaisa suyi kima da daraja a idanun ALLAH da manzonsa da kuma duniya, shizai kare masu martabarsu ta ‘ya’ya mata kuma yazab’a masu mazaje nagari, ba laifin idan har kinada sha’awar yin wud’ancan abubuwan kiyisu acikin gidanki/ku yanda bazaki d’ibarwa kanki zunubi ba, Idan kuma ke matar aurece sai ALLAH yabaki tarin lada mai yawa saboda kinfaranta zuciyar mijinki don haka ni Ina baki shawara akan cewa wannan ba burgewa bace Idan Zaki gyara kigyara, ke yanzu ko d’aukar aya bazakiyi ga ‘yar uwarmu dake can kwance cikin wani hali ba, bazaki wa’aztu da cewa mutuwa na d’aukar ran bawa aduk lokacin da takeso Kuma akowane yanayi yake ba har kike yiwa rayuwarki wannan izgilancin, yanzu Idan aka zare rayuwarki acikin wannan yanayin mezaki je kicewa ALLAHnki” Shiru zainab tayi domin gaba d’aya yau ya kashe mata jiki, tabbas zata gyara kodon samun gobe mai kyau da kuma barranta daga cikin matan da aka tsinewa tun aduniya, ajiyar zuciya ta sauke had’e da cewa “nagode ya shurahbil daka fahimtar dani abunda uncle hussain akoda yaushe yake son nafahimta Amma nakasa saima kallon abun da nakeyi a matsayin takurawa, in Sha ALLAH daga yau nadena bazan qara ba, yanzu kamai damu gida nafasa zuwa bukin” Murmushi yayi tare da jin dad’in yanda ta karb’i gyaransa da hannu biyu sannan yace “A’a basai anyi hakan ba, tunda kinriga kinfito Bari mutsaya shagon d’and’a investment saina saya maki wani mayafin da zai rufe maki jiki kinji ko” cikin jin dad’i ta amasa dasa da “shikenan yayana Ina alfahari dakai” haka kuwa akayi suna kaiwa bakin shagon yayi parking sannan yashiga ya siyo mata wata wani mayafin mai kabri dazai kai mata har guiwa kalar touch d’in kayan dake jikinta, b’ata rai tayi had’e da cewa “a’a yaya ka d’okomun hijab nafi sonsa tunda kayan sun matseni da yawa” “Karki damu in sha ALLAH, wannan ma zai wadatar kedai kisa aranki tubar gaskiya kikayi kuma zaki gyara” “In Sha ALLAH Yaya” tafad’a tare da karb’ar mayafin a hannunsa sannan ta canza, Yana ajiyesu ya nufi gidan Dr.N.I aliyu a anguwar nasarawa kamar yanda yagani rubuce a card d’in, Yana isa ya yakira lambarsa da yayi copy a wayarsa amma yajita switch up, yakira duka biyun yafi ak’irga akashe gashi baisan gidan ba kuma anguwar tsit take balle ya tambaya, hakan yasa yajuya kan motarsa yakoma asibiti, STORY CONTINUES BELOW  Yana isa ya tarar anyi transfer d’insu zuwa psychiatric clinic Amma saboda ta tashi daga baccin sai kuka su Abba da hajia keyi saboda yanayin da take ciki, gaba d’aya ta yayace ward d’in da qara tana buge buge, hatta nurses d’in dake kula da ita sun fara jin tsoronta hakan yasa suka kasa matsawa kusa da ita balle su samu damar yimata allurar da aka saba yimata, umurni wani likita yabasu dasu taru sufara d’aureta sai suyi mata allurar, tana ganin sun nufota da igiya tayi wani irin qaraji daya sasu saurin watsewa gaba d’aya, tana ganin haka ta tashi da gudu zata fita suka kamota, yunqurawa takeyi da duka qarfinta tana son kwacewa daga hannunsu amma da yake su kusan biyar ne takasa saidai takoma tana wani gumza kamar zakanya, kasa kallon yanda suke d’aureta Abba yayi da sauri ya qarasa wajen yana kuka tare da d’an doddo kawa nurses d’in sandar da yake tokarawa yana fad’in, “Kucika mun ‘yata, kada wanda ya d’aure mun ita, kubarta don ALLAH ku k’yaleta nace” dakatawa batool tayi daga kucce kuccen da takeyi tana sauraren muryarsa tare da k’ura masa idanuwa, hakan yasa sukaga damar da zasu ida d’aureta Amma kafin kace me har batool ta ankara, yayumo wacce ke kusa da ita tayi tare da cijeta ga hannu har saida taciro fatar jikinta, fad’a Dr. Yafara yiwa Abba akan yabari suyi aikinsu Amma yaqi gashi har yajawo ta jima d’aya daga cikinsu, haquri hajiya mama tabashi sannan tarik’o hannun Abba had’e da cewa “alhaji don ALLAH kayi haquri kabarsu suyi aikinsu” kwace hannunsa yayi daga riqon da tayi masa ransa a b’ace yace “Bazan iya kallonsu suna cigaba da d’auremun ‘ya haka ba sai kace dabba.” Kallon likitan yayi had’e da cewa, “Kai dr, Ina kun sallamemu ko? To kubarni ni nasan yanda zanyi da ‘yata koda zata kasheni Amma kar wanda ya sake d’aureta” yana rufe baki ya duqa kusa da ita tare da cire mata igiyar ya jefa masu sannan ya fara yimata magana a hankali “batool, batool, zakije gida?” Bai rufe baki ba tajawo qarfen qarin ruwa dake gefenta ya fad’o masa saman kai har saida yafasa masa goshi, da sauri shurahbil yanufo wajen amma Abba ya d’aga masa hannu, hannu takai da niyara chakumo wuyansa amma jinin da tagani nafita a goshinsa yasa tadakata, ja da baya tafarayi a tsorace kamar wacce kejin tsoron a doketa, batare da Abba ya damuba ya mik’a mata hannu ta k’ara matsawa a tsorace, haka yadinga matsawa wajenta tanaja da baya har ta isa jikin gadon ta runtse idanuwanta, ganinsa gab akusa da ita yasa tafara bud’ewa ahankali, ga mamakin nurses da likitan dake wajen sai sukaga Yana mik’a mata hannu tariqo ya mik’e da ita tsaye har lokacin yana riqe da hannunta, juyowa yayi zai fito da ita suka dinga jayewa suna kallon ikon ALLAH, biye take dashi amma ta tattakure kanta abayansa tana nonnoqe kai yace “Kungani ko, nasani qarfin soyayyar da ‘yata keyimun bazai bari ta watsamun qasa a idanuwa ba duk dako bata cikin hayyacinta, shurahbil zo mutafi.” Cike da farinciki hajia mama takai hannunta zata rik’ota ta bugemata hannu tana k’ara shigewa bayan Abba, juyowa Abba yayi yace ma hajia mama “kik’yaleta kada ta sake birkicewa kuma” “Amma yakamata katsaya aduba maka goshinka” “Babu komai tunda jinin ya tsaya nadawo daga baya a gyaramun ko kuma naje chemist” Shurahbil dake neman shiga a gabansu ne yace “Abba acan clinic d’in zamuje ne” “A’a gida zanje da ‘yata, matuqar ta wannan hanyar da naga sunbi zasu kula da ita to bazan barta anan ba, zantafi da ita gida inbata kulawar daya kamata kuma nasamo manya manyan likitocin da zasu dinga duba mani ita” Ai kuwa haka akayi babu yanda Dr. Bayyi dashi akan kada yatafi da ita gida ba Amma yaqi, dole suka barshi ya wuce da ita don rigimar tsohon tafi k’arfinsu Babu yanda zasuyi, sunyi fad’a har sun gaji saidai shurahbil yayita basu haquri. Wajen shiga mota ma haka Abba yayita fama da ita don k’in shiga tayi sai da yayi ta mata dubaru sannan ta amince tashiga motar, Amma duk wanda ya aza qafa da sunan ya shiga ciki sai tayo kukan kura akansa, hakan yasa daga Abba sai kuma shurahbil dake jan motar suka shiga, hajia mama da kuma mahaifiyarsu shurahbil da gwaggo dake rik’e da jariran saidai abba yakira uncle hussain yace yazo ya d’auki da motar sa daya bari don data shurahbil ce su suka tafi…. STORY CONTINUES BELOW  _AFUWAN DA JINA SHIRU BAYAN KWANAKI, NAJE GANIN GIDANE ‘YAN UWA DA KUMA ABOKANAN ARZIK’I SHIYASA KUMA KUNGA SUMA AKWAI BUQATUWAR ACE SUN SAMU LOKACINA, NGD DA SAQONNINKU DA ADDU’O’IN ALKHAIRI ALLAH YABIYAKU DA ALJANNAH FIDDAUSI,👏🏻😍KUCI GABA DA BIBIYAR WANNAN LABARIN AHANKALI DOMIN *SANNU SANNU* BATA HANA ZUWA SAIDAI ADA’DE BA’A KAIBA🤣ONE LUV FILLAH😉🤞💋❤️_ *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏🏻😭_* [6/15, 11:34 PM] +234 703 729 2170: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___7💎 Al-amarin batool kam sai addu’a saboda ako yaushe sai qaruwa yakeyi, gashi Abba yabuga kai ga qasa shi baza’a kaimasa ‘ya asibitin mahaukata ba, mutum ne shi mai kafiya da kuma zuciya hakan yasa su uncle h suka zuba masa idanuwa domin babu rarrashin da basuyi masa ba da kuma lurar dashi amma yakafe kai da fata, musamman yasa aka gyara mata d’aki d’aya yasa duk aka ciccire abubuwan da suka shafi qarfe da zasu iyasa tajima kanta aka fiddasu sannan ya d’auko wani k’warraren likitan k’wak’walwa yafara dubata, wasu allurai likitan ya rubuta da za’a dinga yimata kullum ko wace k’waya d’aya dubu ashirin kuma Abba ya amince, lokacin dasu Uncle h sukayi yunqurin dakatar dashi da kuma nuna masa cewa kud’in sunyi yawa rufesu yayi da maseefa har Saida suka koma bashi hak’uri, Kimanin watanni biyu kenan ana Abu d’aya amma babu wani sauyi, babu wanda ke matsawa wajenta tak’yalesa idan ba Abba ba hakan yasa kullum cikin hidimarta yake gwanin ban tausayi, abincinta da abun shanta duka shine hakama idan za’aba yaran nono shike karb’arsu yaje dasu cikin dubara ya lallasheta tabasu kuma batayi masu komai indai yana tsaye, duk da k’wak’walwarta bata aiki tana matuqar jin tsoronsa, zancen wanka ne kawai ba’a yimata saboda bazata bari ba shi kuma Abba babu kyautawa ace shi zai yimata, sau d’aya yasa su hajia mama suyi mata yana bakin toilet d’in ya tsareta ai kuwa sunsha cizo da yakushi, tun daga ranar sukace bazasu koma ba, gwaggo ma m takoma tun ana sati d’aya da sallamosu, lokaci lokaci takan kira hajia mama ta tambayi lafiyar jikokinta da kuma ta batool tayita kuka tana addu’ar ALLAH yabata lafiya, haka barrister kamal shima yakan zagayosu idan yasamu sarari wajen aikinsa tare da kayayyaki masu yawa yace aba yaransa. Shurahbil kuwa ko yaushe yana bisa hanyar neman Dr. N.I na kimanin wata biyu kenan bayada labarinsa kuma baya samun lambobinsa idan yakira, yau kamar an tsunkulesa yana kwance ya tashi had’e da zura jallabiyarsa ya nufi asibitn da Dr. N.I ke aiki don duk bid’ar daya yimasa hankalinsa bai tab’a kawo masa da yaje can ba. Yana zuwa ya tambaya aka kaishi har office d’insa, cikin sa’a kuwa ya iskota, ajiyar zuciya yayi tare da yiwa ALLAH hamdala sannan yatura gambun ya shiga, Dr.N.I na ganinsa ya mik’e cikin fara’a yana fad’in, “Ahh! Baban yara kaine a office d’ina?” tare da mik’a masa hannu suka gaisa, murmushi shurahbil yayi tare da sosa qeyar kansa sannan ya zauna saman kujerar da yake nuna masa yana fad’in, “Ya zanyi Dr tunda kab’oye mana, nayi nemanka har nagaji ban sameka ba, har nasarawa anguwarku naje amma nakasa samunka sai yau nayi tunanin zuwa nan asibiti kozan sameka.” “Ayya malam shurahbil, ai kayi raggon azanci, kaida har unguwar mu kaje meyasa kak’i tambayawa, ai ko qanqanen yaro katambaya akaika gidana za’a nuna maka, duk da dai nad’anje qauyene wajen wani bincike sai jiya nadawo, yanzu nake cewa anjima Idan narage abubuwa zan shiga asibitin, ya masu jiki hop dai da sauqi ko?” STORY CONTINUES BELOW  “Eh alhamdulilah za’a ce amma ambamu sallama ko ince transfer zuwa psychiatric clinic sai dai Abba bai amince mukaje ba, marar lafiyar na nan gida” “Subhanallahi meya faru da itane?.” Shiru shurahbil yayi kafin yafara labartawa Dr.N.I halin da batool ke ciki, bai b’oye masa komai ba hatta likitocin da Abba kefaman d’aukowa da allurorin da akeyi mata duk saida yafad’a masa, ya matuqar tausayawa halin da batool ke ciki da kuma yaranta, yajima zaune batare da cewa komai ba kafin yace, “Shurahbil karka damu in Sha ALLAH zan taimaka maku kuma kakwantar da hankalinka da yardar ALLAH zata samu lafiya.” “ALLAH ya yarda Dr. Nagode sosai” Shurahbil yafad’a Yana goge k’wallar data zubo masa a idanuwan, “Badamuwa, anjima da marece zanzo saika sanarwa da iyayen naka idan sun amince saika kirani tunda kana da lambata kafin lokacin yayi” “Shikenan Dr. Amma wud’annan lambobin sun dena aiki ko zaka bani wadda zan iya samunka direct” dariya Dr. N.I yayi kafin yace “Ka kira in sha ALLAH zaka sameni yanzu” dama rufe wayoyin yakeyi duk lokacin daya je k’auyen saboda muhimmancin abunda yaje yi, shikesa Idan yatashi hutun wata d’aya yake d’auka don yasamu isasshen lokaci, har sunyi sallama da shurahbil zai fita ya dakatar dashi tare da d’aukar biron dake gabansa da Kuma ‘yar guntuwar takarda ya sake rubuta masa wata private no d’insa da bakowa ya sani ba yabashi had’e da cewa “Ka gaida mani da twins da kuma qannensu” “Zasuji in sha ALLAH nagd sosai Dr ” sannan yawuce zuciyarsa cike da farinciki sai kace wanda aka tabbatarwa da cewa zata samu lafiya. Kai tsaye gida ya nufa, yana shiga ya hangosu uncle h tare da Abba rik’e da little hassan zaune saman wasu kujeru dake can gefe cikin wata ‘yar rumfa, parking yayi sannan yafito cikin motar yanufi inda suke ya gaishesu sannan ya sanar dasu zancen Dr. N.I da batun zuwansa anjima, aikuwa nan mahaifinsa ya titsesa da tambayoyin a ina yasanshi?, waya sanar dashi cewa cikakken likitane da har zai kwashi jiki yaje wajensa bayan bashida tabbacin cewa shid’in likitan k’wak’walwane ko akasin haka, nan yaciro compliment card d’in daya basa ya mik’a masu, sosai Abba yaji dad’i kuma ya amince Dr yazo saboda ahalin yanzu ko qanqanen yaro yakawo masa magani ko kuma wanda zaiba ‘yarsa magani tawarke zai karb’esa hannu biyu matuqar ya tabbatar da nagartarsa balle d’an gida da bazaya tab’a cutar da ita ba… *_WAI WAYE (TUSHEN LABARI)_* _WAYE ABU SUMAYYA_ ‘Dah ne tilo awajen mahaifinsa malan Idris Aliyu, ya had’u da mahaifiyarsa awani k’auye da ake kira k’auyen yarimawa dake cikin garin kano alokacin an turasa makarantarsu wajen koyarwa, kasancewar shi mutumne da baya son ganin anbar d’alibinsa ko d’aya abaya ta fannin karatu yasashi maida hankali gaba d’aya wajenta saboda rashin son karatu, Rashida Basharu shine sunan mahaifiyarsa takasance batason karatu ko kad’an tun tana ‘yar qanqanuwa har takai ‘yar kimanin shekaru goma sha biyar Amma babu abunda yacanza, tsabar repeating d’in da akeyi mata yasahar awud’annan shekarun nata take a matakin aji biyar primary shima d’in daqyar da sud’in goshi akasamu takaisa, social studies shine darasin da take d’aukarsu kuma gwargwado d’alibban nasa suna fahimta inbanda Rashida da akoda yaushe batada wajen zama irin kujerar baya tana sharar baccinta, yafahimci hakanne ta dalilin yawan tambayoyin da yakeyiwa d’alibansa kuma suna bashi amsa daidai gwargwado amma ita saida tazuba masa idanuwa, gashi kusan tafi duka d’aliban ajin be nasu girma, hakan yasa ranar da abun ya fara bashi haushi ya maidota sit d’in gaba inda monitor d’insu yakeyi, cikin b’acin rai dajin takaici yace da ita “as from today this is your sit, I don’t wanna be see you sitting back again you here me ko?.” yaqarasa maganar cike da fad’a tare da rik’e kunnensa d’aya alamar jamata kunne, Rashida da batasan komai yafad’a ba tana ganin yariqe kunne da sauri tamik’e takama kunnuwanta cike da tsoronsa saboda ganin yanda ya d’aure fuska, gaba d’aya ‘yan ajin suka sa dariya har dashi, saida yayi mai isarsa sannan yajuya yabar ajin dama period d’insa yaqare, tana ganin haka ta d’ago kanta had’e da cewa STORY CONTINUES BELOW  “Malan in tashi?” Juyowa yayi had’e da cewa, “Dama ai bani na saki ba ke kikasa kanki, don haka zaki iya tashi idan kin gaji.” “Malan kaifa naga kayi mani na kurmaye kace nakama kunnuwa na.” Dariya yayi sannan ya girgiza kai had’e da cewa monitansu “na’ima tashi kifad’a mata abunda nace.” Ai kuwa na’ima cikin irin zaqewa d’innan tamik’e tana fad’in “cewa yayi daga yau nan shine mazauninki baya son yakoma ganin kin zauna abaya kiji ko?” da sauri rashida ta d’aga kai tana fad’in “yes” suka sake kwashe mata da dariya hadda monitor d’insu dake yimata gwalo, “Keep quiet” yafad’a in a serious tone kafin nan kowanensu yakama bakinsa, harara ya maka mata had’e da cewa, “shemless thing to you” washe baki tayi had’e da cewa “thank you sir” cike da jin haushi yabar wajen yana tunanin ta ina zai fara saitata akan layi. Duk iya dubarar daya kamata yayi wajen ganin itama tamaida hankali wajen fahimtar karatu kamar sauran d’aliban yabi amma abun ya cutara, yabi mata tahanyar yawan yimata tambayoyi ko zataji haushi tamaida hankali amma taqi, yayi zaunar da ita yakoya mata ita kad’ai shima ta gagara fahimta, hakan yasa aka kirawo masa ita a office d’insa don ba qaramin tausayawa rayiwarta yakeyi ba, bayan tazo tagaishesa ya amsa cikin natsuwa sannan yace, “Rashida meyake damunki” shiru tayi har saida ya sake cemata, “meyasa kike son wahalar da mahaifinki bakyason karatu?” Cikin amsar da baiyi be tsammanin jinta daga bakin taba yaji tace, “Malan ni bana sone kuma bana ganewa shiyasa.” “A’a Rashida baki sawa ranki zaki gane bane, Amma inada yaqini akan idan kika jajirce Kuma kika maida hankali da SANNU SANNU zaki iya.” “Bazan iya ba malan.” “Saboda me kikace haka?.” “Saboda aure nake so malan!” Bata qarasa rufe baki ba yayi saurin zamewa daga riqe da fuskansa da yake da hannu ya tokare ga bencin dake gabansa yana mamaki, yajima bai sake cemata komai ba yana nazarin kalamanta masu ban al-ajabi har bayan wasu mintota kafin yace, “Amma Rashida kinsan meye aure kuwa, kinsan illar dake cikin jahilci da rashin ilimi acikin rayuwar d’an adam da kika zab’awa kanki shi?.” “A’a ko d’aya, Amma nidai kawai natsinci rayuwata abisa turbar son aure, wannan kawai shine dalilina.” Wata irin ajiyar zuciya ya sauke sannan yace, “Shikenan tashi kitafi, ALLAH yakyauta yazab’a mana mafi alkhairi?.” “Amin malan” ta amsa masa sannan tamik’e zata fita, har takai bakin qofa ya tsaida ita had’e da cewa “menene cikakke sunan mahaifinki Kuma awace anguwa kuke da zama?” “Sunansa malan bashar mai takalma, anan anguwar muke kusa ga masallacin juma’a dake nan gefen makarantar nan.” Jinjina mata kai yayi sannn ita Kuma tafita abunta hankali kwance…. _don Allah kutayani turawa a groups, gaba d’aya nayi missing nawa kafin komai yayi settling up_👏🏻 *_ALLAH KAJIK’AN IYAYEN MU👏🏻😭_* [6/16, 11:45 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  Page___8💎 Bin bayanta yayi da kallo har saida tafice sannan yayi ajiyar zuciya, azahirin gaskiya yayi mamakin yanda Rashida ta iya bashi amsa kai tsaye batare da tayi shayin komai ba, amma azuciyarsa yaga nagartar da kuma ingancinta data iya bayyana abunda ke cikin zuciyarta wanda da yawan ‘yammata irin wannan nadamunsu amma sai su gagara furtawa balle har asama masu mafita, Wanda kuma yin hakan kuskurene dake haifar masu da jefawa cikin halaka, koda yake mafiya lokuta iyaye sune sila saboda rashin sauraren ‘ya’yan nasu da wani dogon buri da suka d’orawa kansu, mik’ewa yayi tare da d’aukar littafin dake gabansa yanufi ajin da yake da darasi da d’alibansa. Yinin ranar abu d’aya ya dinga tunani shine kalaman d’alibar tasa, bayan yayi nazari da Kuma dogon tunani ya yanke shawarar iske mahaifinta yauidan an tashi makaranta, ana tashi kuwa ya hangota bakin gate ita da abokananta zasu fita da sauri yaturo wata d’aliba be takira masa ita. “Rashida malan Idris nakira ki” yarinyar tafad’a had’e da ficewarta don dama gida tanufa, kallon Rashida meenah qawarta tayi sannan takalli sauran friends d’insu had’e da cewa, “Anya rashida malan Idris ba sonki yakeyi ba?” “Wlh Nima haka nake zargi shamsiya” duka takaimasu had’e da cewa, “Bana son sa’ido, ni malaminane babu komai tsakanina dashi” “Hmm mudai bari muwuce kya cimmana” “A’a don Allah kujirani ba jinawa zanyi ba yanzu zan dawo.” tana gama fad’ar haka bata jira mezasu ceba tanufi wajensa, tana isa inda yake tsaye wajen iccen dalbejiya tace, “malan gani” “Yawwa Rashida dama akan maganar da mukayi dake jiyane.” “Meyafaru malan” tafad’a had’e da duqar da kanta qasa, murmushi yayi sannan yace “Babu abunda yafaru, Amma kin tab’a sanarwa da mahaifinki abunda kika fad’a mani?.” Saida tagyara zaman jikkar dake saman kafad’arta sannan tace “Nafad’a amma sai yayimun fad’a sosai tare da gargad’ina akan cewa kada insake inqara yimasa wannan maganar, inajin mahaifiyarsa nayi masa magana amma sai yace tafita batuna ai banida hankali karatu yakamata ace nayi yanzu, ni kuma daga lokacin ban sake yin maganar ba.” Girgiza kai yayi sannan yace ta tafi, koda takoma ta samu har lokacin suna nan a tsaye bakin gate suna jiranta, tambayoyi suka fara jefo mata amma ko kad’an batabi takansu ba tawuce abunta tana dariyarsu, Anayin sallar la’asar yaje gidansu had’e da yiwa mahaifinta sallama ya fito, dattijo ne sosai amma saboda yanada yalwar wadatar da za’a iyaci sau uku agidansa kowace rana bazaka iya fahimtar hakan ba, kujeru yasa aka kawo masu guda biyu qofar gida, bayan sun zauna suka sake gaisawa sannan malan Idris yayi masa bayanin koshi waye tare da cewa “Dama nazone akan batun Rashida ‘yarka” “Tofah injin malan bawani shashancin ta aikata ba?.” Mahaifin nata yafad’a tare da muskutawa ya gyara zamansa, “ko kad’an baba, kawai yanayin yanda take karatune yasa nace bari na bincika ko akwai wata matsala da kukasan tana fama da ita don asan wane irin taimako yakamata a matsayinmu na malamai mubata awannan gab’ar, saboda idan kalura awud’annan shekarun nata kamata yayi ace yanzu tana makarantar gaba da primary wato secondary amma ace gatanan har yanzu a primary kuma bata fahimtar komai kaga wannan matsalace da yakamata ace anbinciki dalilin da yasa takeyin haka.” jinjina kai mahaifin nata yayi tare da fitar da wani iska abakinsa sannan yace, “Hmmm! Malan karabu da wannan yarinyar, babu wata matsalar dake damunta in banda daqiqanci da kuma shashanci, ko kad’an bata son karatu tuntana ‘yar qanqanuwarta, haka mukayita fama da ita har takai wud’annan shekarun, hatta aji shiddan da kagata saida nabiya kud’i masuyawa sannan nasamu akaturata saboda tasamu takardar shedar qare primary don insamu inkaita tagaba da ita wato secondary, alokacin tana qarama na d’auka quruciya ce sai yanzune data girma na fahimci cewa abun nata iskancine da rashin maida hankali wajen karatu, ko kad’an ba tason karatun shiyasa takeyin hakan.” STORY CONTINUES BELOW  “Amma baba ai wannan babbar matsalace da yakamata ace kazaunar da ita katambayeta saboda ataimakawa rayuwarta, duk yaron da kake gani anhaifesa da baseera, kawai rashin samun daidaituwar layin d’aya kamata su haune kansa kaganesu haka, inada yaqini akan da za’a fara magance mata matsalar da kesa ta kasa maida hankali ga karatu to da tabbas za’asha mamakin ganin baiwar da ALLAH yayi mata,” “Taya zan iya magance mata matsalarta malan bayan bazata yuyu ba?, Shekarunta duka sha biyar aduniya yanzu tashigo shekara ta sha shida, taya zan iya aurar da ita awannan lokacin? Yarinyar da batasan komai ba aduniya ga kuma rashin ilimi da yake d’awainiya da ita, wakake tunanin zai iya karb’ar amanarta idan na damk’a masa?” “ALLAH shine masani baba, tunda wannan itace matsalarta zaifi kyau ace anyi mata auren da ace anbarta ga tutar babu, ba ilimin kuma babu auren daga qarshema inba ALLAH yakare ba abunda ba’aso yabiyo baya, ni Ina ganin da zakayi hak’uri kayi mata auren da yafi, shekarunta basuda illar da zasu hanata aure saboda ada iyayenmu da shekaru goma sha biyu ake aurar dasu kuma su zauna lafiya har su haifemu ba tare da sunyi wani karatu ba.” Rai b’ace mahaifinnata ya mik’e had’e da cewa, “ni bazanyi hakan ba, domin wancan zamanin daban wannan ma daban saboda haka idan wannan yakawoka tashi katafi don wlh ko bataso dole sai tayi karatu, wayasani ko kune kuke b’ata mana yara kuna juya masu ra’ayi saboda son kanku.” “Subhanallahi, gyara kayanka baba ai bazai zamo sauke muraba ba, a matsayina na malami don na bibiyi matsalar dake jawowa d’alibina rashin fahimtar karatu bazai zama illa ba, kuma wannan ai shawarace nabaka saboda kasamawa ‘yarka maslahar rayuwa da kuma kai kanka, idan kana ra’ayi saika d’auka idan Kuma baka ra’ayi kanada damar da zaka ajiyeta, meye abun b’acin rai da har zaikai ga wud’annan kalamai haka!.” “Naji kuma nagode kama hanya katafi.” Mik’ewa malan Idris yayi ransa duk babu dad’i had’e da gyara tsayuwarsa sannan yace “Zan tafi kayi hak’uri don ALLAH bisa shiga rayuwarka data ahalinka da nayi amma karka manta annabi yace _kullukum ra’in wa kullukum mas’ulun an ra’iyatihi_ damu malamai da kuma ku iyaye dukkaninmu makiyayane kuma dukkaninmu abun tambayane akan abubuwan da aka bamu kiwo, kayiwa ALLAH godiya daya baka ‘yar da zata iya fad’a maka gaskiyar abunda ke ranta sab’anin wasu ‘ya’yan da saidai iyaye suganesu da abun kunyar da son ransu ne ya jawo hakan.” Yana gama fad’a yabar wajen cike da mamakin iyayen dake tafka kuskure irin haka da zai kaisu ga dana sani…. *_ALLAH KAJIK’AN IYAYEN MU_*👏😭 [6/17, 11:38 AM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___9💎 Yana barin wajen saiga Rashida tafito zataje islamiya, kallo d’aya tayiwa mahaifin nata dake faman fad’a yana suruttai ta d’auke kai saboda sanin halinsa, ta gabansa tabi zata wuce ya daka mata tsawa yana fad’in, “shashashar yarinyar zo nan.” dawowa tayi agabansa ta durqusa kanta sunkuye ak’asa yaci gaba da cewa, “wane d’an iskan malamine kika turomun har gida ya titseni yana nema yafad’a mani maganganu akanki.” Cikin rashin sani tace, “malami kuma baba?, Wlh ni ban turo maka kowa ba.” Aharzuqe yayo kanta yana fad’in “wato baki san ko waye ba ko? Maza shiga cikin gida idan jikinki yafad’a maki zakiyi bayani daqiqiyar yarinya kawai da batasan abunda takeyi ba.” STORY CONTINUES BELOW  “Baba makarantar islamiya zanje fa.” Tafad’a tana turo baki had’e da ja baya daga durqushen da take, ganin yayo kanta yasa ta tashi tanufi cikin gida da gudu, bayanta yabi yana cigaba da fad’an har ya shiga cikin gidan, hangota yayi tab’uya abayan mahaifiyarta dake shara tsakar gida tana fad’in, “don ALLAH Baba kayi hak’uri ni bansan kowaye ba.” “Koma waye shi ni bai isa ya canjamun ra’ayi ba, karatune sai kinyi ko bakyaso har gaba da secondary in Sha ALLAH, don haka idan zaki dage kimaida hankali kiyi karatu ki dage donni bazan aurar dake yanzu ba har sai kin kammala degree.” Bubbuga qafa Rashida tafarayi tana kuka yayinda mahaifiyarta da baba sukayi tsaye suna kallon ikon ALLAH cike da mamakin wai meyake damun tane da gaba d’aya ta zubar da kunyar da aka san ‘ya mace da ita agabansu tana kukan aure take so, wani irin takaici ne yarufe baba ya karb’e tsintsiyar dake hannun mahaifiyar tata yafara zabga mata jiki tasa ihu tana tsalle tsalle tana fad’in, “wayyo baba kayi hak’uri, ni ban turo kowa ba wlh, malan Idris kad’ai ne ya tambayeni a ina ne gidanmu na fad’a masa amma daga haka bance masa komai ba, wayyo umma kice yadena dukana da tsintsiya fa babu kyau” kad’an yarage ita da baba suyi dariyaganin yanda take tsalle kabar d’an biri, cikin gimtsewa baba yace “Ai k’wanda nadukeki da ita ko kyabar wannan zancen banzar da kikeyi kinatsu kiyi karatu.” “Ni bana son karatun nan baba wlh…” Bata qarasa ba umma tayo kanta da sauri tarufe mata baki gudun kada tajawo mata abun fad’i a makwabta, jefarda tsintsiyar baba yayi yafice gidan yana wani huttai sai kace namijin zaki yabar umma da ita tana yimata fad’a. “Haba Rashida! Haba Rashida! wannan abu dame yayi kama, don ALLAH meyasa bazaki natsu kiyiwa kanki fad’aba, yanzu meye illar mahaifinki don yace kiyi karatu?, ‘yafa mace kike kuma haihuwa zakiyi, da wane ilimin kikeso kiyiwa naki yaran tarbiya idan har bakiyi karatu yanzu ba?.” Ita dai banda dudduba jikinta da shacin tsintsiya duk yabi yakwanta mata babu abunda takeyi, asalima ba sauraren umma take yiba balle tasamu amsoshin tambayar da take yimata, “umma dubi yanda baba ya fasamun jiki da tsintsiyar nan bacin yasan duka da ita babu kyau?” Tafad’a hawaye kwance a fuskarta tana kallon umma, tsabar takaici yasa umma mik’ewa had’e da zungureta tabar d’akin tana fad’in, “ai shikenan ke kika sani tunda bakisan ciwon kanki ba sai kije kiyi abunda kike so, ana yimaki magana don kin raina wayon mutane kin maidani mahaukaciya nakiyi kikeyi, in akwai abunda yafi aure kije kiyi idan kina iyawa, shidai ilimi da kike gani garkuwane acikin kowace irin rayuwa tad’an adam, wanda kuma duk baya dashi babu banbanci tsakaninsa da dabba.” Acan cikin d’aki Rashida tace “Haba umma, haba umma dabba fa kikace, ALLAH dai yatsareni,” “Eh dabba mana, meye banbancin tunda bazai iya fahimtar duk abunda rayuwa take ciki ba balle ya banbance tsakanin baqi da fari acikin al’ummar dake zagaye dashi, matuk’ar baki sauka akan dokin naqin da kika hauba kika natsu kikayi karatu to tabbas kema d’in bakida banbanci da wannan akuyar da kike gani d’aure” tak’arasa maganar tana juyawa akuyar k’asarin dake gabanta, d’ago kan da zatayi taga Rashida tsaye agefen k’ofar d’akin kumbure da fuska tak’urawa akuyar idanuwa, harara ta cillama ta sannan tace, “ki kalleta dakyau kigani k’ilan har saita fiki gata saboda ita babu mai takura mata kuma dole abata abinci taci batare da zagi ko duka da tsangwama ba Amma kefa? Wayasan me gobenki zata haifar maki.” “Kai umma nifa inada ilimin arabi, taya zakice d’aya muke da wannan abar dako tsarki batayi balle tasan farillan arwala dana sallah kuma har kice saita fini gata wai don d’ai banida ilimin boko, nidai don ALLAH kubarni bana son karatunnan wlh nafison aure akansa” awannan karon kasa cewa komai mahaifiyar tata tayi harna tsawon wasu lokuta maganganunta kad’ai take ji nayi mata yawo a k’wak’walwa, a inda take tadawo tarik’o hannuwanta ta zaunar da ita sannan itama ta zauna suna fuskantar juna tace “Rashida kifad’amun gaskiya, meyasa kike son ayi maki aure ba tare da kinyi la’akari da wud’annan qananan shekarun da kike dasu ba.” “Umma nima ban sani ba, kawai ji nakeyi ina tsintar kaina a wasu lokutan cikin yanayin sha’awar son yin auren.” “Rashida kin kuwa san me kalmar aure kenufi?” STORY CONTINUES BELOW  “Eh malamin islamiyarmu yace mana shine kasantuwar mace da namiji a inawu d’aya bayan angabatar da sadaki da kuma waliyai da shedu, sannan yace ashari ance shine idhalu shai’i fishshai’i wato shi…” Saurin dakatar da ita umma tayi gabanta nafad’uwa had’e da cewa “Ya isa Rashida na yarda kina da ilimin arabiy kuma ke ba daqiqiya bace kamar yanda muke fad’a amma da kin amince dayin karatun bokon ma koda secondary ne saboda shi yana taimakawa wajen iya zaman takewa da mutane, ayanda kikayi bayani aure baya kasancewa har saida samuwar namiji da mace, to ke yanzu ina namijin da kika tanada ayi maki auren.” “Umma akwai wani Rabe d’an gidan mai koko dake sona idan kuma bakwa sonsa zaku iya zab’amun duk wanda kuke so” Wata irin ajiyar zuciya iya ta sauke don tasan abun da kamar wuya mahaifin nata ya amince da auren yaron saboda rashin cancantarsa, tashi tayi ranta adagule taci gaba da aikace aikacenta batare da tasake bita kanta ba. Adaren ranar kasa bacci mahaifiyar tata tayi saboda tunanin maganganun ‘yarta, in banda juye juye babu abunda takeyi domin tasan mahaifinta bazai yarda yayi mata abunda take so ba kuma ab’angaren yarinyar tafahimci kalamanta da gaske takeyinsu har cikin zuciya, tanajin tsoron kada rashin yimata abunda take son ya jefata cikin wani mugun hali ko iftila’in rayuwa da zai kaita yabaro ko kuma yatab’a mata mutunci da kuma kimarsu, fashewa tayi da kukan da yasa baba farkowa daga baccin da yakeyi a tsorace had’e da cewa “subhanallahi maman Rashida lafiya kike kuka awannan tsohon daren haka, me akayi makine, meke faruwa dake ne?” Cikin shesshekar kuka tace “Babu komai malan, kawai Ina sone don ALLAH kabar yarinyar nan tayi aure shine alfarmar da zan roqa awajenka amatsayina na mahaifiyarta.” Tsaki yayi had’e da jan mayafinsa ya komawarsa yakwanta yana fad’in dama wannan maganarce ta zaunar dake kina kuka?, To wlh kinji na rantse bazanyi mata aure yanzu ba dole sai tayi karatun da nake so.” “Kada kace haka don ALLAH, bamusan awane yanayi take acikiba wanda yasa ta furta hakan, katunafa mu iyayene daya kamata ace ‘ya’yayenmu na alfahari dasu, kuma kada kamanta su amana ne da ALLAH yabamu ahannayenmu bai kamata ace munwofantar da buqatunsu da ALLAH yad’ora akanmu ba, don ALLAH tunda bata son karatunnan kayi hak’uri muyi mata auren tunda bamusan abunda ALLAH kenufi ba.” Fita batunta yayi yaci gaba da baccinsa tanata faman basa hak’uri da rok’onsa, tun yana jinta har yadena bacci ya d’aukesa, data fahimci hakan taje ta d’auro arwala ta tada sallah tana fad’awa ALLAH daya sauko da zuciyar mijin nata ya amince da yima ‘yar tasu aure, Haka yatashi da asuba ya sake tadda ita tana kukan, shiru yayi yana kallonta na tsawon mintuna kafin yayi tsaki had’e da mik’ewa yabar d’akin, arwala yayi lokacin har antada sallah anan masallacin dake kusa dasu yafice da sauri, be dawo gidan ba har saida rana tafara fitowa nan ma sake iskota yayi tana kukan, tsaki yaja sannan ya zauna agefen gado yana kallonta yace, “Yanzu wannan kukan da kikeyi tun jiya fisabillahi bai isheki ba?” “Taya zai isheni bayan fargaba da tsoron halin da ‘yata zata shiga ciki yana dasqare azuciyata,” girgiza kai yayi had’e dayin wani tsakin na ba adadi kafin yace “to yanzu ya kike son ayi?.” “Kayimata abunda take so tunda bai sab’awa shari’a ba.” “Ita fa rantsuwar da nayi?.” “Zan fidda maka da kono.” Kallonta yayi cike da tausayin yanayin data koma tsakanin jiya da yau, macece ita mai hak’uri da kuma juriya, iya kyautatawa da kuma biyayyar aure tana yimasa, ko kad’an bata son taga ransa yab’aci shiyasa shima bayason ganin nata b’acin rai, matuqar yin hakan zaisa tayi farinciki kamar yanda take faranta masa to zai amince da buqatar yarinya, nisawa yayi sannan yace taje takirawo masa ita, mik’ewa tayi duk jikinta ba k’wari taje takirawota, bata jima da dawowa ba sai gata tashigo, gaidasu tayi suka amsa mata sannan tanemi waje tazauna, STORY CONTINUES BELOW  Gyaran murya mahaifin nata yayi had’e da cewa, “Rashida naso inbaki ilimin dako bayan ranmu zai amfaneki kuma kiyi alfahari dashi amma hakan ya cutara saboda wani buri da kike dash a ranki, mahaifiyarki nagartacciyar matace da tasan dukkanin haqqoqan zaman takewa da bazan iya jurar halin dana ganta daga daren jiya zuwa yau ba, don haka bisa roqo da tayi nahak’ura da ra’ayina na amince da naki kuma zanyi maki abunda kike so saboda wanzuwar farincikinta amma Ina so kisa aranki kuma kirubuta ki ajiye azuciyarki cewa ilimi shine gishirin zaman duniya da bawa kan ribatu dashi adukkanin tsawon rayuwarsa kuma ko yaushene zaki dawo da kanki kinemesa” Shiru yayi na wani d’an lokaci sannan yace, “Don haka idan kinada wanda kike so na amince ki sanar dashi cewa yaturo iyayensa.” “Baba kayi hak’uri amma ni banida wani masoyi sai Rabe na gidan hajia mai koko.” Dariyar takaici yayi sannan yace, “wannan baiyimun ba kicanza wani, domin yaron duka duka shekarunsa basu wuce ashirin ba taya zai aureki har ya iya kula dake, yanzu haka yana can makarantar kwana aji biyar shi yaje yanemi ilimin, to ta ina yaga inda zai ajiyeki.” “To shi kad’aine ke sona baba Amma zaka iya zab’amun duk wanda kaga ya dace.” Cike da mamaki yake kallonta kafin yace, “kinsan me kike fad’a kuwa.” “Eh baba nasani kazab’amun ko waye zanyi masa biyayya kuma zan zauna dashi.” “Shikenan tashi kitafi.” Yafad’a yana murza hannayensa daya had’e waje d’aya, Bayan tafita yakalli mahaifiyarta yace “Kingani abunda nake son kigane kenan, tadami mutane da aure take so amma gashi takasa fiddo da wanda zata aura, ina tausayin rayuwarta saboda nasan SANNU SANNU bata hana zuwa…, ba baki nayi mata ba amma duk daren dad’ewa inada yaqini akan sai taga illar rashin tsayawa tayi karatunnan, kiduba fa ko had’a haruffan hausa bata iyayi taya rayuwa zata zauna ahaka.” “Gaskiyane malan amma mubita da addua shiyafi, yaran zamanine kahaifesu baka haifi halin suba” Anan ya zauna yana bata labarin abunda yafaru jiya tsakaninsa da malamin makarantarsu d’aya iskosa akan matsalar rashin gane karatunta sannan yafad’a mata shawarar daya yanke akan mijin da zai aura mata, fatan alkhairi umma tayi had’e da fatan Allah yasa wanda aka zab’a mata d’in ya amince da ita…. _Note_ _A wannan gab’ar yakamata iyaye su fahimci cewa duk wani kalami da ‘ya’yansu zasuyi yakamata ace sun natsu kuma sun zauna sun fahimcesa kamar yanda mahaifiyar Rashida tayi domin kowane yaro yanada k’wak’k’warar hujja da dalili akan kowace irin kalmace da zai fad’a Wanda sune zasu iya banbance mai kyauce ko kuma akasin haka, kamar dai Rashida ga bayanin data zauna tayiwa mahaifiyarta duk mai hankali yasan cewa zancen auren da take fad’in tana so har azuciya ne bawai abaki kad’ai ba, kuma kowane yaro da yanayin qaddarar da Allah ked’orasa akai tun yana qanqaninsa wacce iyayene solar tabbatuwarta akansa, don haka iyaye mudinga natsuwa muna nazartar kowane harafi kuma kowace kalma tare da kowane muradai na ‘ya’yanmu don sama masu mafita akan abubuwan da zasu iya jefasu da uma mu cikin nadama da dana sani nahar abada, ilimi nada amfani sosai amma idan jiran asamesa zai iya jefa rayuwar ‘yarki/ka cikin wata matsala za’a iya jinginesa har sai bayan an kauda waccan matsalar sai aci gaba da nemansa, ubangiji ALLAH yasanya muradanmu na alkhairi su daidaita dana ‘ya’yanmu domin tabbatuwar farincikinmu da kuma samuwar ingantacciyar rayuwarsu, ba abun mamaki bane abunda Rashida ta aikata domin yasha faruwa ga wasu ‘yan matan kuma yakanci gaba da faruwa, wasu kan furta da baki wasunsu kuma kannuna alama, amma sai kaga iyaye sun kasa fahimtarsu tare da kauda idanuwansu akan abunda suke son (aure) sai kaga sun lalace daga qarshe ma sun jawo masu abun fad’i aduniya wal iya zubillahi ALLAH kashirya mana zuri’armu_ *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/18, 6:47 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 STORY CONTINUES BELOW  _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___10💎 Misalin qarfe goma na safe baba yanufi makarantar su Rashida yasa aka aka kirawo masa malan Idris, cikin girmamawa yayi masa sallama tare dasa wata d’aliba ta d’auko masu kujeru guda biyu ta aje masu a k’ark’ashin inuwar wata bishiya dake a tsakiyar compound d’in makarantar, hannu ya basa suka gaisa had’e da cewa “bisimilah baba” yana nuna masa kujerun, tare suka jero har suka iso wajen, saida ya zauna sannan shima yazauna yana nazarin abunda yakawoshi bayan jiya sun rabu baran baran dashi, shiru yabiyo bayan gaisawar tasu kafin can baba ya nisa yace “Ina fatar kaganeni malan?, nine bashar mai takalma wato mahaifin Rashida wanda jiya kaje wurinsa” murmushi malan Idris yayi kafin yace “naganeka baba, ya gida? Ya iyalin?, Injin dai ko lafiya naganka yanzu?” “Eh lafiya klw alhamdulillah, dama nazone inbaka hak’uri bisa abunda yafaru jiya, sai daga baya dana zauna nayi nazari nafahimci nayi kuskure akan abunda nayi maka, saboda shi gyara kayanka bazai zama sauke muraba ba, zuciyata ta gamsu kuma ta amince da shawararka don haka nazo inbaka hak’uri, don ALLAH kayi hak’uri bisa kausasan kalaman da nayi agareka, kasan duka mai rai ajizine” kansa na aqasa yana murza ‘yan yatsun hannunsa ya d’ago yana kallon baba sannan yace “Karka damu baba, wlh babu komai ai haka rayuwar tagada, wasu mutane nada saurin fahimta da kuma yarda wasu kuma akasin haka, koma dai meye ni babu komai araina nayafe maka, saboda haka kamanta da komai babu wata damuwa, mukan yiwa ALLAH laifi ya yafe mana balle mudaya halitta.” Jinjina kai baba yayi yana qara yaba hali irin nasa tare da tunanin ta inda zai b’ara b’ullo masa da d’ayan zancen daya kawoshi, cikin dakewa yayi gyaran murya had’e da cewa “madalla malan naji dad’i sosai kuma nagode, Allah yayi albarka yasa agama lafiya, hak’ik’a samun mutum irinka awannan duniyar da za’ayiwa laifi kuma adawo arok’esa yafuwa kai tsaye yayafe nada wahala, nagode sosai” “Babu komai ba ai yawuce” “To bari natashi natafi nasan bazaka rasa ajin da zaka shiga koyarwa ba yanzu” “Ai yau aji d’ayane agareni baba kuma tun safe nagama dasu saboda first period ne, Bari dai akirawo maka Rashida ko?” “A’a kyaleta kasan yau juma’a bawani dogon lokaci bane gashi lokacin zuwa masallaci na gabatowa” mik’a masa hannu yayi suka sake gaisawa sannan yajuya zai tafi, har yayi taku biyu sai kuma ya tsaya had’e da juyowa yace “Emm nace bakaji ba?.” Juyowa malan Idris da har yafara tafiya shima yayi had’e da cewa “Na’am baba, magana kakeyi?.” “Eh, dama nace baka fad’amun sunan kaba da kuma inda kake don da alama bautar qasa takawoka nan!.” Saida yayi murmushi sannan yace, “Sunana Nura idris aliyu, Amma anfi sanina da Idris aliyu saboda da haka abokanan karatuna suke kirana a makaranta shiyasa sunan yabini, ni d’an garin nanne a qauyen bebeji.” “Ikon ALLAH, inada aboki acan kuwa, sunansa malan idi ko kasanshi, muna had’uwane idan munje cin kasuwanne dashi.” Dariya yayi had’e da cewa, “in dai malan idi mai awaki kake nufi toshi d’in ai mahaifina ne.” “Allahu akabar malan dawo mu zauna.” Baba yafad’a yana maijin cewa in sha ALLAHU haqarsa zata cimma ruwa, dama shi kuma malan idris kamar yanda yafad’a bayada wani ajin yanzu don haka ya sake dawowa suka zauna, “Aikuwa aminina ne sosai, sharabona dashi tun watanni biyar da suka wuce yacemun zaiyi tafiya to har yanzu kuma bamu sake had’uwa ba, ko har yanzu bai dawo bane?” STORY CONTINUES BELOW  “A’a baba yadawo amma a hanyarsa tadawowa yasamu had’ari yanzu haka yananan gida zaune ana jinya yau sauqi gobe ciwo, wannan watansa na hud’u kenan baya zuwa ko ina” “Subhanallahi, gaske mukajisa shiru kuma gashi ALLAH baisa mukabi bayansa ba muji ko lafiya? Sai satinnan daya wuce muka fara shawarar zuwa nemansa don munzata tafiyar tasa mai dad’ewa ce shiyasa muka jisa shiru, ubangiji ALLAH yabashi lafiya yasa kaffarane, insha ALLAH ranar lahadi munanan tafe mudubashi, bawan ALLAH! malan idi ai mutumen kirkine.” “Amin baba ALLAH ya yarda.” Wannan zancen da baba yaji shine yahana yayiwa malan Idris zancen Rashida alokacin amma sosai yasake samun natsuwar mik’a aurenta a hannunsa kodon nagartar mahaifinsa da kuma tasa, sun d’an jima suna hira anan yake sanar dashi yau d’innan in ALLAH yaso zaije can qauyen yadubo mahaifin nasa kuma insha ALLAH zai fad’a masa cewa yana gaisheshi sannan baba yawuce bayan yakarb’i address d’insa. Bayan yawuce malan Idris yayi dariya tare da cewa “ALLAH mai iko!haka rayuwa take shiyasa akeson kazauna da kowa lafiya, da ace jiya bayyita tausar zuciyarsa ba akan abunda baba yayi masa daba qaramar kunya yau yajiba kasancewarsa abokin mahaifinsa.” Sake murmushi yayi sannan yakoma cikin office d’insa Rashida kuwa tuni cikinta yad’uri ruwa ganin mahaifinta a makarantar, atunaninta yazone saboda abunda yafaru jiya, tsoronta d’aya kada yauma idan takoma gida ya doketa idan malan idi yafad’a masa sauran abunda tace, jikinta har rawa yakeyi atashi taje wajen malan Idris taji abunda yakawo mahaifinta don gaba d’aya ta manta da zancen da tayi dashi da safe akan yazab’a mata duk mijin da yaga dama kuma tunaninta bai kawo mata baba zai iya nema mata malan Idris ba, ana tashi tanufi office d’insa har suna cin karo dashi yana qoqarin rufe office d’in batare data damu ba cikin turo idanuwan dake nuna tsoro qarara a fuskarta tace “don ALLAH malan meya kawo baba makarantar nan!? Wlh inajin tsoron kar ace ka koma cemasa wani abun akaina ya sake dukana, ko ranar da kaje gidanmu saida yazaneni sosai da tsintsiyar shara” qura mata idanuwa yayi yana kallon yanda bakinta ke motsawa da yanda idanuwanta suka firfito saboda tsoro, ji yayi kamar ma bai tab’a ganinta ba sai yau saboda yanda yanayin tsoron nata ya bada wani fasionable atattare da ita, yanda take game hannu tana tambayarsa yasa jikkar hannunta fad’uwa da sauri ya duqa zai d’auko mata itama alokacin taduqo sukayi karo da juna, “Yi hak’uri malan.” tafad’a had’e da d’aukar jikkar ta rataya akafad’a, girgiza kai yayi kamar wani soko sannan yafara tafiya yana murmushi had’e dajin wani abu akanta, da gudu ta cimmasa tace, “malan baka fad’amun kome mahaifina yazoyi anan ba.” “Kashi yace abaki.” Shine amsar daya Bata atakaice yanaci gaba da tafiyarsa, tsaye tayi kamar andasata awurin kafin tasake rugawa ta cimmasa, “malan, malan kashi fa kace!, to ni menayi kuma.?” “Saboda bakyason karatu.” “Amma ai d’azu shiyace ya amince tunda aure nakeso zai yimun!” Tsaye malan yayi zuciyarsa nabugawar da baisan dalilinsa ba kafin yajuyo yana kallonta had’e da cewa, “waza’a aura makine?” gyara jikkarta tayi had’e da ware hannuwanta tana fad’in, “Ban sani ba, da akwai wani Rabe dake sona amma baba yace beyi masa ba, don haka shizai zab’ani miji da kansa” ajiyar zuciya ya sauke had’e da cigaba da tafiya tana biye dashi agefensa yaci gaba da cewa “Kuma ke kin amince?” “Eh, ni nace ya zab’amun duk wanda take so” “Kuma duk wanda aka zab’a makin zaki yarda ki auresa?.” “Eh mana zan yarda tunda ni nace na amince.” “Ko waye shi?.” “Eh, kowaye shi” “Koda ace nine? zaki yarda” “Eh, zanyarda man..” Bata ida fad’aba tayi saurin rufe baki tare da zaro idanuwanta tana kallonsa jin abunda yafad’a, juyowa yayi shima yana kallon cikin idanuwanta d’aya bayan d’aya sannan jinjina mata kai tare da sakar mata murmushi yace “ina sonki! Zaki aureni!” Yaqarasa maganar yana dariya tare da barin wajen batare daya jira jin amsar da zata bashi ba yana jin wani shauqi da kuma farinciki atattare dashi, Ita kuwa Rashida gaban tane yayi mugun fad’uwa tare da sakin jikkar dake sagale a kafad’arta tafad’i k’asa, kallonsa takeyi har ya qurewa ganinta kalmar Ina sonki d’aya fad’a nayi mata yawo a k’wak’walwa, tafi mintuna biyar awajen tsaye kafin tad’auki jikkarta tanufi hanyar gida jikinta kamar wacce aka zarewa lakka, A ranar yini tayi data motsa fuskarsa take tunanowa da kalamansa tayita murmushi, ganinta cikin wannan yanayin yasa umma ta sake tsorata da al-amarinta, don atunaninta tsabar farincikin amincewar da mahaifinta yayine akan zaiyi mata auren kesata wannan nishad’in, d’azu garin kallonta har k’walewa tayi ajikin bangon qofar shiga d’aki, Haka ab’angarensa daya rufe idanuwa babu abunda yake gani sai yanda bakinta ke motsawa da idanuwanta, ahankali yakejin sonta nashiga acikin zuciyarsa da kuma sauran sassan jikinsa, Rashida kyakkyawar yarinya ce irin black beauty d’innan, tanada tsayi sosai don takusa kaimasa a kafad’a, tanada manyan idanuwa da zarazaran gashin ido hancinta bayada wani tsayi sosai amma saboda ramin idanuwa da take dashi zaka d’auka dogon hanci ne da ita hakama bakinta d’an madaidaicine ciccif fuskarta, bai tab’a lura da hakan ba sai yau daya qura mata idanuwa, Daga shi har ita matsuwa sukayi weekend taqare saboda mararin son ganin juna sai dai ab’an garenta takan shiga damuwa idan tatuna da cewa tariga da taba mahaifinta damar zab’a mata mijin da zata aura, gashi ba zato ba tsammani malaminta ya dasa mata soyayyarsa azuciyarta, duk wani motsi da zatayi tsananin sonsa ke sake shiga ranta, kuma ayanda tasan halinsa tunda har tafurta da bakinta kuma ya tambayeta ta amince da duk zab’in da zaimata to bata isa yanzu taje masa da wani sauyin magana ba, Shikam malan idris safiya na wayewa ranar asabar ya isko mahaifinsa ya sanar dashi komai ba tare daya b’oye masa ba akan aminin nashi da suka had’u da kuma zancen ‘yarsa d’aya gani yana so wacce ayanzu yake da nufin aurarwa, sosai mahaifinsa yaji dad’i kuma yayi murna ya tabbatar masa da cewa idan ALLAH yabashi lafiya nan da sati mai zuwa zaije suyi zancen ko yatura qannensa suyo masa maganar, anan yake sanar dashi cewa ai yasan halin aminin nasa yanada matuqar kirki amma akwaisa da zuciya da kuma kafiya, shiru malan idris yayi tuna yanda suka fara kwashewa dashi shekaran jiya wanda yatabbatar zuciyace tasa yayi hakan, nisawa yayi kafin yace “To baffa don ALLAH kayi masa magana dawuri saboda ko yaushe zai iya bada aurenta ga wani, gashi kuma kace yacika kafiya da yawa” dariya baffa yayi tare da bubbuga kafad’arsa yace “To Nuraddeen, ka kwantar da hankalinka in Sha ALLAH bazan bari haka tafaru ba, bari idan sunzo gobe d’in sai nafara b’ulguta masa maganar sai muji me zaice kaji ko?.” haka sukaci gaba da tattaunawa akan matsalar ciwonsa har yake cemasa shi dai yaso ace cikin ‘ya’yansa wani yayi karatun kiwon lafiya kodon taimakon gida da waje, gashi yanzu sai faman kashe kud’i akeyi akan matsalar ciwonsa kuma sunk’i fad’a masu gaskiyar abunda ke damunsa balle a tsammani waraka nan kusa ko kuma nesa. Ranar lahadi misalin karfe sha biyu na rana, baba da wasu abokanan kasuwancinsa su uku da kuma qanensa da shima duk tare ake akasuwa suka kama hanyar bebeji don gano malan idi, basu kaiba sai misalin k’arfe biyu na rana saboda yanayin injinin motar da sukaje da ita Bata cika kyauba sai an lallab’a, qannen malan idi su biyune suka tarbesu tare da shigowa dasu cikin gida inda yake zaune saboda hatta qugunsa yasamu matsala be iya tafiya. Sosai farincikin ganinsu ya bayyana a fuskarsa kamar yatashi sama don murna, haka suma saidai su nasu farincikin ya surku da tausayinsa ga yanda fuskokinsu suka nuna, saboda malan idi mutumne mai dad’in sha’ani da kuma hak’uri, kusan ma halin sane malan Idris ya gado, murmushi ya dinga yimasu yana fad’in “karku damu alhamdulillah Ina samun sauqi, muyiwa ALLAH godiya da yasa fuskokinmu suka sake had’uwa badon haka ba ai shikenan rabuwarmu kenan tun ranar.” Abinci aka kawo masu yasa malan Idris daya shigo gaishesu ya zuzzuba masu abincin, bayan sunci sun sai gashi yasake shigowa da gorunan lemu da ruwa yakawo masu hadda mahaifin nasa da qannensa, har zai fita baffa ya kallesa had’e da cewa, “Dawo nan kazauna” yana nuna masa gefen da baba take zaune, gaban sane yafad’i tare da sadda kai qasa sannan ya qaraso ciki ya zauna amma acan d’an nesa dasu, gyaran murya baffa yayi sannan yace…. _Tofah baffa zai fasa kwai agaban kowa🤣 Bari in gudu kafin kaina yayi girma saboda kunyar da zan tayasa ji😅 don son jin abunda baffa zai fad’a yau to inji ruwan comment idan ko ba haka ba kuda new update sai upper week😒_ *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU_*👏😭[6/19, 9:17 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___11💎 Gyaran murya baffa yayi yana kallonsu baba kafin yace, “Malan bashar nasan kai kasan wannan” yana nuna d’an nasa sannan yaci gaba da cewa “don haka Babu buqatar in sake gabatar maka dashi saidai ko in wud’anna ‘yan uwan nawa, amma ku su alhaji surajo, malan hashimu, sa’idu, malan shu’aibu da malan balarabe ga d’anku nan Nuraddeen wato d’an wajena koda ALLAH zaisa wata rana a had’u zaku iya ganesa shima yagane ku, wud’annan su biyun da kuke gani kuma qannena ne uwa d’aya uba d’aya wato Usman da aliyu, inafatar ko bana raye ace abota da kuma mutuncin dake tsakanina daku bai yanke ba, inaso ya zamana cewa idan anhad’u da juna za’a iya gaisa har kudinga tunowa dani kuna yimani addu’a”+ “Ashsha malan idi! don ALLAH kadena fad’ar haka domin ita cuta ba mutuwa bace, mudai fatanmu d’aya shine ubangiji ALLAH yabaka lafiya kuma ALLAH yaraya manasu shi da sauran ‘yan uwansa ya tashi kafad’unka acikin iyalinka.” Haka suka dinga fad’a tare da yimasa addu’a, Shiru baffa yayi yana kallonsu d’aya bayan d’aya nan take yaji wasu hawaye sun cika masa idanuwa, tari yafarayi wanda hakan yabawa hawayen dake maqale a idanuwansa damar zubowa, sannu duk suka dinga jero masa cikin jin k’warin guiwa ya kaikaita idanuwansu yana goge hawayen had’e da amsa masu, Bayan tarin ya lafa masa ya maido kallonsa ga ‘yan uwansa da kuma d’an nasa suma ya gabatar masu da aminan nasa inda har yak’ara masu da cewa shi awajensa abokan nasa sunfi qarfin yakirasu da abokanai ko aminai saidai yace sud’in ‘yan uwan sane shaqiqai, don haka yana roqonsu dasu riqesu hannu biyu bisa kyautatawa da kuma girmamawa, gaba d’ayansu ji sukayi jikinsu yayi sanyi saboda yanayin yanda yake magana tamkar wanda ke barin wasiya, murmushi yayi ganin yanda fuskokinsu suka canxa had’e da cewa “kada kusaka kawunanku cikin damuwa akan maganganun dake fitowa abakina domin natabbata daga cikinsu akwai wud’anda zasu sanyaya zuciyoyinku kuma su sakaku cikin farinciki marar misaltuwa” juyowa yayi inda d’an nasa me zaune yace, “Nuraddeen tashi katafi, ALLAH yayi maka albarka” ajiyar zuciya malan Idris ya sauke had’e da mik’ewa tsaye yad’an sunkuyar dakai agabansu alamar girmamawa sannan yafice daga d’akin, Bayan yafita baffa ya kalli ‘yan uwansa yace, “usman, Aliyu Ina son kunemawa d’anku Nuraddeen izinin neman auren Rashida ‘yar gidan malan bashar a hannun iyayenta dake zaune agabanku idan har ba’a tsayar mata da miji ba kamar yanda d’annaku yabuqata cewa yana sonta” Wani irin annurine da farinciki ya bayyana a fuskokinsu gaba d’aya jin kalaman dake fito daga bakin aminin nasu in banda baba da kuma aliyu qanen baffa, shidai baba tsantsar farincikine da kuma mamakin jin cewa wai malan idris nason ‘yarsa Rashida, shikuma Aliyu tsananin bak’inciki da takaicin hakanne da yaji yasa yakasa b’oyewa saboda ‘yarsa muneera yaso ya had’a aurensu da shi saboda yanda take tsananin sonshi. Sosai baffa yalura da sauyawar fuskar da d’an uwansa tayi Amma sai ya basar saboda jin Usman na fad’in “Masha Allah, alhamdulillah, agaskiya haka yayi kyau kuma shizai k’ara dank’on zumunci a tsakaninmu, don baka iyayen rashida kunji buqatar d’anku idan har yarinyar nan ba’a tsaida mata da miji ba, to muna nema masa izinin yafara zuwa wajenta donsu daidaita” Gaba d’ayansu suka had’a baki wajen cewa, “to aimu da Nuraddeen da Kuma Rashida duk ‘ya’yanmune, saboda haka indon ta tamu bamuqi jinin yau a d’aura masu aure ba, don haka mu tabakin malan bashar muke jira sai muyanke hukunci” STORY CONTINUES BELOW  Murmushi baba yayi sannan yace “hak’ik’a nayi farinciki, farinciki kuma marar misaltuwa akan wannan al-amarin, narigaku azuciya ne sai kuma ALLAH yasa yaron ya rigani abaki, Amma ALLAH shine shedar azuciyata nayi niyar bawa Nuraddeen auren Rashida saboda yanda nayaba da halinsa da kuma nagartarsa, dad’in fad’awa da naji cewa shi d’an amininane kuma d’an wannan ahali masu d’inbin karamci da kyautatawa, saboda haka kamar yanda kukace ku iyayen duka biyunne to nima haka, gaba d’ayansu ‘ya’yana ne don haka ga mahaifinta nan malan balarabe sai muji tabakinsa.” Yaqarasa maganar yana nuna inda qanen nasa kezaune, murmushi malan balarabe yayi had’e da cewa, “to madallah tunda duk kunbar mani ‘yar tawa nagode kuma ni balarabe Ina so ku sheda cewa ba izini kad’ai ba hatta auren ‘yata Rashida nabawa d’ana Nuraddeen duniya da lahira, don haka duk sadda kuka so asa rana da kuma yanka maku sadaki sai ku nememu in sha ALLAH ko yaushene mu a shirye muke” “Alhamdulillah” kowa yafad’a, baffa yace “Tunda hakane mezai hana ayanka sadakin kuma asa ranar yanzu sai ahuta ko me kukace?” Cikin rawar murya anensa Aliyu yace, “A’a yaya abari har sai sunje sun tambayi yarinyar idan ta amince ina ga hakan zaifi.” “Indai ta b’angaren yarinyar mune babu wata matsala koda had’asu mukayi munyarda da tarbiyarta zata amince ballema shi yaron yaganta yace yana so, don haka ayi abunda yakamata babu damuwa in Sha ALLAH” malan balarabe yafad’a cike da nuna yarda akan ‘yar tasu,ko kad’an ran Aliyu bi yimasa dad’i ba Amma babu yanda zaiyi dole ya haqura tunda duk ‘yan uwan nasa sun nuna amincewarsu, kafin kace me aka yanka sadaki dubu hamsin , nan take abokanan iyayen nasu su hud’u suka had’a kud’in suka ba qannen mahaifin Nuraddeen a matsayin tasu gudun mawar ga d’an nasu, Hakan ba k’aramin sake farantawa baffa zuciya yayi ba tare da yiwa ALLAH godiya daya basa nagartaccin abokanai irinsu, Abunda ALLAH yaso kuma yariga ya had’a ko ana so ko ba’a so to sai ya tabbata, a ranar su baba basu baro garinba har saida aka dindince ranar d’aurin auren nan da sati biyu masu zuwa tare da sadakin Rashida a hannunsu zuciyoyinsu cike da farinciki, nisawa mahaifin Rashida yayi yace “ALLAH mai iko kuma mai yin yanda yaso, mu da mukaje gano marar lafiya sai gashi mun dawo da sadakin ‘yarmu a hannu, tabbas komai nada sanadi arayuwa, ubangiji ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi kuma ya had’e hankulansu waje d’aya” kowanensu ya amsa da “Amin” suna masu jinjina al-amarin ubangiji. Aliyu kuwa suna tafiy bai zame ko Ina ba sai d’akin mahaifiyar Nuraddeen wato matar yayan nasa yay hawwa kmar yanda suke kiranta yana cika yana batsewa, nan ta taso tana tambayarsa ko lafiya ai kamar jira yakeyi ya zayyane mata qarya da gaskiya, ashar ta lailayo ta dire tna fad’in “ai wlh ba’a isa ba, yaushe har shi nuran yayi girman da ya isa yace ga wadda yake so da har za’aje ayo masa qulle qulle a aura masa wata can bare, to wlh bazan tab’a lamuntar wannan abun gori acikin dangi ba, haka kurum ajawo mani abun kunya da fad’a acikin gari, kowa yasan awannan garin namu auren zumunci akeyi, bamuda bare kuma ba’a tab’a kawo mana ita acikin gida ba, shikenan sai yanzu ace akan d’ana za’a fara?to wlh haka bazata sab’uba wai bindiga aruwa” wani farincikine ya rufe Aliyu yaci gaba da ingizata yana zugata haddasu cewa “Nima haka nagani yaya hawwa, Ina laifin ace ko muneera ce an had’asa da ita tunda tana sonsa amma wai antashi an had’asa da wacce batasan kimarmu da darajarmu ba, ga yaran cikin garin basuda mutunci da girmama na gabansu” “Kai rufamun baki, muneera ko shashasha, tun yaushe nake cemata tadinga oqarin jawo hankalinsa amma takasa, shegiya mai gwalmad’ad’d’in qafafuwa ai koma meye laifin tane” “Amma yaya hawwa kemafa kinsan yaronnan da baqin rai yake, har yaushe tag fuska balle taje tayi masa karairayar da zata jawo hankalinsa, yanzu dai ya kamata kisan abunyi kafin yarinyar nan tazo tarabamu da d’anmu ta tsigemu gaba d’aya” “Kai Aliyu tofar da mugun yawun bakinan naka, wannan baqar fata har Ina, Bari naje wajen malan dole a ajiye wannan maganar” fiiiii…tanufi shigifar da baffa ke kwance ta iskosa yana jan carbi, masifa tafara zuba masa yana kallonta har ta gama sannan ya ajiye carbin agefe yace “yanzu ke hawwa awannan yanayin da nake ciki har kinada k’warin guiwar zuwa kiyi tsaye agabana kina wud’annan maganganun, to bari infad’a maki ko kina so ko bakya so sai anyi wannan auren tunda yana son yarinyar” STORY CONTINUES BELOW  “Ni kuma bana son yarinyar, don haka bazai aureta ba” “Saboda meye?” “Saboda ita d’in barece” “A’ina aka fad’i hakan, qur’ani yafad’a ne ko a’a?” “A al’adar garinmu dai ce ba’a tab’a yin hakan ba kuma baza’a fara akan d’ana ba” “Kaji shirmen banza, al’adar tafi alqur’anin ne? To Bari kiji wannan aure kamar anyi angama ne da yardar ALLAH” “Amma malan inkayi mani haka bakayi mani adalci ba sabo…” Bata qarasa rufe baki ba yace “Eh jeki naji d’in ni yanzu barci nakeji bana son wannan hayaniyar!” Duk inda ran hawwa yake inyayi dubu yab’aci, tafice buuuu.kamar zata tashi sama tana maseefa, karo tayi da Usman akan hanyar tsakar gidan da yake family ne duk anan suke zune tafara yimasa qorafi, murmushi yayi sannan yace, “ikon ALLAH, to aike yaya hawwa banda addu’a babu abunda yakamata kiyi tunda shi yaganta kuma yace yana sonta, don ALLAH don annabi ki kwantar da hankalinki, mai k’aya ya daure kuma sai ace mai cira na kuka!?” Aifa nan shima tayi masa tatas har tana k’arawa da cewa ai duk munafuccin da akayi dashi akayisa, shidai murmushi kawai yayi yawuce abunsa batare daya sake tankata ba, Aliyu ne ya iso wajen yana kallon irin hararar data raka d’an uwansa da ita yace, “Ahaf! Ai infad’a maki yaya hawwa duk munafuccin agindinsa yake, shine nan ya qulla komai.” Tsaki taja had’e da barin wajen tana fad’in, “sakarci, to kai meya hanaka kwancewa daya qulla, ai wlh duk sai nayi maganinku ga baki d’aya.” 😨 _TIRQASHI! RASHIDA KINA CIKIN MATSALA, GASHI KEBA ILIMIN ZAMANI BALLE KI KWACI KANKI🤔🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️_ *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/21, 10:25 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___12💎 Kallo Aliyu yabi yaya hawwa dashi kafin yace “Kai wannan mata anyi fitinanniyar halitta anan, duk girmanka baza katab’a gwaninta awajenta ba, jarababbiya da ganinta kasan ba qaramin haquri yaya keyi da ita ba.” Kasa zaune da tsaye yaya hawwa tayi saboda tunanin hanyar da zatabi ta hana auren, in tayi nan tayi can kamar mai jiran sauraren wani sak’on, cije baki tayi aranta tana mai ayyana kalar uqubobin data tanadawa yarinyar matuqar bata samu nasarar ruguje auren ba, Baba kuwa yana isa gida bakinsa ko rufuwa bayayi saboda tsananin farinciki yafara k’walawa Rashida kira alokacin ita kuma tana bayi tana wanka, “A’a sannu da zuwa malan,lafiya naji kana k’wallawa ‘yar taka kira tundaga zaure” tak’are zancen had’e da jawo tabarmar dake gefen d’aki ta shimfid’a masa sannan takoma d’aki ta d’auko ruwa masu sanyi takawo masa, fuskarsa cike da annuri ya nemi waje ya zauna sannan yace, “Yawwa maman Rashida lafiya klw muka dawo, Ina ita Rashidar take, ko tayi islamiya ne?” “A’a yanzunnan tashiga wanka, inaji yauma tayi latti ALLAH yakareta daga dukan malamai.” “Amin ya ALLAH” Yafad’a had’e da d’aukar ruwan data ajiye masa agabansa yasha, “Malan shin ko abun sirrine tsakanin uba da ‘yarsa naji kayi shiru, kai da naga kashigo da azamarka kamar Wanda akaba saqo yakawo mani.” Murmushi yayi mata sannan yace STORY CONTINUES BELOW  “To kusan dai kamar hakanne amma sak’on Kuma bake aka bawa ba ‘yarmu aka ba.” “Tooo…! Kace dai harkar tason kaice, to bari nakama bakina, inbar uba da ‘yarsa susha sha’aninsu” “A’a ranki shidad’e ai abun bai kai can ba, ungo wannan riqe inyi maki bayani” ya ciro kud’i a aljihunsa ya mik’a mata, ansa tayi tana bin kud’in cike da mamaki kafin tace, “malan a ina kasamo wud’annan? Ina wajen ganin marar lafiya kuka tafi ko?” “Eh a can mukaje?” “To wud’annan kud’infa a ina aka samosu?” “Kai maman Rashida wud’annan tambayoyin sunyi yawa, sai kace wanda yasato” “To ai dole na tambaya saboda abun da mamaki!.” “kwantar da hankalinki to wannan sadakin Rashida ne kuma nan da sati biyu za’a d’aura auren in sha ALLAH…” bai qarasa zancen ba sukaji qarar fad’uwar bokiti daga toilet Rashida ta saki jin abunda kefitowa daga bakin mahaifin nata, atare umma da baba sukace, “Ke lafiya?” K’ok’arin maida hawayen da suka zubo mata tayi tare da ciro zanenta dake rataye ajikin k’usa ta d’aura sannan ta yafo towel d’in da tashiga dashi yarufe mata daga samn kai zuwa qirji tafito kanta na sunkuye qasa tawuce d’akinsu, Kallo suka bita dashi kafin baba yace “ALLAH ya kyauta, ni bari inje muyi magana da balarabe yana waje yana jirana.!” “Shine bakace ya shigoba zaka barshi zaune awaje sekace wani baqo” “Bari dai natafi kije ki ajiye kud’innan idan nadawo ma k’arasa maganar.” “To ALLAH ya kiyaye kuma yasa adawo lafiya, ka gaidashi” Yana fita itama Rashida tafito saye da hijabinta na islamiya tace “umma natafi” batare da tabari sun had’a idanuwa da ita ba don kada ta fahimci halin da take ciki, “To adawo lafiya” itama tabata amsa atak’aice, sannan tamik’e tawuce cikin d’aki. Rashida kam tana cikin yanayin da ita kanta batasan taya zata fassarashi ba, karatu akeyi amma tayi zaune tahad’a tagumi tana tunani, gashi dai auren da takeso za’a yimata amma damuwarta d’aya shine yanda alokaci guda soyayyar da malaminta ya dasa azuciyarta cikin kwana biyu tayi tasiri aranta har tana tunanin yanda zata iya auren wani idan bashi ba, ji tayi tafashe da kukan da batasan lokacin da yazo mata ba saidai taji malami na fad’in “Ke Rashida me yake damunki ne?” Firgigit tadawo cikin hayyacinta tana zarar idanuwa had’e dasa hannuwa tana goge hawayen da suka zubo mata, “Mik’e tsaye.” Taji ya sake fad’a tare da nufo inda take riqe da bulala, mik’ewa tayi da sauri tana runtse idanuwanta don duk duniya babu abunda ta tsana kamar a tab’a mata jiki da sunan duka, “Me kike tunani!” “Babu malan” tafad’a atsorace har lokacin idanuwanta na arufe, har zai dukanta sai kuma ya qyaleta had’e da cewa tafitar masa daga aji, maimakon tabashi hak’uri kawai sai taja jikkarta tafice daga dama tun d’azu hankalinta baya wajen balle ta fahimci karatun da yakeyi, acan bayan wasu azuzuwa taje ta zauna, ta d’ora daga inda ta tsaya ga tunanin da yakeyi, Bata bar wajen ba har sai da taga antashi sannan tabi sauran d’alibai suka wuce gida, Tana isa gida ta isko umma na waya da ‘yan uwanta dake borno akan zancen aurenta tana fad’a masu ai har ankawo mata sadaki an kuma sa ranar aurenta nan da sati biyu hakan yasake dagula mata lissafi tawuce d’akinta da sauri, kasancewar dama tana fashin sallah yasa batabi takan kiraye kirayen sallar magrib da akeyi ba tayi kwancenta, ita kuma umma kota kanta batabi ba tad’auki butarta tayo arwala sannan tawuce d’aki ta tayar da sallah. Can misalin qarfe tara nadare bayan baba yadawo sun gama tattaunawa da umma sannan yayi mata bayanin cewa ai bayan sun gama dubiyar da sun kajene aminin nasa ya bijiro da maganar nemawa d’ansa auren Rashida ashe cikin ikon ALLAH ganin da yake yimata a makaranta yaji yana sonta tun kafin inyi masa magana sae gashi yafad’awa mahaifin nasa cewa ya nema masa aurenta.” nan dai ya fayyace mata yanda komai yafaru, ajiyar zuciya tayi had’e da cewa “Alhamdulillah, aini sai yanzu nasamu natsuwa, amma tunda kabarni nake wasu wasin wannan al-amarin tare da taraddi jin kace nan da sati biyu za’ayi auren, amma yanzu Alhamdulillah, ALLAH yatabbatar mana da alkhairi, naji dad’i kuma nayi farinciki sosai ai malan idi mutumen kirkine da kowa zaiyi sha’awar had’a zuri’a dashi, ubangiji ALLAH ya bashi lafiya kuma yasa ayi munada rayuwa.” STORY CONTINUES BELOW  “Amin ya rabbi, ai don ma bakiga yaron ba, ALLAH dai ya tabbatar da alkhairi, tashi kije ki kirawomun ita” cike da farinciki umma tanufi d’akinta ta tsaya abakin k’ofa tana fad’in “Rashida, Rashida..” jin bata amsa ba yasa taqarasa cikin d’akin, kwance ta hangota saman katifarta, kallo d’aya tayi mata tasan da cewa ba bacci takeyi ba kawai idanuwan natane kad’ai a rufe, matsawa jikin katifar tayi had’e da cewa, “Ke Rashida lafiya kikekuwa?” Firgigit tabud’e idanuwanta had’e da saukar dasu akan nata, “lafiya kike?” Tasake maimaita mata akaro na biyu, qoqarin miqewa zaune tayi had’e da sauko da k’afafuwanta k’asan katifar sannan tace, “Umma kainane yake yimun ciwo.” “Ashsha shiyasa yau najiki shiru tunda kika dawo makaranta baki fito ba balle kid’auko abincinki kici, daure kitashi mahaifinki nakira inyaso daga can sai kici abinci kisha magani kinji ko” Kai tad’aga mata ita kuma tajuya tabar d’akin tana fad’in “ALLAH yasawaqe ciwon kai kam ai babu dad’i” Ko minti biyu umma batayi da zaunawa ba Rashida itama tashigo cikin d’akin tajawo hular hijab d’inta ta lullub’e mata rabin fuskarta tanemi gefen qofar d’akin daga ciki ta zauna, “Baba ina wuni andawo lafiya?” Tafad’a tana gyara hular hijabin zuwa kanta.” “Lafiya klw Rashida, lafiya kike kuwa?” Kafin tace wani abun umma tace “Au kagafa na manta infad’a maka ba tajin dad’i, na iskota kwance shine dana tambayeta take fad’amun kanta ke ciwo don tunda suka dawo islamiya banga tafito waje ba balle ko abinci tasamu ta d’auka taci.” “Subhanallahi, injin to da sauqi” yafad’a yana kallon Rashida “Eh da sauqi baba,” tafad’a tana goge zufa a goshinta, wani d’an guntun tsaki yaja had’e da cewa “Matsalar ku kenan mata baku fiye kula ba wani lokacin, shiyasa ake ganin sakacinku yayi yawa ace mutum nada d’a yaga yayi awa kusan biyu a d’aki bai fitoba kuma bazai je yaduba halin da yake ciki ba sai mai faruwa tafaru kaji ana fad’in ai kuwa tun d’azu najishi ko najita shiru ad’aki ashe kaza da kaza yafaru bamu sani ba, to meye amfanin hakan? Kin jita shiru amma kin kasa dubota kiga ko lafiya take sai yanzu da nace ki kirawota, ALLAH ya kyauta” “Ayi hak’uri malan in sha ALLAH za’a dinga kula” Hannunsa yamik’a gefensa a qarqashin pillow dake kan gadon ya d’auko kud’in da yakarb’a a hannun umma ya mik’awa Rashida had’e da cewa, “Ungo wannan ki k’irgamun su nawa ne?” Mik’o hannunta tayi yana makarkata ta karb’a sannan tafara k’irgawa d’aya bayan d’an shi kuma yana kallonta, saida tagama sannan ahankali ta d’ago kanta tace, “Dubu ce guda hamsin” murmushi yayi had’e da cewa, “ban fahimta ba” “Ina nufin naira dubu ce sau hamsin ” girgiza kai yayi cike da takaicin dubu hamsin ma ‘yarsa bazata iya fad’a daidai ba, wannan wane irin rayuwace, kallonta yayi yanaji kamar ya maketa kafin yace, “Rashida kenan, ai bahaka ake fad’aba, naira dubu hamsin zakice a hausance kinji ko?.” ‘Daga masa kai tayi tare da sake mik’a masa kud’in, “A’a kiriqesu a hannunki, nakine mallakinki duniya da lahira” d’ago kai tayi tana kallonsa cike da alamar tambaya atattare da ita, “Eh, kud’in kine na sadaki da aka bayar kuma a musulunce bai halatta kowa yayi amfani dasu ba idan ba keba koda kuwa mune saboda hak’k’in k’ine shiyasa na hannunta makisu a hannunki duk abunda kike so kiyi dasu, mudai munfita hak’k’inki koba haka ba?” Yaqare maganar yana kallon umma, jinjina masa kai ita Kuma tayi alamar tabbatar da zancensa. Muryarta na rawa tace “Babu abunda zanyi dasu baba don ALLAH ku karb’a umma” “A’a kirik’e hannunki abunda babanki yafad’a shine daidai kinji ko?” STORY CONTINUES BELOW  “Umma nifa babu abunda zanyi dasu, baba..” dakatar da ita yayi had’e da cewa, zaki iya ba ummanki ta ajiye maki, tashi kitafi ALLAH yayi maki albarka” Mik’awa umma kud’in tayi sannan tamik’e zata fita, har ta aza k’afarta abakin k’ofar mahaifin nata yace, “Rashida bazaki tambayi ko wanene na zab’a maki ba?” “A’a baba, babu buqatar hakan domin nasan bazaka tab’a yimun zab’in daba daidai ba.” Tana gama fad’ar haka tafice idanuwanta na hawaye, tabbas tasan takamu da soyayyar malaminta amma bazata iya yiwa mahaifinta musu ko kuma gardama akan zab’in da yayi mata ba, kawai zatayi k’ok’ari ta yakisheshi aranta kafin lokacin auren. Shikuwagogan naka matsuwa yayi safiya tawaye yaje makarantar saboda yaga sahibarsa, wacce ke Shirin zamowa matarsa kuma uwar ‘ya’yansa, cikin daren yaje yasiyo mata waya k’irar tecno L7 saboda ya dinga jin muryarta duk da dai gaba d’aya wannan satin zai ganta har yagaji. Tunda sassafe yatashi yayi wanka sannan yaje wajen mahaifiyarsa ya gaisheta tare da cemata zai wuce, ciki ciki ta amsa mata saboda fushin da takeyi dashi akan zaije ya auro masu bare, cikin sanyin murya yace, “Inna har yanzu fushin kikeyi dani?” “Ai dole inyi fushi da kai nura zaka jawo mani abun kunya.” “Kiyi hak’uri inna da kin fad’amun tun farko bakyason in auro maki bare agidan nan da bazanyi ba, amma yanzu kinga su baffa sunyi magana bai kamata ace anwatsa masu qasa a idanuwan duniya ba.” “Aiho shiyasa ni kuma aka watsamun qasar, shikenan tashi katafi.” “Taya zantafi inna fuskarki ahaka, kiyi hak’uri don Allah kiyafemun, natabbata idan kikaga yarinyar kema zaki sota kamar yanda nake sonta” Saida ta sheqe da wata dariyar shaqiyanci kafin tace, “ALLAH natuba kayafemun ni hawwa, ai har abada bazan sota ba, kaidai tashi katafi ALLAH yatsare hanya.” Jikinsa ya matuqar mutuwa dajin kalamanta amma babu yanda ya iya saboda ALLAH shine shedar yanda take jin soyayyar yarinyar bazai iya rabuwa da ita ba, fatanshi dai ALLAH yasawa inna sonta kamar yanda yake sonta, “Me kake tunani haka!” tafad’a a d’an tsawace da yasashi saurin mik’ewa tsaye yana fad’in “Natafi.” “Adawo lafiya,” tafad’a tare da mik’ewa ta rakosa har bakin qofa. Adaidai bakin k’ofar fita gidan bayan yaje wajen mahaifinsa shima sun gaisa yafad’a masa zai wuce ya had’u da qannen mahaifin nasa baffa Ali da baffa Usman kamar yanda suke kiransu, duqawa yayi har k’asa ya gaishesu, baffa Usman ne yafara amsa masa kafin baffa Ali dake gugar bakinsa da ashuwaki ya tofar da yawu agefe yace, “A’a malan nura zaka tafi” “Eh baffa Ali nama yi latti sosai yau gashi inada daraai qarfe takwas naga har bakwai da rabi tayi” “Eh gaskiya kama tashi katafi, ALLAH yatsare hanya.” “Amin baffa Ali nagode.” Har yafara tafiya yakira sunansa ya juyo zai dawo inda suke yace “A’a basai kadawo ba, cewa nayi to adai kula kasan halin mata kar ake kabiyewa shashancinsu suhanaka yin abunda ya kaika kaji ko?” Shiru yayi yana nazarin kalamansa kafin yace, “to baffa Ali in Sha ALLAH.” Sannan yawuce cikin sauri. Girgiza kai baffa Usman yayi had’e da kallonsa kafin yace “Yanzu kai Ali meye amfanin abunda kayi, karkamanta yaronnan d’anka ne bai kamata kana yimasa abubuwan da basu dace ba gudun kada yadena ganin girmanka da kimarka, kaga daga lokacin fa girma yafad’i.” “A’a meye rashin dacewa anan, gaskiyafa nafad’a masa, zamu saki yaron namune sagaga alalata mana shi acan” “Ikon ALLAH, yanzu Ali aganinka har abun yakai ga mata ke lalata maza?” STORY CONTINUES BELOW  “Ahaf nawa akayi, ba shiyasa qara mutum ya nemawa d’ansa mata acikin dangi ya huta ba, Amma meye amfanin kwashe kwashe awaje.” “Oho!.. yanzu nagane inda zancenka yayi, wlh kaji tsoron ALLAH kabar yaronnan yazauna lafiya da mahaifiyarsa, meye amfanin sonkai Ali?, Tunda yaron nan yakawo wacce yakeso don me da baza’a haquraba abarsa?” “Mtssss…” Baffa Ali yaja tsaki tare da barin wajen yana suruttansa. Malan Idris kuwa duk da yana cikin damuwar maganganunda baffa Ali yayi masa hakan bai hanasa fad’ad’a fara’ar saba alokacin daya iso makarantar, Kai tsaye ajinsu Rashida yanufa saboda yanda yake mararin ganinta, duk da itama tana son ganin nasa hakan bai hanata b’uya a qarqashin kujeraba alokacin data hangosa saboda yanda take son samawa kanta mafita tahanyar yakicesa aranta, dube dube yafarayi lokacin daya iso qofar ajin batare daya damu da malamin dake ciki yana yimasu mathematics ba yayinda itako banda fad’uwa babu abunda gabanta keyi,…. *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/23, 11:14 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___13💎 Jin kamar motsi abakin k’ofar ajin yasa malamin dake cikin juyowa, “A’a malan Idris barka da safiya” yafad’a tare da qarasowa wajen ya mik’a masa hannu suka gaisa, “Yawwa malan sale an shigo?” “Eh wlh, wani abu kake nema ne?” “Eh kusan haka dai Amma bari naje zuwa anjima na dawo saboda inada aji yanzu.” “Ok to, Masha Allah” suka sake gaisawa sannan yawuce, yana wucewa tasaki wata irin ajiyar zuciya tare da fitowa a qarqashin kujerar data b’uya tana watsawa nakusa da sit d’insu wani mugun kallo saboda yanda taga sun maido hankalinsu gaba d’aya akanta, da sauri suka d’auke idanuwansu daga kallon da sukeyi mata gudun karta tata masu rashin mutunci, wani juya idanuwanta tayi had’e da aza kanta saman bencin dake gabanta tayi kwancenta, malan Idris nafita yanufi ajin da yake da period ransa duk ajagule, yaso ace yana shigowa yayi tozali da fuskarta saboda yanda yayi matuqar kewarta sai gashi hakan yacutara, haka nan ya daure yana koyarda d’aliban nasa sama sama amma gaba d’ayan tunaninsa da natsuwarta na wajen d’alibar tasa akan dalilin daya hanata zuwa makaranta yau duk da dai wani gefe na zuciyarsa na tabbatar masa da cewa tana cikin makarantar kawai biyi nasarar ganinta bane, adaddafe yasamu period d’insa ta k’are yafice daga ajin, wata d’aliba yakira yace taje ajinsu Rashida tace yana kiranta duk dako agaban idonsa wani malamin ya sake shiga cikin ajin nasu bayan nafarkon yafita. Daidai bakin qofar yarinyar ta tsaya tare da cewa “escuse sir, malan idris yace yana kiran Rashida bashar.” ai Bata rufe baki ba rashida tasake shigewa qarqashin kujerar, dube dube malamin yafara yana kiran sunanta amma taqi amsawa, sukuwa ajin gaba d’aya tsoronta sukeyi saboda sanin halinta shiyasa babu wanda yayi yunqurin tonata gudun kada ta taresaidan antashi tabashi kashi don haka takeyiwa duk Wanda ya takaleta acikin aji. Juyowa malamin yayi had’e da cemata, “kije kifad’a masa bata zo ba.” Yana nan a inda take zaune yarinyar tadawo tafad’a masa cewa, “malan ance bata zoba” yace “Ok wuce aji Kuma karki sake ink’ara ganinki waje kafin afito breakfast kinaji na ko.” “Eh malan” tafad’a tare da rugawa tashige ajinsu, STORY CONTINUES BELOW  Tunanin zuwa gidansu yayi ya dubota, sai kuma yaga kamar hakan ba daidai bane tunda bai tabbatar da batazo ba d’in, don shi har yanzu jikinsa nafad’a masa tana cikin makarantar saidai in akwai wani abu dake faruwa, hanyar clinic d’insu ya nufa ko tana can Amma ga mamakinsa bai iskota ba hakan yasa yawuce dining hall d’insu da kitchen duk bata can, wasa wasa malan idris ya zagaye duk wasu building na makarantar amma baiga Rashida ba, hankalinsa ya matuqar tashi da hakan, don bai tab’a ganin tayi fashin zuwa makaranta ba duk da rashin son karatunta saboda yanda baba keson tayi karatun shiyasa baya d’aukar mata hakan, office d’insa yakoma ya zauna tare da aza kansa saman jikin kujerar yana jin rayuwarsa duk ba dad’i, tun lokacin bai sake leqawo wajen harabar makarantar ba sai da yaji antashi breakfast, miqewa yayi da sauri yakoma jikin tagar office d’in nasa yana kallon qofar ajinsu yanda d’aliban kefitowa d’aya bayan d’aya Amma har suka gama fitowo ko mai kama da ita bai gani tafito ba balle itad’in, cike da takaici yakaiwa jikin bangon naushi had’e da juya zai bar wajen, kamar ance ya sake juyowa ta tagar ya hango ta azo qafarta sannan yaga ta leqo da kanta tana kalle kalle kamar mai neman wani abun, ganin yayi tana yiwa meenah qawarta magana ga kunne had’e nuno office d’insa wanda yasa aransa yaji dad’i atunninsa maganarsa takeyi, abunda bai sani ba Rashida tasa aduba matane idan yana cikin office don tasamu tafito ta sayi abunda zata saya kafin ya rutsar mata, yana kallo tafito tana d’an waige waige har ta isa inda zatayi sayayyar tasaya da sauri kuma tajuya tabar wajen, a maimakon takoma cikin aji sai yaga tanufi bayan class d’in da sauri meenah na biye da ita. Murmushi yayi had’e da sauke wata irin ajiyar zuciya sannan yakoma bisan kujerarsa ya zauna yana dariya saboda yagano dalilin da yasa tab’uya bai gane taba, dariya yasakeyi had’e da cewa, “kunyata Rashida keji kenan!?” Jikkar da yazo da ita yajawo yaciro kwalin wayar daya siyo mata yana kallo sai kace shine ita, a hankali yafurta da taimakon wannan wayar zan tabbatar matar maki da irin soyayyar da nakeyi maki, zanyi iya qoqarina wajen yakice maki wannan matsananciyar kunyar dake nema tazama shamakin da zaya zamo silar takurawa rayuwar aurenmu, maida kwalin wayar yayi cikin jikka ya rufe sannan yamik’e yafito daga office d’in, Saida yad’an jawosa sannan yamik’e ta d’ayar hanyar da zata sadashi da bayan ajinsu Rashida, zaune ya iskota saman wani dutse sunacin dankali da awara sai zob’o da ruwan sanyi dake ajiye gefensu ita da meenah qawarta dake fad’in, “Waike Rashida lafiya malan Idris yazo nemanki d’azu kika b’uya kuma ya sake aikawa akiraki kikaqi zuwa? Naga dai kuna shiri dashi balle ace wani abun, kodai laifi kika yimasa.” Saida ta d’auki ledar ruwan tafasa tasha sannan tace, “wlh meenah babu wani abun dana yimasa kawai Ina cikin damuwane kuma kinsan halinsa ko kad’an baya son ganin d’alibinsa cikin damuwa, bansan irin amsar da zan bashi bane idan ya tambayeni.” “To amma ai wannan shiya Aiko kiranki ma’ana shike nemanki, bakya tunin ko akwai dalilin da yasa yake nemanki?.” Tana rufe baki kamar ance ta d’ago kanta tahangosa tsaye ajikin bangon ajin ya nad’e hanneyensa akan qirjinsa yana kallonsu, k’ok’arin yin magana tayi ad’an tsorace yabud’e mata idanuwa had’e dasa yatsansa akan bakinsa alamun tayi shiru, ita kuwa Rashida dama kanta naduk’e tana cin abincinta don haka bata masan abunda ke faruwa ba, alama ya sakeyiwa meenah da hannu ta tashi ta tafi, cikin tarin qarya data k’irk’iro tace “Emm…Rashida Bari naje naqaro mana ruwa qwaya biyu don wud’annan bazasu ishemu ba” takarb’i sauran nahannunta data fasa tasha tabar wajen, tana wucewa yayi gyaran murya had’e da dawowa tagabanta ya tsaye, a tsorace ta d’ago kai jin murya da qafafuwan data gani agabanta wanda bako shakka ta tabbatar namijine, suna had’a ido dashi tayi saurin mik’ewa tsaye tare da duqar da kanta tana qoqarin rab’awa ta gefenshi tawuce, hannunsa ya d’ora ajikin bangon ya tare ta inda zata wucewa had’e da cewa. “Ina kuma zaki jene?” “Aji zan koma.” Tafad’a har lokacin kanta na sunkuye a qasa, gyara tsayuwarsa yayi sannan yaci gaba da cewa, “to ki zauna ki qarasa cin abincinki mana.” STORY CONTINUES BELOW  “Naqoshi.” “Saboda nazo?” “A’a” “To meyasa?, Bakya son ganina anan ne?.” “A’a” tasake bashi amsa atak’aice, “Meyasa naje nemanki kika b’uya kuma na aika akiraki kikak’i zuwa?.” Shiru tayi saboda bata san ta Ina zata fara bashi amsa ba, har zai sake jefo mata tambayar yaji anbuga qararrawar komawa aji hakan yasa yace, “ki tabbatar kin jirani idan aka tashi ina son magana dake kinji ko?,” yafad’a yana kallonta, kad’a masa kai tayi alamar eh sannan ya koma tahanyar daya biyo ya wuce, ahankali tajuyo tana kallonsa har ya b’ace kafin takoma saman dutsen data tashi ta zauna, hannuwanta tasa ta dafe kanta dasu wasu zaffan hawaye na zubo mata, tambayar kanta tashigayi akan meyasa malan idris ya shigo rayuwarta a daidai wannan lokacin, meyasa yafurta mata kalmar da zata saurin narkar mata da zuciya alokacin da batayi zato ko tsammani ba?, Meyasa tabari zuciyarta tafara sonsa bayan tasan batada iko akan zab’awa kanta abokin zaman da zatayi rayuwa dashi alokin?, Wani irin kuka ta fashe dashi tana mai jin rad’ad’i da kuma zugi acikin zuciyarta, Tafi mintuna biyar zaune ahaka tana kuka har saida tayi mai isarta sannan ta tashi tawanke fuskarta da sauran ruwan dake wajen ajiye takoma cikin aji. Ana tashi tayi saurin d’aukar jikkarta tagudu don batasan abunda yake son fad’a mata ba, Bata so yasake jifarta da wasu kalamai da zasu tunzura zuciyarta har sukaita ga bijirewa zab’in da mahaifinta yayi mata, Amma sai dai kash! cikin rashin sa’a tasamu yana nan tsaye abakin k’ofar ajinsu yana jiranta, k’ok’arin shigewa cikin ‘yan uwanta d’alibai tayi tagudu yayi saurin riqo jikkarta dake sagale a kafad’arta, tsaye tayi cak batare data juyoba yace, “Ina kuma zaki je?” Juyowa tayi saboda d’aliban dake wucewa kada suyi zargin wani abun ta jaye jikkarta ahankali daya rik’e sannan tace, “Gida zanje.” Yanda yaga wasu d’alibban sunyi tsaye suna kallonsu yasa ya shafa kansa yana fad’in muje inrakaki dama tuni ya d rufikke office d’insa ya tsaya nan zaman jiranta don yasan zata iya guduwa, babu yanda ta iya dole tabisa suka nufi gate d’in zuciyarta na harbawa da sauri da sauri, meenah dake can gefe tana jiranta na ganin haka tawuce abinta zuciyarta cike da tambayoyi akan meye tsakanin qawar tata Rashida da kuma malan Idris. Tafiya yakeyi ahankli tamkar wanda baya son su isa gidan yana tambayarta meye dalilin da yasa gaba d’aya yau ta sauya masa ba kamar yanda suka saba ba amma takasa cemasa komai, adaidai bakin wata bushiya dake kan hanyar ya tsaya tare da cewa, “Rashida meyasa inata yimaki magana kika yimun shiru? shin ko bakya sona ne shiyasa kika zab’i wannan hukunci a matsayin amsar da zaki bani don tabbatar mani da cewa bakya sona d’in.” Yaqarasa maganar cike da damuwa a fuskarsa, da sauri ta d’ago kanta tana girgiza masa idanuwanta cike da k’walla kafin tace, “Ko kad’an malam ba haka bane, asalima azuciyata babu wani namiji da nake so kuma nake burin qare rayuwata atare dashi kamarsa, Amma kash kazomun a qurarren lokaci, kazo alokacin da banida ikon zab’awa zuciyata abunda take so face wanda aka zab’o mata, tabbas ina sonka amma nasan wahalace kurum zansha don bazamu tab’a kasan cewa a inuwa d’aya ba” taqarasa maganar tana share hawayen da suka zubo mata a fuska, cike da mamaki yake sauraren kalamanta kafin yace “Rashida ban fahimceki ba, kamarya bazamu lasance a inuwa d’aya dani dake ba bacin kince kina sona kuma kinsan nima Ina sonki, to meye kuma zai dakatar damu daga cimma burukanmu.” “Nauyin bakin da kayi wajen sanar dani soyayyarka har sai dana sallamawa mahaifina akan duk zab’in daya yimun, wannan shine dalilina domin jiya mahifina yazab’o mun wanda zai aura mani kuma har yabiya sadakina, yanzu haka kwanaki goma sha biyune suka ragemun nazamo mallakinsa kuma ni bazan iya hana hakan ba.” Dariya yafara mata har yana riqe ciki don gaba d’aya ya fahimci batasan cewa shine mijin da take iqirarin mahaifinta ya zab’a mata ba, yana kallon yanda ranta yab’aci amma yakasa tsaida kansa har saida yayi mai isarsa sannan yace ” yi hak’uri ranki shidad’e abunne dole inyi dariya..” yaqarasa maganar had’e da d’ago kansa amma ga mamakinsa sai ya hangota ashe tuni har tabar wajen tana gab da isa gida, STORY CONTINUES BELOW  Da sauri ya cimmata yana kiran sunanta, tsayawa tayi tanajin zuciyarta kamar tafad’o saboda takaicin fad’a masa sirrinta da tayi Ashe dama shi ba sonta yakeyi ba tunda har ya iya yimata dariya a daidai wannan lokacin daya kamata ace dukkanin su suna cikin damuwa, qarasowa wajen yayi had’e da rik’e kunnuwansa yana gumtse dariyar dake neman sake fito masa yace “yi hak’uri matata natuba kinji” K’walalo idanuwa awaje tayi had’e da girgiza kai irin bakasan abunda kakeyi ba tace “malan matar kafa kace? Karka manta yanzu nagama fad’a maka cewa antsayar mani da mijin da zan aura kuma har yabiya sadaki kwanaki kad’an suka rage a d’aura mana aure amma ka aza mani dariya saboda kasan Kai d’in bada gaske kake sona ba shiyasa bak damu ba, dama nasan bazaka iya aurena ba tunda banida ilimin boko kawai kafad’i hakanne don ka yaudareni.” “Subhanallahi Rashida mekike cewa hakan, nifa Ina mamakine akan yanda bakisan cewa nine mijin da zai aureki ba, kituna ke d’alibata ce, idan babu soyayya taya kike tunanin zan iya zaunawa ina bibiyarki haka? Ni da kike gani bantab’a soyayya ba kuma ban tab’a bawa wata mace dama ba tashiga rayuwata sai ke, to don me da zan yaudareki Rashida, ita soyayya Babu ruwanta da ilimi ko akasinsa kawai shiga takeyi a zukatan da ALLAH yaga cancantarsu da juna, kiyi hak’uri da banjira amsar da zaki bani ba na gabatar da kaina awajen iyayenki, wlh Rashida sonki nakeyi da gaskiya Kuma aurenki nakeso nayi kizamo mallakina kuma uwar ‘ya’yana” “Don ALLAH malan kadena fad’ar haka, kadena k’ok’arin cusamun sonka azuciya, wud’annan kalaman naka zasu iya sake jefani cikin maraicin rashinka alokacin dana zamo mallakin wani, tun ranar daka furta mani kalmar so nake shan wahala domin duk motsin da zanyi Ina tsinkayo sautin kalmomin a kunnuwana, meyasa zaka nemi sake turani cikin damuwa da wud’annan zantuka naka.” “Amma Rashida meyasa baki tambayi baba kowaye yazab’a maki?” “Saboda bana son nasan koshi waye?” “Koda nine Rashida?.” “Taya zaya zamana cewa kaine” tunanin fad’a mata komai yayi saboda yakawo k’arshen wannan jayayyar tasu tunda ya fahimci batada wata masaniya akan komai gyara tsayuwarsa yayi sannan yashiga labarta mata abunda yafaru ranar da yazo gidansu wanda shine silar daya kai mahaifinta aranar makarantarsu daga nanne ya gano shid’in abokin mahaifinsa da bashida lafiyane har zuwa jiya da sukaje dubosa shi kuma dama ya sanar da mahaifinsa cewa yana son yanema masa aurenta Kuma kasancewar aminaine sosai yasa mahaifinta ya amince, nan take akayi komai aka gama bisa amincewar iyayenta da kuma nasa, yana kaiwa nan ya lumfasa had’e da cewa, “to Rashida kinji abunda yafaru kuma Ina fatar zaki amince dani d’ari bisa d’ari ki aureni, cike da mamaki wata irin kunya tarufe Rashida don gaba d’aya yanda yabata labarin haka taji baba yana bawa ummashi amma arayuwarta bata tab’a kawowa shi d’inne ba, wani irin farinciki takeji aranta marar misaltuwa, ahankali tabud’e baki tare da sunkuyar da kanta k’asa tace, “Kayi hak’uri malamina” sannan tabar wajen aguje, dariya yayi yana binta da kallo har tashige gida, wani yaro yakira tare da bashi ledar dake hannunsa yace yashiga wancan gidan yakaima Rashida sannan shi kuma yawuce zuciyarsa fal cike da farinciki. ••• ••• ••• A b’angaren yaya hawwa kuwa wato mahaifiyar Nuraddeen kasa amincewa da kuma natsuwa tayi akan komawar yaronta garin saboda yarinyar da zaya aura se take ganin kamar duk abunda yasamu yanzu ita da iyayenta zai baiwa, hakan yasa tayanke shawarar zuwa wajen wani malamin tsibbo tace tana son tunkafin ayi auren a tabashi da ita a saka mashi tsanarta ta yanda koda ranar d’aurin aurensu ne bazai yarda ya aureta ba sai a maye soyayyar da yake yimita akan ‘yar qanen mahaifinsa wato muneerat, duk iya tsibbo da bugun k’asar da malamin zaiyi yayi don ganin kozai iya cin nasara Amma ya kasayi daga k’arshe sema cemata da yayi ta tashi tatafi don babu abunda zai iya, domin wannan auren ko tana so ko bataso dole sai anyisa saboda arubuce yake acikin qundin qaddarar yaronta da babu wanda ya isa ya hana ko kuma ya sauyasa hakan, Wanda kuma duk yayi yunqurin hanawa to tabbas babu ko shakka dole zai mutu don bazai iya ja da alqawarin ALLAH ba. STORY CONTINUES BELOW  *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/24, 9:08 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___14💎 Cikin rashin amincewa da zancen malamin Yaya hawwa tace, “Haba malan, cike fa da yarda da aminci muke kawo buqatunmu zuwa gareku, sai kuma ace da kanku zaku wargaza wanan yardar da muke da ita akanku, wlh no bana son ya auri yarinyar nan don ALLAH kasake dubawa ko akwai yanda za’ayi” jinjina kai ya shigayi yana kallon gefe gefensa kafin yafara kiran wasu kalar sunaye, yajima yana suruttansa kafin yasake baje duwatsun dake gabansa, d’ago kansa yayi fuskarsa a d’aure yace da ita “d’auki d’aya” hannunta narawa tad’auka ta mik’a masa ya jawo wani tray dake cike da qasa ya ajiye agabansa, tsakiyar tray d’in ya aza dutsin tare da yin rubutu saman qasar, ya kwashe fiye da mintuna biyar yana abu guda sai faman zufa yakeyi, can ya shafe rubutuna yayi tare da d’ago kansa yana nuna Maya qasar dake cikin tray yace, “duba nan kigani” Tana dubawa taga hoton Nuraddeen shida Rashida lokacin daya riqe kunnuwa yana bata hak’uri, da sauri tadafe qirji tana fad’in “nashiga uku ni kuluwa, malan kaga abunda yaronnan keyi agabanta tun ba’aje ko ina ba, don ALLAH malan kayi wani abun, bazan iya jurewa ganin haka ba” Murmushi malamin tsibbon yayi kafin yace “fiye da haka sai kingani, kawai kitashi kitafi, bayan auren kidawo masan abunda zamuyi amma wannan bazamu iya komai ba” Babu yanda zatayi dole tamiqe jiki ba k’wari taji yace “An buqaci ki ajiye kud’in sadaka kafin kitafi” Cikin jin zafi da takaici tabud’e jikkarta taciro naira dubu uku ta ajiye masa sannan tafito kamar zata tashi sama tana fad’in, “wannan ai shi ake kira da asara, maqaryacin banza da wofi meye bazai yuyu ba aduniya, ai wlh banda wancan shashan Aliyun daya kwatanta mani wajenka kuma yace aikinka sha yanzu magani yanzune babu abunda zai kawoni nan don nasan dama bakomai irinku suka iya ba, malan bakada imani shiyafi dacewa da wannan aikin nazo nan nayi asarar kud’ina ga banza.” Har ta isa gida fad’a takeyi tana qarawa saboda jin zafin kud’inta da aka amsa ga banza kuma ba’ayi mata aikin da take so ba, nafef na ajiyeta tabud’e jikka taciro kud’i taci karo da baffa Ali daya fito daga masallaci, yana hangota ya washe baki had’e da nufo inda take yana fad’in “sannu da zuwa Yaya hawwa” rufe jikkarta tayi had’e da banka masa wata irin muguwar harara sannan tace, “kasallami mai napep d’in nan acikin kud’ina” tawuce abunta, babu yanda ya iya tunda ta tafiyarta dole yaciro wata damuqaqqar d’ari biyar ya miqawa mai napep d’in yace, “ungo bawan ALLAH cire kud’inka kabani canji” mai napep d’in na amsa yatada kekensa had’e da cewa “ai ahaka na d’aukota.” “‘Darin d’in.” “Eh wlh, don ma bance da hamsin ba wannan tsayin da aka sani.” Yana gama fad’a yaja kekensa yabar wajen, da sauri baffa Ali ya cimmata daidai qofar shiga gida yana fad’in “Yaya hawwa wud’an ne kud’i kuma kike biyata da kika sani asarar miqa kud’in da nake dasu gaba d’aya, shi kuma tsabar rashin mutuncin wai har nera d’ari ya karb’a, kuma wlh ita kad’ai ce gareni yau ina zancen nakai ad’an silala mana wake da mai sai gashi anrabani da ita.” “Ai ni be burgeni ba don ba haka naso ba, so nayi ya karb’i d’ari biyu a hannunka, idan kahanashi ciko yacire hularka yaje da ita” “Yaya hawwa meyayi zafi haka?, ALLAH baki haquri, yanzu dai mu ajiye wannan maganar, ya kikaga malamin inadai komai angama ko?” Kallonshi tayi had’e da yaqe hauru hakan yasa shima yasaki murmushi azatonsa andace, ji yayi tace STORY CONTINUES BELOW  “Anko dace Ali, ai har an rabasu yanzu kawai ka qaddarama har ya auri ‘yarka ya gama” Sake washi baki yayi yayi had’e da cewa “ai nafad’a maki aikinshi Sha yanzu magani yanzu, dako kinata faman kunfar baki ga inda za’ayi maki maganin matsalarki cikin sauqi.” Saida tad’aure fuska sannan tajuyo tana kallonsa ido cikin ido ranta ab’ace tace, “Eh nako gani Ali, amma ina tabbatar maka da cewa nima cikin sauqi nima zaka biyani kud’ina da kasa nayi asararsu ga banza ga wofi, saboda rashin mutuncin Ali ni zaka yaudara, ka turani wajen matsiyaci talaka da baisan komai ba akarb’e mani kud’i ga banza kuma ace abunda nake so baze yuyu ba, to wlh kaji narantse maka kud’ina ko sisi bazaiyi ciwon kaiba saika biyani” tana gama magana tawuce abunta, tsaye baffa Ali yayi yana kallonta cike da mamaki kafin yayi hanzarin bin bayanta, “Yaya hawwa nifa ban fahimci me kike nufi ba” “Oho! Ni ba abinda ya dameni kaji nafad’a maka saika biyani kud’ina ko in d’ibesu ajikin waccan gwalmammiyar ‘yar taka kona rage zafi.” “Haba Yaya hawwa, meyakawo zancen ‘yata anan, don ALLAH kiyi shiru kada afahimci abunda ke faruwa.” “Meya dameni ko anji, d’a dai nawane kuma nace bana buqatar wacce za’a aura masa amma anqi afahimceni, to Ina ruwan mutum da duk matakain dana d’auka, kaga ni kaje duk yanda zakayi kahad’o mani kud’ina in koma wajen malan bakada imani, nasan shi kad’aine ke iya maida abunda bazai yuyu ba ya yuyu.” ( _wal iya zubillah, yya haww kam kinyi nisa kina buqatar addu’a, duk wani mai sab’o yakan b’oye baya son kowa yasani amma ke qarara kike nunawa mutane ke bakya tsoron ALLAHn da yayiki ma balle d’an Adam, ubangiji ALLAH ya shiryeki da duk masu hali irin naki_). ••• ••• ••• Da gudu taqarasa cikin zauren nasu tare da tsayawa tana fitar da nishi ahankali, murmushi tayi had’e dasa hannuwa tasake rufe fuskarta, “Alhamdulillah” tafad’a tare da sake leqowa tana hangosa daidai lokacin daya miqawa yaron ledar sannan ya juya yakoma tahanyar da suka biyo, da sauri takoma itama cikin gida tana fad’in “wai kodai mafarki nakeyi?” Daidai lokacin ta k’araso tsakar gidan umma najin me take fad’a tace “meye kuma kike tambayar ko mafarki kikeyi.” Cikin farinciki taqaraso inda take zaune tana gyaran wake tace, “Babu komai ummata” “Anya Rashida?, gaskiya da walakin goro acikin miya wannan farinciki da naga kinayi” kafin tarufe baki sai ga yaron da malan ya aiko yayi sallama had’e da cewa, “wai gashi inji malan idris yace abawa Rashida” kallon yaron umma tayi sannan tamaido kallonta ga Rashida data sunkuyar da kai qasa, murmushi umma tayi sannan tamik’a hannu takarb’i ledar had’e da cewa, “kace angode.” Har yajuyazai fita umma takirasa ta warware hab’ar gefen zanenta taciro naira hamsin tamiqawa yaron tace, “kace masa angode kaji ko.” “Kibarsu umma ai har yawuce nagode.” Yaron yafad’a tare da ficewarsa da gudu”ikon ALLAH, kaga yaro mai tarbiya, ubangiji ALLAH yai maka albaraka kaji.!” Acan cikin zauren ya amsa da “Amin” sannan yaficewarsa, juyowa umma tayi tana kallon Rashida dake duk’e tana tayata tsince waken, tanaji zatayi magana da sauri tamik’e tana cire jikkarta dake kafad’arta tashige d’aki don tasan babu abunda umman tata bata sani ba, ita dai umma abunma dariya yaso yabata wai yau Rashidar tace dajin kunya, “ALLAH ka sake shirya mana” tafad’a sannan taci gaba da gyaran wakenta, acan cikin d’aki kuwa Rashida kasa tsaida kanta daga murmushin da takeyi tayi tafad’a akan katifarta tare da mulmulawa tajawo pillow tarungume tana dariyar da umma bazata iya jiba ta runtse idanuwanta had’e da furta “I luv you malamina, I luv you Nuraddeen” Saida tagama sabbatunta tukuna ta tashi tacire uniform d’inta ta sanyo doguwar riga tafito don taya mahaifiyarta aiki, sosai umma ke kallie da sauyin walwalar da ‘yar tata ta samu tare da farincikin da take ciki wanda bako shakka tasan abunda take tsammanin rasawane akwanakin baya tasamu tabbacin samunsa, dariya tayi cikin tsokana da nuna cewa bata san abunda ke faruwa ba tace “Rashida nikuwa wai meye tsakaninki da wannan malamin naku daya aiko maki da saqo d’azu, gashican ma akan kujera na ajiye har babanki yadawo” Saida tayi dariya sannan tace STORY CONTINUES BELOW  “Kai ummata ai kunsan komai?” “A’a nikam ban san komai ba amma dai yanzu abani labari insha, don naga alamar farinciki ya banbanta ranar yau data sauran ranaku ukun da suka gabata, fad’amun meye sirrin ‘yatah.” Dariya ta sakeyi had’e da cewa. “Kai ummata, nafahimci komai nakeyi kina sane dashi qyalewa kawai kikeyi.” “Eh mana, ai duk uwa takan banbance tsakanin farinciki da kuma damuwar ‘ya’yanta, wasu lokutan kawai tanayin shirune har zuwa lokacin da take tunanin gazawa zata iya bayyana atattare dasu, awannan lokacinne take zamewa jigo kuma garkuwa agaresu har zuwa lokacin da jarumta zata zamo mabayyaniya agaresu. Duk da ban takura kiba wajen sanin halin da kike ciki, akoda yaushe nakan roqi ALLAH d’aya gaggauta yaye maki damuwarki kuma ya matso maki da farinciki marar misaltuwa Kuma alhamdulillah yau natabbata ubangjina ya karb’amun” “ALLAH sarki umma, tabbas ubangiji ya amsa maki addu’arki ga ‘yarki don kuwa ya yae mata damuwarta Kuma yasakata acikin farincikin da baya misaltuwa, ada bana iya banbance soyayya da shaquwa sai ranar da malam idris ya furta kalaman soyayya agareni, aranar ne nasan meye so kuma meye shaquwa, na fahimci gaba d’aya soyayyata da Rabe koda na auresa babu so da qauna aciki shirmene kawai nakeyi gashi najayewa kaina damar da zan iya zab’ar wanda nake son rayuwa dashi tahanyar bawa baba zab’i akan duk mijin daya auramun, hakanne ya jefani cikin matsananciyar damuwa da kuma rashin madafa har nake tunanin farincikina yatafi kenan har abada, ashe bansan cewa wanda yakawo sadakina kuma nake kallo a matsayin zab’in da mahaifina yayi mani shine wanda zuciyata keso, nan take na yankewa kaina hukuncin nesanta kaina da muradin zuciyata saboda insamu damar yiwa mahaifina biyayya, aqoqarin yin hakan ne malan Idris ya walwalemun zare da abawa har nafahimci cewa shine wanda yakawo sadakina kuma shine wanda zan aura” taqarasa maganar tare da miqewa tana kwashe kwanonin data gama wankewa, murmushi umma tayi sannan tace, “Ikon ALLAH, ai abunda baki sani ba tun kafin mahaifinki yasan alaqar dake tsakaninsa da mahaifin yaron ya yanke shawarar bashi aurenki, kuma ranar juma’ar daya je makarantarku wannan maganarce takaishi wajensa amma saboda ALLAH yariga ya tsaro komai yanda yake son yinsa si gashi kafin yasanar masa da cewa yabashi auren ‘yarsa shi da kansa yafad’awa iyayensa anema masa aurenki” “Tabbas ALLAH shikeyin al-amarinsa ayanda yakeso akuma lokacin daya dace, domin aranar ne nima malan Idris yafurta cewa yana sona wanda aranarne kuma nace baba yazab’amun duk wanda yakeso zan aura.” “To kingani yanda komai yafaru cikin sauqi, kece kawai kika wahalar da kanki, da ace ranar kin sanar dani komai to da bakisha wahala ba, ubangiji ALLAH yatabbatar da alkhairi atsakaninku.” “Amin ummata” tafad’a tare da rungumeta, girgiza kai umma tayi had’e da nad’a mata hannu abaya tace “Ja’irar yarinya ni cikani tunda ke kin zama ruwa biyu, yau kunya gobe rashinta, ALLAH ya shiryeki” haka suka cigaba da aikace aikacen gidan abun gwanin sha’awa tamkar ba ‘ya da mahaifiya ba saboda yanda umma ta sakar mata fuska tabata damar yin fira da ita sosai saboda tasamu damar nazartar kalaman ‘yar tata acikin maganganun da sukeyi. Bayan la’asar baba yadawo yaci abinci ya huta umma ta d’auko masa saqon da malan idris ya aikowa Rashida dashi, karb’a yayi had’e da bud’ewa yaga kwalin wayane da kuma wata leda daban, sa yayi aka kirata yace taciro wayar yagani taciro tana wani sissinne kai yace tabud’e kwalin, Wayace qirar techno L7 sabuwa dal harda charger d’inta da earpiece, karb’a yayi yaduba had’e da kunna wayar yaga har layi akwai ciki yace “To ki kula Kuma kiji tsoron ALLAH, ubangiji ALLAH yatsare kuma yasanya albarka” sannan ya miqawa umma itama tasa albarka tamik’a mata, Sai da suka yimata jan kunne akan matsalolin waya da kuma rashin alfanun da take jawowa idan mutim baiyi tak tsantsan ba sannan suka sallameta, har zata wuce baba yasake kiranta had’e da cewa d’auki wannan ledar ki wuce batare daya damu da sanin ko menene acikin d’ayar ledar ba, umma ce tace “malan to kaduba sauran kayan?.” STORY CONTINUES BELOW  “Indai ke kinduba alhamdulillah ya wadatar.” “A’afa nikam mezai sani bincikarsu batare daka gani ba!.” “To k’yaleta can dasu bazai wuce ‘yan turarukka bane da sauransu, Kuma kema kinsan nasha yimaki irinsu ko kuwa?” Yaqarasa maganar cike da tsokana yana yimata dariya, murmushi kawai tayi had’e da kauda kai gefe tana k’ara gyara zamanta. Aikuwa kamar baba yasani koda Rashida tabud’a ledar turarukkane guda uku sai tarkacensu sweet da cingwam, sosai taji dad’in kyautar don ba qaramin son sweet take dashi ba, Bayan sallar magrib baba yashigo ya leqa d’akin Rashida had’e da cewa takula da gidan zasu fita sannan yaje yacewa umma tafito suje, dama d’azu sunyi magana akan bayan magrib zai kyaita taga kayan d’akin daya siyawa Rashida idan sunyi gobe sai akwasosu, Basu jima da fitaba wayar Rashida tafara ruri wanda har saida yasa taji tsoro, kasancewar tana yawan amfani da wayar ummanta yasa duk tad’an San wasu abubuwan amma wasukam saiya zauna zaman koya mata saboda bata sani ba, gashi ita wayar daya sawo matama touching ce ita kuma tafi iya mai keypad, ta dad’e wayar na ruri kafin tasamu daqyar ta d’aga, “Assalamu alaikum.” Tafad’a kamar mai koyon magana kafin taji ta d’aya b’angaren an amsa mata da, “wa’alaikissalam d’alibata, ya akayi baki d’aga watar da wuri ba” “To malamina ban iya bane, ko yanzu ALLAH ne yataimakeni hannuna yakai inda ake d’agawar badon haka ba saidai ta qaraci kukanta tagama” tabashi amsa kai tsaye ba tare da wata kunya ko shayi ba, saida yayi dariya sosai sannan yace “Kai d’alibata, sedai kice naqarashi kirana nagaji nagama, oh ni Nuraddeen ya zanyi da d’alibata?” “Haquri zakayi tunda ba tason bokon.” Tafad’a tana dariya. “Hmmm ALLAH dai yakai damo ga harawa, boko kam ai kamar kinyishi kingama…” “Tirqashi! Ashe kuwa akwai ‘yan kallo, Allah yabani kon koya to.” “Amin, ya kike?.” “Lafiya klw malamina.” “Masha Allah, haka nekeson akoda yaushe kunnuwana sudinga ji, ya baba da umma duk suna lafiya?” “Eh suma lafiya klw yanzunnan suka fita.” “Allah yadawo dasu lafiya.” “Amin.” Shirune yabiyo bayan gaisawar tasu kafin yace, “Rashida nifa har yanzu nakasa samun natsuwa wajen tabbatar da wane irin so kike yimani, sai nake ganin kamar zuciyarki bata yarda da soyayyar da nake yimaki ba.” “Meyasa kace haka bayan Kai tsaye n nuna maka raunin da zuciyata tayi saboda yanda zantuka da kuma kalamanka suka narkar da ita, kamata yayi ace nice nake shakkun haka saboda banida wata nagartar daya kamata ace na cancanci samun soyayyarka.” “Hmm d’alibata kenan! Ai ita soyayya Bata dubin nagarta ko kuma dacewa da cancanta, kawai had’uwar jinice da kuma zukata da ALLAH kehad’awa lokacin daya so, karki sake tunanin cewa baki cancanci soyayyata ba domin hakan zi iya tarwatsa mani zuciya, Ina so koda zamuyi aure ya kasance mungamsu da qaunar da muke yiwa junanmu ta yanda bazamu tab’a bari wani abu yashiga tsakaninmu ba balle har wata rana aganmu arana ko kuma muyi yunqurin rabuwa da junanmu, Ina matuqar sonki da qaunarki wanda natabbata hakn daga ALLAH ne, zan tsaya maki wajen ganin nariqeki hannu biyu batare da nabari kin koka ba.” “Hmm! Malamina ai wannan abune mai wahala matuqar mutum naraye, zanyarda akan bazaka sakani koka waba amma indai wannan rayuwarce da wataran farinciki wataran Kuma baqin ciki to dole zan koka tawani b’angaren, babban burina shine ace ka so ni ayanda nake d’innan koda bazan samu ilimin bokon da kake muradi ba sannan kayi hak’uri da raunina alokacin dana gaza, ni kuwa nayi alk’awarin riqeka kai kad’ai acikin zuciyata batare dana had’aka da kowa ba, zanyi jarumta wajen kula da kai da kuma baka farinciki har iya qarshen rayuwata.” Shiru yayi yana sauraren kalamanta da yakeji tamkar karta dena, tabbas yayarda kowane bawa da irin baiwar da ALLAH yayi masa, Rashida batada ilimin boko amma duka kalamanta cike suke da fikrah da kuma ma’ana, a ‘yan shekarunta baiyi tsammanin zai iya samun nagartaccin kalamai daga wajen taba, asali ma yad’auka wayayyiyar mace ‘yar boko ita kad’ai tasan yanda ake sarrafa harshe wajen furta kalmomin soyayya, murmushi yayi sannan yace STORY CONTINUES BELOW  “Indai wannan ne muradinki da Kuma burinki to ki kwantar da hankalinki, ni Nuraddeen nayi alqawari zan soki so mai tsanani Kuma zan d’aukaka darajarki acikin ‘yan uwanki mata.” “Ina godiya da hakan malamina” tafad’a cike da farinciki, firarsu sukasha sosai kafin ya canxa akalar firra zuwa wajen koya mata yanda zatayi amfani da wayar, dariya tayi sannan tace. “Malamina kahutar da kanka don bana fahimtar komai ahaka, inda ma ace a ikacene kake nuna mun to da zanfi fahimta amma wannan left da right da kake fad’a awajen asambuli kawai nake ganesa.” Dariya yayi sosai kafin yace “shikenan gobe kifito da wayar sai innuna maki wasu abubuwan a aikace kinji ko?.” “To shikenan, seda safe naji motsi qila su baba ne suka dawo” “Ok. To kigaishesu.” “Zasuji in sha ALLAH malamina.” murmushi yayi ahankali ya furta mata “I love you so much Rashida.” Dariya kawai tayi had’e da ajiye wayar tayi tsakar gida, “hello, hello.” Yadinaga fad’a amma ga mamakinsa yaji shiru, yatabbata ajiye wayar tayi batare data kashe ba ta tafiyarta, dariyar shima yayi sannan yakashe wayar ya ajiye, ji yakeyi Ina ma rashidarsa zata iya karanta message day tura mata dad’ad’an kalaman da zasu dad’a sanyaya mata zuciya kuma suqara mata qaunarsa, amma kash yasan dole soyayyarsa tasamu tawaya tawannan gefe. ••• ••• ••• Baffa kuwa tuni yaba baffa usman shanunsa guda biyu yace aje asayar dasu kud’in afara sawo kayan aikin da za’a fitarwa da Nuraddeen sashen da zai ajiye matars, kafin kace me tuni baffa Usman yayi yanda yace har anfara aza gini mai kyau, wanda duka baffa Usman ne yakira wud’anda suka fitar da zanen yanda za’ayi ginin, ciki da falo sai toilet da kitchen duk acikin sashen da aka d’ibar masa tsakankanin shiyar mahaifinsa data baffa Ali…. *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/25, 9:34 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___15💎 Wasa wasa gini yafara girma saboda aikin akeyi ba dare ba rana, duk wani tanadi da baffa yayi sai daya fiddosa yabawa baffa usman yace ayi duk abunda yakamata kafin lokaci yayi don baya son aikin yakai har lokacin da za’a kawo amarya, acewarsa hakan yafi da ace ankawo yarinyar mutane cikin matsuwa inda bazata samu sakewa ba, sosai duk wanda ya kalli baffa cikin natsuwa zai fahimci bakad’an yake matuqar jin jiki ba, ammasaboda qarfin hali akoda yaushe qoqarin b’oye hakan yakeyi don gudun kada adakatar da auren. Ita kuwa yaya hawwa kullum cikin masifa take wai ama faman kashewa k’asa kud’i a banza anqi atanada Amma tun daga baffa har zuwa baffa Usman Babu wanda ya tankata inba baffa Ali dake sake zugata akan ccewa inbatayi da gaskeba duk nan baffa zai qarar da kud’in gashi yana jinya abarta da wahala, sake rufe idanuwa tayi ita ala tilasa a ajiye ginin inyaso Nuraddeen d’auki shigihwa guda a cikin shigihun dake sashen nasu a gyarawa yarinyar, nan ma baris baffa yayi da ita saima cigaba da bada kud’i da yakeyi ana cigaba da aikin, tayi masifar tayi har tagaji don kanta tabari amma babu abunda ke dad’a b’ata mata rai irin yanda taga ana narkewa wajen kud’i da irin manyan shanun da yasa aka kama aka sayar, hakan ba k’aramin takaici da bak’inciki yake sata ba idan ta tuna, gashi har yanzu takasa had’a kud’in da malam bakada imani yace tahad’o wajen yimata aiki balle tasan ko meye madafarta, wata shawara ta yanke aranta na zuwa wjen baffa ko zata samu cikon kud’in da take nema wajensa, kwance ta iskoshi duk ya had’a zufa saboda wutar da aka d’auke sai zafi ya taso masa, “A’a malan kaid’ai kake a d’akin ba kowa? Sukuma ‘yan albarka sun d’auke wutar duk zafi yataso, kai ALLAH dai ya rangwanta mana” tafad’a tana jaye labulayyen taga saboda iska yashigo sannan taqaraso wajensa ta tallabosa ya tashi zaune yana fad’in “wash! bi ahankali hawwa, bayannan inajin yana yimun zafi sosai” “Sannu malan, sai hak’uri kasan dama shi sauqi ahankali yake shiga, ALLAH dai yabaka lafiya.” “Amin hawwa.” Yafad’a yana kallonta cike da mamaki don yasan wani abun take so, bai qarasa tunanin da yakeyiba yaga ta d’auko mafefeci tafara yimasa fiffita had’e da cewa, “malan kaga aurennan ya matso gashi babu fashi sai anyisa kuma inada buqatar inyi wasu ‘yan gyare gyare, shine nace mezai hana ko ‘yar dubu goma ka qara mani insamu in gyaggyara kafin lokacin ya qaraso” murmushi yayi don dama uasan za’a rina, indai hawwar daya sani ce Babu yanda za’ayi kaga tana yimasa wud’annan abubuwan batare da tana son wani abu daga garesa ba, d’an nisawa yayi sannan yace, “Hawwa dubu gomafa kikace?, Yanzu ke ko hidimar gyaran inda yaronnan zai zauna da nakeyi bakya gani har zaki zomun da wannan zance, haba hawwa ai kamata yayi ace kinkawo nahannunki anqara dasu bawai kinemi karb’a ba” “Amma naga ainima duk hidimarce zanyi ko malan, ko kafiso akawo yarinyar nan babu wani abun kirki da aka tsinana agidan?.” “To meza’ayi tunda dai naga ba kishiyarki bace balle kice haka, in Kuma maganar abubuwan da za’aci a rarrabane to kibari lokaci yayi ina sane dasu, mufa wajen ango muke ba amarya ba balle muce wata hidima zamuyi.” “Dakata malan kawai idan bazaka bayar bane kafad’amun Amma bazai yuyu kazauna kana fad’amun yanda ranka keso ba.” Taqarasa maganar had’e da miqewa ta jefar da mafefecin gefe, “Meyayi zafi haka daga magana hawwa karki manta yaronnan d’an mune mu muka haifesa kinga kuwa gaba d’aya hidimar tamuce dani dake kuma yakamata ace kema kin kawo taki gudun mawar, ni nazatama kina can kina qoqarin had’a masa lefe ashe aiki nizai qararwa.” Ya iyar da zancen yana dariya, wani irin mugun tsaki taja sannan tabar d’akin, girgiza kai yayi yace “ALLAH ya shiryeki hawwa.” ••• ••• ••• Ta b’angaren baba kuwa tuni yaga yakammala had’a kayan d’akin Rashida da taimakon d’an uwansa malan balarabe, haka itama umma bisa amincewar Rashida tasa ‘yan uwanta sukazo tabasu sadakin Rashida da kuma abunda ALLAH ya hore mata da wanda suka kawo mata tace suje tare da rashidar duk abunda takeso ta fannin kayan kici dana aikace aikacen gida asawo mata, tun safe suka fita basu dawo ba har sai qarfe biyar na marece, sosai umma taji dad’in sayayyar da sukayo mata don Babu abunda basu siyoba sai wanda aka manta, shire shiren auren sukeyi sosai don tuni sun fara rabon minti da cingwam, soyayya kuwa tsakanin Rashida da Nuraddeen sai wanda yagani, cikin sati d’aya suka d’inke waje d’aya tamkar wasu masoyan da suka jima da shekaru suna soyayya, kullum cikin satin sai yaje wajenta fira da daddare wani lokacin kuma da marece, tuni d’aliban makaranta da kuma malamai suka sanda alaqar dake tsakanin malam Idris da Rashida wanda mafi yawansu sunsha mamakin yanda malam idris yake d’an kwalisa kuma wayayye da yasha boka zai auri Rashida wacce kaf makarantar babu wanda baisan da zaman taba saboda tsabar takkwalci, wasu kanyi fatan alkhairi gareta akan ALLAH yasa ta sanadiyarsa tamaida hankali ga karatu wasu kuma kanyi dariya had’e da cewa ya kwasarwa kansa daqiqiyar yarinya kuma jahila, duk abubuwan da mutane kefad’a suna dawo masa a kunne amma ko sau d’aya bai tab’a jin damuwa akan haka ba, yariga yaji ya gani aduk yanda Rashidarsa take yana sonta kuma yana qaunarta ahaka, ana gobe juma’a da zai koma gida yazo fira wajen Rashida da daddare bayan tafito tayi masa shimfid’a a zaure ya zauna takoma cikin gida ta kawo masa ruwa yasha sannan itama tazauna saman kujera irin tazaman gida dake facing d’insa, “Sannu da zuwa malamina.” Tafad’a tana jujjuya wayarta dake hannunta kafin shi kuma ya amsa mata da “yawwa habibty, kina lafiya?.” “Lafiya klau alhamdulillah, ya shire shiren tafiya?, gobe sai gida ko?” STORY CONTINUES BELOW  “In sha ALLAH, ko Zaki rakani?.” K’walalo idanuwa tayi waje had’e da cewa “na shiga uku ni ‘yar babanta, rufan asiri kada kasa abugani ajaridu” “Saboda kinje gidanmu ana saura sati d’aya bukinmu?, Ai ni kuwa sai nake ganin da nan da can duka d’ayane Babu wani abun aciki!.” “Hakane, Amma dai kasan hakan ma bazata faruba gaskiya.” “To naji, nima dai da wasa nakeyi amma Ina so ne idan Allah yasa nakoma ranar lahadi za’azo akawo lefe” “ALLAH yakai ranmu kuma yasa ka isa lafiya.” “Amin habibty, amma Ina so don ALLAH kiyi haquri da duk abunda kika gani, ba haka naso ba yanayin abunne yazo ahaka.” “Malamina kenan! Ni koda duka lefenne baka samu damar yiba bazanji komai ba saboda inada yaqini da kuma tabbaci akanka, nasan idan nazama mallakinka zakayi mani fiye da abunda bana tsammani don haka ka kwantar da hankalinka, bakada damuwa akan haka.” Yaji matuqar dad’in kalamanta kuma yasake samun natsuwa akan halayyarta donmin ayanda halayyar ‘yan matan yanzu take basa da fahimta wajen maganar aure balle uzuri amma ita gashi cikin sauqi ta fahimcesa kuma ta amshi uzurinsa, bai wani jimaba yakoma had’e da yimata bankwana don gobe tun da wuri zai wuce saboda akwai abubuwan da yake tunanin yi idan yakoma, har bakin qofa tarakosa tare da yimasa ALLAH ya kiyaye sannan tajuya takoma cikin gida, yana barin wajen yanufi wani shagon sayarda kayan sawa da sauran abubuwa dake cikin gari don dama tun jiya ya amshi kud’in adashin da suka had’a shida sauran malamai sunayi dubu d’ari da hamsin, akwatunansa yasaye guda biyu da d’an qarami na sama naira dubu goma sha biyar sannan yasayi atamfuna guda goma masu sauqin kud’i da kuma lace guda biyu na dubu goma sha uku uku, sai shadda d’aya da material yard shima mai sauqin kud’i k’waya uku da doguwar riga k’waya biyu itama da qananan kaya suma kala uku, ya kashe kusan dubu hamsin da wni abu a fannin kaya kawai sannan yasake cire wasu dubu talatin yace ahad’a masa kayan shafa da hijabai da mayafi, kud’in sunyi kad’an sosai amma yace ahad’a mashi su yanda suka samu, takalmi da jaka kala biyu ya siya sai sauran tarkacen underwears kud’in suka qare ya rage dubu d’aya ce ta rage masa a aljihu, hakanan yakwashi kayan yakoma d’akinsa yana mamakin yanda kud’in suka shige kaf cikin ‘yar wannan qaramar sayayyar gashi kuma bai qarasa had’a sauran kayan ba, dama zancen inda yake tunanin gyarawa da ya ajiyeta tuni baffa ya sanar dashi yakwantar da hankalinsa duka abunda yakamata ayi za’ayi kawai yaji da had’in lefe da kuma abunda zaiba yarinyar nabuki, hakan yasa yasamu natsuwa sosai har yasamu damar yin wannan sayayyar, safiya na wayewa ya kama hanyar zuwa gida tare da akwatunansa yana tunanin abunda zai iskowa wajen mahaifiyarsa idan taga kayan… *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [6/26, 11:11 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___16💎 Tun daga qofar gida da mashin ya ajiyesa yaga alamar cewa aiki akeyi agidan nasu saboda tarin yashi daya gani da masu aiki da sai faman shige da fice sukeyi da kayan aikinsu, yaran gidansu dake gefe suna buga k’wallone suka hangosa da gudu suka nufo inda yake suna fad’in “oyoyo yaya nura, ya nura oyoyo” suka qaraso wajen su kusan bakwai suna ruguguwar d’aukar kayan, cikin tsawa ganin yanda suke jan jikkunan akwatayyen suna ruguguwar d’auka yace “ha’a kai kunada hankali kuwa! Ji iskanci zaku lalata kayan mutane, maza ku ajiye kubani waje.” Dariya suka aza masa ganin yanda ya zazzare masu idanuwa, kansu yayo ahasale kamar zai dokesu suka bar wajen aguje sunaci gaba da dariya, d’aya daga cikin sune daya d’arasu hankali ya tsaya yana had’e da cewa “yi hak’uri yaya nura” kwafa yayi kafin ya d’auki d’ayar jikkar da tafi girma da qarami yacewa yaron, “yusuf d’auko mun wannan d’ayar.” Cikin jin dad’i yaron ya tallabo jikkar ahankali tamkar wanda ya d’auko k’wai yabi bayansa, Kai tsaye shigifar da baffa ke kwance yanufa da kayan yaron nabiye dashi sukayi sallama suka shiga, baffa na ganinsa ya washe baki had’e da cewa, “Kai agaida mutanen yarimawa, sannu da zuwa sannu da zuwa.” STORY CONTINUES BELOW  “Yawwa baffa, munsameku lafiya” Nuraddeen yafad’a yana ajiye kayan had’e da komawa kusa da mahaifinnasa ya zauna, shima yaron ya ajiye ta hannunsa inda yaga ya ajiye sauran sannan yafita, binsa da kallo baffa yayi kafin yajuyo ya maido kallonsa ga Nuraddeen yace “lafiya klw Nuraddeen yaron can nake kallo kaf cikin yaranmu shi kad’ai ALLAH yayiwa natsuwa sak irin taka, shiyasa yake matuqar burgeni, gaba d’aya halinsa ba irin na sauran yaran bane da kuma mahaifinsa, kaga ikon ALLAH bazaka tab’a ganinsa kace yaron Aliyu bane don gaba d’aya tun daga kamarsa da halin kai hatta tafiyarsa duk irin na Usman ne kai kace shiya haifesa” murmushi yayi had’e da cewa “ALLAH sarki baffa, ao dama zumunka ka haifa maka, ni kaina jinina yafi had’uwa da nasa akan sauran yaran, yanzu nagamo dasu abakin gida gaba d’ayansu basajin magana baffa saidai addu’ar ALLAH ya shirya.” “Amin fatanmu kenan!, Kai dai ka kula kuma dikkaninsu ka rik’esu gaba d’aya da zuciya guda saboda abu d’aya like kuma duk lalacewarsu bakada wud’anda suka fimaka su aduniya don haka kayi haquri da yanda halinsu yake ka sosu ka qaunacesu don bazaka iya canzasu ba, ubangiji ALLAH yayi maku albarka ku duka” “Amin baffa, insha ALLAH zan kula da hakan har qarshen rayuwata.” “Masha ALLAH da kuwa naji dad’i sosai.” Juyawa gefe yayi tare da jawo ledar magungunansa yana duddubawa sannan yace “Baffa ya qarfin jikin naka?” “Alhamdulillah ina samun sauqi sosai.” “Amma baffa jikinka ya gagara nuna haka har yanzu, kodai canza maka maganukkan nan za’ayi?.” “A’a nace maka nasamu sauqi sosai, yakabaro can wajensu ‘yar tawa, suna lafiya?” “Duk lafiya klw baffa” “Madalla kasamu kaje kawatsa ruwa daga nan sai kashiga kagani komai yakusa kammala.” “To baffa, dama cewa nayi ga kayannan nagama had’awa sai ‘yan abubuwan da baka rasa ba.” “Ahhh to masha ALLAH, ai wannan Bari kakeyi har saika huta sai ka kirawo ita mahaifiyar taka da sauran dangi abud’a agani, agaisheka ALLAH yayi albark.” “Amin baffa.” Yafad’a tare da miqewa ya nufi sashen da mahaifiyarsa take, har ya aza qafa zaishiga cikin rumfar d’akin nata ya hangota wajen da dabbobi suke tana dama masu qasari, juyowa yayi tare da nufo inda take yana fad’in, “Ahhh..innarmu ashe kina nan.” Dayake kanta aduqe yake batama lura da shigowarsa ba sai yanzu da taji maganarsa ta d’ago kai da sauri had’e da cewa. “A’a oyoyo oyoyo, d’an baffansa shigowar yaushe?” Takwankwahe hannun rigarsa yayi had’e da saka hannunsa cikin bahon da take had’awa dabbobin qasari yayi yana murmushi yace, “banjima da isowaba innarmu, ai nazata yarannan sunshigo sun fad’a maki, wajen baffa kawai nafara isa na duboshi da jiki.” “Rabu da ja’iran banza, yanzu haka wasa ta d’auke masu hankali basu shigo suka fad’a munba aida tuni na isa wajen kafin ka zazzagewa mahaifin naka aljihunka, gashi yanzu sun jamun tsiyar da k’ilan ko sisi bazan samu ahannun kaba.” “Kai innarmu! Ai kinsan yanzu ba’ayi albashi ba ko sisi banzo dashi ba balle baffa klya karb’a.” “Kai ni rufemun baki, kai da baffan naka ai ba’a gane kanku, Ina dai lafiya naga yau ka iso kafin a hau masallaci kai da baka isowa gidannan sai bayan sallar juma’ah wani lokacin ma har ana gab da sallar la’asar.?” “Lafiya klw innarmu kinsan yanayin yanda rayuwar take, balle yanzu da abubuwa suka shigo gabana.” “ALLAH yakyauta, tashi kaje ka watso ruwa kaci abinci kafin afara kiraye kirayen sallah.” “To innarmu, wai kije baffa na nemanki.” “Kai nifa akwai aikace aikacen da nakeyi bana so inje yafara mani suruttannan da basuda gaira balle dalili.” Kasa cewa uffan yayi ya girgiza kai cikin ransa yana mai addu’ar ALLAH ya shirya masa mahaifiyarsa. STORY CONTINUES BELOW  Har yayo wankansa ya sauya kaya tana nan zaunenta ita da wata mata da tazo wajenta suna fira, wannan karonma girgiza kai kawai yayi yawuce abunsa, har yad’anyi nisata k’wala masa kira yazo, “Kashiga kitchen akwai sauran d’imame ka kad’auka kaida mahaifinka don namanta bansamu tun d’azu nasa ankai masa ba.” agogon hannunsa ya duba yaga sha biyu saura amma ace har lokacin mahaifinsa bai karyaba wannan wace irin rayuwace mahaifiyarsa keda ita bayan tasan ko cikakkiyar lafiya bayada, kamar zaiyi kuka yace. “Innarmu badai sai yanzu baffa zai karyawa ba?” “Eh mana, ai kaji nafad’a maka mantawa nayi, kaje ka d’auka katafi in kuma so kakeyi saika gama tuhumata to bisimillah.” “Bahaka nake nufi ba innarmu, kinsan ba cikakkiyar lafiya yake da ita ba ko kad’an bai dace ace yakai wannan lokacin bai karya ba domin hakan zai iya shafar ‘yar sauran lafiyar data rage masa,” mik’ewa tsaye tayi had’e da dukan qirji tana zaro idanuwa tace “Nashiga uku ni kuluwa, yanzu yaronnan nizaka qarewa magana akan mahaifinka, eh lallai ta tabbata za’a rabani da d’ana tun ba’aje ko Ina ba, to tunda nabar ubanka da yunwa zoka dokeni kaji ko nura?.” “A’a innarmu ai batakai can ba ALLAH yabaki hak’uri.” Yafad’a tare da shiga kitchen ya d’oko abincin sannan yawuce, yanaji matar dake zaune tare da ita tana fad’in. “Kai hawwa! Haka nura yakoma maki marar kunya daga jin zancen aurensa?, To wlh sai kintashi tsaye inba haka ba da ankawo yarinyarnan yasan yanda lamarin yake shikenan kashinki yabushe, dubi wannan rashin kunya daya zuba maki daga ganin zaiyi aure to inata da anyi auren, gaskiya akwai aiki babba e’ehhhmmm nura kam ya lalace” cike da takaici ya qarasa barin wajen ba tare da yaji amsar da zata fitowa daga bakin mahaifiyar tasa ba, yana kaiwa bakin qofar shiga d’akin da baffa yake yaci karo da baffa Ali shi kuma zai fitowa, yana gaishesa amma kota kansa baibi ba jikinsa har rawa yakeyi ya isa wajen yaya hawwa ya kwarmato mata duk da dai baffa yace yaje ya kirawota, binsa da kallo yayi sannan yawuce cikin d’akin ransa a dagule, baffa isman daya gani zaune ya sashi sakin murmushi had’e da duqawa har qasa ya gaisheta bayan ya ajiye kwanon tuwon agaban baffa, Baffa Usman na murmushi ya amsa masa cikin fara’a had’e da cewa, “Agaida ango d’an gidan baffa, sannu da qoqari, ashe da tsiminka ab’oye kasa yayana yanata wahala.” Cike da kunya ya noce kai qasa yana murmushi baffa Usman yaci gaba da cewa, “Madalla to ai ka kyauta, ALLAH yayi albarka yaqara bud’i.” “Amin baffa Usman.” Ya amsa masa a kunyace, jiyayi baffansa yace, “Meye nan ka ajiye nura.” “Tuwone innarmu tace akawo maka.” “Kai kaci naka.?” “A’a baffa alhamdulillah naqoshi.?” “To Nima dai Alhamdulillah don qanena ya sawo mani abunda na samu na karya kuma har nasha magani, ubangiji Kuma ALLAH ya shirya yaganar.” Dashi har baffa Usman sun fahimci yanayin damuwar da yashiga yanzu amma saboda shi mutumne mai haquri da rashin son aibata babba gaban qarami a maimakon yayi fad’a sai ya sauya maganar ta hanyar addu’a.” Kamar iska haka sukaga yaya hawwa tashigo d’akin rai ab’ace tana dube dube ALLAH kad’ai yasan abunda baffa Ali yafad’a mata wanda shi ya haifar da shigowar tata ahaka, tsaye tayi cak ganin akwatunan tana cika tana wani batsewa kafin ta kalli Nuraddeen tace, “Amma kai wannan yaro munafuki ne, yanzu kasan da wud’annan kayan kazo a matsayina na mahaifiyarka a maimakon ka kaisu can saika tsaya anan dasu ka ajiye don d’ai munafucci, to meye alaqar uwaye maza da kayan lefe indai ba k’ulle k’ulle ake son ayimun ba wai don har ka renamun da wayo ina yimaka magana kace ba’a wani yimaku albashi ba, to su wud’annan uban kayan daka jido uban waye yabaka kud’in….” Bata qarasaba taji baffa yace, STORY CONTINUES BELOW  “Ubansa ne yabasa ko bai isa ba?” Shiru tayi tare dayin tsaye tana girgiza jiki ita mai zuciya, cikin b’acin rai da takaici baffa ya katsa mata tsawa had’e da cewa “maza kizauna kafin ranki yab’aci.” Cikin tsiwa tazauna saboda sanin halinsa kafin nan baffa Ali yashigo tare da sauran matan, shidai baffa Usman dama tunda tashigo ya noce kai qasa yana karanto addu’o’in daya sani abakinsa, shid’in mutumne mai sanyin hali da kuma haquri tamkar yayan nasa amma ko kad’an bai iya b’acin rai ba, shiyasa ba kasafai yake kula wasu abubuwan ba don gudun b’acin rayuka, batare da baffa yanuna komai aransa ba yasa matan qannen nasa suka jawo kayan aka shiga bubbud’awa kowanensu na yaba kyawon da sukayi tare da ALLAH yasanya alkhairi, har aka gama Yaya hawwa batace uffan ba sai da taji matar baffa Usman tace, “Nura kam kayi qoqari sosai kuma kaya sunyi kyau amma ni banga sarqoqi da ribon ribon d’in ‘yar tawa ba ko ka mantane..” ai kamar jira takeyi kafin tarufe baki tace, “To tsohuwar munafuka, irin kune masu qaryar arziqi alhalin bakuda komai, da zakice babu kaza da kaza duk wud’annn kayan da yayi inba raahin imani ba ace har sai yaqaro wasu ko don bake kika haifesa ba ba’asan amshi ba sai dai karb’a zakice hakan.” Tabud’e baki tabata amsa baffa usman yace, “kul..bilqeesu karki fara.” tashi Nuraddeen yayi yabar d’akin ransa ab’ace yayinda matar baffa Usman tace, “Haba maigida, yanzu meyayi zafi acikin wannan maganar da zata jefomun wud’annan kalamai, inadai ‘ya’yane nima ina dasu kuma Alhamdulillah idan amshi kad’ai nasani tunda ‘ya’ya mata nake dasu banida takaici dama haka ankasan macce da abata, ita kuma dake alfaharin..” Bata qarasa ba yace tabar d’akin tunda tayi ALLAH sanya alkhairi shi dai baya son fitina, dole tafita tanajin wani sululi aranta saboda Babu ranar da Yaya hawwa bata goranta mata rashin d’a namiji saboda gaba d’aya ‘ya’yanta biyar duk matane har sun aurar da biyu saura uku. Tana wucewa baffa Ali yace, “amma dai Usman yakamata ka tsawtarwa matannan taka, ni bansan abunda yaya hawwa ta tare mata ba duk tabi ta renata, Wlh yaya wannan balkisun da kake gani so takeyi tawatse mana zuria amma inba haka ba daga fad’ar gaskiya saita rufe yaya hawwa da baqar magana, ai wannan rashin mutuncin ne..” yana rufe baki matarsa da tuni tuquqin baqincikin ganin wud’annan kayan bana ‘yarta bane ya mamaye mata zuciya taja wani irin dogon tsaki tabar wajen, “Itafa wannan kace me?” Baffa Usman yafad’a yana nuna masa hanyar data fita, tsuru tsuru yayi da idanuwa tare da noce kai qasa baffa yyi murmushin da yafi kuka ciwo sannan yace “Ubngiji ALLAH yaganar damu muduka” Mere baki Yaya hawwa tayi kafin tace, “Amin, Ali kwasomun kayannan tunda angama gani gobe akirawo makwabta suma su gani kafin atashi kaiwa” tana gama fad’a tawuce abunta don kar wnda yaga damarta, jiki narawa baffa Ali yanufi kayan baffa yace… *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU_*👏😭 [6/27, 10:52 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___17💎 Kul Aliyu kada kasake inga hannunka yakai ga kayannan, Babu inda za’aje dasu anan za’a barsu har zuwa jibi, inyaso kyasanar da ‘yan uwanki ko mutum d’ayane sai yazo aje akai kayan tare dasu bilkeesu, har tafidda qafarta d’aya awaje tana shirin aza d’ayar tajuyo da qarfi jin abunda baffa ke fad’a. STORY CONTINUES BELOW  “Malan menaji kana fad’i?” “Abunda duk kunnuwanki suka jiyo maki kuma maza kifice mun da gani.” Fita tayi ranta ab’ace ta tsaya abakin qofa tana zazzaga maseefa ita kad’ai yayin da baffa yace su baffa Usman suriqasa yana so yashiga ban d’aki suka barta can tanata kumfar baki, wunin ranar kusan aqofar d’akin ta wuni tana zazzaga masifa inda taka shiga ba nan taka fita ba tana nemn wanda zai tankata, sai akayi sa’a hatta baffa Alin dake biye mata baice da ita uffan ba ya shirya yawuce masallaci wajen sallarsa ta juma’ah, bayan sun dawo Nuraddeen ya nufi sashen da ake gyara masa cike da farinciki duk da kuwa zuciyarsa dasqare take da damuwowi kala kala, Ba kad’an tsarin part d’in nasa ya burgesa ba, baran ganin kitchen d’insa da toilet ba’a waje suke ba, hakan ya matuqar yimasa dad’i arai, tuni an kammala komai fentine kurum ya rage, sai wearing na wutar nefa da ba’ayi ba, suma akwai komai aqasa nan da kwanaki za’a ida kammlawa, ya jinjinawa qoqarin mahaifin nasa sosai tare da yimasa godiya da addu’ar ALLAH yaqara masa lafiya da tsawon rai. Yaya hawwa kuwa duk iya dubarunta da kinibibin da zatayi wajen gani kayan sun dawo hannunta tayi amma takasa samun nasara saboda yanda baffa yakasa ya tsare daga qarshema cewa yayi kar wanda takoma kawo masa da sunan yazo ganin lefe saboda gobe za’a kai lefen, annan ma taso tayi maseefa amma tayi shiru don taga take taken yanzu baffa daidai yake da ita, kad’an yake jira yayi mata rashin mutunci shiyasa ta aminci da abunda yace, gashi tagama zagaye anguwa da makwabta azo aga lefen d’anta takoma saidai duk wacce tazo ganin lefen sai tace mata anrufe, haka sukata fita kowa da kalar tsogumin da yakeyi akan ta aika masu suzo ganin lefe kuma tace anrufe qilan bawani abun azo agani d’an nata yayi ba shiyasa takasa gwada masu gudun kar tayi abun kunya, duk wud’annn suruttai da akeyi suna dawoma kunnuwanta wanda hakan yamatuqar b’ata mata rai, qwafa tayi had’e da cije baki tana girgiza qafa daga zaunen da take kafin tace, “Wlh malan kayi da gwana, sai kace wannan abun daka yimun da bakayi shiba, yanzu banida lokacinka, Amma kabari idan nagama da wannan figaggiyar yarinyar da za’a kawo nadawo kanka, alokacin zaka gane cewa ka tabka babban kuskure.” Ita kad’ai take suruttanta ad’aki wanda abun har ya riga daya zame mata jiki ka, sallamar Nuraddeen tajiyo abakin k’ofa tana hango yana cire takalmansa kafin yashigo, ciki ciki ta amsa masa sallamar don yanzu gaba d’aya tamaida laifin akansa tad’ora, waje yanema ya zauna ita kuma tajuyar da kai gefe, sunkuyar da kansa yayi qasa cikin damuwa kafin yad’ago had’e da cewa. “Innarmu barka da marece” “Yawwa” tafad’a adaqile batare data juyo takallesa ba, “Innamu don Allah kidena wannan fushin inba so kikeyi infad’a cikin fushin ALLAH ba, don ALLAH kiyi haquri kifad’amun duk abunda kike so zanyi maki amma don ALLAH kidena wannan fushin dani” jin abunda yace yasa tad’anyi ajiyar zuciya had’e da juyowa tace, “Duk abunda nikeso zaka yimun?” Cikin rawar muraya yace “e..e.eh zanyi maki indai bai sab’awa ALLAH ba.” Fad’a murmushinta tayi sannan tace “Ka kwantar da hankalinka bazansa kasab’awa ALLAH ba, so nakeyi ka nunamun cewa ni mahaifiyar kace, ka d’auko lefencan yadawo d’akinnan saboda nagaji da abun gori da kunya da makwabta keyimun, yanzu fisabillahi inba mahaifinka da iyayi ba, Ina ruwansa da harkar mata, Ina lefe sha’aninmu me na mata don me zaiyi wani kane kane aciki, Nima ina so ingwadawa duniya jarumtar da d’ana yayi amma gaba d’aya yazo ya hana” “Amma innarmu naga da nan da can wajensa duka d’ayane kuma ai kayan gobe ma za’a kaisu tunda har na sanar da ita tafad’awa iyayenta.” “To.to shikenan tashi katafi, don kasanar da ita sai me, Ina ni nahaifeka Kuma nafad’a maka kayannan wasu ‘yan uwana duka basu gani ba sai faman yab’a mani magana sukeyi akan haka, ai shikenan ka kyauta tinda so kakeyi nazama abun nune a anguwa” taqarasa maganar tare da fashewa da kuka, Babu banban burinta kamar ace kayan sun dawo d’akinta, don tad’au alwashin zabce rabi tabar mata rabi, don bazata yarda ba ace kura da shan bugu…ita da d’anta ace wata tafita moriya dashi tun ba’aje ko ina ba, sau biyar kad’ai yatab’a siya mata atamfa amma gashi kusan kala ashirin da wani abu yahad’awa wacce zai aura, shiru yayi cike da mamakin meye abun kuka anan da har mahaifiyar tasa zata fashe masa dashi, cikin sanyin murya yace STORY CONTINUES BELOW  “Kiyi hak’uri innamu bari nakira yarinyar nafad’a mata cewa amfasa kawo lefen gobe, shikenan haka yayi maki.” Da sauri tace “eh yayi, kirata yanzu agabana kafad’a mata” ba musu ya ciro wayarsa yakira Rashida, bugu d’aya ta d’aga had’e da cewa “hello malamina.” Cikin jin dad’in sauraren muryarta yace “Habibty ya kike? Kina lafiya?.” “Lafiya klw, ya naji muryarka bayanda nasanta ba, ko kana kewatane. Taqare zancen cike da zolaya tana dariya, murmushin yayi shima had’e da kallon mahaifiyar tasa data kafesa da idanuwa tana harara suna had’a idanuwa ta d’aure fuska tare da kauda kanta gefe, murmushin ya sakeyi sannan yace. “Sosai habibty I really missed you.” Murmushi tayi don tafajimci meyake nufi saboda duk k’ananan kalmomin nan na soyayya yafara koya matasu kuma tana saurin fahimta da kuma haddacewa, matsalarta d’aya bata iya rubutawa balle takaranta sai dai inda ajami za’a rubuta mata, sanin har izuwa lokacin tana kan layi yasa yaci gaba da cewa, “habibty zancen kawo lefe da za’azo gobe odan baki fad’awa su umma ba to kifad’a masu sai ranar attanin za’a kawo saboda wani dalili kinji ko.” “To shikenan, dama ban fad’aba sai yau nake tunanin fad’a masu don haka babu matsala.” “Yawwa nagode sai anjima idan nakira” da haka yakashe wayar yana kallon umma da farinciki kwance a fuskarta fal tace. “To ko kaifa, yanzu kaga sai ad’auko lefen akawo zuwa gobe ‘yan uwana sun gani an uma tsaida wud’anda zasuje jebi sai akai ko kuwa” “Hakane innamu ALLAH yatabbatar da alkhairi.” Qirikiri tayi mui da baki batare data amsa masa da abin ba don itakam Bata fatan yazauna da yarinyar ballantana tayi fatan wani alkhairi a tsakaninsu. Mik’ewa yayi zai fita tabiyo bayansa had’e da cewa “Nace babu d’an wani abu a hannunka nan, kasan kullum mahaifin naka nanan zaune waje guda sai abunda ‘yan dubiya suka bashi, d’an tanadin da yayi kuma ya lalatashi wajen wannan ginin wahala, baice komai ba yasa hannu a aljihu yaciro d’ari uku a aljihunsa ya miqa mata had’e da cewa, “kiyi hak’uri da wannan innarmu sukad’ai suka ragemun” karb’a tayi ta saka a hab’ar zane ta d’aure tana biye dashi har waje tace “ba laifi, ALLAH yayi albarka” “Amin innamu,” inna balkisu ce taqaraso wajen riqe da leda irin poly bag d’in nan tana murmushi “A’a malan Nuraddeeni fita za’ayi” tafad’a batare data kalli gefen da yaya hawwar takeba, cikin sakin fuska da girmamawa yace “Eh inna bilkisu fita zanyi in ALLAH ya yarda, ina wuni?” “Lafiya klw yaron kirki dama saqone ‘yan uwanka saleema da kareema suka aiko dashi sukace akawo maka ka k’ara a lefe.” Washe baki yayi yana kallon mahaifiyarsa tasa da tunda taga inna bilkisu taqaraso wajen ta d’auke kai ko zata juya, karb’ar ledar yayi tare da komawa cikin rumfar d’akin mahaifiyar tasa ya jawo tabarma had’e da zazzage kayan, cike da mamaki yace “Kai kai kai inna bilkisu kice hidima na d’orawa ‘yan uwana, wannan irin abun arziqi har ina, gaskiya nagode sosai wlh ALLAH yabar zumunci km yasaka masu da alkhairi.” “Amin ya rabbhi ai ba komai yiwa kaine, kadaici da haquri abunba yawa kasan d’iya mata ne basu san amshi ba saidai karb’a” murmushi yayi yana kallon mahaifiyar tasa da tabbas yasan maganace inna bilkisu tasakar mata amma hankalinta nawajen kallon kayan dasu kareema suka aiko dasu atamfa biyu sai sarqoqi kala biyar da jikkar ribon dozin biyu da kuma hulunan sawa masu kyau qwaya biyar, murmushi inna bilki tayi ganin yanda Yaya hawwa tasaki baki sannan ta sake fiddo da wasu bugaggin shaddodi irin wud’anda akeyiwa rini har guda biyu ta sake miqa masa tace, “Nima ga tawa gudun mawar aqarawa ‘yata dasu, ALLAH ya sanya alkhairi kuma yakauda idon maqiya.” Tana gama fad’a tajuya tayi tafiyarta don gurinta ya gama cika, damuwar da takeso tagani a fuskar Yaya hawwa da takaicin da take son tusa mata arai tagansu qarara kuma taji dad’i, STORY CONTINUES BELOW  Godiya ya dinga yimata yana fad’in ALLAH yabar zumunci kafin yajuyo wajen mahaifiyar tasa amma ga mamakinsa sai yaga tayi fuuuu..tabar wajen ranta ab’ace, kwashe kayan yayi yanufi wajen baffa dasu yana mai yabawa qoqarin ‘yan uwan nasa, sunyi masa abunda kaf dangi babu wanda yayi tunanin yimasa kuma yaji dad’i sosai, haka shima baffa cike da jin dad’i yayita sanya masu albarka, Yaya hawwa taci alwashin cewa koda ansa kayan alefen d’anta saita ciresu a gaban bilkisu tasa masu kalanzir ta qyasta ashana ta qonesu, ita ba ayi mahaluk’in daya isa ya nuna mata cewa ita da d’anta gajiyayyu bane balle ace za’a wani taimako masu har ayimata gori agabanta, ALLAH ALLAH ta dingayi gobe tayi kayan sudawo hannunta don tagwadawa inna bilkisu ita bata isa amma kash koda k’arfe 10 na safe yayi har baffa yasa ankira masa wani mak’wabcinsa dake da mota gwab irin ta haya d’innan yace da baffa Usman da kuma baffa Ali suje sukai kayan babu buqatar sai ankwashi ayarin mata guda anje kai lefe don d’ai d’orawa mutane hidima, duk yanda baffa Ali yaso zagayawa yazo ya sanar da yaya hawwa abun yacutara don baffa zaunar dashi yayi cikin d’akin yace karya kuru yatashi har sai angama kammala komai, baffa Usman shiya kwashe kayan yana kaiwa cikin mota yana dariyar yanda yaga baffa Ali na faman mutsu mutsu da qafafauwa yana son tashi amma baffa ya hanashi, bayan angama kaf baffa yaciro dubu goma aqarqashin katifar da yake kwance yaba baffa Ali yace idan sunkai lefen subayar asayi kayan wanka da ake kaiwa a al’adance. Kallon baffa Ali yayi had’e da cewa “tashi kutafi kuma wlh karka sake inga kanufi cikin gidannan ina kallonka babban kwabo kawai” Baice komai ba yamiqe yafita yana waiwayen cikin gida, ji yakeyi har wani cizonsa maganar keyi amma baffa ya kasa ya tsare ga kuma baffa Usman biye dashi yana gimtse dariyar dake cinsa, kamar yaro haka ya dinga kumbure fuska har suka bar qofar gidan, Hamdala baffa yayi kafin nan yatura yusufa daya hango zai shiga cikin gida yace yakirawo masa Yaya hawwa, da qunquni tashigo cikin d’akin tare dayin tsaye bakin qofa fuskarnan ba annuri ko kad’an saboda fushin da takeyi dashi akan abunda yayi mata tace “gani lafiya?” Shikam dariya ma tabashi ganin yanda take cika tana batsewa akan d’an qaramin abunda yafaru tun kwana biyu da suka wuce, to inata da wannan baisan mezai faruba shiyasa yace qara yafad’a mata da kansa da ace taji ga wani, wannan dalilinne ma yasa yahana baffa Ali komawa cikin gidan don yasan halinsa tsab zai iya qarawa wutar fetur, cikin tsokana yace, “Haba hawwa wannan irin cika da batsewa da kikeyi haka sai kace ba uwar ango ba, yihaquri zo muyi magana fushi ba naki bane kinji.” “Malan nifa inada aiki cikin gida inzaka fad’amun abunda zaka fad’a to kafad’a sauri nakeyi.” “To yihakuri kishigo mana.” Badon taso ba haka taqaraso cikin d’akin tayi masa tsaye qiqam akai, murmushi yayi sannan yace, “Dama zancen lefennan ne..” bai qarasa ba tace, “Sai akayi me, ai jiya munriga mungama magana da yarona baza’a kaishi yauba sai gobe don haka nima inada hakk’i da d’ana yau nakira ‘yan uwana abamu lefe suma sugani daga nan zamu fidda wud’anda zasuje kai kayan gobe in ALLAH yakaimu don wlh baza’aje da kowace shegiya acikin gidannan ba naji kana kawomun wasu kalan dangi ehe.” Baki bud’e baffa ke kallonta har ta dasa aya kafin yace, “ikon ALLAH, waike kam hawwa har yaushe zakiyi hankaline?, Meye amfanin maido da hannun agogo baya da kikeyi yanzu bayan da yardar ALLAH nasan lefennan da kike magana har yakusa isa inda yakamata, don ALLAH kidinga tunani kirege fitina domin in mune aduniya gobe bamu bane, mutuwa na tare damu akoda yaushe saboda haka muzama masu hak’uri..” bai rufe bakiba yaga tajuya da qarfi tana kallon inda aka ajiye akwatunan had’e da lailayo asshar ta tule saboda ganin wurin da tayi wayam shiya tabbatar mata da abunda yake fad’i gaskiya ne, dole yariga da yasan hakan saita faru don haka ya gyara qafafuwansa had’e da mik’esu yayi kwanciyarsa, Masifa tadinga zazzaga masa had’e da miyagun kalamai tana bubbuge abubuwan dake cikin d’akin tamkar wata mahaukaciya yayi tamakar baisan tanayi ba har tagaji don kanta tabari, amma yinin ranar mutanen gidan sunsha zagi manya da yara acewarta duka sunsan da zancen suka munafucceta, shi kuwa Nuraddeen da mahaifinsa sunsha tsiga da miyagun kalamai kala kala, Kai inkaji kace ba d’anta da mijinta take yiwa suba, yayi mata ranstuwa yana magiya akan baisan da baffa zaisa su baffa Usman suje kai lefen ba yafi aqirga amma fir taqi yarda, saboda tsoron fushinta har kuka yadinga yi yana roqonta Amma tace yafice mata daga d’aki Bata son ganinsa, itama saboda takaici da baqincikin rashin cikar muradinta har da k’walla tayi tana tsinewa yarinyar albarka.🤭🤣 STORY CONTINUES BELOW  ••• ••• ••• A can garin yarimawa kuwa tarba tamusamman baba da qanensa malan balarabe suka yiwa su baffa Usman, sosai sunji dad’in karramawar da aka yimasu don musamman baba balarabe yasa aka gyara masu kaji ga fura da nono mai sanyi sannan aka yimasu abinci da abunsha musamman, ko kad’an baffa Usman baiso tsayawaba bayan sun bada kayan amma malan balarabe yayita roqonsu dole ganin girmansa yasa suka haqura suka tsaya, sunci sun sha sunyi nak sannan su baba sukayi masu godiya, musamman baffa Ali da har saida yayo guzurin nama a aljihunsa don yaji dad’in bawa yaya hawwa labari, dubu uku malan balarabe yabasu yace susha mai ahanya angode sosai baffa Usman yace bazasu karb’a ba hakan kuwa ba qaramin b’atawa baffa Ali rai yayi ba don har yafara hango lalurorin da zaiyi da nasa kud’in idan anbashi, haka aka rabu cikin farinciki da murna tsakaninsu baffa Usman da iyayen Rashida kowanensu na yabawa karamcin da suke dashi. Duk da ba wasu kayane masu yawa ba ayanda ake qaryar lefe azamaninnan duk wanda yaga lefen sai ya yaba kyansu tare da qoqarinsaa matsayinsa na malami kuma mai matsakaicin k’arfi, *A gurguje* Acikin kwanakin da suka rage a d’aura auren Rashida da malan Idris abubuwa da dama sun faru musamman ta b’angarensa don kusan Yaya hawwa fidda hannuwantatayi a sha’anin auren Saida ‘yan uwa da abokanan arziqi aka had’u akayita bata haquri sannan ta haqura gaba d’aya gidan bata magana da kowa duk gaba takeyi dasu akan haka har lokacin da auren ya matso ana saura kwana biyu, babu wani shagali da akayi inba walima ba wacce itama ab’angarensu Rashida aka shiryata don sukam suna cikin farinciki sosai musamman iyayen Rashida da ita kanta, shima Nuraddeen ba’a barsa abaya ba amma idan yatunada matsalolin mahaifiyarsa duk sai yaji auren ya fice masa arai saboda tsoron abunda masoyiyar tasa zata fuskanta acikin gidan musamman wajen mahaifiyarsa da kuma baffa Ali, ko ranar da akazo jere yana jin irin walaqancin dasu muneera da baffa Ali sukayi masu banda inna balkisu da tazo ta jajirce wajen da ba qaramin kunya tasu akayi ba hakan yasa baffa yakirata ya damqa mata ragamar kula da mutanen amaryar da zasu zo har zuwa lokacin da za’a kammala shagalin, Anyi walima taji da gani don su baba balarabe sun taka rawar gani sosai kuma sunyi duk abunda yakamata ayi tun daga kan abubuwan ciye ciye dana lashe lashe, musamman aka yanka rago ranar walimar saboda had’ewa akayi haddata saukarta ta alqur’ani, malamai da dama sun halarci walimar sunyi nasihohi kalakala akan zamantakewar aure da kuma biyayya ga ALLAH da manzon tsira, baqar abayace mai kyau da tasha duwatsu ta ko ina jikinta da Kuma farar alkibba ta saka gashi tasha kwalliya had’e da lalle tayi kyau sosai kamar ba itaba, wani abu da zai qara burgeka ga walimar shine yanda malan Idris da abokanansa da sukayi zuwan bazata awajen walimar Jim kad’an da farawa yasha shaddarasa fara qal d’unkin riga da wando kaftani, nan take aka halarto masa da kujera kusa da inda Rashida ke zaune, wani irin farincikine ya lullub’eta a hankali tad’ago kai takallesa tayi murmushi shima yayi mata sannan tamaida kanta qasa, sosai iyayenta sukaji dad’in halartarsa wajen domin hakan yanuna masu irin muhimmancin da take dashi awajensa, nan aka cigaba da gabatar da nasihohin amarya da ango na saurare wasa wasa Rashida tafara jin gabanta nafad’uwa kafin can kuka ya kubce mata wanda ba sau d’aya aka saba ganin amare nayin hakan ba, anyi komai lafiya anqare batare da wata matsalaba kuma anyiwa amarya da ango fatan alkhairi tare da zaman lafiya da zuria masu albarka sannan kowa ya watse, yanda Rashida ke kuka sosai ba qaramin tab’awa malan Idris zuciya yayi ba don har saida yaso ya keb’e da ita don ya lallasheta amma kunya ta hanashi saidai akan hanyarsu ta komawa gida yakirata awaya ya lallasheta, Saida yaji tayi shiru tadena kukan sannan yakashe yana fad’in, “Sai gobe habibty idan nazo d’aurin aurenmu..” bai qarasa ba takashe wayar tana dariya don tasan wannan tsokanar da biyu yayita, dariyar shima yayi sannan yakashe wayar yanajin wani irin farinciki marar misaltuwa aransa… Bayan yakoma gida ya tarar da mahaifiyarsa nafad’a ita da inna bilkisu akan jagorancin da baffa yabata tayi mata tas had’e da cin mutunci kala kala, tun inna bilkisu nahaquri har taji bazata iyaba ta tanka mata sunata zubar da rashin arziqi kala kala, mutanen gida sunyi basu haquri har sun gaji amma sunqi su dena, kowacensu jitakeyi zuciyarta abaki tamkar ta kashe ‘yar uwarta, gashi baffa Usman bayanan shi kuma baffa baya iya tafiya balle yatashi ya tsawatar masu, yayi kiransu har yagaji amma babu wacce ta tanka masa balle yasaran zasu dena, ga ‘yan uwa da abokanan arziqi da sukazo bikin da mak’wabta duk sunyi cirko cirko suna kallon ikon ALLAH, abunda zaifi baka haushi ma yanda hatta ‘ya’yansu manya da yara duk suna wajen a tsaye, wani irin baqin cikine da damuwa suka taso masa waje d’aya suka turnuqe masa zuciya, ji yakeyi babu babbar damuwarsa aduniya yanzu irin wannan jarabawar da yake ciki kasancewar gashi da ransa ba mutuwa yayi ba amma yakasa iya dakatar da fitina acikin ahalinsu a lokacinda ‘yan uwansa basa gida, hawayene suka zubo masa daga cikin idanuwa ahankali ya rufesu yana karanto sunayen ALLAH, cikin ikon ALLAH kuwa yaji wani k’arfi da kuzari sunzo masa yafara jan gindi yana nema yasamu ko bakin qofane yakai wataqil ganin idanuwansa susa sudena, cikin azabar da shikad’ai yasan ko meyakeji ya iso bakin qofar d’akin jikinsa na rawa lumfashinsa na fita sama sama da qyar yabud’e baki yace, “Bilkisu” saiga Nuraddeen yashigo cikin hanzari saboda hayaniyar da yaji tana tashi, da sauri yayo kansa yana fad’in, “Baffa lafiya? Ya akayi kazo nan da kanka.” Cikin zubar hawaye ya d’ago kansa yana nuna masa tsakar gidan daya hango anyi dandazo ana sauraren fad’an inna bilkisu da Yaya hawwa ga mamakinsa kawai sai ya hango baffa Ali gefe zaunensa yana sharb’ar tuwo ita kuma matarsa agefe tana tintsirar dariya, baisan lokacin daya dafe saiti zuciyarsa yan bud’ar baki saboda lumfashinsa dake neman d’aukewa, kan Nuraddeen yayi wani yunqurin lumfashin baffa ya d’auke tare da langab’ewa daga jikinsa da yake, “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun” yafad’a da qarfi tare da fashewa da kuka yana girgizarsa yana fad’in, “baffa, baffa, baffa don ALLAH kada katafi kabarni.” Jin hakan ya maido hankalinsu bakin qofar d’akin da Nuraddeen ke rungume dashi, da gudu baffa Ali yayi kansa daidai lokacin shima baffa Usman yashigo gidan sargafe da kwashensa a kafad’a, jefar da ita yayi yanufi wajen d’an uwansa tare da jawosa ga jiki daga rungumen da yake ga Nuraddeen. Girgizas ya shigayi yana fad’in, “yaya, yaya” alokaci guda yana tattab’a tafin hannunsa, gefen wuyansa da kuma k’asan hancinsa inda lumfashi kefita, jin fitar iska kad’an daga hancin nasa ya tabbatar masa da cewa yanada sauran lumfashi ya kinkimesa yayi cikin d’aki dashi had’e da cewa Nuraddeen yakawo masa ruwa, dama tun a bakin gida da yaji hayniya nafitowa daga cikin gidan yatambayi Yusuf d’an baffa Ali abunda kefaru, jin da matarsa ake fad’an yasa yashigo ransa ab’ace sai gashi ya isko wannan tashin hankalin, muryar Nuraddeen daya dawo riqe da cup da ruwa yana fad’in, “baffa gasu.” Yasashi fitowa daga tunanin daya shiga, karb’ar ruwan yayi ya yayyafawa baffa a fuska har sau biyu amma bai farfad’oba, Yaya hawwa dake tsaye abakin qofar ita da suran mutanen gidan suka fashe da koke koke suna wayyo, a fusace baffa Usman yajuyo yace, “gaba d’ayanku kub’acemun da gani, kuma dake dake duk sai nayi qararku idan kuka sake yayana yamutu, shashashun mata kawai, ku b’acemun da gani” yaqarasa maganar cikin tsawa yana nunasu da yatsa idanuwansa sunyi jajur tamkar wanda aka zubawa yaji aciki, jiki ba qwari kowa yabar wajen tare da komawa cikin gida sukayi jigum jigum tamkar basu bane suka gama cacar baki ba yanzu. STORY CONTINUES BELOW  Sake d’ebo ruwan yayi ya sake shafawa baffasu har sau uku a fuska yana mai addu’a ALLAH yasa yafarfad’o, cikin ikon ALLAH sukaji yaja wani dogon lumfashi cikin dasashshiyar muryar da babu wanda kejinsa saidai sukaga bakin namotsi yana fad’in “hazbunallahu wani’imal wakeel” wani irin sanyi da farinciki baffa Usman yaji azuciyarsa ya runtse idanuwans a hawayen dake maqale suka zubo, ahankali yafara bud’e idanuwansa ya saukar dasu saman na baffa Usman dake hawaye ya riqo hannunsa, “Sannu Yaya” baffa Usman yafad’a yana murmushi kafin suma su Nuraddeen da baffa Ali suyi masa sannu fuskarsu cike da farincikin farfad’owar tasa, cikin rawar murya had’e da damuwa baffa Usman yace “Yaya bari naje wajen musa ya aro mana mota akaika asibiti” yana k’ok’arin d’agasa daga jikinsa ya kwantar dashi akan katifa, cikin muryar dake nuna yana jin jiki yace, “A’a Usman ba sai munje asibiti ba Alhamdulillah nasamu sauqi, amma Ina so don Allah Aliyu yafita daga d’akinnan bana son ganinsa yanzu, bantab’a tsammanin cewa duk wannan fitinar dake faruwa acikin gidannan ba yana ciki kuma koda fad’amun akayi wlh bazan yarda ba, amma sai gashi da idona nagansa zaune shida matarsa iyalinmu nafad’a anrasa wanda zai rabasu shida ita, wannan wace irin rayuwace haka ace d’an uwan bazai iya karewa ‘yan uwansa mutuncin suba, da ranmu kenan yayi haka inaga bama raye.” ‘bata rai yayi yana qunquni wai aishi baisan yanda zaice masu ba tunda duka matan yannens ne Amma anaso aga lifinsa, cike da takaici baffa Usman dake kallonsa yace, “Bakomai Aliyu duniya ce, idan mutum ya gyara kansa, idan kuma ma yab’ata kansa, rayuwa da kake gani batada tabbasa kuma shi zumunci ba wasa bane, don haka duk abunda kayi don kanka, mudai iya fatanmu da kai ALLAH yagyara maka halinka” juyowa yayi wajen baffa yaci gaba da cewa “ka k’yaleshi yaya indai duniyace ta ishesa riga da wando” mik’ewa yayi ransa ab’ace yabar d’akin yanaci gaba da qananan maganganunsa, baffa ya kalli Nuraddeen dake gefe idanuwansa sunyi jawir saboda b’acin rai da kuma kukan da yayi yace “Nuraddeen ya hidima?” Murmushin qarfin hali yayi masa sannan yace “Alhamdulillah baffa, ya jikin naka?” “Alhamdulillah Nuraddeen, ubangiji ALLAH yayi maka albarka ya albarkaci zuriar da zaku samu, gobene d’aurin auren ko?.” “Amin baffa, Amma don ALLAH a d’aga d’aurin aurennan har kasamu lafiya, kaga sai muje asibiti gobe adubaka tunda yanzu marece yayi sosai” “Hakane yaya, gaskiya yakamata muje asibiti, zamannan gida naga babu wani sauqi da ake samu abunma sai qara tsamari yake.” Baffa Usman yafad’a had’e da kawo mafici yana yimasa fiffita. “Kul! Usman kada in koma jin zancen d’aga auren nan yakoma fitowa daga bakinku da kai har Nuraddeen, wlh ko rasuwa nayi banyafe ad’aga d’aurin aurennan ba kunji nafad’a maku, lafiya da kuma rashinta duka daga ALLAH ne haka itama rayuwa da mutuwa duk ahannun ALLAH suke, aure kuma hukuntawarsa ce adaidai lokacin daya so, don haka ban lamunta ad’aga aurennan ba saboda rashin lafiyata, mutuwa da kuke gani bata hana komai aduniya balle rashin lafiya, don haka abar komai ynda aka tsarashi da yardar ALLAH Kuma zan samu sauqi kunji ko nafad’a maku?” “Eh Yaya” suka amsa masa atare kowane najin wani abu azuciyarsa. Sosai baffa yasaki jiki don ya nuna masu yaji sauqi sosai sukayita fira har bayan isha’i, amma cikin jikinsa shikad’ai yasan meke damunsa, duk wannan hali daya shiga Yaya hawwa bata koma tunanin koda leqa ta gefen da d’akin baffa yake ba balle taje tadubo sa saboda fad’an da baffa Usman yayi masu wanda hakan ba qaramin sake qonawa baffa rai yayi ba har yake tunin tabbas koda mutuwa yayi yasan hawwa bazata tab’a damuwa ba balle yasa ran zata tuna dashi tayi masa addu’a, hawayene suka gangaro masa a fuska yayi saurin gogewa don kada sugani, baffa Usman bai bar d’akin ba sai kusan qarfe d’aya na dare shi kuwa Nuraddeen kwancensa yayi wajen baffa sukaci gaba da firarsu wacce rabinta duk nasihace yakeyi masa akan rayuwar aure da kuma amana da hak’k’ok’an da ALLAH ya d’ora masa na matarsa, yayi mashi nasiha sosai akan muhimmancin hak’uri da iyali da kuma kyautata masu har aka kira sallar asuba, da kanshi ya riqasa sukaje baye yayo arwala sannan ya maidosa shikuma ya koma yayo tasa had’e da wucewa masallaci acan sukaci karo da baffa Usman shima ya zauna bayan anyi sallar asuba yayi masa nasiha sosai, bayan sun dawo ne masallaci lokacin rana tafito baffa Usman yasa aka kirawo masa yaya hawwa da bilkisu anan d’akin da baffa yake, Amma har matarsa bilkisu tazo Yaya hawwa nacan abunta zaune don cewa tayi baza tajeba saboda jiya agaban mutanen gida yara da manya ya wulaqantasu don haka Babu inda zataje tunda bashi ya ajiyeta ba. STORY CONTINUES BELOW  Sun jima suna jiran isowarta amma fiye da minti talatin babuta ba tsammani, hakan yasa baffa Usman ya maido hankalinsa ga bilkisu batare da yajira bayanin komai abakin taba yayi mata tas dama tun jiya da daddare yafara sauke fushinsa akanta yau kuma yasake d’orawa hak’uri tayi ta basa tana roqonsa gafara ya katsa mata tsawa had’e da cewa, “Kiyimun shuru ba wannan nake son ji daga bakinki ba, wlh daga yau nakoma jin kin tankawa yaya hawwa acikin gidannan sai ranki yayi mummunan b’aci don bazan lamunci garin shashanci irin naki kibiye mata kuna fitinar da zata haifarwa da d’an uwana matsala ba, daga yau duk abunda zatayi maki Ina so taci albarkacinsa matuqar ni inada muhimmancin agareki a matsayinsa na yayana.” “Shikenan zanyi yanda kace in Sha ALLAH, Yaya kai Kuma don ALLAH kayi hak’uri bisa damuwar da muka haifar maka da ita jiya” tafad’a tana goge hawayen jin d’acin hukuncin da maigidan nata ya yanke mata, taso ace yabarta takoyawa Yaya hawwa hankali idan ita mahaukaciyace amm dole tabar maganar ko don yiwa mijinta biyayya, girgiza kai baffa yayi don baiso baffa Usman yayi mata hakanba agabansa, yaso ace amtsayinsu na miji da mata sun kashe sun binne a d’aki amma sanin yanda zuciyar d’an uwan nasa take idan ransa ya b’aci yasa bai dakatar dashi ba, cikin taushin murya baffa yace, “Babu komai bilkisu, kiyi hak’uri kema nasan duk dalilin jagorncin dana azaki ga aurennan ya haifar maki da wannan fitinar awajen iyalina, don ALLAH kuci gaba da hak’uri da ita kunsan hali zanen dutsi, ubangiji ALLAH ya shiryeta kuma ya ganar da ita, Usman don ALLAH kada kasa bilkisu tacire hannunta awannan hidimar domin burinta aduniya bai wuce a kunyata a wannan al-amarin ba, don haka Ina baku haquri na yau d’ai kujurewa duk abunda zatayi har agama lafiya kaji ko?” yaqarasa maganar yana kallon baffa Usman da gaba d’aya yaso iyalinsa tafita harkar sha’anin auren saboda matsalolin hawwa, wata ajiyar zuciya ya sauke sannan ya kalli d’an uwan nasa yace “Duk abunda ka yanke Yaya shine daidai kuma dole ayisa ubangiji ALLAH ya kauda fitina kuma yasa agama taro lafiya.” “Amin ya rabbhi Usman nagode, ALLAH ya zaunar dakai lafiya da iyalinka kuma yanda kake kula dani tare da yimani biyayya kaima ALLAH yabaka mai yimaka haka, yanda ka kula da sha’anin Nuraddeen kaima ALLAH yakula maka dana dukkanin zuri’arka nagode nagode sosai..” yaqarasa maganar yana mai fashewa da kuka saboda tunanin abunda zai faru bayansa don shikad’ai yasan yanda yakeji acikin jikinsa, Abunda duk ALLAH yatsaro babu wani mai iya hanashi sannan ita matar mutum kabarinsa yau misalin qarfe biyu da rabi na rana masallacin juma’a na unguwar yarimawa yacika da tarin dan dazon mutane ‘yan kasuwa da malamai don sheda d’aurin auren MALAN NURADDEEN IDRIS ALIYU (MALAN IDRIS) da kuma amaryarsa RASHIDA BASHAR MAI TAKALMA, inda nahango baffa zaune agefe sai kuma baffa Usman tsaye agefensa yana gaggaisawa da mutane cikin farin yadinsu boyel d’unkin babbar riga sunyi matauqar kyau kai kace tagwayene kowanensu sai fara’a yakeyi saboda tsammanin cikar burinsu, haka baba da qanensa malan balarabe suma sunsha manyan rigunansu kalar ruwan omo iri d’aya fuskokinsu cike da annuri suna yiwa baqi masauki kafin isowar ango, Nuraddeen na hango tare da abokanansa sai wasar hauru yakeyi cikin had’ad’d’iyar shaddarsa milik suna tahowa shima d’unkin babbar rigane ajikinsa ya matuqar zauna masa had’e da yimasa kyau sosai wanda ko ba’a tambaya ba kasan cewa shine ango, suna qarasowa aka nuna masu masaukinsu acan gefen dake tsakanin iyayensa dana amarya limamin masallacin juma’ar yafara gabatar da sigar aure kamar yanda yazo a musulunce sannan aka gudanar da yarjejeniyar karb’arwa Nuraddeen auren Rashida daga hannun iyayenta bisa sadaki dubu hamsin laqadan ba ajalanba yayin da iyayenta suka damqawa nuradden amanar aurenta tahannun iyayensa bisa yarda da amincewar cewa zai kula da cinta, shanta, suturarta da kuma lafiyarta sannan aka tofa addu’a, wani murmushi baffa yasaki had’e da cewa, “Alhamdulillah, dama sannu sannu bata hana zuwa saidai adad’e ba akaiba, ubangiji ALLAH ka amintar da wud’annan bayi naka bisa dukkanin alkhairanka awannan rana da dukkanin ranakun da zasu biyo bayanta har iya qarshen rayuwarsu” baffa Usman dake gefensa ya amsa masa da “Amin Yaya” yana dariya, shikuwa gogan naka ana gama d’aura auren lumshe idanuwansa yayi yanajin wani irin farinciki na ratsa dukkanin sassan jikinsa da kuma rouhinsa, yajima ahaka kafin d’aya daga cikin abokanansa ya zunguresa suka bushe masa da dariya suna yimasa sheri. STORY CONTINUES BELOW  ••• ••• ••• Acan gida kuwa bebeji gaba d’aya anguwar mutanen arziqi suna wajen d’aurin auren Amma banda baffa Ali da tun jiya da yayi fushi akan maganar da baffa suka yimasa yasha alwashin ko d’aurin auren bazai jeba, Babu yanda baffa Usman baiyi dashi ba amma yace babu inda zaije tunda suka had’e masa kai suka nuna masa cewa shi bawani tsiya bane acikinsu, ganin lokaci na qurewa yasa ya ajiye masa kayan da suka d’unka su uku suka wuce cike da tsammanin cewa zai biyosu abaya, Amma ga mamakinsu har aka gama d’aurin auren bai jeba wanda hakanma yasake tab’a zuciyar baffa sosai ganin cewa idan baya raye sukad’aine zasu iya karb’arwa ‘ya’yansa aure amma ace yaqi halartar auren d’an nasa, awannan karonma sake danne damuwarsa yayi saboda gudun haifarwa da d’ayan d’an uwan nasa damuwa. Bilkisu ma sake zage damtse tayi cike da farinciki tamkar wani abun bai tab’a faruwa ba jiya tayi duk abunda yakamata, duk wasu baqi da zasuzo kai tsaye Yaya hawwa kace masu suje wajen qirjin biki wato kinfi uwar ango bilkisu don ta tozartata amma ita hakan ko ajikinta don baffa Usman yabata isasahin kud’i tayi abinci ita da ‘ya’yanta su kareema da sukazo, koda suka jewa Yaya hawwa yimata fatan alkhairi ko kallon banza basu isheta ba balle ta tankasu suka juyowarsu batare da sun damu ba don dama saida bilkisu taja masu kunne kafin sutafi, baffa Ali kuwa shida matarsa bini bini sun fito tsakar gida ko kunyar mutane basaji sun yadawa bilkisu magana au da Yaya hawwa itako tayi kamar bata masan sunayi ba. Kasancewar akwai ‘yar tazara tsakanin garuruwan guda biyu wato qauyen yarimawa da kuma bebeji yasa su baffa suka roqi alfarmar abasu amaryarsu suwuce da ita don tuni suka zo da motocinsu k’waya biyar da za’a d’aukar amaryar, ko kad’an baba bazasu iya yimasu musu b saboda tsananin girmama juna da sukeyi don haka sukace abasu mintuna ashirin za’a fito da amaryar su baffa nata godiya tare da yaba karamcin da suka yimasu… *_ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭_* [7/1, 11:24 AM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___19💎 Cike gidan yake maqil da ‘yan uwa da abokanan arzik’i na nesa dana kusa da suka zo taya umma da baba murnar aurar da ‘yar tasu tilo, duk wanda ka kalla awajen kasan cewa cike yake da tsantsar farinciki saboda yanda fuskokinsu ke d’auke da annuri anata gudanar da buki wan shagali. Fuskar baba cike da fara’a ya shiga cikin gidan bakinsa d’auke da sallama yana rarrab’awa ta gefe gefe saboda yanda gidan yacika maiqil da ‘yan buki sai faman shiga raha akeyi wasu na shiga wasu nafita, duk inda yabi sai faman gaishesa akeyi ana tayashi murna tare da ALLAH sanya alkhairi, da qyar ya samu ya shiga ciki had’e da nufar wani d’aki da suke ajiye kayayyaki aciki yasa wata tobashiyarsa ta kirawo masa umma dake can tsakar gida tasha adonta cikin wani had’ad’d’en leshi wanda saika duba da kyau zaka iya gane itace, yajima zaune cikin d’akin yana tunanin shikenan yau zai rabu da ‘yarsa tilo da yakeji har cikin qoqon ransa kafin umma tasamu takuccikke daga baqin dake dad’a shigowa tanufo inda take, a jigace tashigo cikin d’akin tana fad’in, “ai sai kuyi babu wanda zan sake d’ebowa abinci in zaku tashi kuje kud’ebo da kanku ku tashi, ai Kuma ‘yar takuce bani kad’ai nahaifeta ba balle kubarni da aiki, don haka ni nagaji bazan qara yimaku wani abunba, shikenan daga kara saiku barni da aiki.” Murmushi baba yayi yana kallon fuskarta sannan yace, “haba uwar amarya, wannan irin fad’a haka da kikeyi halan keda wa.” “Nida matan balarabe mana, su daya dace ace suke tarbar baqi suna kai masu abinci shine sunka koma gefe kowace ta hakince sai kace tukane suna kiran akawowa wance da wance abinci, sun barni ni kad’ai ke hidimata sai kuma fareeda ‘yar wajen yaya maryama.” STORY CONTINUES BELOW  “A’a’a to wannan maganar tafi qarfina tsakaninki ne da qannenki ba Mai shiga tsakani, ni dama zancen kai amarya ne yakawoni kinga gari ba guda ba..” kafin yaqarasa tayi saurin cewa, “To ai sai anyi sallar la’asar za’aje ko kuwa?” “A’a, bayin ALLAHn nan sun roqi alfarmar abasu amaryarsu su wuce da ita don gaba d’aya suka zo d’aurin auren tare da motocin d’aukar amarya, don haka kishiryata in sha ALLAH yanzu zasu wuce da abussu” “Amma malan bamuga ‘yan biko ba haka zamu miqa masu ita kamar…” “Haba maman Rashida kada kice komai da yanzun da anjima duka d’aya ne, kuma shi biko ai al’adace ba addini ba don haka kiyi hak’uri tunda har iyayensa maza sukayi magana tamkar sun turo bikon ne, aje ashiryota gamunan muna jiranta muyi mata hud’u ba sai suwuce.” Jiki a sanyaye umma tafita tamkar wacce k’wai ya macewa a ciki, duk tsawon kwanakinna bata tab’a d’aukar cewa tabbas zata rabu da ‘yar tata ba sai yanzu, cikin k’arfin hali tanufi d’akin da Rashida ke ciki kwance tana kuka bayan andawo da ita wajen wanka ita da ‘ya’yan malan balarabe qanen mahaifinta su uku, sunyi lallashi har sun gaji sun qyaleta suna ganin umma tashigo duk suka mik’e suka fita, dai dai wajen kanta umma taje ta zauna tare dasa hannuwa ta d’ago kanta, cikin kuka tafad’a ajikinta tana sheshheka, ko kad’an umma ba tayi yunqurin hanata ba domin itama kanta kukan ne yazo mata, saida sukayi mai isarsu sannan cikin muryar dattako umma tafara yimata magana har lokacin tana jikinta. “Rashida kuka bai kamaceki ba, domin wannan ranar farinciki ce agareki da kuma mu iyayenki da Allah yabamu ikon ganin mun sauke d’aya daga cikin haqqoqanki daya d’ora mana kuma ranace da kika dad’e kina jiran zuwanta don haka kinatsu ki saurari abunda zan fad’a maki amatsayina na mahaifiyarki.” Share hawayen da suka sake zubo mata tayi sannan tasa hannuwanta ta tallafo fuskarta tana share mata qwalla had’e da cewa. “Rashida! Ina so kibud’e kunnuwanki kiji abunda zan fad’a, gidan aure da kike gani ba wajen zaunawa kace zaka huta bane ko kace kayisane don kasuwanci, wajene na gwaggar maya don meman lada da kuma aljannarki, shi gidan miji wajene da zaki jajirce wajen nunawa duniya nagartar gidanku da kuma ahalinki, duk wata kima da darajarki annan ne zaki tabbatar da ita ta hanyar nuna kamalarki ga ahalinda zaki riska ku zauna dasu, mijinki shine aljannarki kuma shine farincikin ki na duniya da lahira, haquri da kike gani shi ginshiqine na tabbatuwarki isashshiyar mace awajen mijinki, shi kuma ladabi da biyayya sune zasu zamo maki tubalin da zai mai dake kasaitacciyar mace awajen mijinki, girmama iyayensa abune da zai qara maki kwarjina da tarin soyayya azuciyar maigidanki, kauda kai kuma da iya dad’ad’an lafuzza ga ‘yan uwansa shi zaisa su soki har su zauna dake lafiya, kwanciyar hankalin da zaki bawa mijinki ita kuma jigoce ta yalwatuwar arziqinsa, kyautatawa da yin alkhairi ga mutane shizai jawo maki girmamawa ga manya da yaran da kike tare dasu, kiriqe ALLAH, ki guji abun hannunki, kibi mijinki kiyiwa mahaifiyarsa biyayya tamkar yanda kike yimani ga duk abunda bai sab’awa ALLAH ba, rashin kunya, tsiwa da sakin baki acikin mutane sukan xubarwa da mutum kima da daraja don haka ki nisancesu, Ina mai roqonki da duk k’arfin tsanani da wahala kada kid’aga harshenki akan na mijinki, idan son samune kada ki zalinci kowa kibari ke azalinceki da SANNU SANNU ALLAH zai yi maki sakayya, shi khairan da sharran duka ‘yan aikene duk inda ka aikesu za suje kuma su dawo maka, kiyi k’ok’ari kishuka alkhairi don ki girbesa, kizama mai haquri da juriya sannan kizauna da kowa lafiya, kiriqi tsafta nasan kinada ita amma ki qara haka girki shima duk da bani da wani haufi akai amma ki kula sosai wajen kiyaye lokacin yinsa da wajen dafasa, banda almubazzaranci ko rashin yiwa miji godiya ga duk abunda yakawo, kiriqi addu’a da azkar na safiya da marece da lokacin kwanciya insha ALLAH zasu zamo maki fitila arayuwarki, ki guji fushin mijinki, ki nesanta da duk abubuwan da kikasan baya so ta hakanne zaki samu cikakkiyar natsuwa a gidan aurenki, Ina roqon ubangiji da yayi maki albarka, yakare mani ke aduk inda kika shiga ga sharrin mutum dana aljani, ALLAH ya albarkaci dukkanin zuri’ar da zaki samu ya kareki daga fad’awa ko wace irin fitinar rayuwa ta duniya da kuma lahira.” STORY CONTINUES BELOW  Duk da Rashida nacikin damuwar rabuwa da iyayenta hakan bai hanata jin dad’in lafuzzan mahaifiyarta ba agareta, gaba d’aya zuciyarta da kuma qwaqwalwarta sun gamsu da nasihohin data yimata kuma tayi alqawarin zatayi aiki dasu komai rintsi komai wuya, cikin sheshhekar kuka tace, “Amin ummata, zan kula da duk abubuwan da kika fad’a mun kuma nayi maki alqawarin zamowa mai tsananin haquri da yiwa mijinta biyayya tamkar yanda naga kinayi.” Rungumeta umma tayi tana murmushi had’e d cewa, “A’a Rashida, bana so kiyi yanda kikaga inayi nafiso kiyisu fiye da yanda nakeyi kinji ko?.” Cikin kuka tace, “In sha ALLAH, ummata zanyi, don ALLAH kiyafemun duk wani abu Dana yimaki, ummata Ina matuqar jin kewar rubuwa dake.” Taqarashe maganar tare da naniqeta ajiki tamkar zata tsagata ta shige tana mai k’ara tsananta kukanta, “Rashida kenan! wake maganar yafiya anan bayan ummanki cike take da soyayyarki da kuma alfaharin samunki taya har za’ayi kiyi wani laifi kome qanqantarsa agareta kuma har yasamu muhalli acikin zuciyata?, Babu komai tsakanina dake face tarin d’inbin albarka da nake yimaki fata awajen ALLAH” cireta tayi daga jikinta sannan tamik’e taci gaba da cewa, “kije kishirya Rashida mahaifanki na jiranki a d’akin kaya kinji ko?.” Tana gama fad’ar haka tajuya tafice daga d’akin, wajen qanwarta aunty marwiyya tanufa tayi mata magana akunne sannan tawuce wajen bak’in da suka shigo yanzu, da sauri ita kuma aunty marwiyya tashiga d’akin da Rashida take tasa ta tashi tashiga toilet tayo wanka da ruwan turarukka masu qamshi sannan tasa ta tsuguna saman turaren wutan da tana fitowa ta isko tahad’a mata, bayan yagama shiga jikinta tabata wani had’in madara daya sha kayan gyaran ni’imar jiki tace tashanye sannan tahau kimtsata yanda ya kamata, ba’afi mintuna ishirin ba sai gashi tafito da ita cikin had’ad’d’iyar shiga mai kyau da kuma d’aukar hankali, duk inda Rashida ta gotta sai zuba qamshi takeyi fuskarta a lullub’e, daidai lokacin malan balarabe yashigo cikin gidan yana fad’an afito da amarya anbar mutane zaune suna jira, ganinta yasa yayi shiru tare da nufar d’akin da d’an uwan nasa ke ciki suna jira, acan aunty marwiyya tanufa da ita suka shiga kan Rashida naqasa har lokacin tana zubar da k’walla, Saida ta duqar da ita agabansu sannan ita kuma tajuya tabar d’akin, naseeha sosai suma suka yimata sannan suka aika aka kirawo umma itama ta sake yimata wata sama sama, rungume baba tayi tana kuka mai tsima rai tare da roqonsa gafara nan take shima yaji kukan na nema ya kucce masa, da sauri yamiqe yana fad’in “nayafe maki Rashida ALLAH yayi maki albarka” ya fice daga gidan yana goge hawayen da suka zomasa, wajen umma tanufo ta sake rungumeta tana kuka umma ta dafa kanta had’e da cewa, “Kitafi gidanki cikin amincin ALLAH da kuma yardarsa Rashida, ALLAH ya albarkaci rayuwarki yakareki ga dukkanin sharrin shaid’an da kuma ahalinsa” tana gama fad’a itama tajuya tayi cikin gida tana hawaye. Aunty marwiyya ce tazo tarik’ata sai kuma yaya Maryam (yayarsu baba) dama tuni ansanar da ‘yan bukin duk mai halin zuwa kai amarya ya gyara yanzu za’a kaita ba sai anjima ba kamar yanda aka tanada, Kai tsaye aka fiti da Rashida tana reren kuka yayinda suna isa bakin gida suka tarar da motar da aka tanada don amarya har anbud’e ana jiran isowarta, aunty marwiyya ta duqar da ita tana mai rad’a mata akunne cewa ta tashiga da _”Bismillah tawakkaltu alallah wala haula wala quwwata illah billah”_ Cikin zuciya tadinga karantota duk da kuwa kukan da takeyi na nema ya rinjayi zuciyar tata sannan sukuma sauran mutane suka shiga sauran motocin aka tayar, dama mota biyarce aka kawo takai amarya sai motarsu baffa sukuma tuni ana fitowa da ita sukayi musabaha da malan balarabe da kuma baba had’e da yin godiya suka wuce gaba, saida mota biyu tashiga gaba bayan tasu baffa sannan wadda rashida keciki tabi bayansu sannan biyun suka bi bayanta suma, wani irin kuka mai tsimarai Rashida keyi tana nazarin kalmar da akoda yaushe take d’auka mai sauqi wajen furtawa (aure nake so) wacce gaba d’aya bata natsu wajen fahimtar kome take nufi ba sai yanzu da aka rabata da iyayenta, tabbas tana farincikin samun muradinta da kuma auren amma rabuwa da iyayenta gaba d’aya ya shamakance ta da bayyana wannan farinciki, tafiya mai d’an nisa sukayi kafin su isa garin bebeji lokacin har anfara kiraye kirayen sallar magrib amma koda suka isa dandazon yaran shiyar dake qofar gidan suna ihun ga amarya bazai bari kaji sautin kiran da akeyi ba, motar da take ciki na tsayawa gabanta ya fad’i da sauri tafad’a jikin aunty marwiyya tana kuka, STORY CONTINUES BELOW  “A’a Rashida wai kukannan naki bazai qare bane? Yakamata kiyi hak’uri haka domin duk wata d’iya mace dake gidan mijinta saida ta fuskanci hakan.” A hankali ta tsagaita kukan sannan yaya maryam tarik’ota tafito daga cikin motar tana fad’in kiyi addu’ah _”hazbunallahu wani’imal wakeel”_ Rashida tafad’a acikin zuciyarta kafin ta azo qafarta tafito daga cikin motar fuskarta a lullub’e, ihu yara suka hau suna fad’in, “yeeee.. amarya, amarya, ke kicce kinaso da bakice kina so ba da ba’a baki shiba.” ahankali suke tafiya da ita tamkar k’wai har sukazo bikin k’ofar shiga gidan, qafarta ta dama ta aza tana karanto addu’ar ” _”Allahummah inna naj’aluka fi nuhirihim, wana uzu bika min shururihim”_ ma’ana (ya ALLAH! mu muna sanya ka a gabansu, kuma mina neman tsarinka daga sharace sharracensu.) sosai taji tasamu ‘yar natsuwa daga ynayin da takeji suka shiga da ita, cike da farin ciki Yaya balkisu ta tarbesu hannu biyu ita da sauran ‘yan uwa dasu kareema ‘ya’yanta suna “sassannuku da zuwa, ku wucikke, masha ALLAH, kuwucikke da ita nan.” Ana nuna masu shiyarta wacce koba tambaya kasan b’angaren amarya ne, suna tsaye kafin su shiga suka jiyo muryar matar baffa Ali tna fad’in, “To mudai gidannan bamu da bare sai yanzu, ALLAH kasa ba’a d’ebo mana miyagun dangi ba..” kafin wasunsu su ankara da abunda tace inna bilkisu tace dasu “kuwucikke mana kun bar mana amarya tsaye kada qafafuwanta suyi ciwo.” Murmushi aunty marwiyya tayi had’e da cewa “A’a muna jiran agwada mana sashen uwar mijin tatace mukaita wajenta tukuna.” “Ahaf illar bare kenan komai nasa daban yake, To mudai ba haka mukeyi ba anamu al-adar, kufara shiga da ita d’akinta tukuna sai tafito da kanta tagano d’akin uwar mijin nata donmu auna hankalinta, mu haka mukeyi inyaso ku kwa jirata anan har tafito” suka sake jin matar baffa Ali dake can bakin k’ofar d’akinta zaune saman wata kujera tafad’a tana tamnar cingwam, cikin sakin fuska Yaya Maryam tajuyo had’e da cewa. “To kuyi hak’uri tunda har bare nada wata illa Kuma ahaka kuka gani kukace kuna so, kuma mu al’adarmu zamubi ba taku ba tunda bare muke.” Wani irin dad’i inna bilkisu taji da amsar da Yaya maryam taba matar baffa Ali kafin tace dasu “kuwucikke ga shiyarta can” tana murmushi ta wuce gaba suka bi bayanta, sallama sukayi Yaya hawwa nakwance saman gadonta d’an bono tana jinsu fiye da minti biyu Amma bata msa ba balle ta taso hakan yasa inna bilkisu leqawa taciki tana fad’in. “Assalamu alaikum Yaya hawwa ga bak’i nan sun iso.” Tana qoqarin shiga ciki, wata irin tsawa Yaya hawwa ta dakawa inna bilkisu da tasa saida Rashida tazabura had’e da rik’e Yaya Maryam tana fad’in, “Kul! kada wanda ya sake ya shigomun d’aki, bak’i ai nakine don haka kiyi qoqari ki karramasu ki zame mata uwar miji hakan zaisa nasan cewa ked’in ‘yar kanzagice lamba d’aya.” Shiru bilkisu tayi tanaji kamar ta zubar da kwallah saboda walaqancin da yaya hawwa tayi mata agaban mutane gashi tayi alqawarin bazata sake kula ta kanta ba balle tamayar mata da magana daidai yanda tayi mata, murmushin dake cike da takaici tayi tare da juyowa tana kallon ‘yan kawo amarya da sukayi cirko cirko suna sauraren ikon ALLAH, cikin qarfin hali tace, “Kuyi hak’uri kuzo muje akaita d’akinta ga motocican suna jiranku naji sunata faman yimaku oda” taqarasa maganar tare da juyawa tana qoqarin b’oye damuwarta. Adai dai bakin k’ofar shiga sashen Rashida inna bilkisu ta tsaya, sunaji matar kawo Ali ta tintsire da dariya tana fad’in “Yaya hawwa tayi tsiyar kenan ko bilki.” Had’e da tuntsirewa da wata dariyar, gab d’ayansu babu wanda ya tankata suka wuce ciki bakin Rashida d’auke da addu’a jikinta har wani rawa yakeyi sannan tashiga haka lokacin da zata shiga d’akinta har ta aza qafa aunty marwiyya tadawo da ita baya had’e da aza qafarta ta dama tace, “kiyi bisimillah da ayatul kursiyu, sannan ki karanta _allahummak finihim bima shi’ita_ (ya ALLAH ka isar mani su da abinda kaso) don wannan gida da kike gani sai kinyi hak’uri, baiwar ALLAH nan kad’aice nagani da alamaun mutunci.” STORY CONTINUES BELOW  “Marwiyya menene haka!” Yaya Maryam tafad’a tana kallonta, “Hmm Yaya Maryam kenan! Wlh tunanin abunda zan barwa yrinyarnan yasa nakasa tankawa da wllh tundaga waccan angulun har uwar mijin tata saina yimasu wankin babban bargo.” “Ya isa haka marwiyya ALLAH yakyauta.” Lokacin Rashida tagama addu’arta sannan suka shiga, nan kallo yakoma cikin d’akin don ba qaramin k’ok’ari baba yayi ba, hatta tv da vedio da fridge duk saida yasa aka sakawa Rashida, komai yayi kyau gwanin burgewa, nasiha suka sake yimata da tayi taka tsantsan da sha’anin mijinta da kuma duk wani abu da zai had’ata da mutanen gidan don kaucewa rashin mutunci sannan sukace tarik’e inna bilkisu hannu biyu ta d’auka ‘yar uwarta ce da zata dinga magance matsalolinta kafinsu don sun yaba da halinta, daidai lokacin inna bilkisu tashigo sashen ita da ‘ya’yanta salame da kareema d’auke da ledojin ruwa dana muhallip da kuma wani kwali babba dake cike da tarkacen biskit da mintuna da cingwam wanda bafffane ya aiko dasu yace abawa ‘yan kawo amarya, sake gaggaisawa akayi ta sake basu hak’uri bisa abunda yafaru sannan ta basu kayan, cikin jin dad’i sukayi godiya sannan yaya maryam tace. “To bilkisu ga amanar Rashida nan mun baki, duniya da lahira mun amince kiyi mata hukunci daidai yanda kike yiaw ‘ya’yanki idan tayi ba daidai ba, mun baki amanarta ki kula da ita batada kowa saike don ke muka sani yanzu, Rashida qaramar yarinya ce da hankalinta bai isa banbance daidai da rashinsa ba don haka kiyi mana taimakon d’orata akan hanya aduk lokacin data kauce, mungode mungode sosai, ALLAH yasaka maki da alkhairi kuma yabaku haqurin zama.” “Amin nagode nima, karku damu da abunda yafaru sharrin shed’annne kunsan halinsa la’ananne ne, dukkaninmu abu d’aya muke kuma in sha ALLAH zamu kula maku da amanar Rashida domin itama ‘yar muce.” Sosai su aunty marwiyya sukaji dad’in kalamanta kuma sun samu ‘yar natsuwa akan d’azu, mik’ewa sukayi da zimmar fita don tuni sauran mutane da yaran sunfita sukad’ai ake jira Rashida tarik’esu tanata kuka, duk qarfin zukatansu suma saida suka zubar da kwallah saboda tausayinta, so suke sutafi amma tariqesu gam saida su kareema sukazo suka b’anb’areta ajikinsu sannan, riqeta sukayi suna lallashinta su kuma suka wuce inna bilkisu na biye dasu kowacensu na k’walla, Suna fitowa matar baffa Ali ta toshe hanci had’e da rangad’a uwar gud’a tana fad’in, “wayyo duniya budurwar wawa, wai iyayen amarya da kuka wannan ai anyi abun kunya, koda yake qila amaryar tasu ta gagara yi abunka da yaran zamani shine su suka yimata.” Wucewarsu sukayi suna tir da halin fitinanniyar mat irinta inna balkisu nata basu hak’uri har bakin k’ofar gida, sunaji tana fad’in. “Munafucci dodo akan wasu yake qarewa” Wanda bako shakka sunsan da inna balkisun take… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/3, 11:01 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___20💎 Bayan sun tafi Inna bilkisu tadawo tare da tsayawa tsakar gidan saitin da matar baffa Ali ke zaune ta rangad’a wata uwar gud’a tana fad’in. “Alhamdulillah ALLAH kaine abun godiya, ita dai hassada ga mai rabo takice kuma duk hassadar mai hasada bai isa ya canza abunda ALLAH ya qaddaro ba sannan shi son kai baya tab’a kai mutum ga nasara, sannan kuma tabbas shi naka sai naka amma dad’in zama sai bare, yarinya dai tashigo gidan mijinta kuma ko ba’aso dole akirata da matar Nuraddeen, uwar gidansa kuma uwar ‘ya’yansa suruka a wannan gida, masu had’e had’e da kuma qulle qulle sai su canza dabara domin ruwa kam ya riga daya qarewa d’an kada..sai ayi sauri acanza dabara, yarinya dai ALLAH ya mallaka mata Nuraddeen a matsayin miji domin shi tariqe tun farko kuma shi zai tayata fad’a su ko ‘yan baqinciki sai dai su mutu don nagaba yariga da yayi gaba.” STORY CONTINUES BELOW  Tana gama fad’ar haka tawuce d’akinta tana jin wani sanyi aranta, koba komai tasamu zuciyarta ta rege nauyin da tayi mata akan maganganun da suka ta cab’a mata ita da Yaya hawwa. Wani irin mugun ashar matar Baffa Ali ta lailayo mata had’e dayin kukan kura tanufi wajen qofar d’akinta tana rafkar mata gambu. “Bilki, Bilki, Bilki tsakanina da ALLAH tun wuri ki kama kanki ko in tata maki rashin mutunci, ki kama bakinki kafin inyi maki wankin babban bargo agidannan, yo da kike zancen ruwa ya qarewa d’an kada ai bakiga k’arshen wasan ba, in dai nice ruqayya matar Ali gadanga tunda kika shigarmun hanci wlh saina nasa zaman gidannan ya gagare ki dake har ‘yar koron taki da aka kawo, kwad’a yayyiyar banza da wofi anga yarinya masu maiqo shine za’a maqale mata, to daga ke har ita sai nasa kun kuka da kanku.” Tana gama fad’a ta banka gambun qofar da qarfi cike da jin haushin rashin tanka mata da batayi ba tajuya tabar wajen, Yaya hawwa najinsu daga kwancen da take taja tsaki had’e da cewa. “Sakarkarin banza duk kuyi ku gama zan dawo takanku, don da d’ai d’ai zanyi maganinku acikin gidannan.” Ita dai Rashida tun tana kukan har ta dangana ga ALLAH tayi kwancen tana tunanin wannan sabuwar rayuwar da zata fara a d’aya b’angaren tana sauraren firar dasu salame da kareema keyi, muneera ce tafad’o cikin d’akin ko sallama babu tayi tsaye qiqam tana raba idanuwa batare da takalli wud’anda ke wajen ba da alama itama rashin mutuncin tazoyi saboda yanda take bud’ar hanta, sudai su salame na kallonta basuce da ita uffanba ta rab’a tagefensu tanufi uwar d’akin, kallon kareema salame tayi ta d’auke fuskarta tana kallon muneera dake qoqarin hankad’a labulen ta d’aure fuska had’e da cewa, “Ke malama Ina zuwa?” Juyowa tayi cikin ba’acin rai itama had’e da cewa “to sa’idanawa masu barci da ido d’aya Ina ruwanku da inda zani, Ina dai amaryar nan ba ‘yar uwarku bace balle kuce zaku hanani shiga” “Bashi aka tambayeki malama ba, amsa zaki bamu ba rashin kunya ba don kinsan nan gidanta kika zo” kareema tafad’a a tsattsaye, tsaki muneera tayi had’e da kutsawa tashiga cikin d’akin Rashida na kwance saman gado fuskarta lullub’e da mayafin da aka rufo mata tasa hannu ta yayeshi da qarfi, da sauri Rashida tamiqe zaune tana kallon muneera dake riqe da mayafinta data cire, idanuwa muneera ta qura mata tana kallon gashin kanta daya zubo har gadon bayanta sanadiyar jawo mayafin da tayi ribon d’in ya cire, kyakkyawar fuskarta ta qurawa Ida kafin can kamar an tsunkureta ta zabura had’e da cewa, “Au yihakuri fa na manta ke amarya ce Saida lallab’awa..” mere baki tayi sannan tafara takawa tana qarewa d’akin kallo kafin ta maido hankalinta gareta, “Dama kece ya nurana keso? kece ya zab’o a matsayin mata bayan yasan Ina qaunarsa, dama kece kika zamo katangar data shiga tsakanina dashi Kuma har kika datsemun duk wani mafarki da kuma burin mallakarsa dana dad’e inayi, kika wargazamun farinciki tare da sani zubar da k’wallah acikin kowane dare?, Hmmm to kinyi kuskure yarinya a wud’annan qananan shekarun naki baki kai matsayin da zaki mallaki ya nura naba kuma na hak’ura, domin na d’au alwashin shid’in mallakina ne ni kad’ai, kid’auka wannan auren jeka nayi kane kukayi saboda dole kirabu dashi ko kina so ko bakyaso, mallakina ne shi Kuma ki kalleni da kyau kigani nice daidai shi saboda nid’in ‘yar uwar sace kuma jininsa don haka d’an uwa sai d’an uwa badai bare ba.”+ Taqarasa maganar tana wani kallon sama da qasa irin ita wayayyiyar nan , sai alokacin Rashida ta d’ago kai cikin mamaki tana qarewa muneera kallo wacce tun shigowarta data kalleta ta aza itama cikin matan gidanne saboda yanda taganta ajeme cikin wata kod’ad’diyar atamfa wacce duk da itama a qauye take bazata iya ko gugar leda da ita ba, sak kamar muneera irinta ‘yan matan qauyennan ne da suka jima basuyi aure ba ga wasu uban qassan wuya da suka taso mata fuska cike da jar foda, kallo d’aya zakayi mata kasan cewa ba yarinya bace zata kai shekaru 20 aduniya ga matsalar qauyanci da rashin wayewa da suka taru suka sake jemeta waje d’aya sai kace wacce tashekara aru aru d’in nan, watanni ne tsakaninta dasu kareema wanda hakanne yasa babu wata girmamawa tsakaninta dasu sai reni, shiyasa da sukayi mata magana bata sauraresu ba hakan yasa salame tamiqe taje d’akinsu ta d’auki wayarta takirawo Nuraddeen ta sanar dashi abunda ke faruwa dama yana bakin gida baiyi nisa ba sai gashi ya shigo da sauri, yana shiga kareema na qoqarin shiga uwar d’akin saboda yanda taji tana yab’a mata maganganu da sauri yariqo hannunta yace tawuce, abakin qofar shigowa taci karo da salame tadawo zata shiga tariqe hannunta tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Muje salame ai yayan yadawo, barta dashi.” Wucewarsu d’akin mahaifiyarsa da tagama had’a masu ‘yan abubuwan da zata basu tana fad’a suzo suwuce gidajen mazansu dare yayi don har ankira sallar isha’i, nan suka fara bata labarin abunda kefaruwa tace. “Hmm! ALLAH dai ya kyauta, Amma ni wlh har yarinyar nan tafara bani tausayi, koni nan dana girmeta nesa ba kusa ba ya naqare da matsalar Yaya hawwa da ruqayya da kuma rashin kunyar yaransu inba Nuraddeen da Yusuf ba, sukad’aine nake jin sanyinsu amma kaf gidannan babu wanda keda ragi, sudai iyaye kishi suke dani gashi kowacenmu da mijinta balle ace ai saboda haka, sukuma yaran iyayen ke lalatasu shiyasa Amma banda haka har ina za’ace muneera ta isko matar yayanta tana yimata rashin kunya, zumuncine da yariga ya lalace saidai ALLAH ya kyauta.” “Hakane inna, amma kema da alifinki? Kidena biye masu balle shiga harkarsu, inaji d’azu kin dawo kina maidawa Inna ruqayya da maganganu ai kinga hakan bai dace ba, ka kyale mutum duk abunda zaiyi tunda dai kasan adoke bai isa ya dokeka ba amma saikiyita biye masu ana fitina.” Kareema tafad’a ranta a d’an b’ace, shiru Inna Bilkisu tayi tana nazarin kalamanta don tasan gaskiyane tafad’a kawai dai abun da ciwone shiyasa bazaka iya haquraba wataran, muryar salame taji itama tana fad’ar. “Eh Inna ALLAH gaskiya kareema tafad’a don ALLAH kidena biye masu, kinsan abun fad’i agarinnan baya k’arewa, kuma mu kece mutuncinmu da kimarmu agidajenmu, da wani abun yafaru agidannan akaji dasa bakinki ba zamuji dad’i ba, don ALLAH kiqara haquri dasu wata rana sai labari” “Shikenan, ALLAH yaganar damu kutashi kutafi” tabasu amsa atak’aice. Acan sashen Nuraddeen kuwa tsaye yana qoqarin shiga yaji maganganun muneera sun dakar masa kunne a lokacin da take cewa d’an uwa sai d’an uwa badai bare ba da sauri ya qarasa shigi ciki tare da fizgota ya jefota falo yana fad’in “uban waye ya fad’a maki d’an uwa sai d’an uwa, itama yanzu ‘yar uwace awajenmu tunda na aurota na kawota a gidan nan don haka maza kifice kibani waje ko in tattaka ki awajennan wawiya kawai da bata iya magana ba” turo baki tayi tana susar kai had’e da cewa, “Kai ya nura nizaka yiwa walaqanci akan wannan ‘yar yarinyar..” kanta yayo da gudu tafita ta tsaya bakin qofar d’akin tana cigaba da fad’in “Wlh ALLAH ya nura ni bazan yarda ba ai kasan ina sonka sosai shine kaje ka auro wannan abar..” Bata rufe baki ba cikin tak’a biyu ya cimmata a bakin qofar d’akin had’e da sakar mata wani mugun rank’washi akai, ihu ta saka tare da dafe kanta tabar shiyar aguje tana kuka, rumfar d’akinsu ta shige tafad’i qasa tana murje murje da qafafuwa tana wayyo Inna zai kasheni, aguje tafito d’akin tanufi wajenta yanajin haka ya koma Uwar d’akan Rashida na zaune a gefen gado kanta qasa idanuwanta na zubar da hawaye, durqusawa yayi a gabanta tare da tara hannusa hawayen dake neman saukowa daga idanuwanta suka sauka akai, cikin rashin jin dad’in abubuwan da suka faru yace, “Habibty kuka kikeyi?” Shiru tayi tare dasa hannunta akan hanci taja majina sanna a hankali ta d’ago kai tana kallonsa, ganin yana qoqarin saka idanuwansa acikin nata yasa tayi saurin maida kan qasa, magana yaci gaba dayi cikin tattausan lafuzza, “Habibty kidena wannan kukan bana so, akwai basosa masu girma da kike bina wajen rarrashin zuciyarki daga abubuwan da nine silar data b’aci har ta tinzira kyawawan idanuwannan naki fitar da wud’annan tsadaddin wayen, kiyimun afuwa kada kisa zuciyata tayi mani tsattsauran hukunci akan haka, kinfi kowa sanin tarin qaunar da nakeyi maki azuciyata saboda haka gada kibari shaid’an da sharrin zuciyar wasu yasa maki kokwanto ko wani shakku akaina, muneera yarinyar baffa Ali ce, tana matuqar sona amma ban tab’a jin qaunarta azuciyata ba shiyasa tazo tana maki wannan haukar, kiyi haquri daga yau nayi maki alqawarin bazata sakeba kinji?.” Saida ta share hawayen da suka jiqa mata fuska tana sake jan majina sannan tace “Amma meyasa ka aureni bayan kasan tana sonka.?” STORY CONTINUES BELOW  “Saboda ke kad’ai nakeso habibty, ke kad’aice keda mallakin dukkanin wani sansani dake cikin zuciyata, gangar jikina, zuciyata da Kuma rouhina duka mallakinkine babu wani qanqanen fili daidai da k’warar zarrah da zan iya baiwa wata aduniya, Wannan dalilin shiyasa ban aureta ba.” “Amma ai ‘yar uwarka ce, inaga kamar ita tafi dacewa ka aura.” Murmushi yayi tare da kamo hannuwanta biyu ya riqe yana murzawa a hankali yace. “Idan ita ‘yar uwatace ke Kuma rayuwa tace habibty, shin da d’an uwa da rayuwa wayafi dacewa ace mutum yariqa da kyau da kuma muhimmancin da zai zamo masa abokin zama” “Rayuwa mana” Ta furta ahankali tana murmushi, murmushin shima yayi had’e dasa yatsa ya lakutar mata hanci yana fad’in “Gud gel” Da sauri tasa tafin hannayenta tarufe fuskarta, “yawwa bari naje nadawo yanzunnan kinji habibty, kada kisake kuka daga wannan lokacin saboda yau ranar farinciki ce agaremu.” Kad’a masa kai tayi sannan yafice daga d’akin bayan ya d’auki makullan shiyar tasa dake gefen bedside d’inta, yana fita yajawo qofar yasa makulli had’e da juyawa zai bar gidan, yanaji Inna ruqayya matar baba Ali na zage zage harda fad’in. “Lallai nura ya lalace yanzu ya dakeki akan bare, kina ‘yar uwarsa zai walaqantaki akan matarsa lalle dole Yaya hawwa tasan abunyi, ke ya dokeki?” Tasake nana tawa tana d’agowa muneera kanta, murmushi yayi tare da kad’a kai sannan yawuce abunsa, ita kuma tab’are baki tare da nunawa inna ruqayya tsakiyar kanta, “Yishiru taso muje wajen yaya hawwa, wlh yau sai ranar nan tazamo masu ranar bak’inciki, yishiru nace maki” taja hannunta suka nufi sashen Yaya hawwa lokacin tana zaune bisa abun sallarta Bata dad’e da gamawa ba, kukan muneera da taji yasa yasa tayi tsaki tare da ajiye tasbahar hannunta gefe kai kace tasan ALLAH tana tofe addu’a had’e da shafewa a fuska. “Ke.ke. lafiya aka zomun qofar d’aki ana mani reren kuka sai kace munafukar amarya!.” Tafad’a tana lunke sallayar had’e da komawa saman gadonta zata kwanta, “A’a Yaya ai kwanci bai ganeki ba saboda waccan itace munafukar amaryar da naji kina fad’i, fisabillahi ace daga kawo yarinya yau har tajawa yarinyarnan duka awajen d’an uwanta don tana muna fuka…zonan nuna mata inda ya dokeki muneera don bazan yarda ba.” “To sakaryar uwa mai malalaciyar ‘ya yanzu akan d’an rank’washin da yayi mata akai zaki zomun kawo qara don rashin mutunci ko nace takakka.” Yaya hawwa tafad’a tana kallon Rashida da tawani duqo Kai tana nuna mata da yatsa tanaci gaba da reren kuka “ke dallah rufemun qaton bakinnan naki kamar rijiya kona ci ubanki, ca nake uban waye yakaiki shiyarsa har ya rankwasar maki kai.” turo baki tayi tana susar kai had’e da cewa. “To ba amaryar naje gani ba, shine nake jamata fad’amata ni ‘yar uwarsa ce Kuma ni nake sonsa…” Bata k’arasa ba Yaya hawwa ta kwatseta tana fad’in “maza fitarmun d’aki shashasha mai gwalmammin qafafuwa ke kuma da bakisan abunda kikeyi ba kika kwasota kuka iskeni ko yanayin da nake ciki bakya tunani ke tama ‘yarki kikeyi, to idan kinfita kijamun qyaurena zanyi lokacinsu su kuma.” “Amma Yaya hawwa ya zakiyi mani haka?” “Kije kafin dukkanin damuwata taqare akanki rakkiya.” Afusace tafita tare da rafko qofar d’akin tana suruttai jar ta iso shiyarta, tun tana tsammanin wani zai tankata har tagaji tahaqura saboda rashin samun wanda ya kulata. ••• ••• ••• Acan b’angarensu umma da baba kuwa tun cikin mota yaya Yaya maryam ta gargad’i kowa akan kada atada zancen abunda yafaru saboda kada atayarwa mahaifiyarta da hankali, haka da akazo qofar gida saida tasake gargad’insu, kasancewar itace babba yasa kowa kama bakinsa aka shiga ana fatan Allah yasanya alkhairi, aunty marwiyya kuwa da zata tafi Saida tacewa umma “to aunty bawai kinnrabu da ‘yarki ba Kuma shikenan, a’a tashi tsaye zakiyi wajen yimata addu’a da nema mata kariya wajen ALLAH daga sharrin miyagu da mahassada.” Gaban umma ne yafad’i tace. STORY CONTINUES BELOW  “Marwiyya injin dai ko lafiya kika fad’i haka.?” “Lafiya klw aunty kinsan dai halin gidan yawa dole baza’a rasa gutsiri tsoma aciki ba, amma babu komai.” Wata ajiyar zuciya umma ta sauke duk da dai bata natsu da amsar da tabata ba had’e da cewa. “Shikenan marwiyya, Allah yatsare da tsarewarsa amma addua’a dama ai baza’a dena ba, ngd sosai Allah yabar zumunci, ki gaida mun da alhaji.” “Amin aunty zaiji in sha ALLAH, ALLAH yahutar da gajiya.” “Amin seda safe a gaida yara.” Tunda tafita umma taji ta kasa samun natsuwa har baba yadawo, cikin gajiya had’e da nuna kasalar dake tattare dashi yafad’a gefen gado yana fad’in. “Wayyo ni bawan ALLAH.” Murmushi tayi jiki a sanyaye had’e da mik’ewa takoma ta gefensa ta zauna tana d’an mammatsa masa k’wandunansa, “Sannu da hidima malan.” “Sannu mamn Rashida ya gajiyar taku hidimar.?” “Alhamdulillah, saidai Ina matuqar kewar yarinyata sosai.” “Naga hakan atattare dake amma ya zamuyi tunda ita mace dama ‘yar gidan wani ce, ni kaina ina kewarta sosai, ki kwantar da hankalinki addu’armu kawai itace ubangiji ALLAH yabasu zaman lafiya.” “Amin ya gaffar.” Tafad’a tana goge ‘yan qwallan da suka zomata. ••• ••• ••• Nuraddeen nafita yanufi wajen masu saida naman kaji dana rago ya siyo namansa na kaza sannan yasa akayo masa d’aurin naman rago guda biyu, da gorar fresh yaghouth guda biyu, uku wajen baffa yanufa ya kaimasa qulli d’aya sannan yanufi sashen Yaya hawwa bakinsa d’auke da addu’a, tura gambun yayi ahankli daga can kwance tace “Waye?” “Innar mu nine yafad’a yana qarasowa cikin d’akin, gefe ya zauna tare da gaisheta ta amsa daga kwancen da take batare da ta taso ba, shiru yayi na mintoto kafin yace “Innar mu ga wannan?” Ya ajiye ledar abakin gadon, “ALLAH amfana.” tafad’a tana qyaren d’ayar ledar dake hannunsa, “Saida safe innarmu.” Yafad’a tare da miqewa ya nufi qofar fita, har ya aza qafarsa tace, “Miye wannan a d’ayar ledar?” Shiru yayi yakasa Bata amsar don baisan me zaice mata ba, “Dawo itama ka ajiye.” “Innar mu..” “D’auka duka biyun ka b’acemun da gani” tafad’a a fusace, cike da mamakin mahaifiyar tata ita dako bud’a abunda ya kawo mata batayi ba amma tace a ajiye mata duka, duk ya zatayi dasu, dawowa yayi ya ajiye ledar sannan yace. “Kiyi hak’uri innar mu seda safe” sannan yafice kamar zaiyi kuka, gashi gaba d’aya duka kud’in ya kashe naira d’ari biyu kacal ta rage masa, tsaye yayi bakin rumfar yana tunanin yanda zaiyi ya samu wasu kud’in gashi abokanansa duka sun shige Kuma bazai iya iske baffa yace masa yabashi kud’i ba bayan duk wannan jidima daya yimasa, yanke shawarar zuwa ya siyo naman d’ari biyun yayi ko kuma idan abule Mai naman ya amince ya karb’i bashi har gobe don bazai iya koma mata babu komai a hannu ba, daidai ta wajen d’akin baffa zai wuce yaji yakira sunansa, shiga yayi had’e da cewa. “Gani baffa lafiya.” “Lafiya klw Nuraddeen, wai wannan tsumuiniyar da kakeyi ta lafiya ce kabaro yarinyar mutane ita kad’ai zaune, daga Ina kake yanzu kuma Ina zakaje?.” d’an sosa kansa yayi had’e da cewa, “Daga wajen innar mu nake baffa yanzu zan dawo bajimawa zaniyi ba.” Yaqare maganar yana kallon agogon hannunsa saboda lokacin tashin abule ya kusa, daga cikin idanuwansa da Kuma yanayinsa baffa ya fahimci komai, aransa ya tabbatar da cewa Yaya hawwa tayi tsiyar don zata iya komai don ta quntata masu awannan ranar, “tashi katafi” yafad’a yana mai addu’ar ALLAH yaganar da ita, har zai fita sai Kuma baffa yace, “Yawwa Nuraddeen zo d’auke ledar nan naman nan yayimun qarfi bazan iya ciba.” “Amma baffa mai taushi nace yasa maka bansan ya akayi yasa mai qarfi ba.” “To nidai naci d’aya hakanan ALLAH yayi albarka d’auka katafi dashi.” d’auka yayi don yasan halinsa baya son gardama yaji yace. “Had’a da madarar nan tayimun sanyi sosai naga har qanqara gareta, gobe kasiyomun fura da nono nafi gane masu.” Shiru Nuraddeen yayi don yagama fahimtar mahaifinsa ya gano komai shiyasa yayi haka, “Baffa ka ajiye ko zuwa gobe sai asake dafa maka, ita madarar Kuma dama kamar nono take tahuce sai kasha.” “A’a d’auka tafi dasu nace maka” dole ba yanda zaiyi ya d’auka had’e da yimasa saida safe ya fice, baffa na kallonsa ya koma cikin gida batare da ya fitar daya tashi yiba, murmushi yayi yace, “ALLAH ya kyauta sannan ya komawarsa ya kwanta, sashensa yabud’e ya shiga tare da karanta addu’a ya rufe. Koda ya shiga ya tarar har tayi bacci ya ajiye ledar hannunsa had’e da nufar inda take kwance da alama sallolin magrib da isha’i tagama bacci ya d’auketa, hannuwansa yasa ya tallabota tare da cire mata hijabinta ya dinga hura mata iskan bakinsa a fuska, ahankali tafara bud’e idanuwanta suka sauka saman fuskarsa ai kamar wacce aka mintsila tayi saurin zamewa daga hannunsa tana tattaro hijabinta tana rufe jikinta, murmushi yayi daga duqen da yake tare da cewa “tashi muje ki wanko bakinki a toilet.” Yaqare maganar had’e da mik’ewa ya riqo hannunta suka nufi toilet d’in tana biye dashi tana kallonsa, bata tab’a kula da kyan da ALLAH yayi masa ba sai yau… [7/5, 7:07 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___21💎 Murmushi yayi don yakula da kallon da take yimasa saboda hasken wutar lantarki data haskesu lokacin da suke qoqarin shiga toilet d’in, seda yashiga sannan ya sake mik’a mata hannusa tariqo ya shigo da ita cikin toilet d’in, alama yayi mata data iso gaban fanfon dake tsaye ciki irin na qarfe d’innan da xaka gani a tsakiyar gida ko anguwanni ana d’ib’ar ruwa, ahankali tafara takowo kanta na sunkuye a qasa, cikin takun da baiwuce biyu zuwa uku ba ta isa gaban fanfon had’e da duqawa wajen, d’ayan hannunta ta d’ora saman kan fanfo zata kunna taji shima ya d’ora nasa akai da niyar kunna mata, d’ago kai tayi ta kallesa suka had’a ido ya sakar mata murmushi, da sauri ta sinne kanta qasa itama tana mayar masa da murmushin, ahankali yafara juya kan fanfo har lokacin hannusa na saman nata, ganin ruwan sunfara zubowa yasa ta tara d’ayan hannunta tana d’ibar ruwan tana kuskure bakinta had’e da wanke fuskarta, qoqarin jaye hannunta tayi yariqesa gam tamkar wanda za’a kwacewa hakan yasa ta kasa tashi tayi duqenta awurin, tanaji yana wasa da hannunsa akan nata kafin yacirosu akan fanfon bayan yasa d’ayan hannun nasa ya kashe batare da yasaki hannunsa sake riqe da nata ba,+ Bayan sun fito toilet yanufi falo da ita ya zaunar da ita qasan center carpet d’in dake shimfid’e ya d’an tura center table d’in dake tsakiyar don sud’an samu isashhen fili da bazasu matsuba, ledar daya shigo da ita yaje ya d’auko tare da shiga kitchen ya d’auko wani d’an k’aramin tray da cup d’aya ya d’aurayosu ya kawo agabanta yana fad’in. “Washh amarya bakya laifi.” yana kallon yanda ta noce kanta qasa tana wasa da ‘yan yatsun hannunt, riqo hannun yayi yanabin ‘yan yatsun da kallo had’e da cewa. “Habibty lallen nan yayi kyau sosai gashi garin wannan wasar taki kina nema ki gogemunshi da wuri haka.” Tana qoqarin janye hannun yayi ‘yar dariya tare da yimasa kiss wanda yasa Rashida jin wani yanayi atattare da ita, ja baya tayi kad’an kafin ya saki hannun yana mai basawa kamar baisan me tayi ba, naman ya zube masu a plate had’e da ciro gorar fresh youghout d’in acikin leda ya tsiyaya a cup, “Habibty matso kici abinci nasan bazaki rasa jin yunwa ba.” Yafad’a tare da nufo bakinta da yankan naman daya d’auko, kauda kanta gefe tayi alamun bazata ciba shima yasake maida hannunsa a gefen yana fad’in. “Haa mana.” Kamar yanda akeyiwa yara harda d’an bud’e bakinsa murmushi tayi tare da girgiza masa kai tace. “Naqoshi malamina.” Harararta yayi da wasa kafin yace, “Ai baki isa ba.maza kibud’e bakinki bana son musu Kuma.” Ganin ya d’aure fuska yasa tabud’e bakin ya tura mata naman ciki yana fad’in “gud gel” haka yayita bata tanaci har naman yakusa qarewa, riqe masa hannu tayi lokacin da yasake d’auko wani yankan cikin marairaice fuska kamar zatayi kuka tace. “Kayi hak’uri malamina naqoshi tun d’azu ci kawai nakeyi saboda kace baka son musu amma ALLAH idan naqara wani akai yanzu zan iya yin amai.” “Kin tabbata.” “Sosai malamina” “Ok bari nima na tabbatar idan har da gaske kikeyi” noce kanta qasa tayi ganin yasake matsowa kusa da ita gabanta na dukan uku uku taji ya d’ora hannunsa saman cikinta da saurin ta rintse idanuwa yanda yake shafa cikin ahankali yasa dariya ta soma zomata da sauri tariqe hannun tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Don ALLAH kadena, ALLAH kayar da Dani na qoshi sosai” tana ‘yar dariyar da saida haqoranta suka bayyana. “Eh to na amince amma har yanzu da akwai inda bai ida cika ba, ungo wannan ki shanye saiki cike wajen kinji ko d’alibata.” Yafad’a tare da mik’a mata cup d’in daya tsiyaya fresh youghout d’in, ba musu takarb’a tunda yariga yafad’a mata cewa baya son musu shi kuma yafara cin sauran naman daya rage yanayi yana kallon yanda take kurb’arsa ahankali, murmushi yayi don gaba d’aya komai na yarinyar na burgesa musamman yanda take motsa bakinta, nad’e takardar naman yayi bayan ya cinye ya ture ta a gefe tare da jawo sauran da kecikin gorar yafara sha shima, saida ya kusa shanye sa sannan ya ajiye gorar da sauran da ke ciki ko rabin gora beyi ba a lokacin itama ko rabin nata bata sha ba, miqewa yayi ya d’auke late d’in tare da ledar naman da kuma gorar youghout d’in daya rage ya nufi kitchen dasu, ledar ya kad’a a dosbin ya d’auraye plate d’in ita Kuma gorar ya ajiye a gefe don har lokacin ba’a cire fridge d’inta acikin kwali ba balle a jona, A inda ya barta anan ya sake iskota zaune tana jujjuya cup d’in da sauran youghout d’in dake ciki, kallonta yayi had’e da cewa. “Habibty dare fa yayi ko bakyajin bacci ne?” Miqewa tayi taje ta d’auraye cup d’in tare da wanko bakinta shi kuma yawuce toilet don ya watso ruwa, koda tadawo falon tajiyo motsin ruwa a toilet komawarta inda take tayi ta zauna tana kallon tsarinfalon nata da kayan da iyayenta suka zuba mata, sosai ta jinjina masu sabo kyan kayan da kuma yanda aka qawatashi da frem masu kyau kalar coppy colour, kujerunta da labulayenta duka suma kalarne sai ‘yar madai daiciyar tv dake ajiye saman tv stand da qatuwar flower acan gefen falon daga kudu tana wannan tunaninne taji ya shigo falon saye da doguwar jallabiya yace “Habibty je kiyo arwala muyiwa ALLAH godiya daya nuna mana wannan ranar.” Bayan tafito ya jasu sallar raka’a hud’u sannan ya sallame, addu’o’i yayita kwararo masu na samun zama lafiya da kuma zuri’a masu albarka, bayan yagama yajuyo yayi mata tambayoyi akan abunda ya shafi tsarki da kuma wanka, yasha mamaki sosai yanda yaji tabashi amasarsu yanda ya kamata hakan yasa baiyi zurfi ba wajen yimata tambayoyin saboda kusan qarfe sha biyu harda rabi tayi, miqewa yayi ya nufi tsakar gidan ya kashe fitila sannan yadawo cikin falo itama ya kashe har lokacin tana nan zaune gabanta na fad’uwa duk da dai bata san gaskiyar abunda zai biyo baya ba Amma keb’antarta daga ita sai namiji awake d’aya abune da Bata tab’a yiba don haka dole tsoro da fad’uwar gaba su kamata, tana jinsa yana kiran sunanta tamakure a gefen kujera jikta na rawa. “Habibty taso muje mu kwanta.” Yafad’a yana qoqarin had’iye dariyarsa ganin yanda ta sake shigewa can bayan kujera, “Habibty, habibty…” yaci gaba da fad’a ahankali yana qoqarin isa inda take, a hankali hannunsa yakai saman kafad’arta tazabura tana shirin yin qara ya jawota ta fad’o jikinsa, “meye haka habibty? Nifa mijinkine da ALLAH ya halatta maki kiyi duk yanda kikeso dani da kuma gangar jikina haka kema ya halasta mani ke da duk wani abunda ke tattare dake, Ina sonki kina sona, menene abun tsorata da juna, karki manta nayi maki alqawarin zan kula dake Kuma zan baki farinci mai d’orewa matuqar Ina raye, zan soki soyayya mafi girma aduniya, irin soyayyar da zatasa harna mutu bazaki manta dani ba, Rashida kece duk wani bugun lumfashina don haka kiyarda dani bazan tab’a bari kicutuba aduniya, Ina so matuqar zuciyarki ta amince da kalaman dake fitowa daga qarqashin zuciyata ki kwantar da hankalinki muje mu kwanta abunmu kinji ko?.” Ahankali ta d’aga masa kai jikinta narawa jin yanda nasa jikin ke gugar nata tana qoqarin zamewa, riqeta yayi sosai sannan ya d’agata cak ya d’auketa yawuce uwar d’aka da ita, bai direta ko ina ba sai tsakiyar gadon ya zagaya ta gefe yacire jalabiyar dake jikinsa had’e da kashe fitilar ya hau saman gadon shima, jawota yayi ajikinsa yaji ko Ina rawa take na jikinta, ahankali ya sake mannata aqirjinsa sosai cikin kwantar da murya ya rad’a mata a kunne. STORY CONTINUES BELOW  “Don ALLAH kinatsu habibty? Nayi maki alqawarin bazan cutar dake ba ko kad’an, kinga gidan yawa muke kada muyi abunda zaisa aganomu kinji ko?” A hankali ta d’aga masa kai cike da tsoro hawaye na zubo mata, “Kin amince?.” Nanma d’aga masa kai yasakeyi, cike da jin dad’i yakai bakinsa a goshinta yayi mata kiss, don aransa ya raya matuqar Bata amince ba bazai tab’a yimata dole ba saboda yanayin inda suke ciki zai iya zame mata abun gori idan har wajen tilastata yasa tayi abunda zaisa ajiyosu, ita kuma ta amsa masa ta amincene atunaninta na yakwana d’akin da ita badon tasan meye ainahin abunda yake roqon amincewarta aciki ba. ( _Karku manta Rashida yarinya ce, ba lallai bane don ta furta kalmar aure takeso kuma tasan me ake aikatawa acikin aurenba, batada wasu cikakkin abokanai inba meenah ba kuma a qauye ta tashi ba dolene ace tanada wayewar sanin ko meye ba don haka kada kuyi mamakin jin nace batasan me yake shirin yimata ba da har yake neman amincewarta ba da Kuma yanda ta tsorata har dasu rawar jiki saboda abune da bata tab’a yiba arayuwarta balle ace tasaba, tanada ilimi akan aure amma batada ilimin auren a aikace ko zahirance, sab’anin ‘yan matanmu na yanzu da tun kafin akai yarinya tasan meza’a aikata_). Bakinsa ya d’ora akan idonta d’aya yayi mata kiss haka ma ga d’ayar kafin ya gangaro ga abu mafi burgesa atattare da ita shine bakinta ya d’ora nasa akai da sauri tajaye tana hawaye, “Don ALLAH kadena bana so?” “Kiyi haquri habibty wannan shine fa auren.” Bil haqqi ta wangame baki zata saka masa kuka yayi saurin rufesa da nasa yana tsutsa ahankali, tun tana qoqarin kwacewa har ta gaji tafara lumshe idanuwa tana karb’ar saqon yanda ya kamata, jinta tayi awani baqon yanayi tare da kasa attaka komai saboda yanda jikinta ya mutu had’e da yin sanyi, hakan yabasa damar cigaba da aika zafafan sak’onnin da zuka dad’e yana son isarwa azuciyarta hannayensa kuwa nak’ara taimaka masa akan dukkanin muradansa naganin ya maida ita cikakkiyar mace a wannan daren, sosai take amsar saqwanninsa tana fitar da lumfashi a hankali, cikin tausayi da nuna jinqai yafara qoqarin sarrafata had’e da karanto addu’ar saduwa har ya cimma burinsa. Kasancewar bai zomata cikin tashin hankali ba yasa yayi nasarar rabata da budurcinta duk dai shima kansa saida ya wahala wajen qoqarin samun hanya, Rashida kam tasha kuka sosai, tayi dana sanin furta kalmar aure takeso don har seda taroqesa a maidata makaranta zatayi karatu sosai, wannan abun ba kad’an yabashi dariya ba hakan yasa yahaqura duk da bawani jimawa yayi ba balle gamsuwa, saboda duk duniya bayada burin daya wuce Rashida ta samu cikakken ilimin boko kamar yanda take dana arabiya, Wannan dalilin yasa yanaji yana gani ya haqura tare da komawa rarrashinta, da qyar yasamu taui shiru bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, amma kallo d’aya zaka yimata kasan baccin bana dad’i bane, Jin alamun gari yayi sanyi da iskan da ake kad’awa sosai yasa yafahimci ruwa za’ayi don haka ya gyara kwanciyarsa tare da jawota ajikinsa yanajin wata sabuwar sha’awarta na taso masa, murmushi yayi cikin farinciki da jin dad’in yanda yasameta sannan ya ja masu bargo suka lullub’a. ••• ••• ••• Yaya hawwa kuwa yana fita ta tashi zaune had’e da jawo ledojin guda biyu tafara bud’e tafarkon, ganin naman ragone yasa ta turesa gefe tajawo dayar tabud’e, wahe baki tayi had’e da cewa “d’an kwal uba ga naman kaza zaka bani na rago, duk da dai naga irin wanda nake so ne Mai kitse kasiyo.” Zaunawa daidai tayi tabud’e qafafuwanta tasa naman a tsakiya tayago naman kaza taci sannan ta d’auko yankan na ragon Mai kitse bayan ta birkid’eshi da yaji taci, haka tayitayi har ta canye naman ragon da kaza d’aya sannan tajawo gorar youghout d’in ta aza asama, wata uwar gyatsa tayi had’e da cewa “d’an buhun uba, wato inana kwance turus kashige d’aka da mata kusha wannan uwar dad’in ni kuma ka had’ani da mai kitse kad’ai, yo waya fad’a maka shikad’ai nake so bana son ita wannan abar mai fika fikai. STORY CONTINUES BELOW  Nad’e d’ayar kazar tayi ta tura aqarqashin filo tare da gorar youghout d’in d’aya, shi kuma sauran takoma ta kwanta tana sha tana suruttanta har bacci ya soma d’aukarta, can cikin bacci taji kamar ana Kiran sallar asuba da sauri tamiqe tanufi sashensu Nuraddeen tafara bubbuga qofar, kasancewar baaccin ya soma yimasa nauyi sosai shiyasa baiji ba saidai baffa Usman ne yaji qarar ana dukan qofa daga wajen sashen Nuraddeen da sauri yafito don ya zata shine, ganin Yaya hawwa tsaye bakin qofar yasa yaqarasa wajen yana murzar idanuwa cikin rage murya yace “Lafiya Yaya hawwa kike buga masu qofa awannan lokaci?.” “Aiho Usman ashe kaima kafito, ja’irin yaro kaji har ankira sallar asuba bai fitoba shine nace Bari na tadashi don Karya makara” kallon sararin samaniya baffa Usman yayi kafin yace. “Ikon ALLAH! To aike yaya ba’a isa kiran sallar asuba ba, qarfe uku da rabi yanzu ko baki duba agogo bane.” “Kace wlh, Niko naji kiran sallah yanzu shiyasa nataso.” dariya yayi don ya fahimci zallar damuwane yasa kunnuwanta ke hakaito mata kiran sallah awannan lokacin, dariya suka jiyo shiyarsu baffa Ali wanda har da zai fito Inna ruqayya tariqesa ta hanasa fitowa. “Wlh waccan yayar tashiga uku, mace baqin hali sekace gareta farau suruka, shiyasa naso muneera ta auresa don ta gyara mata zama wannan takurawa har Ina, fita batunsu baban yusufa koma ka kwanta.” Tafad’a tana dariya had’e da kashe wutar d’akin, Girgiza kai baffa Usman yayi had’e da cewa “ki koma ki kwanta Yaya hawwa idan asuba tayi zan tashesu.” “Asubar batayi ba kenan!” “Eh” yafad’a tare da juyawarsa yakoma d’aki, Daren ranar kam kasa komawa bacci tayi in banda saqawa da kuma warwarewa azuciyarta babu abunda takeyi, Baffa shima kansa abun dariya yabashi don duk abun dake faruwa akunnensa yanaji saboda alokacin shima ba bacci yake yiba, zaune take abunsa yana karatun al-qur’ani kafin yafara sallolinsa daga zaunen yajiyo bugun qofarta, rashin qafafuwa ya hanasa tasowa da sai ya riga baffa Usman fitowa, sosai matar tasa tabashi dariya ya d’aga hannuwa sama yana addu’a ALLAH ya shirya masa ita yaganar da ita kura kuranta tun wuri bai qure mata ba sannan yaci gaba da ibadunsa tare da roqawa d’an nasa samun dukkanin bud’i na duniya da zaman lafiya had’e da ‘ya’ya nagari… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/5, 11:35 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___22💎 Yaya hawwa kuwa har akayi kiran sallar asuba na farko idanuwanta biyu tanaji anfara kiraye kirayein sallar tamik’e had’e da azo qafarta bakin qofar d’aki kawai taji saukar ruwan sama ya kuccike ba zato ba tsammani don tun wurairan biyu da hadarin ya kankama iska ya taso ta ko Ina sai kuma daga baya ya kwanta hadarin kuma ya wargaje cikin ikon ALLAH nan take kuma da asubar ya sake had’uwa saiga ruwa, tsaye Yaya hawwa tayi kamar tafashe da kuka tana kallon sama, wata irin walk’iya akayo da tsawa alokaci d’aya da gudu takoma cikin d’akin tanemi waje ta zauna gefen gado idanuwa sunyi mata qululu, yau take jiran ad’auke ruwa gobe take jira amma sai sake sauka sukeyi kamar da bakin k’warya, hakan yasa kosu baffa Usman basu samu fita masallaci ba balle malan Nuraddeen ango sai dai kowanensu yayi sallarsa a d’aki tare da iyalinsa, STORY CONTINUES BELOW  Nuraddeen kuwa saboda sanyi da qyar yasamu yayi wankan tsalki ba tare daya tayar da Rashida ba da sai faman yatsine fuska takeyi cikin baccin saboda babu ruwan zafi, sallarsa yayi sannan ya shiga cikin kicin d’inta ko zaiga inda aka ajiye rishow d’inta, cikin sa’a ya hango kwalin electric stove ya jawo had’e da cirosa daga ciki ya jona ga socket d’in kitchen d’in sannan ya ciro tukunya cikin kwalinta itama ya d’ora bayan ya d’an kara hannunsa saitin electric d’in yaji yafara zafi ya d’ebo ruwa ya zuba sannan yakoma cikin d’akin, gefen gadon ya zauna tare dasa yatsansa yana d’an shafa lab’b’anta, ahankali yaga tafara bud’e idanuwanta suka sauka akan nasa daya qura mata, suna had’a ido tayi saurin rufewa had’e da cuno d’an k’aramin bakinta ta kauda kanta gefe, dariya yayi kafin yace “haba ta malan nura fad’amun waya tab’amun ke kike juyamun kai haka.” Shiru tayi batare data amsa masa idanuwanta na arufe, hannunta ya cire daga saman qirji da yake ta riqe bargon yana shafa lallen dake jiki a hankali tare da yimasa kiss, jaye abunta tayi da sauri tana fad’in “kadena bana so..” Kafin tarufe baki taji ya had’e bakinsa da nata ya sakar mata wani irin sihirtaccen kiss. Idanuwanta ta lumshe tanajin tamkar na’urar jikinta ta d’auke ta had’e da dawowa. “Morning habibty kin tashi lafiya?” Kad’a masa kai tayi tana tunani abubuwan da suka faru jiya tsakaninta dashi kawai saita tsinci kanta cikin matsananciyar jin kunyarsa, “taso muje kiyi wanka yafad’a had’e da miqewa, har zai d’aukarta sai Kuma ya tuna bai had’a ruwanba ya. “Afuwa habibty bari naje na had’a maki ruwan wankan tukunna.” Yaqarasa maganar tare da barin d’akin koda yaje ruwan har sun tafasa ya juye a boket yakai toilet, wani bokitin ya sake d’auka yahad’a mata ruwan tare da detol sannan yakoma ya d’aukota tamkar wata baby, Cikin jin kunya tace “don ALLAH ka ajiyeni zan iya tafiya da kaina.” Zaro idanuwa yayi yana kallonta had’e da cewa. “Da gaske kike?” “Eh ajiyeni kagani mana.” Tana turo baki agaba, Saida yayiwa bakin kiss sannan ya ajiyeta qasa tafara takawa ahankali yana biye da ita har takai bakin qofar shiga toilet d’in, tana aza qafarta d’aya ta d’ago d’ayar ta aza tayo baya baya zata fad’i da sauri ya tareta tafad’a akan jikinsa saboda wani irin masifaffen zafi da taji a tsakiyarta don ma ALLAH ya taimaketa bai jimataba saboda ba duka ya shigeta ba, binta da kallo yayi ganin yanda tsoro yasa taturo idanuwanta da suka cika tab da hawaye tana shirin yin kuka yace “Sorry habibty, kibi a hankali mana kinga da yanzu kin fad’i” kafin tace wani abu ya d’auketa ya qarasa shiga da ita ciki, qasa ya direta sannan yajawo wata ‘yar kujerar da kecikin bayin ya zaunar da ita had’e da nad’e hannuwan rigarsa yasa cup yafara d’ebo ruwan yana yimata tsarki dasu, ture hannunsa takeyi tana had’e qafafuwanta Amma yayi kamar bai ganta ba saida ya gasata sosai sannan yace tayi wankan tsarki sai tafito, Ita kam banda satar kallonsa tana mamkinsa babu abunda takeyi, wai yau itace malaminta ke d’auka hadda suyimata tsarki, lalle aure wani babban alamarine daban, da sauri tasa hanuwa tarufe fuskarta tana dariya alokaci d’aya kuma tanajin qaunarsa naqara ruruwa azuciyarta, tajima zaune tana wud’annan tunanin kafin tayo wankan tafito tasamu harya shimfid’a mata abun sallah tare da fiddo mata da doguwar riga da hijabi yabata tasa ta tada sallah, waje yake son fita amma har lokacin ruwa akeyi sosai gashi har goma da kwata tayi yarinyar mutane bataci komai ba, Yanke shawarar fita haka yayi sai gashi yaji qarar wayarsa dake ajiye saman bedside, da sauri yaje ya d’auka yaga lambar baffa Usman duk sai yaji wata irin kunya ta kamasa, kasa d’agawa yayi akaro na farko har sai akaro na biyu ya d’aga had’e dayin sallama ya gaishesa. murmushi yayi sannan yace “Lafiya klw Nuraddeen, katashi lafiya.” “Lafiya klw baffa Usman.” “Ya kwanan iyalin naka? Yau mun tashi da ni’ima.” STORY CONTINUES BELOW  “Alhamdulillah kam ga ruwa nan masha ALLAH sai fatar alkhairin dake cikinsu” yafad’a tar da basar da d’ayar maganar, murmushi baffa Usman ya sakeyi kafin yace, “Kabud’e k’ofa ga abun karinan Aysha zata kawo maka da sauri kasan ruwan nada qarfi kada su dokarmun auta tayi ciwo..” ‘yar dariya Nuraddeen yayi had’e da cewa. “To baffa Usman, ko abari inzo in karb’a kada ruwa sudoketa nayi laifi, dama yanzu nake Shirin fitowa.” “A’a jira gatanan zuwa, ai babban d’a baya laifi,” “To baffa Usman mungode.” “Masha ALLAH ka gaida iyalin naka” Yakashe wayar don yasan bazai amsa ba saboda kunyar da yake da ita, miqewa yayi had’e da zuwa bakin qofar don har yaji isowar ta, yana bud’ewa yace “Aysha shigo da sauri mana kada ruwan ya jiqaki.” “A’a Yaya Inna tace inyi maza indawo kada natsaya, Ina kwana?” “Lafiya klw autar baffa yasu Inna?” “Duk lafiya klw suke, Ina aunty.” Juyawa yayi yakalli qofar d’akin bayan ya anshi kayan hannunta sannan yace “shigo mana tana ciki ku gaisa ko bakya sonta?” Rufe baki tayi sannan tajuya da gudu tabar wajen tana fad’in “Ina sonta mana Yaya ka gaisheta anjima zamuzo ni dasu aunty fadila.” Juyawa yayi ya koma ciki ya tarar har ta sake gyara d’akin ta koma ta kwanta, amaimakon ya tada ita sai kawai shima yabi bayanta yakwanta abinsa had’e da jawota ajikinsa, tanaji yafara shafo cikinta yana yawo da hannunsa ta rintse idanuwa sosai irin tayi baccin nan, cakulkuli yafara yimata yana fad’in “kima bud’e idanuwanki nasan ba bacci kikeyi ba.” Yanaci gaba da yimata cakulkulin, juyowa tayi tana dariya tashige jikinsa tana fad’in “don ALLAH kadena bana so.” Cikin kwaikwayon muryarta shima ya maimaita abunda tace. “Shikenan to ni kiyimun Ina so.” Aikuwa ta taqarqare tana yimasa cakulkuli tana dariyar shima yanayi, jawota yayi ya rungume jikinsa sosai yana fad’in “to ya isa haka kibarni nima bana so” yana rirriqe mata hannuwa ita kuma tana qoqarin kwacewa, da wayo da wayo yasamu ya sake biyan buqatarsa amma awannan karon Mai gaba d’aya yayimata don seda yaji yasamu natsuwa sosai, Kuka kam Rashida tashashi har dasu majina, sai faman rarrashi yakeyi fiye da jiya yana qoqarin jawota ajiki turesa ta dingayi tana fad’in “ni ka qyaleni tunda wayone da Kai bazan sake yarda da kaiba.” Dariya ya dinga yimata yana cewa. “Yi hakuri nadena bazan sake ba.” Saida yaga tayi shiru sannan ya tashi yaje ya juyo sauran ruwan zafin d’azu yakai masu toilet yadawo ya sake d’aukarta izuwa toilet d’in, nan ma saida ya cukulkulata sannan ya taimaka mata tayi wankan shima yayi suka fito, ji yake wani irin sonta na qara ruruwa azuciyarsa da bayajin zai iya rayuwa idan babu ita. Saida suka shirya tsaf sannan ya d’auko abun karin da baffa Usman yasa Aysha takawo masu ya ajiye agabanta, soyayyen kwaine sai ruwan tea da kuma qaton burodi guda sai suga da gwangon madarar ruwa guda biyu tare da bonvita, qananan cups ya d’auko a kitchen tare da plate yajuye soyayyen qwan akan yahad’a mata tea mai kabrin gaske yabata, tana jin yunwa sosai hakan yasa ba musu ta karb’a tafara sha tana had’awa da soyayyen qwan tak’i cin biredin, Babu yanda beyi da itaba akan taci tace taqoshi don dama ita ko agida biredi bai shamata kai ba. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/6, 10:32 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 STORY CONTINUES BELOW  _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___23💎 Haka yagaji ya qyaleta yaci gaba da cin biredinsa tare da kora ruwan tea kafin can ya turesu gefe yana kallonta, murmushi tayi ta tura soyayyen k’wan data d’ebo cikin baki had’e da sunkuyar da kanta k’asa. “Malamina wannan kallo haka fa?.” Tafad’a tana kai ruwan tean abakinta, “Ke d’ince indai kina agabana bazan iya dena kallonki ba, musamman idan kina motsa wannan d’an mitsitsin bakin naki dake d’auke da tausasan lab’b’a tamkar tuffa sai inji bana gajiya da kallonki.” “Ehhm.” “Baki yarda bane?” “Haba! Nayarda sosai kuwa.” “Habibty! Hak’ik’a ba k’aramar sa’a nataka ba da ALLAH ya mallaka manike a matsayin matata kuma asusun ajiyar ‘ya’yana har nakanj alfahari araina tare da ganin babu abunda yai sauran mani aduniya face naci gaba da yiwa ALLAH godiya bisa wannan kyauta da yayimun, haqiqa kowace mace da irin baiwar da ALLAH yayi mata aduniya amma inada yaqini akan cewa taki baiwar ta musammance, nayarjewa kaina in rayu rayuwa ta har abada a qarqashin inuwarki ke kad’ai batare dana kwad’aita izuwa wata inuwar ba.” Yanda taqura masa ido tana sauraren kalamansa ya sashi jinjina mata kai had’e da rufe idanuwansa yabud’e alamun tabbatar mata da zancensa sannan yaci gaba da cewa. “Kiyarda dani Rashida Kuma kibani damar d’awainiya da dukkanin murdanki da burukanki aduniya natabbata zanyi qoqarin cika makisu koda kuwa zan rasa raina, ni Nuraddeen nayi maki alqawarin zan kula dake, zan tarairayeki zan bud’e maki dukkanin qofofin zuciyata kiyi duk yanda kike so aciki, zan mallaka maki dukkanin sassan jikinsa da kuma rouhina, zanyi maki uzuri acikin lafuzzanki da kuma ayukkanki agareni, zan killaceki tayanda Babu wani mahaluqin daya isa yacutar mani dake, zan d’aukaka darajarki da martabarki acikin ‘yan uwanki mata, burina d’aya shine ki soni so mai girma kuma ki qaunaceni tayanda duk tsanani bazaki tab’a yarda arabaki dani ba domin farincikina yana wan zuwane matuqar kina tare dani to tabbas zan kasance mai alfahari da rayuwata har abada, Rashida Ina sonki so marar misaltuwa, Ina qaunarki qauna mai tsananin da zan iya sadaukar da dukkanin farincikina akan naki farincikin.” Murmushi tayi tana maijin wani sanyi na ratsa zuciyarta da kuma sassan jikinta, tabbas tayarda cewa idan ALLAH ya jarabci bayinsa awanI b’angaren to yana kawo masu mafita a ta wani b’angaren daban, daga daren jiya zuwa wayewar safiyar yau cike take da tsoro da kuma tashin hankali ganin yanda mahaifiyar mijinta da wasu ‘yan uwansa suka nuna qarara cewa basa farinciki da aurota wanda hakan ba qaramin jefata cikin damuwa da karaya yayi ba amma ayanzu ganin tsantsar soyayyar da mijinta keyi mata acikin idanuwansa da saqon da bakinsa ya isar Kai tsaye daga zuciyarsa yasa tasamu natsuwa da qwarin guiwa d’ari bisa d’ari wajen jajircewa ta nayarda martani akan soyayyar da mijinta keyimata kuma tashirya tsaf wajen yaqar duk wani shamaki da zaizo ya shiga tsakaninta dashi, zata lullunka dukkanin haqurin da akace tayi tare da jurewa dukkanin b’acin ran da zata fuskanta don ganin sunyi rayuwarsu yanda suka tsara cikin so da qaunar juna. Wata kasalalliyar ajiyar zuciya tayi had’e da riqo hannayensa biyu tana kallon cikin idanuwansa tace. “Ka kwantar da hankalinka malamina domin kai kad’aine zuciyata keso, Kai kad’ai taquduri alqawarin yiwa hidima har qarshen rayuwarta, bazan gujeka ba komai rintsi komai wuya, zanyi maka biyayya iya qarfina, zan kula da kai iya qoqarina sannan zan baka farinciki daidai iyawata, zan zauna da ‘yan uwanka lafiya zan Kuma kyautawa iyayenka tamkar nawa iyayen sannan zanyi fad’a da qarfin ALLAH ga duk abunda zai rusa rayuwar aurenmu, abu d’ayane bazan iya yimaka alqawari ba, shine na baka soyayyata tahar abada.” STORY CONTINUES BELOW  Taqare zancen tana sinne kanta qasa had’e da qumshe dariyar da tazo mata saboda ganin yanda ya turikke idanuwansa awaje, cikin rud’ewa ya rumk’e hannuwanta sosai kamar zaiyi kuka had’e da cewa. “Why Rashida!. Meyasa bazaki iya bani soyayyar kiba tahar abada?” D’ago kanta fuskarta ad’aure tana kallonsa tace. “Kayi hak’uri saboda gaba d’aya nariga da nabaka ita tunda dad’ewa har agaban Aabadan kaga kuwa bazan iya sake baka itaba tunda tuni tana hannunka.” Taqare maganar tana dariya had’e da kallon yanda ya dafe saiti zuciyarsa da hannayensa biyu yana murmushi, cikin wani irin shauqi yariqo gefen kuncin ya d’aga d’ayan hannunsa kamar zai mareta yana fad’in. “Ke ko!” tayi saurin runtse idanuwanta tana dariya, ji tayi ya rungumeta had’e da sumbatar goshinta yace. “Kai habibty Zaki kasheni da soyayyarki, waya koya maki soyayya haka.” Yana sake sakar mata kiss agoshi, gyara zaman kanta tayi a qirjinsa had’e da cewa. “Malamina mana..” duk sukasa dariya, atak’aice dai ranar sun faranta zukatan junansu da dad’ad’an kalamai dake d’auke da nagartacciyar soyayya. Ganin ruwan basuda ranar d’aukewa yasa qarfe d’aya da rabi nayi na rana ya fito haka don gabatar da sallar azahar, kallo d’aya zakayi masa katabbatar da natsuwar dake cikin zuciyarsa saboda farincikin dake shifid’e a fuskarsa, kasancewar ruwan sun d’an rage yayyafine akeyi amma mai d’an qarfi yasa bai tsaya yin sallarsa b’angaren baffa ya wucewarsa masallaci, bayan yadawo yashiga inda mahaifinsa yake cike da jin kunyar rashin fitowarsa da safe ya gaishesa, sallama yayi baffa ya amsa masa sannan yashiga yana zaune riqe da littafin majma’ul baharaini yana tilawarsa, kallo d’aya yayi masa ya d’auke kansa ya mayar ga littafin yana murmushi ganin yanda yake wani faman sissinne kai qasa. “Baffa Ina wuni?” Yafad’a kamar zai nutse aqasa saboda kunya, batare da baffa ya d’ago kansa ba yace. “Lafiya klw Nuraddeen, ya yinin iyalin naka duk lafiya kuke?” “Lafiya klw baffa ya ruwa?.” “Ruwa kam gasunan Masha ALLAH sun sauka, kaga badon rashin qafafuwannan nawa ba da sai gona.” “To baffa ya za’ayi sai haquri, in sha ALLAH ijaba takusan sauka, inaji ajikina ka kusan miqewa da qafafuwanka da yardar ALLAH” Murmushi yayi irin nasu na manya tare da rufe littafin sannan yace, “Hmm! Nuraddeen kenan! Kai yanzu kana tunanin zan miqe awannan halin da nake ciki?, Duk da dai shi ciwo da mutuwa duka a hannun ALLAH yake bana tunanin zan wud’an qafafuwan nawa zasu sake taka qasa” _Laa taqnad’u min rahmatillah (kada ka yanke tsammani ga rahamar ALLAH)_ sukajiyo baffa Usman dake qoqarin shigowa yafad’a had’e da yin sallama, murmushi baffa yayi had’e da cewa. “Malan Usman uban ango yau Ina kashige tun safe ban sake ganin kaba sai yanzu?, kodai d’an naka kake tayawa angwanci?” Sosa qeya Nuraddeen yashigayi yana murmushi tare da kallon baffa Usman dake qoqarin zaunawa kusa ga d’an uwan nasa yana dariya yace, “To Yaya idanma nayi ai ba garemu farauba balle ta qare kanmu, in banda abunka Yaya duka duka shekarun naka nawane da kake zancen mutuwa koda yake ita batada takamammen lokaci amma muna fatar ba jikoki kad’ai ba har ‘ya’yansu kariqa a hannu kafin wannan lokacin har su girma suna biye da kai kuje gona, rayuwa dai muke fatan tayi mana fad’a.” “Usman kenan tunda ALLAH kace nayi shiru, Amma karka maanta shekaruna fa yanzu sun haura hamsin da wani abu aduniya, idanma ALLAH bai nufi nagani ba ina roqon kai da d’an uwanka yagwada maka.” Yafad’a yana sharar k’wallah ganin haka yasa baffa Usman ya kauda zancen had’e da cewa, STORY CONTINUES BELOW  “Ya qarfin jikin naka? Kasha maganinka?” “Eh yanzu da hawwa tashigo tabani nasha, jiki kam gayanan Alhamdulillah, yawwa kai namanta infad’a maka maman taka ba tada lafiya, shine dalilin shigowarta tace mun tana fama da ciwon ciki da gudawa don haka ka aika ko filagin da limotin ne asiyo mata ko kuma kaje da kanka.” Baffa yaqarasa fad’a yana kallon Nuraddeen Baffa Ali ne ya d’ago labulen qofar had’e da kallon Nuraddeen sannan ya kalli baffa daga bakin qofar yace, “Ya jikin?.” “Da sauqi Aliyu bazaka shigo ba?” “A’a sauri nake zanje gona nad’an duba wasu abubuwan kasan zaman gida bana namiji bane sai mata.” Batare da baffa yadamu da maganar daya soka masa ba yace. “To ALLAH yayi taimako yadawo da kai lafiya.” Shidai baffa Usman na zaune yana kalonsa don tun jiya take d’aure masa fuska had’e da rashin yimasa magana. “Baffa Ali ina wuni?” Nuraddeen yafad’a daidai lokacin da yake qoqarin barin wajen batare data kalli ko gefen da baffa Usman yake ba, dawowa yayi had’e da sake d’ago labulen sosai yanda zaiga fuskar Nuraddeen d’in snnn yace, “Af..shin nura ne? Ai ban lura da kaiba, ashe kasamu damar fitowa yanzu, to agaisheka.” Baice masa komai ba saima noce kansa qasa da yayi shi kuma yawuce yana dariyar qeta don acikinsu yasan babu wanda bai b’atawa raiba da kalamansa. Murmushi baffa yayi sannan ya fara ba baffa Usman magana akan yaci gaba da haquri da halin d’an uwansa, in Sha ALLAH da SANNU SANNU zai gane dukkanin kuskuren da yakeyi. Miqewa Nuraddeen yayi had’e da cewa. “baffa Bari naje na siyowa innar mu maganin” “To adawo lafiya.” Yabashi amsa atak’aice tare da maida hankalinsa wajen baffa Usman sukaci gaba da firarsu. Bayan mintuna biyar da fitarsa sai gashi yadawo da ledar magani a hannunsa yanufi sashen mahaifiyar tasa yana isa tana fitowa da sauri daga d’aki had’e da cewa, “Miqomun butar nan Nura.” tanufi bayin aguje, kad’an yarage dariya tafito masa yayi saurin d’aukar butar yabita da ita yakai mata abakin toilet sannan yadawo, juyawa yayi da niyar fita tayi masa tari alamun ya jirata, tafi minti biyar acikin toilet d’in kafin tafito riqe da ciki, daddafe ta iso cikin d’akin yana zaune yana daddanna wayarsa tace. “Nura banda lafiya.” “Subhanallahi innar mu meyake damunki?” “Bari nura d’azunnan naji cikina ya murd’a nashiga bayi basai ga gudawa ba, ciwon ciki uwa zan mutu gashi kai kashige abunka kamar bazaka fitoba balle kasan halin da nake ciki.” “Yi hak’uri innar mu, yanayin uwan da aka tashi da sune na d’auka kema kina nan abunki kwance saboda qarfin ruwan.” “Kai! haba nura ina naga takwanciya awannan halin, ai mayata bayi tafi biyar acikin ruwannan, inaji nura naman nan bayada kyau, kodai wani abun kasa aka saka maka aciki?” Tafad’a tana qoqarin zaunawa saman gadon, Bata qarasa zaunawa ba tasake fita aguje zuwa bayi, duk da mahaifiya ce amma abun dole ya basa dariya, yana zaune tadawo tana “wash ALLAH na, nura kaji tsoron ALLAH anya da zuciya d’aya kabani naman nan? Wlh gudawarnan tayi yawa ko qarfin jikina banaji, gaba d’aya ruwan jikina sun qone qurmus nura.” Kauda kansa ya dingayi yana basar da dariyar tare da cewa. “Sannu innarmu, wlh da zuciya d’aya na ajiye maki, kefa mahaifiyata ce, taya zanso abunda zai cutar mani dake?” STORY CONTINUES BELOW  “To Ina nasani nura ko kazab’i matarka akaina shiyasa kayimun haka! Ko ko dai kitsennan ne yatab’amun ciki kasan sonshi nake Amma baya shafamun lafiya.” Ledar hannunsa ya bud’e ya d’auko maganin daya siyo mata ya b’alla matasu tare da d’ebo ruwa atukunyar dake cikin d’akin bayan gambu ya miqa mata, “Gashi innar mu kisha, maganine baffa yace naje nasiyo maki dana shiga wajensa. Idan anjima kikaji ba canji sai inje inkirawo maki Ibrahim mai allura aqara maki ruwa” “Yawwa agaisheka ALLAH yayi albarka.” Tafad’a tana karb’ar maganin ta afa abaki sannan ta kora ruwan sama tana b’ab’bata fuska. “Wannan magani sai d’acin tsiya, shiyasa nafi ganewa maganin gargajiyar nan na basir.” Tana gama fad’a ta d’aga gefen filonta tajawo sauran kazar d’aya data rage jiya tare da gorar youghout d’in tace. “Ungo nan nura kaje da ita ku silala, batayi komai ba saboda sanyin da kayi.” “Innar mu bari dai agyaro maki ita tunda kinga bakijin dad’i sai anjima kici.” Daqquwa tayi masa had’e da cewa, “Zaka karb’ane ko saina b’ata maka rai, ai duk wannan namanne da naci yajawomun wannan wahalar, tashi kaje dashi can ni bazan ciba ta sake kawomun wahala, gaba d’aya tama fita raina, ungo had’a da wannan gorar madarar ta wahala ku qara can.” Duk qoqarinsa wajen ganin ya danne dariyar karta fito saida tafito a wannan karon ta jefesa da gorar had’e da cewa, “‘dan buhun uba, dariya ma zaka azamun taahi ficemun da gani ja’irin banza da wofi..” Da sauri ya miqe yafita riqe da sauran naman bayan ya d’auki gorar youghout d’in data jefomasa yana dariya. “Oh ALLAH! ALLAH yaqara yawancin rai innar mu nikam naga yanda Zaki kwashe da ‘yan jikokinki!” “Innar mu sanni ALLAH yakyauta Kuma yabaki lafiya.” “Amin, zaka gane bari dai insamu lafiya d’an buhun uban nan duk sai naci mutuncinku da Kai har wannan tsigi tsilar yarinyar.” Shiyarsa ya shige ya tadda Rashida dasu Aysha zaune suna tayata fira bayan sun kawo mata abincin da baffa Usman yasa aka dafa masu, suna ganinsa suka miqe had’e da gaishesa suka fita, bud’e hannuwa yayi yana fad’in “baza’a yimun oyoyo ba?” Tasowa tayi ahankli tana tafiya tashige cikin hannayen nasa, har zai maida ya kulle ta duqe ta qasa had’e dayin zaunenta qasan carpet d’in ta jingina ga kujera tana dariya, “Kazo kaci abinci qarfe uku ke shirinyi kada yunwa takamaka.” Tafad’a tare da jawo kular jallof d’in shinkafar da su Aysha suka kawo mata tasha kayan ciki…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/7, 7:47 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___24💎 Zaunawa yayi tare da tankwashe qafafuwansa yana bud’e kular dake gabanta, “munzama ‘yan gatan baffa Usman meye yasa aka kawo mana” STORY CONTINUES BELOW  Yafad’a yana qarasa bud’e kular, “wow my fav…” “Kana son jalop rice kenan?” “Sosai kuwa habibty musammamn idan tasha kayan ciki, wannan aikin Inna Bilkisu ne don tafi kowa sanin abubuwan dana fiso aduniya in kika cire su baffa da innar mu agidannan.” Murmushi tayi had’e da mik’ewa taje ta d’auko plate da cokula biyu ta zuba abincin ta ajiye masa agabansa, ledar hannunsa ya miqa mata had’e da cewa. “Ungo wannan kisa a electric tunda naga akwai nepa sai ki gyara mana.” Hannu biyu tasa ta karb’a tana fad’in “Angode ALLAH ya qara bud’i.” “Amin ya rabbhi, amma jeki ki ajiyesa kitchen sai kidawo muci abincin.” Bayan sun kammala ya shiga toilet don ya watso ruwa ita kuma tawuce kitchen wajen aikinta, yana fitowa yadawo falo yacire fridge d’inta dake cikin kwali ya jona, cikin ‘yan sakanni yafara sanyi yaje ya d’auko sauran youghout d’in da suka rage jiya tare da wanda yazo dashi daga wajen Yaya hawwa yasa a fridge, tsakar gidansu ya leqo yakira Yusuf yabashi nira d’ari yace yaje ya siyo masa ledar package water sannan yakoma ciki, kitchen yanufa ya samu tana yanka albasa ya rungumota tabaya had’e da turo kansa ta wuyanta ya yimata kiss, murmushi tayi ta d’ago kai tana kallonsa, “cikani mana kada in yanke.” “Bazaki yanke ba tunda ina wurin, natabbata kaifin wuqa bazai iya cutar dake ba agabana.” “Hmm to ai shikenan.” Tafad’a tare da ajiye wuqar agefe, “Aw baki yarda bane?.” “A’a nayarda, kawai nagama yankan albasarne Bari in zuba kafin ruwan su ida tsanewa.” Had’e da jaye jikinta daga riqon daya yimata, daidai lokacin yusuf yayi sallama yana fad’in, “Yaya ga ruwan.” Fita yayi ya karb’a tare da cemasa “Yusuf ba zakazo kugaisa da auntyn taka ba?.” Qarasa shigowa yayi tare da d’an d’aga muryarsa yace “Aunty ina wuni?” Rashida dake kitchen tajiyo ana gaisheta tafito had’e da cewa, “Lafiya klw, kana lafiya.” “Lafiya klw” yabata amsa sannan yawuce abunsa, “Yusuf kenan d’an gidan baffa Ali.” Nuraddeen yafad’a yna kallonta, “ALLAH sarki yaron tubarkallah kyakkyawa dashi kamar kai.” Taqarasa maganar tana dariya tare da komawa cikin kitchen ganin yanda ya juyo yana harararta irin da wasa d’innan. Kai ruwan yayi yasa a fridge sannan yadawo cikin kitchen d’in tare da jinginawa ajikin qofar yana kallonta, “me kikace? Yusuf mene?” “Ni! Bance komai ba fa.” “Banyarda ba ALLAH sai kin sake maimaita abunda kikace” Yafad’a tare da fizgota tafad’o jikinsa, qurawa idanuwanta kallo yayi itama tabishi da kallo hannunta na dafe da qirjinsa, “maimaita abunda kika fad’a.” Taji yasake furtawa cikin wata kasalalliyar murya, turo d’an bakinta tayi zata jaye jikinta daga riqon daya yimata ya sake matseta sosai, “Karfa naman yaqone.” Tafad’a tana cuno baki gaba, tagefen da tukunyar take yad’e karkata kansa yana kallo kafin yace. “Ok inajinki, maimaita nace,” “Kai malamina, cewafa nayi kyakkyawa da…” Kafin ta qarasa ya game bakinsa da nata yana sakar mata wani irin passionate kiss, kafin nan yace, STORY CONTINUES BELOW  “Daga yau bana son inji wannan bakin naki ya yabi kowane irin namijine agabana kinji ko?” Jikinta a mace ta d’aga masa kai had’e da cewa. “Kayi hak’uri baza’a sake ba.” Kiran sallar la’asar da yaji yasa ya kauda zancen had’e da cewa. “Habibty bari naje nayi la’asar idan kin qarasa Aysha zatazo ta rakaki cikin gida kigaishesu daga nan siki dubo innar mu da jiki don batajin dad’i ni Kuma daga cn zan biya wajensu kamal zasu rakani yarimawa wajensu baba balarabe nayo godiya” “Don ALLAH in shiraya zakuje dani nagano ummata?.” Tafad’a had’e da marairaice fuska kamar zatayi kuka, bayason ranta yab’aci don haka kawai yace tashirya, amma yafad’i hakanne bawai don zai dawo ba sai don karta aza masa rigimar da zata jawo b’acin ranta. Cikin d’oki tarungumesa had’e da cewa “Sai kadawo bari nayi sauri naqarasa aikin.” “Ok amma kifara shiga kigaishesu tukuna kafinna nadawo d’in kinji ko.” ‘Daga masa kai tayi ya sakar mata murmushi tare da yimata kiss a goshi sannan yawuce d’aki yayo arwala tare da sauya kayan jikinsa izuwa manyan kaya ya feso turare yafito yana gyara zaman hular kansa, kallo d’aya tayi masa taci gaba da kwashe naman tana fad’in “Tubarkallah malamina kayi kyau.” “ALLAH habibty?.” “Sosai kuwa, adawo lafiya nima bari naje na shirya kafin kadawo.” Murmushi yasakar mata sannan yafice daga sashen, inda Yaya hawwa yasake shiga ya dubota da jiki sannan ya shiga shiyar baffa Ali har lokacin bai dawo ba Inna ruqayya kad’aice zaune tana yiwa munira fad’a akan tazo ta tsefe kanta, tana ganinsa tayi shiru tare da d’auke kai gefe. “Inna ruqayya ina wuni?.” “Lafiya” Tafad’a tana sake juyar da qeyar kansa gefe, idanuwansa ne suka sauka akan muneera data wani dashe haqora tana susar kai had’e da kallonsa ya zabga mata harara yana fad’in. “Ke lafiya wannan kallon?.” “Ina wuni yaya.” Tafad’a tana sake bayyana fara’arta garesa, tsaki yaja had’e da miqewa yabar wajen, yana jin inna ruqayya na fad’in. “Iskancin banza da wofi, har ni za’a gwadawa cin gira kusa da ido, yaro da SANNU SANNU zaka zo hannuna da Kai har waccan ‘yar iskar jarababbiyar yarinyar daka kawo sai kun yabawa aya zaqi, ke kuma zaki tashi ki tsefa kan ko sai nasa wannan tab’aryar na makeki.” Tafad’a tare da jawo tab’aryar dake gefenta, “Kai Inna don ALLAH abar tsifar nan zuwa jibi…” Bata rufe bakiba taga tayo kanta da tab’aryar ta tashi da gudu tabar wajen tana susar kanta. Shiyar baffa Usman yanufa Inna Bilkisu na tankad’en gari shi kuma baffa Usman na arwla da sauri saboda jin ana qoqarin tada sallah, a tsaitsaye ya gaisheta ta amsa cikin fara’a tare da tambayarsa iyalin tasa, murmushi kawai yayi yace. “Inna sannu da hidima ALLAH yasaka da alkhairi ya qara bud’i.” “Amin nura, ai babu komai d’a nakowa ne, kaidai kakula da amanar yarinyar mutane daka karb’o, ALLAH yabaku zaman lafiya, “Amin inna dama cewa nayi ko Aysha zata rakata cikin gida tagaishesu?.” “Af kaji nura da wata magana, Aysha ai qanwar kace ko bak fad’amun ba kanada ikon aikinta duk inda kaga dama balle nan cikin gida maza ka hanzarta kaje kasamu sallah kada jam’i ya wuceka in sha ALLAH babu wata matsala.” Kusan tare suka fita da baffa Usman cikin sauri sauri don su samu ayi jam’in dasu, Duk inda yakamata akai Rashida acikin gidan Aysha ta kaita in banda wajen yaya hawwa da baffa, shima d’in Inna Bilkisu ce tace tabari idan nurah yadawo sai sutafi tare, duk cikin gidan babu inda Rashida tasamu matsala hatta ga ‘yan uwansa da suke uba d’aya Wanda b’angarensu nacan gefe sai wajen Inna ruqayya, tasha tambayoyi da maganganu kala kala da kallon banza amma da yake gaba d’aya hankalinta baya wajen saboda ganin yanda magrib ta gabato bai dawo ba zancen zuwansu gida tagano ummata, shiyasa ko ajikinta don bata maji wasu maganganun ba Aysha ce kawai taji itama taja bakinta ta tsuke tamkar bataji ba. STORY CONTINUES BELOW  Har akayi sallar isha’i Rashida nazaune tana jiran dawowarsa amma shiru hakan yasa tad’auko wayarta da tunjiya data ajiyeta cikin jikkar hannuta bata sake waiwayarta ba sai yanzu da yake tasan wayar akashe take shiyasa tana d’aukowa tayi saurin kunnawa, tana gama logging tafara qoqarin lalubo lambarsa saiga kiransa ya shigo, cuno baki tayi sannan ta d’aga wayar kamar zatayi kuka tace. “Shine kayi tafiyarka kabarni ko?” ‘Dan murmushi yayi don dama uasan za’ayi hakan sannan yace. “Yihaquri habibty koda nakammala sallah nasamu suna jirana a mota kinga bazai yuyu in b’ata masu lokaci ba, amma nayarda nayi laifi ayimun afuwa ga munan munkusa qarasowa gida.” “Ai dama nasan haka zakace, shikenan ALLAH yakawoku lafiya, ya umma dasu baba?” “Lafiya klw suke ga saqonan sun bayar akawo maki,” “To shikenan sai kadawo.” “Yawwa habibtynah I love you.” “I luv you too” itama tafad’a akunyace sannan takashe wayar, Bayan yadawo yaci abinci ya watso ruwa ya huta lokacin har qarfe tara na dare yayi suka fito tare da rufo qofar tana saye da hijabinta, d’akin Yaya hawwa suka nufa yayi sallama tana kwance tabashi izinin shigowa tare da qara nishin da takeyi, “Shigo nura har yanzu dai jikinnan ya qiyamun duk da dai ciwon cikin yafad’a gudawar daice har yanzu.” Tafad’a tana qara mimmiqewa akan gadon batare da tasan tare yake da ita ba sai daya koma gefe yana cewa Rashida dake lab’e bayansa gabanta na dukan uku uku. “shigo mana” Wata irin zabura Yaya hawwa tayi sai kace ba itace tagama nishi tana fad’in har yanzu jikin nata yakasa koma mata daidai had’e da cewa. “Fita, fita, fita tsaya can bkin qofa Ina zuwa, Kai ma tashi fita tabarma na nan gefe ka shinfid’a ganinan fitowa” tana nuna masu qofar fita da hannu, jikin Rashida na rawa tajuya zata fita da sauri yariqo hannunta, “Haba innar mu keda bakida lafiya mezaisa sai kin wani fita, Rashida cefa ba wata ba ni kuma d’anki ne, me zaisa kice muzauna awaje.” “Kaga kayi abunda nace maka, idan Kai d’ana ne ita wannan abarfa, karka manta shifa bare ba’a bashi amana Taya za’ayi inbarta tashigo tagane mani sirrin d’aki asamu damar cutar dani, maza kufita nace.” Juyawa yayi yana riqe da hannunta yana d’an mammatsawa ahankali saboda tasamu suka fito d’akin, Tabarmar dake gefe Rashida tajawo yana kallonta ta qaqaro murmushi ta sakar masa had’e da shimfid’awa ta suka zauna, murmushin shima ya sakarmata kafin Yaya hawwa tafito a dudduqe ta zauna abakin qofar shiga d’akin nata, kallonta yayi yace “Ina wuni innar mu, ya qarfin jikin?” “Lafiya klw” tafad’a fuskarta ad’aure tana qarewa Rashida data sinne kanta qasa kallo da yake akwai wuta, d’ago kai Rashida tayi batare da tasan tana kallonta ba tace, “Ina wuni? ya qarfin jiki.” “Lafiya” ta amsa mata tana dalla mata wata irin muguwar harara, addu’a ta shigayi cikin zuciyarta saboda tasamu sauqin yanayin da take jin kanta aciki, can tajiyo dirar muryar Yaya hawwa akunnuwanta. “To atashi atafi idan shikenan Ina so inyi magana da d’ana.” Jiki ba qwari Rashida tamiqe tabar wajen. “Kai nura nifa inkan bid’ar lafiya ga yarinyar nan kada ka koma kawo man ita shiyata saboda natsaneta bana son ganinta ko kad’an.” “Haba innar mu, ai yakamata ace ko albarkaci na taci, bai dace ace kinyi mata haka ba ko kad’an, don ALLAH kicire wannan tsanar da kikayi mata tunda batada dalili.” STORY CONTINUES BELOW  “Iyyeee lallai nura kace wani abu, wato ni zaka gwadama cewa kaima cikakken namiji ne yanzu saboda waccan ‘yar abar, koda yake bansan wane kalar surk’ulle akayo maka ba kabi ka lashe dole kafad’a mani magana, to bari kaji nafad’a bana sonta zo ka dokeni, yarinya bare da ita har kace banida dalilin tsanarta bayan ta ruguje mana al’adar gida.” “Haba innar mu, al’adafa ba addini bace..” “Kai ni tashi tafi kabani waje ban iya sauraren wud’annan suruttan naka.” “To jikin fa?” “Nawarke tashi kaje.”tafad’a cike da takaicins. “ALLAH yabaki hak’uri innar mu seda safe.” Yafad’a tare da miqewa yafice, yanaji tasaki wani uban qyacci dake nuna akwai wata aqasa amma ransa yaroqi ALLAH ya fahimtar da mahaifiyarsa taso matarsa farincikin sa… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/7, 10:03 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___25💎 Koda yafito yasamu bata wajen kuma babu alamar takoma part d’insu don arufe yake, shiyar Inna Bilkisu ya leqa ko zai gata acan, cikin sa’a ya hangota gefe zaune ita dasu na’ima da fadila yayun Aysha suna fira ita kuma Inna Bilkisu na d’aura jiqaqqar ayar da take sayarwa, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya gaida Inna Bilkisu had’e da cewa Rashida. “Ashe nan kika shigo?” “Eh nafita d’auko ayar nan ne naganeta tsaye abakin qofar shiga shiyarku shine nace tazo nan tajira kafito saboda wajen akwai sauro sosai.” Inna Bilkisu tafad’i haka tana kallon Rashidar data noce kanta qasa tayi kamar batasan da shigowarsa ba saboda kunya. Sosa d’an qeyar kansa yayi had’e da cewa “eh da yake munshiga gaida innarmune shine nace tajirani muje wajen baffa.” Tashi kuje Rashida kinbar mijinki tsaye, miqewa tayi tayi mata seda safe itama su aysha nace mata “aunty seda safe” suka wuce. Kafin su isa wajensu baffa don da alama duk suna can d’akin da yake ya kalli fuskarta da yake akwai hasken wutar nefa ko Ina agidan yace “habibty kiyi hak’uri da abunda innar mu tayi maki kinji ko?” “Laa..bakomai mai malamina ai don ta isa ne, karka damu ni banji komai ba tunda mahai fiya take agaremu.” Murmushi yayi yan qara jin qaunarta aransa kafin ya jawota ajikinsa “Ina sonki sosai d’alibata.” dariya tayi tare da k’wace jikinta daidai lokacin suka iso bakin qofar shiga d’akin baffa sunajin tashin firarsu, sallama yayi suka amsa sannan yashigo ita Kuma tayi tsaye abakin qofar, Sosa kansa ya shigayi had’e da kallon baffa Usman yace, “Baffa zuwa tayi tagaisheku.” “A’a’ah to to Masha ALLAH, shigo da ita.” Leqowa yayi had’e da cemata tashigo, tashigo bakinta d’auke da sallama kanta na qasa a duqe ta duqa har qasa tana gaishesu, daga baffa sai baffa Usman suka amsa mata shikuwa baffa Ali gefe ya koma abunsa tare da d’aukar redion baffa ya kara akunne don kar yaji abunda suke fad’a, ya jiki tayiwa baffa had’e da yimasa addu’ar ALLAH yabashi lafiya, STORY CONTINUES BELOW  Ba baffa kad’ai ba hatta baffa Usman sun yaba da Rashida sosai tare da yimata nasiha akan tabi mijinta akan dukkanin abunda bai sab’awa ALLAH ba, kafin su sake had’asu subiyun suyi masu nasiha sosai akan haqqoqin junansu dake kansu, har suka gama baffa Ali baice komai ba saida baffa yace “To Ali kai bakace masu komai ba, yakamata a matsayinka na mahaifinsu kasa masu albarka da ‘yar nasiha ko kuwa?” Ganin Babu alamun wasa a fuskar baffa Yasa ya ajiye redion had’e da cewa. “To duk abunda yakamata ince ai kunce sai dai nayi d’an qari akai, Kai nura kasani zumunci ba wasa bane don haka kanunawa matarka tariqe maka ‘yan uwa da daraja kada ta walaqan tasu haka kaima, kada kanunawa matarka fifikonta akan ‘yan uwanka don ana rabuwa da mata amma ba’a rabuwa da ‘yan uwa, ‘yan uwa da kake gani duk inda suke sunfi bare..” “Haba Ali..” baffa Usman yafad’a ransa ab’ace da zimmar dakatar dashi baffa yariqe hannunsa alamar ya qyaleshi. Cikin isa yaci gaba da cewa “Kuma kar inji kar ingani kisake inji ance kin ware mana d’aya acikin ‘yan uwa duk d’aya muke, bama son had’e had’e balle anyi ance don cikin ahali guda kika shigo bamu yarda kiraba mana d’aya biyu ba, yanada ‘yan uwansa mata da kika iskosa dasu don haka kada mugun kishi yasa inji ance kin rabashi dasu ko kin hantaresu kinji nafad’a maki?.” “In sha ALLAH baffa nagode sosai” Rashida tafad’a cikin girmamawa da kuma sakin fuska, Hakan baqaramin yiwa su baffa Usman dad’i yayi ba don azatonsu nan take yarinyar zata nuna b’acin ranta wanda da wannan baffa Ali zai samu damar cusguna mata akoda yaushe, “To Rashida munsan gidanku Kuma munsan tarbiyarki don haka kiji kiqi ji ki gani kiqi gani, duk idan akace akwai taron mutane to dole saida hak’uri saboda sai kaga mabanbantun halayye da Kuma d’abi’u don haka kisa haquri kuma kiriqi ALLAHn ki ubangiji ALLAH yayi maku albarka ya zaunar daku lafiya kuma yabaku zuri’a masu albarka.” “Amin baffa ngd” tafad’a tana maijin dad’in addu’arsa. Miqewa Nuraddeen yayi aransa yana mai godewa ALLAH daba baffa Ali kad’ai yabashi a matsayin qanen mahaifi ba badon haka ba da baisan meye makomar rayuwarsa data iyalinsa acikin gidannan ba, amma yanzu koba komai yasan idan yaji d’aci awani b’angaren to zaiji dadda’an zaqi awani b’angaren guda. Saida safe yayi masu sannan yawuce agaba tana biye dashi abaya, adarare baffa Ali ke satar kallonta aransa yaji natsuwar yarinya ta kwanta masa arai duk da dai zuciyarsa bata buqatar haka, Amma Babu yanda zaiyi don yabon gwani yazama dole, ko maqiyin ALLAH ya kalli Rashida yasan batada makusa ta ko ina gata da shawar kallo a fuska, kallo d’aya zakayi mata taburgeka idan kuma ka zauna da ita cikin qanqanen lokaci zata shiga ranka wanda hakanne yasa cikin lokaci qalilan soyayyarta tayiwa Nuraddeen mugun d’auri azuciya. Kwanci tashi babu wuya awajen ALLAH tuninrashida tabuge sati d’aya agidan, abubuwa da dama sun faru na b’acin rai gareta amma bata tab’a tada kai ta kalla ba, kullum addu’arta shine kada ALLAH yabarta da dubararta acikin alamurranta kuma yabata haquri mai yawa agidanta, tana samun kula sosai awajen Inna Bilkisu dasu baffa Amma awajen yaya hawwa banda tsangwama da kyararta babu abunda takeyi, Babu ranar da zatazo bataje ta gaisheta ba kuma duk take saita b’ato mata rai, hakan kuma bazai hana gobe ta koma ba, musamman tacire kular da take zuba mata abinci kullum safiyar ALLAH Amma bai hana ta iskota da kwano tace tazubo mata abinci, wanki da sharar gida duka yimata takeyi amma koda yaushe dad’a tsigarta takeyi, kulawa da tarairayar da take samu awajen Nuraddeen yasa bata ajiye abubuwan agabanta balle su dameta, gashi akullum idan umma takirata cikin yimata wasiya da haquri take Wanda hakan yaqara zame mata linzami wajen gudanar da rayuwarta agidan, baffa kuwa tun tana jin kunyarsa har tadena ta d’aukesa tamkar mahaifinta, lokuta da dama takan shiga wajensa idan Nuraddeen baya nan da littafanta na arabiya ya dinga qaramata daga inda ta tsaya agida, wasu lokuttan kuma tayi masa gyaran d’aki ta share ta kawo masa abinci yaci, hakn kuwa ba qaramin tai maka masa yayi ba don daka kallesa zaka fahimci yasamu sauyi arayuwarsa, Wannan dalilin yanqara haifar mata da tsana mai qarfi azuciyar Yaya hawwa fiye da wacce take yimata ada, hakan yasa tasake d’aura d’amarar ganin tafidda ita gidan tako wane hali, duk ranakun da Nuraddeen yake gida Yaya hawwa batada wajen zama imba shiyarsu ba, haka zata ararrashe akan kujera tace akunna mata kallo adafa mata wannan a soya mata wancan, duk wani motsi da zasuyi akan idonta basuda wani shaqat, ga Nuraddeen mayen soyayyane yanaso akoda yaushe yadinga rab’ar jikin matarsa Amma bayada wannan damar saboda yanda tayi masu kane kane, tun Rashida Bata damuwa har taso ma jin daban saboda tun hutun sati biyun daya d’auka yagama sangartata da kuma lalatata da kalolin soyayyarsa, sun koma saidai suyi soyayyar a kitchen idan tace ta d’ago mata wani abun sai yayi kamar zai fita shi kuma anan yake samu ya lallab’a sushige suyita soyayyarsu kamar wasu munafukai, randa Yaya hawwa tagani kusan Tara masu jama’a ta tashiyi saboda masifa sai kace ba miji da mata ba, wai sun maida ita ‘yar iska sun barta a d’aki ita kad’ai, A ranar baffa yakirata yayi mata fad’a sosai akan taqyale yaran nan tadena shiga shiyarsu inbada qoqqwaran daliliba kada mutuncinta yazube, ai kuwa tayi masa tas tace bazata Dena ba in ya isa ya taso ya riqe mata qafafuwa ta hanata shiga, tsananin b’acin rai ranar daqyar yayi bacci saboda ciwon daya nemi taso masa kamar zai kashesa. Haka aka d’aukesa akayi asibiti dashi da safe aka duddubasa had’e da yimasa allurai sannan suka dawo, Aranar data tashi shiga shiyar duk saida tasa aka kirawo mata yaran gidan tace su ahigo suyi kallo suma su d’ebe qeyar ido, adako korarsu takeyi tana hantararsu muneera ba kunya itama tabisu sukaje suka cika d’akin tab ko masokar tsintsiya babu banda hamami babu abunda ketashi aciki, da yake lokacin har tagama girki kawai ta d’auki na baffa tanufi qofar fita riqe dashi zata kaimasa bayan tasa takunna masu kallon, tana wucewa Yaya hawwa tayi tsaki had’e da cewa “yarinya indai wannan gidanne sai nasa kinficesa da kaifin qafafuwanki.” Nuraddeen kuwa dama yana uwar d’aki kwance yana bacci sai dai kawai yajiyo yayar yara afalo da sauri yafito don ganin ko lafiya, Tsaye yayi cak yana kallon ikon ALLAH sake da baki tare da kallon mahaifiyar tasa data ashisahire saman kujera, tsabar b’acin rai baisan sadda yayi kukan kura ba yafara fatattakar yaran daga d’akin, aguje duk suka fita in banda muneera da tayi tsaye tana kallonsa had’e da susar kanta, wani irin zazzafan mari ya d’auketa had’e da cewa. “Uban me kikeyi anan.” Kallon yaya hawwa data miqe tsaye tana gyara zanenta tayi dafe da kunci tana kuka tace, “Inna ce..” tare da nunata, “Buhun uba!, yaushe nace kishigo ba yara nakira ba kika taso da wud’annan gwalmammin qafafuwa naki kika biyosu don kina sakarai, Kai kuma akan me zaka koresu suna kallonsu.” Shiru yayi hannunsa riqe da kunkuru ya sa d’ayan ya shafo kansa sannan cikin b’acin rai ya sake d’auke muneera mari yana fad’in, “maza kibar d’akinnan kafin naji maki” b’are baki tayi tare da fad’uwa zaune wajen tasa wata irin muguwar qarar da saida Yaya hawwa dake shirin komawarta tazauna akan kujerar tazabura tana fad’in. “Ke munafukar ALLAH tashi kifita kafin nima naqara maki.” Rashida, Rashida, Rashida, Nuraddeen yashiga k’wala mata kira ransa ab’ace, dama gashi cikin b’acin rai ya wuni saboda halin da mahaifinsa ke ciki, basu jima da dawowa daga asibiti bane yasamu ya kishin gid’a sai ga wani b’acin ran mahaifiyarsa na neman qara masa…. [7/9, 12:00 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___26💎 Rashida kuwa dake can d’akin baffa takai masa abinci bata san wainar da ake toyawa anan ba saida Aysha yarinyar Inna Bilkisu ta iskota aguje tafad’a mata, murmushi kawai tayi batare data nuna abun yadameta ko kad’an ba taci gaba da yiwa baffa yankan farcen da take yimasa don koda tashigo ta iskosa yagama cire na hannuwa yana dubarun yanda zai duqo ya cire ta qafafun shine takarb’i rezar tana qarasa masa suna d’an fira jefi jefi.+ Muryar Aysha dake a tsaye har lokacin ta tsinkayo daga dogon tunanin da take akan ynayin rayuwar da take ciki dangane da matsalolin uwar mijinnata na yau da kullum tana fad’in, “Aunty fa Yaya nakiranki.” Adai dai lokacinne tariqe farcen qarshe da zata qarasa cirewa baffa akaifar, saida tacire sannan ta d’ago kai tana kallonta had’e da cewa. “Jiki ganinan tafe kinji.” Kallonta baffayayi lokacin tana mik’ewa daga zaunen da take bayan ta d’auki k’yallen data aza qasan qafafuwan nasa qumbar da take yankewa na zuba akai ta kakkab’ik kesa awaje tadawo ta lunkesa ta mayar a inda yasa tad’aukosa d’azu. “A gaida Rashida ALLAH yayi maki albarka, sai nakeji gaba d’aya jikina yayimun sayau tamkar an d’auke mun wani abu akai.” Baffa yafad’a yana jujjuya yatsun hannuwansa, dariya tayi had’e da cewa. “Kasan dattice idan ta tararwa mutum shiyasa wanda suka saba yankawa idan tataru basajin dad’in zama da ita ajiki, baffa bara naje nadawo nazuba maka abincinka kaci sai kasha magani.” Yana kallon qafafuwansa yanda faracen sukayi masa tas saboda shi mutumne mai tsananin zafta da son gyara jiki yace. “To jeki, ALLAH yasa kigama lafiya, yakawo maki rabo Mai albarka.” Akunyace tabar d’akin batare data amsaba tana murmushi tanufi qofar shiga part d’insu, tana kawowa Inna ruqayya nakawowa itama saboda qarar ‘yarta data jiyo, qoqarin kaucewa Rashida tayi ta bata hanya tawuce amma saboda rashin imani irin na Inna ruqayya tasa kafad’a da qarfi ta mangajeta tafad’a ajikin ginin shiyar tasu kanta kuma yabugi gambun qofar tayi baya baya tafad’awa sauran buloluwan da akayi aikin sashensu dake ajiye gefen jikin ginin. Cike da azaba zafin buguwar da tayi tasaki wata irin qarar da saida Nuraddeen dake falo zaune ya dafe kansa zabura, da sauri yafito sukaci karo da Inna ruqayya da babunko d’igon imani da tausyi atattare da ita tabaro Rashida can kwance ta tahowarta tana masifar waya tab’a mata ‘ya, ko kallonta beyi ba shima ya wucikke warsa tare da tsayawa bakin qofar ya leqo don ganin ta Ina yaji muryar qarar Rashida, daidai lokacinne yaga Inna Bilkisu tarugo aguje tare da ‘yarta fadeela tana fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun Kai ruqayya wannan wane irin rashin imanine haka ki bangaje yarinyar mutane tafad’i kuma duk da kinji qararta bazaki tsaya kiduba halin da take ciki ba.” Har ta aza qafarta tashiga d’akin tajuyo cike da maseefa tadawo don dama jiraye take da inna Bilkisu, bangaje nura tayi dake tsaye bakin qofar kamar an dasa yana kallon ikon ALLAH, gaba d’aya saboda yanda gaskiya tayi masa yawa kasa cewa komai yayi sai bin Inna Bilkisu data tallabota tana d’an bubbuga gefen uncinta had’e da kiran sunanta yakeyi. “To munafuka algunguma, sarkin ashibanci da son yabo, fad’i ba atambayeki ba tsabar kicifi da iyayi ina ruwanki, meya shafeki no aciki ko dake akeyine da zakizo kisamun baki, kinsan me tayi manine da zakizo kisamun baki, Ina yanzu kika jiyo qarar muneera acikin d’akin nan Amma tsabar mugunta Ina kallonki ko ajikinki tunda ba ‘yarki bace, sai yanzu don antab’a bare Zaki taso mana da wani migun bakinki kisa mani baki, to wallhi ahir d’inki Bilki da shiga sabgata ko inyi maki rashin mutunci, ni uban waye nasakawa baki da aka tab’amun tawa ‘yar.” Inna ruqayyace tafad’i haka tare da fitowa tayi tsaye akansu batare data damu da ganin halin da Rashida keciki ba. “Fadeela jeki d’ebo mun ruwa ki kawo inaga yarinyarnan suma tayi.” Da sauri fadeela tabar wajen taje ta d’ebo ruwan takawo Inna Bilkisu ta karb’a ta yayyafawa Rashida. “Mtssssss.. ALLAH ma yasa tamutu idan taso ba abunda yashamun kai iyayenta keda asara bani ba.” ‘dago kai Inna Bilkisu tayi had’e da kallonta hawaye cike da idanuwanta, kasa magana tayi ta maido kanta had’e da sake zuba ruwa a hannunta tashafawa Rashida, wata irin doguwar ajiyar zuciya Rashida tayi tare da dafe goshinta dake mata rad’ad’i tana fad’in. “Wash..” “Sannu Rashida.” Inna Bilkisu tafad’a tana kallon inda ta dafe goshin nata ya kumburo, sai alokacin nurah ya qaraso wajen idanuwansa sun kad’a sunyi jawur kamar an watsa masa barkono aciki, wani irin zugi da rad’ad’i yakeji kallon halin da matarsa keciki amma yakasa tab’uka komai saboda jin nauyin Inna Bilkisu dake wajen tana kula da ita, had’a idanuwa yayi da ita ta sakar masa murmushin daya tabbata cikin qarfin hali tayisa don takwantar masa da hankali, “Nura d’auki matarka kushiga ciki, kaga goshinnan nata yabugu kad’an lullunda matashi koya saki, ALLAH yasawaqe kuma yaqara maku hak’uri.” STORY CONTINUES BELOW  Ya tsinkayo muryar Inna Bilkisu nafad’a cike da damuwa, duqawa yayi da niyar riqota, Inna ruqayya tariqo wuyan rigarsa had’e da cewa. “Ai wallahi baaka isa ba, mutum befi mutum ba balle ka dakarmun ‘ya na qyaleka, wuce muje naga ubanme kayiwa ‘yar tawa take wancan reren kukan.” Ta jasa suka nufi cikin sashensa yana biye da ita, wani irin tuquqi yakeji aransa da badon matar qanen mahaifinsa bace ko wace yau sai ya koya mata hankali, qoqarin miqewa tsaye Rashida tayi hawaye na zubo mata daga cikin idanuwanta Inna ruqayya tayi saurin d’agata had’e da riqota sosai tanufi cikin shiyar tata. “A’a Inna Bilki bana son ganin abunda zai faru tunda tsakninsa ne da ‘yan uwansa, kawai ki kaini shiyarki” Rashida tafad’a tana sake goge hawayen dake faman kaida kawo saman fuskarta akaro na ba adadi, Kiyi hak’uri Rashida in sha ALLAH komai zai wuce.” Sashenta tanufa da ita suna kai bakin dangaramar da zaka taka su ahiga cikin d’akin jiri ya sake d’ibarta da kad’an tafad’i, da sauri fadeela tariqota ita da Inna Bilkisu tana dafe da kanta sukaqarasa shiga da ita. Acan cikin d’akin Rashida kuwa yaya hawwa na can hakince saman kujera tana kallonta, ita kuma muneera na zaune sai faman reren kuka takeyi tana susar kai sai kace wata sabuwar amaryar da akayiwa auren dole, duk abunda akeyi tana jiyosu daga tsakar gidan amma tayi kamar batasan anayi ba, bini bini take juyowa tana kallon muneera dake kuka can kuma sai tayi shiru ta qurawa tv ido tana susar kai tace. “Au munafuka dama kukan na qaryane! Wato anga abunda sai gidan masu kud’i ake gani d’an ba’a saba ba kin baza idanuwa sai kallo kike yi, ja’ira kawai.” Ta kaimata dunguri a qeyar kai, sake fashewa da kuka tayi tana cije gefen d’an kwalinta had’e da sosa qeyar kan nata data daka, Inna ruqayya ce tashigo d’akin har lokacin tana riqe da kwalar rigar Nuraddeen tana fad’in. “Wato kasan matar taka bata cikin d’akin shine ka kamamun ‘ya ka zalunta to wlh bazan yarda ba, ai kana ganinta ka zame kaje ka auro wata shine yanzu kake nema ka cuceta don baka samu yanda kake soba, wuce muje naga abunda kayimata” muneera naganinta ta taso tanufo inda take tana sake tab’e baki. “Buhun uba me zan gani haka ruqayya, d’an nawa kika shaqowa wuya haka sai kace wanda yayi sata! Uban me yayi maki.” Cikasa Inna ruqayya tayi kafin tariqo mueera tana fad’in. “Aiho dama kina cikin d’akin Yaya hawwa?, Kukan muneera najiyo nazata shikad’aine aciki shine na tasosa agaba yazo ya fad’amun abunda yayi mata gabanta har take wannan reren kukan saboda nasan duk abunda yasata kuka to ba kad’an bane” Tafa hannuwa Yaya hawwa tashigayi tana sallalami had’e da gyara d’aurin zanenta kafin tace, “Ke ruqayya sharri zakiyiwa yaron nawa don kinga bayyi magana ba?, shi dake da matan mezaiyi da ‘yarki yarinya kamar an tsoma kaza acikin ruwan zafi anfiddata, tsigalalliyar yarinya munafuka kawai da ita, mai yagaggen baki zakuyi masa sharri, to maza kufita kafinna karya mata wud’annan gwalmad’ad’d’in qafafuwan nata.” “Dakata yaya hawwa gaskiya nagaji da wannan cin kashin naki, aci zalin yarinya agabanki bazakiyi magana ba kuma sai kiqara mata da kushe mata halitta, gaskiya nagaji kidena don nima ina son abuta a haka, shikenan daga zuwa tambayar meyayi mata sai kidinga cab’a mani magana…” Bata rufe baki ba ta Nuraddeen yafito a fusace riqe da belt a hannunsa dama tuni tsananin b’acin rai yasa ya shige uwar d’aki yayi zaune bakin gado yana tunanin ko meyi zai yimata ya rage rad’ad’in abunda tayiwa habibty d’insa, babban takaici ma wai shi Inna ruqayya ke zargi akan muneera ko mezaiyi da ita, meye ma zai tsinta ajikinta da zatayi masa wannan sharrin, yana zuwa ya finciko muneera daga jikinta idanuwansa jajir ya jefar da ita a qasa had’e da nuna Inna ruqayya yace. “So kikeyi nafad’a maki abunda nayi mata ko, to bari kigani na nuna maki, bari kiga kome nayi mata yanzun nan.” Jibgar muneera yafarayi da belt d’in yana watsa mata tako ina tana ihu, sheqeqe Yaya hawwa takalli Inna ruqayya data turo idanuwa waje tana kallonsa tace “yawwa qarawa shegiyar, yimata lilis munafukar yarinya kawai, daga mari sai uwarki tabisa da mugun sharri, yita jibgarta sai tagane shayi ruwane?” Tafad’a tare da rab’awa ta gefensu tayi tafiyarta, qoqarin riqesa Inna ruqayya ta shigayi tana tsigarsa amma da yake zuciyarsa tariga tarufe a fusace ya d’ago kai yana cewa. “Wlh kibar ganin ke matar qanen mahaifinace duk kika matso wajennan saina had’a dake.” Ganin yanda fuskarsa ta sauya yasa tayi gum da bakinta tayi waje tana haragagon neman taimako, duka kam ranar muneera tashashi tun tana ihu har takasa shi kuma yace bazai dena dukan taba har sai lokacin data bar d’akin da qafafuwanta yanda gobe koda wasa akace tashigo shiyarsa bazata shigoba, Inna ruqayya kuwa tayi ihun neman taimakon har tagaji babu wanda yazo ai kuwa tana ta zundumawa mutanen gida zagi wai duk munafukaine sunaji za’a kashe mata ‘ya kowa ya qyale, STORY CONTINUES BELOW  Inna Bilkisu kuwa ji tayi kamar ta taka tsabar farinciki don koda baiyi komai akai ba ta d’au alwashi akan sai tayi mashi fad’a daya tashi tsaye ya qwatowa matarsa ‘yancinta a gidan matuqar shi ba lusarin namiji bane, sai gashi da kanshi yayima kansa fad’a. Yaya hawwa kuwa dama sashenta tawuce tashige d’aki had’e da haye gadonta ta soma bacci batare data sakebi ta kansu ba, su baffa Ali da baffa Usman su kuma basa gida balle su kawo mata d’auki , Sai da jikin muneera yayi tib’is tukuna tafara qoqarin k’watar kanta daga hannunsa ganin babu sarki sai Allah, da jan gindi tafito shiyar Inna ruqayya na tsaye bakin qofar takasa komawa sai faman zunduma masa zagi takeyi, da sauri ta riqota had’e da ida jawota tafito sukayi shiyarsu tana kuka yace. “Wannan shine abunda nayi mata, kuma kad’an tagani, idan nakoma ganin qafarta cikin shiyata saina maida ita gurguwar qarfi da yaji.” Sannan ya juya yakoma ciki, Toilet ya fad’a had’e da d’ibar ruwa acikin durom d’in dake ciki yafara sakarwa kansa yana sakin wata irin ajiyar zuciya. Yajima aciki kafin yafito ya hau gyaran falon had’e da sharesa tass, feffesa room freshener yayi soboda tsamin da yaji d’akin nayi sannan yanemi kujera mai zaman mutum uku ya kwanta rigingine kansa na kallon silin zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa Acan shiyar Inna Bilkisu kuwa saman gadonta suka kwantar da Rashida, hannuwanta da idanuwanta tashiga duddubawa tana son gaskata abunda zuciyarta ke rayamata akanta tun kwanaki biyu da suka wuce saboda yanda ta canza, murmushi tayi had’e da cewa, “Alhamdulillah ALLAH kaine abun godiya.” har lokacin takasa Dena murmushin da takeyi, kallonta fadeela tayi had’e da cewa, “Inna menene?.” Bata tanka taba saidai kallon Rashidar data koma yi tana qoqarin rufe idanuwanta saboda baccin da take ji, baccinta mai isarta tayi kafin nan tafarko tana jin wata irin matsananciyar yunwa dama d’azun data gama abinci bata samu taci ba saboda tare sukeci dashi shikuma alokacin bacci yakeyi, Kasancewar koda ta tashi bakowa ad’akin yasa tasauko saman gadon had’e da fitowa bakin qofar d’akin ta saki wata uwar hamma dake nuna ba qaramar yunwa take jiba. “A’a Rashida har kin tashi?.” Inna Bilkisu dake sharar cikin rumfar tasu tafad’a tare da d’agowa tana kallonta. “Eh inna barka da marece, shara kikeyi?.” “Eh wallahi wajenne ya d’anyi datti ga baffanku yana kan hanyar dawowa ke sanshi baya son datti ko kad’an, ya qarfin jikin naki?” “Alhamdulillah da sauqi Inna bari na riqa maki.” “A’a ki barshi ai nakusa qarasawa, maza jeki tun d’azu mijinki na ciki nasan ran nan nasa a cunkushe uake yanzu, kuyita haquri har ALLAH yakawo qarshen wannan al-amarin kinji ko.” Duqar da kanta qasa tayi tana wasa da ‘yan yatsun hannunta tana murmushi sannan tabar wajen, har takusa shigewa Inna Bilkisu tace, “Au Rashida.” Juyowa tayi tana kallonta taci gaba da cewa “dama nace ki kula da kanki saboda yanzu bake..” Bata qarasa ba saboda hango Inna ruqayya da tayi nafitowa daga cikin d’akinta sai tayi shiru had’e da cewa “Jeki rashida maya magana dake anjima” “Mtssss…munafucci kunun kanwa!.” Inna ruqayya tafad’a tana jefo wata tasar Inna Bilkisun data gani cikin rumfarta. Batace mata qanzil ba taci gaba da shararta ita kuma tawuce shiyarta batare data fahimci kome Inna Bilkisun ke nufi ba. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/9, 10:52 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 STORY CONTINUES BELOW  _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___27💎 Tana shiga Kai tsaye kitchen tashiga ta d’ebo abincin a plate, tun kafin taqaraso cikin d’akin tasomaci saboda azabar yunwar da takeji, kwance ta iskosa idanuwansa arufe amma babu alamun bacci yakeyi saboda yanda k’wayar idanuwansa ke rawa, qasan carpet a bakin kujerar da yake kwance ta zauna tana cigaba da cin abincinta hannu baka hannu akushi, a hankali ya jaye hannusa dake saman goshinsa yana kallonta fuskarta a sake tamkar babu abunda yafaru, abincin dake gabanta ya kalla sannan ya kalleta cike da tambaya, saboda iya saninsa tunda tazo gidan tare suke cin abinci yazu ko kimanin tsawon watanni hud’u kenan, to meye dalilinta nayin haka kenan ko haushinsa takeji ya tambayi kansa had’e da tashi zaunne yana kallonta. ‘Dago kai tayi ta kallesa tare da sakin murmushi daga haka Bata cemasa qanzil ba Kuma shima bai cemata ba sai data canye abincin tas had’e dayin gyatsa. “Alhamdulillah” tafad’a tana lashe yatsun hannuwanta har lokacin idanuwansa nakanta, turo baki tayi yasakar mata murmushi tare da miqewa ya d’auko mata ruwa a fridge ya miqa mata, karb’a tayi tasha sannan tamiqe tare da d’auke plate d’in takai kitchen, tray d’in data had’a abincinsu akai ta d’auko takawo agabansa ta ajiye sannan takoma saman kujerar kusa dashi ta zauna had’e da d’ora kanta saman kafad’arsa. “Malamina ka sauko kaci abinci, nabarka da yunwa ko?.” Seda yad’an harareta sannan yace. “Bazanci ba!.” ‘Dan turo idanuwanta tayi awaje tana qyaqqyaf tasu had’e da cewa, “meyasa?. Abincin da kafiso ne nayifa!” Taqarasa maganar tana b’ata rai tare da nad’e hannuwanta saman qirjinta, mintsili ya kaimata a kumatu had’e da cewa. “Saboda bakya son naci shiyasa kikaci naki bayan kinsan tare mukeci ko fushi kikeyi da nine akan abunda yafaru.” “Laaaa…wlh ba haka bane malamina, kawai yunwa nakeji sosai shiyasa na fara ci, atunanina ma bacci kkeyi, kayi hak’uri nazuba maka kaci nasan kana jin yunwa kaima.” “E.ehm bazanci ba.” Yasake fad’a yana nad’e hannayensa akan k’irji kamar yanda tayi d’azu ya juya mata baya, saqalo hannayenta tayi ga wuyansa ta rad’a masa akunne, “afuwan habibyyy..” taja qarshen cikin wani salo daya sashi juyowar da bai tashiba cike da mamaki don bai tab’a jin takirasa da wani suna ba inba malaminta ba, “me kikace habibty?, Pls sake fad’a naji.” Maqe kafad’a tayi had’e da cewa, “o’oh sai in kaci abincin tukuna zan fad’a har sai kace ya isa” zamewa tayi daga kan kujerar tana dariya ta zubo masa abincin a plate, jallop rice ce tasha kayan ciki da kifi dasu irin baqin kifinnan gasashshe mai d’an karen dad’i, saman kujerar tadawo tana riqe da plate d’in abincin da cokali aciki, d’ebowa tayi a spoon takai masa abakinsa ya juyar da kai gefe, “Meye?” “Kifad’a mana.” Yafad’a had’e da d’an d’aure fuska, dariya tayi sannan tace, “Shikenan! Nafad’a habiby, habiby, habibyyy..” bud’e baki yayi zaiyi magana ta tura masa cokalin abincin abaki had’e da sakin dariya, murmushi yayi tare da nunata da yatsa. “Ke ko?” Haka tadinga bashi abaki yanaci har yaqoshi ta tattara kayan takai kitchen ta dawo, miqa mata hannu yayi ya zaunar da ita a tsakankanin kafafuwansa ya turo kansa tagefen wuyanta. “Habibty!” Yafad’a cikin wata irin kasalalliyar murya, “uhmm, habibyn habibty!.” Shiru yayi na wasu mintota yana nazarin irin kalaman da zaiyi amfani dasu wajen bata hak’uri akan abunda yafaru, juyo fuskarta yayi yayi mata kiss saiti inda ya d’an kumburo a goshinta sannan ya sake maida kansa agefen wuyanta yace, “kiyi hak’uri, kiyi hak’uri, kiyi hak’uri bisa abubuwan dake faruwa, nasan cewa ba kad’an kike kauda kanki ga abubuwan da mahaifiyat da kuma wasu ‘yan uwan keyi maki ba, kwata kwata banajin dad’insu har ga ALLAH domin ke amanace agareni, nakan tsinci kaina cikin damuwa mai tsanani aduk lokacin da naga ana cutar mani dake, zuciyata na quna inajin wani d’aci a maqoshi domin babu abunda nake so araina duniya fiye da inganki cikin farinciki, zallar hak’urinki da tarbiyarki suke galaba akaina wajen kawar mani da damuwa badon haka ba inada tabbaci akan da tuni zuciyata da kuma rouhina sun daina aiki ajikina saboda kasa jurewa ganin duk wani abu da zai cutar dake, nayarda cewa shi so sa’ane kuma dacene tun a ranar dana had’u dake, domin kin zame mani gwana takowane fanni, a kyau kece gwanata, a hak’uri Banda yake, a iya kula da tarairayar miji kinfi mata dubu, girki tsafta da kawaici sai dai nace Masha ALLAH, Alhamdulillah domin duka nasamu awajenki, na tabbata kece alkhairina na duniya da kuma lahira don haka Ina mai sake baki haquri ga yanayin da muka tsinci kanmu aciki, natabbata wata rana zai zamo labari.” Tunda abubuwannan kefaruwa bata tab’a zaunawa ta zubar masu da hawaye ba sai yau, koshi saboda wani nauyine da takeji azuciyarta taji ya sauka saboda dad’ad’an kalaman daya fad’a mata hakan shine yayi silar zubowar hawayenta batare data shirya ba, wud’anda batasan da wace kalma zata fassarasu ba, na bak’in cikin abubuwan da suke faruwa da itane ko kuma na farincikin soyayyar mijinta dake lunkuwa azuciyarta. hannu yasa ya juyo da ita gaba d’aya suna kallon juna tare da tallabo fuskarta yana kallon kyawawan idanuwanta dake zubar da hawaye, bakinsa ya nufo dashi wajen fuskarta tayi saurin rufe idanuwanta hawayen dake maqale aciki suka samu damar gangaro, jira takeyi taji saukarsa akan nata amma sai taji akalarta sauya saboda harshensa da taji saman fuskarta yana lashe hawayen, sannan yadawo ga bakinta ya sakar mata wani irin french kiss daya sa ta sake lumshe idanuwa tana mayarnmasa da martani. Sunfi tsawon mintuna biyar ahaka kafin ya zare bakinsa daga nata had’e dasa hannuwa yariqe fuskarta yana kallon idanuwanta d’aya bayan d’aya, STORY CONTINUES BELOW  “Habibty kidena zubar da hawayenki domin duk d’igar da zasuyi suna yintane tamkar d’igar ruwan wuta abisa zuciyata, nasan ke jarumace kuma akoda yaushe nasara natare dake don haka kikara hak’uri kafin ALLAH ya yalwata mana mutashi nan kinji ko?” “Habiby ba Ina zubar hawayene akan abubuwan dake faruwane ba, hawayena na zubane adalilin samun nagartaccen miji kamarka, kalamanka nada matuqar tasiri agareni domin ako yaushe d’auke suke da saqonni masu ma’anar dake gamsar dani irin soyayyar da kake yimani Wanda hakan shine babban burina arayu, bana son wannan haqurin da kake bani domin mahaifiyarka ai mahaifiyatace hakama ‘yan uwanka nawane don haka duk runtsi zai jure komai akanka matuqar kana tare dani.” “Habibty bakyajin zafin abubuwan da ake yimaki ne?.” “Inaji mana amma girman soyayyarka bata barin hakan yayi tasiri azuciyata.” Tafad’a tare da rungumesa. Rungumeta shima yayi sosai tamkar wanda za’a k’wacewa ita yace. “I dont want to miss you in my life…, I love you for ever and ever and ever..” Rashida da wasu kalaman tafahimta wasu kuma bata fahimcesu ba tayi murmushi itama tace “Nima haka.” dariya yayi don yanada tabbacin ba duka ta fahimci meya ce ba amma tace itama haka duk da dai dad’ad’an kalamaine yayi bamasu illa ba. “Habibty kema me?” Yafad’a yana sake shigar da ita ajikinsa sosai. “Yanda kace mana.” Tabashi amsa atak’aice itama tana dariya, “Tom nagode gobe kishirya zamu fara lesson in sha ALLAH.” “Ni bana so.” “Ai baki isa ba.” Nuraddeen yafad’a had’e da sakinta yana yimata cakulkuli, cikin mintuna qalilan ya mantar da ita duk wani b’acin rai da takeji azuciyarta. Rayuwa kenan haka ALLAH ke jarabtar bayinsa da sukayi imani dashi akoda yaushe, baffa dai gashi da rai amma wasu abubuwan sun buwayesa, duk fitinar da akeyi yanaji Amma Babu halin tashi, ahankali yaji damuwa naneman tayar masa da ciwonsa yayi saurin jawo hisnul muslim d’insa yana karanta addu’o’in hammu wal hazan (damuwa da baqinciki) cikin ikon ALLAH yaji komai na gushe masa, Saida yaji yasamu sassauci da salama acikin ransa sannan ya ajiye yaci gaba da ambaton ALLAH. Bayan sallar magrib su baffa Ali sun dawo don basu shigo gidan ba saida suka gama sallah, baffa ya zayyane masu duk abunda yafaru agidan wud’anda kunnuwansa suka jiyo masa, sosai baffa Usman yaji ba dad’i sab’anin baffa Ali da yace. “Ni wlh Yaya nazata wani abun mai muhimmancin ne yasa ka tsaidamu gashi tun d’azu yunwa nakeji, ai indai muneera ce da uwarta abunda ma yafi haka zakaji, ni bari inje inci abinci inaga yafimun.” Yana gama fad’a yamik’e ya wuce sashensa, cike da mamaki suka bishi da kallo kafin su ahiga tunanin nemo mafita, Baffa Ali na shiga ko sannuda zuwa babu inna ruqayya da tun d’azu take zaman dakon isowarsa tace. “Alhamdulillah muje malan, wlh yau saika qwatarwa ‘yata haqqinta akan cin zalun da aka yimata.” “Ke ruqayya fara bani abinci tukuna yunwa nakeji.” Yafad’a yana zaunawa saman tabarmar dake shimfid’e abakin qofar d’akin, sanin zai iya birkice mata idan tamatsa masa da zancen yasa taje takawo masa abincin ta ajiye agabansa, ruwa taje ta d’ebo takawo masa jikinta har tsima yakeyi ta zauna tabasa labari, Yana gamawa tashiga bashi labarin qarya da gaskiya ya mik’e cikin b’acin rai yanufi shiyar Yaya hawwa yana k’walla mata kira, iskota yayi zaune tana cin abinci bisa ‘yar barandar dake cikin rumfarta akan kujerar tsugunno ta tsakar gida shima yanemi waje ya zauna. Saida takai loma abaki ta had’iye sannan yace. “Ina jinka Ali mike faruwa?” Cikin kwantar da kai yace. “Haba Yaya hawwa yanzu ace agabanki yaron nan zai kama ‘yar uwarsa yayi mata mugun duka baki d’au mataki ba.” STORY CONTINUES BELOW  “Uwarta taja mata.” tabashi amsa atak’aice tanaci gaba da tura lomar tuwonta hankali kwance. “Koma dai meye ai kamata yayi ace kin hanasa tunda ‘yar tawa ba jaka bace kuma ko meye ai kece kika jamata, babban abunda kebani takaici shine keda kikace bakyason yarinyar nan kin tsaneta meye na wuni kullum a d’akinta? Kodai yanzu kin fara amincewa da zab’in barene.” “Hmmm! Ali kenan, wai ku atunaninku zuwa d’akinta da nakeyi na ALLAH ne? Yaro man kaza ai duk wanda yace baya sonka to tabbas har amutu bazai tab’a sonka ba, ai tsuntsu biyune nake jifa da dutsi d’aya don haka ka kwantar da hankalinka, wannan shashashar ‘yar taka ita nakeyiwa yaqi amma ita da mahaifiyarta suna neman b’atawa shiyasa na zura idanuwa saboda kada ad’agoni, duk wani shiri nawa ya kammala don gaba d’aya nagama aiwatar da abunda na karb’o wajen malan bakada imani, k’waya d’aya yarage ina kammalasa zakaga aiki da cikawa..” Yaya hawwa taqarasa maganar had’e da miqewa tana d’auraye hannunta agefen d’akin. dashe hauru baffa yayi had’e da cewa. “ALLAH yaya hawwa?” “Naka wasane Ali, an fad’a maka ja da baya tsorone, ai tuni nashirya maka maina tsaf da zan yaqi waccan yarinyar mai kama da miyagun mayu, yanda nakejin natsaneta yanzu bana tunani zan iya d’aga mata qafa har sai tabar gidannan don haka idan harkana son gurinka yacika dole kadakatar da uwar iyayin nan da muneera daga shiga sha’anin Nuraddeen, inba haka ba kuwa to dasu b’ata mun aiki k’wanda na tabbatar na dakatar dasu nida kaina.”… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/11, 2:50 AM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___28💎 To shikenan Yaya hawwa yanzu nai magana, amma tuntuni sai zuba idanuwa nakeyi naga matakin da kikace zaki d’auka amma shiru yau gshi kimanin watanni hud’u kenan da kawota. “Kaji dai abunda nafad’a maka koma meye kawai kazuba idanuwa kagani.” Tafad’a tana qoqarin shigewarta d’aki, seda safe yayi mata sannan ya wucewarsa yana ayyana abubuwan da zasu faru idan burinsa ya cika. Yana fita Kai tsaye waje yayi sai bayan sallar isha’i lokacin har karfe 9 tawuce, yana shiga sashensa inna ruqayya ta sake tarbarsa da maganar cewa yayi “Kai ruqayya matsalata dake rashin hak’uri, yanzu dai ki kwantar da hankalinki munyi magana da Yaya hawwa kuma tace tana nan ta d’aukar mataki akan al-amarin.” “Hmm wane mataki zata iya d’auka akai bayan duk abunda yafaru dasa hannunta itace ummul aba isu tana kallo ya narkarmun yarinya agabanta batace komai ba, Kai nifa wlh nagama gano bata son auren yarinyar nan da yaronta, kaduba yanda take kashe wuni ashiyarta kuma wai don ta Rena mana da hankali tace bata sonta.” “Ashsha ana baki kina roqo, Bari in fad’a maki wlh yarinyar nan Yaya hawwa bata qaunarta tuni taje takarb’o magani wajen malan bakada imani…” Nan ya kwashe duk yanda sukayi da Yaya hawwa ya sanar da ita, lokacin muneera na kwance can acan gefen gado kafin takoma d’an d’akin da take kwana, Inna ruqayyace tace tabari har mahaifinta yadawo taji matakin da aka d’aukar masa na dukan daya yimata, wannan dalilin yasa tayi kwancenta nan ita da qannenta maza su uku ciki harda yusuf tana jiran dawowarsa. Baffa Ali daya saki baki yanata bata labari kawai sai yaga muneera ta taso tana susar kai tanufo inda suke zaune gefen gado tana fad’in. “Baffa ni babu ruwana da matarsa kawai so nake ku a auramun shi, wlh baffa Ina son ya nura sosai.” Zarar idanuwa baffa Ali yafarayi don bai zata muneera na cikin d’akinba da ko kad’an bazaiyi wannan maganar agabanta ba, STORY CONTINUES BELOW  “Yi haquri muneera, ai zancen yanda za’ayi aurenne muke tattaunawa.” Inna ruqayya tafad’a had’e da riqo hannunta, turo manyan lab’b’anta tayi cike da rashin iya magana tace, “Wallahi Inna qaryane, ai duk Ina jinku maganine zakuyi ko korar masa mata, yo a maimakon haka kuyi mani magani na auresa kurum..” da sauri tajawota had’e da toshe mata baki shi kuma baffa Ali ya dafe kai don yasan ALLAH kad’ai ke hana muneera taje ta watsa wannan magana, abunda basu sani ba hatta Yusuf idanuwansa biyu basuyi bacci ba qannensa ne kawai baccin ya d’auka. “Shiii muneera kirufa mana asiri kidena wannan zancen kada wani yajiki, yanzu da kike wannan maganar mu ba yarinyar mukeso tafara fita ba sai ke kuma ki auresa, kinjimun shashashar yarinya.” Inna ruqayya tafad’i hakan tana murgud’e mata bakin da hannu data toshe mata shi. “Kai Inna da zafi.” Muneer tafad’a itama tana jaye mata hannun sannan taci gaba da cewa, “ni ku aura munshi a haka ko mata dubu garesa ALLAH zan auresa balle d’aya, so kukeyi sai na sake shekarewa aci gaba da cemun kwancen gidansu nura wlh ALLAH ni nagaji da jira.” Taqarasa maganar tana fashewa da kuka, takaici ne yarufe baffa Ali kamar yatashi ya rufeta da duka shima, Amma yasan hakan na iyasa tafallasa komai don ba qaramar sakarya bace, lallashinta suka shigayi tare da tabbatar mata da cewa itama wannan shekarar kota halin qaqa saita auri masoyinta ya nura sannan suka samu tawuce d’akinta takwanta, fad’a baffa Ali ya shiga yiwa Inna ruqayya akan meyasa bata sanar masa da muneera na d’akinba ai da bai d’auko zancenba agabanta. “Yo kukan da taci yau ai sanin matakin da aka d’auka akansa kad’ai zaisa taji sanyi azuciyarta shiyasa nace ta zauna har kadawo.” Tsaki yayi had’e da juyawarsa ya kwanta cike da takaicinta da ita har ‘yar tata. A ‘bangaren su Nuraddeen kuwa ana gama sallar isha’i yadawo gida, d’akin baffa ya shiga ya gaishesa tare da yimasa ya jiki lokacin suna zaune shida Rashida tagama b’ab’balla masa maganinsa yasha bayan tazuba masa abinci yaci tana karanta masa wasu addu’o’in dake cikin littafin (adda’u wad dawab) littafin daya qunshi nau’o’in cutuka da kuma kalolin maganukkan da za’asha ayi amfani dasu don samun waraka, d’aya daga cikinsu take fad’awa baffa alokacin, wuri yanema a gefe ya zauna yan sauraren bayanin da take yiwa baffa. “Baffa kaga wannan addu’ar ana karantata ga duk wanda ciwo yayi masa tsanani kuma aka rasa gano kowane irin ciwone ke damunsa, sai a nemi ruwa masu kyau acikin madaidaicin kwanon shan ruwa, sai a nemo kanwa da gishiri a zuba aciki, anemo albasa itama a yayyanka ta aciki sai marar lafiyar yasa duka hannayensa acikin ruwan bayan ya saka duk wud’ancan abubuwan da aka buqata sai ya karanta qula quzzai (falaq, nasi da kuma ikhlas) kenan, sannan yakaranta ayatul kursiyu karatun na sauka acikin ruwan da hannayensa ke ciki, sannan sai ya karanta wannan addu’ar kamar haka ( _Bismillahi arqiq, wallahu yashfik, min kulli da’in mardud, wamin kulli aynin au aynil hak’k’imu ALLAHU yashfik, allahummah rabbannas, ashfi bil ba’as washfi antashshafi’i laa shifa’a illa shifa’uka, shifaa’allahu laa yugadirus saqama_). sai atofa acikin ruwan acire hannayen daga ciki, sai a d’ebi ruwan marar lafiyar yasha sannan ya tauna albasar dake ciki, asake d’iba yayo wanka dasu sauran sai a dinga watsawa ko ina a cikin d’akin da yake ciki ana fad’in ( _ikhrij aduwwallah_) har ruwan su qare, to da yardar ALLAH duk marar lafiyar da aka dage anayi masa haka ko ya dage da kansa yanayi zai samu sauqi da ikon ALLAH, kaga zuwa gobe idan ALLAH yakai ranmu sai mufara baffa saboda ba’asan in da dace yake ba ko ba haka ba.” Cike da farinciki baffa ya dafa kanta had’e da cewa. “Hakane ‘yata, ALLAH yayi maki albarka kuma yasa adace.” “Amin baffa.” Tafad’a tana rufe littafin fuskarta d’auke da murmushi, juyowa tayi gefen da Nuraddeen ke zaune ta gaishesa had’e da yimasa sannu da zuwa sannan tamik’e tabar d’akin tana yiwa baffa seda safe. Bin bayanta da kallo baffa yayi kafin yayi ajiyar zuciya yace. “Alhamdulillahillazi bini’imatihi tatimmusswalihat, haqiqi Nuraddeen Ina tayaka murna da kuma alfaharin zab’in da kayowa ‘ya’yanka, banida shakku akan cewa ALLAH yagama mallaka maka rabin addininka yanzu yarage wajenka kanemi rabin don samun kyakkyawar makoma, Ina roqon ALLAH nima daya dubi zuciyata ya shirya mani mahifiyarka, bansan meyake damunta ba da har zata d’auki karan tsana ta azawa wannan nagartacciyar yarinya wacce samunta tamkar samun zinarine acikin qasa, narasa wane irin zunubi na aikata da har iyalina ta kasance ahaka, ubangiji ALLAH kaganar da ita tun aduniya basai ranar da nadama baza tayi amfani ba.” Nisawa nuraddin yayi yana d’an muskutawa sannan yace, “Amin baffa.” Sun d’an jima kad’an suna fira kafin yayi masa saida safe snadiyar baffa Usman daya shigo d’akin riqe da ‘yar ledarsa wacce tazamo masa jiki duk daren ALLAH sai ya riqowa baffa ita, wani lokaci gasashshen nama ne aciki, wani lokaci kuma kifi ko kuma sharare (had’in dankali da kifi). ‘Dakin Yaya hawwa yashiga itama ya gaisheta sannan ya d’auko mata zancen abunda yafaru d’azu, duk da cikin girmamawa da kuma tausasa harshe yake yimata maganar hakan bai hanata yimasa tas ba sannan ta jadda masa cewa bazata dena abunda take so ba tunda gidansa ne kuma ita ta haifesa duk yanda taga dama haka zatayi, daga qarshema korarsa tayi tace yaje yabata waje bacci take ji, haquri yabata sannan ya tashi yawuce sashensa, ruwa yafara watsowa sannan sukaci abinci bayan sun gama itama tashiga toilet ta watso ruwan had’e da yin shirinta na kwanciya tahaye gadonta, duk abunda takeyi yana zaune gefen gadon yana kallonta da gefen idanuwa saida ta kwanta ya mulmula tare dasa hannu ya jawota yana fad’in. “To ranki ya dad’e ai baki isa ba, kin manta karatu zamuyi ne?”. STORY CONTINUES BELOW  Jan abun rufarsu tayi had’e da rufe fuskarta “habiby kabarni bacci nakeji don ALLAH.” “Tab..ina yimasa Amma kinsan ALLAH bazaki kwantaba, kawai kitashi, Yanzu muna qarfe tara awa d’aya da rabi kacal zamuyi seki koma ki kwanta abunki kinji ko, daure kitashi mana habibtyn habibyyy.” yafad’a yana d’agota daga kan filo, wartsake idanuwanta tayi don tasan tunda yafad’a to dole haka za’ayi tajuyo tana d’an harararsa. “Naji dai ko mai zaki mun bakomai.” Yafad’a yana ciro littafi da biro a gefen bedside loka, murmushi tayi ta aza kanta saman kafad’arsa yace. “Karki damu, zan baki abunda kike so.” Hakan daya fad’a yasa ta zauna daidai, cikin qwarewa yafar koya mata qananan kalmomin turanci da kuma hausa irinsu (I, you, she, we, he, they, them, us, e.t.c) (ni, ku, ita, shi, su, mu da sauransu.) Gwargwado kuma ta maida hankali tana fahimta sai dai bini bini tanayi tana duba agogo, awa d’aya na bugawa tayi baya da jikinta zata kwanta ya tarota yana dariya. “A’a habibty kiji tsoron ALLAH saura rabin awafa.” “Bacci nakeji habiby.” “Kiyi haquri, rabin awar tawace addu’o’i zaki koya mun, kinga sai kema kizama malamata.” “Habiby mubarshi sai gobe.” Rashida tasake fad’a tana zamewa daga riqon daya yimata tayi kwancenta, a ‘yan kwanakin nan yarasa meyake damunta take yawan bacci, gyara mata kwanciyarta yayi sannan ya miqe yaje yayo arwalar bacci ya kashe masu wuta shima ya kwanta, addu’ar bacci yayi masu ya shafe mata jikinta sannn ya jawota ajikinsa ya rungumeta sosai sukaci gaba da baccinsu hankali kwance. Misalain qarfe shabiyu biyu da rabi na dare Rashida n bacci taji wata irin qara da kururuwa na fitowa daga cikin falonta, addu’o’in data sani tafara karantowa abakinta sannan ta sauko kan gadon, fitilar d’akin ta kunna had’e da kallon yanda Nuraddeen ya qaqume abun rufarsu yana baccinsa hankli kwance, toilet tawuce tayo fitsari had’e da d’auro arwala akai tanufo falon, wani irin qugi taji yna tashi cikin dakewa takoma ta d’auko wayar Nuraddeen ta kunna karatun k’ur’ani tanufo falon dashi, tana shiga taga wata irin qatuwar mage tayo kanta tadake tana kiran sunan ALLAH tare da runtse idanuwanta, tsaye tayi tana jiran taji mezai faru da ita amma sai taji wani iska maiqarfi kamar guguwa yayi wani qugi daidai saiti kunnenta sannan yayi shuuu…yawuce ta gefen labulen tagarta. Sautin karatun ta sake qarawa sannan ta shimfid’a abun sallah ta kabbarta sallarta cike da yaqini da kuma miqa dukkanin al’amurranta ga ALLAH, hankali kwance take gudanar da sallolin nata na nafila kamar yanda tasaba duk daren ALLAH matuqar tanada tsarki har aka kusa kiran sallar asuba, daidai lokacin Nuraddeen ya farko tare da laluba gefen da take kwance yaji ba kowa, d’an shafa goshinsa yayi cikin yanayin bacci tare da jaye mayafin da suka lullub’a ya sauko akan gadon, falon yanufo ya tarar da ita zaune ta d’aga hannayenta tana addu’o’inta kamar yanda tasaba, murmushi yayi tare da komawa toilet ya d’auro arwala shima yayi raka’o’insa biyu na raka’atanil fijir sannan ya zauna yana jiran atada sallar asuba. Tana gama sallar asuba tayi zaunenta tana karanto azkar d’inta na safiya da marece har rana tafito sannan tawuce kitchen tad’ora dahuwar indomie kafin ta d’ora abun kari saboda yunwar da takeji shi kuma ya riqa mata gyare-gyaren uwar d’akin dana falo yana gamawa ya iskota kitchen zaune da plate gabanta tana cin indomien data gama dafawa. Cike da mamaki yake kallonta kafin yace. “Habibty lafiyarki kuwa? Qarfe shida da rabi na safe yanzu, sekace wacce takwana da yunwa…” Bai qarasa rufe baki ba ta tashi aguje tayo waje wajen makwarara tana sheqa amai, da sauri yayo kanta ya riqeta, gaba d’aya indomien da taci saida ta amayeta abun gwanin tausayi, kujerar tsugunno ya d’auko mata a kitchen ya zaunar da ita sannan yaje ya d’ebo ruwa ya wanke mata bakinta da inda ya b’ata mata hijabin dake sanye ajikinta, d’aki ya kaita ya zaunar saman kujera had’e da cire mata hijabin sannan yadawo tsakar gidan ya wanke bakin makwararar da tayi aman ya sake d’ebo wasu ruwan ya wanke hijabin ya shanya sannan yakoma cikin falon yana jero mata sannu, kuka ta saka masa kai kace wata qaramar yarinyace sosai. “Habibty meye haka, laifinki ne fa, kinsan bama Kari dawuri don me zakici abinci yanzu beside kofa brush bakiyi ba ba dole k’wayun cutukan da suka zauna maki a baki su sakaki amai ba.” Nuraddeen yafad’a yana qoqarin jawota ajiki, k’wacewa tayi tana fad’in. “Ko ba yunwa nakeji ba, kuma cikina duk a toshe yake bana jin dad’insa.” STORY CONTINUES BELOW  “Ayya yi haquri habibty, amma anya wannan ci da kikeyi a kwanakinnan ba macijin cikine ke damunki ba, ga yawan bacci dana lura kinayi gaskiya yau zanyiwa baffa Usman magana idan yaje daji yasamo maki maganin macijin ciki da basir.” “Wlh kuwa habiby nima nafara jin tsoro kada yafara cimun hanji kaga yanzu banci komaiba.” Rashida tafad’a tana yamutsa fuska, daidai lokacin taji ana yimata motsi aciki, wuntsil wuntsil, da sauri tamiqe tsaye tana zaro idanuwa tare da dafe saiti inda taji motsin kamar zatayi kuka yace. “Habiby wallahi macijinnan da gaskene, kaji yafaramun motsi, wayyo ummata, wayyo zan cinyemun hanji.” Da gudu takoma kitchen d’in ta d’auki sauran indomien ta qarasa cinyewa shi kuma yana tsaye yana kallon ikon ALLAH, duk Wanda yasan ciki kallo d’aya zaiyiwa Rashida ya fahimci tanada shi saboda hasken da tayi ga breast d’inta suma duk sun cicciko duk da bai sata laulayi ba yakan sata jin matsananciyar yunwa da Kuma yawan bacci wud’an gaba d’aya Nuraddeen ya ta’allaqasu da cewa yawan bacci basirne ke damunta shi kuma yawan cin abinci macijin ciki ne da ita sabod ko kad’an ransa bai kawo masa zancen cikine da ita ba, be side bema San yanda ake gane cikin mace ba idan tanada shi, ko amai da yaga tayi a tunaninsa rashin brush ne da batayi ba kafin taci abincin…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/11, 11:57 AM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___29💎 Bayan tagama tayi gyatsa had’e dayin hamma sannan yace. “Habiby bacci?” “Kuma?” Yafad’a yana kallonta, kashe electric d’in tayi sannan tajuyo ta d’ora kanta saman qirjinsa tana sake sakin wata hammar akaro na biyu ta sake cewa.”bacci nakeji.” Muje nima shi nakeji, Nuraddeen yafad’a tare da sunkutarta yanufi d’aki da ita, cikin muryar dake nuna baccin takeji sosai tace. “Habiby jiyafa tsoro aka bani a falon nan!.” “Kamarya habibty, tsoro anan falon Kuma? to sai Kikayi qaqa.” Yafad’a tare da direta saman gadon, Saida tasaki wata hammar sannan tace. “Addu’a nayi.” “Shine baku tasheni ba yafad’a yana kwanciya bayanta tare da jawo masu mayafin lullubinsu ya lullub’esu, cikin nauyin baccin dake d’ibarsa take basa labari shikuma yana isar da saqonsa ba tare daya fahimci sauran abubun da take fad’a masa ba har ya cimma burinsa, gyara kwanciyarta tayi yace. “Yihaquri Bari muyi wanka tukuna saikiyi baccinki” daqyar yasamu ta tashi suka tsarkakikke jikinsu sannan suka koma sukayi kwanciyarsu. Kamar yanda Nuraddeen ya fad’a haka akayi, ya sanarwa baffa da cewa ya samoma Rashida maganin macijin ciki dana basir take fama dasu, da baffa yasamo yazo ya gyarasu Inna Bilkisu na gefe tana gyaran ayarta ya miqo mata, “ungo maganin nan ki kaiwa yarinyar nan Rashida tun shekaranjiya Nuraddeen yafad’amun tana fama da matsalar macijin ciki da basir asamo mata, to bansamu shiga dajin ba sai yau, wannan ganyen dafashi zatayi tasha, shi kuma wannan sassaqen ta dakesa sai tarinqa sha tare da hura ko kunu, yarane basuda aiki sai cin maiqo ALLAH dai ya kyauta.” Dariya tafaryi had’e da cewa, “yanzu shi nuran yafad’a maka cewa tana fama da basir da macijin ciki?” “Haka yace mun mana tunda tana yawan bacci da cin abinci sosai bini bini yace taji yunwa, ai kinga wud’an matsalolin ke damunta ko kuwa.?” STORY CONTINUES BELOW  “Ikon ALLAH, malan kenan sake dai tunani, ai akwai d’ayansu dake iya haifar da irin wud’an matsalolin koma fiye dasu, be cemaka yaga tana haskeba ka had’o mata da maganin shawarah ba?” Inna Bilkisu taqarasa maganar dariya na kuccikke mata cike da mamakin Nuraddeen daya kasa gane matarsa nada ciki, kodon yaga ALLAH yabata lafiyayyene, shiru baffa Usman yayi na tsawon mintota kafin yagano inda zancen Inna Bilkisun ya nufa, murmushi yayi irin nasu na manya sannan yace. “To.to..to haka ankayi? Masha ALLAH, ubangiji ALLAH ya inganta, ja’iri zaisa in tafkawa kaina b’arna.” “Ai kuwa dai, Ina ruwan malan Nuraddeen, to bai d’au hannu ba shiyasa.” Tafad’a tana dariya. Daidai lokacin Nuraddeen yafito sashensa yayo inda Inna Bilkisu take a hirgitse, “Inna Bilki Rashida ce ba lafiya tun jiya da daddare take fama da zazzabi mai zafi yanzu haka gata can sai amai take faman yi ko za’a kaita asibiti ne?” Kallonsa baffa Usman yayi had’e dayin murmushi cikin xolaya yace. “To ko dai macijin cikinne yataso mata Nuraddeen?” “A’a inaga dai wannan karon qila shawara ce ko?” Inna Bilkisu tafad’a tana kallonsa, “Inna Bilki inaga itace ko akwai sauran maganin da baffa ya d’ebowa fadeela kwanakki abata har zuwa anjima inga ko zamu samo aron mota muje asibiti…” Bai qarasa ba Inna Bilkisu tace “Kai don ALLAH rufemun baki, ba don dai nasan kayi boko ba da nace maka takkwali kuma Mai qaton kai” tana gama fad’a tanufi sashen nasa baffa Usman na dariya ya shige d’aki suka barshi tsaye yana bitar kalaman Inna Bilkisu, can ya zaro idanuwa cike da mamaki har yana rufe baki yabi bayanta da sauri don samun qarin bayani cike da jin dad’i. Kwance ta iskota saman kujera mai zaman mutum uku cikin bargo sai rawar sanyi takeyi, sannu tayi mata sannan tajuyo ta kallesa tana fad’in, “yanzu kai Nuraddeen kan shirin zama baba amma har yanzu akwai wauta atare da kai, tana cikin wannan hali tun jiya ko ince kwanakin baya amma ka kasa kaita koda nan chemest ce adubata sai kira mata basir da macijin ciki kakeyi?” Cikin jin kunya yashiga sosa k’eyar kansa yana sissinne kansa qasa, murmushi tayi kafin suga Rashida tamiqe tayi waje da gudu da d’an sauran qarfin da take dashi, da sauri yaje ya kamata tana kwarara amai tamkar zata amaye hanjinta, ji yakeyi kamar yayi kuka ko ya maido da ciwon ajikinsa saboda tsantsar tausayinta, rungumota yayi gaba d’aya ajiki yana zuba mata sannu jikinta duk yayi yaushi, ruwan daya ajiye gefe abokiti ya d’iba ya wanke mata bakinta sannan ya d’agota tamkar ‘yar baby ya maidota d’aki tana sakin lumfashi da qyar, gaba d’aya ya mance da zancen Inna Bilkisu awajen sai daya gama gyara wajen yakoma cikin d’akin tace. “Idan akwai ‘yan ruwan zafi ka d’ebo mata ka lallab’ata tasha ko kad’anne in sha ALLAH Aman zai tsaya, bari naje nadubo maqwabcinnan namu idan motarsa nanan kayi masa magana kuje asibit, sannu Rashida sai hanquri Kuma yanzu har lokacin da ALLAH yarabaku dashi lafiya, ALLAH ya inganta kuma yaqara sauki.” Tana gama fad’a bata jira me zaice ba tafito tazari hijab d’inta, baffa Usman ta tarar bakin gida zaune ta sanar dashi halin da ake ciki, cikin sa’a mutumen nana yajawo motar Inna Bilkisu ta taimaka masa aka fito da Rashida, har zata bisu baffa Usman yace a’a tadawo taje can cikin gida ta sanar masu da halin da ake ciki, su kuma yace su wuce idan akwai buqatar wani yazo to yakira sai Inna Bilkisu tabiyosu a baya tunda nan cikin garine ba nesa ba. Suna isa nan take aka d’ebi jininta don ayo mata gwajin ciki bayan an bata taimakon gaggawa irin nasu na qauye, tashin farko ana aunawa a kaga tana d’auke da ciki har na tsawon wata hud’u da sati d’aya, duk da Nuraddeen yasan da haka tun gida da Inna Bilkisu tafad’a masa Amma bai gasgata hakan ba sai yanzu da likita ya tabbatar masa, tsabar farinciki ji yakeyi yau tamkar ya take kan jariri sai faman washe haqora yakeyi yana yiwa yiwa likita godiya, likita kam abun har dariya ya soma bashi ganin yanda gaba d’aya murna da farinciki suka rud’ar dashi,. Girgiza kai yayi yana dariya yace “malan Nuraddeen wanna irin farinciki haka inaga haihuwar farko ce za’ayi maka ko?” Murmushi yayi yana sosa kai likitan yaci gaba da cewa STORY CONTINUES BELOW  “Ahhh.. Masha ALLAH Ina tayaka murnar zama fresh baba, ALLAH ya inganta.” “Amin Dr. nagode sosai” Nuraddeen yafad’a yana miqa masa hannu cike da farinciki. Takardar magani da ruwan da za’a qara mata da allurai ya miqa masa yana fad’in. “Amma zakuyi haquri zuwa nan da anjima koda za’a sallameku don tana buqatar qarin ruwa sosai, ALLAH yaqara sauqi” “Amin Dr mungode” Nuraddeen yafad’a tare da ficewa daga cikin d’an office d’in nasa. A can gida kuwa koda Inna Bilkisu ta sanarwa da Yaya hawwa dasu Inna ruqayya babu wacce ta nuna tadamu acikinsu don duk a tunaninsu aikin bokansu ne yafara aiki, tana fita sashen Yaya hawwa ta kece da dariya tana fad’in. “Wani aikin sai malan bakada imani, ba kince ke taurin kaiba yarinya, anturo maki su mutsibbata da janjabilu su tsorataki yanda bazaki iya zama a d’akin ba sunce kinfi qarfinsu, anturo maki ashiq ya shiga jikinki amma yayi duk shawaginsa da dubarunsa shima ya kasa, na dasa na binne don ashiga tsakaninki da d’ana ya dakeki muhuta duka shima mun kasa nasara saboda baqin naci irin naki, shiyasa nace ayi maki mai kankat aturo maki mugun ciwon da zaisa kidinga wari kina sakin quraje dole ko baiso ya gujeki, kuma da dukkan alamu malan bakada imani yasa munyi nasara a kanki wannan karo, shegiya tsigitsila sai kinbar gidannan tunda bana ubanki bane, ba inda zanje ALLAH ma yasa kimutu. Haka kuwa akayi har marece yayi aka sallamota babu wanda yatafi daga cikinsu inba baffa Usman dasu Aysha da fadeela ba saboda Inna Bilkisu ta tsaya yin girki da gyara gidan sai Kuma yusuf d’an baffa Ali, Allah sarki baffa duk ji yayi ba dad’i da aka sanar dashi halin da take ciki, yaso ace lafiya take da babu abunda zai hanashi kai jiki asibitin, duk da yanzu sanadiyar addu’ar data bashi yanayi wata ran kuma tayi masa ko kuma baffa Usman yayi masa yafara samun sauqi sosai, Yaya hawwa kuwa sai yakwan biyu baiga ko qwayar idanuwanta ba, Inka gata tazo wajensa to wasu tarako cikin ‘yan uwa dake zuwa dubasa ko intake karb’ar kud’in da zatayi abincin da zataci duk da kuwa ko yaushe Rashida na kai mata idan tayi. Addu’a yayi mata sosai akan ALLAH yabata lafiya yanajin wata irin qaunarta na ratsa zuciyarsa musamman ma da akayi masa albishir tana d’auke da juna biyu, sai yaji kamar ya taka saboda tsantsar farinciki, nan yasa aka kira masa Nuraddeen yace kada yasake yafad’awa kowa cewa tanada juna biyu koda mahaifiyarsa ce har sai cikin yafito, haka ma Inna Bilkisu da baffa Usman duk ya roqesu su b’oye wannan sirrin na jikansa domin komai zai iya faruwa dashi idan har wani abun ya Sami yarinyar da abunda ke cikinta. Baffa Usman dama ba mutumne mai surutu ba ita kuma Inna Bilkisu tafi kowa son a b’oye zancen cikin gudun kada acutar da ita. Bayan an sallamosu sun dawo gida baffa yasa su baffa Usman suka riqasa yaje har d’akinta yayi mata ya jiki, akunya ce ta amsa yayi mata addu’a tare da gargad’inta akan cikin sannan suka mai dashi, yanda take d’an miqewa yana d’an aza qafafuwansa a qasa shi zaisa kana kallonsa kasan ya samu sauqi sab’anin da dako tashi tsaye baya iyayi balle har ya iya aza qafafuwansa a qasa, dudduqe yake kuma bai iya miqewa tsaye koda an riqasa, Amma yanzu cikin yardar ALLAH yana miqewa yayi tafiya idan anriqasa saidai baya aza qafafuwan da kyau ya taka qasa shiyasa mutanen gidan keta kallonsa cike da mamaki suna jero masa sannu. Satinta d’aya cikin d’aki tunda aka salla mota bata fitowa ko bakin qofa tana jinyar jikinta don har yanzu bai koma daidai ba bata son cin komai sai fura da kwad’on zogale hakan yasa tadena girki don ko qamshinsa bata so, Inna Bilkisu kullum cikin sayen ganyen zogale take a b’oye tana aika mata dashi haka baffa duk yafita sai ya sawo mata damammiyar fura tasha nono, abunka da qaramar yarinyar dake taka matakin farko na cikar girmanta mace nan take suka karb’i jikinta ta murmuje tayi haske abunta, bata aikin komai saboda fadeela da aysha keyi mata share share da wanke wanke, shi Kuma Nuraddeen shike kula da gyara mata d’akinta da wankanta, sosai yake bata kulawar da baya barin kowa shigowa sai idan aikowa akayi ko kuma cikin matan gidanne sukazo dubata da jiki shima d’in sai ya tabbatar ya saka mata hijabi tukuna yake cewa su shigo. STORY CONTINUES BELOW  Yaya hawwa kam ranar tunda safe ta shiga sashen daga tsakar gida tana qwalla masa kira da sauri yafito had’e da duqawa yana gaisheta, kallonsa tayi tun daga sama har qasa ta mere baki had’e da cewa. “Sannu bawan mata, wai ita har yanzu bata warke bane?” “A’a innar mu da sauqi dai.” “Mtssa to ni nagaji da d’ora sanwar nan Ina jiran aminci don yau zanyi baqi, sai ka sanar da ita don kada ab’ata mani lokaci.” “To innar mu.” Yafad’a jiki a sanyaye yana mamakin wannan hali na mahaifiyarsa, tun ranar da abunnan yafaru tsakaninsa da muneera har zuwa ciwon Rashida bataxo sashen ba balle tazo ta dubata, amma yanzu rashin kai mata abinci na sati d’aya yajawo tazo tana qorafi akai, muryarta ya tsinkayo daga tunanin daya tafi tana fad’in. “Kaji ko.” “E.eh innar mu.” Nuraddeen yabata amsa da sauri cikin i’ina, Jan tsaki tayi tare da kallon qofar d’akin Rashida ta cije baki had’e da girgiza kai sannan tabar wajen, jiki sanyaye yabar wajen shima yakoma cikin d’aki yana kallon Rashida dake baccinta hankali kwance batare da tasan ma wainar da ake toyawa ba, K’arar wayarta dake ruri yasa ta motsawa had’e da bud’e idanuwanta suka sauka akan fuskarsa, murmushi yayi tare da mik’a mata hannu yariqota ta tashi zaune sannan ya d’auko wayar dake sake ruri akaro na biyu ya miqa mata, murmushi ne ya bayyana a fuskarta lokacin da idanuwanta suka sauka saman screen d’in wayar ta kalli Nuraddeen tace. “Laaaa..Habibi baba ne.” “To kid’auka mana kada ta tsinke.” yafad’a tare da miqewa yabar d’akin yana tunanin abunda yakamata ya dafawa Yaya hawwa tunda ko kad’an Rashida bata son qamshin girki shiyasa ta denayi, shi kansa saidai yanemi ruwan tea yasha ko kuma yaci abincin da Inna Bilkisu ke aiko mata dashi. Cikin jin dad’i Rashida ta d’aga had’e da gaisheda mahaifin nata da tuni labarin tana da ciki ya isa kunnensu… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/12, 10:35 AM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___30💎 Cike da so da qauna ya amsa mata yana tambayarta ya qarfin jikin nata, a kunyace ta amsa da taji sauqi sosai, nan yayi ta saka mata albarka bisa zuwan da baffa Usman yayi wajensu amadadin baffa suna godiya bisa tarbiyar da suka bata tare da yabon kyawawan halayenta bisa haquri da juriya da take dasu da yanda take girmama kowa acikin gidan, hakan ba qaramin jin dad’i da alfahari ta sakasu ba shi da umma bugu da qari ga albishir da suka samu cewa sun kusa samun jika nan kusa bada jimawa ba, wannan dalilinne yasa yakirata da wannan safiyar don yanuna mata tsantsar farincikin data sakashi don har seda yayi qwalla. “Rashida Ina matuqar alfaharin kasantuwarki ‘yata saboda kin janyo mani girma da kimata sun qaru a idanun duniya kin sakani farincikin da ko mai ‘ya’yaye goma bai isa yanuna mun shiba, kin fahimtar Dani cewa ba ilimin boko kad’aine kesa kayi alfahari da d’anka ba matuqar kabashi tarbiya da ilimin addini, Ina mai addu’a ALLAH yakareki Kuma yafaranta zuciyarki kamar yanda kika faranta tamu nida mahaifiyarki, ki kula da kanki sosai kinga yanzu bake kad’ai kike ba, ki dage da yiwa abunda ke cikinki addu’a da neman tsari daga sharrin shed’an tun kafin yazo duniya domin shine hikimar ALLAH da yabar uwa tayi renon cikinta har na tsawon wata tara don samu isashhen lokacin yimasa addu’a badon haka ba da yanda akayiwa nana maryam kun fayakum haka za’a yiwa kowace mace saboda haka ki kula sosai kinji iko, kiqara hak’uri Kuma ki kai kukanki ga ALLAH da SANNU SANNU zai yaye mana damuwarmu, ALLAH yayi maki albarka, ga umman taki.” Baba yafad’a yana miqawa ummu wayar, STORY CONTINUES BELOW  “Ummata.” Rashida tafad’a hawaye na biyo kuncinta saboda tausayin kanta da halin da take ciki da basu sani ba, goge hawayenta tayi wani b’angare na zuciyarta nafad’a mata cewa bai kamata tayiwa ALLAH butulci ba tunda iyayenta nacikin farinciki Kuma ako yaushe addu’arsu natare da ita. Muryar umma ta tsinkayo a kunnuwanta tana fad’in, “yarinyata ya kike?” “Lafiya klw ummata ya kuke kuma da wajensu aunty marwiyya da baba balarabe, kowa duk lafiya ko umma.?” Rashida tafad’a cikin sanyin murya tana qaqaro murmushi a fuskarta tamkar tana gabanta. “Kowa lafiya klw ya qarfin jikin naki, kinacin abinci kuwa?” “Naji sauqi ummata, abincin daine bana iyaci ummata..” saida umma ta kalli baba dake gefenta sannan yace “dama nasan za’ayi haka, ki daure kinacin abinci kada kirame shima yaron cikinki kisa yafito ba lafiyayye ba kinji ko, fad’amun me kike so inba malan Idris idan yashigo yakawo maki.” Murmushi Rashida tayi aranta tana cewa, ALLAH sarki uwa, akoda yaushe kulawarta tamusamman take fiye da takowa aduniya, shiru tayi tana nazarin me zatace kafin can taji umma nafad’in “Akawo maki garin d’an wake kina so.?” nan take taji d’an waken yabiyo mata arai, “eh ummata Ina so, ahad’omun da busashshiyar zogale da kike ajiyewa kina yimana dambu shima inaso” “To kice dai a had’o har da tsakin yin dambun ko,” “eh umma har dana fate fate.?” “Duk dai Rashida, wannan yaro ko yarinya anyi makwad’aita.” Umma tafad’a tana dariyar, tamkar tana agabanta haka rashidar tayi saurin rufe fuska itama tana dariya, naseeha tayi mata sosai had’e da bata ‘yan shawarwarin yanda zata reni cikin sannan sukayi sallama, wani farinciki Rashida taji ya mamaye ranta cikin jin dad’i ta yane zanen gadon dake jikinta ta sauko daga kan gadon. Falo tafito taduba bataga habibynta ba tafito tayo kitchen don tasan bai wuce can yana had’a masu breakfast, ai kuwa tana zuwa ta iskosa yana gyaran kayan miya har ya d’ora sanwar shinkafa ta tafaso saboda electric ne kuma wutar tanada qarfi sosai, qamshin shinkafar data tafaso ne yabugi hancinta lokacin data aza qafarta zata shiga kitchen da sauri takoma baya had’e da toshe hancinta amma ina tuni aman yaci qarfinta da gudu takai bakain makwarara tana sheqasa, ji Nuraddeen yayi kamar ya aza hannu akai yafashe da kuka saboda takaicin wannan abun da yaya hawwa tace ayi gashi aman datayi kusan sati da kwanaki batayi ba yau duk ta rankasa, sosai aman ya galabaitar da ita don tun tana durqushe saida takoma zaune hawaye nabimata a kunci, gashi daya matsota saita turesa saboda warin girkin da yakeyi, rufo kitchen d’in yayi da sauri ya d’ebo ruwa ya wanke mata baki zuwa lokacin batada sauran qarfin da zata iya hanasa rab’ar jikinta duk dako qamshin girkin dake jikinta da bata so, riqata yayi ya kaita d’aki ya kwantar da I bisa gado yana jero mata sannu yaje yacire kayan jikinsa ya watso ruwa sannan ya d’auko plaks d’in ruwan zafi dake kan fridge tare da kayan tea ya had’a mata mai kaurin gaske ya tadata zaune yadinga Bata tana sha, saida ta shanyesa cikin kofin tas tace yaqaro mata wani ta shanye sannan takoma ta kwanta tana fad’in “kayi haquri habiby, kagaji da rashin girkin da nake yimaka ko shiyasa kad’ora abunka yau…” Bata qarasa ba ya d’ora yatsans abakinta yana girgiza mata kai. “Ko kad’an habibtyn habiby bazan tab’a gajiya da halin da kike ciki ba tunda nine sila, don haka kidena fad’ar haka kinji ko.?” Ya qarasa maganar yana jan karan hancinta, hannunta tasa tariqo nasa had’e da cewa. Kaima kadena fad’ar cewa kaine sila domin yanayin wannan ibadar gidan aurence tazo mana a haka.” ‘Dan duqowa yayi ya sumbaceta agoshi yana murmushi ta wani lumshe idanuwa sannan ya gyara mata abun rufarta daidai qirjinta yace. “Kiyi baccinki kada kifito har in qarasa, kwana biyu naga yadace yau akaiwa su baffa abinci shiyasa kika ga nad’ora girkin tunda ke dake dafawar bakyajin dad’i.” Yana gama fad’a ya juya zai bar d’akin tariqo hannunsa alokaci d’aya tana lumshe masa idanuwa bayan ya juyo tace. “Ina sonka malamina habiby nah.” STORY CONTINUES BELOW  Dawowa yayi yad’an shafa cikinta d’aya d’an fara tasowa sai dai ba sosai ba saboda tsawon da take dashi. “Ina sonki so mai yawa kuma marar misaltuwa habibty.” Bai jira mezata ceba yayi saurin wucewa ransa cike da nishad’i, in dai soyayyace tsakaninsa da habibtynsa yasan basa gajiya kuma ba ranar gamata, yanzunan ne zasu qone abincinnan batare da sun ankara ba shiyasa yayi saurin baro d’akin, murmushi tayi tarufe idanuwanta nan da nan bacci yazo yayi gaba da ita, bai jima da d’aukar taba can cikin baccin aka fara nuno mata miyagun halittu kala kala suna neman firgitata amma sai taga wani glass yayi mata shamaki tsakaninta dasu sun kasa yimata komai, da wata irin kalmar shahada tafarko cikin matsananciyar qarar da tasa Nuraddeen shigowa cikin d’akin a rud’e riqe da ludayin miya a hannu, da alama ita yake motsawa yaji qarar sautin kalmar shahadarta. Saman madubi ya ajiye ludayin yanufi inda take zaune tana karanto addu’o’in data sani abaki zuciyarta cike da tsoro sai faman harbawa takeyi da sauri da sauri, tattab’a fuskarta da tayi sharkaf da zufa ya dingayi hankalinsa atashe yana fad’in “habibty lafiya?.” “Lafiya habiby.” Tabashi amsa tan dafe d’an cikinta da yaji yana motsi sakamakon firgitar da tayi, “Tashi mukoma falo.” Yariqota ahankali yana kallon yanayin da take ciki, don riqotan da yayi yaji yanda qarar bugun zuciyarta ke tafiya da sauri da sauri sboda tsananin firgicin da tayi, ruwa ya d’auko a fridge yabata tasha bayan ya zaunar da ita, wayarsa ta karb’a ta kunna baqara tare da cewa yamiqo mata qillen tsamiyar dake ajiye saman fridge ta tsotsa saboda zuciyarta data fara tashi don har lokacin bai qarasa girkin da yakeyi ba. Bayan ya miqo mata tsamiyar yafice ya nufi can cikin gida da niyar kirawo fadeela tazo taqarasa aikin dama miya ce kad’ai bai qarasa ba. Yana fitowa yaci karo da muneera zaune bakin rumfarsu tana tsifar Kai, fiye da sati d’aya Inna ruqayya na fama da ita ta tsefesa sai yau da taga dama sannan ta zauna zaman tsifar, tana ganinsa ta dashe baki shi kuma ya d’auke kansa gefe cike da takaicinta, “ya nura.” Muneera tafad’a tare da tasowa tabiyosa har lokacin hannunta nacikin kanta tana tsifar da yatsunta, bai tankata ba har yakai bakin qofar d’akin Inna Bilkisu had’e dayin sallama, juyowar da zaiyi ya jira fitowarta sukayi karo da muneera dake biye dashi kansa yabugi nata sosai tayi baya zata fad’i yayi saurin tarota tafad’a saman hannunsa, abunka da d’an uwa duk yanda take bazaiso abunda zai cutar da itaba har takai ga taji ciwo, muneera na ganin haka ta dashe baki tare da sake sakin jikinta. “Meye haka, dalla miqe sakarai, meye kike faman bina haka.” ganin ko qwakkwaran motsi takasayi sai wni kafesa takeyi da idanuwanta irin na mujiya yasa cike da takaici ya saketa, tim kakeji qasa tamkar an yarda kayan wanki. “Wayyooo..quguna ya nura zaka karya ni.” Tafad’a tana qoqarin tashi, daidai lokacin Inna Bilkisu tafito had’e da cewa.”a’a Nuraddeen shine kayi tsaye anan sai kace baqo injin dai lafiya?.” “Lafiya klw Inna Bilkisu dama fadeela nake son tazo tad’an qarasa mana wani aiki, jikin Rashidar ne yad’an motsa yau..” “Ya nura nizan qarasa maka kowane aiki ne basai fadeela ba.” Muneera tafad’a tana wani turo lab’b’a ala tilas itaga mai kishi, “to Nuraddeen kuje ga muneera nan kaji tace zata qarasa maku.” Muskutawa yayi had’e da gyara tsayuwarsa sannn yace. “Don Allah Inna Bilkisu kitaimaka kituromun fadeela.” Batare daya damu da zancen muneerar da tayi masa ba, “Nuraddeen..” Inna Bilkisu tafad’a cikin sigar lallashinsa akan muneerar taje gudun wata matsala tafaru amma yayi saurin dakatar da ita tahanyar cewa “Don Allah Inna Bilkisu.” Yana had’a hannayensa sannan yawuce ita muneera ta sake bin bayansa. Saida Inna Bilkisu ta sauke ajiyar zuciya sannan ta qwalawa fadeela kira. “gani inna” Fadeela tafad’a tana fitowa daga cikin d’aki da alama baccima ta farayi, “maza jeki yayanku nakiranku, kice ma Rashida Ina gaisheta da jiki.” “To Inna.” Fadeela tafad’a tare da komawa d’aki ta d’auko hijabi tasaka tanufi sashensu, tana isa baki qofar shiga shiyar muneera ta riqe mata hijabi. “Wallahi babu inda zaki shiga tunda yahanani nima, munafuka kawai sai wani shishshige masa kikeyi bacin kinsan nice zan qara aurensa.” “Ha’a meye haka kuma aunty muneera, cikamun hijabina.” “Bazan cikakiba, wuce muje kikoma inda kika fito.” Nan rigima ta kaure tsakaninsu muneera tayi bake bake a bakin qofar shiga sahen nasu Rashida riqe da hijabin fadeela ta kafe akan ba inda zata fadeela sai kiciniyar k’wacewa takeyi ta shiga, hakan yajawo hankalin Nuraddeen dake cikin d’aki yafito had’e da katsawa muneera tsawa yace. “Waike wace irin marar kunya ce, zaki sake mata hijab ko sai nazo na takeki wajen.” Yafad’a had’e da yowa kanta ransa ab’ace. Da sauri ta saketa tare da komawa gefe tana fad’in “ya nura to nima in shigo?” “In karya maki k’afa k’azama.” Turo lab’b’a tayi tana fad’in. “Badai shiyar kane baka so nashigo ba, wallahi saina fad’a inna shima akaika wajen maln ba…” Bata qarasa maganar ba sakamakon wata uwar tsawa da Inna ruqayya dake fitowa daga b’angaren yaya hawwa tayo mata jin zata tona masu asiri, “kee muneera maza kibaro wajennan kafin ranki ya b’aci, yayan naki ke fad’a kina fad’a don rashin kunya, zaki jaye ko saina iskoki.” Taqarasa maganar tare da nufar wajen, qafafuwa muneera ta shiga bubbugawa tana fad’in. “Inna shifa zan aura kukace Kuma zakice nabaro wajensa, ya nura ni takace kuma ko bakaso sai ka aureni, kashirya a wannan shekarar dole muyi aure.” dariya Inna Bilkisu dake kakkamta kaya a cikin rumfarta tana sauraren suruttan muneera tayi aranta tana cewa tabbas iska na wahalda mai kayan kara, Nuraddeen dake tsaye shikuma yana kallon ikon ALLAH tsaki yaja tare da shigewarsa don bai fahimci ma inda zancenta yayi ba, a fusace Inna ruqayya taqaraso wajen taja hannunta tana d’imarta a baya “ke kam anyi samna anan, shin b’angaren nasa aljannah ne da zaki nace sai kin shiga, bana fad’a maki kifita shirginsa ba kafin yasake nad’a maki wani dukan?” Dai dai bakin shiga rumfar tasu ta tirje tana kuka had’e da fad’in. “Ni bazan fita harkarsa ba Ina sonsa, kuma ai keda baffa kunce zaku kaisa wajen malan bakada imani asa mashi soyayyata ya akayi har yanzu baya sona, ni bazan yarda ba kawai yau akaishi wajensa a d’aura mana aure gobe bana son aurensa qarshen shikarar nan don wallahi waccan munafukar zata iya aura masa fadeela gashinan sai faman tura masa ita akeyi tana shisahige masa..”[7/12, 10:22 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Hi fan’s am so sorry akan yanda kuka matsu mukoma asalin labari, Karku manta ita SANNU SANNU bata hana zuwa..no matter how matuqar ALLAH yabani aron lumfashi da kuma rayuwa zan sadaku da farkon labarin da muka faro, karku manta *baku san ko waye Abu sumayya ba?, bakusan asalinsa ba? taya ya had’u da matarsa batool shima baku sani ba? meya jawo batooul tabar iyayenta har na tsawon shekaru bakwai? Shin Abu sumayya ya cancanci mutuwa adaidai lokacin da yakamata yasan ko waye mahaifinsa?, meyasa mahaifin batoul ya sheganta shi, Shin batool itama ta cancanci ta fuskanci jarabawar da take ciki adaidai lokacin da take d’okin sake had’uwa da iyayenta?* 😅Inada yaqini akan shima baku sani ba kuma bakuda duka amsoshin wud’annan tambayoyin, wannan waiwayen tushen labari da mukayi shi kad’ai zai amsa maku duka wud’annan tambayoyi kuma da sannu ya sadaku da farkon labarinku, saboda haka kujuri zuwa rafi na tabbatar ranar da tulun zai fashe na nan zuwa🤣Ina matuqar godiya bisa yanda kuke qaramun k’warin guiwa ta hanyar comment d’inku, nakanyi farinciki kuma na nishad’antu da hakan akoda yaushe, FILLAH INA SONKU OVER💋😍_ Page___31💎 Har Nuraddeen zai wuce yadawo yayi tsaye yana jin maganganun dake fitowa daga bakin muneera, tun daga farko har qarshe babu abunda baiji ba yafito ransa a’bace yana watsawa Inna ruqayya da tayi tsuru tsuru da idanuwa tana ‘yan kame kame wani irin mugun kallo da yasa cikinta murd’awa, nunata da yatsa yayi yace.+ “Wai ni za’a kai wajen wani malami ko boka don in so wannan abar?” Yaqare maganar yana nuna muneera sama da qasa da hannu, murmushin gefen baki ya saki cike da takaici kafin yaci gaba da cewa. “To wallahi Inna ruqayya koda matan duk duniya zasu qare bazan tab’a auren muneera ba Kuma badon bana sonta ba sai don kawai kinzamo mahaifiyarta, duk da ‘yar uwata ce ita bazan iya aurenta ba har duniya ta nad’e don haka idanma mafarki kukeyi to wlh kufarka kunema mata mijin daya dace da ita, wannan Nuraddeen da kike gani in sha ALLAH mallakin Rashida ne ita kad’ai, zuciya da kuma ruhi gaba d’aya natane bana tunani ko a mafarki kwakwalwata zata aminta da shigowar wata azuciyata ko wacece ita ciki kuwa har da muneera d’in da kuke qaqabar ‘yar uwata ce domin bare tagama mani komai aduniya..” wata irin qara muneera tayi had’e da ciyo kwalarsa tana kuka, “wallahi ya nura baka isa ba, don ka kawai aka halitto ni bazai yuyu na auri wani inba kaiba..” Bata qarasa maganar sanadiyar wani zazzafan mari daya d’auketa yana kallon wuyar rigarsa data riqo, qafa yakai zai hankad’ata tayi saurin duqewa wajen tare da riqe masa qafafuwa tana kuka, “don ALLAH ya nura karka damu da inna, kafita batunta da halayenta ni kai nake so, zan zauna da kai ko mata nawa zaka aura amma karka yimani hukunci akan halin Inna ita da baffa sune basa son matarka haka ranar naji suna fad’a wai Inna hawwa takaita wajen malan bakada imani za’a dinga turo mata aljanu suna tsoratata, yanzu haka ciwon da takeyi sune sukasa yaturo mata shi..” baya baya Nuraddeen yayi kamar zai fad’i saboda tsorata da kalaman dake fitowa daga bakin muneera, duk da dai ciwon da Rashidarsa keyi ba irin wanda take nufi bane amma maganarta akwai qamshin gaskiya aciki idan yayi la’akari da tsoron da Rashida kecewa ana bata da Kuma yawan firgitarta acikin barci, kasa cewa uffan yayi har saida Inna Bilkisu dake tsaye cikin rumfarta tana sauraronsu ta matso wajen ganin yanayin daya shiga ta dafashi tana fad’in. “Karka kuskura ka amince da wannan soki burutsun na muneera kasan halinta da shirme, idan kuma har gaskiya take fad’a to kada ka tsorata domin da wannan tsoron naka za’ayi amfani wajen cutar da kai da kuma matarka kayarda ba mai yimaka sai ALLAH kuma Babu wanda ya isa ya cutar da kai sai abunda alqalamin qaddara ya rubuto akanka, maza kawuce kaje wajen iyalinka ba abunda zai sameku in sha ALLAH tunda kun riqe ALLAH, sharri shi Kuma d’an aikene duk inda kaje zai dawo ya sanar maka.” STORY CONTINUES BELOW  Taqare maganar tana kallon Inna ruqayya da tsabar kunya tasa tayi wuri wuri da idanuwa tana faman susar wuyanta. Wasu zafafan hawaye yaji son zubo masa wai ace qiyayyar da mahaifiyarsa keyima matarsa har takai ga za’a iya had’a baki da ita acutar mashi da ita don d’ai cikar burin wasu, cikin zafin rai ya dubi Inna Bilkisu yace. “Inna Bilkisu me yarinyar nan tayi masu da suke nema su cutar da ita, nine fa d’ansu duk wani abu na mataki daya kamata su d’auka akaina ya dace ba itaba.” Girgiza kai Inna Bilkisu tayi had’e da cewa. “ALLAH dai ya kyauta, kawai kashiga ciki in sha ALLAH babu abunda zai sameta.” “Munafuka! aikin kenan ko yaushe sa ido, to Ina ruwanki tunda duk abunda akayi d’in da sanin mahaifiyarsa ita data haifesa, meye naki nasa baki, ke kuma shegiya mai baqin baki kamar aku da yaushe akayi haka? wato ke uwar soyayya zaki qaqaba mana sharri tsakar rana, tashi muje yau sai kin gane kurenki” irin borin kunyar nan Inna ruqayya tafara wud’annan suruttan had’e da rufe muneera da duka tana janta, “Dakata Inna ruqayya! ku gaggauta zuwa kusa a kwance qullin da akayi maku akan matata idan ba haka ba duk abunda yafaru da ita to sai nayi shari’a daku..” kafin yarufe baki yaji saukar wasu zafafan marora har biyu a fuskarsa, Yaya hawwa ce da tun d’azu da taji muneera ta sako baki tana zuba tafito tayi tsaye tana qare masu kallo ta sakar masa wud’annan marora bazato ba tsammani, cikin d’aure fuska da rashin tsoron duk abunda zaije yadawo tace “Don buhun ubanka dake kwance anyi qullin kuma baza’a kwance ba kayi duk abunda ka iya, inkaga dama kaje koton duniya ni hawwa bana tsoron uban kowa akan wannan tsigalalliyar yarinya bare daka auro mani, Kai nifa nagaya maka natsani matarnan tun wuri ka rabu da ita ko agaban idanuwanka insa ta walaqanta, shashashan banza da wofi har kace zakayi shari’a damu akan bare.” tunda Nuraddeen ya soke kai qasa bai d’ago ba sai hawaye dake faman kwarara daga idanuwansa, yarasa wannan wace irin qiyayya ce mahaifiyarsa keyi ma Rashida da har Bata shakkun kowa akan zata iya illatata. ‘Dago kansa yayi yana kallon Yaya hawwa yace. “Innar mu kiyi hak’uri, aurena da Rashida muqaddirine daga ALLAH, Ina sonta sosai shiyasa nakasa haqura da ita tun farko, don ALLAH ko donni ki daure kisawa zuciyarki soyayyarta, inada yaqini akan zakiyi alfaharin samunta a matsayin suruka, kigujewa wannan mummunar al’adar da kike tunanin daidace kada ta jefaki cikin fushin ALLAH.” “To saketa idan kana so kada nashiga cikin fushin ALLAH, idan bahaka ba nayi maka baki ka lalace.” Taqarasa maganar tana gyara tsayuwarta da d’aurin zanenta, “Haba Yaya hawwa meyayi zafi haka keda d’anki, ai idan kikayi kuskuren yimasa baki damuwar akanki zata fad’a, don ALLAH da girmansa kiyi hak’uri kibar yaronnan tunda yana son matarsa, yaran zamani da kike gani bad’ai suke dana da ba zaifi kibarsu suyi rayuwarsu yanda sukesu ke Kuma iya naki kibisu da addu’a,” Inna Bilkisu tafad’a tana kallon Yaya hawwa cike da girmamawa. “Bilki.” “Na’am Yaya hawwa.” “Bilki.” Yaya hawwa ta sake fad’a akaro nabiyu tana kallonta, itama ta sake amsa mata kamar d’azu. “Ya isheki haka babu ruwanki da d’ana, kifidda bakinki a wannan maganar saboda ba huruminki bane, ni nahaifi d’ana baruwanki ko yankasa zanyi shishshigin naki ya isa haka kina jina, idan kuwa ba haka ba zan zageki tass awurinnan nayaga maki rigir mutunci ba abunda yadameni, ke kike da abun fad’i agari bani ba don haka bar wajen nan tun wuri kinaji na ko?” “ALLAH yabaki haquri.” Inna Bilkisu tafad’a tare da barin wajen zuciyarta cike da tausayin Nuraddeen, wata irin gud’a Inna ruqayya tasaki had’e da cewa, “su uwar gulma andaiji kunya idan ansanta, sai aja tsomakaran qafafuwa asani inda akayi yau shishshigi baiyi rana ba.” Bata tankata ba tawuce abunta Yaya hawwa tajuyo tana kallon gefen da Inna ruqayyace take tace. “Ai kece babbar uwar gulmar kuma zan dawo ta kanki.” “Kai nadawo gareka zaka saketa ko kafiso sai naga walaqantata agidannan.” “Innar mu don ALLAH kada kirabani da Rashida Ina matuqar sonta.” STORY CONTINUES BELOW  “Maida son akan waccan mai idanuwa kamar na mujiya koba komai ‘yar uwarka ce” Yaya hawwa tafad’a tana nuna muneera dake jingine ajikin k’arfen rumfa ta takure waje d’aya, wani irin shu’umin murmushi Inna ruqayya ta saki tana ayyana abubuwa aranta, cikin katsa tsawa taji tace masa. “Ka saketa nace..” duqewa yayi agabanta yana fad’in “innar mu kiyi hak’uri bakina bazai iya furta wud’annan kalaman agareta ba.” “Bazaka sake tab’a saina tsine maka?.” Tafad’a tana qoqarin bud’e baki ta tsine masa, da gudu Rashida dake lab’e tafito ta durqushe agabanta itama tana hawaye. “Don ALLAH kada ki rabamu innarmu, kifad’i duk abunda kike so zamuyi amma kada kirabamu ko don albarkacin abunda ke cikina.” Rashida tafad’a tana kuka, wani irin mugun kallo yaya hawwa tabita dashi tana kallon yanayinta da d’an cikin daya taso kad’an ajikinta kafin tace…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/13, 6:45 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___32💎 Buhun uba mezan gani haka?, Munafukan ALLAH dama cikine dake ake yimani rufa rufa agidan nan? tirqashi to idan tunaninki yabaki cewa wai cikin dake jikinki nada wata kima ko daraja awajena da har zai iya dakatar dani daga qudurina to kinsha qarya, dake har wannan abun dake cikinki bana sonku bana qaunar ganinku, don haka kai kasaketa kaji nafad’a maka kafin raina yab’aci” Yaya hawwa tafad’a cikin zaro idanuwa tana kallon Nuraddeen da izuwa yanzu gaba d’aya qasusuwan jikinsa sunyi sanyi, ga wani irin zazzab’i daya ji yana shirin taso masa, a hankali ya d’ago kai bakinsa na rawa yace. “Innar mu kidubi girman ALLAH kada kirabani da Rashida, wlh zan iya mutu idan kika rabani da ita, nayarda bakya son Rashida amma abunda ke cikinta bai kamata ki k’isa ba saboda jinin kine kuma jinina.” Tana bud’e baki tayi magana taji muryar baffa da tun d’azu yake yaqar zuciyarsa dake Shirin mutuwa ta sanadiyar raunin daya samu tamaidasa marar amfani aduniya, bayan da rayuwarsa ba mutuwa yayi ba cikin qarfin hali da jajircewa da kuma miqa dukkanin yaqininsa ga ALLAH akan zai iya abunda yasawa ransa yafara qoqarin rarrafawa yana dafa bango, addu’a yake maimaitawa azuciyar yana ambaton dukkanin sunayen ALLAH abakinsa yashiga bin bango yana fad’uwa yana tashi, wani azababben ciwo yakeji na qara taso masa tun daga kan qugunsa har zuwa tsakiyar qasan tafin qafafuwansa amma haka yaci gaba da takawa saboda rad’ad’in da yakeji da ciwo azuciyarsa yafi ciwon da yakeji yanzu atattare dashi har ALLAH ya kawosa inda zasu iya ganinsa, fad’uwa yayi zaune zufa na tartsikke masa tako ina ajikinsa yana fitar da lumfashinsa sama sama, ji sukayi cikin d’aga murya baffa yace. “Karka kuskura kasaki matarka Nuraddeen ko bana raye aduniya, ke kuma d’anki ne bazan hanaki kiyi duk yanda kike so dashi ba amma Ina so kisani aduk lokacin da kikayi nasarar sa Nuraddeen yasaki matarsa to kisani ranar nima babu aure tsakaninmu kije kema na sakeki.” Afirgice yaya hawwa ta d’ago kai tana kallonsa jin kalaman dake fitowa daga bakinsa cike da mamaki, shikuwa Nuraddeen duk da babu wani qarfi ajikinsa da gudu yataso yayo wajen mahaifin nasa da shed’arsa kefita sama sama batare daya tsaya fahimtar maganganun dake fita daga bakin saba, fuuuu.. Yaya hawwa tayi tawuce sashenta ranta ab’ace, ko kad’an bata damu da yanayin data gansa ba balle tayi tunanin taya akayi yazo wajen, amma gaba d’aya yara da manya dake gidan sunyi mamakin ganin baffa a wurin batare da kowa ya riqosa ba, kansa suka taru hadda muneera dasu Inna ruqayya ana yimasa sannu duk da Inna ruqayya bakad’an taji zafin bayyanarsa awajen ba saboda yanda ya b’ata mata masu tsarin, Rashida kuwa tunda tajuyo takalli baffa daga durqushen da take shima yana kallonta tayi murmushi lokaci d’aya kuma hawaye na yimata kara kaina a fuska kasa tashi tayi har saida Inna Bilkisu tazo ta riqata ta tashi tana mai godiya ga ALLAH daya hana faruwar abunda Yaya hawwa taso faruwarsa. STORY CONTINUES BELOW  Wajen suka nufa lokacin Nuraddeen ya rungume Baffa yana kuka cike da tagwayen farin ciki da suka lullub’e masa zuciya, na farko ganin akaro na biyu ALLAH yasake bawa mahaifinsa damar sake taka qasa da qafafuwansa na biyu kuma yanda ALLAH yakawo masa ginshik’in daya shiga tsakanin hana faruwar rabuwarsa da masoyiyarsa, shi kansa baffan kuka yakeyi Amma nasa na takaici da baqincikin irin matar da ALLAH ya jarabcesa da ita, d’ago kansa yayi yana shafa kan Nuraddeen yace. “Kayi hak’uri dukkani tsanani yana tare da sauqi, Alhamdulillah wama sha’a fa’ala.” ‘Dago kai Nuraddeen yayi yana jin wani sanyi azuciyarsa ya kalli Rashida da har lokacin kuka takeyi ya girgiza mata kai alamun tayi shiru tare da sakar mata murmushi, hannu tasa tagoge hawayenta itama tana mayar masa da nata sannan tajuya tashiga sashensu ta d’ebo ruwa a joke, duqowa tayi tana karanta addu’o’in data iya had’e da tofawa tabawa baffa, murmushi yayi yakarb’a ruwan yana saka mata albarka yasha sannan ya miqawa Nuraddeen sauran yace ya shafa masa a qafafuwansa, bayan mintuna kad’an baffa ya gwada qoqarin tashi da sauri Nuraddeen ya miqa hannuwa zai riqosa ya dakatar dashi, su dai mutanen gida duk suna nan tsaye cirko cirko suna kallon ikon ALLAH, duk da baffa najin zugi da zafi atattare dashi hakan bai hanasa gwada miqewar da kansa ba yana cije baki saboda zugi da rad’ad’in da yakeji har ALLAH ya taimakesa ya miqe da kansa, rufe idanuwa Rashida tayi hawayen dake cikin idanuwanta suka samu damar zubowa sannan tabud’e tana fad’in “Alhamdulillahillazi bini’imatihi ta timmusswalihat, ya mujibudda’awat, Alhamdulillah kathiran.” Ihu yaran gidan suka fara suna tsalle ganin yanda baffa yafara tafiya ahankali yana dafa bango batare da anriqasa ba, juyowa Nuraddeen yayi ya rungume Rashida agaban kowa yana fad’in. “Ke alkhairice arayuwata da kuma ta mahaifina, ya ALLAH kada kabani damar shaqar lumfashi a inda babu habibty d’ina.” Cike da jin kunya Rashida ta notar da kanta qasa tana murmushi tare da d’an turesa daga rungumar daya yimata ta juya tabar wajen cike da farinciki azuciyarta.” Juyawa yayi shima yabi bayan yaran dake biye da baffa suna tafi da ihun murnar ganin ya samu lafiya, Suna barin wajen inna ruqayya taja wani irin dogon tsaki cike da takaicin Rashidar babu babban baqin cikinta yanzu kamar cikin da tagani ajikinta wanda tamada yaqinin shizai qara zamowa shamaki kuma katangar da zata rugujewa ‘yarta samuwar nata farincikin, cike da son muzanta Rashida daidai lokacin da ta aza k’afarta zata shiga sashenta tace “Aikin banza da wofi, zuri’ar ‘yan tsibbu da mayu da gani anyo gadon buge bugen qasa.” Tsaye cak Rashida tayi tana sauraren kalaman da take jifarta dasu kafin tashigewarta batare da tajuyo ba balle ta tankata zuciyarta fad’a mata kada ta tab’a damar da kanta don tace mata haka, dama shi d’an adam haka yake duk abunda yake aikatawa sai yayi tsammanin kowama yana yinsa, konkad’an baici ta damar da kanta ba tunda tasan sunan da tayi mata da ita yafi dacewa ba itaba. Da gudu muneera tabiyo bayan Rashida har zata aza qafarta ta shiga sai tatuno jan kunnen da ya nura yayi mata. “Rashida” muneera takira sunanta cikin sanyin murya, juyowa tayi tana kallonta, ganin tana son yimata magana amma takasa shigowa tace. “Aunty muneera shigo mana.” “A’a bazan shigo ba ya nura na iskoni sai ya maidani tamkar jaki yasha Kara.” Murmushi Rashida tayi tare da dawowa bakin qofar inda take tsaye tace, “to gani aunty muneera” susar kanta tashigayi kafin tace, “naji Inna tana cemaki wai zuri’ar ‘yan tsibbu saboda kinyi wani abu aruwa kinba baffa yasha yawarke har yana tafiya, don ALLAH da gaskene shi kikeyi?” Murmushin da bai kai cikiba Rashida tayi tare da gyara tsayuwarta sannan tace “A’a muneera ba gaskiya bane, ni bana tsibbu kamar yanda Inna ruqayya tafad’a maki balle iyayena ko zuriarmu, Amma muna roqon ALLAHn daya halicci cuta kuma yayi maganinta cike da yaqini kuma ya karb’a mana, adduace nayiwa baffa d’azu don yasamu sauqin rad’ad’in ciwon da yakeji sai aka dace da ijaba ta sauka bayan jimawarsa azaune yana shan magani da kuma amfani da addu’o’i Wanda inada tabbaci akan tasirinsu ne yanzu yazamo silar samun sauqinsa bayan natofa masa addu’a aruwa yasha.” STORY CONTINUES BELOW  “Laaa ashe Inna qarya takeyi, don Allah Nima zakiyiwa ya nura aruwan yasha sai ya aureni.” Muneera tafad’a had’e da matsowa kusa ga Rashidar bayan ta d’an sassauta murya, Saida Rashida tayi dariyar da duka haqoranta suka bayyana sannan tace, “a’a aunty muneera bazan yimaki ba domin duk son da kike yimasa baikai adadin wanda nake yimasa ba, saidai Ina baki shawara akan kema kije kiroqawa kanki ALLAH daya baki shi, amma nidai bazanyi ba.” Taqare zancen cike da mamakin sakarci irin na Rashida, Ture lab’b’a muneera tayi cike dajin haushinta tajuya tabar wajen tana fad’in “‘yar baqin ciki, ALLAH ko bakyaso saina auri ya nura, bazaki zauna ke kad’ai ashiyar nan ba tundanima Ina qaunarsa, shegeyw mai tsawo kamar na iccen rama” dariya Rashida tayi sannan tawuce abunta had’e da turo qofar. Na’ima da Aisha ma yaran Inna Bilkisu dake zaune dawowarsu daga wajen niqa kenan don duk abunda yafaru basa nan akayi suma suka sawa muneera dariya jin abunda yafaru tsakaninta da Rashida, kansu tayo tana susar kai suka tashi suka ruga aguje tabisu tana zunduma masu zagi dama Inna Bilkisu nacan d’akin baffa ana murnar samun lafiyarsa. Ita ko Inna ruqayya sashen Yaya hawwa tanufa ta iskota cikin d’aki in tayi nan tayi can tana daddagar hannu had’e da cizon baki tana girgiza kai, “hmmm yanxu fa shikenan bakida abunyi yariga d’aya jawo maki reni ga yarinya, ya zubar maki girma agaban idanuwan d’anki sai yanda sukaga dama zasuyi acikin gidannan.” Ina ruqayya tafad’a tana watsa hannuwanta baya tariqesu tana jiran amsar da zata fitowa daga bakin Yaya hawwa don tasan yanda zata sake tunzurata idan ta zubar da maka manta a fusace Yaya hawwa tajuyo had’e da cewa “inaaa wallahi qarya ne, bai isa ba matuqar Ina raye, ai fad’a da aljani sai anshirya kuma duk lalacewar bushiya tafi qarfin a takata da qafa koda kuwa da takalmi ne, ni hawwa ban tab’a sawa raina abuba nakasa, atarihin zuriarmu ba’a tab’a sakin mace ba don haka baza’a fara akaina ba, badai ya hana nura ya saki matar saba, to ni kuma zansa matar nurah tabar nura nahar abada koda hakan na nufin zan mutu wlh sai tabar cikin gidan nan ita d’in banza da wofi.” Murmushi Inna ruqayya tayi kafin yace, “ahh to Nima dai shi nagani, wallahi idan bakiyi da gaske ba saita rabakinda d’anki da mijinki, yanzu haka fa Ina kallon wasu surqulle da tayi da wasu sabbatu ta tofa masa aruwa yasha sai gashi ya tashi da qafarsa, ke wannan yarinyar itama Ina ganin da nata shirin take don ko yayan Bata barsa ba tunda kikaga kimanin watanni goma sha yana zaune duk rigima da fitintinun da akeyi agidannan bai tab’a tasowa ba sai yau don yaji ance a saketa, aikam kema kinsan sedai ALLAH ya kayauta Amma tagama da Yaya balle nura.” Takai qarshen zancen had’e da fashewa da wani kukan munafucci, “Ke ruqayya fita, fita kibarni inji da abunda ke damuna don yau dole in koma wajen malan bakada imani, wannan shegen cikin dake jikinta dole adakatar da zuwansa duniya da ransa kafin ita Kuma musn nayi da ita.” “Gaskiya kam Yaya hawwa, ai yarinyar nan wlhi tagama tona mana asiri.” “Mtss..zan zageki ruqayya kitafi nace, akwai mai tona maku asiri kamar hasararriyar yarinyar dake gabanku, ai bakiga tonon asiri ba sai ranar data bud’e baki tafad’a duniya cewa iyayenta shashashune da basu san ciwon kansu ba tukuna, ni nafara tunanin bazan iya had’a zuria da itaba a haifo mun jika sak aku kuturu da gwalmammin qafafuwa.” Yaya hawwa taqare zancen tana turo Inna ruqayya waje had’e da rufo qofar d’akinta. Tsaye Inna ruqayya tayi tana ayyana kalar abunda zata yimata duk ranar da burinta yacika akan wannan walaqancin da take yimasu ita da ‘yarta sannan tawuce ranta ab’ace, d’akin da baffa yake tanufa fuskarta sake don kar afahimci yanayin da take ciki, lokacin mutane sun taru sai shigowa sukeyi suna fita ana yimasa barka da arziqi, baffa Ali da baffa Usman suma na zaune gefe fuskokinsu d’auke da farinciki duk da shi baffa Ali bahaka yaso aransa ba, yaso sai sungam shirinsu tsaf Mai faruwa tafaru koda zai samu lafiya gudun kada ya dakatar masu da shiri, yaqe kawai yakeyi amma haushi da takaicin taahin d’an uwan nasa yayi masa katutu azuciya, shi kam baffa yana tsaye yana gaggaisawa da mutanen dake shigowa, Kallo d’aya Nuraddeen yayiwa Inna ruqayya ya d’auke kai had’e da barin d’akin don yanzu shi ko ganinta baya son yi, bayan an watse yarage su kad’aine mutanen gida zaune baffa sai faman zagaya falo yakeyi yana yiwa ALLAH godiya, kallo d’aya zakayi masa ka fahimci tsantsar farincikin da yake ciki saboda ynda ya bayyana a fuskarsa. STORY CONTINUES BELOW  Wata irin muguwar dariya sukaji baffa Ali ya kwashe da ita harda tuntsirawa yana nuna baffa cike da isgilanci sannan yace. “Ho.ho.ho Yaya kace yau ba zama, tun d’azu ka kasa zaune ka kasa tsaye sai faman zagayar d’aki kakeyi, halan tsoron zaunawa kakeyi gudun kada asake damqeka waje d’aya, koda yake gaskiya ka zaunu dole ka guji abunda zai sakesa ka zauna inba dole ba.” Wani irin dimmm…baffa yaji har jiri na neman d’ibarsa jin kalaman dake fitowa daga bakin d’an uwan nasa, badon yasan lokacin da mahaifiyarsu ta haifi baffa Ali ba da tabbas yace daqyar idan shi jinin sane, saboda gaba d’aya halayyarsa kwata kwata batada kyawo, Babu hankali da lissafi acikin kowane irin zance da zaiyi, amma babu yanda ya iya dole yayi haquri dashi tunda jinin sane, fatarsa d’aya ALLAH ya ganar dashi matsalolinsa ya gyara kafin wuri ya qule masa, murmushi yayi sannan yakoma inda yake zama lokacin da yake jinyar yana kallonsa sannan yace. “Aliyu, ai ita jarabawar ALLAH takan zone ga bayinsa muminai, tabbas na zaunu anan wurin kuma nakanji na tawaya sosai, shiyasa yau da ALLAH ya yaye mun wannan lalurar nake ganin yakamata nayi farinciki na nuna masa cewa nagode da lafiyar daya bani, ba tsoro nakeji ALLAH yasake jarabtata ba domin shiyasan dalilinsa nayin hakan, nagode da irin naka farincikin daka nuna mun domin yasa nad’auki wani darasi aciki.” Girgiza kai baffa Usman yayi had’e da cewa. “Ashsha Ali Kai kam wane irin d’an uwane haka? Shin kana ganin abunda kayi burgewa ne ko kuma zai samaa maka nishad’ine shiyasa kayisa? To kasani kayi kuskure mai girma domin kayi izgilanci da al-amarin ALLAH wanda shi keyin yanda yaso alokacin da kuma yaso. “juyowa yayi ya kalli baffa sannan yaci gaba da cewa. “kayi hak’uri da kalamansa in sha ALLAH zaiyi nadamar yinsu ko yaushene.” Baffa Usman nagama fad’ar haka yabar d’akin dama tuni itama matarsa Inna Bilkisu takoma cikin gida don cigaba da aikinta saboda marecen dake gabatowa, nan take baffa Ali yaji jikinsa yayi sanyi kuma yafahimci bai kyauta ba. “Yi hak’uri Yaya.” Yafad’a tare da miqewa shima yabar d’akin, Inna ruqayya nabiye dashi a baya… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/14, 6:58 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___33💎 Ranar kam baffa kasa kwana yayi saboda abubawan da suka tarar masa azuciya, tsantsar farincikin samun lafiyarsa da irin kalaman da d’an uwansa ya jefesa dasu, Abu mafi cimasa rai shine yanda matarsa uwar d’ansa tayi biris da al-amarinsa, duk masoyansa na nesa dana kusa sunzo tayasa murnar samun lafiyarsa amma ita da take matarsa mallakinsa da tafi kowa ribantuwa da ita takasa zuwa ta dubasa balle tanuna masa farincikin da tayi, wasu zafafan hawayene suka zubo masa yana mai nadamar zab’enta a matsayin abokiyar rayuwarsa kuma uwar ‘ya’yansa, ganin zai sake jawowa kansa wani b’acin rai da damuwa yasa yashiga bayi yayo arwala yatada sallah yana mai miqa godiyarsa ga ALLAH daya fitar dashi cikin jarabawar da take ciki batare da anrabasa da imanin saba, Bayan sati d’aya da samun lafiyar baffa duk masu zuwa dubasa sun gama zuwa ciki har da iyayen Rashida, baba da umma da malan balarabe da matansa sai yayarsu hajia maryama da kuma aunty marwiyya, haka sukayo mota guda sukazo dubasa wanda ranarce tafarko da umma tazo gidan, duk da tanajin ‘yan wasu matsaloli da ‘yarta ke ciki tayi farinciki sosai ayanayin da taganta, don ba qaramar kulawa take samu daga wajen Nuraddeen ba, lokacin ne cikinta yacika wata biyar dam, tayi haske ta murje ko Ina na jikinta ya cika fam sai sheqi da kyalli takeyi abunta, ga d’an cikin daya fito ya zauna mata d’agwas ajiki gwanin sha’awa, duk wani motsi nata na akan idanuwan Nuraddeen da baffa, duk abunda take so taci suna bid’o mata batada wata matsala saboda yanzu komai tanaci kuma tadena yawan aman da takeyi si can baka rasa ba. Rashida tayi farincikin ganinsu sosai har tanaji kamar takoma ciki, da zasu tafi baffa yahad’a masu sha tara ta alkhairi shida baffa Usman suka rakasu har bkin mota, haka kurum Rashida ta tsinci kanta da fashewa da kuka tanaji kamar karsu tafi subarta tariqe ummanta sosai, saida Nuraddeen yayi da gaske yasamu ya lallab’ata suka koma cikin gida sannan su kuma suka wuce cike dajin kewar ‘yar tasu. Duk wasu abubawa da baffa yasan nashine a d’akin da yayi jinya yana cika satin nan guda da warkewa ya kwashesu yamayar asalin shiyarsu wato d’akin Yaya hawwa dama jinya ce takaisa can shiyasa yanzu da ALLAH yabashi lafiya ya dawowarsa saboda yasamu damar tsawatar mata, sosai hakan da yayi ya matuqar b’atawa Yaya hawwa rai har tana cewa ita ya komawarsa can d’akin kar yazo ya takurata, yi yayi kamar bai jitaba yaci gaba da kwaso kayansa yana maidowa nan cike da burin dakatar da ita ga dukkanin mugun nufinta. STORY CONTINUES BELOW  Hakan kuwa da yayi ya matuqar yiwa Nuraddeen dad’i ya sake maida hankalinsa wajen renon cikinsu, wata irin mahaukaciyar soyayya yake nunawa Rashida wadda ko alittafan novel bata tab’a jin irinta ba balle a finafinan zamani, kusan ko yaushe yana gida idan yataso makaranta, tare sukeyin komai kuma yanaci gaba da koya mata karatunta, ba laifi tana fahimta sosai don yanzu karatun hausa kowane irine zata iya karantawa, haka shima na bokon don su ( _come, go, sit-down, walk, run, stop, shoutup, ask_) duk ta iya, haka ma fannin had’a jimloli da turanci irinsu, ( _I will be there soon, stop crying, don’t worry, why do you ask, tell them e.t.c_) duk ta iya saboda yanda ya d’aukesu da muhimmanci shiyasa yafara koya mata ire irensu saboda yanda zai samu sauqin mu’amala da ita cikin sauqi idan suna cikin mutane, haka shima duk wasu addu’o’in da be iyaba yana koya daga wajenta, rayuwarsu cike take da burgewa gwanin ban sha’awa saboda yanda suke son junansu, qauna da kuma kulawa abun ba’a magana, kallo d’aya zakayi masu kafahimci yanda kowanensu ke shirye da sadaukar da farincikinsa akan d’an uwansa, furuci da kalamansu d’ai idan ka saurara zaka fahimci cewa shirya suke da su mutu wa junansu, daidai da qwarar zarra basa ba baqinciki damar da zai shigo masu cikin rayuwa, sun yarda da juna kuma sun amince akan zasuyi rayuwa tare kuma zasu mutu atare shiyasa sukeda tsananin fahimtar juna, cikin Rashida na tsufa qwaqwalwarta na dad’a bud’ewa wajen d’aukar karatun da Nuraddeen ke koya mata, Wanda si yanzu ne tafahimci cewa Babu wata wahala cikin karatun kamar yanda take tunani kawai rashin so da maida hankali yasa takasa natsuwa tayisa. Tuggu da makirci kuwa har yau Yaya hawwa takasa dena shiryawa Rashida shi, idan tayi wannan tayi wancan ta binne nan ta binne can amma duk wanda tayi sai ALLAH ya kubutar da Rashida, sau da yawa tasha zuwa tayi binne binnenta a bayan d’akin Rashida sai ALLAH yatura yara garin wasa su tonosa, musamman ta karb’o maganin da zai sawa Rashida baqin jini agun Nuraddeen ta zauna ta dama matashi cikin fura da nono saboda sanin yanda take matuqar son furar ta ajiye gefe da zimmar idan Rashida tashigo gaishesu zata bata tasha, malan bakada imani ya tabbatar mata da cewa matuqar ta shata Nuraddeen zai tsaneta da ita har abunda ke cikin cikinta kuma bazai qara ko awa d’aya da ita ba a matsayin matarsa zai saketa da kansa, kuskuren da tayi ta manta cewa da bakinta tasha fad’a agaban kowa cewa ba tason Rashida da ita har abunda ke cikinta, shiyasa lokacin da taba Rashida furar da tazo gaishesu baffa dake zaune yana karyawa yafahimci akwai wani abu ciki, har Rashida tamik’e cike dajin dad’i tana yimata godiya baffa yakirata, wata baqar leda yajawo agefensa dake d’auke da fura da nono da ba’a dama ba masu yawa ya miqa mata yace taje da ita tadama masu ita da mijinta sai tabashi ta hannunta yasha, yanda taga furar tayi kyau yasa taji tabiyo mata arai amma bazata iya musawa baffa ba tunda yace yana so, miqa masa furar tayi tana binta da kallo kafin takarb’i wacce ya miqo mata aleda tabar d’akin, tana fita Yaya hawwa tafara masifa akan ya za’ayi tabata abu ya karb’ar mata, murmushi kawai yayi tare da girgiza kai yace “hawwa kiji tsoron ALLAH, yarinyar nan da bakinki kike iqirarin baki sonta akan me zaki bata wani abu yanzu, shiyasa nafahimci akai wata badaqalar da kike shiryawa aqasa ni kuma na karb’e furar.” “To amma ai badonta zanyi ba saboda abunda ke cikinta kuma naga tana sonta sosai.” Saida ya mere baki sannan yace, “saboda abunda ke cikinta? Kin manta shima kince bakya sonsa bakya qaunarsa? Taya za’ayi yanzu kiyiwa mahaifiyarsa abu donsa baya baki sonsa.” “Nifa malan kadena jifata da sharri ba abunda nasawa furar nan, kyautatawa ce kawai amma kana bid’a kamaida cibi yazama qari.” “To fad’awa wani hawwa, Amma dai bani ba, kinfi kowa sanin nasan halinki kar babu abunda bazaki iya iyaw yarinyar nan ba tunda baki sonta baki qaunarta, idan kuma kince ba haka bane ungo furar kisha ke.” Yafad’a yana miqa mata furar a hannunta. “Ungo riqa kisha nace.” Yasake fad’a akaro na biyu yana kallonta. Ganin ta had’e rai tare da juyar dakai gefe yasa yayi murmushi cike da takaici yace. “Hmm! ALLAH yaganar dake hawwa, bakida gaskiya ko kad’an acikin alamurranki, zan so ace kin daure kin zibar da makaman yaqinki akan yarinyar nan tunda har rabo yariga yashiga tsakani, kiyaqi zuciyarki kiyarda da qaddarowar ALLAH acikin aurennan idan ba haka ba zakiyi babban dana sani da Kuma nadama lokacin da basa da amfani, yanzu haka hawwa zuciyata cike take da nadamar zab’arki da nayi amatsayina uwar d’ana gashi nadamar batada amfani tunda har rabo ya gitto a tsakaninmu, lokaci yariga yaqure mani da zan iya maida hannun agogo baya badon haka ba wallahi bazan zab’awa d’ana mahaifiyar da Bata tsoron ALLAH kuma take shirka dashi.” Baffa nagama fad’in haka ya d’auki furar yaje toilet da ita yazuba da yake na qasane ya jefar har da kofin aciki sannan yafita yana mai neman sauqi da sassaucin jarabawar da ALLAH yayi masa da ita. STORY CONTINUES BELOW  Ita kuwa kamar ta k’walla ihu haka taji don izuwa yanzu tafara fara kaiwa maqura bisa tufk’ar da takeyi baffa nayi mata walwala, gaba d’aya ya kasa ya tsare akan al-amarin yarinyar ko shine mahaifinta ai hakan ya isa, miqewa tayi had’e da riqe qugu tana hurar hanta tace, “Shikenan! Yanzu kam wasan yazo qarshe, zanyi amfani da dukkanin abunda na mallaka a duniya don cikar burina da nuna maka cewa baka isa ka dakatar dani ba.” A fusace tajuyo ta d’auki mayafinta da sauri da sauri tabar gidan ta nufi jejen wani mugun boka da tuni taso zuwa rashin kud’i ya hanata ana cemasa boka mai abun mamaki wato (bargaji) kamar yanda kowa yasanshi dashi yau taquduri komai yakeso zata bashi matuqar zai fitar mata da waccan matsiyaciyar acikin zuri’a. Rashida kuwa na komawa sashenta ta kwab’e hijab d’in dake jikinta zuciyarta cike da farincikin tafara samun karb’uwa a wajen uwar mijinta ganin alkhairin data yimata, ALLAH sarki baiwar ALLAH bata san cewa yanzu haka tana can kan hanyar illatata ba da kuma tabbatar mata da tsanar da take yimata ba, kitchen ta nufa da tulalen cikinta daya shigo wata na tara, nan da kwana ashirin ko yaushe ana tsammanin haihuwarta, wani d’an madaidaicin bokiti ta d’auko taje ta dama furar da baffa yabata tasha sosai sannan taje toilet ta watso ruwa tadawo falon taqara shan furar sannan takai kitchen ta ajiye, tana fitowa saiga Nuraddeen ya dawo daga makarantar can yarimawa da yake koyarwa, don tunda cikinta ya tsufa yadena zuwa yayo kwanaki acan sai dai kullum yaje ya dawo, cike da yanga tanufo inda yake don ta tarbosa tana fad’in, “oyoyo habibynah welcome back my love my everything.” Bud’e da baki yabita da kallo yana kafeta da idanuwansa maau matuqar d’auke mata hankali, murmushi tayi ganin yanda yake kallon takowarta izuwa garesa da d’an cikinta daya yimata kui, dama saye take da wata doguwar riga data d’ame mata jiki ko ina cikin yafito sosai ya matauqar qara mata kyau kamar ba ita ba, rufe idanuwansa yayi had’e da bud’ewa sannan ya bud’e mata hannayensa kafin taqaraso yana fad’in “thank you habibtynah kece haka kuwa?” tana qarasowa tarungesa ya mayar da hannuwansa yana shafa bayanta yana dariya, tace “Ni d’ince kuwa donma babynka ya b’atamun tsari.” “Kai habibtyn habiby! ba ruwan baby na kyau ma naga ya qara maki sosai.” Yafad’a yana janta zuwa d’aki, cuno baki tayi had’e da cewa. “Ba wani nan habiby wayau dai zaka yimun, Amma kabari nahaife maka babyn nan naka zakaga yanda zanyi fresh in koma ‘yar gayu, baran ma idan nafara zuwa school d’in da kace zaka kaini, hmmm sai kasha mamakin ganin yanda habibtyn nan taka zata canza.” Tak’are maganar tana aza kanta saman kafad’arsa riqe da hannusa, “ALLAH habibty nah?..” Nuraddeen yafad’a daidai lokacin da yake qoqarin zaunawa saman kujera had’e da turo idanuwa waje. turo nata itama tayi tana kad’a masa kai alamar tabbatar da zancenta had’e da cewa “serious habiby”. Jawota yayi ya zaunar da ita saman cinyarsa yana shafa cikinta ahankali sannan ya d’ago kansa yana kallonta yace “you’re serious ko? to nafasa babu inda zakije.” Saida tayi dariya sannan tarungumosa ta aza kansa saman breast d’inta tace, “haba dai habiby!, kaima dai kasan wasa kakeyi, kaga! Mudai bar wannan maganar ka tashi muje na tayaka kawatso ruwa sai kaci abinci, duk da yau dai ba abunda kake so nadafa maka ba, Eba ce da miyar shuwaka nayi maka.” Saida yayi kissing d’in cikin nata sannan ya d’ago kai ya lakuci hancinta sannan yace, “anything habibty indai daga wajen kine I luv it koda kuwa bana son sa.” Yafad’a yana kashe mata ido d’aya. Jan hannunsa suka nufi uwar d’aka tana fad’in “you different habiby.” Dariyar da saida haqoransa suka bayyana yayi had’e da jawota tafad’o masa ajiki ya jingina jikin wardrobe d’in dake cikin d’akin yana k’arewa kyakkyawar fuskarta kallo suna shaqar lumfashin juna yace “you’re different zakice habibty ba you different ba kinji ko?.” ‘Dan turo baki tayi sannan yace, “koma yane ai kaine ka koyamun shi ahaka” tafad’a a shagwab’e tana b’alle masa mab’allin rigarsa, da haka Nuraddeen ya shiga zolayarta yana aika mata da wasu zafafan saqonni masu wuyar fassarawa har yasamu ya lallabata cikin azanci yabiya buqatarsa. STORY CONTINUES BELOW  Tare suka shig wankan bayan sun fito ta kimtsa agurguje had’e da zuwa ta kawo masu abinci sukaci suka qoshi sannan yace ta taso suje tamotso jikinta don yaga qafafuwanta sun fara kumburi, Kitchen tafara shiga tasha ruwan farin zob’on da umma tabata satin daya wuce da sukaje dubosu tace tadinga sha zai taimaka mata wajen kakkatse tsak’in dake fita yayin haihuwa da wani wanda Inna Bilkisu tabata shi kuma tace maganin tsinkau tsinkau yakeye, Sha takeyi tan wani b’ab’b’ata rai yana tsaye yana kallonta har tagama sannan tafito. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/14, 10:32 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___34💎 Habiby wai har ina zamuje ne motsa jikinnan haka naga duk kabi ka kasa ka tsare.” Rashida tafad’a tana cuno baki ba, jawo hannunta yayi had’e da cewa, “Idan mukaje ai kya gani, nalura bakya son kina motsa jikinki kuma kinsan ko awonmu na qarshe da mukaje saida likita ya jamana kunne akan kirinqa yawan motsa jiki zai taimaka maki wajen aihuwa, don haka dole yanxu kiyi hak’uri muje ko don chu luv d’inmu, mud’an zazzagayo” Zaro idanuwa tayi waje had’e da rufe baki tace, “don ALLAH karufan asiri habiby, wlh bazan iya ba, ka kuwa san halin mutanen garin nan naku kuwa?, Kawai kayi haquri zan motsa anan cikin gida karka jawowa kanka zagi.” Zai sake magana ta aza yatsanta akan leb’ensa had’e da cewa. “Pls.. habibyyyyy.” Tare da Jan k’arshen sunan cikin shagwab’a. Bayanda ya iya da ita dole ya hak’ura don aduk lokacin data yimasa irin wannan kiran ji yake baya iya musa mata akan komai, “To yanzu fad’amun ya kike so ayi, motsa jikinnan dai kinsan dole kiyisa ko saboda lafiyarki Kuma ina so ki haifomun my chubby luv very strong!” Yafad’a yana kallon cikin idanuwanta. “Muje ka rik’amun k’afa fuwana zanyi set back (wani salon motsa jikine da mutum zai kwanta ko kuma zaunawa yana yin gaba yayi baya na tsawon wasu sekonni sannan yadawo gaba, haka zai dingayi har na tsawon mintunan da yaji zai iya.)” “Anya zaki iya habibty.” Ya tambayeta cike da tsoro, “o’oh zan iya mana, ai masu ciki nayi kuma babu abunda ke samunsu.” Haka kuwa akayi suka koma falo ya taimaka mata sosai tayi set back d’inta fiye dana mintuna ashirin har tagaji ta dena saboda mararta da taji tad’an amsa mata, sake taimaka mata yayi ta watso ruwa saboda yanda zufa kefita jikinta sannan yariqota suka dawo falo ta zauna tare da miqe qafafuwanta ya shiga yimata tausa har bacci ya d’auketa. ••• ••• ••• Tafiya mai nisa Yaya hawwa tayi kafin takai cikin dajin boka mai abun mamaki (bargaji), tana kaiwa ana kiran sallar la’asar tayi tsaye abakin wani beji tana dube duben ta inda zata hango bukkar bokan da aka fad’a mata cewa daidai wajen yake zama sai gashi ta isko wanen wayam Babu alamar wata bukka awajen, tafi minti biyar kafin tajuya zata bar wajen cikin wani irin sauti marar dad’in ji taji ance. “Maraba dake hawwaaa.., maraba da zuwa gidan miyagun aljanu, gidan biyan buqatun shed’anu da bau tsoron ALLAH, gidan rashin tausayi da imani, gidan da babu kunya balle mutunci, gidan cin amana da mugunta, gidan da babu jin tsoron ALLAH wajen kashe mai rai ya zamo matacce, Mai lafiya mu maidashi naqasashshe, shikuwa mai hankali mu maidashi mara hankali, marabanki abokiyar ta’bewa da hasara, meke tafe dake.” Cikin dakewa da rashin tsoro Yaya hawwa tace. STORY CONTINUES BELOW  “ALLAH ya taimaki bargaji…” “Keee dakata, ba’a kiran sunan ALLAH anan domin wud’anda alqawarin tab’ewa ya tabbata akansu kad’ai ke zuwa wajen, yanda kika manta dashi kika zo nan haka zaki manta da sunan har saikin bar wajennan.” Taji ankatseta cikin wata irin murya daban, “To boka mai abun mamaki Ina roqon ayi mani afuwa zan kiyaye haka.” “An maki abokiyar b’acewa, muna sauraronki fad’i buqatarki.” “So nakeyi a haukata surukata tabi daji Kuma kada takoma dawowa gidan d’ana har abada.” “Bazai yuyu ba, kicanza buqata.” Taji anfad’a tawni b’angaren, juyawar da zatayi sai ga bukkar ta hango gabanta da bai wuce taqa goma tsakani da ita ba. “Boka mai abun mamaki saboda me bazai yuyu ba, bana son takoma shiga rayuwar d’ana shiyasa nake son agusar mata da hankali na har bada..” bata rufe baki ba taji an d’auketa kyawawan maruka har guda biyu, tana shirin magana taji ana jawota zuwa inda bukkar take, Saida akazo daidai bakin qofar shiga ciki taji an durqusar da ita wajen ana zuba mata ruwan buloli tako ina ajikinta ana fad’in “kada ki kuskura kiyi kuka domin shizai qaro fushin alhajimalan akan tambayar da kika yimasa.” Yaya hawwa naso tayi kuka amma ta kama bakinta tarufe da hannuwa, duk saukar bulalar da taji ajikinta saita turo idanuwa waje tana had’iye kukan har aka gama” Gaba d’aya jikinta saida yayi laushi sannan aka k’yaleta ana maimaita mata cewa “ba’a tambaya awajen.” Kad’a kai tashigayi tana d’aga hannuwa alamun bada haquri kafin taji an sake janta an maidata ajikin bishiyar da take tsaye d’azu. “Ki canza buqata muna sauraronki.” Aka sake fad’a, cikin rawar murya tace. “Du..du.duk yanda akayi mata boka mai abun mamaki.” Wani irin iska taji ya taso had’e da guguwa taji ance “d’ago kanki.” Tana d’agowa cikin guguwar aka nuno mata hoton Nuraddeen zaune alokacin da yake tattausawa Rashida qafafuwa, banda fuskarsa da hannuwansa da tagani bisa qafafuwa yana mammatsawa wud’anda ta tabbatar na Rashida ne bataga komai ba, duk iya leqe laqen da zatayi don taga fuskarta kasa gani tayi bokan ya kece da dariya had’e da cewa. “Bazaki ganta ba domin ko mu anyimana shamaki da ganinta, tanada matuqar riqon ibada da addininta don haka baza’a iya galaba akanta ba, wannan auren had’in mai sama da qasane don haka bazamu iya rabashi ba, kawai mafita d’aya itace zamu iya fitar da ita cikin gidan idan mukayi sa’a da tana cikin rashin tsalki kowane irine to zamuyi nasarar yimata kurciyar da zata b’ace tayi nesa dashi, iya qarfin addu’arta iya tasirin da kurciyar zatayi akanta.” “To boka haka ma yayi, me zan..” bata qarasa ba tayi saurin rufe baki tunawa da dukan da tagama sha akan tambayar da tayi, dariya bokan ya kece da ita sannan yace. “Bama karb’ar komai anan, mun b’ace kuma dole mub’atar, juya can kafin kitafi kiyi sallar la’asar.” Kafin tace wani abu taji an sake janta izuwa bakin wancan bukkar ta d’azu, jikinta ne yahau rawa tazata wani dukan zatasha taji cikin wata irin murya daga cikin rumfar ance. “Shigooo, shigoooo” Jiki narawa tamiqe tashiga cikin rumfar, wani irin mugun hayaqine da wari suka tarbeta nan da nan tafara tari, dishi dishi tafara ganin wani mutum marar ma’ana tamkar mahaukaci yace “kijuyo anan ki sallaci sallarki ta la’asar.” Tsabar b’acewar Yaya hawwa da muguwar zuciya tanaji tana gani ta kabbarta sallah agaban wannan mutumen, ruku’inta da sujada gaba d’aya shi tayiwa su sannan ta sallame. Ji tayi ansake fizgota da qarfi anfito da ita izuwa bakin waccan bishiyar ta d’azu tashiga waiwaye waiwaye tana nemn inda zataga masu jan nata haka saboda tsavar bushewar zuciyarta. “Kitafi, ki saurari biyan buqatarki akoda yaushe kuma kitafi da baya baya har kifita jajin nan, rashin aikata haka kuma zai ruguza dukkanin murdanki.” Taji ana fad’a cikin wani salon murya da tamkar mutum biyu keyinta, da haka Yaya hawwa tafita jejin duk da tsananin nisan da yake dashi kafin akai hanyar cikin gari, fad’uwa kam tashata tafi a qirga kafin tasamu tafito, gashi duk tabi ta guggurje a qafafuwa, amma da yake taji tagani tana fitowa tayi wata irin ajiyar zuciya had’e da cewa “wahala ruwace nasan watarana wucewa zatayi” sannan taja qafafuwanta tawuce gida. STORY CONTINUES BELOW  Tana dawowa taci karo da baffa abakin gida suna tattaunawa akan wata magana wacce itace mafitar da baffa yasamawa kansa akan al’amarin Yaya hawwa da zata sama masa kwanciyar hankali dashi har dansa da iyalinsa. Shiru yayi yana kallonta tun daga sama har qasa lokacin da tazo wucewa don lokacin ana kiraye kirayen sallar magrib, cike da takaici ya katsa mata tsawar da saida tasata dawowa da baya har tana shirin fad’uwa saboda rashin kuzarin dake tattare da ita. “Daga gidan wa kike kuma da izinin wa kika fita?.” Baffa yafad’a had’e da yawo kanta a fusace, d’aga hannunsa yayi da niyar marinta ko zai rage rad’ad’inta da yakeji azuciyarsa, baffa Usman ne da tun d’azu ya sinne kansa qasa duqe yayi saurin tasowa yariqe masa hannu, “Haba Yaya kada kayi haka domin kasani annabi ya haramta mana dukan matanmu musamman akan fuskokinsu, koda yaushe kaike tunasar damu akan haka taya za’ayi yau Kai kuma kayi yunqurin aikata hakan kuma awake, inaga hakan bai dace ba, don ALLAH kayi haquri ka had’iye fushinka.” Wani irin kuka mai ban tausayi baffa yafashe dashi yana nunata da hannu. “Wannan wace irin matace Usman kadubeta sama da qasa batada banbanci da jakar da tagama birkid’a aqasa, dubi lokaci qarfe bakwai saura mintota ace mace Bata cikin gidanta, wannan wane irin sakarci da lalacewa ne?, Narasa wane irin girman zunubine dana aikata ubangijiya had’ani da wannan fitinanniyar mace da gaba d’aya bata san ciwon kanta ba, wlh da nasan haka rayuwarta zata kasance agidana da banyi fatar yin aure ba har nakoma ga mahaliccina.” “Kayi hak’uri Yaya jarabawace, itama kayi qoqarin canyeta kamar yanda kacanye na bayan, ALLAH shine masani bisa dalilin jarabtamu ta hanyar abubuwan sonmu da kuma jin dad’inmu, muje muyi sallah kaji har anfara tayar da salloli” Bugun iska baffa yayi da bayan hannunsa had’e da cewa “tir! hawwa ubangiji ALLAH ya shiryeki ya ganar dake” sannan ya juya suka nufi masallacin. Cije leb’enta na qasa tayi had’e dayin k’wafa sannan tajuya tawuce cikin gida tana ayyana kalar matakin daya dace ta d’aukarwa baffa idan ta gama da Rashida… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/15, 10:27 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___35💎 Bayan kwana biyu kullum Yaya hawwa cikin zuba idanuwa take taga abunda zai samu Rashida amma shiru har lokacin babu abunda ya sameta saima lafiya da take taqara samu, haka ma ta b’angaren boka bargaji duk iya sihirce sihircen da zaiyi yayi amma yakasa samun nasara ko daidai da qwarar zarra da zai iya cutar da, yatura baqaqen aljanu da mugaye kala kala don su juyar mata da qwaqwalwa saboda tsananin fusatashin da tayi nason ja dashi tahanyar nuna gazawarsa ga aikin amma duk wanda yatura a qone yake dawo masa ko kuma naqashe saboda qarfin addu’o’in da takeyi da yawan sauraren karatun alqur’ani, ko kad’an Rashida bata wasa da azkar kuma bata yadda tazauna babu arwala ba ko kuma cikin janaba balle yasamu damar aiwatar da aikinsa wanda hakanne yaqara mata matuqar tsaro da kariya daga sherin shed’anun, musamman ya tura mata aljanun da zasu dinga tsereta koda zatayi kuskuren mantawa dayin addu’a lokacin kwanciyarta ko kuma lokacin da zata Tara da mijinta, a tunaninsa yafi komai sauqi Amma sam agurin Rashida bata wasa da hakan, haka ma tsakar dare yakan turo wasu da zasu dinga zuwa suna tsoratata shima da sunje saisu tarar da ita tana nafilfili wanda takanyi hakanne aduk lokutan da tajita cikin tsoro ko miyagun mafalkai, ko kad’an nauyi da girman cikinta basusa tayi sakaci da ibadar taba domin ita tad’auka a matsayin jigon dake tafiyar da rayuwarta cikin aminci, babban farincikin ta d’aya aduniya shine yanda hankalin Yaya hawwa bai karkata wajen cutar mata da abunda ke cikinta ba wanda ako yaushe idan ta tuna da hakan takan yiwa ALLAH godiya, STORY CONTINUES BELOW  Yauma kamar kullum tana zaune saman kujera taba qofar falonta baya tana karatun al-qur’ani saboda tuni ta kammala girkinta da kuma ‘yan gyare gyaren gidan da takeyi sai ga Nuraddeen ya shigo cike da farinciki yana kiran, “habibty, habibty, habibtyyy..where are you my habibtynah?.” Kasancewar takama farkon aya yasa takasa katsewa ta amsa masa har sai da takai k’arshen ayar, juyowa tayi daidai lokacin daya shigo yayi saurin zuwa yarungumota ta baya had’e da sumbatar gefen wuyanta yana fad’in, “Masha ALLAH da samun nagartacciyar mace ma’abociya riqo da addini kamarki, ALLAH yayi maki albarka momyn chuluv d’ina.” Hannunsa dake saman kafad’arta tasa hannunta tariqo had’e da sumbatarsa tace. “Welcome habiby abban chubby d’insa, ALLAH yasa alkhairine wannan kira da naji kana yimun tun daga bakin qofa?.” Dawowa gabanta yayi ya amshi qur’anin dake hannunta ya saka mata alama a inda take sannan yarufe tare da ajiyesa gefe, hannunsa ya d’ora akan cikinta yana murmushi, daidai lokacin abunda keciki ya motsa, da sauri yacire hannunsa yana zaro idanuwa awaje, dariya ta bushe masa da ita had’e da cewa. “Lafiya abban chubby d’insa?” “Kai!.motsifa naji yakeyi habibty.!” “Eh mana, baka tab’a ji bane?, Ai shine cikakkiyar lafiyarsa idan yana wannan motsin inji likita, ai wannan bashine karo nafarko daya fara motsiba, kaine kawai baka tab’a cin sa’a ganin saba alokacin da yakeyi.” “Najifa tsoro!” Nuraddeen yafad’a cike da mamaki yana kallon idanuwanta, kallo d’aya zakayi masa kasan tsokana ce tasa yafad’i haka, dariya tayi had’e da cewa. “Tab lallema habibtyn! nan, to meye abun tsoro anan? Kenan ni da yake ajikina sai in mutu idan naji motsinsa?” “Ahh..rufamun asiri bance haka ba, to idan kika mutu ni kibarni Ina?, Yihaquri dama zolayanki nakeyi.” Yafad’a yana dariya, Dukan wasa takai masa a gefen kafad’a had’e da d’an harararsa cikin shagwab’a tace. “Kai ko!” “Afuwan bazan qara ba, yanzu dai albishirinki?” “Goro fari qalqalqal.” Yanzu muka gama waya da baba yace zancen komawarki gida wanka abarshi tunda anan kike awo har sai ALLAH ya saukeki lafiya sai amaidaki dake da babyn, kinga dai nima zan d’an qara morewa Ina dinga ganinki keda chuluv d’ina kafin lokacin.?” ‘Bata rai tayi kamar zatayi kuka don har tafara shireshiren komawarta sati mai zuwa amma sai gashi yazo ya wargaza mata tsari, cike da jin haushi tafara kaimasa duka ‘yan k’wallah nafito mata shi kuma yana dariya, “Wato zuwa kayi kafad’awa su baba kada abarni na koma?, Kuma shine za kazo ka aza mani dariya ko? Why habiby meyasa zaka yimun haka?.” Tafad’a tare da fashewa da kuka, ganin da gaske takeyi saboda hawayen da suke zubowa daga idanuwanta yasa yatsaya da dariyar da yakeyi yana qoqarin riqe mata hannuwa. “Srry habibty ba haka bane, wlh bana son kiyi nesa dani ne?, Kuma idan kin lura duka duka kwanaki nawa suka rage ki haihu?, sati biyu kacal fane, ai kinga da ace kin koma can Kuma haihuwar tazo ankwasoki anyo nan k’ara kiyi hak’uri ki haihu nan abunki, kinga ranar da kika haihu idan an sallamome nayi maki alqawarin da kaina zan d’aukeki in kaiki gida kinji ko?.” Yaqarasa maganar cikin sigar rarrashi, fad’awa tayi ajikinsa tana kuka ya rungumeta yana shafa kanta zuwa bayanta cike da mamakin yanda abu kad’an ke sata kuka yanzu, sun jima ahaka yana cigaba da rarrashinta tahanyar dad’ad’an kalamai masu sanyi da kwantar da zuciya kafin ya d’agota yana kallon idanuwanta, sadda nata tayi qasa yasa hannu ya tallabo fuskar yana goge mata hawayen. “Kina so in fad’a maki wani albishir da zai faranta maki rai.?” ‘Dago idanuwanta tayi takallesa tare da cuno baki gaba tace, “ni bana so idan kasan zai sake b’atan rai.” STORY CONTINUES BELOW  “No..no..wannan nasan zakiji dad’insa Kuma zai saki farin ciki sosai.” Yafad’a yana sumbatar ‘yan qanan lab’b’anta, “ALLAH da gaske?” “Sosai kuwa.” “Ok. Ina saurarenka.” Tafad’a tana qarasa goge hawayen dake nema su bushe a fuskarta. Murmushi yayi yariqo hannuwanta had’e da cewa “Habibty!, nasamu gurbin cigaba da karatuna, sunana yafito ajerin sunayen wud’anda gwamnati ta d’auki nauyin zuwansu qasar malesia don suqaro karatu, baban farinciki anan ma shine dana dawo naje Ina sanarwa da baffa yake fad’amun cewa yasama mana gida haya da zamu zauna idan kindawo daga wankan biqi kafin nawuce, kinga sai musha soyayyarmu hankali kwance babu takurar gidan yawa.” Cike da farinciki tarungumesa tana fad’in. “Alhamdulillahillazi bini’imatihi ta timmusswalihat, congrat habiby gaskiya nayi farinciki sosai, ALLAH sarki baffa ai da yabarmu anan d’in, kullum baya gajiya dayi mana hidima da son faranta mana, ALLAH yabiyashi yasaka masa da mafi qololuwar alkhairinsa.” “Amin ya rabbhi habibty.” Yafad’a yana dariya cike da jin dad’in addu’ar da tayiwa mahaifinsa, “Amma habiby yaushe ne zaku wuce?” Tafad’a tana d’agowa daga jikinsa, shiru yayi kamar mai wani tunani kafin yace “Ehmm..inaga kamar nan da wata uku sukace, amma ungo takardar kiduba kigani.” Yafiddo takardar daga aljihunsa yana miqa mata. “A’a kabarta, Amma gaskiya abun ya matse sosai, kamata yayi ace ko nan da wata biyar ne, kaga lokacin chubby child d’inka yad’an saba da kai…” tafad’a tana d’an b’ata rai. “Karki damu zan iya cewa a d’agamun lokaci saboda matata da chuluv na buqatata akusa dasu koda nan da zuwa wata goma ne idan kina buqata.” “A’a rufamun asiri, ai dama ce ta lokaci d’aya idan tasamu to yayi amfani da ita.. ALLAH yakaimu lokacin kuma yasa munada rayuwa.” “Amin habibtynah. Shiyasa nake qara sonki saboda wannan kaifin fahimtar da kike da ita.” “Bawni wayau da zakayimun, ALLAH zamuyi kewarka sosai idan katafi.” Taqare maganar tana shafa tulelen cikinta daya qara girma sosai cikin kwana biyu d’innan. “ALLAH dai ya saukeki lafiya kuma yabamu rayayye mai albarka.” “Amin habiby.” “Yawwa nace wane suna kike so mu sakawa babynmu idan kin haihu?.” “Emmm..idan macece sunan Inna nake so a saka mata hawwa’u mudinga kiranta (jiddah) idan kuma namijine sunan ka nake so yaci wato (Nuraddeen).” Tuni baffa yagama samarwa su Nuraddeen hayar wani d’an madaidaicin gida acan farkon gari kusa da asibiti mai d’auke da d’akuna biyu da falo d’aya sai kitchen da toilet, sai tsakar gidan da girmansa bai wuce iya mutum biyar su kwanta ba, yayi hakanne don su samu sakewa su huta da takurar Yaya hawwa shi kuma yasamu yaqaro aure ko yakoya mata hankali, wannan itace shawarar daya yanke tsakaninsa da baffa Usman da tuni yayi magana da Inna Bilkisu za’a bashi auren ‘yar yayarta da ALLAH yayiwa rasuwa tagudo tadawo nan garin sanadiyar wahalar da take Sha a hannun ‘yan uwan mahaifinta, qaramar yarinyace da Bata wuce shekara goma sha uku zuwa Sha hud’u ba da yake su can qauye basu d’auki abun wani abubu har da shekara goma zuwa goma sha biyu suna aurar da yarinya, cikin sa’a kuwa iyayen Inna Bilkisu suka yarda saboda yanda sukaga baffa Usman yariqe masu ‘yarsu hannu biyu shiyasa suka yarda da nagartar yayan nasa suka amince da aura mashi yarinyar koba komai hakan zaisa idan ‘yan uwan mahaifinta sukaji tayi aure su dangana da batun komawarta can. Duk wannan abun da akeyi Yaya hawwa batada labari tana can tana haukar rashin ganin aikin boka da bai kama Rashida ba, gashi wannan bokan ba’a yimasa katsalandan ko tambaya balle takoma taji ba’asi, gaba d’aya abu ya isheta ya sha mata kai tarasa yanda zatayi, Inna ruqayya kuwa tuni itam tabazama wajen bokaye tunda taji abunda Yaya hawwa tafad’a akan bazata had’a zuria dasu ba don arufe mata baki Kuma akarkato masu da zuciyar Nuraddeen ga muneera har sai ya aureta, Adaidai wannan lokacin da Rashida da Nuraddeen ke cikin halin tsaka mai wuya a hannun bokaye cikin Rashida ya cika wata wata tara dam da haihuwa, duk abunda yakamata Nuraddeen ya tanada na kayan baby da mamansa gwargwado ya tanada, haka kuma duk abubuwan da mahaifiyarsa keyiwa matarsa bai tab’asa ya yarda haqqinta ko d’aya ba akansa, duk wata kyautatawa yana yimata daidai gwargwado kuma kullum dashi har Rashida basu fasa zuwa gaisheta ba amma Rashida bakinta d’auke da addu’o’i take zuwa gaisheta ko yaushe sanin halin da ake ciki, musamman itama ya saimata kaya kala biyu ya kimata da zimmar taci suna dasu idan ALLAH ya sauki Rashida lafiya, yau tunda safe Nuraddeen yatashi da fad’uwar gaba wacce yarasa dalilinta amma yanata addu’ah batare daya bari Rashida ta fahimci halin da yake ciki ba, Da daddare suna kwance ta mulmulo wajensa had’e da d’ora kanta saman kafad’arsa tana yawo da hannunta saman qirjinsa, a hankali yayi gyaran murya had’e da cewa. “Habiby lafiya yau naganka sai ahankli, meyake faruwa da kaine?” Wata ajiyar zuciya yayi had’e da cewa. “Habibty babu b’oyo a tsakninmu domin kin zama ni nazama ke, nayi qoqari wajen ganin ban bari yanayin da nake ciki ba yayi tasirin bayyana a fuskata har kika fahimta, amma tsantsar kulawarki agareni yasa hakan ta gagara, bansan yau meke faruwa ba tun safe nake jin yanayina daban duk babu dad’i ga wata irin fad’uwar gaba dake damuna, addu’a nakeyi amma sai qara tsananta abun keyi narasa ya zanyi habibty, cikin kwantar da kai da sigar rarrashi tafara yimasa magana cikin sanyin murya tace. “Haba Nuraddeen, hasken idaniyata, zuciyata da kuma ilahirin gangar jikina, Kai kuwa meye zai tayar maka da hankali bayan kasan kanada ALLAHnka akoda yaushe kuma yana tare da kai, me zaka jiwa tsoro aduniya kai dake tare da sa albarka iyayenka, me kake shakku acikin rayuwarka bayan kana da yaqini akan zamu kasance atare, don ALLAH kadena fargaba akan komai koda kuwa wani abunne zai sameka ko kuma ya sameni, natabbata cewa tsantsar imaninmu da miqa wuya ga ALLAH shine kan iyasa ajarabcemu, muzama masu juriya cikin al-amurranmu alokacin da wani abu kenema ya gitto mana cikin rayuwa, sai musamu kanmu masu riskar ubangijinmu amadakata kyakkyawa, kacire komai aranka in Sha ALLAH babu abunda zai faru, nasan harda tunanin haihuwarnan yasa kakejin haka, to kasanyawa ranka salama in sha ALLAH zan sauka lafiya kuma zan haifa maka chuluv d’inkacikin qoshin lafiya kaji ko” taqare maganar tana sakar masa kiss ta ko ina afuskarsa har da saman tsinin hancinsa, cikin dariya ya rungumeta shima yana sumbatar goshinta yace. “Nagodewa ALLAH daya sanya cikakkiyar natsuwata a hannunki, ALLAH yayi maki albarka yasa kigama da duniya lafiya, nayarda da shawarwarinki da kuma duk tsarin da ALLAH yayi mani arayuwa, ALLAH kasanya farinciki ya zamo cikar gurbin yanayin da nake ji.” “Amin habibynah jarumin mazan duk duniya.” Karan hancinta yaja tare da lakatar kuncinta yace. “Abaki kenan amma idan nace ingwada jarumtar tawa yanzu ai bazaki yarda ba, chuluv d’innan nawa naga nema yake tun kafin yazo duniya yafara takuramin.” “Karkai masa sheri domin Babu ruwansa, habibtynka ce kawai keyi maka rowa saboda nauyin da tayi amma yau bazata yimaka ba matuqar kanada buqata akanta.” Tayi hakanne saboda ta tabbatar da tagusar masa da damuwarta amma ita tunda cikinta yashiga wata na tara takejin wahalar kwanciya da ita, hakan yasa shima yadena takura mata. Cike da farinciki ya mirgino fuskarsa na kallon tata yace. “Da gaske habibtyn habiby zaki iya jurewa?.” Kad’a masa kai tayi alamar ta tabbatar da hakan, cikin dubaru da tausayi yafara sarrafata ta hanyar da yasan bazata wahala ba har ya biya buqatarsa, tun kafin yagama taji mararata na murd’a mata ga wani ciwon baya da taji yarufeta amma saboda qarfin hali da kwad’ayin samun natsuwarsa yasa tajure har saida yagama. “Habibty tashi muyi wanka.” Yafad’a yana qoqarin saukowa saman gadon, Sai data cije baki cikin tsananin zafin da takeji tace. “Kaje kafarayi habiby daqyar idan zan iya yanzu saboda marata namun zafi.” “Yi haquri habibty duk nine najawo hakan, Bari nad’aukeki sai muyo ko?.” “A’a kafara zuwa kayi, idan kafito ko arwala ce nasamu nayi kafin asubar tunda annabi ya halarta yin hakan.” Miqewa yayi har ya aza qafarsa zai shiga sai kuma yadawo had’e da sumbatar goshinta yace. “Ina matuqar sonki da qaunarki habibty and I dont want to loose you any more in my life, be couse you’re my everything, if I say everything I mean everything including my entire life, I love you for ever and ever and ever.” Cikin wani yanayi da ita kad’ai tasan ya takeji tayi masa murmushi tare da cewa. “me too all I have.” Show some luv pls👏 #COMMENT #VOTE #SHARE *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/16, 10:46 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ 😭😭 _THE MOST BREAKING HEART & HEART TOUCHING PART OF THE BOOK_💔💔 Page___36💎 Sake miqewa yayi ya nufi toilet d’in bakisa d’auke da addu’a ita kuma ta lumshe idanuwanta tana jin wani irin azababben bacci na son d’aukarta, a wannan lokacinne madubin boka bargaji ya nuna masa cewa Rashida bata cikin tsarki, nan take yafara surqullensa yana turo mata miyagun aljanu masu matuqar qarfi, wani iskane yataso da qarfi cikin d’akin da sauri Rashida tafarko daga nannauyan baccin daya soma d’aukarta tana cije baki, kan kace me tuni tafara ganin duniyar na juya mata, qoqarin kama addu’o’i tafarayi abakinta amma duk wacce tajawo saita kucce mata, wasu Halittu tafara gani cikin iskan daya mamaye gabanta suna nufato inda take kowane da kalar sigarsa suna qoqarin illatata amma qarfin addu’o’in da takeyi ya shamakance tsakaninta dasu, hakan yasa suka gagara yimata komai saboda aduk lokacin da suka tunkarota wani irin gilashi mai qarfi suke ganin ya shiga tsakaninsu da ita, basu dena tsorata taba ita ma batadena karanto addu’o’in da suke bakinta ba har saida azabar ciwon da take ji ya tsanantar mata, gaba d’aya tarud’e tashiga tashin hankali, wani irin yanayi take jin kanta aciki wanda tunda aka haifeta bata tab’a jin kanta acikiba, yanayine da kallo d’aya zakayi mata kasan cewa naqudace ta taso mata adaidai wannan lokacin, tun tana jurewa har tafara gazawa idanuwanta suka fara zubarda k’walla tana kiran “ALLAH, ALLAH.” don alokacin iya shi kad’aine bakinta ke iya furtawa. Ganin duk aljannun da bargaji keturawa sun kasa nasara yasa yakira wani mugun shed’anin aljani wanda aduk lokacin da aiki yayi masa tsanani ko yake nema ya gagareshi shi yake turawa kuma cikin ikon ALLAH zasuyi nasara saboda ALLAH ya riga daya sakar masu talala, cikin wani qamari da girgiza ya dumfaro Rashida da alokacin bata iya furta komai saboda azabar naquda data rufeta, wani surqulle boka bargaji ya sakeyi yanda idanuwan Rashida zasu bud’e, tun tana kwance saman gadon har tajid’o dafe da cikinta alokacin aljanin ya bayyana da wata irin mummunar siffa agabanta nan take ta some wajen ba tare data koma sanin inda take ba, duk iya abunda boka bargaji zai iyayi shida shed’anun dake taimaka masa wajen ganin ankawar mata da hankali ko mugun sammun da akayi mata yayi tasiri akanta sunyi amma cikin ikon ALLAH da nuna qarfin addu’a hakan ya cutara, nasara d’aya sukayi shine d’auketa da akayi akabar garin da ita, sanadiyar hakan aljanin ya dinga buga Rashida a jikin itatuwa yana wurgi da ita bisa duwatsuna, yamatuqar fusata ganin yanda yakasa aiwatar da aikin uban gidansa akanta Wanda wannan dalilinne yasa saida y azabtar da ita sannan ya Kai ya jefar inda suke sa ran bazata tab’a rayuwa ba kafin safe.+ ••• ••• ••• A ‘ban garen Nuraddeen kuwa yana fitowa wanka riqe da d’an qaramin towel yana tsane ruwa akansa yace. “Habibty ki daure kitashi muje intayaki kiyo wankan nan, nasan yanda kika tsani kwana cikin irin wannan halin na janaba baccin bazai yimaki dad’i ba idan kikayi kwanciyarki a haka, gashi biyu har da rabi nadare ya somayi nasan lokacin tashinki shima yakusayi tunda ukku takusa. Pls daure ki tashi kinji?” Yaqare maganar had’e da juyowa yakai kalonsa inda take kwance, gabansa ne yayi mugun fad’uwa da sauri ya nufi inda yabarta kwance yana jaye mayafin da suke lullub’ewa don gaskata abunda idanuwansa kefad’a masa, a firgice yaja baya ganin bata wajen kwance da sauri ya nufi falo cike da fargaba amma ga mamakinsa nan d’in ma bata nan, kasa gasgata kansa yayi ya dinga d’add’aga pilows d’in kujeru da gefe gefen kujera cikin tashin hankali gabansa na bugawa da sauri da sauri, curtains d’in tagogi falon ya shiga d’ad’d’agewa yana kiran sunanta, babban taahin hankalinsa ma qofar falon daya gani kulle Wanda yatabbatar masa daba fita tayi ba, da gudu yakoma uwar d’akan yana rerrega qarqashin gado da bayan wardrobe yana sake kiran sunanta da qarfi, bud’e qofar toilet d’insu yayi yaqara shiga yana dudubata har bayan gambu kafin ya fito jikinsa na rawa yabud’e d’akin gaba d’aya, gaba d’aya ya manta darene haka yadinga kiran sunanta yana bud’e qofar kitchen, STORY CONTINUES BELOW  Jin qarara muryarsa da baffa Usman yayi yana kiran sunan matarsa yasa shi fitowa da sauri sanin halin haihuwar da a ciki ko yau ko gebe, “Nuraddeen lafiya.?” Baffa Usman yashiga bubbuga qofar shiyar tasa yana tambayarsa. Sai a sannan Nuraddeen yanufo wajen da sauri yabud’e k’ofar daidai lokacin shima Baffa yafito, tare suka had’a baki shida baffa Usman lokacin daya bud’e qofar suna tambayarsa ko lafiya?. “Baffa Rashida!.” “Me yasamu Rashidar?” baffa yatambayesa firgice ganin yanda yaga hankalinsa atashe, “Baffa ban ganeta ba…” Kafin ya rufe baki a tsorace baffa yatura kansa cikin shiyar baffa Usman na biye dashi yana fad’in “kamar ya baka ganeta ba, ita tsinken allurace da zaka nemeta cikin d’akin kuna tare k’arasa?.” Bayansu yabiyo tare dayin gaba yana fad’in “wlh baffa yanzu nabarta anan kwance nikuma nashiga in watso ruwa koda nafito ban ganeta banganta ba, dube dube suka shigayi suna leqe leqen cikin d’akin cike da mamaki, Tare suka fito da fitillu a hannunsa suna dudduba cikin gidan amma babu alamun Rashida balle mafarinta, “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, Inna lillahi wa’inna ilaihirrajiuun..” Nuraddeen yashiga fad’i yanajin kansa na jujjuya masa, “Baffa nashiga uku, dama yau jikina nafad’amun wani abu zai faru dani, baffa ina Rashida zata shiga awannan cikin tsohon daren ba tare dana sani ba?, Wlh baffa akwai abunda ke faruwa ba daidai ba.” “Nuradden ka kwantar da hankalinka za’a ganeta, abun tambayar a ina tashiga?” “Shine tambayar baffa, Kuma ko Ina akulle nagansa kamar yanda nabarsa, baffa kataimakeni inajin tsoro kada acutar mani da ita.” Nuraddeen yafad’a yana goge hawayen da suka fara yimasa kwaranya a idanuwa, ko Ina na cikin gidan su baffa suka shiga zazzagayawa harda Inna Bilkisu data farko lokacin hankalinta atashe jin abunda ke faruwa, d’akuna tashiga bi tana tambaya jikinta duk amace har zuwa wancan d’ayan b’angaren ‘yan uwansu dake cikin gidan amma amsar d’aya ce, ba’a ganta ba!. A cikin darenhankalin kowa yabi yatashi anata sallalami, baffa Ali kuwa kallon inna ruqayya da itama ta dan shiga tsinke yayi yana nuna mata Yaya hawwa dake tsaye ta rafka uban tagumi fuskata cike da damuwa kamar da gaske ammaqasan zuciyarta cike take da farinciki yace. “Dubi Yaya hawwa, narantse da ALLAH tasan komai, d’akin kalleta Zaki tabbatar da kawai tashuka tsiyar don farincikine tattare da ita bayan waccan damuwar da kika hangota aciki.” Murmushi tayi had’e da cewa. “Ranar bayyanar asalin tata damuwar nakusa tunda tagama cimma nata burin.” Ganin kowa yayi cirko cirko ana jajanta maganar b’atan Rashida yasa Nuraddeen yanufi qofar gida a hargitse yana sabbatu da sauri baffa Usman yariqesa yana fad’in, “Ina zakaje Nuraddeen acikin wannan tsohon dare, qarfe uku fa ake magana yanzu, kayi hak’uri har muga abunda safiya zatayi.” Wani irin kukane yazo masa yana kallon baffa Usman cike da mamaki yace “Baffa da bakinka kake fad’in inbar iyalina acikin wannan tsohon dare batare da sanin awane hali take cikiba?, Baffa amana ce fa agareni, bayan haka katuna halin da take ciki idan akace salame ce baffa kanaga zamu iya runtsawa awannan daren muna jiran wayewar safiya sannan muje nemanta?, Don ALLAH baffa kabarni inje koma meye yasameni nida ita, zuciyata nayimun rad’ad’in da zan iya mutuwa awannan lokacin idan natsaya dakon jiran dawowarta.” Yana gama fad’ar haka yabud’e gambun yafita batare daya jira amsar da zata fitowa daga bakin saba, dagudu ya fice cikin gidan ko fitila babu a hannunsa Saida yakusa kai farkon gari sannan yafara yawo yana kiran sunanta, inyayi nan yayi can batare daya damu da yanayin dare ko duhun dake da garinba., Idan yayi wancan lungu ya shiga wancan yakoma wannan haka yayita yawo yana kiran sunanta, kallo d’aya zakayi masa kasan kwanciyar hankali tagama gushewa a jikinsa, wasa wasa har qarfe hud’u tayi ba batun Rashida, kaf ya zagaye k’auywn nasu da qafa ko takalma bashida yana kuka yana ambatar sunanta tamkar wani k’aramin yaro duqewa yayi yasaki wata irin qara had’e da jin kansa yana jujjuya masa, yafi minti biyar ahaka kafin ya miqe tunawa da ‘yar qramar kasuwar garin da yayi ya nufi can da gudu, rumfuna rumfuna yadinga bi yana leqawa amma began taba, hanyar asibiti yanufa lokacin biyar da rabi na asuba yafara zagayenta tamkar wani tsohon mahaukaci sannan yashiga ciki yana lelleqa d’akunan majinyata, ganin nan ma Babu labarinta yasa yafara shiga dazukka dake cikin qauyen tamkar wani mashayi saboda yanda yake tangad’i saboda tsananin tashin hankali da gajiya, tun yana kuka har hawayen nasa suka qare, haka suma su baffa suka shiga nemanta cikin qauyen Amma babu labarinta, misalin qarfe shida na safe ko salla basuyi ba suka wuce qauyukkan dake maqwabtaka dasu amma har qarfe bakwai na safe balabarinta, a hanyarsu ce ta dawowa suka cikaro dashi saman hanya yashe mutanen gari sun zagayesa, da gudu baffa yaqarasa kusa dashi cike da damuwa ya tallabosa, ckallon yanda yayi bijib bijib da jiki ga qafafuwansa duk sun yayayyanke qaya ta sossokesa yasa baffa ya fashe da kuka yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, allahummah ajirni fi musibati wa’ahlifni khairan minha.” Cikin yanayin dake nuna Nuraddeen nacikin matsananciyar damuwa ya d’ago kansa yace, “Baffa kunga matata Rashida?. Baffa kubarni anan kuje kudubo mun ita, raina fansane agareta koda zan mutu kuje kutaimaketa, qarfina yaqare gaba d’aya, lumfashinanema yakeyi ya rabu da gangar jikina saboda rashin sanin a ina take, Kuma awane hali take ciki, baffa kutaimaketa jikina yana bani cewa Rashidata nacikin wani hali..” bai qarasa maganar ba sanadiyar lumfashinsa daya d’auke, jijjigasa baffa yashigayi yana kuku had’e da kallon baffa Usman da shima kukan yakeyi yace. “Usman kataimakeni kada inrasa d’ana da nafiso aduk fad’in duniya.” Kan baffa Usman yaqarso wajen har baffa ya ciccib’o Nuraddeen da sauri baffa yaqarasa wajen ya kama masa shi suka nufi hanyar asibiti dashi asheme ko motsi ba yayi. Kan kace me batu ya gama zagaye qauyen nasu cewa matar Nuraddeen ta b’ata da tsohon cikinta wata tara. Baffa Ali kuwa fad’a yakamayi yana fad’in tun farko Saida suka guji wannan auren saboda Babu alkhairi acikinsa yanzu gashinan zasu jawo masu abunda yafi qarfinsu don yasan iyayen yarinyar nan dole suje su kaiwa ‘yan sanda rahoto azo adamesu da ‘yan tambayoyi, Su baffa na isowa asibiti likita yaduba Nuraddeen tare da yimasa wasu allurai ya fad’a masu sumace yayi amma yanzu zai farfad’o, yana rufe baki Nuraddeen na tasowa da qarfi daga kwancen da yake akan gadon asibitin cikin matsananciyar qara yana fad’in. “Rashidaaaa….” *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU👏😭* [7/17, 11:04 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Amincin Allah ya tabbata agareku masoya littafin SANNU SANNU…haqiqa zan iya cewa tunda nafara littafinnan ban tab’a jin dad’in rubutunsa ba kamar jiya, saboda yanda naga ruwan comment d’inku har da wud’anda Raina bai tab’a kawomun cewa suna karatun saba, na matuqar jin dad’i har sai da zuciyata takoma tana rayamun cewa anya soyayyar da kuke yiwa Rashida batafi wacce kuke yiwa Billy ba?😰 What ever d case am feel a little jealous oo..😉lolz..nagode nagode sosai jazakumullahu bikhair, I LUV YOU ALL FILLAH_🤍❤️ Page___37💎 Juyowa su baffa sukayi tare da likitan suna rigegeniyar isa inda yake, tsaitsaye sukayi gabansa fuskokinsu cike da tausayinsa ganin yanda nan take duk yabi ya zabge kamar wanda ya buge watanni yana jinya, riqasa likitan yayi daga zaunen da yake ya maidashi kwance yana fad’in. “Relax malan Nuraddeeni, in Sha ALLAH komai zai daidaita kaji ko?” A hankali yarufe idanuwansa wasu zafafan hawaye suka zubo masa afuska, juyowa yayi yana yabud’e idanuwansa suka sauka saman na baffa Usman, kamo hannunsa yayi yariqe sosai har lokacin hawaye nazubowa daga cikin idanuwansa yace. “Baffa kun ganta kuwa?.” “Kayi hak’uri Nuraddeen, in Sha ALLAH za’a ganta, kafara qarfafa zuciyarka tukuna tayanda zaka iya fad’an nemo masoyiyarka aduk inda tashiga, kada kabari raunin zuciya ya bayyanarwa da duniya gazawarka ga masoyiyarka dake neman taimakonka takowane fanni.” Baffa usman ne yafad’i hakan yana rumqe hannunsa sosai, cikin yanayin dake bayyana dukkanin raunin da Nuraddeen ya samu ta fannin zuciya, gangar jiki, kwakwalwa da kuma ruhinsa yace, “kaicona da riskar wannan lokaci da nayi, meyasa mutuwa batayi gaggawar d’aukata ba kafin wannan ranar tazo mani?, Meyasa rayuwa zata yanke mana wannan hukunci a daidai lokacin da muke tsananin buqatar juna?, Meyasa soyayya tayimun d’aurin goron dana kasa gano alfanun dake cikin komawar Rashida agaban iyayenta saboda kawai Ina buqatar kasancewa tare da ita akoda yaushe? Meyasa duniya zata juya mana baya a lokacin da ALLAH keshirin yimana kyautar da zata bamu jin dad’in zamanta?, Meyasa?, Meyasa baffa?” Yaqarasa maganar yana qara fashewa da wani irin matsanancin kuka maicin rai, da sauri baffa yajuya yabar d’akin saboda bazai iya jurar sauraren kukan d’an nasa ba, kowace hawainiya dake d’igowa daga cikin idanuwansa jinta yakeyi tamkar saukar qyanqyashe a saman zuciyarsa, baffa Usman kuwa sake rumqe hannun Nuraddeen yayi sosai cikin dakewa yace. STORY CONTINUES BELOW  “Kayi haquri, kayi haquri, kajure kada zuciyarka tasa ubangijinka yayi fushi dakai, Babu dalilin dakesa ALLAH yayiwa bayinsa jarabawa kamar tsantsar imaninsu agaresa, wlh wlh Ina tabbatar maka da cewa duk inda matarka take bazata tab’a walaqanta ba domin ita yarinyace mai tawali’u ga ubangijinta, yarinyace mai tsananin riqo da addini da kiyaye dokokin ALLAH don haka dole ALLAH zai jarabceta harma damu dake tare da ita, saidai abu gudane nake da tabbaci akai da kuma kyakkyawan zato zuwa ga ubangijinmu cewa zai kula mana da ita aduk inda take fiye da kulawar da zamu yimata, mumunin k’warai shi ALLAH ke jarabtar kuma duk tsananin ibadarka da tsoron ALLAH bazai hana ajarabci imanin kaba saboda aqaramaka d’aukaka awurin ubangiji idan kaci jarabawarka, kayi haquri in sha ALLAH za’aganeta yau d’innan kaji ko?.” Duk da dai babu wani rad’ad’i da ya denaji azuciyarsa da kuma quncin dake damunsa ya yarda da duka kalman baffa Usman kuma zai gwada amfani dasu, kalaman data dinga fad’a masa daren jiya ne suka shiga yimasa yawo a kwakwalwa _Haba Nuraddeen, hasken idaniyata, zuciyata da kuma ilahirin gangar jikina, Kai kuwa meye zai tayar maka da hankali bayan kasan kanada ALLAHnka akoda yaushe kuma yana tare da kai, me zaka jiwa tsoro aduniya kai dake tare da sa albarka iyayenka, me kake shakku acikin rayuwarka bayan kana da yaqini akan zamu kasance atare, don ALLAH kadena fargaba akan komai koda kuwa wani abunne zai sameka ko kuma ya sameni, natabbata cewa tsantsar imaninmu da miqa wuya ga ALLAH shine kan iyasa ajarabcemu, muzama masu juriya cikin al-amurranmu alokacin da wani abu kenema ya gitto mana cikin rayuwa, sai musamu kanmu masu riskar ubangijinmu amadakata kyakkyawa, kacire komai aranka in Sha ALLAH babu abunda zai faru, nasan harda tunanin haihuwarnan yasa kakejin haka, to kasanyawa ranka salama in sha ALLAH zan sauka lafiya kuma zan haifa maka chuluv d’inkacikin qoshin lafiya kaji ko_ Tsananin jin yanda kansa keyi masa ciyo tamkar zai tsage yasa yai saurin dafe kansa da hannu bibbiyu yana sakin wata qara, da gudu baffa yadawo cikin d’akin ya tsaya yana fad’in. “Nuraddeen kayi haquri karka jawo nima in rasaka.” “Baffa kaina zai fashe.” Nuraddeen yafad’a hawaye na dararo masa ta gefen idanuwa, juyowa baffa yayi yana kallon likita dake gefensa yace. “Likita don ALLAH kuyi masa allurar bacci koya samu koda ‘yar qaramar natsuwa ce azuciyarsa.” “Abunda nake tunanin yi kenan nima.” Likitan yafad’a tare da ciro biro a aljihunsa ya rubuta masu allurar bacci yace aje asiyo, baffa Usman ne yakarb’a da sauri ya nufi gefen da pharmacy take acikin asibitin ya siyo yakawo masa, daidai bakin qofar da zai shiga d’akinne yaci karo da baffa Ali suka shiga tare, miqawa likitan dake can gefen wani marar lafiya yana sa masa drip allurar yayi yace yadwo nan inda Nuraddeen d’in yake ya jirasa, shi Kuma baffa Ali tsaye yayi saman kan Nuraddeen yana kallon yanda ya zabge lokaci d’aya, ajiyar zuciya yayi sannan ya maida kallonsa ga baffa dake tsaye yace. “Yaya Ashe jikin nura haka yazama, ni yanzu yaran gari sukaje suna fad’amun cewa ai kunanan asibiti da nura ya zauce saboda b’atan matarsa” “To kadai gani Ali, jarabawar da ALLAH yad’oro muna kenan! Ubangiji ALLAH yabamu ikon canyeta.” “Amin Yaya, Amma to ba wannan ba yakamata yaronnan yasawa ransa salama, idan ALLAH yatsaro za’aga yarinyarnan to za’a ganta, in Kuma ALLAH be nufa ba to yayi haquri basai yaje ya illata kns ba zai samu wata matar tunda ba ita kad’aice mace ba, mata ne gasunan ko ina sai yazab’a ya darje, nan kusa ba nesa ba ga ‘yar uwarsa nan muneera sai tamaye masa gurbinta ai inaga shikenan ko?” Cike da b’acin rai baffa ya nufosa had’e da shaqe wuyansa ya had’a da jikin bango. “Aliyu dama kai bakada hankali ban sani ba? Mekake nufi da idan ba’a ganeta ba? Wlh damuwata tafi yawa akan b’atar yarinyar nan fiye da halinda Nuraddeen ke ciki domin nasan cewa ganinta ne kad’ai zai kawo masa sassaucin wannan halin da yake ciki saboda itace farincikinsa, shine kake fatar kada aganeta saboda ita d’in ba ‘yarka bace?, Yaqarasa maganar cikin d’aga murya tare da qara shaqesa tayanda ko lumfashi mai kyau baya iyayi, kakarin d’aya farayi ne yasa baffa da likita sukayo kansa suna rirriqesa amma suka kasa cire hannunsa daga wuyansa, cikin b’acin ran daya sauya masa kalar idanuwansa dake fari izuwa jajaye yace. STORY CONTINUES BELOW  “Kaje ka muri sauran mintotan da suka rage maka kafin jami’an tsaro su iso gareka, Ina tabbatar maka da cewa dukkaninku sai nasa ansa kunfad’i inda kuka kai yarinyar mutane, idan ba haka ba zanyanke duk wata alaqa da Kuma ‘yan uwantakar dake tsakanina dakai nasa akulleku har sai natabbatar da kunfad’i inda take tukuna.” Yana gama fad’ar haka ya sakesa tare da wullasa gefe sannan yabar d’akin da asibitin gaba d’aya, baffa Usman ne ya tsaya har saida akayiwa Nuraddeen allurar bacci wanda duk abunda ke faruwa idanuwansa kad’aine arufe amma yana saurarensu. Take bacci ya d’aukesa bayan an laqa masa gorar ruwa guda. Juyowa yayi yana kallon baffa Ali da har lokacin ke zaune qasa yana lalubar wuyansa saboda azabar zafin riqon da baffa yayi masa a kuma lokaci guda yana fidda lumfashi d’aya bayan d’aya yace. “Ga d’anka nan ka kula dashi idan kaga dama, idan kuma baka gani ba zaka iya tafiya.” Yana kaiwa nan shima yabi bayan baffa, har yakusa fita ya juyo had’e da cewa. “Yawwa Ali namanta in fad’a maka cewa zaka iya qarasa rayuwarsa idan kana buqata tunda bakwason ganinsa cikin farinciki balle raye.” Sannan yawuce. ••• ••• ••• A gefen wani babban titi shed’anin da bargaji yaturo ya sace Rashida ya jefar da ita bayan yagama azabtar da ita lokacin qarfe hud’u da rabi na dare ko motsi batayi, abunda ke cikinta sai faman motsi yakeyi saboda azabar daya sha ga lumfashin uwa dake taimaka masa na neman yarabu da gangar jikinta, cikin iyawar ALLAH da nuna isarsa ga bayinsa da sukayi imani dashi kuma yake taimaka masu alokacin da suke neman taimako yasa sanyin asuba nafara sauka lumfashin Rashida ya daidaita ga gangar jikinta, wani dogon lumfashi taja had’e da qoqarin bud’e idanuwanta a hankali a hankali, ganinta agefen titi gashi duhu ya mamaye gari ko hasken mota bata gani saboda dogayen ciyawun da sukayi shamaki tsakaninta da titi balle ahangota yasa tafara qoqarin tashi, bataji wani dogon rauni ba a zahirance sai ‘yar gugguljewar da ko ina ajikinta yayi da kuma azabar da takeji can cikin qashin bayanta da kuma mararta wanda in bata manta ba acikin wannan halin take kafin ta tsinci kanta acikin wannan yanayin da take kallo tamkar mafarki, jin an shureta cikin ciki ya tuna mata da d’an dake cikinta da sauri tasa hannu tana tattab’a cikin, duk inda taji alamun abunda ke ciki yayi motsi sai takai hannunta akai shi kuma sai ya janye yakoma wani gefen, haka ta dingayi tana murmushi kafin tafara qoqarin fitowa daga cikin ciyawun tana takawa da qyar saboda nauyin cikin. Hango wani haske da tayi acan tsallaken titi yasa tayi yunqurin tsallakawa don samawa kanta tsaro daga abun dakan iya cutar da ita awajen. K’iiiiiiiii…kakeji da qarfi motar dake tafe gabanta da gudu matuqin yaja burki ganin mutum ya gitta masa, nan take tsananin tsoro daya gama zama abokin rayuwarta yasa tasaki wata irin qara tare da duqewa wajen, k’iris kad’an ya rage Mai motar yabugeta Amma ALLAH ya taimakesa kafin motar takai ga jikinta yayi nasarar tsaida ita, qara hasken fitillun motarsa yayi don gasgata idanuwansa dake gane masa mace da tsohon ciki agabansa, da sauri ya bud’e motar yafito jin wata irin qara da Rashida tayi tana fad’in, “Wayyo ummata zan mutu.” Saboda azabar naqudar da tataso mata lokaci guda, “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun., Baiwar ALLAH daga Ina? kike da asubancin nan haka?” Kasa magana tayi sai yarfi da hannu takeyi tana cizon baki, kallo d’aya yayi mata ya fahimci haihuwace zatayi saboda ganin ruwan dake bin qafafuwanta Wanda bako shakka fawace tafashe. Gabas da yamma, kudu da arewa yaduba Babu wani mahaluqi dake tahowa daga saman titin, shimad’in yayi sakkon fitowane saboda wani emergency operation da aka kirasa cewa zaiyi da safennan, shine dalilin fitowarsa cikin sauri zaije airport don ya hau jirgi sai gashi ya had’u da wannan tsotsayin, sake kallon Rashida yayi yaga she’s too young da alama ma haihuwar farince duk rashin imaninsa bazai iya barinta awajen ba, gashi tana stage d’in da take matuqar buqatar taimako, bai tsaya saurarar zuciyarsa ba kawai ya runtse idanuwa yana karanto addu’a daga bakinsa ya tallabeta ya sakata cikin motar ya tayar ya nufi hanyar asibiti mafi kusa dasu acikin garin, kallon yanda take nishi da qarfi alamun haihuwar na kusa yakeyi had’e da qara gudun motarsa, A wata qatotuwar asibiti yayi parking had’e da fitowa da sauri ya bud’e bayan motar ya sake d’aukota yanufi cikin asibitin da ita yana kiran “nurse, nurse..” da gudu suka fito suka karb’eta suka nufi cikin wani d’aki da ita, wata nurse ce tashiga da sauri cikin wani office tayowa dr dake on duty magana suka fito tare da ita, har zasu shiga d’akin da aka shiga da Rashida yayi saurin tsaishesu yana fad’in STORY CONTINUES BELOW  “Dr. don ALLAH ka taimakawa yarinyarnan, haihuwa ce zatayi kuma inaga wannan itace tafari, ga dukkan alama yamatuqar Shan wahala don tadad’e tana labour, yanayinta ya nuna tayi riching final stage da zata iya haihuwa wato 10cm don ALLAH kayi iya qoqarinka wajen taimakonta ta haihu lafiya.” Yaqare maganar yana had’a hannayensa waje d’aya, riqa hannunsa Dr yayi yana mai bashi k’warin guiwar cewa zai iya sannan ya wuce batare daya tanka ba. Safa da marwa mutumen ya dingayi abakin d’akin yana mai addu’ar ALLAH ya sauketa lafiya kafin yaciro wayarsa yakira matarsa. Bugu d’aya ta d’aga had’e da cewa. “Swthrt har ka isa airport d’in.” Cike da damuwa yace “A’a fatima banma je wajen ba, yanzu haka Ina asibiti..” miqewa tayi daga kwancen da take ta tashi zaune had’e da cewa “swhrt lafiya kuwa? meya same kane? Dama tunda zaka tafi Saida nafad’a maka hankalina bai kwanta da tafiyarnan ba qara kabari sai safiya tawaye ido naganin ido amma ka nace kai sai alokacin zaka tafi.” Taqare maganar had’e da fashewa da kuka. “Haba Fatima meye haka kikeyi? Kinaji na ki saurareni kiji me zanfad’a, Babu abunda ya sameni kawai ansamu matsalace akan hanyata ta zuwa filin jirgin…” Nan yaciga da yimata bayani dalla dalla sannan takwantar da hankalinta, cike da damuwa yaci gaba da cewa. “Idan zaki iya munanan _mom maternity clinic_ kiyi sauri kizo kinji ko.” “On my way Dr. In Sha ALLAH.” Tafad’a tana goge hawayenta had’e da kashe wayar. Daidai lokacin shima yasaki wata irin ajiyar zuciya tare da runtse idanuwa saiga likitan yafito da sauri ya nufo inda yake tsaye. “Dr. Lafiya?.” Mutumen yafad’a yana kallonsa cikin tashin hankali, shiru Dr. ya d’anyi kafin ya kallesa had’e da cewa. “Am sorry ansamu matsala. Dole zaka samana hannu anan.” Yajuya wajen nurse d’in dake biye dashi ya karb’i takarda a hannunta yana miqa masa. “Zaka saka hannu saboda dole sai anyi mata tiyata bazata iya haihuwa da kanta ba.” “Kamarya Dr.? Inada tabbaci akan takai adadin yanda ake buqatar ta haihu mezaisa kace Kuma bazata iya haihuwa ba yanzu.” “Saboda yaron baizo daidai ba, ma’ana amai makon yazo takai sai yazo ta qafafuwa aturance muna Kiran irin wannan haihuwa da “breech presentation” wato haihuwar da tazo a baibai ba normal haihuwa ba.” Shafa kai mutumen yayi had’e da cewa. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun.” Kafin yafiddo wasu i.d card guda uku had’e da license d’insa nazama likita a aljihunsa ya miqa masa da sauri, karb’a Dr. Yayi ya shiga dubawa, d’aya national i.d card d’insa ce, d’aya kuma i.d card d’in dake nuna yana aiki a qarqashin asibitin aminu kano ce dake garin birnin kano, d’ayar kuma shedar cewa shi qwararren likitane a fannin matsalar mata wato (gynicolgy) inda yaga an rubuta Dr. Nura ahmad. ‘Dauke da lambobin dake nuna cewa shi cikakken likitane babba a fannin wato (consultant). ‘Dago kai Dr yayi yana kallonsa ya jinjina masa kai alamar bashi tabbaci akan abunda yagani, cike da girmamawa Dr. Yasake bashi hannu suka gaisa saboda ganin shi babban sane. “Don Allah Dr zan iya shiga na taimaka mata?. Nasan insha ALLAH zata iya haihuwa da kanta basai anyi mata tiyata ba.” Shiru Dr yayi kafin ya bashi hanya yana nuna masa qofar shiga d’akin, da sauri ya shiga ya tarar da Rashida kwance ta matuqar jigata, nan take yasa handglove batare daya cire kayan dake jikinsa ba ya nufi inda take kwance, Saida yafara zuwa saiti fuskarta yace. “Kiyi fad’a da kowace irin qadadara ce data fiddoki cikin dare awannan yanayin, ki qoqarta wajen ceto abunda kecikinki inada tabbaci akan komeye zai zamo sanyin idaniyarki, kada kibari qaddararki ta rinjayi nasararki wajen rasa abunda ke cikinki ta hanyar gazawarki, kiyi addu’a kuma ki jajirce kibamu had’in kai in sha ALLAH zamuyi nasarar wannan aikin da zamuyi.” Binsa kawai Rashida tayi da kallo batare data iya tanka masa ba hawaye na tsiyaya tagefen idanuwanta, tabbas ba k’aramin tasiri kalamansa suka yimata ba hakan yasa taquduri bayar da rayuwarta ga abunda ke cikinta. STORY CONTINUES BELOW  Nan take yafara ba nurses d’in umurnin miqo masa kayan aiki, cikin k’warewa da hikima irin wadda aikinsa ya koyar dashi yafar qoqarin jujjuya yaron da zimmar mayar dashi ya koma daidai, fiye da mintuna ashirin ya kwashe yana abu guda amma hakan ya cutara, kallon irin wahalar da tasha yayi amma duk da haka bata sare ba da sauri yasa hannu ya goge hawayen da suka zo masa tare daba nurses d’in umurni dasu canzo masa kayan aikin da zai karb’i haihuwar ayanda yaron yazo koda kuwa za’a rasa ranshi saboda aceto rayuwarta, Nan take aka had’a komai yashiga fara aikin cike da addu’ar ALLAH yasa ayi nasara, kusan wasu mintuna ashirin ya kwashe sannan yayi nasarar fiddo da yaron lafiya, yana fiddosa na’ura nagwajin d’aukewar lumfashin Rashida, haka shima yaron tsabar wahalar daya sha koda aka cirosa ko motsi baya yi, da sauri yajawo oxygen d’in dake can gefen gadonta ya harhad’a ya jona mata da taimakon nurses d’in dake wajen…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/18, 10:56 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___38💎 Juyowa yayi yana kallon Dr dake wajen tare dashi wanda yakamata ace shine ya karb’i haihuwar ya miqa masa hannu suka gaisa sannan yace. “Nagode sosai, in Sha ALLAH zata samu lafiya, ayanayin wahalar da tasha dole nasan hakan zata kasance, nayi abunda na Nemo alfarmaryi sauran kuma nagareku.” Yaqarasa maganar yana cire handglove d’in dake hannunsa, murmushi Dr yayi yana yabawa qwarewar Dr. nura tare da jinjina masa akan namijin qoqarin da yayi, wanda badon haka ba babu ko shakka saidai suyi mata tiyata gudun abunda zai iya faruwa da ita ko d’anta, solutin nasa yayi shima had’e da cewa. “Weldone sir, sunana Dr sani Bilal Ina zaunene d’aya daga cikin gidajen dake cikin asibitinnan, naji dad’in had’uwa dakai sosai.” “Masha ALLAH sunana..” saurin katsesa yayi tahanyar fad’o masa cikakken sunansa daya gani arubuce jikin i.d card d’insa ta asibiti wato “Dr. nura shu’aib k’wararren likita afannin matsalolin mata dake aiki da asibitin aminu kano dake garin kano.” Murmushi yayi sannan yanufi gefen da nurses d’in ke gyara babyen har lokacin be koka ba, karb’arshi yayi ya d’aga qafafuwansa sama kansa na qasa yad’an twad’i d’uwawunsa sai gashi ya canyara ihu, murmushi farinciki yayi sannan ya miqa masu shi yana kallonsa, yaron kyakkyawane sosai gashi da girma tubarkallah, kallo d’aya zakayiwa jaririn kafahimci ba qaramin kulawa yasamu ba alokacin da yake cikin ciki, yana wannan tinaninne yaji wata nurse a firgice tace. “Dr….” Saboda ganin yanda yaron yafara amai yana fizge fizge, da sauri ya qaraso wajen ya karb’esa nan take yagano yaron yasha ruwan naquda, qoqarin zuqe masa su ya shigayi da taimakon Dr sani da gaba d’aya hankalinsu ya tashi, miqa masu shi yayi yace suyi maza maza su kaishi sashen ba jarirai taimakon gaggawa, haka kuwa akayi kafin kace me har sun isa wajen nurses d’in b’angaren suka karb’esa suka fara bashi kulawa kafin likitan dake b’angaren yaqaraso, yana zuwa yashiga duddubasa cikin k’warewa da iya aikinsa. Bayan komai ya daidaita shima yaron aka saka masa oxygen saboda yanda lumfashinsa ke kokuwar barin jikinsa. Dr. nura kuwa nurses nafita da jaririn ya nufi inda Rashida ke kwance ya qura mata idanuwa, gaba d’aya kamannunta dana yaron sunsha banban, wataqil shi mahaifinsa yabiyo, Yafad’a aransa, ficewa yayi daga d’akin yana tura hannuwansa cikin aljihu, sai alokacin ya tuno da wayarsa daya ajiye a can gefen gadon da Rashida take kwance da sauri yakoma ya d’auko, kusan 10missed call yagani Kuma duka na matarsa ne fatima wacce take da tabbacin tashigo asibitinne shine takirasa taji inda take, murmushi had’e da danna lambar ya sake kiranta, bugu d’aya ta d’aga tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Swthrt kana inane? Tun d’azu kabarni a tsaye.” Tafad’a cike da qorafi akan haka. “Fatima kenan! Yihaquri ki qaraso tanan gyani emergency Ina tawurin tsaye Ina jiranki.” “To.” Tafad’a had’e da kashe wayar sannan tanufi hanyar da zata sadata da wurin, daidai lokacin shima yanufo qofar fitowa daga wajen sukayi kicib’is da ita d’auke da kwandon kuloli har dasu qatuwar leda da flaks, zaro idanuwa yayi yana kallonta cike da mamaki yace. “Fatima duk meye haka?” dubon agogon hannunta tayi taga kusan qarfe goma da rabi na safe ta dafe kai had’e da cewa. “Kayi haquri nadad’e ban qaraso ba ko?, natsaya had’a mata wud’annanne, Ina jarin da aka haifa? tahaihu ko?” Tafad’a tana gyara zaman mayafinta cike da tausayi yabita da kallo, daga jin cewa ya tsinci maiciki a hanya suna asibiti zata haihu shine Fatima zata had’o wud’an abubuwa haka saboda tsananin son haihuwa da take da ita, ya ALLAH kadubemu da idon rahama muma kabamu namu masu albarka, yaqarasa fad’a aransa yana goge ‘yan kwallan tausayinta da suka zubo mata. ••• ••• ••• Dr nura da Fatima mijine da mata dakeda matuqar kyakkyawar fahimta a tsakaninsu, kalla d’aya zakayi masu kafahimci aurensu auren soyayyane saboda yanda suke matuqar son juna, sunyi aure tun shekaru goma sha uku da suka wuce amma har zuwa tsawon wannan lokaci basu samu haihu ba, Fatima macece mai matuqar son yara amma jarabawa ta ALLAH ko b’atan wata bata tab’a yiba, anyi masu duk wasu gwaje gwajen da bincike bincike don agano dalilin rashin haihuwar tasu amma likitoci sun tabbatar masu dashi har ita duka lafiyarsu qalau basuda wata matsala data hanasu haihuwar kawai lokacine beyi ba, hakan yasa gaba d’aya suka tattara komai akan batun haihuwa suka watsar gefe suka rungumi junansu hannu biyu cikin so da qauna da kuma kulawar juna, fatarsu akoda yaushe da addu’arsu shine ALLAH ya basu masu ‘ya’ya masu albarka aduk lokacin daya so kuma yanufa, Dr nura cikakken d’an asalin jahar borno ne amma wasu lokutan suna zama a kano saboda aiki daya kaishi can, dalilin fitowarsa yau tunda asuba shine kiran gaggawar da akayimasa tun jiya da daddare ne cewa ana buqatar ganinsa gobe qarfe takwas na safe akwai matar da zasu yiwa tiyata, shiya yayi asubancin tashi zuwa filin jirgin da zai tashi qarfe biyar na asuba don ya isa dawuri, ashe rabon ya taimaki Rashida a wannan lokacin ya fiddosa. ••• ••• ••• Wata irin ajiyar zuciya Dr. nura ya sauke had’e da riqo hannunta yace, “Kai fatima daga fad’a maki zancen matar nan zata haihuwa shine zaki tsaya kwaso kaya haka!.” Dariya kawai tayi masa batare da tace komai ba saboda Babu abunda takeso alokacin irin taga matar da yace ya tsinta da babyn data haifa, d’akin da Rashida ke kwance yanufa riqe da hannunta har suka shiga. A bakin gadon Rashida yaja burki ya tsaya yana nunata da hannu. “Fatima kinga baiwar ALLAH da nake fad’a maki nagani tafito daga cikin wani daji tashigo gaban motata, badon ALLAH yatsare ba dana bugeta gata da tsohon ciki.” Cike da tausayi tariqe hannunsa gam kamar zatayi kuka yace. “Swthrt meya fiddota waje a lokacin gata qaramar yarinya mai qanan shekaru, yanzu haka sharri da baqincikin d’a namiji yasata fitowa, kai walh wasu mazan basuda imani.” “A’a fatima karkice haka tunda bamusan dalilin daya fiddota be daga gida ba, wataqil wata matsalarce daban.” “Hmm! Bazaka gane ba swtht wlh yanzu hakan mijinne yakorota saboda wani banzan dalilinsa, ya ALLAH kadubi maraicinmu.” Tafad’a tana d’aga hannuwanta sama hawaye nazubo mata daga cikin idanuwa, qara matsowa tayi kusa da Rashida taduqo had’e dasa hannu tana shafa fuskarta, “ALLAH sarki yarinya, ALLAH yatashi kafad’unki, wlh swthrt da ganin yarinyar nan akwai ban tausayi cikin al-amarinta, yanzu I babyn nata yake?” “Yana can shima anbashi gado bayada cikakkiyar.” Yafad’a tare da juyowa yafito wajen tana biye dashi ya zuba hannayensa acikin aljifan wandonsa, kallonta yayi yaga yanda gaba d’aya jikinta yayi sanyi, murmushi yai sannan yaci gaba da cewa “muje can kiga yaron nata, so nake idan kin amince nabar komai ahannunki kafin nadawo nan da zuwa jibi idan yafarfad’o muji daga Ina take, thank God ma nayi waya da Dr qasim can wajen aiki yace anyi shifting theater da zanyi sai nan da 24hrs saboda jinin patient d’in daya hau sosai.” STORY CONTINUES BELOW  “Babu damuwa swhrt ALLAH yabasu lafiya, idan da imani da tausayi a qirjin bawa ko bakasan mutumba ai katausaya masa, shikuma taimako bakasan ta inda zai yimaka rana ba wataran, na amince Babu wata damuwa akan haka.” “ALLAH fatina?” Dr nura yafad’a yana dariya. “Sosai kuwa, yanzu kafasa bin jirgi kenan?” “Eh da motar haya zanje sai inbar maki wannan koda wani abun zai taso, zan kira Salim ya kasance kusa idan kina buqata.” “Noo..kabarshi kasan bama inuwa d’aya da qanennan naka yafiye reni da yawa.” “To shikenan muje kigano yaron.” ••• ••• ••• Baffa kuwa na fitowa daga asibiti kai tsaye gida yanufa ransa duk a dagule, gaba d’aya ya rasa mekeyi masa dad’i aduniya, yana shigowa cikin gidan ya tarar da yaya hawwa zaune a bakin rumfarsu Inna ruqayya takira mai tallar fankasu (na alkama) ta tasashi agaba sai ci takeyi tana dangwala yaji, tana ganin lokacin da baffa yawuce ta gabanta fuskarsa cike da damuwa amma ko kallon banza bi isheta ba, saida taci mai isarta taqoshi sannan tamiqe had’e da cewa yaron ya jirata tana zuwa ta karb’o masa kud’insa. ‘Daki ta iskosa zaune abakin gefen gado ya rabka wani uban tagumi yana tunanin ta inda zai fara sanarwa da iyayen Rashida halin da ake ciki, cikin nuna halin ko inkula akansa tace. “Malan bani naira d’ari in biya yaron can kud’insa na fankasu dana ci.” Tafad’a had’e da tura yatsa cikin baki tana qwalqwalo wanda ya laqemata a hauru, hannunsa yasa cikin aljihu yaciro d’ari biyu ya miqa mata ta amsa ba gode balle nagode taficewarta, ba’a jimaba tadawo tamiqo masa canjin naira d’ari ya sake miqa hannu ya karb’a yatura cikin aljihu, “Yawwa nace ina nura take?, Nifa tunda yafitarnan hankalina ba kwance yake ba kar yaje garin neman gira ya rasa ido…” Ai kafin tarufe baki baffa yamiqe tsaye yana nunata da d’an yatsa had’e da cewa. “Qarya kike, wlh qarya kikeyi kice kindamu da Nuraddeen, wai yanzu ke a tunanin ki ke uwace ahaka? tir da halin uwa ko in haka take, maqaryaciyar banza maqaryaciyar wofi, shashasha da batasan abunda takeyi ba, sakaryar uwa kawai to kitambayeni Nuraddeen damuwa kikayi dashine ko a’a?” “Ya haka malan sai kace wanda ke jiraye dani daga tambayarka yarona saika rufeni da kwandon fitina?” “Naji hawwa jiraye nake dake amma idan harda gaske kikeyi kina son ganin d’anki sai kifad’a mani ina ‘yar mutane take tukuna, don bana haufi akan cewa duk inda yarinyarnan taje ko aka kaita kinada sa hannu aciki, don haka kifad’amun inda yarinyar mutane take naroqeki da ALLAH.” “Buhun ubannan, lallai malan kace wani abu, meya dameni da wannan yarinyar da har zakace akwai sa hannuna aciki, to wlh kul kar inji…” Bata rufe baki ba ya d’auketa kyakkyawan marin da saida ta birkita, kafin ta taso yaqara mata wani, zuciyarsa na tafarfasa yace. “Anzo wajen hawwa, ahalin yanzu bana yimaki kallon daraja da kimar cewa ke matatace, baki isa kiyi mani jan kunne ba agabana, ayau kimanta da cewa ni Idris d’innan ne da kika sani mai sanyin hali da kuma haquri, wannan Idris d’in dake gabanki shirye yake daya sallamaki har abada, ahalin yanzu ba duka kad’ai da ALLAH ya haramta miji yayiwa matarsa ba hatta azabtarwar da zata iyasa kirasa rayuwarki na har abada zan iya yimaki saboda zaluncin da nake tuhumarki da aikatawa yarinyar mutane, don haka tun wuri ina fad’a maki kitanadi kalaman da Zaki fad’awa jami’an tsaro idan sunzo takanki don wlh bazan bar duk wanda keda hannu acikin b’atar yarinyar nan ba. Tsaye Yaya hawwa tayi tabisa da kallo cike da mamaki don ko amafarki Bata tab’a tsammanin cewa baffa zai iya yimata hakan ba, tureta yayi daqarfi daga gabansa da take yawuce yabar d’akin, yanajin yanda tafad’a akan qarfen gado kanta yabuge qum..amma ko juyowa beyi ba balle ya kalleta ya wuce abunsa zuciyarsa cike da tsanarta , Shikuwa Baffa Usman yana fitowa daga asibiti kai tsaye tashar mota yanufa ya shiga motar da zata kaishi cikin birnin kano, gidajen redio da telebijin yaje yabada iya kud’ad’en dake hannunsa don asa masa sanarwar b’acewar rashida ta kafafen labarai saida ya tabbatar anyi komai tukuna sannan yashiga motar da zata kaishi qauyen yarimawa, cikin sa’a ya tarar da malan balarabe yazo wajen baba, cike da karramawa suka tarbesa duk da dai fuskarsa ta gama nuna baya cikin yanayi mai dad’i. Bayan sun gaisane cikin natsuwa yayi masu bayanin halin da ake ciki ya qara masu da cewa yanzu haka shima Nuraddeen d’in yana asibiti rai a hannun ALLAH, STORY CONTINUES BELOW  “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun” kad’ai baba ya iya furtawa daga nan bai koma cewa komai ba saidai sukaga ya b’ingire qasa daga zaunen da yake, ranar baffa Usman yaga tsantsar tashin hankali wanda ba’a samasa rana domin adaidai lokacinne itama umma data shigo d’akin kawo masa ruwa ashe duk abunda baffa Usman ke fad’a taji da kunnenta ne saidai sukaji fad’uwar kofin dake hannunta kan kace me itama tafad’i wajen a some… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/19, 6:49 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___39💎 Cike da tashin hankali baba balarabe yaje ya d’ebo ruwa cikin gida aka yayyafa masu, kusan atare suka farfad’o amma babu wanda ke iya magana acikinsu, banda hawaye babu abunda kezuba daga cikin qwayar idanuwansu, ganin haka yasa malan balarabe yaje wajwn nemo mota don akaisu asibiti, yace wa baffa Usman dake gefe ya rabka uban tagumi cikin yanayi mai wuyar fassarawa yajirasa nan da mintota zai dawo. Kallo d’aya zakayi masu kasan akwai maganganu acikin bakinsu saboda yanda suka qurawa baffa Usman idanuwa Amma Babu bakin magana sai hawayen kawai da zasu iya fassara maka yanayin da suke ciki, ba’a jima ba malan balarabe yadawo da mota da Kuma matarsa d’aya don seda yakoma go ya d’auko kud’i, nan take suka d’aukesu suka nufi asibiti, Waya baffa Usman ya d’aga yakira baffa yace ya iskosa yarimawa ga abunda ke faruwa yanzu haka suna asibiti, cikin azama baffa yakamo hanya batare daya sanarwa da kowa halin da ake ciki ba, tafe yake yana addu’o’i abakinsa har yasamu mota, tund’azu ALLAH ne kad’ai yasan awane yanayi baffa kejin kansa saboda tunanin yanda zai fuskanci iyayen Rashida ya sanar dasu zancen b’atar ‘yarsu ashe har d’an uwansa yaje yasanar dasu, saidai ayanayin daya ce suke ciki yanzu kuma shine babban abunda yafi d’aga masa hankali, har aka iso qauyen yarimawa baffa baisan an iso ba saboda tsananin yanda damuwa tayi awan gaba da dukkanin ilahirin natsuwarsa. Kai tsaye asibitin ya nufa yatarar dasu baba balarabe da baffa Usman tsaitsaye cikin halin jimami suna jiran fitowar likita, qarasowa wajensu yai jikinsa duk Babu qwari, cike da jin kunya had’i da damuwa yaba malan balarabe hannu suka gaisa, fuskarsa asake ya amsa masa yana mai tambayarsa halin da Nuraddeen ke ciki tare da jajantawa juna akan abunda yafaru, suna nan tsaitsaye likita yafito ya nufo inda suke, tambayarsa suka shigayi ya jikinsu baba da umma yace su biyoshi office tukuna, Baffa da malan balarabe ne zaune saman kujerun dake kallon likitan shi Kuma baffa usman na tsaye, seda Dr yayi gyaran murya sannan yafara fad’a masu halin da suke ciki, Sanadiyar tashin hankali da baba yashiga a lokaci d’aya ya haifar masa da ciwon hawan jini wanda ahalin yanzu yakamu da mutuwar sashen jiki ma’ana yasamu (stroke), ita kuma umma sun dubata amma sun kasa gano abunda kedamunta ba abunda take kira inba Rashida ba, wanda hakan yasa dole sai munyi mata gwajegwaje a qwaqwalwarta ko anan ne tasamu matsala. Wannan shine cikakken bayanin da likita yayi masu akan binciken da sukayi, gaba d’ayansu sun shiga tashin hankali jin abunda likita yafad’a “innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, ALLAH Kai kasan dalilin jarabta wud’annan bayi naka, ya ALLAH ka samasu hak’uri da juriya kuma kabayyana masu ‘yarsu aduk inda take.” malan balarabe yafad’a had’e da sakin wata irin ajiyar zuciya. STORY CONTINUES BELOW  Baffa da Baffa Usman kuwa jin duniyar sukayi gaba d’aya tayi masu k’uncin da suka rasa sanin ina zasusa kansu. ••• ••• ••• A ‘bangaren Nuraddeen kuwa tun safe bai farko ba har sai bayan sallar la’asar, ko daya farfad’o yad’an samu sauqi sosai amma yana tuna zancen b’atan Rashida zazzab’i yataso masa, cikin qarfin hali yamiqe ya sauko daga kan gadon yana yatsina fuska, ganin bakowa wajen yasa yamiqi hanyar fita cikin asibitin don baffa Ali da aka bari ya kula dashi tuni yabar wajen, acan bakin wata bishiya ya hangosa shida wasu yasa andamamasa furarsa hankali kwance yana sha suna fira, bai tsaya bi takansa ba ya wuce gida, tafe take yana harhad’a hanya har ALLAH yasa ya isa gida lafiya, sashensu yanufa ya shiga cikin d’akin, tsaye yayi yana kallon ko ina cike da fatar zaiga Rashidarsa ta iso gare adaidai lokacin, yafi minti biyar ahaka kafin ya duqe wajen yasaki wani irin kuka mai tsima ran duk wanda ke saurare, jin yayi andafo kafad’arsa da sauri yaciro kai yana kallon sama cike da zimmar ganinta amma sai yaga ashe Inna Bilkisu ce, hannu tasa tagoge masa hawayen da suka jiqa masa fuska sannan ta riqosa ya tashi ta azasa saman kujera, cikin sanyin muryar dake nuna tattare take da damuwa tace. “Nuraddeen bazan hanaka kuka ba, domin b’atan Rashida ba kai kad’ai yashafa ba har mu, Amma Nuraddeen Ina so infad’a maka cewa yanzu ba lokacin kuka bane agareka, lokacine da zaka tattaro dukkanin natsuwarka kayi yaqin gano matarka aduk inda take, Ina so kayi amfani da kud’in da kake dasu ahannunka, iliminka da kuma qarfin jikinka kaje kagano matarka aduk inda take, wannan kukan da wani kwanciya duk ba mafita bane agareka, kazuba kud’inka a kafafan yad’a labarai asa maka cigiyarta, kayi amfani da iliminka wajen tsananta addu’a kuma kasa malamai ayi maka, kayi amfani da qarfin jikinka wajen shiga lungu da saqo kadubo matarka, idan ALLAH yayi za’a ganta Ina tabbatar maka da zaka had’u da ita tunda baka zauna ba kaji ko, don ALLAH kadaure duk yanayin da kake jin kanka aciki kanunawa duniya cewa kana son iyalinka ko tana tare da kai ko bata tare dakai, damuwa dolece amma kada kabari tayi tasirin da zata cutarwa da Rashida kai, don na tabbata aduk inda take matuqar tana a hayyacinta kaine mutum nafarko da zatayi fatan kasancewarsa cikin qoshin lafiya da kwanciyar hankali, don haka kayi haquri kuma karb’i qaddararka hannu biyu ta hanyar qarfafa zuciyarka kaji ko?.” “Eh Inna Bilkisu nagode.” Yafad’a yana goge hawayen da suka jiqa masa fuska, miqewa tayi tafita tana fad’in, “Ina zuwa.?” Binta da kallo yayi aransa yana burin inama ace itace mahaifiyarsa, daya rungumeta yayi kukan sosai yanda zata fahimci yanayin da yakeji koya samu sassauci, yana wannan tinaninne Inna Bilkisu tadawo riqe da kwanon abinci da wani kwanon ruwa da damammiyar fura aciki, saida tad’an riqe fuska tukuna ta ajiye masa kwanon abincin agabansa tace “Maza sauko kaci abinci kaji.” “Bazan iyaba Inna Bilkisu, wlh bana tunanin abinci zai iya shiga bakina bacin bansan halinda Rashida ita da abun cikinta ke cikiba.” “Ungo wannan to kasha, ai haquri zakayi, idan bakaci ba taya zaka samu qarfi ajikinka har ka iya zuwa nemota. kadaure ko rabine kasha kaji ko.” Inna Bilkisu tafad’a had’e da bud’e kwanon ruwan takai abakinsa, awannan karon Babu yanda zaiyi dole yafara tsutsar furar ahankali yana sha tamkar wani jariri, cike da tausayi ta raja’a akallonsa kawai sukaji anbuge kwanon furar yafad’i qasa gaba d’aya tazube, d’ago kai dashi har ita sukayi da sauri don ganin wanda yayi wannan aika aikar, dik da dama gaba d’aya zukatansu sun gama hakaito masu dako wacece, cike da masifa Inna hawwa tafara magana. “Kam buhun uban nan, Bilki me nake shirin gani anan?, So kikeyi shi kuma yaron nawa bayan halin da yake ciki ki hallaka mani shi ta hanyar asirce manishi sai yanda kikayi dashi don mugunta?, To wallahi jinina yafi qarfinki munafukar banza munafukar wofi, hadda wani d’auko abu kina bashi abaki, kai Kuma sakaran banza da bakasan inda duniya tayi ba kasaki baki kana sha.” Yaya hawwa taqarasa fad’a tare da jawo hannunsa zatabar falon dashi tana cika tana batsewa, cike da tausayin mugun halin da ALLAH yayi mata yajarab tawar rayuwa dashi Inna Bilkisu ke kallonta kafin tace. “Dakata Yaya hawwa, kiji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH kitausayawa yaron nan halin da yake ciki, a matsayinmu na iyaye bamu kad’aine ALLAH ke hukunta ‘ya’yanmu akan haqqoqan muba idan suka danne, hatta mu kanmu ubangiji na kamamu da haqqoqansu kuma yayi mana hukunci mai tsauri idan muka taushe masusu, su amana ne agaremu kuma ALLAH zai tambayemu, Nuraddeen d’anane duniya da lahira tunda nake auren qanen mahaifinsa, don haka banga ribar da zan samu ba idan nacutar dashi, dama haka rayuwa take idan kana abu sai kayi tsammanin kowa ma yanayi, kitaka sannu haqqin d’anki kad’ai ya isheki aduniya balle na sauran rayukan da basuji basu gani ba, agidannan Banda darajar mijina da yayansa da kike ci saita haihuwa da kikayi badon haka ba da saina koya maki darasin rayuwa, amma ko yanzu muje zuwa da sannu duniya zata koya maki.” STORY CONTINUES BELOW  Rab’awa tagefensu tayi tawuce bayan ta d’auko kwanon abincin data kawo masa tare da furar da Yaya hawwa ta b’arara, “Kagani ko shashashan banza da wofi, bakasan mai sonka ba, dubi yanda tayi tsaye ta cimun mutunci agabanka amma ka kasa cewa uffan saboda tariga data gama da kai, dallah wuce mutafi samna sakaran banza, biye yake da ita kamar hoto har suka fito sashen tana rafka uwar masifa da zagezage, daidai bakin qofa taci karo da fadeela Inna taturota tagyara inda furar tazube, hannu tasa ta bangajeta gefe da kad’an tafad’e da sauri Nuraddeen yariqe mata hannu. “Gidan ubanwa zakijene” Yaya hawwa tafad’a tana watsa mata wani mugun kallo, “Inna ce tace nazo nagoge inda fura ta zube..” “To ahalin kicifaffi anyo gadon ashibilanci da iyayi maza kiwuce kibar nan kafin in makeki, shegu d’iyan bani na iya..” Da sauri fadeela tabar wajen tun kafin tarufe baki ita kuma tajawo gambun qofar tarufe har lokacin tana riqe da hannunsa kamar wani qaramin yaro, ‘Daki tashiga dashi ta zaunar saman gefen gado ta jawo wani kwano da dambu aciki sannan ta d’ebo ruwa ga kofi ta ajiye agabansa, “Maza kaci kada yunwa ta illataka, yanzu haka duk inda ta tafi tana can hankalinta kwance tabarmu da tashin hankali anan.” ‘Doga kansa yayi yana kallon mahaifiyar tasa had’e da cewa. “Kamarya duk inda tatafi innar mu, taya Rashida zata bar gidannan da tsohon cikinta haihuwa ko yau ko gobe?.” “Eh mana, ai haka na iya yuyuwa idan taji tagaji da zama dakai, to don ta tayar maka da hankali tunda taga kana sonta, ya kamata kiyi tunani anya ba guduwarta tayi ba tunda auren naku na had’ine?.” Murmushin da yafi kuka ciwo yayi kafin yace. “Innar mu kenan! Ai aurena da Rashida ba had’in iyaye bane balle tagudu tabarni, ni naganta da kaina nace Ina sonta kuma itama ba tilastata akayi sai ta aureni ba, ita da kanta taji tana sona kuma ta amsa mani, kinga batun guduwa anan ga masoyan da sukaji sun amince da juna ai bata taso ba, Rashida inada tabbaci akan d’auketa akayi amma su waye? Meyasa? Duka ban sani ba, tsorona d’aya aduniya kada ace mahaifiyata nada sa hannu aciki, Ina addu’a kar ALLAH yasa tsanar da kike yimata bata Kai mizanin da Zaki iya salwantar da rayuwarta ba.” Hannuwanta yariqo had’e da durqushewa agabanta sannan yaci gaba da cewa, “innar mu duk duniya banida maccen da takai matsayinki araina domin ke kika haifeni, kikayi d’awainiya dani tun Ina cikin cikinki har zuwa girmana amma duk da haka farincikina da kwanciyar hankali na suna tattarene a hannun matata Rashida, don ALLAH idan kinada masaniya akan inda take don ALLAH innar mu kisanar dani kafin nakoma marar amfani adoron duniya.” Wani banzan kallo tayi masa kafin a hasale tace. “Tashi fita kabani waje tunda naga kai bakasan abunda kakeyi ba.” Tsom ya tashi ya miqe jikinsa ba k’wari ko kad’an ya koma sashensa, bai jima da shiga ba yafito sanye da wasu kaya yamiqi hanyar fita gidan. “Ina zaka?” Yaji muryar Yaya hawwa tana fad’a cike da gadara, batare daya juyo ba yace. “Zantafi nemo farincikina.” Bai tsaya sauraron abunda zatace ba yaci gaba da tafiya, daidai bakin qofar fita gidan yaci karo muneera tashigo aguje da alama wani tajawo sauran k’iris ta bangajesa tawuce, jikinta na rawa tatsaya tana fad’in. “Don ALLAH ya nura kayi haquri” kota kanta baibi ba yawuce abunsa batare dama yasan da ita awajen ba, biyo bayansa tayi tana fad’in, “ya nura, ya nura.” Ko juyowa beyi ba balle ma yakalleta har tasa ran zai tanka mata, hakan yasa tafashewa da kuka had’e da rugawa cikin gida, da sauri Inna ruqayya tafito tana fad’in. “Ya rasulu manzon ALLAH, muneera keda wa acikin gidannan, fad’amun inji waya tab’aki ne, qara tale baki tayi tana cigaba da rere kukanta wanda nan take yasa hankalin mutanen gida yadawo wajen saboda sanin halin da ake ciki, STORY CONTINUES BELOW  “Ke muneera lafiya? Wata tsohuwa data dudduqo daga wancan b’angaren dake cikin gidan tafad’a tana tokare sandarta akusa da ita, “ke fad’amun waya tab’eki ko d’an gidan uban waye inje dashi har iyayen da suka haifesa inci masu mutunci tas, fad’i Ina jinki keda waye?” Cikin kuka tace, “Inna koba ya nura neba inayi masa magana ya qyaleni ko kallona beyi ba yai tafiyarsa.” Kallon dan dazon mutanen gidan dake wajen Inna ruqayya tayi had’e da had’a wasu yawu masu kabrin gaske saboda sanin halin ‘yar tata, hannunta tariqo tana fad’in. “To zo muje d’aka kiji kinsan yau yana cikin yanayi marar dad’i.” “Wlh Babu inda zanje ai bani na b’atar masa da mata ba balle yadinga qyaleni yana fushi dani kuma Inna ai haka kukeso tunda kunce bakwa son ya aureni tana cikin gidan.” ‘Dago kai gaba d’aya mutanen gidan sukayi had’e da maido kallonsu ga inna ruqayya data fara kalle kallen gefenta, tsohuwar dake kusa garetace tace. “Ke muneera kirufa mana asiri gidannan, wannan sheri da kike neman qaqabawa uwarki har ina?” “Ai wlh basheri bane itama innar tasan gaskiya nafad’a, har magani suka karb’o aka barbad’awa ya nura saboda akarkato zuciyarsa yafara sona muyi aure amma gashinan beyi amfanin komai ba, ni wlh ALLAH bazan yarda ba sai an auramun ya nura.” Taqare maganar tana bubbuga qafafuwa tana kuka. Ana haka saidai mutanen dake wajen suna tafa hannuwa suna sallallami sukaga Yaya hawwa da bawanda ya lura da lokacin data fito tayi tsaye wajen tana kallon sakarci irin na muneera tayo wani irin kukan kura ta damqi wuyan Inna ruqayya tana fad’in “Buhun uba, d’an nawa zaku kai ayiwa asiri don kuna munafukai algungumai, to wallahi ALLAH baku isa ba yau nafison garin bebeji ya tarwatse ya watse akan wannan rashin mutunci da kuka tafka mani matsiyata da bakusan abun arziqi ba.” Taqare maganar tana kaimata naushi a gefen fuska, kokuwa suka shigayi ita da ita cikin sanyin muryar qasaqasa ta yanda baza’a jiba Inna ruqayya ta dinga bata haquri gudun kada suyiwa kawunansu tonon asiri, Amma saboda yanda Yaya hawwa taji zafin abun aranta ko saurarenta batayi taci gaba da tsigarta tana jifarta da miyagun kalamai, cikin b’acin rai da hasala Inna ruqayya tasa hannu biyu biyu ta tureta tana fad’in. “Ke hawwa bari nafad’a maki shuru shurufa ba tsoro bane, sannan shi abun fad’i kowa yana dashi qulle agindinsa saidai idan bai fito bane, karkiga na qyaleki kinemi maidani sakarai agaban mutane Ina d’an naki ba damuwa da rayuwarsa kikayi ba balle har kinuna mani cewa ke uwar sace, naji munkai nura wajen mlamin tsibbu a karkato da zuciyarsa ga muneera, ai nayine don farincikin ‘yata, amma kefa? d’an naki kike zuwa kikai wajen bokaye don farin cikin kanki dana wasu, ko kina tunanin ban san cewa ke kika b’atar da yarinyar nan ba da har zakizo kina yimani cin mutunci agaban mutane, to anyi masa asirin duk abunda kika iya kije kiyi, in shed’anci kike taqama dashi na damaki na shanye Kuma wallahi da sannu zan koya maki hankali, banza ke atunaninki duk wannn walaqancin da kike yimani kinasa ran zan barshine yatafi abanza? Wlh kinsha qarya dama jira nake kigama yaqin ni kuma nakwashe ganimar, kuma tunda kika yimun wannan tozarcin wlh saina tabbatarwa da duniya cewa kece nan kika b’atar da surukarki kika sa ahallaka maki ita don bakya sonta.” Inna ruqayya taqare maganar tana shed’a guda guda had’e da gyara d’aurin d’an kwalinta. “Kan hatta kazak kaza..ni zakiyiwa sharri ruqayya don ‘yarki ta tona maki asiri, to baki Isa ba wlh…” Nan suka shiga tonawa kansu asiri mutanen dake wajen nata la’antarsu da miyagun halayensu. Inna Bilkisu kuwa fashewa tayi da kuka tashige d’aki tana mai tausayawa halin da Rashida keciki, baffa kuwa da tun d’azu suna bakin qofar shigowa tsakar gidan yanata ko kuwar shigowa ciki saboda abunda kunnuwansa suka jiyo masa lokacin da zasu shigo amma baffa Usman yariqesa yace yabari har sai sun gama fad’in komai da zai zamo masu hujja tukuna, kasa haquri yayi ya fizgikke daga riqon da yayi masa jikinsa narawa idanuwnsa na hawaye yashigo yana nuna yaya hawwa da hannu yace…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [7/20, 9:15 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 STORY CONTINUES BELOW  _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___40💎 Kin cuceni hawwa kinci amanar zaman da mukayi dake, haqiqa ba qaramin kuskure natabka ba wajen zab’awa d’ana ke amatsayin uwa, gashi yanzu duk wani farincikin mu dani har shi kin rusa mana shi, naso nacigaba da haqurin zama dake ko don albarkacin d’anmu har lokacin da mutuwa zata rabamu, amma bazan iyaba, ko kad’an bazan iyaci gaba da zama da mushirikar mace da bata tsoron ALLAH ba kamarki, macen da batada imani da tausayi, son kanta yasa ta cilla mutane da yawa cikin wani hali, ALLAH yasani nayi iya qoqarin zaman da zan iya dake amma yanzu kitafi na sakeki, na sakeki hawwa saki biyu, keji duk abunda kika yimun nayafe maki duniya da lahira albarkacin yaronmu, Amma Ina so kisani bazan tab’a d’aga maki k’afa akan sauran haqqoqan bayinsa da kika zalunta ba, wlh ni da kaina zan tsaya na bimusu shi koda duka abunda ALLAH ya mallakamun aduniya zai qare musamman haqqin wannan qanqanuwar yarinyar da kika d’auka, yarinyar da zuciyarta bata san komai ba sai tarin qauna da soyayya agaremu, tayi mana halacci mai d’inbin yawa kama daga soyayyar da take yiwa d’anmu har zuwa kulawar data bani agidannan nasamu lafiya da haqurin cin kashin da kika tayi mata amma kikasa qafa kika shure duk wud’annan abubuwan keda marasa imanin da kuka had’a baki kuka cutar mana da ita, in sha ALLAH, ALLAH bazai barki ba har sai ya hukuntaki tun aduniya kafin kije lahira.” Yana gama maganar yajuya yafice daga gidan ko gani bayayi saboda tsananin b’acin rai, tafiya mai nisa yayi baffa Usman na biye dashi kafin yasamu waje ya zauna, kuka ya shiga rerawa tamkar qaramin yaro cike da nadamar sanin Yaya hawwa da yayi aduniya, gaba d’aya ji yakeyi yatsani duk wani abu daya dangance ta balle ita kanta, Saida yayi kukansa mai isarsa sannan yamiqe suka nufi asibiti, akan hanyarsu suka gamu da baffa Ali sai faman sabbatu yakeyi wai Nuraddeen ya maisheshi d’an iska ya gudu daga asibiti yabarshi, gashi yasa agaban mutane likita yayi mashi wala qanci, har ya d’an gotasu zai wuce baffa Usman yajuyo don da alama duk kansu basuga juna ba sai yanzu. “Ali Ina kanufa kuma haka?, Ko har Nuraddeen d’in yatashi an baku sallama ne.?” “Af Yaya kun dawo? Injin an dace anga yarinyar?, ” “Kai ka amsamun tambayar da nayi maka, yarinya kam idan da rabon agata ko anqi ko anso ai ganinta za’ayi da yardar ALLAH.” Baffa Usman yabashi amsa yana kafesa da idanuwa, “Aw Nuraddeen kake magana?, ai kabarni da shashashan yaro, wai daga infita inyo sallah yaronnan ya gudu daga asibiti, sai dawowa nayi natarar da likaita na tambayarsa yarufeni da fad’a agaban mutane baka ganiba abunnan zak kunya.” Shiru baffa Usman yayi cike da mamaki yana kallonsa kafin yaji muryar baffa yace “Ba komai Aliyu, Nuraddeen ai d’an kane duk abunda kayi masa ko kabari ya samesa kanka kayiwa, shidai zumunci yananan rataye aqasan al’arshi duk wanda ya gyara yaga da kyau wanda kuma ya munana yaga akasin haka, ni dai addu’a ta d’aya shine ubangijin dake tare da waccan yarinyar shima yakare mani shi aduk inda ya tafi, kuma Allah ya qaddara had’uwarsa da ita cikin amincinsa da yardarsa.” Yana gama fad’ar haka yanufi hanyar gidan daya d’aukarwa su Nuraddeen haya yana fad’in. “Usman zo mutafi.” Bayansa baffa Usman yabi shi kuma baffa Ali yawuce gida yana maijin d’acin maganganun da baffa yafad’a masa, “wato duk abunda nayi masa baiga qoqarina ba, amaimakon yaga laifin d’ansa laifina yake gani, ai shikenan gobema ranace” haka baffa Ali yaba hanya yana fad’a cike dajin haushin d’an uwan nasa har ya isa gida Cikin sa’a sukayi nasarar ficewa daga anguwar ba tare da kowa ya gansu ba, daga su sai jikukunansu guda biyu na kaya da kuma ‘yar jikka ta ratayawa irin ta maza dake sagale a kafad’ar baba suka nufi tasha, sunjima zaune abakin wani shago kafin baba yatashi yaje ya d’ibi ruwa a randar dake ajiye bakin qofar masallacin dake cikin tashar yayi arwala, Saida ya d’ibi wasu a buta yaje ya kaiwa umma itama tayi arwalar had’e da ciro sallayar da sukazo da ita cikin kayansu ta shimfid’a sannan yabar wajen da sauri jin antayar da sallar yana fad’in, “Kibi jam’i maman Rashida Ina fitowa zamu shiga motar duk da muka samu tagama lodi.” Ana gama sallar addu’a kad’ai yayi yafito da sauri da sauri tare da tallabar jikukunan nasu dake gabanta yana fad’in. “Hanzarta maman Rashida naji motoci sun fara tashi.” Tofi tayi acikin hannayenta dake sama bayan tagama yimasu addu’ar ALLAH yazab’a masu wajen zuwa mafi alkhairi arayuwarsu had’e da shafawa sannan tamiqe tanad’e sallayar tabi bayansa, suna isa motar Niger na d’agawa wacce ita yaso su samu don d’azu yana arwala yaji drivern motar nafad’in passinger biyu ya rage masa tacika, sai gashi kafin ya d’oko kayan nasu su iso wajen har ansamu ciko, shiru yayi had’e da ajiye jikkunan yana kallon umma da sai yanzu ta ida qarasowa wajen, STORY CONTINUES BELOW  “Ai har motar tacika, kingata can yanzu tawuce” yafad’a cike da damuwa don baya son abunda zaizo ya dakatar dasu daga tafiyar wanda hakanne yasa ma ya kasa sanar da d’an uwan nasa. Murmushi tayi tare da cewa, “ka kwantar da hankalinka, inda tanufa qilan zuwanmu can d’in ba alkhairi bane.” “Hakane kuma.” Yabata amsa tare da nufar rumfunan da motocin kowace jaha ke tsayawa lodi, duk motar daya duba bai wuce yaga mutum biyu ko ukku aciki har yawuce kusan motocin jahar, gombe, sokoto, katsina, adamawa da kuma bauchi babu inda yaga mota takusa cika balle tashi, har yajuya zai bar wajen yaji ana fad’in. “Borno mutum uku, mutum uku borno.” Da sauri ya juyo yanufi inda motar had’e da cewa driver borno zaije. “To kashiga, saura mutum biyu.” Karan motar yafad’a yana sake d’aga murya yana fad’in “mutum biyu borno.” A sauri baba yasake matsawa kusa dashi yace “ai mu biyune nida matata.” Yana rufe baki saiga cikon mutum d’aya an samu, da d’an gudu gudunsa yaje yakira umma tare da d’oko masu jiku_ kunansu, miqa hannu umma tayi takarb’i d’ayar ganin sunyi masa yawa saboda yanayin yanda yake tafiya tunda ba lafiya yacika ba yayi saurin wucewa yana fad’in. “A’a kedai d’aga qafarki muje.” Suna zuwa akasa kayansu bayan mota suka shiga drivern ya tayar da motar suka bar tasha, suna hawa titi had’e da kama hanyar tafiya baba yarufe idanuwansa had’e da sakin wata irin ajiyar zuciya, kallonsa umma tayi itama tana ajiyar zuciyar tare da aza kanta saman kafad’arsa tana karanto addu’ar tafiya yayinda mutum ya hau abun hawa, wacce tafito daga bakin mafificin halitta kuma ya tabbatar mana da cewa duk wanda yayita alokacin daya hau abun hawansa zaiyi wata tafiya to ALLAH zaikaresa da ga sharrin duk wani abunqi dake cikin tafiyar da sharrin qarfe ko kuma had’ari, zai sanya tarin alkhairai masu d’imbin yawa acikin tafiyar tasa da yardar ALLAH. _”ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBARU subhanallazi sahhara lana haza wama kunna lahu muqrinin, wa inna illa rabbina lamunqalibuun, allahummah Inna nas’aluka fi safrina hazal birri wattaqwa, waminal amali ma tarda, allahummah hawwan ala safarana haza wad’wi Anna bu’udahu, allahummah antasswahibu fis safri, walkhalifatu fil ahli, allahummah inni a uzu bika min wa’thaa’issafri, wa kaabatil manzwari, wasuu’il munqalabi fil mali wal ahli.”_ Domin samun fassarar wannan addu’ar zaku iya duba littafin hisnil muslim, addu’a ta tis’in da shida (96) don nemawa kai kariyar ALLAH daga sharrace sharracen miyagun mutanen dake kan hanya da kuma munanan had’urran da sukayi yawa alokutan tafiye tafiyenmu, Tana addu’ar hawaye nazubo mata a fuska, hannu baba yasa yagoge mata had’e da cewa. “Kinsan inda muka nufa yanzu?” Girgiza masa kai kawai ta iyayi tana mai tunanin yanda duniya tajuye masu daga farinciki Mai yawa na bayan shekaru zuwa baqincikin da basusan iya adadin lokacin da zasu d’auka dashi kafin yabarsu, “Jahar borno muka nufa kuma Alhamdulillah akwai wani babban mutum dana sani acan abokin alhajin da nake saro takalma a shagonsane ana cemasa alhaji shu’aibu maiglass, muna yawan had’uwa dashi idan yaje wajensa ni kuma naje kaimasa kud’insa in amso takalmi, yanda alhajin kejin dad’in mu’amalar kasuwanci dani yasa wata rana ya had’ani dashi muka gaisa har yake fad’amun ai aminin sane yana zowa daga borno me shima yayi sayayar kayan glass nayin qofofin zamani, to tun daga lokacin duk yazo in muka had’u sai yayi mani alkhairi don babban mutumne sosai, kinga idan munje sai munemi gidansa kafin musamu inda zamu zauna. “Shikenan duk da dai mutum bashida tabbas amma tunda ba muda wata mafitar ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi kuma yakaimu lafiya.” “Amin, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH babu wata matsala.” STORY CONTINUES BELOW  “ALLAH yasa.” Tafad’a tana share qwalla a idanuwanta. ••• ••• ••• Baffa Ali kam yayi sanyi sosai akan abunda yafaru, yayi dana sani mai yawa akan biyewa harkar mata da yayi wacce ta jefasa cikin halin qaqa nikayi, yayi nadamar shiga al’amurran Yaya hawwa Amma duk da haka yana jin tsanar baffa mai tsanani azuciyarsa bisa abunda yasa akayi masa shida iyalinsa a matsayinsa na d’an uwansa, hakan yasa tunda suka dawo yafita harkar kowa yana rayuwarsa shi kad’ai, baruwansa da kafatanin mutanen gidan acewarsa suma munafukaine tunda aka kasa samun wanda zaiyi belinsa acikinsu, had’uwa dubu kuwa idan zasuyi da baffa bazai d’aga Kai ya kallesa ba balle yasa ran zai gaishesa, dama dama baffa Usman yakan d’an saki jiki dashi sugaisa yawuce shima d’in ba sosai ba, Kuma hakan ko kad’an bai dami baffa ba saima addu’ar neman shiriya daga ALLAH. Muneera kuwa tuni ta manta da babin ya nura rayuwarta takeyi kamar ba itace muneerar dake faman kukan son ya nura dare da rana ba, Amma tasha alwashin bazata tab’a sure ba inba saurayin birni d’an kwalisa ba irin ya nura, shiyasa takeci gaba da yiwa maqwabcinsu da yace yana sonta walaqanci kuma Inna ruqayya tagoyi bayan haka, saidai duk da haka yanzu basuda bakin fitowa tsakar gida suyi tijara kamar yanda suka saba gudun kada a mayar masu da jawabin abunda baffa yasa akayi masu wanda ita kanta tana kallon baffa amatsayin azzalumi wanda yaci amanar d’an uwansa, dama mai hali baya fasa halinsa. ••• ••• ••• Dr. Nura kuwa tunda safe yaso yin tafiyarsa zuwa kano amma yanda yaga Fatima takwana da tana fama da ciwon kai wanda dama lokaci zuwa lokaci yana taso mata yasa yafasa tafiyar, gashi sai kiransa akeyi wajen aikinsa akan wani emergency daya taso na gaggawa, Babu yanda batayi dashi ba akan yatafi kodon issue d’in Rashida amma ya kafe akan matuqar ba sauqi yaga ta samu ba babu inda zaije, hakan yasa tayi qarfin halin tashi taje tayo wanka tare da kiran mai aikinsu tace takawo mata abinci taci, bayan taci ya d’ebo mata magani tasha, a maimakon takoma ta kwanta sai tawuce part d’inta, zaune ta isko Rashida a palour rungume da little Nuraddeen tagama dama mashi madarar (NAN) da ake had’a masa da ita zata bashi. “ALLAH sarki aunty yanzu nake cewa idan nagama bawa yaronki madara zanje naduboki da jiki, injin da sauqi ko?” Rashida tafad’a tana qoqarin d’aurama little Nuraddeen dake qoqarin kamo fidan madarar abun tare abinci idan ya zuba awuyansa, murmushi Fatima tayi had’e da miqa hannu takarb’esa tana yimasa wasa sannan ta zauna takarb’i fidan tana bashi madarar, har kusan qarfe sha d’aya da rabi Nuraddeen yaji tsit har lokacin Fatima bata dawo ba, part d’inta yanufa ya iskota kwance little Nuraddeen nasaman cikinta yana bacci ita kuma da Rashida na zaune suna kallon wani wa’azi a tsahar sunnah tv, a daidai bakin qofa ya tsaya yayi gyaran murya yana kallonta kafin yace. “Iyyeeeee lalle kinsamu sauqi madam, shine kika barni acan Ina jiran tsammanin dawowarki ashe kuna nan keda maman baby kuna kallonku, ikon ALLAH, to wannan wace irin jinyace nakeyi, ga marar lafiya anan ni kuma mai jinyar anbarni acan.” Ahankali ta tashi zaune don kada little Nuraddeen yafarka tana kallonsa had’e dayin murmushi tace. “To ai laifinka ne, nafad’a maka nasamu sauqi amma baka yarda ba ai yanzu ka ganewa idanuwanka ko?” “Eh to! Yanzu kam ai nayarda.” Kallon Rashida da kanta ke qasa a sunkuye yayi had’e da cewa. “Mman baby Ina kwana antashi lafiya, tunda yau tunanin takwarana abban takwara bazai bari agaisheni ba.”yaqare maganarcike da tsokana. “Laa..uncle jirafa nakeyi kugama magana sai nagaisheka, Ina kwana ya jikin aunty.” Rashida tafad’a had’e da d’ago kai tana dariya. “Lafiya klw, auntynki kam aike zan tambaya tunda kinsa ta wartsake.” Murmushi kawai tayi tare da maida kanta qasa ba tare da tace komaiba yace. “Madam tunda naga kin samu sauqi kuma akwai sauran lokaci bari kawai nawuce ko kuwa?” “Gaskiya kam.” Fatima tafad’a tare da tasowa tabi bayansa sab’e da little a kafad’arta, “ALLAH ya kiyaye uncle.” Rashida tafad’a tana kallonsu cike da burgewa, itadai a kullum rayuwar ma’auratan na burgeta don akwai fahimta sosai a tsakaninsu, hakan na yawan sa tanajin sha’awar kamanta irinta da habibynta amma da zaran ta tuna da mahaifiyarsa sai tayi saurin kauda wannan tunanin aranta. Akan gado ta ajiye little ta taimaka masaya shirya tsaf ta sake d’ebo masa breakfast ta tsaresa ya sakeci sannan tace. “To ranka shidad’e ALLAH ya kiyaye kuma yasa Kati tafiyar sa’a, kaje lafiya kuma kadawo lafiya tare da kyakkyawan albishir d’in had’uwa da iyayen maman baby, duk da inajin damuwa idan natuna zan rabu da kyakkyawan qaramin maigidannan nawa” taqare maganar tana kallon little Nuraddeen dake baccinsa hankali kwance, jawota yayi ajikinsa had’e da cewa. “Ki kwantar da hankalinki insha ALLAH muma namu natafe ga ALLAH kinji ko matar?” “Ina fatar ganin wannan ranar akoda yaushe.” Sumbatar goshinta yayi sannan tasake sab’a Little Nuraddeen a kafad’a ta rakasa har bakin gate hannuwansu na sarqe da juna, dama tuni yakira qanensa ya fitar da motar waje yana jiransa, shi zai kaishi tasha ya hau mota sai yadawo mata da motar gida don dama yadena zuwa da ita tun lokacin da little na asibiti saboda tunanin ko wata matsalar zata taso da za’a buqaci motar, Saida taga tashinsu sannan ta d’aga masa hannu had’e da komawa gida, Suna isowa junction d’in da zasu juya su shiga tasha motar su umma na sauka, lokacin qarfe sha biyu saura minti biyar na rana, har zai shiga junction d’in dr.nura yace ya tsaya ya karb’o masa swan water gora biyu awani shago dake wajen, parking qanen nasa yayi agefe tare da rage glass d’in motar, adaidai lokacin su kuma su baba suka fito daga cikin tashar suna qoqarin tsallakowa titi zuwa d’ayan hannun da motar su Dr nura tayi parking…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭[8/12, 10:06 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___51💎 A qoqarin su na tsallakowa zuwa d’aya b’angaren baba na tallabe da jakunkunan su umma tamiqa hannu zata karb’i d’ayar dake sagale a kafad’arsa ganin yanda yake tafiya daqyar saboda yawan da suka yimasa tana fad’in. “Malan kenan! ALLAH kafiye qarfin hali da yawa, miqo wannan jakar ko itace in riqa maka tunda sunyi maka yawa.” Maganar takeyi tare da qoqarin karb’ar jikkar ahannunsa har lokacin suna a tsakiyar titi kai kace cikin gida suke hankali kwance, wata motace tashigo ta junction d’in aguje tana yimasu oda amma saboda hankalin su gaba d’aya baya akan titin ba suma kula da zuwan nata ba balle suji odar da akeyi masu. abunka da mutumen qauye ba ruwansu da tunanin ai nan birnine akwai banbancin dake tsakanin titunansu dana qauye.+ Ganin motar na tunkarosu ka’in da na’in inda yasa dr.nura dake kallonsu tun d’azu ta cikin glass d’in motar yayi saurin fitowa tare da rugawa ya jayikkesu da qarfi, cikin tashin hankali duk suka saki jakunkunan nasu tsakiyar titi gabansu na matsanancin fad’uwa, yana jayesu motar na wucewa aguje kamar iska wacce kad’an ya rage ta buge Nuraddeen garin taimakonsu. Kallo d’aya zakayi masu kafahimci tsantsar tsoron daya ziyarto zukatansu alokaci d’aya, binsu yayi da kallo cike da takaici kafin yakoma yakwaso jakunkunan nasu dake tsakiyar titi. “Haba baba!, shifa titi da kuke gani ba gidajenmu bane da zamuyi yanda muke so akai ba, wajene da ke cike da barazanar d’aukar duk wata rayuwar da tayi kuskuren gittawa akai ba daidai ba sanadiyar ababen hawan dake kai da komo akansa, yanzu da wani abun ya sameku wani hali kuke tunanin zaku jefa halinku aciki, don ALLAH baba kudinga duba tituna dakyau idan zaku tsallaka saboda akwai banbanci tsakaninsu da naku na karkara.” Ya qarasa fad’a ransa a d’an b’ace yana miqa masu jakunkunansu. “Kayi haquri yaro, injin bakaji ciwo ba.” Umma tafad’a tana goge ‘yan guntayen hawayen da suka zubo mata. “A’a baaba, Amma dai adinga kula saboda gujewa qananan had’urra da manyansu.” “Mungode bawan ALLAH daka taimakemu, badon haka ba da mun afkama abunda mukayi qoqarin gujewa, mungode sosai da wannan taimakon da kayi mana, ALLAH ya saka da alkhairi yayi maka albarka.” Baba yafad’a yana kallon Dr nura daya shiga duniyar tunanin muryar umma da yaji, tabbas yatab’a jin mai irin muryar nan tata amma a Ina ne? shine ya kasa tunawa. Daidai lokacin qanensa ya qaraso wajen riqe da gorar ruwan guda biyu a hannunsa daya siyo masa, “Yaya lafiya?.” Ya tambayesa yana kallonsu umma had’e da yatsine fuska, halinshi kenan aduk lokacin da zai had’u da talaka saboda yanda yaqi jininsu, shiyasa basa wani shiri da yayan nasa da matarsa ko kad’an, don tsakaninsu da talaka d’an jimmane da d’an jummai injisa. “Ba komai, muje.” Dr.nura yabashi amsa had’e da wucewa yana kallonsu, bayanshi yabi ummat nayita sa masa albarka suka nufi tasha ya ajiyesa sannan yajuya ya maida motar tare daba Mai gadi makullin motar yaba Fatima sannan yawuce gida. STORY CONTINUES BELOW  ••• ••• ••• Ana gama sallar asuba bayan rana tafito bab balarabe ya gyara tare da fitowa yanufi kitchen inda uwargidansa ke ciki tana had’a abun karyawa. “Subhanallahi, hajia har yanzu baki gama had’a abun karinnan ba?, Kinfa sani babu kowa atare dasu kuma akwai magungunan daya kamata susha da safennan bayan sunci abinci, tun jiya saida nafad’a maki haka amma ace har qarfe takwas na nema tayi baki gama had’awa ba, kinsani badon wannan ba da tuni ni nabar gidannan natafi nadubo ya d’an uwana ya yatashi da jiki.” Yafad’a ransa a d’an b’ace yana qoqarin rufe mab’allan gaban rigarsa, juyowa tayi had’e da gaishesa sannan tace. “Kayi haquri, na samune yarannan sun jiqamun gawayin da zanyi amfani dashi seda nakoma had’a itacen murhu, amma kad’an yarage na kammala sai naba Hassan shida Hussain subiyo bayanka dashi.” “Mtssss..” tsaki yaja had’e da ficewa yabar gidan yana fad’in. “ALLAH ya kyauta.” Ya matuqar shan mamaki lokacin daya isa qofar gidan yaganta kulle da kwad’d’o, maqwabtansu ya aika akayo masa sallama da maigidan ya tambayesa su yace shima baisan inda suka jeba, yafi qarfin Rabin awa abakin qofar gidan yana tambayar mutanen dake anguwar tasu amma wanda duk ya tambaya amsar d’aya ce shine basu sani ba, kan kace me qofar gidan tacika da mutanen anguwar ana ta’ajibin ina su baba suka shiga, shi kuwa baba balarabe banda aikin Kiran wayar baba da umma babu abunda yakeyi, cike da tashin hankali yake kiran lambarsa idan ya jita akashe sai ya kashe yasake kiran ta umma amma duka Babu wacce yayi nasarar samu, waje yanema ya zauna yaci gaba da sake gwada kiran nasu cike dasa ran cewa awannan karon zata shiga, Dafe kansa yayi da duka hannayensa tare da fad’in. “hazbunallahu wani’imal wakel.” Duk mutanen dake wajen sun matuqar tausaya masa ganin yanda hankalinsa ya tashi alokaci d’aya kowanensu nafad’in albarkacin bakinsa akan tafiyar baba batare daya sanar da d’an uwansa ba, duk dako mafi yawancinsu sun san dalilin da yasa suka aikata hakan. Baki suka dinga bashi kafin sufara watsewa d’aya bayan d’aya ya rage daga shi sai su Hassan da hussaini da basu jima da isowa wajen ba d’auke da kwandon abun karin da aka had’o masu da flaks d’in ruwan zafin tea. Sai Kuma maqwabcinsu dake gefe zaune shima yana gwada kiran wayar baba. Auntynsu gaba d’aya Yaya maryam baba balarabe yakira ya sanar da ita abunda ke faruwa nan take ita da mai gidanta suka iso wajen cikin tashin hankali suma, nan ya shaida mata abunda yafaru jiya da iyayen Rashida sukazo wanda yake tsammanin shine dalilin da yasa suka yanke shawarar barin garin saboda baqinciki da quncin da suke ciki. Fashewa tayi da kuka tana fad’in “Amma wannan mata ta cucemu ta rabamu da ‘yarmu da kuma d’an uwanmu, ubangiji ALLAH ka isar mana, ALLAH ka isarwa Rashida da iyayenta.” Kasa cewa komai baba balarabe yayi sai jinjina kai da yakeyi, haka Yaya maryam taci gaba da kukanta tana yiwa Yaya hawwa ALLAH ya isa bisa rusa masu farinciki da tayi, wata irin ajiyar zuciya maigidanta ya sauke kafin yace. “A gaskiya wannan baiwar ALLAH tacutar da mutane da yawa kuma in Sha ALLAH haqqoqansu bazasu barta ba, yanzu Kai balarabe duk ka tambaya nan maqotansa basuda wani labari akan inda sukaje ko wani saqo da suka bari kafin sutafi.?” “Na tambayesu Yaya sunce basu san komai ba akan tafiyar tasu, ni ina tunanin tun cikin dare sukabar garinnan.” baba balarabe yafad’a yana murza goshinsa saboda ciwon kan da yaji yana nema yarufesa, Kallon Yaya maryam yayi dake shartar majina tana dannar wayarta da alama itama gwada kiransu takeyi yace. “Yaya maryam kidena wahalda kanki bazaki samesu ba, nakira yafi a qirga amma ban samesu ba.” To yakamata asa ab’alle gidan ko za’a samu wani saqo da suka bari don natabbata bazasu tafi haka ba har sai sunbar wani saqon,” maigidan Yaya maryam ne yafad’i haka tare da zuba hannayensa a aljihu. STORY CONTINUES BELOW  Maqwabcin su sake gefe zaune baba balarabe yayiwa magana da ataimaka masu da wani abun da zasu iya b’alle kwad’on dashi, cikin gidansa yashiga yake ya d’auko zarton ya kawo masu, kallon babban d’ansa da zai wuce da alama gona yayi had’e da cewa. “Qasimu zoka taimaka kayanke masu kwad’onnan.” Baba balarabe yafara shiga bayan anyanke kwad’on sannan Yaya maryam Mai gidanta na biye dasu abaya, tsafa suka isko gidan babu alamar an hargitsa komai aciki kafin sutafi, Yaya Maryam tashiga dudduba ko ina cikin d’akin ta hargitsesa amma basuga komai ba, sallamar aunty marwiyya data shigo tana reren kuka tasata fitowa tsakar gidan dasu baba balarabe ke tsaitsaye, kuka takeyi had’e da lailayo miyagun addu’o’i kala kala tana yiwa Yaya hawwa, rarrashinta suka shigayi da bata magana kafin su yanke shawarar fara nemansu a tashoshin motar dake cikin qauyen nasu da zagaye. Wani yarone yayi sallama had’e da cewa. “Wai mai mashin yace yana jiran matar da yakawo takawo mashi kud’insa” sai alokacin aunty marwiyya ta tuna da aibata sallami mai mashin d’in ba, kawai yana ajiyeta ta tahowarta, nera d’ari baba balarabe yaciro ya miqawa yaron tace a’a yabari taje dakanata, a tsakiyar zauren gidan jikkarta takucce tafad’i wajen saurin taje ta sallamesa tare da bashi haquri, tana duqowa ta d’auki jikkar idanunta sukayi tozali da takardar da baba yarubuta duk an tattaketa. _KUYI HAQURI ZAN NEMEKU ADUK LOKACIN DA NAGA DACEWAR HAKAN, DAGA ‘DAN UWANKU BASHAR”_ Shine abunda ta gani a qasan takardar da har tayi nufin wucewa tabarta, da sauri ta d’auka tana kakkab’e qasar dake jiki ta koma cikin gidan bayan taba yaron kud’in yakai masa tace yabashi haquri, “Balarabe, balarabe.” Tadinga kiransa tun kafin takai cikin tsakar gidan tana gyara mayafinta da jikkarta dake nema su sub’uce mata. Kad’an yarage suyikaro dashi a daidai bakin qofar shigowa tsakar gidan da sauri yaja baya yana fad’in. “lafiya marwiyya ko sun dawo ne?” Takardar ta miqa masa hannunta narawa ya karb’a yana binta da kallon mamaki kafin ya maida kallon nasa ga takardar, saida ya karanceta tsaf sannan ya d’ago kansa yana kallon aunty marwiyya, “Waya baki?” Ya tambayeta don ya tabbatar da rubutun dake ciki nad’an uwan nasa ne. “A tsakiyar zauren nasameta ajiye a qoqarin d’auko jikkana data fad’i wajen saurin in sallami mai mashin.” Juyawa yayi yana kallon Yaya maryam dake tsaye ita da maigidanta suna jiran jin ba’asi tare da takawa ya isa wajensu, cikin raunin muryar dake tabbatar da irin sanyin da jikinsa yayi yace dasu. “Wannan itace abinda mukayi tsammanin Yaya bashar zai barmuna muketa nema kuma Alhamdulillah gata mun samu.” Da sauri Yaya hawwa takarb’i takardar don gaba d’ayansu sunyi boko saidai baiyi wani zurfi ba daga bakin sakandirene suke ajiyesa, wannan dalilinne yasa abaya baba ya kafe akan sai Rashida tayi karatu sosai saboda alwashin daya d’auka akan cewa zurfin karatun da bai samu yayi ba zaisa ‘ya’yansa suyisa kosu nawane. Karanta takardar Yaya maryam tafarayi da qarfi kamar haka. _Assalamu alaikum ‘yan uwana, fatan alkhairi mai yawa da kasancewa cikin amincin Allah arayuwarku har zuwa lokacin da ubangiji zai sake had’a fuskokinmu daku, haqiqa samun ‘yan uwa kamarku abune daya isa mutum yayi alfahari dashi har iya qarshen rayuwarsa, Ina Mai godiya agareku bisa kulawa da d’awainiyar da kukayi nida iyalina, mungode ALLAH yabaku aljannah da rahamarsa, nasan alokacin da kike karanta wannan takardar kuna cikin halin tashin hankali da damuwa saboda rashin sanin inda muke, Ina roqonku daku kwantar da hankalinku, muntafine bisa Imanin cewa hakan da mukayi shine mafi alkhairi agaremu, shine hukuncin da zai sama mana sauqi da rad’ad’in abunda mukeji aranmu, don haka muna roqon addu’arku akoda yaushe, nagode ‘yan uwana Ina alfahari daku, musamman balarabe daya zamemani ginshiqi arayuwa,_ _KUYI HAQURI ZAN NEMEKU ADUK LOKACIN DA NAGA DACEWAR HAKAN, DAGA ‘DAN UWANKU BASHAR_ STORY CONTINUES BELOW  Kusan atare sukayi ajiyar zuciya gaba d’ayansu kafin Yaya tace. “Assha bashar, meyasa zakayi haka?, Meyasa zaka jefa kanka da iyalinka uwa duniya don gushewar farincikinka? duka wannan damuwar tasu akan Rashida ce, to gashi sun gudu sunbar garin, idan ALLAH yakuma nufi farincikin nasu dawowa agaresu shikenan sun sake nisanta kansu dashi?.” “Lalle kam Yaya sun ragon azanci duk da dai bamusan ya suke jiba, amma muyi masu addu’a kamar yanda ya buqata, ALLAH yasa rabon had’uwarsu da ‘yarsu ne ya fishshesu.” Baba balarabe yafad’a yana sake sakin ajiyar zuciya akaro na ba adadi. Sosai ganin takardar yad’an sa sun samu natsuwa, sun jima agidan suna jajanta abun kafin sufito baba balarabe yabayar asawo masa wani kwad’on ya kulle gidan dashi, bayan ya kulle ya miqama yaya maryam makullan tace yabarsu hannunsa kafin suyi tunani akan abunda ya dace suyi tunda baza abar gidan haka ba. Sai da mijinta ya goyata ga mashin d’insa suka wuce sannan yaraka aunty marwiyya bakin titi itama tahau mashin, suna wucewa shima shima yawuce yana maijin duniyar tayi masa wani iri daban. ••• ••• ••• Duk wani bayani daya kamata boka yayima su inspector najida yayi masu shi ba tare daya basu wata wahala ba, anan ya tabbatar masu da cewa shima baisan inda baqin aljanin daya turawa Rashida ya kaitaba, ataqaice ma shi aljanin baiyi nasarar shiga jikinta ba kuma ma yanzu baya tare dashi saboda anqoqqonasa ya bijire masa, shi kansa yanzu tsoronsa yakeji saboda yanda yake cutar dashi tare da azabtar dashi, koda inspector najida takira baffa yazo Police station d’in tayi masa bayani, ya matuqar jin dad’in cewa aikin shed’anunbaiyi tasiri akan Rashida ba, dama shi yanada matuqar yaqini akan hakan saboda riqon ibadarta, abunda kawai baiji dad’in jiba shine rashin sanin inda suka kaita lokacin da sukaci nasarar d’auketa, addu’a yayi had’e da roqon ALLAH ya gaggauta bayyanata. Nan yasaka hannu akan ayi releasing case d’in akayi komai aka gama, har ya juya zai tafi inspector najida tace. “Baba ya batun Inna hawwa.?” “Ku saketa kawai.” Yabata amsa atak’aice tare da juyawa yabar station d’in. Har ya tare abun hawa zai hau sai kuma ya juyo ya dawo wajen inspector najida, koda ya shigo office d’in kanta na duqe tana ida cike sauran information d’in daya kamata kafin ya ajiye file d’in inda ya kamata. A hankali ta d’ago kai ta kalli baffa tace. “Baba ya akayi?” “Akan maganar hawwa ne, Ina so ku ajiyeta kafin nasamo asibitin da za’a kula da ita, koba komai ta haifamun d’a wanda nake alfaharin samunsa aduniya.” Rufe file d’in dake gabanta tayi ta ajiye biron data gama rubutu sannan ta d’ora hab’ar bakinta akan hannuwanta data had’e waje d’aya tana kallonsa, murmushi tayi sannan tace. “Baba kanada zuciya mai kyau, haqiqa da maza zasu kasance masu duba alkhairin matansu komai qanqantarsa arayuwa koda sun rabu dasu, to ina da tabbaci akan mata bazasu wahala aduniya ba sosai, haqiqa kayi qoqari ubangiji ALLAH yasaka maka da alkhairi.” Murmushi baffa yayi had’e da cewa. “Amin ‘yata nagode ALLAH yayi maki albarka ya d’aukaki acikin al-amurranki,” “Amin” ta amsa masa had’e dajin dad’in addu’arsa…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/16, 11:24 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 STORY CONTINUES BELOW  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___52💎 Baffa nashiga gida ya tadda Nuraddeen yafito daga wanka yana shiryawa, cike da girmamawa ya tarbesa tare da karb’ar ledar daya shigo da ita ga hannu yana fad’in. “Sannu da zuwa baffa.” “Yawwa Nuraddeen, barka da rana wanka akayi?.” “Eh baffa, Ina son inje dubo innar mu ne.” Batare daya tanka saba yawuce bakin katifar dake cikin d’akin ya zauna. “Nuraddeen zubikke abinda ke cikin ledar nan awani kwano kazo muci yunwa nakeji” Acan gefen d’an madaidaicin durom d’in dake cikin d’akin Nuraddeen ya d’auko wani kwano cikin kwandon da suke kife kwanonin abincin da suke amfani dasu yazo ya d’auki ledar ya zube soyayyar doya da k’wai d’in dake cikin ledar daya zo da ita yana fad’in. “Ya akayi haka baffa?, Ga abinci nan Inna Bilkisu ta aiko yusuf ya kawo tund’azu.” “Ai nasani Nuraddeen, wannan ina fitowa daga police station ne nagata ana siyarwa saita burgeni nace bari nasiyo mana.” “To baffanmu, ALLAH yasaka maka da alkhairi.” Nuraddeen ya qarasa maganar had’e da ajiye kwanon agabansa, saida yafidda ledar ya saka cikin shara tukuna sannan ya dawo ya d’ebo masa ruwa cikin durom d’in yazo ya ajiye agabansa, har zai juya baffa yace. “Zo zauna muci mana, ko kaci wancan d’in ne.” Azahiri baiya jin cin abincin amma ganin yanda mahaifin nasa ya tsaresa da idanuwa yasa yaje ya wanko hannuwansa yasa hannunsa suka soma ci, tunda suka fara babu wanda ya koma cewa uffan har suka kusa gamawa, cire hannu baffa yayi ya d’auki ruwan yasha ya yiwa ALLAH godiya sannan yace. “Nuraddeen ya zancen tafiyarka? Naga lokaci sai sake gabatowa yakeyi” Da qyar Nuraddeen ya iya had’iye abincin dake cikin bakinsa kafin ya d’ago kai yana tankwashe qafafuwansa yace. “Baffa maganar tafiyar nanfa ni na haqura da ita gaskiya, bana tunanin zan iya sa qafa inbar qasarnan mahaifiyata na cikin wannan yanayin, bacin haka ma baffa nifa har yanzu bancire tsammanin cewa Rashida zata dawo ba, jikina yana bani cewa duk inda take Ina ranta kuma tana cikin damuwa kamar yanda nake cikinta, bana son lokacin da zata dawo ta isko bana qasar, hakan zai sakata cikin shakku da kokwanto cewa nadamu da b’acewarta, shiyasa kawai nake tunanin gwara inzauna in bawa mahaifiyata kulawa har zuwa lokacin da ALLAH zai dawo da Rashida agareni. “Nafahimceka Nuraddeen, Kuma nayarda da zancenka, Amma karka manta dama tana zuwa ga bawane sau d’aya arayuwa, sai kuma sa’a idan tasa ALLAH yasake baka wata damar, batun mahaifiyarka kabarshi a hannuna zankula maka da ita har lokacin da zaka dawo, zanyi hakanne don ALLAH da kuma zamowarta uwa agareka amatsayinka na d’a tilo da nake so fiye da komai arayuwata.” “Ita kuma matarka Ina so kayarda dani, na d’aukarma alqawarin zanci gaba dasa anayi maka sauka da addu’a har zuwa lokacin da ALLAH zai bayyana mana ita, zanyi qoqarin fahimtar da ita komai alokacin da tadawo izuwa gareka kuma na sadaka da ita akaro na biyu, na tabbata zata fahimceni tunda yarinyar nada ilimi da kuma fahimta. Shiru yayi cike da son mahaifin nasa ya fahimci abunda yake nufi, baya son abunda zaisa Rashidarsa taji wani shakku azuciyarta akan soyayyar da yake yimata tahanyar barin qasar alokacin da bata tare dashi, nisawa yayi kafin yace “Baffa..” Da sauri baffa ya dakatar dashi tahanyar d’aga masa hannu yana fad’in. “Shikenan! Na fahimceka ALLAH yasa hakan shiyafi alkhairi, Yana gama fad’ar haka yamiqe zuciyarsa a cunkushe duk da yayi qoqarin hana hakan ya bayyana a fuskarsa amma saida nuraddin ya fahimci hakan. STORY CONTINUES BELOW  Toilet baffa ya wuce shi kuma yamiqe ya d’auke kwanon sannan ya Ida gyarawa, yana tsaye baffa yafito ya watso ruwa tare da canza wasu kayan yace dashi. “To ni zan fita, zanje wajen baffanka akwai mganar da nake son tattaunawa akan mahaifiyarka dashi.” Bai jira jin amsar da zai basa ba yafice don baya son ya fahimci rashin jin dad’insa akan hukuncin da yake qoqarin yankewa kansa wanda yazab’awa rayuwarsa. Zaune Nuraddeen yayi akan katifa yadafe kansa da hannayensa duka yana furta, “Rabbi yassir wala ta’assir.” Yajima ahaka yana tunanin yanda rayuwa tayi masa d’aurin goro tahanyar rasa farincikinsa Rashida da kuma gudan jininsa dake jikinta, a b’angare d’aya kuma tsananin damuwar da yake ciki ta halin da mahaifiyarsa ke ciki dake neman tsaida dukanin al’amurransa, yanzu kuma ga fushin mahaifinsa na nema ya bayyana agaresa ta dalilin hukuncin da yaga yafi dacewa agaresa, miqewa yayi yabar gidan shima bayan yasa kwad’o ya rufesa sannan yanufi police station d’in, Bai wani sha wahala ba inspector najida tasa aka kaishi inda take don ancanza mata waje saboda yanzu Bata qarqashin kulawar hukumar, tamkar ajiya take a hannunsu shiyasa aka kaita can cikin wani d’aki abayan station d’in daya tab’a gobara ya qone, tun daga kan tagogin wajen da qofofi duk sun qone, haka ma samansa abud’e yake saboda qonewar da rufin yayi, asalima nan jami’an ‘yan sandan ke zagayawa domin biyan buqatocinsu na yau da kullum wato fitsari da bayan gida, duk wata rana da iska ko ruwan sama da akeyi akanta suke qarewa gashi an d’add’aureta gudun kada ta tsere, suna nufo wajen Nuraddeen yafara yatsine fuska yana toshe hanci saboda tsananin warin da yakeyi yana bin d’an sandar da kallo Mai cike da tarin tambayoyi har suka isa inda take, da sauri ya saki hancinsa yana zaro idanuwa waje hangota da yayi kwance cikin wajen dake kama da juji hannuwanta da afafuwanta d’aure da gudu ya isa wajenta tare da tallabota izuwa jikinsa batare daya damu da yanayin da take ciki ba yana fad’in. “Innar mu, innar mu.” A hankali ta d’ago kanta tana kallonsa kafin ta saki wata irin muguwar qarar da tasa baisan lokacin daya saketa ba ya koma gefe, wani qaqari tashigayi kafin yaga anfara juyata cikin qonanniyar dattin dake cikin wajen ana birgima da ita tamkar wata halittar da batada qaffuwa, qananun gilasaiyen dake wajen ne suka shiga yayyanke mata jiki tana cigaba da wata qara mai cike da nuna tsantsar azabar da take ciki, ganin haka yasa yasake zuwa ya tallbota yariqeta yana kuka yana fad’in. “Kidena innar mu, don ALLAH kidena innar mu kada kijima kanki.” Rungumeta yayi tsam don kada ta kucce masa yana aza kansa bisa jikinta, ganin haka yasa tasa baki ta kaimasa cizo ahannu har saida taciro da naman jikinsa amma yaqi sakinta saima sake rungumeta da yayi sosai yana kuka yana fad’in “kibari innar mu.” Yanayin qugi da gumzar da qarar da takeyi yasa inspector najida da sauran ‘yan sandan zagayowa sukayi tsaye suna kallon ikon ALLAH, lallae duk lalacewar uwa uwace kuma baza’a tab’a iya shiga tsakaninta da d’an taba. Wani yunquri tayi da yasa d’aurin dake hannuwanta faccewa da qarfi ta turesa gefe har saida yabugi jikin bangon wajen ya dawo, ‘yan sandan naganin haka suka shigo wajen had’e da qoqarin rirriqeta, ganin tana neman tafi qarfinsu yasa wani d’aya daga cikin ‘yan sandan qaqqarfa ya d’auketa kyakkyawan marin da yasa saida ta kife qasa, wani irin kukan kura Nuraddeen yayo kansa had’e da cakumar wuyansa ya kaisa jikin bango ya shaqesa yana fad’in. “Kai waye da har zaka dakarmun mahaifiya agabana?, Kasan me ake kira da uwa kuwa?, Kasan muhimmancinta ga ‘ya’yansa da zaka dokarmun abita?.” Maganar takeyi idanuwansa sun kad’a sunyi jawur ga wasu irin jijiyoyi sun taso masa a goshi yana turo idanuwa awaje.” Jin yafara kakari yasa wasu ‘yan sandan dawowa wajen suna qoqarin janyesa amma gaba d’aya su ukun ya turesu yafara kaimasa naushi a fuska da ko ina ajiki, dukansa yakeyi yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Wayace ka daki mhaifiyata?, waye yace ku d’auremun ita haka?, Akan me zaku kawota anan ita ba dabba ba?” Duk d’an sandan daya nufosa sai yakai masa duka hakan ya b’atawa inspector najida rai nan take tbasu damar suyi masa duka, ai kamar jira sukeyi suka rufar masa da duka Saida suka yi masa liqis sannan suka qyalesa tace a d’aukesa ajefasa cell. Ranta a b’ace takira baffa lokacin yana wajen baffa Usman suna tattaunawa akan asibitin daya dace akai Yaya hawwar ta sanar masa da abunda Nuraddeen yayi nayiwa ‘yan sandansu duka a police station d’in. Jikinsu narawa shi da baffa Usman suka nufo wajen kowane da abunda yake saqawa aransa. ••• ••• ••• Kwanan Dr.nura biyu yana rage aikace aikacen daya isko sun tarar masa a asibitin tasu sannan ya nufi anguwarsu umma agarin yarimawa, awannan karon bisa mashin yake tunda baizo da motarsa ba shiyasa batare daya sha wata wahala ba yasamu wani mutum ya tambayesa zancen iyayen Rashida da har lokacin yaga gidan a kulle da kwad’o. Nan mutumen ya sanar dashi komai har yana d’ora masa da “yanzu haka ina tabbatar maka cewa babu Wanda yasan inda iyayenta suka nufa balle asan halin da suke ciki.” Wani irin jiri ya d’ibesa da yasashi saurin dafe bushiyar iccen dake kusa dashi yana fad’in. “Hazbunallahu wani’imal wakeel, wannan wane irin mummunan labari ne kunnuwana suka jiyomun.” “Abun gaskiya ba dad’i sai haquri.” Mutumen yafad’a had’e da wucewarsa, koda ya d’ago kai daga jimamin da take ciki da niyar yimasa wata tambayar sai yaga har yabar wajen, bai bar anguwar ba har saida yasake tambayar mutum uku don ya tabbatar da abunda nafarkon yafad’a suna bashi amsa iri d’aya da tasa sannan yabar anguwar jikinsa a sanyaye, kwana biyu yaqara kafin yakoma borno cike da tunanin irin amsar da zai baiwa Rashida idan ta tambayesa iyayenta, daga qarshe dai ya yanke hukuncin zai bari har zuwa wani satin idan sunje taganema idanuwanta ammashi tabbas bazai iya fad’a mata ba. Sosai yayi qoqarin sakin jikinsa lokacin daya koma amma saida Fatima tafahimci akwai abunda ke damunsa, yanda ta tsaresa da tambaya yasa ya sheda mata komai ba tare daya b’oye mata ba tare da shawarar daya yanke, nan take tagoya masa baya tan kukan tausayin Rashida akan halin da zata shiga idan sukaje ta tarar iyayen nata basa nan. rungumeta yayi yana lallashinta don yasan halinta sai takai gobe tan kuka har yakai ga Rashida tafahimci abunda ke faruwa. A b’angaren little Nuraddeen kuwa yayi wayau sosai don har ya iya zama, sak kamarsa da Rashida ke dad’a fita da kagani babu tambaya kasan yaron tane. Wani irin so takeyi masa marar misaltuwa da yasa Bata qaunar abunda zai sashi kuka ko kad’an, duk Wanda ya kallesa sau d’aya sai yaqara saboda yanayin jikinsa da kuma tsabtarsa shiyasa duk wanda ya gansa sai yayi sha’awar d’aukarsa, a daddafe suka hau yima Rashida Shirin komawa gida ita da little sai murna takeyi, katsar watsar tasamu satin ya qare wani yashigo yakama gobe zasuyi tafiyar don harda Fatima za’a. Basu suka gyara ba sai kusan qarfe d’aya na rana saboda wasu ‘yan abubuwa da Nuraddeen ya tsayayi, shidai Nuraddeen sai binta yakeyi da kallo yana jimamin abunda zata riska idan sunje, Saida yayi mata nasiha sosai akan rayuwa da kuma muhimmancin yadda da qaddara mai kyau ko marar kyau, sannan ya tabbatar mata da cewa sauran maganin little Nuraddeen na cikon wata d’aya daya rage in Sha ALLAH zai karb’a sai ya kaimata idan lokacin yayi tana tayi masa godiya harda ‘yar qwallarta, haka ma Fatima tayi mata godiya sosai suka rungume juna kafin suwuce su d’auki hanyar zuwa kano tana murna tana qarawa. ••• ••• ••• A b’angaren su umma kuwa Saida suka kwashe kwana uku suna yawo acikin borno kafin baba yagano Wanda yake nema, haka suke buge yini suna yawon tambayarsa in kuma dare yayi sai suje asibiti su shige cikin majinyata su kwanta da safe kuma su sake fita nemansa har ALLAH yasa suka ganesa, hannu biyu mutumen ya karb’esu bayan baba yayi masa bayanin dalilinsu na zuwa garin saida, sosi ya jajanta masa tare da yimasa addu’ar ALLAH ya bayyana masa inda ‘yarsa take, nan yabasu wajen da zasu zauna acikin gidansa acan baya inda d’akunan masu aikin gidan suke sannan yace suyi haquri zai sama masu abunyi nan da kwana biyu, bayan kwana biyu ya tambayi baba in zai iya zaman tsaron wani sabon shagonsa daya bud’e zai dinga biyansa albashi duk wata dubu goma idan ya amince bisa amana da Kuma yardar daya yimasa, nan take ya amince har yana duqawa had’e da yimasa godiya, ita kuma umma d’aya daga cikin matan alhajin taroqa ta dinga yimata aiki duk wata zata biyata dubu hud’u, daga alhajin har baba basuso hakan ba amma nan take umma ta amince da zatayi aikin, acewarta hakan zai d’an d’auke mata hankali da ace tayi zaune ita kad’ai bata komai sai aikin tunanin b’atan ‘yarta. Babu yanda suka iya tunda ta amsa zatayi, ajiyar zuciya alhajin yayi kafin ya kalli matar tasa bayan sun wuce yace. STORY CONTINUES BELOW  “Hajia nafeesa don ALLAH kada kiyiwa baiwar ALLAHn nan abunda kika saba yiwa sauran masu aikinki, mutanene masu kirki da daraja agarena don haka kada kiwatsamun qasa tahanyar tozartar dasu don suna aiki aqarqashinki, zamane zamuyi dasu nad’an wani lokaci kafin su koma inda suka fito, saboda haka Ina roqonki daki mutuntasu don girman ALLAH kinji ko.” Saida ta yatsina fuska sannan ta mere baki had’e da kallon gefe tace. “Naji..” Hajiya nafeesa itace matarsa ta biyu, matada kirki ko kad’an ga son walaqanta mutane matuqar suka amsa sunan talauci atttare dasu kuma suka zamo qarqashinta, shiyasa yaja mata kunne tun kafin aje ko Ina saboda shi mutumne mai dattako, yau itace rana ta uku da umma tafara aiki a sashenta, Babu ruwanta da shiga sha’aninta iya karta tayi abunda tasata ta koma sashenta, kamar kullum yau umma tagama gyaggyara kitchen bayan aikin da tayi saiga baqi hajia nafeesa tayi, sai da aka kwashi mintuna uku sannan ta d’ibi ruwa da lemuna ta kaimasu a falo tare da russunawa ta gaishesu sannan ta koma kitchen, sake kirawota tayi had’e da cewa. “Umma jeki ki kawo masu fruit” Saida taje kitchen tabud’e fridge d’in taga babu komai sun qare sannan tadawo taduqa tare da cewa. “Hajia ba’a samu kawo wasu ba, Kuma naciki sun qare.” Batare da hajia nafeesa ta damuba taje d’aki tad’auko dubu uku tadawo falon tare da jefowa umma kud’in tace. “Jeki kicewa driver nace ya kaikai inda aka siyo mana kisawomun, kiyi sauri Ina jira yanzu yanzu kinji ko.” “To hajia.” umma tafad’a tare da d’aukar kud’in tabar falon. Tafe suke ita da drivern har suka kai daidai wajen da zata siyo fruit d’in yayi parking acan gefen titin yana nuna mata tsallake inda suke yace “Umma ki tsallaka acan kice daga gidan alhaji aka turoki, zasu had’a maku duk abunda suka san ana buqata.” “To” Umma ta and masa tare da bud’e marfin motar tafito tana waige waigen gefe gefe don tasamu ta tsallaka. A daidai lokacin motarsu Dr nura tazo wucewa yana sauri ganin har qarfe d’aya na rana yayi saboda bayason suyi dare ahanya gashi ko cikin garin basu fita ba…… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/18, 1:25 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___53💎 Umma na tsallakowa a dai dai tsakiyar titin Dr. Nura na kawowa da sauri ya sakar mata oda yana qoqarin juya starring nasa wanda kad’an ya rage ya bugeta, daga Fatima har Rashida runtse idanuwa sukayi had’e da dafe kai suna fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun.” Ita kuma umma tsabar tsoro duqewa wajen tayi jikinta na rawa, gefe yayi parking had’e da fitowa ganin takasa motsawa daga duqen da take a tsakiyar titin ya nufi wajenta. Kafin ya isa har drivern da sukazo tare yazo ya jayeta ya nufi wajen motar yana masifa da ita, “Umma kar kizo ki jazamun bala’i, duka duka yau kwanana uku da d’auka aiki agidannan kizo kisa akoreni, fisabillahi idan kinsan bazaki iya tsallakawa ba ai saiki fad’amun, gashi yanzu da kinja mani fitina.” Maganar yakeyi kamar zai doketa saboda tsananin takaici, ganin babu abunda yasamu matar yasa Dr nura juyawa yakoma wajen motarsa yana girgiza kai had’e da fad’in ALLAH ya sawaqe, kallon Fatima yayi dake faman jijjiga little Nuraddeen dake kuka saboda tsoron qararsu da yaji ta tadashi daga baccin da yakeyi yace STORY CONTINUES BELOW  “Bari na tsallaka nabawa matar can haquri duk da dai naga bataji ciwo ba.” “Haba saurifa mukeyi, tunda ALLAH ya kare kuma ba laifinka bane kawai mutafi ALLAH ya tsare gaba.” “Amin ya amsa yana qoqarin bud’e marfin motar ya shiga sai yaga drivern ya iso wajen masu fruit d’in, fasa shiga yayi ya nufi wajensa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya amsa gaisuwar da masu fruit d’in keyi masa dake nuna sun sanshi, “Amm..don ALLAH kabawa matar can da muka kusan samun tsotsayi da ita haquri, sauri nakeyi amma tunda ALLAH ya tsare naga dacewar nayi maka magana tunda tare kuke kabata haquri.” “Babu komai ranka ya dad’e, ALLAH ya tsare gaba kuma ya kaiku lafiya.” “Amin.” Yafad’a tare da miqa masa hannu suka sake gaisawa sanna ya juya yashiga motar ya tayar suka kama hanya shi kuma drivern ya amshi fruits d’in ya tsallaka inda ya ajiye motar tasu, ta glass Dr nura ke kallonsa lokacin daya biyo bayansa don yayi utorn yace da Fatima. “Matar wai kinsan wani abun, ashema motar gidace, sai yanzu na hango lambar dady dake jiki, kingasu nan sun biyo bayan mu.” “Allah sarki, to ko waye waccan matar?, Inaga dai sabon drive ne dady ya samu, Amma shima bayada mutunci, don me sunzo a mota bazai iya tsallakawa yayi parking acan ba sai dai ya tsaya acan tsallake kuma ya turo matar mutane a wannan babban titi hakan shi bazai iya fitowa ba sai ita.” “Iskanci samarin yanzune, Amma zanyi magana da dad a dinga tsawatar dasu akan tsofaffin mutane, inaga d’aya daga cikin masu aikine hajiya nafeesa ta turo kinsan halinta.” “Zata iya yuyuwa gaskiya, ALLAH ya kyauta.” A daidai lokacin da suka tsaya a bakin junction suna jiran traffic tabasu hannu drivern yazo saiti dasu Dr nura ya juyo ya kallesa yana fad’in. “Kin gashi ko?” Fatima tajuya ta kalli drivern daya qore sautin kid’an motar yana kad’a kai, dai dai lokacin itama rashida ta d’ago kai ta gefenta tana kallon motar da taji suna fira akai, motace mai kyan gaske don zata iya cewa takusa kyn ta Dr.nura ko kuma suzo d’ai, matar dake ciki tajuyar da kanta can gefe take kallo da jikinta yabata kmar ta santa kota tab’a ganinta awani wajen amma rashin juyo fuskarta da tayi yasa takasa tantance haka, tan wannan tunanin ne little Nuraddeen ya tsanyara kukan da ya maido hankalinta agaresa tare da qoqarin turasa cikin mayafinta don tabashi nono, a lokacin ita kuma umma tajuyo fuskarta ta b’angaren tana qarewa yanayin kyawon garin da yanda motocin suka tsaitsaya suna jiran abasu hannu suwuce amma kasancewar glass d’in motar tasu Dr nura tinted ne yasa takasa hango ‘yar tata dake ciki tana kicaniyar bawa little Nuraddeen har traffic d’in tabasu hannu, jin motarsu tafara tafiya yasa Rashida d’agowa tare da maida kallonta wajen amma sai taga wayam tuni har motar tajuya ta d’ayan hannun takoma baya sukuma suka miqe hanyarsu tabarin cikin garin. ••• ••• ••• Baffa ya matuqar tsorata da abunda yaji inspector najida tace Nuraddeen ya aikata, sukayita bata haquri shida baffa, daqyar suka samu tabasu belinsa saboda yanda ranta ya matuqar b’aci kafin tace. “Baba kaja masa kunne don idan ya sake maimaita hakan zamu kaishi a hukuntashi ne saboda babban laifine civilian yasa hannu ya bugi kowane irin kaki, don haka kajamasa kunne, kawai na qyalesa ne albarkacinka daya sai mun ganar dashi kuskurensa” “To ‘yata nagode nagode sosai.” Kallon Nuraddeen da duk yafita hayyacinsa yayi had’e da cewa “tashi muje.” “Babu inda zanje baffa matuqar innarmu na wannan wajen.” Nuraddeen yabashi amsa had’e da d’agowa yana kallonsa da ijiyarsa da aka bubbuge ta kumbure. Cike da mamaki suka bishi da kallo kafin baffa Usman yace. “Haba Nuraddeen, kayi haquri, zamu d’auke mahaifiyarka anan amma kasan komai sai anshirya, kabi komai ahankali insha ALLAH zamu fidda ita nan kuma zata samu lafiya, yanzu haka muna tattaunawa akan maganar ne inspector najida ta kirawomu, kayi haquri ka taso muje kaji ko.” STORY CONTINUES BELOW  “Baffa bazan iya ba.” Yafad’a tare da miqewa zai koma cikin cell d’in baffa ya bishi da kallo, saurin dakatar dashi baffa Usman yayi had’e da cewa. “Dawo Nuraddeen za’a fiddo da ita kaji!” Baffa zaiyi magana baffa Usman ya dakatar dashi had’e da cewa “a’a ya kabarshi, inspector najida ya za’ayi kubamu ita.” Baffa Usman ya qarasa maganar yana kallonta. “Bayada matsala baba, dama Bata qarqashin kulawarmu don haka zaku iya zuwa ku d’auketa ko yaushe, Amma d’aukarta akwai had’ari sosai saboda yanayin da take ciki bai kamata ace an d’auketa ankaita cikin mutane ba, wannan kawai shine matsalar.” “To mungode, Kai Nuraddeen kaji abunda tafad’a, me kace.” “Ni zan iya kulawa da mahaifiyata koma a inane, kawai ni bana buqatar zamanta ne a hannun wud’annan mutanen.” Shiru sukayi kafin sufice waje suna tattaunawa akan inda yakamata akaita daga qarshe suka yanke shawarar ajiyeta can gida a d’akinta, ciro waya baffa Usman yayi yakira maqwabcinsu dake jigilar motar haya, Bayan mintuna sai gashi yazo da motarsa sukaje aka d’auko Yaya hawwa tana kucce kucce, aka sata baya sannan Nuraddeen shima ya shiga ya riqeta, kallon baffa Usman baffa yayi yace yashiga gaba, shi zai biyosu abaya ya shiga suka wuce, Godiya ya sake yiwa inspector najida sannan ya nemi Mai mashin ya hau yabi bayansu. Ba qaramar wahala Nuraddeen yasha ba kafin su isa gida don duk ta yakusheshi, haka ma da zasu shigar da ita daqyar da sud’in goshi yasamu yashigar da ita cikin gida har d’akinta don hana kowa ya tab’ata yayi ganin yanda sai ihu da dariya yaran shiya ke yimata. Baffa na saman mashin ya kira baba balarabe yana tambayarsa jikinsu baba balarabe, nan ya sheda masa halin da ake ciki na b’atansu, baffa yashiga tashin hankali sosai marar misaltuwa yashiga sallallami har ya iso gidan, yana isowa ya tadda baffa Usman tsaye shida baffa Ali yana surfa masa masifa akan don me za’a kawo masu mahaukaciya acikin gida tahanasu bacci ta illata masu iyali, yana ganin baffa ya d’aure fuska had’e da zunduma ashar sannan yabar wajen, baffa dake cikin alhini da damuwan b’atan iyayen Rashida kota kansa bebiba balle yadamu da abunda yayi masa yashiga yima baffa Usman bayanin abunda ke faru. “Astagfirullah, astagfirullah, astagfirullah ALLAH ka sassauta mana wannan jarabawar dake b’ullo mana d’aya bayan d’aya.” Baffa Usman yafad’a yana zabga uban tagumi, ahaka Nuraddeen ya taraddasu baffa yayi masa bayani, awannan karon damuwa tayi masa nauyin da bayada kuzarin yin kuka balle ya zubar da hawaye, gefen baffa ya zauna ya d’ora kansa saman kafad’arsa ko zai samu sassaucin yanayin da yakejin kansa aciki, tabbas ubangiji baya zalunci kuma baya goyawa mai zalunci baya domin yayi hani da hakan, haqiqa halin da mahaifiyarsa ke ciki ta cancanci zama ciki fiye da hakan saboda haqqin wud’annan bayin ALLAH da tayi sanadiyar fad’awarsu cikin wani hali suda ‘yarsu, A hankali ya d’ago kansa yana kallon baffa yace. “Baffana shin kana fushi da inna ne har yanzu?.” “A’a Nuraddeen bana fushi da ita Amma aduk lokacin dana tuna cewa ita wani sashece acikin rayuwata kuma mahaifiyar d’ana nakanji ba dad’i.” “Kayafe mata Baffa nasan hakan zaisa tasamu sassucin halin da take ciki.” “Ko kad’an Nuraddeen bani tunanin haqina na daga cikin dalilan da ALLAH ke hukuntata domin tun aranar da ALLAH ya wanzar da tsinkewar alaqar dake tsakaninmu nayafe mata dukkanin haqqina dake kanta kuma ALLAH shine sheda akan haka.” Sake maida kansa yayi saman kafad’ar tasa sannan yace. “Kayi haquri baffana, haqiqa dukanin mumini baya kaucewa jarabawarsa, in Sha ALLAH da sannu quncinmu zai koma farinciki.” STORY CONTINUES BELOW  “ALLAH ya qaddara hakan Nuraddeen.” Cike da tausayi baffa Usman ke kallonsu, haqiqa ALLAH shi yake fidda farin tuwo acikin baqar tukunya kamar yanda ya fidda Nuraddeen acikin Yaya hawwa, Wanda gaba d’aya kyawawan halayensa na mahaifinsa ne ya gado, sunjima awajen kafin akira sallar la’asar suje suyo SALLAH sannan suka kama hanyar yarimawa. Gidan baba balarabe suka sauka suka jajanta masa akan abunda yafaru kafin sujuyo sudawo gida. Da daddare suna zaune sunacin abinci sukaji sanarwar batun tafiyarsu Nuraddeen nan da kwana uku ana masu aqa gargad’insu dasu kasance cikin shiri, Nuraddeen na kallon yanda yanayin fuskar baffa takoma lokacin da aka fara sanarwar har aka gama yana saurare yayi ajiyar zuciya had’e da cewa Allah ya sawaqe. Cikin kwanaki ukun da suka rage kullum Nuraddeen shike zuwa da kansa d’akin Yaya hawwa da aka kulleta ciki ya bata abincin safe rana da kuma dare, haka kuma yakanyi qoqarin gusar mata da duk wata najasa da tayi da dattin dake taruwa cikin d’akin, Bata barin qazanta ko kad’an atattare da ita koda kuwa tana dukan sane har sai yaga ya tsaftace ta. Shi kuma baffa tuni suka gama yanke shawarar Kai Yaya hawwa asibitin mahaukata ta uduth dake jahar sokoto wanda tafiyar takama ranar dasu Nuraddeen zasu wuce, shire shire kawai baffa keyi nakai Yaya hawwa asibitin batare daya koma kula zancen maganar tafiyarsu Nuraddeen ba saboda yanda yaga yafita batun abun, Da daddare awayi safiyar ranar baffa na zaune shida baffa Usman suna fira saiga Nuraddeen yadawo kayansa duk ajiqe sanadiyar ruwan saman da akayi suka yimasa duka, binsa da kallo sukayi har yaje yacire kayan jikinsa ya canzo wasu yazo ya zauna inda suke yana mai saqale hannuwansa waje d’aya ya d’ora akn qirji, “A’a, Nuraddeen daga Ina kake haka ruwa sukayi maka duka?.” Baffa Usman yafad’a yana kallonsa, saida ya kalli mahaifinsa dake qoqarin had’o tea a cup sannan yace. “Daga wajen bankwana nake baffa Usman.” Miqo masa cup d’in tea daya had’a Mai zafi har yana tururi baffa yayi had’e da cewa. “Bankwana fa kace Nuraddeen, Ina zaka jene?” Saida ya kurb’i tea d’in yana sake motsasa da cokalin dake ciki saboda zafinsa sannan yace. “Baffa kayi hak’uri bisa qin fahimtarka da nayi akan maganar tafiyata, a yanzu amince zanje saboda gujewa dana sanin rashin amfani da damar dake iya zowa mutum sau d’aya arayuwarsa, zanje nayi karatu, karatun da zansa kuyi alfahari dani har iya qarshen rayuwata, karka manta lokacin da kake jinya kaso ace d’aya daga cikin zuri’arku yayi karatu a fannin lafiya, to tabbas zan cika maka wannan burin da yardar ALLAH, al-amarin innar mu da Rashida kuwa, wa’ufawwidu amri ilallah, natabbata zai dafa maka wajen kula da komai, don haka shirin da nayi bazan warwaresa ba, da yardar ALLAH zantafi.” Kallo baffa Usman baffa yayi mumushi d’auke da fuskarsa yace. “Kaji ko Usman, dama nafad’a maka bazan takura Nuraddeen ba, bazan tilasta saba amma ina da yaqinin bazai Bari wannan damar da ALLAH yabamu tawuce Saba.” “Alhamdulillah haqiqa naji dad’in sauya wannan hukuncin da kayiwa kanka da kayi, ubangiji ALLAH yayi maka albarka yasa kaje cikin sa’a, ALLAH yafaranta zuciyarka ybka kariya aduk inda kake kuma yayi maka jagora..” Haka baffa yaci gaba da kwararo masa addu’o’i yana riqe da hannunsa baffa Usman na tayashi fuskokinsu d’auke da farinciki, murmushi Nuraddeen yayi ganin haka a fuskarsu had’e da cewa. “Saidai baffa nakasa zuwa wajen baba balarabe inyi masa bankwana saboda rashin sanin da wace irin fuska zan kallesa in iya fad’a masa cewa zanje karatu waje a daidai lokacin da nine na zamo silar b’atan ‘yarsa da kuma iyayenta. STORY CONTINUES BELOW  “Karka damu Nuraddeen nasan bayada matsala zai fahimceka, Amma yanzu lokaci yaqure saboda qarfe bakwai naji ance zaku had’u a babbar ma’aikatar jahar nan don qarfe takwas jirginku zai tashi, don haka ni zani magantu dashi da yardar ALLAH kaji ko?” “Shikenan baffa babu damu.” Yafad’a tare da shanye sauran tea n ya ajiye cup d’in agefe, hannu yasa aljihu ya fiddo kud’i ya miqawa baffa. “Ga wannan baffa, Inna Bilkisu ce da sauran mutanen gida da naje yimasu bankwana suka bani, banso karb’a ba Amma sun tilasta adole na karb’a.” “ALLAH sarki, angode ALLAH yabada ladar zumunci,” “Amin baffa.” “Yawwa Usman ka tayamu godiya idan kaje, ALLAH yasaka da alkhairi.” “Amin Yaya Babu komai ai yiwa kaine.” Baffa usman yafad’a yana murmushi. Nan suka shiga fira tare dayi masa nasihohi kala kala akan yariqe addininsa da al’adunsu nad’an bahaushe idan yaje kafin baffa yaje ya d’auko kud’ad’en da yake ajiya saboda tafiyar. Saida yasake qidanyasu dubu d’ari biyu da ashirin don ya tab’a wasu ma sannan ya miqawa Nuraddeen yace. “Ga wannan ka qara dasu, banida cikakken qarfi ko arziqi da na yimaka fiye da hakan, to kayi haquri dasu su kad’ai ALLAH ya horemun.” Qin karb’a yayi had’e da cewa “A’a baffa kabarsu ai su zasu bamu duk abubuwan da muke buqata idan munje, muradinsu kawai muyi karatu sosai mudawo mutaimakawa qasarmu, don haka kabarsu akula da lafiyar innar mu dasu.” Daqyar baffa suka tilastasa ykarb’i dubu d’ari suka ajiye d’ari da ishirin d’in kamar yanda ya buqata. Shirune yabiyo bayan wasu lokuta kafin Nuraddeen yace “baffa kuroqamun sa albarkar baffa Ali koda bayan natafine a matsayinsa na mahaifi agareni, naje nayi masa magana nafad’a masa zancen tafiyata amma ko juyowa beyi ya kalleni ba.” Murmushin takaici baffa yayi zuciyarsa cike da damuwar halin da d’an uwansa ke nunawa, baffa Usman ne yace. “Kayi haquri Nuraddeen, in sha ALLAH komai zai wuce kaji?” “To baffa Usman ALLAH ya yarda.” Miqewa baffa Usman yayi yace zai wuce baffa ya rakkosa har qofar gida suka yiwa juna seda safe sannan yatafi. Aranar kam zaune baffa suka kwana shida Nuraddeen suna firar bankwana cike da shauqin rabuwa da junan da zasuyi. Tunda asubar fari Nuraddeen ya ida shirya kayansa lokacin shima baffa yagyara tsaf suka nufi can gidan saboda Nuraddeen naso yayi bankwana da mahaifiyarsa, a kan hanya suka had’u da baffa Usman yanata sauri zaije can suka sake juyawa suka nufi gidan tare, a bakin qofar d’aki suka tsaya Nuraddeen yabud’e ya shiga Yaya hawwa na kwance tana bacci bisa tabarmar data rage kad’ai a cikin d’akin don gaba d’aya Nuraddeen ya kwashe kayan dake ciki saboda gudun kada tajima kanta ya mayar dasu acan d’ayan d’akinsa nada. A hankali ya qarasa ciki yaduqa saiti fuskarta yakai hannu zai shafa sai kuma ya fasa, wasu irin hawaye suka zubo masa a fuska yayi saurin gogege yana fad’in. “Innar mu ALLAH yabaki lafiya, ALLAH ya yaye maki wannan lalurar albarkacin haihuwa da tarbiyar da kka bani, ALLAH yasa kaffarar kankarar zunubbanki ne wannan hlin da kike ciki, Ina maibaqincikin barin qasarnan babu addu’arki da sanyawar abarkarki atttare dani, fatan alkhairi uwata kafin nadawo agareki.” Yana gama fad’ar haka yamiqe da sauri yana hawaye yabar d’akin, kamar an tsinkili Yaya hawwa ta tashi da qarfi tanufo wajen qofar tana fad’in. “Nura, nura, kana Ina d’ana, Ina kake nura” Jawo qofar baffa Usman yayi da sauri ya rufe had’e da murd’a key. STORY CONTINUES BELOW  Part d’insa ya bud’e har ya fara qura yana bin ko Ina da kallo, memory d’in da sukayi da Rashida tashiga dawo masa akai musamman daya kalli kitchen wanda ya zamomasu tamkar wani waje da suke d’ebewa juna kewa wajen aikawa da juna kalaman soyayya da kuma isar da saqon zuciya, bud’e cikin d’akin yayi ya shiga nan take yaji qafafuwansa na nema su gagaresa tsayi ya durqushe wajen yana kuka kamar ransa zai fita. Yanajin qarar sautin ihu da bugun qofar da yaya hawwa keyi tana Kiran sunansa Amma rad’ad’in da yakeji azuciyarsa yanzu daya dawo masa fal ba zaisa ya iya sake waiwayarta ba, Qarar wayarsa data fara ruri yasashi tsaida kukan nasa had’e da miqewa yashiga uwar d’akan ya jawo wata jikkar dake d’auke da pics d’in aurensu na ranar walima yaciro hotunanta inda take ita kad’ai tare da d’aukar wayarta data bari sannan yabar d’akin, Saida ya kulle part d’in yaba baffa makullan yana d’iba agogon hannunsa qarfe bakwai daidai ya d’auki butar dake gefe ya wanke fuskarsa su Inna Bilkisu na tsaitsaye suna kallonsa idanuwansa sunyi jawur saboda kukan da yayi har sun d’an kumburo. “Inna Bilkisu mu zamu wuce asamu a addu’a.” yafad’a yana kallon muneera data rakub’e gefe ya sakar mata murmushi, dashire hauru tayi tana fad’in. “Ya nura ALLAH ya kiyaye hanya yabada ilimi Mai albarka, ALLAH yasa koda zaka dawo aunty rashidarka itama tadawo, akaro nafarko da yaji muneera tafara burgesa kenan yasake sakar mata wani murmushin had’e da cewa “Amin muneera, ALLAH yazab’a maki kema miji nagari kafin nadawo In isko kin haifi mani d’a ko d’iya.” Washe haqoranta tayi gaba d’aya tana fad’in “amin ya nura amma d’an bunni irinka.” Juyawa yayi yana kallon Inna ruqayya da tun d’azu ke zabga masu wata it muguwar harara had’e dayin tsaki yace. “Nawuce Inna ruqayya.” Ko kallonsa batayi ba balle yasa ran zata tanka masa daga qarshe saima tashi da tayi tabar wajen, “Nuraddeen zo mutafi mana ga malan bello can a qofar gida da motarsa kai kad’ai muke jira.” Baffa Usman yafad’a tare da bin bayan baffa daya fice daga gidan, rufa masu baya shima Nuraddeen yayi inna Bilkisu da sauran mutanen gida nabiye dashi suna yimasa addu’a, Koda suka isa har motocin wud’anda zasuje sun soma tashi zuwa filin jirgin aminu kano da sauri yafita shima yaje ya gabatar da takardar shed’arsa da i.d card d’in da suka bashi sannan akace yashiga motar dake qoqarin tashi wacce itace ta qarshe. Bayansu su baffa suka sake bi har suka isa filin jirgin, suna Isa aka fara kiran sunayen matafiyan kafin akai ga sunansa yaje ya duqa ya kwashi albarkar su baffa tare da rungumesu yana mai sake roqon dasu kula da mahaifiyarsa Wanda ananbaffa ya tabbatar masa da cewa kada yadamu suma dasun koma zasu wuce sokoto sufara amsar katin Kai mahaifiyar tasa asibitin ta mahaukata da sauran shire shire. Yaji dad’i sosai kuma yasamu qwarin guiwar tsayawa ya jajirce akan karatunsa don ya tabbata mahaifin nasa zaikula da mahaifiyarsa duk da kuwa bata a qarqashin inuwar aurensa. Basubar wajen ba har saida sukaga tashin jirginsu sannan suka juyo suka dawo gida cike da kewarsa…. _’yar uwa mekika fahimta acikin rayuwar littafin SANNU SANNU?, Nidai nafahimci girman uwa komai lalacewarta awajen nuraddin😍don haka bana wasa da mamana kaima karkai wasa da mamankaa,💃🏼💃🏼 domin itacee farincikinka duniya gabaa d’ayaaa (D.one voice)_ Kimanin awanni biyar da rabi suka shafe akan hanya kafin su isa garin kano, iya jigata Rashida tayita don ba kad’an ta tsargu da zaman na mota ba kasancewar bata tab’ayin koda makamancin irin sa bane, bini bini Fatima da Nuraddeen ke juyowa baya su kalleta har zuwa lokacin da suka iso.+ Kai tsaye gidansu dake unguwar sharad’a phase2 suka nufa, da sauri mai gadi ya taso ya bud’e masu had’e da russunawa yana gaishesu dr.nura ya d’aga masa hannu yana fad’in “ahh…malan sule sannu da aiki, kana lafiya?.” “Lafiya klw ranka shidad’e barka da hanya an iso lafiya?” “Lafiya klw malan sule” Dr .nura yafad’a daidai lokacin da yake karya starring motar had’e dayin parking, Fatima ce tafara fitowa tana fad’in. “Ya ALLAH! Sweety wlh duk nagaji.” Daga can cikin motar taji yace, “To matar ke kenan, inata ga mmn baby ko ba haka ba?” Ya qare maganar had’e da juyawa yana kallon Rashida dake qoqarin sab’a Little Nuraddeen a kafad’a zata fita, dariya Fatima tayi ta zagaya tacan gefe tabud’e mata gambun motar had’e da karb’ar little tana fad’in. “Sannu maman boy, ai ko da gani babu tambaya kinfini jigata, tafiya kam mai tsawo babu dad’i ko kad’an gaskiya in bata jirgi ba.” Ita dai Rashida Banda murmushi da takeyi tana shaqar yanayin iskan garin tare da bin tsarin gidan da kallo babu abunda takeyi har yafito cikin motar ya kulle tare da wucewa gaba sukabi bayansa, Suna shiga duk suka zube tsakiyar falo a gajiya, Saida suka d’an huta sannan Dr nura yawuce part d’insa ita kuma Fatima tamiqe d’auke da little had’e da cewa Rashida tabiyo bayanta suka wuce part d’inta, har ga ALLAH Rashida ba hakan taso ba aranta, taso suna isowa sukaita wajen iyayenta duk da lokacin dare ya somayi don takwas na dare tawuce amma babu yanda ta iya dole tayi haquri idan talura da yanayin yanda kowanensu ya dawo agajiye, “Maman boy kishiga toilet kifara watso ruwa kafin nan nima naje na watso nawa, sai in kawo maki little shima ayi masa.” muryar Fatima ce taji tadaki kunnenta tana qoqarin ficewa daga d’akin, sai alokacin tayi yunqurin fita daga tunanin data shiga tare da d’aga mata kai sannan tafice sab’e da little dake faman baccinsa hankali kwance. Rashida tajima zaune agefen gadon tana qarewa d’akin kallo kafin tamiqe tashiga toilet ta watso ruwan, A b’angaren Dr.nura kuwa koda Fatima taje har yafito wankansa, “sweety shine baka jira nazo nataya kaba?” Tafad’a cikin shagwab’e fuska. “Ina tuba matar kawo little maza kije kema kiyo naki musamu muranka sallolin dake kanmu mukai maman boy gida.” Shiru tayi na tsawon daqiqa d’aya dake nuna damuwarta akan maganar, har ga ALLAH tanajin rad’ad’i aranta idan ta tuna halin da Rashida zataje ta riska na rashin iyayenta, ba wani dogon shiri yayi ba face doguwar riga jalabiya daya zura ajikinsa sannan ya karb’i little a hannunta yana fad’in. “Kidena bana son irin wannan dogon tunanin zai iya sakaki cikin damuwar da zata iya ankarar da ita halin da ake ciki.” “Shikenan Dr, Amma kana ganin bazamu bari sai gobe muje kaita ba? Ni sai nake ganin kamar dare yayi yanzu. “Noo…hakan zaisa tayi kuka damu idan mukace mubari sai gobe, amma in mukaje yanzu mun kaucewa duk wani zargi daga gareta akan cewa rashin zuwanmu ne akan lokaci ya haifar da hakan kin gane?.” ‘Daga masa kai tayi sannan tashiga toilet, batafi mintuna biyar ba itama tafito tawuce falo tajawo akwatin kayanta dama tun d’azu Mai gadi ya shigo masu dasu ciki tawuce itama tashirya cikin doguwar rigar wani yadi marar nauyi, karb’arsa tayi takoma d’akin da Rashida ke ciki ta isko ita har tagama shiryawa tana ranka sallolin kanta tunda qasaru ne, tad’an jima zaune kafin taqarasa tamiqa matashi had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Ungoshi kiwatsa masa ruwa kifito falo muna jiranki.” Karb’arshi tayi tana fad’in “sannu aunty yaron nan nabaku wahala, shikenan shi baza’a ajiyesa shi kad’ai ba sai an tsaresa?” “Ikon ALLAH! kin jiki da wata magana mmn boy, ai lalura ce takawo hakan, Amma badon haka ba mezaisa yana baccinsa ayita reto dashi hakan?” Fatima taqarasa maganar tana murmushi sannan tamiqe tafice daga d’akin, a falo taci karo da Dr nura yadawo daga wajen ba maigadi saqo ya sawo masu abinci a wani restaurant dake kusa dasu a can bakin titi. Hijab d’inta ta d’auko tadawo falon yana zaune ya miqe had’e da kabbarta sallah har suka gama ranka sallolin atare, suna zaune Rashida tafito d’auke da little ta gyarashi sai qamshi yake saye da hijab d’inta har qasa, duqawa tayi ta gaishesu suka amsa kowanensu fuskarsa d’auka da murmushi kafin Dr nura yamiqe had’e da karb’ar little d’in a hannunta ya zauna d’aya daga cikin kujerun dake falon, ita kuma ta zauna kusa da Fatima da har lokacin bata tashi daga inda sukayi sallar ba tana addu’a, sai da tagama suka shafa tare Rashida nafad’in. “Amin ya Allah masu albarka auntynah.” Zaro idanuwa wje Fatima tayi had’e da cewa. “Nashiga uku ni batulu, yaushe kika fara shiga zuciyar mutane mmn boy kina gano sirrin addu’o’in da sukeyi.” Dariya Rashida tayi sannan tace. “Ba shiga zuciya bane auntyna, abunda ya tsaya mani araine har yakai yasa bana iya gama duk wata ibada tawa ba tare dana roqi ALLAH daya kawo mana qarshen saba, balle ke da nasan duk yanda nakai ga jin zafinsa kinfini shiyasa natabbatar idan ni ina yin addu’ar samun yayewar wannan abun toke zaki fini yin hakan sosai, ubangiji ALLAH yanda kuke bawa yaron nan kulawa kuma ALLAH yakula daku yabaku zuri’a masu albarka.” Tare duk suka had’a baki ita da Dr.nura suka amsa da Amin. Maigadi ne yayi sallama Fatima taje ta karb’o saqon ta kawo falo ta ajiye sannan taje ta d’auko plates guda uku da cokulla da wani tray babba da yuqa ta ajiye bayan ta d’aurayosu, zuzzuba abincin tayi dake cikin robobin take away sannan taje ta wanko fruit d’in Rashida takarb’a ta gyara masu, miqewa tayi taje ta d’auko little a saman jikin Dr nura dae kwance saman kujera tana fad’in. “Bisimillah yallab’ai.” Saida sukaci suka qoshi Dr ya d’auki makullin motarsa tare da d’aukar little dake saman kujera yana ‘yan wasanninsa da hannuwa sannan ya fice yana fad’in. “Ina jiranku a waje.” Kwashe kayan suka farayi suka wawwanke komai had’e da gyara wajen sannan suka bi bayansa, dama kayan Rashida nacikin mota ba’a fiddo komai ba inba ‘yar jikkar baby bag d’in little dake sagale a hannunta ba, shiyasa shikad’ai ta gyara ta sauyawa kaya ita kuma tamaida wud’anda ta cire ajikinta. Kasancewar akwai ‘yar jayawa sosai tsakaninsu yasa koda suka isa anguwar tasu Rashida qarfe tara da rabi nadare har yayi, duk d’okin da Rashida keyi nason zuwa taga iyayen nata suna nufo anguwar taji gabanta yafara fad’uwa, a hankali tafara kirawo sunayen ALLAH tana mai neman tsarinsa daga dukkanin sharrin dake iya cutar da ita ko d’anta. A daidai bakin qofar gidan ya tsaya da yake akwai wutar nepa da d’aid’aikun mutane dake kai da kawo cikin anguwar, ko gyara tsayuwar motar beyi ba ta b’alle marfinta ta ruga aguje tanufi qofar gidan tana kiran “umma, ummaa.” Turus ta tsaya ganin qofar rufe da kwad’o gabanta na tsananta fad’uwa, juyowa tayi jiki ba k’wari tace. “Uncle ya naga gidan arufe?.” Tana qarasowa inda suke a firgice. Maqwabcinsu ne taga yazo wucewa zai shiga gidansa kafin dr yace wani abun tabi bayansa da sauri tana fad’in. “Baba, baba na kande!.” Da sauri ya juyo yana kallonta cike da mamaki yaja da baya, ya matuqar tsoratar ganinta awannan lokacin ba zato ba tsammani, matsawa ta sakeyi kusa dashi jikinta na rawa tace, “baba nakande nice fa Rashida, nice Rashidar umma fa, don ALLAH baba kada ka gujeni ka tsaya kafad’amun Ina su umma da baba sukaje, Ina son nagansu baba nakande, Ina matuqar kewarsu, kafad’amun ina ne suka tafi don ALLAH.” STORY CONTINUES BELOW  Wata irin ajiyar zuciya ya sauke cike da ta’ajibi yace. “Rashida!” “Na’am baba nakande.” “Rashida ke ce?” “Eh baba, Ina su ummata suka tafi?” Jinjina kai baba nakande ya farayi kafin yafashe da kuka yana fad’in. “Wayyo ALLAH na Rashida sai dai kiyi haquri…” Bata qarasa jin abunda zai fad’a ba tsabar fargaba da tsoron abunda take tunanin zai fad’a yasata fad’uwa wajen, da gudu su Dr. Suka qaraso wajen Fatima taduqa ta tallabota tana kiran sunanta, Dr nura dake riqe da little ya miqama baba nakande hannu dake kuka yace. “Assalamu alaikum, baba meye kafad’a mata halama haka?.” “Yaro kaine?” Baba nakande yafad’a yana share hawaye don ya wayesa, “Eh baba.” “Dama tana hannunka?” “Eh baba,” “To meyasa bak sanar da ita komai ba?, Gashi yanzu tun kafin infad’i abunda zan fad’a tasome.” Ganin halin da take ciki yasa Fatima takoma cikin mota ta d’auko gorar ruwan swan d’in dake ciki ta yayyafa mata had’e da shafa matasu ga fuska, Ahankali Rashida tabud’e idanuwa tare da fashewa da kuka tana fad’in. “Nashiga uku aunty don ALLAH kada kucemun iyayena sun mutu sun barni..” “Haba Rashida, waya fad’a maki cewa iyayenki sun mutu?, Iyayenki na raye amma bamusan inda suka dosa ba, sun bar garinnan kwata kwata saboda b’atanki..” Kan baba nakande yarufe baki tuni sukaga Rashida tafara fizge fizge idanuwanta sun kakkafe.” Da sauri Dr yace Fatima takarb’i little da sai faman kuka yakeyi ya tallabi Rashida yasa cikin mota, “baba don ALLAH idan ka amince kazo muje asibiti dakai, nasan bazaka rasa sanin wasu daga cikin dangin taba.” Duk da baba nakande najin tsoron halin mutunen duniya tausayin Rashida yasa bai tsaya tunanin komai ba yashiga motar ya bisu, da gudu Dr nura ke taka motar har suka isa asibiti, cikin gaggawa aka karb’i Rashida kasancewar wajen aikinsa ne ba tare da antsaya wani b’ata lokaci ba, ba’a jima ba likitan daya shiga dubata yafito had’e da tambayar Dr nura cewa dama tanada hawan jini (hypertension)?. Nan yabashi amsar cewa tana dashi lokacin data haihu amma yayi tsammanin cewa wannan is normal yariga ya wuce, “Noo..gaskiya ba haka bane, yanzu hakan shine ya tsar mata, sai dai baiyi mata worst sosai ba za’a iya shawo kansa da yardar ALLAH, inaga ko yanzu saboda bata jima da haihuwa bane hakn tafaru, amma in sha ALLAH komai zai dai daita don Babu wata matsala bayan shi, yanzu haka anyi mata allur bacci ne saboda tasamu isashhen hutu” “Alhamdulillah Dr. Ngd sosai.” “Ba damuwa dr.nura, ALLAH yabata lafiya.” “Amin Dr” Nuraddeen yafad’a yana kallon baba nakande dake zaune yayi tagumi….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/20, 11:50 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  _ASSALAMU ALAIKUM, GAISUWA DA FATAR ALKHAIRAN ALLAH AGAREKU MASIYANA, INA BAKU HAQURU AKAN RASHIN AMSA MAKU IDAN KUNYI COMMENT😅 KUYI HAQURI IN SHA ALLAH DAGA YAU ZAN GYARA, KUNA QORAFI AKAN HAKA ASHE ABUN SON KAINE WATO WANZAM BAKA SO GA KANKA,🤣 YO IDAN HAKAN NA BATA MAKU RAI ME KUKE TUNANI AGARENI NIDA NAZAUNA NAYIMAKU TYPING DON KU NISHA’DU SAI ACE ANWAYI GARI KO THANKS BAZAN SAMU AWAJENKU BA BALLE COMMENT, DUK DA DAI NI NASA KAINA AI KUNSAN BABU DADI DON NA TABBATA KUNA KARANTAWA, SHIYASA NIMA NA SHAREKU DON KUJI IDAN ABUN KWAI DA’DI😂 BUT TUNDA KUN QARA, TO ZAN GYARA KAMAR YANDA NAKEYI ADA, INA FATAR KUMA ZANGA CHANJI AWAJENKU TA HANYAR DA’DA’DAN COMMENT ‘DINKU👏 NGD SSAI_ Page___55💎 Tuni baba balarabe da Yaya maryam dasu aunty marwiyya suka isa asibitin cikin daren sanadiyar wayar da baba nakande yayiwa baba balarabe ya sanar dashi zancen dawowar ‘yar d’an uwan nasa shi kuma yakira Yaya maryam takira aunty marwiyya ta sanar da ita, kowanensu cike da farinciki yake a zuciyarsa naganin ‘yar tasu duk da dai a yanayin da take ciki na nema ya gusar masu da farincikin, Little kuwa yayi kuka har ya gaji saboda tsabar yunwar da yakeji, goyashi fatima tayi bacci ya d’aukesa shi kuma Dr nura ya koma gida don ya d’auko masu abunda zasu iya buqata kafin gobe don yasan bazasu wuce gobe ba shiyasa koda su baba balarabe suka iso asibitin Fatima kad’ai suka tarar sai baba nakande, ita tawuce dasu d’akin da Rashida take kwance tare da yimasu bayani ataqaice kafin Dr ya iso. Jugum jugum ya tarar dasu kamar wud’anda k’wai ya fashewa cikin ciki ya wuce ciki ya ajiye kayan dayazo dasu yana kallon gefen da Rashida ke kwance hannunta laqe da drip sun kusa qarewa sannan yajuyo yanufi inda baba balarabe ke zaune shida mijin Yaya maryam, “Assalamu alaikum.” Yafad’a yana miqa masu hannu suka gaggaisa kafin baba nakande yayi masu bayanin cewa shine mutumen da yazo da Rashida, cike da girmamawa suka sake gaishesa kafin ya nemi waje yazauna yana fuskantarsu, matsowa su aunty marwiyya sukayi wajen suma suka gaisa sannan Dr nura yagabatar masu da kanshi ataqaice yaqare maganar yana nuna masu Fatima. “Waccan kuma iyalina ce.” “Masha ALLAH.” Baba balarabe yafad’a sannan yace. “Ni sunana malan balarabe, qane ga mahaifin ita waccan yarinyar Rashida, ita Kuma wannan sunanta Maryam wato Yaya agaremu nida mahaifin Rashida, wannan qanwar mahaifiyar tace sunanta marwiyya sai kuma shi wannan mijine ga ita yayar tamu wato alhaji ubale.” “Dukkaninmu da kake gani abu d’aya muke babu banbanci, Kuma mukad’aine iyayen Rashida acikin wannan garin, munyi baqin ciki sosai alokacin da muka rasata wanda sanadiyar hakanne ya haifar mana da shiga matsanancin damuwa kala kala har yakai ga su iyayenta da suka haifeta sun kasa jurewa rashinta sunbar garin bayan doguwar jinyar da sukayi a asibiti.” A yanayin bayanin da baba balarabe keyi yasa Dr nura gamsuwa akan cewa su d’in shaiqanta ne na jini don haka yasaki jiki sosai dasu had’e da yimasu bayanin yanda suka tsinceta dalla dallah da irin wahalar da yaronta yasha wanda shine sanadiyar da yasa basu nemesu ba tun wuri, duk da dai yayi qoqarin ganin yasamu iyayenta alokacin Amma ALLAH bai yarda ba, gaba d’ayan su kuka da tausayin halin da Rashida tashiga ita da yaronta suka shigayi suna Mai godewa ALLAH daya miqata ga hannun mutane nagari masu d’imbin karamci da halacci, a daidai lokacin little dake goye a bayan Fatima ya tashi yafara mutsu mutsu yana neman yin kuka Nuraddeen yamiqa mata hannu ta sancikke masa shi, miqasa yayi hannun malan balarabe had’e da cewa. “Wannan shine abunda ALLAH ya albarkaceta dashi wanda muka rad’a masa suna Nuraddeen bisa yardarta da kuma amincewarta.” Hannun baba balarabe na rawa ya karb’esa yana qare masa kallo don wajen d’auke yake da hasken wutar lantarki kamar rana, tabbas ko ba’a fad’a ba wannan yaron jinin sune don kamarsa sak da d’an uwansa wanda itama mahaifiyar tasa wato Rashida dashi take Kama, wasu zafafan hawayene suka zubo masa yana maijin inama d’an uwansa bai tafi ba yaga irin kyautar da ALLAH yayi masa ta hanyar dawo masa da ‘yarsa da kuma jikansa a hannunsa. STORY CONTINUES BELOW  Rungume yaron yayi yanaji tamkar d’an uwan nasa ne kafin yaji hannun Yaya maryam data kasa dangana tana qoqarin karb’arsa. Murmushi tasaki alokaci d’aya hawaye nasake suko mata saman fuska itama lokacin data karb’i yaron tana fad’in. “ALLAH mun gode maka daka dawo mana da Rashida lafiya daga hannun bayinka salihai masu kyakkyawar zuciya, ya ALLAH ka lullub’esu da tarin ni’imominka tare da yalwataccen farinciki marar yankewa acikin zukatansu da kuma fuskokinsu,” Taqarsa maganar had’e da d’ago yaron tana sumbatarsa. “ALLAH ka isarwa mahaifiyarka Nuraddeen ita da iyayenka, yayi maka sakayya kaida mahaifinka ga muguwar kakarka data nemi salwantar maku da rayuwa kida mahaifiyarka, ALLAH…” Katseta mijin nata malan ubale yayi tahanyar cewa. “Haba Maryam, menene haka? Keda yakamta kigodewa ALLAH sai ki koma kinayiwa bayinsa mummunar addu’ah? Shin ashe hakan ya kamatan ceki kiyi bayan kinsan ALLAH maiyin sakayyane ga bayinsa wud’anda aka zalunta?.” Shiru tayi had’e da miqawa aunty marwiyya little itama takarb’esa, shafa kansa ta shigayi cike da qaunarsa tana yaba kyawon da ALLAH yayi masa da yanayin jikinsa mai cike da ban sha’awa. Ganin gaba d’ayansu sun shagala yasa Fatima komawa cikin d’akin da Rashida ke kwance, tana zuwa ta isko tafarka daga allurar baccin da akayi mata lokacin kusan qarfe d’aya saura mintota nadare, da sauri Fatima ta matsa kusa gareta tana jero mata sannu, qoqarin tashi zaune tayi ta dakatar da ita tana fad’in “a’a komawarki ki kwanta maman boy.” Tana dafa kafad’arta had’e da qoqarin maida ita kwance, “Aunty da gaske su ummata sun tafiyarsu?, Da gaske ba’asan inda suka tafi ba?, Shikenan bazan sake ganinsu ba?” Rashida tafad’a had’e da riqe hannuwanta tana kuka, cikin dakewa Fatima da tuni zuciyarta tayi rauni hawaye sun soma kaida kawo a fuskarta tace. “A’a maman boy, Zaki ga su ummanki komai daren dad’ewa, hakan bayana nufin kun rabu bane Rashida sai dai kawai ubangijinki na auna imaninkine ta hanyar yimaki jarabawa wata bayan wata Kuma dama haka rayuwar mumini take, idan anyi masa jarabawa ya canye ta sai asake yimasa wata jarabawar wacce tafi tafarkon da akayi masa don kawai a d’aukaka darajarsa da kuma imaninsa idan ya canyesu, kiyarda cewa zasu dawo agareki nan kusa bada jimawa ba in Sha ALLAH.” Cikin kuka tace “Yaushe? Awane lokaci kuma aunty? Bayan zukatansu sunriga sunyi imanin cewa sun rasani kenan har abada.” “Kisa aranki cewa kusa zasu dawo, haba maman boy karki manta ALLAH subhanahu wata’ala yana cewa.” _”Laa taqnad’u min rahmatllah (kada mu kuskura muyanke qauna ga rahamar ALLAH)_” “Don haka kada kicire tsammanin cewa rahamar ALLAH zatasa iyayenki sudawo matuqar kika miqa dukanin al’amurranki agaresa kamar yanda kikayi abaya, haqiqa wawa, lusari, Wanda baisan kanshi kad’aine ke rabka hannuwa yana tsammanin cewa ALLAH bazai jarabcesa ba bayan kuma yace yayi Imani, walh Rashida ALLAH da kansa ke cewa matuqar kukace kunyi Imani to.” _”wala nabluwannakum bi shai’in minal haufi wal ju’i wa naqsin min amfusi wassamarat, wabasshirisubirin, allazina iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa Inna ilaihirrajiuun, ma’ana idan kunyi Imani dani to (zamu jarabceku da abubuwan tsoro, da yunwa da rashin rayuka daga kawunanku da kuma tsirrai, muna yima masu haquri bushara wud’anda idan musiba tasamesu sai suce ga ALLAH mukazo Kuma agareshi zamu koma)”_ “Saboda haka ki daure ki zamo cikin bayinsa masu haquri da yake yiwa bushara kinji ko!” Cikin kuka dake cike da sauti Rashida tafad’a jikinta tana fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, allahummah thabbit aqadami wa haqqiq Imani,..” Qarar kukan nata yajanyo hankalin su baba balarabe dake waje da sauri suka shigo cikin d’akin har suna rige rigen qarasowa bakin gadonta, tana ganinsu taqara fashewa da wani kukan had’e da rungume aunty marwiyya tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Wayyo ummana..” Babu yanda suka iya domin rasa iyaye tako wace irin fuska ce yanada matuqar rad’ad’i arai wanda dole ko ana so ko ba’aso awannan gab’ar dole abarta tayi kukan domin ko anhanata yinsa rad’ad’in da takeji azuciyarta bazai barta tahanu ba, sai da tayi mai isarta tayi shiru sannan tajaye daga riqon da tayiwa aunty marwiyya takwanta akan gado tana ajiyar zuciya har lokacin hawayen basu dena fita daga idanuwanta ba, sannu suka dinga yimata d’aya bayan d’aya tana amsawa had’e da binsu da kallo hawayen naci gaba da zubo mata. Rarrashinta suka taru sunayi had’e da ban magana da dad’ad’an kalamai Amma gaba d’aya ita ba abunda take gani sai hoton fuskokin iyayen nata da batasan ranar da zata koma had’uwa dasu ba. Gaba d’aya takasa tsaida zubar hawayenta wanda hakan yasa Dr nura yaje yakira Dr daya dubata yazo ya sake yimata allurar bacci bayan aunty marwiyya ta aza mata little daya fara qananun kuka tabashi nono yasha, Bacci mai nauyi sosai ya d’auketa sannan baba balarabe yace da aunty marwiyya taje gida tunda dare yayi sosai lokacin qarfe d’aya da rabi, Atafau tabuga kai ga qasa akan babu inda zataje anan zata kwana, don gani take za’a iya sake d’auketa idan taje gida kafin tadawo gobe da safe. Adole aka qyaleta tunda ta nace akan haka, Kiran mijinta tayi tasanar dashi anan zata kwana Kuma cikin sa’a ya amince mata don mutumne da baida matsala kuma ko bayan hka su biyu suke ga mijin nata shiyasa Bata damu da sai takoma gida ba. Yaya maryam ma daqyar baba balarabe ya samu tabi mijinta sannna yajuyo yana kallon Fatima dake riqe da little yace. “Fatima dake da Dr. Yakamata ku koma gida saboda akwai gajiyar tafiyar da kukayo kuna buqatar hutawa sosai, inyaso nida qanwar mahaifiyar ta zamu kwana anan idan Babu damuwa koda za’a buqaci sawo wani abu kunga ni Ina nan babu matsala.” Ji Fatima tayi kamar ta k’walla ihu don har ga ALLAH bataso barin asibitin ba amma saboda dr.nura ya amsa yasa dole babu yanda zatayi ta haqura ta miqawa aunty marwiyya little kamar zatayi kuka ta karb’esa sannan sukayi saida safe suka tafi sai tunzurar baki takeyi, kallonta yayi yana tuqi yayi murmushi had’e da cewa. “Fatima meye abun b’acin rai naga kina turar baki haka?” Saida ta kallesa sannan ta maida kanta gefe tace. “Meyasa kaima bakace anan zamu kwana ba, ALLAH bana son rabuwa da maman boy ita da little hisby d’innan nawa, shine kai harda wani miqewa da sauri irin bakama damu ba.” ‘yar dariya yayi daidai lokacin suka iso inda ‘yan sandan dake security akan titi suke yayi slow da motar had’e da ciro i.d card d’insa ya nuna masu suna yayyada bayan motar da wajen boot sannan suka basa izinin wucewa. Bayan sun wuce wajen ya juyo ya kalleta tare da aza hannunsa saman nata yace. “Kiyi haquri kinji matar?, Ba haka nake nufi ba amma yakamata kisn cewa yanzu bamuda wani sauran iko akanta, mu kawai masu taimako ne, munemi cikar ladar taimakon da mukayi, kada mu nemi shiga hurumin da iyayenta kad’ai suke da haqqi akansa, kada mutauye ladarmu tahanyar nuna ra’ayin zukatanmu bayan munsan ayanzu sunfimu tsananin buqatar kasantuwa da ita, koba haka bama ai dole murabu dasu ko bama so, don haka daga yanzu kifara koyawa zuciyarki yanda zata jurewa rashinsu akusa damu kinji ko?” Batare data amsa masa ba ta d’ora kanta kawai saman kafad’arsa tana shafa hannunsa har suka iso gida. Shima baba balarabe kiran iyalansa yayi yace surufe gida shi sai gobe zai dawo. ••• ••• ••• Su baffa nadawowa daga filin jirgi suka harhad’a kud’ad’en da zasuje kai yaya hawwa asibiti tare da wata ‘yar qaramar jikka da kowanensu yasa kayansa kala d’aya da zasuyi amfani dasu don sai gobe zasu dawo kasancewar akwai nisa sosai tsakanin kano da kuma sokoto garin shehu, wanda koda sun isa dawuri bazasu kammala abunda ya kaisu ba har sai dare yayi, don haka dole suyi haqurin juyowa gobe idan ALLAH yakaimu bayan sun kammala abunda sukeyi.Bankwana sukayi da Inna Bilkisu bayan baffa Usman ya jadda mata da kada abar Yaya hawwa da yunwa kafin sudawo, suyi qoqari kota tagane su dinga ajiye mata abinci har ALLAH yadawo dasu lafiya sannan suka tafi, akan hanya sukaci karo da Inna ruqayya ita da baffa Ali tafe suna magana qasa qasa, kallo d’aya baffa Ali yayi masu ya d’auke kai Inna ruqayya kuwa harara ta zabaga masu had’e dayin tsuki tawuce tana fad’in.+ “Qarya dai fure take ba ‘ya’ya, Kuma raminta qurarrene, sunyi abu yasha masu kai, gashinan garin neman gira anrasa ido, ba’a samu yabo ba ansamu wahala.” Kanta baffa Usman yanufo ransa ab’ace baffa yariqe hannunsa had’e da cewa. “Haba Usman kada kataya mahaukaci hauka, ai kabarta tafad’i abunda ke ranta domin da kanta take, tafi muje ko nine a matsayinta zanfad’i abunda yafi hakan musamman idan akwai b’acewa atattare dani.” Yaja hannunsa suka tafi. Yanajin sadda suka kwashe da dariya baffa Ali nafad’in. “ALLAH dai yaraka taki gona.” Inna Bilkisu kuwa da kanta taje tabud’e d’akin Yaya hawwa ta ajiye mata abinci had’e dayin tsaye abakin qofar d’akin tana kallonta, ganin tayi ana buga Yaya hawwa ajikin bangon d’akin kafin a d’agata sama ayar qasa batasha mamaki ba sai da taga anjuyar da kanta gefe yana kallon sama sannan an mammal qwashe mata hannuwa sun koma baya, qafafuwanta kuma anbud’esu kowace anjata gefe, ahaka taga tana jan ciki tazo inda abincin yake tasa kanta ta turesa ya zube qasa sannan tafaraci da baki kamar yanda dabbobobi keyi, kuka ne ya qwacewa Inna Bilkisu ganin yanda aka maida ita kamar wata muguwar dabba da sauri taja qofar d’akin tarufe tabar wajen tana kuka, kobata tambaya ba tasan wannan aikin shed’anun aljanune don haka taje ta d’auko redionta tasa karatun qur’ani tanufi d’akin, da sauri Yusuf yariqota had’e da cewa. “Inna Bilkisu kada kiyi haka, bakisan wud’anne kala bane kada garin taimako kema su nemi cutar dake, kibari tunda su baffa sunje nemamata mafita anema mata.” Wata qara sukajiyo daga d’akin da tasa yusuf jawo hannun Inna Bilkisu yana fad’in “kinji ko inna Bilkisu, ALLAH kimaida kada kitafi, ALLAH zai baki ladar niyar da kikayi.” Inna ruqayya da baffa Ali nashigowa kuwa tsuki sukaja had’e da cewa. “Bisimillah, ‘yar mahaukatannan tafara, wlh mukam dai anzaluncemu da aka ajiye manaita anan tana neman kashe mana kunne da baqar qara sai kace dujjal.” Dariya baffa ya kwashe da ita had’e da zuwa ta tagar d’akin yana leqen Yaya hawwa yace. “Ikon ALLAH, ke ruqayya zo kiga yanda matarnan mai shegen cin zarafi da iya walaqanci ta koma, wlh kyace wata qwaguwa ce,” leqawa tayi tafashe da dariya tace. “Ala gwai, wlh naji dad’i, dubi qafafuwan shegiya uwa na lala tacciyar mace, ke muneera..” Ta kwalawa muneera kira dake d’aki kwance tana bacci. Cikin magagin bacci tafito tana susar kai tace, “Matso nan kiga Yaya hawwa dake maki sherin gwalmammin qafafuwa kiga yanda ALLAH yamayar mata da nata.” Leqawa muneera tayi had’e da murza idanuwanta don ta tabbatar da abunda suka gane mata da sauri ta jid’o had’e da cewa. “Tab.. ALLAH Inna hawwa takoma uwa banqararriyar kaza.” Suka kece da dariya, shidai Yusuf da Inna Bilkisu nagefe suna mamakin yanda baffa Ali da Inna ruqayya kefitar da munanna kalamansu ga Yaya hawwa cike da isgilanci, sai kace ada ba itace wacce suka d’auka shugaba kuma aminiyar duk wasu shawarwarinsu da al’amurransu na duniya ba….. _”‘yar uwa shin ko kinsan da wud’anne kalar mutane kike rayuwa dasu acikin duniya?, shin kina iya banbancewa wud’anda ke sonki da kuma maqiyanki acikin mutanen dake zagaye dake?,sanin hakan nabuqatar natsuwa da kuma nazari, tabbas ni nakoyi darasin sanin cewa mutum mugune kuma bayada tabbas awajensu baffa Ali haka kuma na d’auki darasin zaunawa nagano banbancin masoyin gaskiya da kuma naqarya awajen Inna Bilkisu, nayarda cewa mutum bayada alqibla wajen rashin gano ainahin kalarsa. Don haka kema yiqoqari ki tsinci naki darasin acikin wannan littafin mai suna SANNU SANNU Bata hana zuwa.._🥰 STORY CONTINUES BELOW  *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/21, 11:20 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___57💎 ••• ••• ••• Sosai wan saheke Rashida tasamu sauqi zuwa azahar aka basu sallama, kai tsaye gidan Yaya maryam aka nufa da ita duk da baba balarabe yaso ace gidansa zata zauna, Amma ganin yanda Yaya Maryam d’in ta kafe kai da fata lalle wajenta zata zauna yasa ya haqura tunda itace yayarsa babu yanda zaiyi, Tunda Rashida ta bar gida yaune karo nafarko da taji tana son had’uwa da mijinta wato habibinta mahaifin d’anta Nuraddeen, suna kan hanyarsu ta zuwa gidan Yaya maryam da yake Dr nura ne ya d’aukosu a mota, Fatima na gefensa riqe da little sai Yaya Maryam da aunty marwiyya da ita Rashida abaya, shi kuma baffa mijin Yaya maryam ne ya d’aukosa saman mashin d’insa suka biyo bayansu, takalli aunty marwiyya tace. “Aunty ya nura fa?” Wata uwar harara ta zabga mata had’e da juyar da kanta gefe, ganin haka yasa ta kama bakinta har suka isa gida, Dr nura nayin parking su baba balarabe dake biye dasu na tsayawa da mashin d’insu, Yaya Maryam ce tafara fitowa sannan aunty marwiyya suka nufi cikin gidan, hakama Fatima itama tafito tare da riqo hannun Rashida dake qoqarin fitowa tayi mata jagora sukabi bayansu, A can cikin gida aunty marwiyya tafara fad’a tana fad’in. “Yaya wannan yarinyar batada hankali, kinji tambayar da takwyimun a mota wai ina ya nura? Wlh badon batada lafiya ba da saina d’auketa mari don ko sunan garinsu bana sonji balle sunansa.” “Hmmm banni da ita marwiyya Ina jinta, bi izinillahi ko shikad’ai ya rage namiji aduniya bazata koma gidansa ba, ai tunda haka tafaru to ta tabbata komai mahaifiyarsa zata iya yimata saboda qiyayyar da take yimata kuma mu shedane akan haka, shikenan kuma don muna sakarkari sa mubarta takoma masa a kashe mana ita, narantse kozai mutu sai yasaketa tunda ba ita kad’ai bace macce aduniya ba.” “Wannan shine daidai Yaya Maryam, in yaso yaje can uwarsa ta aura masa wacce take so.” Aunty marwiyya tafad’a a qufule. Tana rufe baki suna shigowa, ta sakarwa Fatima murmushi had’e da cewa. “Wucikke matar Dr.” Batare data kalli inda Rashida take ba. A falo suka shiga suka zazzauna kafin mijin Yaya maryam yashigo shima su Dr da baba balarabe nabiye dashi abaya. Bayan sun zauna Yaya Maryam tamiqe taje takawo masu ruwa da lemuna masu sanyi da ‘yar sauran samosar data had’a da safe da take sayarwa ta ajiye masu, “Balarabe kutab’a wannan kafin kuwuce.” Saida suka fara tab’a hira ana tayiwa little da Fatima ta ajiye tsakar falo yana faman yimasu qyaqya dariya sannan tamiqe taje ta d’ora masu dahuwar taliya da kifin gwangwani ga ‘yar qaramar tukunyar gas cooker d’inta saboda tayi saurin nina, ai kuwa cikin mintotan da basu wuce goma ba ta nina ta zuzzubo a flate ta kawowa kowa, sake d’auko had’ad’d’en zob’onta na siyarwa da takeyi tayi ta kawo masu sannan itama ta zauna tana cin nata, “Kai amma zob’on nan yayi dad’i yaya maryam ya akeyinsa?” Fatima tafad’a tana sake kai cup d’in zob’on abaki. “Kai matar Dr Banda zolaya, zob’on na siyarwa?” STORY CONTINUES BELOW  “Eh mana, gaskiya kina gyarasa sosai, ai wannan zob’on ko shugaban ‘yan hasada yasha dole ya yabashi balle masu so da gaske.” Dariya duk suka samata harda Rashida da tun d’azu takasa kai koda cokali d’aya abaki sai faman cakularsa takeyi, “Hmmm! Yakamata nabiya kud’in zobonnan tunda yasa madam Santi har na tsinkayo ana yimata waigi.” Dr nura yafad’a yana dariya ganin aunty marwiyya na gyarawa Fatima hilon dake bayanta, juyowa tayi had’e da cewa. “Au..Ashe da gaske yakeyi, kai aunty marwiyya zakija yadinga tsokanata kuwa.” Kallon Rashida baba balarabe yayi had’e da d’aure fuska yace. “Ke Rashida maza kici abinci kinji ko?” Ganin bada wasa yakeyi ba yasa tafaracin abincin tana b’ata fuska tamkar wacce keshan magani. Yanda su Dr suka saki jikinsu cikin ‘yan uwan Rashida Kai ka rantse kace Abu d’aya suke ko kuma sun jima da sanin juna, hakan Kuma ba qaramar shaamquwa da yarda ta sake shiga tsakaninsu. Bayan kowa yaci yasha ya qoshi, baba balarabe yayi gyaran murya had’e dayin doguwar addu’a da nasihohi masu ratsa jiki bisa abunda ya faru sannan yarufe dayiwa su dr.nura shida matarsa godiya sosai shida su Yaya Maryam, irin godiyar da suke yimasu da kyawawan addu’o’i had’e da fatan alkhairi har seda suka fara jin kunya, daga qarshe aunty marwiyya tace. “Mungode sosai Fatima matar nura uwar nura, muna roqon Rabbissamawati wal ardi daya azurtaku da ‘ya’yaye nagari masu albarka da zakuyi alfahari dasu duniya da lahira, ALLAH yakareku daga dukknin sharrin abinqi ya lullub’eku da rahamarsa da tausayinsa yayi maku arziqi mai yawa ya share maku dukkanin kukanku.” “Amin ya ALLAH aunty.” Suka amsa cike dajin wani dad’i da sanyi da farinciki azuciyarsu, Itama Rashida hawaye nazubar mata a idanuwa ta rungume fatima tana fad’in. “Dukkanin alqawurranku agareni wanzazzune hakama alkhairanku tabbataccine akaina, karamcinku da halacci masu girmane da mizaninsu yakai girman da bazan iya biyanku aduniya ba, amma har zuwa fitar lumfashina zuciyata da Kuma rouhina cike da qaunarku mai tsanani take, duk wani fitar lumfashi nawa cike yake da fatan alkhairan ALLAH agareku da kuma farinciki mai d’orewa, ina roqonku da kada kucireni acikin rayuwarku kada kumanta dani kubani damar da zan iyaci gaba da rayuwata tare daku matsayin ‘yan uwa batare da zumunci ya yanke a tsakaninmu ba har izuwa ranar da zan kwatanta faranta maku zuciya kamar yanda kuka faranta tawa data ahalina koda sau d’aya ne.” “Bazamu mantaki ba Rashida, bazamu rabu dake da little ba don kunzamo wani yankin daya sama mana farinciki na wani d’an lokaci arayuwarmu wanda muke fatan yatabbata atare damu har abada” Fatima tafad’a itama had’e da rungumeta tana kuka, kuka sukeyi sosai sai kace wud’anda suka rabu kenan har saida Dr nura ya cewa Fatima ta taso sutafi yana mai mamakin yanda shaquwa mai tsanani haka tashiga tsakaninsu a qanqanen lokaci, ‘Daukar little tayi ta sumbacesa agoshi tare da wucewa gaba suka rakosu qin miqasa tayi har saida ta shiga mota Dr nura na Shirin tayarwa sannan ta badashi tana goge qwallan da suka zubo mata, shi kanshi Dr nura saida yaji ba dad’i Amma babu yanda suka iya dole yaja motarsa sukabar wajen. Su kuma yana tafiya rigima ta kaure tsakanin baba balarabe da yace a dole akira Nuraddeen da ahalinsa asaanar dasu yayinda sukuma su aunty marwiyya sukace atafau bazai yuyu ba, daga qarshema Yaya Maryam bugawa Rashida tsatsauran Jan kunne tayi akan karta sake koda mafarkine tayi tunanin zata koma gidan Nuraddeen tunda mahaifiyarsa bata sonta. Shikuwa baba balarabe duk da Yaya Maryam na sama dashi haka yatabbatar mata da cewa dole sai yasanar da Nuraddeen anga matarsa saboda haqqinsane kuma har lokacin tana aqarqashin igiyar aurensa, hakan yasa suka rabu baran baran, rayuwakan kowanensu a b’ace. STORY CONTINUES BELOW  Yana komawa gida yashiga Kiran lambar baffa data baffa Usman Amma shiru kowace switch up, hakama ta Nuraddeen yakira yafi a qirga itama akashe saboda bai fara anfani da sabon layin daya siya acan. Hakan yasa hankalinsa tashi sosai marece nayi yanufi garin bebeji, yana isa yaci karo da baba Ali ya tsaya yana tambayarsa, sunjima suna magana kafin baba balarabe yabar wajen jikinsa a sanyaye, wata ‘yar iskar dariya baffa Ali yayi sannan yawuce yana fad’in “da sannu duk sai kun gane kurenku har ita wacce sanadiyar b’atanta aka rufemu nida iyalina aka yimana dukan mutuwar da gangar jikinmu takasa d’auka” Kwana baba balarabe yayi yana juyi akan abunda baffa Ali ya sanar dashi duk da dai wani b’angaren na zuciyar tasa bai yarda da hakan ba. ••• ••• ••• Su Baffa kuwa a maimakon kwana d’aya da zasuyi agarin sokoto sai da sukayi kwana biyu saboda shawarar da wani likitan yabasu akan sukai marar lafiyarsu kware shine abunda zaifi masu sauqi, hakan yasa suka sake kwana d’aya acan har saida suka gama shirya duk abunda yakamata acan asibitin kware suka biya kud’in da za’a basu mota da jami’an lafiyar da zasu d’aukota sannan suka juyo zuwa gida bayan sun bada address d’in da za’a tura masu motar nan da kwana biyar, gaba d’aya wayoyinsu sun mutu saboda rashin charji da basuda wannan ne dalilin da yasa baba balarabe yayita kiransu bai samu ba. Saida suka iso zamfara don dama motar da zata ajiyesu acan sai daga nan su shiga wacce zata kaisu kano suka shigo kafin motar da suka samu ta kano ta cika suka shiga masallacin dake cikin tashar sukayi sallah sannan suka samu wani saurayi ya ara masu chargarsa sukasa wayar baffa charji, minti talatin sukayi sannan motarsu tacika lokacin baffa har yasamu d’igo biyu a ‘yar wayar tasa qirar kamfanin itel mai madannai. Mintuna biyu yayi da kunnata kiran baba balarabe ya shigo. Cikin natsuwa baffa ya d’aga had’e da amsa sallamar da yayi masa sannan suka shiga gaisawa. “Am dama wata magana naji cewa Nuraddeen yabar qasar nan shine nace bari nakira naji shin ko gaskiya ne.?” Wani irin nauyi baffa yaji Amma bayada wata hanyar da zai iya basa amsar tambayar da yayi data wuce eh ko kuma a’a, tamkar baffa nagabansa ya duqar da kai had’e da cewa. “Eh malan balarabe hakane amma…” Kafin yaqarasa baba balarabe ya katsesa ta hanyar cewa. “To madallah, shikenan nagode.” Had’e da kashe wayarsa, duk inda ransa yake in yayi dubu ya b’aci, Ashe akwai ranar da Nuraddeen zai nuna irin wannan halin ko inkula agaresu adaidai lokacin da suka rasa ‘yarsu a hannunsa, Ashe har yanada qwarin guiwar da zaya iya barin gari acikin yanayin da yake kuma har yatafi batare daya yimasu sallama ba?, Me suka yimasa da suka cancanci haka daga wajensa? Ai koba komai ana bankwan saboda ba’asan halin rai ba, kuma ai yakamata ace ko don kaucewa zargi yazo yayi masu bayani, wud’annan tambayoyi sune suka dinga Kai da komo acikin zuciyarsa da kuma qwaqwalwarsa, rashin samun amsar sune yasake tunzurasa sosai, Ransa ab’ace yanufi gidan Yaya Maryam yakirata tare da zayyane mata duk abunda kefaruwa, dama tayi mamakin ganinsa shida jiya suka rabu baran baran da ita sai gashi har yana fad’in ko mijin Rashida naso ko baya so duk inda yaje dolene ya saketa, kuma dole duk wata alaqa dake tsakaninsu su datseta koda hakan na nufin zasu mayar masa da d’ansa a hannun sane. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/23, 10:36 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 STORY CONTINUES BELOW  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___58💎 Shiru Yaya Maryam tayi na tsawon daqiqu uku kafin tace. “Hakan shine daidai, dama abunda nayita qoqarin lurar dakai kenan ka kasa ganewa, to amma batun cewa za’a mayar masu da yaro don yanke duk wata alaqa dake tsakaninmu kabarta don ni gaba d’aya bana buqatar jinmu yakoma zama atare dasu tunda basa da zuciyar imani.” Sun jima suna tattaunawa kafin yabar gidan har lokacin yanajin d’aci akan maganganun da baffa Ali yafad’a masa. ••• ••• ••• Baffa nagama waya da malan balarabe yakalli d’an uwan nasa ya sakar masa murmushi cikin qarfin hali sannan ya juyar da kansa gefe, yana maimaita innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun aransa. Dafa kafad’arsa baffa Usman yayi had’e da cewa. “Meke faruwa ne Yaya?” “Abunda Nuraddeen yayi gudun faruwarsa.” Yabashi amsa had’e da juyowa suna fuskantar juna. “Kayi haquri Yaya, dama dole hakan zata faru, mu auna kanmu a matsayinsu mugani, don haka dole zamu lallab’asu har su fahimcemu, ayanayin yanda damuwowi sukayi masu yawa kamarmu, abune mai wahala su iya riqe fushinsu alokacin da sukaji labarin tafiyarsa musamman idan sun jine daga bakin daya kasa yimasu kyakkyawan bayanin da zayasa sufahimta, shi kuwa rashin bayani acikin kowane al’amari shike haifar da husuma da kuma aikin dana sani, don haka dole muyi haquri har zuwa lokacin da zasu fahimcemu.” “Shikenan Usman, amma duk da haka mufara jaraba zuwa wajensa idan mun sauka.” Awa hud’u ta d’aukesu kafin su isa kano, ana ajiyesu tasha suka sake shiga motar da zata kaisu qauyen na yarimawa, cikin qananan daqiqu suka isa sukaci sa’a kuwa yana zaune bakin gida yana arwala suka yimasa sallama, bai amsa ba har saida ya gama arwalarsa ya d’aga kansa sama yayi addu’ar da akeyi bayan gama arwala sannan ya kallesu fuskarsa a sake ba yabo ba fallasa ya amsa masu salamar. “A’a malan Idris, malan Usman sannunku da zuwa yanzu kuke tafe?.” Yafad’a yana qoqarin ajiye butar da yayi arwala agefe, kallon baffa Usman baffa yayi kafin suji ya sake cewa. “Kai Hassan kushiga ciki ku kawo ruwa a butoci magrib taqaraso ana batun tada sallah.” “Am sannunku da zuwa bari naqarasa masallaci kafin ku iso liman na batun tayarwa.” “To shikenan!” Baffa yafad’a cike da mamaki a fuskarsa. Basu sake Shan mamaki ba sai da suka fito sallah suka tarar da tabarma an shimfid’a a qofar gida da kwanonin abinci, “A’a malan Usman ya akayi kukayi tsaitsaye? bisimillah kuzo kuzauna mana, Gaggaisawa suka shigayi kafinsu baffa sufara qoqarin canza maganar izuwa asalin wacce takawosu, Amma ga mamakinsu sai sukaga kawai yajawo kwanoni abinci yana fad’in bisimillah malan idris muci abinci ko.” Babu yanda suka iya saboda yanada matuqar muhimmanci agaresu da bazasu iya yimasa musu ba, wanke hannayen su sukayi sukasa suka fara cin abincin tare har suka qare, Bayan sun kammala, baffa yace. “Don ALLAH malan balarabe kayi haquri ka sauremu, nasan an aikata maku ba daidai ba, amma kuskurene da babu wanda ya isa ya kauce masa, tabbas Nuraddeen yabar qasarnan saidai bada son ransa ba, nine natirsashi ganin yana shirin ruguza rayuwarsa, kuma dama ce wacce yasamu tun kafin wud’annan matsalolin su faru, ganin ba lallai bane ya sake samun wannan damar ba kuma ga yanayin da yake ciki yasa daya tirje akan babu inda zaije saboda yana tsammanin dawowar matarsa garesa wanda abune gaibi akan dawowarta yasa natilasta masa zuwa koya fita daga cikin halin damuwar da yake ciki.” STORY CONTINUES BELOW  “Hmmm malan Idris kenan!, Ai bance kunyi wani laifi ko kuskure ba, meye laifinku don kunyi qoqarin inganta rayuwar d’anku?, Meye laifinku don kunyi abunda zai sakaku cikin farinciki?, Ba kuda wani laifi don haka kumanta da komai, fatana d’aya muma ALLAH yabamu ikon d’aukar darasin da kuka koyamana muma mu inganta rayuwar ‘ya’yanmu kamar yanda kukayi koma fiye da hakan.?” Duk iya qoqarin da sukayi wajen ganin sun lurar dashi ya fahimci gaskiya hakan ya cutara daga qarshema cewa yayi. “Don ALLAH da girmansa malan usman mubar wannan magana kada tajawo rugujewar sauran mutuncin dake tsakaninmu, d’anku dai ALLAH yabashi ilimi mai albarka mukuma ALLAH yatsare mana ‘yarmu aduk inda take yabata juriyar shanye duk wani abu da zai nemi duqufar mata da farinciki.” “Amin” suka amsa masa dashi bayan sun sake bashi haquri sannan suka wuce zukatansu a dagule. Bayan suntafi yakira Yaya Maryam lokacin tana zaune itada Rashida tana bawa little da sai qara wayau yakeyi nono, “Na’am balarabe ya akayi? Duk lafiya dai kuke ko?” “Lafiya klw Yaya, dama iyayen yaronnan mijin Rashida ne sukazo bada haquri….” “Kaga rufemun babinsu bana son ji, ai Ina mumuka haifi aburmu kuma muka bashi aurenta ko! don haka yanzu mun raba, ko suna so ko basa so yazama dole yabawa Rashida takardar ta, bazata koma gidansa ba ko mutuwa zaiyi, shashancin baza da wofi.” Yaya Maryam ta katsesa tana masifa, Wata irin zabura Rashida tayi had’e da miqewa tsaye da kad’an little yafad’i, Yaya Maryam tayi saurin riqosa had’e da kashe wayar tana binta da wani mugun kallo mai cike da tarin tambayoyi, hankalinta atashe takalleta tana fad’in “Mekike fad’a haka gwaggo!,” da yake da haka suke kiran sunanta sannan taci gaba da cewa. “Wai wa ake zancen zai sakeni?, Duk fa iya adadin kwanakinnan dana d’auka zuciyata cike take da mararinsa, idanuwa da kunnuwana cike suke da son ganinsa da kuma jinsa, kawai nayi shirune saboda kada kuga rashin kunyata tayi yawa amma Ina son na had’u da mijina, shine kuma kuke cewa sai ya sakeni?, Meye laifinsa?, Wne zunubin ya aikata da za’ayi yunqurin rabashi da ni?” “Ungo nan marar kunyar yarinya.” Yaya Maryam tafad’a had’e dayi mata daqquwa tanaci gaba da cewa. “Ke wane zunubin kika aikata da uwarsa ta rabaki dashi, kin ganemun shashashar yarinya da batasan ciwon kanta ba, to bari infad’a maki wlh munfiso kimutu atare damu muyi maki sallah murufeki da mumaidaki gidansa uwarsa ta sake halakar mana dake, don haka tunwuri kiciresa aranki matuqar kina son muzauna lafiya dake kinji nafad’a maki.” “Haba gwaggo! Haba gwaggo wannan wani irin tsattsauran hukuncine zakuyi mana, inada yaqini akan tunda wannan jarabawa tasameni shima t yake cikin irin tashi jarabawar, don ALLAH kada kura bamu kodon yaronnan.” Taqarasa maganar tana kallon little dake hannun ita Yaya Maryam d’in had’e da fashewa da kuka, har ga ALLAH Yaya Maryam taji tausayinta, Amma Babu yanda ta iya, wannan ita kad’aice hanyar da zasubi su kub’utar da ‘yarsu daga sharrin uwar mijinta, wacce itama tanacan cikin mummunan yanayin da basuda labari akai, cikin dakewa da qarfin hali tace. “Rashida kawai kuhaqura da juna, yaro kuma Allah shizai rayashi ko bakwa tare don haka kibi umurninmu kizauna lafiya.” Wani kukan ta sake fashewa dashi had’e da durqushewa qasa tana fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, astagfirullah ALLAH natuba kayafemun laifukana, ya ALLAH ka sauqaqamun wud’annan jarabawowin rayuwa kada sufi qarfin zuciyata susa na sab’a maka,” kallon yya matram data kauda kai tana goge ‘yan guntayen hawayen da suka zubo mata tayi. “Gwaggo baifa sakeni ba, taya zaku rabamu?, Karku manta dani harshi zamu iya sake ahiga wani hali idan kuka yimana haka, kunada iko akaina ammashi sam bai kamata kununa iko akansa tahanyar tirsasashi ya sakeni ba.” STORY CONTINUES BELOW  “Kedai zaki shiga wani halin keda kike ganin bamu isa mutirsasaki akan abunda muke ganin shine alkahiri arayuwarki ba, amma bandashi tunda har ya iya mance awane irin hali zaki shigaba keda abunda ke cikinki ba ya tsallake qasarnan ya tafiyarsa duk da yasan abunda yafaru dake Amma saboda ya gyara rayuwarsa kuma ya farantawa iyayensa yatafi yabarki acan duniyar da bai masan inda kike ba don ya inganta gobensa, ba kekad’ai da ba kyanan ba hatta mu iyayenki da yasan muna nan ya wofantar damu ta hanyar tafiyarsa batare da saninmu ba, wannan shi kike tunanin har zai shiga wani hali idan aka rabaku.? Tir da wannan banzan tunani irin naki” tana gama fad’ar haka tafice d’auke da little da yayi bacci a hannunta Tunda tafara magana Rashida ta dasqare a inda take tsaye, shin Anya maganganun da gwaggon tata ke fad’a gaskiya ne ko a’a?, Ko kwanto tashigayi akan cewa habibyn nata zai iya tafiya acikin yanayin da ake na b’atanta kuwa?, Inaaa hakan bazai yuyu ba , tabama kanta amsa had’e da miqewa tana goge hawayenta, dole yau sai tahad’u da mijinta koda hakan na nufin za’a rabata da lumfashinta ne, dole ta qaryata d’ayar zuciyarta dake neman gasgata kalaman da gwaggo tafad’a mata. ‘Dakin da anan ne aka bata tashiga ta d’auko mayafinta da sauri tanufi qofar fita gidan, kota halin qaqa yau tanada buqatar zuwa ta had’u da masoyinta kuma mijinta, sand’a tafarayi gudun kada taganta ta hanata zuwa har ta isa bakin qofar gidan Tana fitowa taci karo da Fatima aqofar gida ita da Dr ya kawota. Cikin farinciki Fatima tarungumeta tana fad’in “‘yar halak ina zakije ne ko kema kinyi kewar tamune kamar yanda mukayi?” Ganin yanda idanuwanta sukayi jajir saboda kukan da tayi yasa Fatima cewa. “Subhanallahi, maman boy meyake faruwa?” Hakan yasa Dr fitowa daga cikin motar yana kallonta had’e da qoqarin rufe marfin motar, qarasowa wajensu yayi kafin yace. “Maman boy lafiya?” Yanda sukaga ta sake fashewa da wani kukan yasa Fatima riqo hannunta zata shiga cikin gidan da ita da sauri taja baya tare da tirjewa. “Don ALLAH uncle ku kaini naga ya Nuraddeen, Ina son ganinsa Ina so nahad’u dashi Amma su baffa sunqi amincewa,” “Kamar ya Rashida?” Dr.nura ya tambayeta cikin rashin sani. “So sukeyi su raba aurena dashi uncle kuma Ina son mijina, bayada laifi, akan abunda yafaru amma gaba d’aya sun kasa fahimtar hakan! don ALLAH ko sau d’ayane kataimaka akaro nabiyu ka had’ani da mijina kamar yanda kahad’ani da iyayena.” Maganar takeyi tana kuka had’e da game hannayenta waje d’aya, Alama yayiwa Fatima dasu shiga motar sannan yajuya shima yashiga had’e da tayarwa, hannunta Fatima tariqa tabud’e gambun bayan motar tasata ciki sannan tarufe itama tashiga yaja motar sukabar qofar gidan, “Ina muka nufa?” Ya tambayeta adaidai lokacin da suka fito qauyen. “Bebeji.” Tabashi amsa ataqaice tana goge hawayen da suka jiqa mata fuska sharkaf, Tafiya mai d’an nisa sukayi kafin su iso gaba d’ayansu Babu wanda kecewa wani uffan, tuqi yakeyi da hannu d’aya, hannun d’aya kuma ya azoshi saman tagar qofar yariqe hab’arsa dashi ita kuma Fatima sai faman jujjuya kwalin wayar dake hannunta takeyi wacce dama itace dalilin zuwan nasu saboda kewarta da tayi mata yawa kullum cikin zancenta ita da little yasa Dr yasiyowa Rashida wayar don suriqa gaisawa sai gashi sun tarar da ita cikin wannan halin.Bini bini take juyowa takalleta cike da tausayi kafin Dr yamiqo mata wayarsa. “Kamomin Yaya maryam” Scrolling contact d’insa ta farayi har takai ga lambar Yaya Maryam da yayi saving da Ya Maryam kano takirata. Bugu d’aya ta d’aga muryarta a hargitse. STORY CONTINUES BELOW  “Dr.” “Na’am, anwuni lafiya.?” “Lafiya klw, yanzu nake zancen kiranka na nemi Rashida sama ko qasa narasa saboda nayi mata fad’a.” “Karki damu tana tare damu, dama shine kiran dana yimaki.” “Tirqashi Amma wannan yarinyar anyi shashasha, shine zata fita fisabillahi bazata fad’amun ba, gaba d’aya duk tabi ta tayarmun da hankali?.” “Kiyi haquri, Bata kyauta ba gaskiya amma yanzun nan zamu dawo tare in Sha ALLAH.” Kasancewar akwai cikakkiyar yarda tsakaninsu yasa bata damu sosai ba duk da abun ya b’ata mata rai, asalima gaba d’aya ranta bai kawo mata cewa Rashida zatayi tunanin zuwa tahad’u da Nuraddeen ba balle har ta taka da kanta taje garin nasu, Koda suka iso angama sallar isha’i suka samu gefen wani shago sukayi parking, Fitowa tayi cikin motar suma suka biyo bayanta har suka iso inda za’a iya hango gidan, “Inane gidan Rashida?” “Wancanne uncle.” Tafad’a tana nuna gidan da yatsa. “To muje ko.” “A’a uncle bazan iya ba, kawai ni shi kad’ai nake son nahad’u dashi.” “Bari to naje nasa ayo mani sallama dashi.,” Yafad’a tare da tunkarar gidan. Tsaye kawai take duk qafafuwanta sunyi sanyi tanaji tamkar basu imata, kallon anguwar takeyi d’aya bayan d’aya, Kafin tahango Yusuf tafe yanufo inda suke gefen wani tsoho dake saida kalanzir saman d’an teburinsa, “Lado abani kalanzir na naira ashirin?” “Ahhh… yusufa d’an gidan yayansa nura, Wai ina yashige ne kwana biyu nadena ganinsa.?” “Laah…ashe lado bakasan yaje qasar waje ba?” “Kai yusufa!, Kace wlh.” “Wlh lado da gaske nakeyi.” “Kai ALLAH ban yarda da kaiba, shi nuran d’an mahaukaciya ne da zaibar qasar nan bayan matarsa da tsohon ciki tab’ata, sai kace wanda bedamu da ita ba,” “To ni kabani kalanzir d’ina kada innar mu tabugeni, ai sai katambyi mutane kaji, yanacan yaje k’aro karatunsa.” “Tirqashi! Amma gaskiya be kyauta ba.” Kukan da Rashida ke qoqarin dannewa ne yaci qarfinta had’e da kucce mata. Da sauri Yusuf daya miqa hannu zai karb’i kalanzir d’in da lado kemiqo masa suka d’ago kai tare jin kukan da suka jiyo agefensu. “Yaa rasulu manzon ALLAH, ke baiwar ALLAH lafiya.?” Lado yafad’a had’e da sakin kalanzir d’in yana kallon Fatima da Rashida dake tsaye hasken k’wan shago na yadosu, da hannu Yusuf ya shiga nuna Rashida don fuskarta bazata tab’a b’oye masa ba aduk inda tashiga, kasa magana yayi sai faman ja da baya yana fad’in. “Aun..aunt..auntyyy..” Yaruga aguje yabar wajen had’e da nufar gida yana k’walawa su baffa…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/24, 10:40 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  Page___59💎 Baffa, baffa, baffa ga aunty tadawo, abunda Yusuf kefad’a kenan har ya isa bakin qofar shiga gida, karo yaci da mahaifin nasa wato baffa Ali shida Dr. nura dake qoqarin barin wajen fuskarsa a cunkushe babu alamun walwala atattare da ita, kad’an yarage Yusuf yafad’i garin kallon Dr nura daya ga yanufi inda su Rashida suke, da sauri ya riqo hannun baffa Ali yana jansa had’e da nufar inda ya gasu Rashida yana nuna masa wajen da hannu, gaba d’aya Yusuf ya rud’e ya manta da cewa ba mahaifinsa yakamata yasan da dawowar taba sanin irin matsayin da take dashi awurinsa. Baffa Ali kuwa binsa yayi har suka isa wajen lado mai kalanzir, lokacin kuwa har su Rashida sunbar wajen saboda irin amsar da Dr nura nura yazo masu da ita, “Lado Ina aunty?” “Kai yusuf wace aunty kuma?.” “Haba lado! Anan fa nabarta ita da wata mata, nan wajen!.” Yaqare maganar yana nuna masa inda suka tsaya. “Aiho nan naga sunbi suda wani mutum.” Lado yafad’a yana d’aure ledar daya zubawa wata yarinya kalanzir. Dagudu Yusuf yabi hanyar baffa Ali shima yabi bayansa don yatabbatar da da hakan, Suna kawowa su Rashida naqoqarin shiga mota ya shiga qwala mata kira. “Aunty, auntyyyy..” Juyowa tayi tana goge hawaye harya iso wajen, da sauri baffa Ali yab’oye bayan wani kango yana hangosu don kada taganshi. “Aunty ina zaki tafi kuma, kizo muje gida don ALLAH, ya nura nason ganinki shida su baffa da Inna bilki, kowama nason ganinki munyi kewarki sosai don ALLAH kizo muje kinji aunty.” “Yusuf me zanje inyo agidanku Bayan wanda nazo don shi gaba d’aya yabar qasar, zantafi Kuma bazan sake dawowa acikin gidanku ba saboda bakwa sona.” Tafad’a tana kuka tare da juyawa zata shiga motar, riqe hijab d’inta yayi shima yana kukan yace. “A’a aunty muna sonki don ALLAH kada kitafi.” Hannunta tasa tacire hannunsa daga riqon daya yiwa hijabinta sannan tafad’a cikin motar Dr. Nura yaja sukabar wajen. Kuka Yusuf keyi kamar ransa zai fita had’e da nufar hanyar zuwa gidan baffa, da sauri baffa Ali yafito daga mab’uyar daya shige yatare gabansa had’e da kamo hannunsa, “Kai Yusuf ina zakaje ne acikin daren nan?” Ya tambayesa had’e da d’aure fuska yana kallonsa. Cikin sheshshekar kuka Yusuf yace. “Gidan baffa zanje.” “Kaje kayo ubanmi acan?.” “Zanje infad’a masa Aunty tadawo amma ta tafi kuma tace bazata sake dawowa ba.” Saida ya sakar masa wani mugun ranqwashi akai sannan yace. “To uban waye ya aikeka? idan Auntyn tadawo qanwar uwarka ce kota ubanka da zakaje kasanar dasu tunda tace bazata koma dawowa to meye naka aciki.?” Qoqarin bud’e baki yayi don ya bashi amsa sai Kuma yayi saurin rufewa da hannunsa sanadiyar yanda ya murd’e masa kunne so had’e da cewa. “Karka sake inji kafidda wannan maganar waje kaji nagaya maka, inba haka ba yanda Yaya hawwa ta b’addata kaima haka zansa a b’adda kai, kaga shikenan baka ba ganin kowa naka wata qilama kamutu gaba d’aya ahuta, shashashan yaro kawai, har kamanta akanta akaje aka kullemu ni da mahaifiyarka, babu kalar azaba da kuma dukan da bamu sha ba ahannun ‘yan sanda kuma duk ta dalilinta, to bari kaji duk kasake naji wannan maganar abakin wani sai nayi maka d’an banzan duka kuma wlh kadena cin abincin gidana kenan har kamatu, shegen yaro da bansan halin waye kad’auko ba, maza kawuce gida kafin in jijjimaka anan” STORY CONTINUES BELOW  Sosai Yusuf ya tsorata dajin kalaman da baffansa ya fad’a masa don haka yanufi gida yana kuka kamar ransa zai fita, kasa shiga d’akin mahaifiyarsa yayi yakoma saman barandar part d’insu ya Nuraddeen dake rufe ya had’a kai d guiwa yanaci gaba da kukansa, tun qarfe takwas yake zune wajen yana kuka har wucewar goma da rabi nadare kan kace me tuni zazzab’i ya taso masa ya fara rawar sanyi, Inna Bilkisu ce tafito zata zagaya bayi tagansa wajen a kwance had’e da cewa. “Kai Yusuf lafiya kazo nan ka kwanta ko sanyin nan bakaji?, Maza tashi kawuce d’aki kar mura takama ka” Ba tare data tsaya sauraren amsar da zai bata ba tawuce bayi don yin lalurar data fiddota, koda tadawo ta tarar har lokacin yana a wajen kwance ko motsawa baiyi ba daga inda tabarshi “Ikon ALLAH, wai bakaji me nace maka bane Yusuf.?” Tafad’a tare da qarasawa wajen tana d’agosa, yanda taji jikinsa ya gashe da zafi sai faman rawar sanyi yakeyi yasa tayi saurin rungumosa ajiki tana daddafa kansa. “Subhanallahi, Yusuf dama baka lafiya shine kazo nan ka kwanta.” ‘Dago kansa yayi yana qoqarin yimata magana saiga baffa Ali ya shigo shida baffa Usman, ai yana ganin haka da sauri yaqarasa wajen yana fad’in. “Kai Yusuf mekakeyi wajen? Ko munafuccin ne kaima zaka koya.” Ya zata maganarce yake fad’a mata, Inna Bilkisu najin haka tacire Yusuf daga jikinta had’e da zaunar dashi saman barandar tanufi inda mijinta yake tsaye yana jinjina irin kalaman da d’an uwansa ke alqanta iyalinsa dasu, shi kuwa baffa qiiiii…yaja hannun Yusuf har yana neman fad’uwa yana fad’in. “Wannan yaron anyi mai kunnen qashi, ina dai kasan abunda nace maka shine zakazo nan kasaki baki don rashin jin magana” hed’e da jefasa saman gadonsu d’an bono bayan sun shiga d’aki, ••• ••• ••• Dr kuwa banda tunanin kalaman da baffa yafad’a masa babu abunda yakeyi, wannan wace irin rayuwace muke ciki aduniya?, Wanda ma kayarda dashi alokaci d’aya sai ya sauya maka, ancuci yarinya kuma ankoma ana binta da sharri, a iya saninsa inzai tuna Rashida tafad’a masa cewa mahaifin mijinta na qaunarta Amma sai gashi maganganun daya fad’a masa akanta sunsha banban da irin kalaman daya dace afad’a ga wanda ake so, saita madubinsa yayi yana kallon yanda hawaye ke tsiyayowa daga cikin idanuwanta dake rufe ya saki wata irin ajiyar zuciya, tabbas ta cancanci tayi kuka ba kad’an ba, ko kad’an bazai hanata tayi shiba awannan karon saboda abubuwan sunyi mata yawa, a qaramcin shekarunta bai kamata ace tafuskanci irin wud’annan damuwowin ba donma Allah yataimaka ansamu jininta yakoma normal da tuni qila zuciyarta tabuga, duk da dai bai sanar da ita gaskiyar abunda yafaru tsakaninsa da baffa Ali ba daya nuna masa cewa shine mahaifin Nuraddeen, kawai dai ya fad’a mata cewa ance baya nan yabar qasar. Tare suka shiga gidan da ita lokacin da suka iso yaya Maryam na tsaye tsakar gida tana jijjiga little da sai faman kuka yakeyi tun d’azu. Miqa hannunta tayi ta karb’esa kanta naduqe aqasa batare data bari sun had’a ido da yaya Maryam ba data zuba mata ido tana kallo. ‘Daki tawuce, su kuma suka tsaya suna gaisawa da ita, “Sannu Dr har kin dawo.?” “Eh ya gida yaya Maryam.” “Gida Alhamdulillah Dr, kunbarni da yaro sai faman tsula Mani kuka yakeyi?” Murmushi yayi had’e da cewa. “Afuwan ai gamu mun dawo, dama kwana biyu Fatima tadameni da zancen ta shine nace bari muzo dubata sai gashi munci karo da ita, ganin babu alamun walwala atattare da fuskarta yasa nace bara muje da ita wani wurin taraka mu, I fatar za’ayi mana afuwa bisa wannan kuskuren?” Yafad’i hakanne saboda yasan ran Yaya Maryam b’aci zaiyi idan tasan gaskiyar inda sukaje. “Ba komai Dr, ai kaga Fatima gaisawa kawai mukayi tabi bayansu saboda sukad’ai tadamu dasu” Shiru yayi na tsawon wasu ‘yan sakanni kafin yace. “Amm! Dama yaya maryam cewa nayi yakamata ariqa kwantarwa da Rashida hankali saboda yanayin damuwowin da suka tarar mata azuciya don kar takoma shiga wani halin, nasan kuna qoqari sosai tunda gashi naga cikin kwanakinnan tacanza ba kamar yanda muka zoba saboda yanayin natsuwar da tasamu, amma don ALLAH aqara bata kulawa, sha’aninta akwai bantausayi aciki sosai.” “Ikon ALLAH!, Ai dama nasan dole qara tace zata kai wajenka Dr tunda muna ganin mutuncinka, yakamata ace rashida ta fahimci abunda muke guje mata faruwarsa saidai takasa gane hakan…” Nan takwashe komai tafad’a masa akan abunda yafaru ba qari balle ragi, sosai Dr yashiga rud’ani daya auna maganganun guda biyu, da wud’anda baffa yafad’a masa da kuma na yaya Maryam yagano akwai wani abun aqasa wanda ba daidai ba, ko meye kuma ALLAH kad’ai yasani.” Haquri yabata tare da sake roqonta a lallab’ata in Sha ALLAH da sannu zata fahimcesu sannan ya koma bakin motarsa yana jiran fitowar Fatima. Rashida kuwa saida taba little nono yasha ya qoshi Fatima na gefenta tana dad’a bata haquri tare da rarrashinta sannan tamiqa mata shi ta kwanta saman qatuwar katifar dake cikin d’akin nata, anan maganganun da suka faru tsakaninta dashi a daren ranar suka shiga dawo mata a kwakwalwa, tabbas ita ta qarfafa masa yin wannan tafiyar kuma ko kad’an hakan da yayi ba laifi bane, Amma meyasa ya aikata hakan batare daya sanar da iyayenta ba.? Meyasa baiyi tunanin abunda zai iya faruwa ba akan wannan kuskuren da yayi, kamata yayi ace ya fahimci cewa komai na duniya kan iya sauyawa idan aka samu sauyin al’amurra, kama daga ra’ayi, buqata, lafiya, wajen zama da kuma yanayi na yau da kullum, gashi yanzu yaje yabar baya da qura, babbar damuwarta shine rashin sanin har tsawon wane adadin lokaci zai d’auka kafin yadawo. Jitayi Fatima nafad’in “maman boy zamu tafi, yana waje yana jirana, don ALLAH kimaida al-amurranki agaresa kidena kukannan bayada amfani, ga wannan wayace uncle d’inki ya siya maki zamu rinqa magana, akwai lambata da tashi aciki kuma na saka maki ta yaya maryam data aunty marwiyya saiki kirasu, kada kiyarda inkira injita akashe, ko yaushe ina son ki kasance tare da ita kinji ko?.” ‘Daga mata kai tayi sannan tajuya zata tafi tana d’auke da little. “Au! yau babu rakiya maman boy?” Ta juyo tana kallon rashida dake qoqarin tasowa alokacin. Har bakin mota ta rakata tare da yiwa Dr.nura godiya sosai tamiqa mata Little sannan suka wuce… _Darasi: ‘yar uwa ki guji aikata laifi komai qanqantarsa domin bakisan iya adadin mutanen da Zaki iya cutarwa ba ta dalilinsa, wanda hakan kad’ai na iya zamowa dalinlin tsanantar hukuncinki awajen ALLAH, domin shi mai yafe haqqinsane amma banda haqqoqan rayukan da kika cutar, laifi d’aya yaya hawwa ta aikata akan rashida amma mutane da yawa sun cutu adalilinta, ciki kuwa harda qaramin yaro (yusuf) dake fuskantar damuwa da kuma barazana ta dalilin hakan._[8/21/2020, 8:13 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___56💎 Saida suka gama shaqiyancin su day izgilanci tukuna suka baro wajen, A hankali Inna Bilkisu ta tako zuwa bakin rumfar d’akinsu suna qoqarin shiga d’aki jikinta a sanyaye tace. “Ruqayya, Ali kuji tsoron ALLAH, duniyar nan da kuke gani batada tabbas, shin ashe halin da Yaya hawwa take ciki bai isa yazame muna aya da kuma darasi ba?, Karku manta tare da muke zaune da ita acikin gidannan, itama mutumce kamarmu amma ALLAH yajarabci rayuwarta tahanyar komawa a cikin wannan yanayin da take ciki wanda muma bamufi qarfin ALLAH ya jarabcemu fiyema da yanda muke ganinta, I zuwa yanzu ya kamata ace mudukanmu munyi karatun ta natsu, mu zamo tsintsiya mad’aurinmu d’aya duk abunda yasamu d’ayanmu mu d’auka mu yasama kuma mu wa’aztu domin wannan halin da take ciki wlh iznane agaremu.”+ “To jikanyar limamai, Ina ruwanki meya shafeki da al’amarinmu?, Dama akace maki ke muke tsoro da zakizo kice muji tsoron ALLAH?, Ke nifa bilki bana son sa ido kiyi sha’aninki kibarmu muma muyi namu, yo Ina ruwanmu da halin da take ciki ai haukane ba’agareta farau ba kuma ta cancancesa, wlh Banda ALLAH ya isa tsakaninmu da ita bisa abunda taja akayi mana Babu abunda zamuyi mata, aikin banza in wa’azi kike son yi to jeki kiyi mata ita dake d’auke da haqqoqan mutane akanta take damunmu da kuwace kuwace tana hanamu bacci.” Inna ruqayya tafad’a tana harararta, tsaki baffa Ali yaja had’e da juyowa yana kallonta cike da takaici yace. “Ke Bilki, mufa yanzu babu ruwanmu da al-amarin kowa agidan nan don haka kifita harkarmu, baruwanki da duk abunda zamuyi koda kuwa kafirci ne, kabarinki daban namu daban kinajina ko!” Jinjina kai Inna Bilkisu tashigayi kafin tace “Wal’iya zubillah, Ali meyakawo wannan zancen, ai _inni laku minnannaasihin (ni kawai agareku mai nasiha ce)_ ubangiji ALLAH kashiryemu kuma yabaku haquri.” Tana gama fad’an haka tajuyawarta tabar wajen tana maijin takaicin halin da suke ciki. Muneera kam tutse baki tayi tana susar kai tace. “Inna wai meyasa kuke yima Inna Bilkisu haka?, ALLAH tanada kirki kawai don baku gane bane, amma lokacin da kuke rufe wajen ‘yan sanda ALLAH duk ita take kula damu tana bamu abinci.” A hasale Inna ruqayya tayo kanta tana fad’in “Ke dallah rufemun baki, akace maki donku takeyi, duk wata maqarqashiyar rufemun da akayi ai da had’in bakinta ita da baffanninku, ai kinga kuwa dole su baku abinci ko don gudun duniya tazagesu.” “Kai Inna, ALLAH ba haka bane, ai mukad’ai ke zaune dasu ina duniyar take balle ta zagesu, kawai kice keda baffana bakwa son gaskiya kuma wlh sai anyi maku irin na inna hawwa idan baku dena ba, ni Babu ruwana, abunda ma nece mata (banqararriyar kaza) wlh da gaske ni haka naga takoma.” Kanta baffa Ali yayi da wani icce dake gefensa tafice da gudu daga gidan tana susar kai… ••• ••• ••• Baba da umma kuwa suna zamansu hankali kwance Babu wanda ke takurasu, gwargwado suna cin mai kyau kuma suna shan maikyau, hakama alhaji naqoqarin ganin ya kyautata masu saboda su samu kwanciyar hankali da natsuwa kuma Alhamdulillah ba laifi sun d’an fara ragewa kansu damuwa, wasu lokutanne kawai take bijiro masu idan suka tuna da ‘yarsu sai ‘yar matsalar hajia nafeesa dake musgunawa umma tahanyar yawan baqaqen maganganu da tsawar da take yimata duk kuwa da taka tsantsan da takeyi da ita, ga Rashin kunyar da yaranta keyi wanda shike sakesa hajia nafeesa fitina idan aka qiyi masu yanda suke so. STORY CONTINUES BELOW  Yauma umma na kitchen tsaye tana jiran albasar data yanka acikin ruwan mai tasoyu sannan tazuba kayan miyan da zata dafa jallof dasu sai ga yaronta d’an shekara goma mai suna Shakur ya shigo, dube dube ya farayi cikin kitchen d’in kafin yace. “Ke umma zuba mun abinci.” “Yi haquri Shakur abincin bai ida nuna ba.” “Nidai kizuba mun haka zanci.” “A’a bari dai nahad’a maka qanzon nan naturawa (cornflaks) kafin ka qarasa sha nagama kaji ko.” Bubbuga qafa yafarayi zai b’are mata baki da kuka tayi saurin jawo plate ta zuba masa shinkafar data yiwa per boiling gudun kada kukan nasa ya jaxa mata walaqanci awajen mahaifiyarsa, “Ungo gashi” tafad’a tana miqo masa plate d’in farar shinkafar data zuba man da take soyawa da magi mai star akai yanda zaiji dad’inta ya karb’a yawuce abinsa. A daidai saman inda dining table ke ajiye yaje ya zauna qafafuwansa na reto a qasa ya fara cin abincinsa hankali kwance ko d’an sauran qarfin shinkafar daya rage tanuna baya ji tunda yunwa yakeji. Jim kad’an hajia nafeesa tafito cikin wani material mai shegen kyau yasha d’unkin riga bubu waya laqame akunnenta tana takawa d’ai d’ai, da alama wayace takeyi da wata, idanuwa ta qwalalo awaje hango d’an tsakiyar ranta wato Shakur yana cin shinkafar da kallo d’aya zakayi mata kasan Bata dahuba saboda yanda take tsaitsaye, wajensa taqaraso ta d’auke plate d’in dake gabansa tana fad’in. “Ina zuwa hajia hafsat, zankira daga baya.” “Kai shakur a ina kasamu wannan?.” “Momy a kitchen ne nasamu.” “Waya baka?” “Umma mai aiki…” Tun kafin yarufe baki tashiga qwallawa umma kira da qarfi, umma najin haka tasan a fusace take. Tsoron qasqanci da walaqancinta yasa umma fitowa da sauri alokacin da tasake kiranta tana fad’in. “Na’am hajia, gani.” Jeho mata plate d’in da sauran shinkafar tayi ya bugi goshinta sannan yafad’i qasa duk shinkafar ta wawwatse mata ajiki. “Har ke waye da zaki bawa yarona abinci gaya babu miya kuma d’anye wanda be nuna ba, ke wace nake tambayarki?” Hajiyar tafad’a a tsawace. Qasa umma tayi da kanta saboda batajin duk qasqancinta zata iya sa’insa da matar dako sa’ar qanwarta mawiyya batayi ba. Masifa tashigayi inda taka shiga ba nan take fita ba har tan fad’in umma tadena ganin tagirmeta zata iya zabga mata mari akan yaronta wai so takeyi takashe mata shi shiyasa tabashi d’anyen abinci salon cikinsa ya kumbure masa, cikin fushi tace. “To wlh maza ki tattarata ki kwashe kuma sai kin zauna anan gabana kincinyeta tas kamar yanda kikasa yarona yacita.” Haka tayita masifa da ita har alhaji dake tsaye a harabar gate shida wani abokinsa suna magana yajiyo harshen nata, hakan yasa yayi cikin gidan ransa a d’an b’ace da zimmar yimata magana ya tadda umma durqushe a gabanta tana kakkab’e shinkafar dake jikinta had’e da qoqarin tattara wadda ta zube qasa ita kuma tana tsaye kanta tana faman jijjiga jiki, motsin da taji ya sata juyowa tana kallonsa had’e da cewa. “Yawwa qwanda daka shigo ka ganewa kanka abunda tayi, irin wannan iskancin da sukeyi kesa kake ganin kamar ina wulaqanta ‘yan aiki, farar shinkafa na isko fa taba Shakur ko nina batayi ba salon taja masa wahalar da zata kashesa, musamman idan ta kumbura masa ciki.” “Sai ke kuma kika yimata me?” yatambaya ransa a b’ace.” “Shine da raina yab’aci nawatsa matashi kuma nace ta tattarar dashi ita tacinye.” STORY CONTINUES BELOW  “Ok. Ni ina wahalar samo abinci ke kina zubarwa qasa, shikenan umma ajiye ki tashi wajen.” Yafad’a tare da matsowa wajen ita kuma umma takoma gefe ta makure, “Duqa ki tsincemun abina tas ki miqomun keda kika watsar dashi.” Yace ma hajia nafeesa tare da nufar inda shakur yake zaune. Sanin halinsa yasa hajia nafeesa duqawa tsince abincin tana hararar umma tana kumbure fuska sai kace wacce aka hurawa mabusa. Riqo hannun shakur yayi had’e da cewa. “Shakur d’in baba ya akayi kake cin waccan shinkafar haka?” “Abba yunwa nakeji kuma umma bata gama abinci ba da nace tazubomun haka sai tace inbari ta had’amun cornflakes shine nace bana so da taga zanyi kuka sai ta zubomun a haka saboda nace zanci.” “Bakasan cin shinkafa have done zata iya kumbura maka ciki ba.” “Abba bazata yimani komai ba yunwa nakeji.” Daidai lokacin hajia nafeesa tagama tsincikke shinkafar tazo tamiqo masa tana faman cika da batsewa, Murmushi yayi sannan ya karb’a ya ajiyewa Shakur agabansa yace “Ungo kayi bisimillah ka qarasa canye abinka kaji ko, Amma kada kasake yin haka Babu kyau.” “Alhaji fa yayi qasa.” Hajia nafeesa tafada kamar zatayi kuka. “Eh yaci babu abunda zai yimasa in sha ALLAH, Ina kinsan da haka amma kikace ita tacinye sa ko.” Juyawa yayi yana kallon umma yace. “Umma kiyi haquri, kuma daga yau bazaki sake yin aiki agidannan ba.” “A’a alhaji kada ayi haka, indai akan wannan ne babu komai zanci gaba dayi, bana son na zaunane waje d’aya, nafi son ind’an dinga mommotsa jikin.” “A’a baza’ayi haka ba, aishi d’an adam daraja ne dashi yakamata ace angirmamashi musamman wanda ya girmeka, walaqanci bayada dad’i ko kad’an don haka kije zanyi magana da hajia fareeda sai ki koma acan b’angarenta inaga zaifi tunda kinfiso kina motsa jikin naki.” “To shikenan alhaji ngd, bari na qarasa wannan girkin.” “A’a umma kibarshi ita zata qarasa da kanta.” Da qarfi hajia nafeesa ta d’ago kai tana kallonsa yayin da umma tafice daga part d’in tana godiya ga ALLAH daya kawo alhaji ya kub’utar da ita daga cin mutuncin da tayi niyar yimata kuma ya yaye mata damuwar zama da ita da kalolin walaqanci da cin kashin da takeyi mata. Jinjina mata kai yayi idanuwansa acikin nata alamun da gaske yakeyi sannan yace. “Kuma ba wannan girkin kad’ai zaki ida da kanki ba, daga yau nayi maki alqawarin babu wata macce da zata koma zama part d’inki da sunan yi maki aiki har sai lokacin da kika canza kuma kika san darajar mutane, don haka ya rage wajenki kidafawa kanki da yaranki abinci ko karki dafa duka ruwanki, wannan shine hukuncin dana yanke akai, idan kuma kikak’i ji to wlh kinji na rantse bakyaqi gani ba. Yana gama fad’ar haka ya juyawarsa ya fice, dama tuntuni yake son d’aukar mata mataki akan cin zarafin da take yiwa bayin ALLAHn dake qarqashinta ALLAH bai bashi iko ba sai yau. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/21/2020, 11:20 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 STORY CONTINUES BELOW  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___57💎 ••• ••• ••• Sosai wan saheke Rashida tasamu sauqi zuwa azahar aka basu sallama, kai tsaye gidan Yaya maryam aka nufa da ita duk da baba balarabe yaso ace gidansa zata zauna, Amma ganin yanda Yaya Maryam d’in ta kafe kai da fata lalle wajenta zata zauna yasa ya haqura tunda itace yayarsa babu yanda zaiyi, Tunda Rashida ta bar gida yaune karo nafarko da taji tana son had’uwa da mijinta wato habibinta mahaifin d’anta Nuraddeen, suna kan hanyarsu ta zuwa gidan Yaya maryam da yake Dr nura ne ya d’aukosu a mota, Fatima na gefensa riqe da little sai Yaya Maryam da aunty marwiyya da ita Rashida abaya, shi kuma baffa mijin Yaya maryam ne ya d’aukosa saman mashin d’insa suka biyo bayansu, takalli aunty marwiyya tace. “Aunty ya nura fa?” Wata uwar harara ta zabga mata had’e da juyar da kanta gefe, ganin haka yasa ta kama bakinta har suka isa gida, Dr nura nayin parking su baba balarabe dake biye dasu na tsayawa da mashin d’insu, Yaya Maryam ce tafara fitowa sannan aunty marwiyya suka nufi cikin gidan, hakama Fatima itama tafito tare da riqo hannun Rashida dake qoqarin fitowa tayi mata jagora sukabi bayansu, A can cikin gida aunty marwiyya tafara fad’a tana fad’in. “Yaya wannan yarinyar batada hankali, kinji tambayar da takwyimun a mota wai ina ya nura? Wlh badon batada lafiya ba da saina d’auketa mari don ko sunan garinsu bana sonji balle sunansa.” “Hmmm banni da ita marwiyya Ina jinta, bi izinillahi ko shikad’ai ya rage namiji aduniya bazata koma gidansa ba, ai tunda haka tafaru to ta tabbata komai mahaifiyarsa zata iya yimata saboda qiyayyar da take yimata kuma mu shedane akan haka, shikenan kuma don muna sakarkari sa mubarta takoma masa a kashe mana ita, narantse kozai mutu sai yasaketa tunda ba ita kad’ai bace macce aduniya ba.” “Wannan shine daidai Yaya Maryam, in yaso yaje can uwarsa ta aura masa wacce take so.” Aunty marwiyya tafad’a a qufule. Tana rufe baki suna shigowa, ta sakarwa Fatima murmushi had’e da cewa. “Wucikke matar Dr.” Batare data kalli inda Rashida take ba. A falo suka shiga suka zazzauna kafin mijin Yaya maryam yashigo shima su Dr da baba balarabe nabiye dashi abaya. Bayan sun zauna Yaya Maryam tamiqe taje takawo masu ruwa da lemuna masu sanyi da ‘yar sauran samosar data had’a da safe da take sayarwa ta ajiye masu, “Balarabe kutab’a wannan kafin kuwuce.” Saida suka fara tab’a hira ana tayiwa little da Fatima ta ajiye tsakar falo yana faman yimasu qyaqya dariya sannan tamiqe taje ta d’ora masu dahuwar taliya da kifin gwangwani ga ‘yar qaramar tukunyar gas cooker d’inta saboda tayi saurin nina, ai kuwa cikin mintotan da basu wuce goma ba ta nina ta zuzzubo a flate ta kawowa kowa, sake d’auko had’ad’d’en zob’onta na siyarwa da takeyi tayi ta kawo masu sannan itama ta zauna tana cin nata, “Kai amma zob’on nan yayi dad’i yaya maryam ya akeyinsa?” Fatima tafad’a tana sake kai cup d’in zob’on abaki. “Kai matar Dr Banda zolaya, zob’on na siyarwa?” “Eh mana, gaskiya kina gyarasa sosai, ai wannan zob’on ko shugaban ‘yan hasada yasha dole ya yabashi balle masu so da gaske.” Dariya duk suka samata harda Rashida da tun d’azu takasa kai koda cokali d’aya abaki sai faman cakularsa takeyi, “Hmmm! Yakamata nabiya kud’in zobonnan tunda yasa madam Santi har na tsinkayo ana yimata waigi.” Dr nura yafad’a yana dariya ganin aunty marwiyya na gyarawa Fatima hilon dake bayanta, juyowa tayi had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Au..Ashe da gaske yakeyi, kai aunty marwiyya zakija yadinga tsokanata kuwa.” Kallon Rashida baba balarabe yayi had’e da d’aure fuska yace. “Ke Rashida maza kici abinci kinji ko?” Ganin bada wasa yakeyi ba yasa tafaracin abincin tana b’ata fuska tamkar wacce keshan magani. Yanda su Dr suka saki jikinsu cikin ‘yan uwan Rashida Kai ka rantse kace Abu d’aya suke ko kuma sun jima da sanin juna, hakan Kuma ba qaramar shaamquwa da yarda ta sake shiga tsakaninsu. Bayan kowa yaci yasha ya qoshi, baba balarabe yayi gyaran murya had’e dayin doguwar addu’a da nasihohi masu ratsa jiki bisa abunda ya faru sannan yarufe dayiwa su dr.nura shida matarsa godiya sosai shida su Yaya Maryam, irin godiyar da suke yimasu da kyawawan addu’o’i had’e da fatan alkhairi har seda suka fara jin kunya, daga qarshe aunty marwiyya tace. “Mungode sosai Fatima matar nura uwar nura, muna roqon Rabbissamawati wal ardi daya azurtaku da ‘ya’yaye nagari masu albarka da zakuyi alfahari dasu duniya da lahira, ALLAH yakareku daga dukknin sharrin abinqi ya lullub’eku da rahamarsa da tausayinsa yayi maku arziqi mai yawa ya share maku dukkanin kukanku.” “Amin ya ALLAH aunty.” Suka amsa cike dajin wani dad’i da sanyi da farinciki azuciyarsu, Itama Rashida hawaye nazubar mata a idanuwa ta rungume fatima tana fad’in. “Dukkanin alqawurranku agareni wanzazzune hakama alkhairanku tabbataccine akaina, karamcinku da halacci masu girmane da mizaninsu yakai girman da bazan iya biyanku aduniya ba, amma har zuwa fitar lumfashina zuciyata da Kuma rouhina cike da qaunarku mai tsanani take, duk wani fitar lumfashi nawa cike yake da fatan alkhairan ALLAH agareku da kuma farinciki mai d’orewa, ina roqonku da kada kucireni acikin rayuwarku kada kumanta dani kubani damar da zan iyaci gaba da rayuwata tare daku matsayin ‘yan uwa batare da zumunci ya yanke a tsakaninmu ba har izuwa ranar da zan kwatanta faranta maku zuciya kamar yanda kuka faranta tawa data ahalina koda sau d’aya ne.” “Bazamu mantaki ba Rashida, bazamu rabu dake da little ba don kunzamo wani yankin daya sama mana farinciki na wani d’an lokaci arayuwarmu wanda muke fatan yatabbata atare damu har abada” Fatima tafad’a itama had’e da rungumeta tana kuka, kuka sukeyi sosai sai kace wud’anda suka rabu kenan har saida Dr nura ya cewa Fatima ta taso sutafi yana mai mamakin yanda shaquwa mai tsanani haka tashiga tsakaninsu a qanqanen lokaci, ‘Daukar little tayi ta sumbacesa agoshi tare da wucewa gaba suka rakosu qin miqasa tayi har saida ta shiga mota Dr nura na Shirin tayarwa sannan ta badashi tana goge qwallan da suka zubo mata, shi kanshi Dr nura saida yaji ba dad’i Amma babu yanda suka iya dole yaja motarsa sukabar wajen. Su kuma yana tafiya rigima ta kaure tsakanin baba balarabe da yace a dole akira Nuraddeen da ahalinsa asaanar dasu yayinda sukuma su aunty marwiyya sukace atafau bazai yuyu ba, daga qarshema Yaya Maryam bugawa Rashida tsatsauran Jan kunne tayi akan karta sake koda mafarkine tayi tunanin zata koma gidan Nuraddeen tunda mahaifiyarsa bata sonta. Shikuwa baba balarabe duk da Yaya Maryam na sama dashi haka yatabbatar mata da cewa dole sai yasanar da Nuraddeen anga matarsa saboda haqqinsane kuma har lokacin tana aqarqashin igiyar aurensa, hakan yasa suka rabu baran baran, rayuwakan kowanensu a b’ace. Yana komawa gida yashiga Kiran lambar baffa data baffa Usman Amma shiru kowace switch up, hakama ta Nuraddeen yakira yafi a qirga itama akashe saboda bai fara anfani da sabon layin daya siya acan. Hakan yasa hankalinsa tashi sosai marece nayi yanufi garin bebeji, yana isa yaci karo da baba Ali ya tsaya yana tambayarsa, sunjima suna magana kafin baba balarabe yabar wajen jikinsa a sanyaye, wata ‘yar iskar dariya baffa Ali yayi sannan yawuce yana fad’in “da sannu duk sai kun gane kurenku har ita wacce sanadiyar b’atanta aka rufemu nida iyalina aka yimana dukan mutuwar da gangar jikinmu takasa d’auka” STORY CONTINUES BELOW  Kwana baba balarabe yayi yana juyi akan abunda baffa Ali ya sanar dashi duk da dai wani b’angaren na zuciyar tasa bai yarda da hakan ba. ••• ••• ••• Su Baffa kuwa a maimakon kwana d’aya da zasuyi agarin sokoto sai da sukayi kwana biyu saboda shawarar da wani likitan yabasu akan sukai marar lafiyarsu kware shine abunda zaifi masu sauqi, hakan yasa suka sake kwana d’aya acan har saida suka gama shirya duk abunda yakamata acan asibitin kware suka biya kud’in da za’a basu mota da jami’an lafiyar da zasu d’aukota sannan suka juyo zuwa gida bayan sun bada address d’in da za’a tura masu motar nan da kwana biyar, gaba d’aya wayoyinsu sun mutu saboda rashin charji da basuda wannan ne dalilin da yasa baba balarabe yayita kiransu bai samu ba. Saida suka iso zamfara don dama motar da zata ajiyesu acan sai daga nan su shiga wacce zata kaisu kano suka shigo kafin motar da suka samu ta kano ta cika suka shiga masallacin dake cikin tashar sukayi sallah sannan suka samu wani saurayi ya ara masu chargarsa sukasa wayar baffa charji, minti talatin sukayi sannan motarsu tacika lokacin baffa har yasamu d’igo biyu a ‘yar wayar tasa qirar kamfanin itel mai madannai. Mintuna biyu yayi da kunnata kiran baba balarabe ya shigo. Cikin natsuwa baffa ya d’aga had’e da amsa sallamar da yayi masa sannan suka shiga gaisawa. “Am dama wata magana naji cewa Nuraddeen yabar qasar nan shine nace bari nakira naji shin ko gaskiya ne.?” Wani irin nauyi baffa yaji Amma bayada wata hanyar da zai iya basa amsar tambayar da yayi data wuce eh ko kuma a’a, tamkar baffa nagabansa ya duqar da kai had’e da cewa. “Eh malan balarabe hakane amma…” Kafin yaqarasa baba balarabe ya katsesa ta hanyar cewa. “To madallah, shikenan nagode.” Had’e da kashe wayarsa, duk inda ransa yake in yayi dubu ya b’aci, Ashe akwai ranar da Nuraddeen zai nuna irin wannan halin ko inkula agaresu adaidai lokacin da suka rasa ‘yarsu a hannunsa, Ashe har yanada qwarin guiwar da zaya iya barin gari acikin yanayin da yake kuma har yatafi batare daya yimasu sallama ba?, Me suka yimasa da suka cancanci haka daga wajensa? Ai koba komai ana bankwan saboda ba’asan halin rai ba, kuma ai yakamata ace ko don kaucewa zargi yazo yayi masu bayani, wud’annan tambayoyi sune suka dinga Kai da komo acikin zuciyarsa da kuma qwaqwalwarsa, rashin samun amsar sune yasake tunzurasa sosai, Ransa ab’ace yanufi gidan Yaya Maryam yakirata tare da zayyane mata duk abunda kefaruwa, dama tayi mamakin ganinsa shida jiya suka rabu baran baran da ita sai gashi har yana fad’in ko mijin Rashida naso ko baya so duk inda yaje dolene ya saketa, kuma dole duk wata alaqa dake tsakaninsu su datseta koda hakan na nufin zasu mayar masa da d’ansa a hannun sane. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/23/2020, 10:36 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___58💎 Shiru Yaya Maryam tayi na tsawon daqiqu uku kafin tace. “Hakan shine daidai, dama abunda nayita qoqarin lurar dakai kenan ka kasa ganewa, to amma batun cewa za’a mayar masu da yaro don yanke duk wata alaqa dake tsakaninmu kabarta don ni gaba d’aya bana buqatar jinmu yakoma zama atare dasu tunda basa da zuciyar imani.” STORY CONTINUES BELOW  Sun jima suna tattaunawa kafin yabar gidan har lokacin yanajin d’aci akan maganganun da baffa Ali yafad’a masa. ••• ••• ••• Baffa nagama waya da malan balarabe yakalli d’an uwan nasa ya sakar masa murmushi cikin qarfin hali sannan ya juyar da kansa gefe, yana maimaita innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun aransa. Dafa kafad’arsa baffa Usman yayi had’e da cewa. “Meke faruwa ne Yaya?” “Abunda Nuraddeen yayi gudun faruwarsa.” Yabashi amsa had’e da juyowa suna fuskantar juna. “Kayi haquri Yaya, dama dole hakan zata faru, mu auna kanmu a matsayinsu mugani, don haka dole zamu lallab’asu har su fahimcemu, ayanayin yanda damuwowi sukayi masu yawa kamarmu, abune mai wahala su iya riqe fushinsu alokacin da sukaji labarin tafiyarsa musamman idan sun jine daga bakin daya kasa yimasu kyakkyawan bayanin da zayasa sufahimta, shi kuwa rashin bayani acikin kowane al’amari shike haifar da husuma da kuma aikin dana sani, don haka dole muyi haquri har zuwa lokacin da zasu fahimcemu.” “Shikenan Usman, amma duk da haka mufara jaraba zuwa wajensa idan mun sauka.” Awa hud’u ta d’aukesu kafin su isa kano, ana ajiyesu tasha suka sake shiga motar da zata kaisu qauyen na yarimawa, cikin qananan daqiqu suka isa sukaci sa’a kuwa yana zaune bakin gida yana arwala suka yimasa sallama, bai amsa ba har saida ya gama arwalarsa ya d’aga kansa sama yayi addu’ar da akeyi bayan gama arwala sannan ya kallesu fuskarsa a sake ba yabo ba fallasa ya amsa masu salamar. “A’a malan Idris, malan Usman sannunku da zuwa yanzu kuke tafe?.” Yafad’a yana qoqarin ajiye butar da yayi arwala agefe, kallon baffa Usman baffa yayi kafin suji ya sake cewa. “Kai Hassan kushiga ciki ku kawo ruwa a butoci magrib taqaraso ana batun tada sallah.” “Am sannunku da zuwa bari naqarasa masallaci kafin ku iso liman na batun tayarwa.” “To shikenan!” Baffa yafad’a cike da mamaki a fuskarsa. Basu sake Shan mamaki ba sai da suka fito sallah suka tarar da tabarma an shimfid’a a qofar gida da kwanonin abinci, “A’a malan Usman ya akayi kukayi tsaitsaye? bisimillah kuzo kuzauna mana, Gaggaisawa suka shigayi kafinsu baffa sufara qoqarin canza maganar izuwa asalin wacce takawosu, Amma ga mamakinsu sai sukaga kawai yajawo kwanoni abinci yana fad’in bisimillah malan idris muci abinci ko.” Babu yanda suka iya saboda yanada matuqar muhimmanci agaresu da bazasu iya yimasa musu ba, wanke hannayen su sukayi sukasa suka fara cin abincin tare har suka qare, Bayan sun kammala, baffa yace. “Don ALLAH malan balarabe kayi haquri ka sauremu, nasan an aikata maku ba daidai ba, amma kuskurene da babu wanda ya isa ya kauce masa, tabbas Nuraddeen yabar qasarnan saidai bada son ransa ba, nine natirsashi ganin yana shirin ruguza rayuwarsa, kuma dama ce wacce yasamu tun kafin wud’annan matsalolin su faru, ganin ba lallai bane ya sake samun wannan damar ba kuma ga yanayin da yake ciki yasa daya tirje akan babu inda zaije saboda yana tsammanin dawowar matarsa garesa wanda abune gaibi akan dawowarta yasa natilasta masa zuwa koya fita daga cikin halin damuwar da yake ciki.” “Hmmm malan Idris kenan!, Ai bance kunyi wani laifi ko kuskure ba, meye laifinku don kunyi qoqarin inganta rayuwar d’anku?, Meye laifinku don kunyi abunda zai sakaku cikin farinciki?, Ba kuda wani laifi don haka kumanta da komai, fatana d’aya muma ALLAH yabamu ikon d’aukar darasin da kuka koyamana muma mu inganta rayuwar ‘ya’yanmu kamar yanda kukayi koma fiye da hakan.?” Duk iya qoqarin da sukayi wajen ganin sun lurar dashi ya fahimci gaskiya hakan ya cutara daga qarshema cewa yayi. “Don ALLAH da girmansa malan usman mubar wannan magana kada tajawo rugujewar sauran mutuncin dake tsakaninmu, d’anku dai ALLAH yabashi ilimi mai albarka mukuma ALLAH yatsare mana ‘yarmu aduk inda take yabata juriyar shanye duk wani abu da zai nemi duqufar mata da farinciki.” STORY CONTINUES BELOW  “Amin” suka amsa masa dashi bayan sun sake bashi haquri sannan suka wuce zukatansu a dagule. Bayan suntafi yakira Yaya Maryam lokacin tana zaune itada Rashida tana bawa little da sai qara wayau yakeyi nono, “Na’am balarabe ya akayi? Duk lafiya dai kuke ko?” “Lafiya klw Yaya, dama iyayen yaronnan mijin Rashida ne sukazo bada haquri….” “Kaga rufemun babinsu bana son ji, ai Ina mumuka haifi aburmu kuma muka bashi aurenta ko! don haka yanzu mun raba, ko suna so ko basa so yazama dole yabawa Rashida takardar ta, bazata koma gidansa ba ko mutuwa zaiyi, shashancin baza da wofi.” Yaya Maryam ta katsesa tana masifa, Wata irin zabura Rashida tayi had’e da miqewa tsaye da kad’an little yafad’i, Yaya Maryam tayi saurin riqosa had’e da kashe wayar tana binta da wani mugun kallo mai cike da tarin tambayoyi, hankalinta atashe takalleta tana fad’in “Mekike fad’a haka gwaggo!,” da yake da haka suke kiran sunanta sannan taci gaba da cewa. “Wai wa ake zancen zai sakeni?, Duk fa iya adadin kwanakinnan dana d’auka zuciyata cike take da mararinsa, idanuwa da kunnuwana cike suke da son ganinsa da kuma jinsa, kawai nayi shirune saboda kada kuga rashin kunyata tayi yawa amma Ina son na had’u da mijina, shine kuma kuke cewa sai ya sakeni?, Meye laifinsa?, Wne zunubin ya aikata da za’ayi yunqurin rabashi da ni?” “Ungo nan marar kunyar yarinya.” Yaya Maryam tafad’a had’e dayi mata daqquwa tanaci gaba da cewa. “Ke wane zunubin kika aikata da uwarsa ta rabaki dashi, kin ganemun shashashar yarinya da batasan ciwon kanta ba, to bari infad’a maki wlh munfiso kimutu atare damu muyi maki sallah murufeki da mumaidaki gidansa uwarsa ta sake halakar mana dake, don haka tunwuri kiciresa aranki matuqar kina son muzauna lafiya dake kinji nafad’a maki.” “Haba gwaggo! Haba gwaggo wannan wani irin tsattsauran hukuncine zakuyi mana, inada yaqini akan tunda wannan jarabawa tasameni shima t yake cikin irin tashi jarabawar, don ALLAH kada kura bamu kodon yaronnan.” Taqarasa maganar tana kallon little dake hannun ita Yaya Maryam d’in had’e da fashewa da kuka, har ga ALLAH Yaya Maryam taji tausayinta, Amma Babu yanda ta iya, wannan ita kad’aice hanyar da zasubi su kub’utar da ‘yarsu daga sharrin uwar mijinta, wacce itama tanacan cikin mummunan yanayin da basuda labari akai, cikin dakewa da qarfin hali tace. “Rashida kawai kuhaqura da juna, yaro kuma Allah shizai rayashi ko bakwa tare don haka kibi umurninmu kizauna lafiya.” Wani kukan ta sake fashewa dashi had’e da durqushewa qasa tana fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, astagfirullah ALLAH natuba kayafemun laifukana, ya ALLAH ka sauqaqamun wud’annan jarabawowin rayuwa kada sufi qarfin zuciyata susa na sab’a maka,” kallon yya matram data kauda kai tana goge ‘yan guntayen hawayen da suka zubo mata tayi. “Gwaggo baifa sakeni ba, taya zaku rabamu?, Karku manta dani harshi zamu iya sake ahiga wani hali idan kuka yimana haka, kunada iko akaina ammashi sam bai kamata kununa iko akansa tahanyar tirsasashi ya sakeni ba.” “Kedai zaki shiga wani halin keda kike ganin bamu isa mutirsasaki akan abunda muke ganin shine alkahiri arayuwarki ba, amma bandashi tunda har ya iya mance awane irin hali zaki shigaba keda abunda ke cikinki ba ya tsallake qasarnan ya tafiyarsa duk da yasan abunda yafaru dake Amma saboda ya gyara rayuwarsa kuma ya farantawa iyayensa yatafi yabarki acan duniyar da bai masan inda kike ba don ya inganta gobensa, ba kekad’ai da ba kyanan ba hatta mu iyayenki da yasan muna nan ya wofantar damu ta hanyar tafiyarsa batare da saninmu ba, wannan shi kike tunanin har zai shiga wani hali idan aka rabaku.? Tir da wannan banzan tunani irin naki” tana gama fad’ar haka tafice d’auke da little da yayi bacci a hannunta STORY CONTINUES BELOW  Tunda tafara magana Rashida ta dasqare a inda take tsaye, shin Anya maganganun da gwaggon tata ke fad’a gaskiya ne ko a’a?, Ko kwanto tashigayi akan cewa habibyn nata zai iya tafiya acikin yanayin da ake na b’atanta kuwa?, Inaaa hakan bazai yuyu ba , tabama kanta amsa had’e da miqewa tana goge hawayenta, dole yau sai tahad’u da mijinta koda hakan na nufin za’a rabata da lumfashinta ne, dole ta qaryata d’ayar zuciyarta dake neman gasgata kalaman da gwaggo tafad’a mata. ‘Dakin da anan ne aka bata tashiga ta d’auko mayafinta da sauri tanufi qofar fita gidan, kota halin qaqa yau tanada buqatar zuwa ta had’u da masoyinta kuma mijinta, sand’a tafarayi gudun kada taganta ta hanata zuwa har ta isa bakin qofar gidan Tana fitowa taci karo da Fatima aqofar gida ita da Dr ya kawota. Cikin farinciki Fatima tarungumeta tana fad’in “‘yar halak ina zakije ne ko kema kinyi kewar tamune kamar yanda mukayi?” Ganin yanda idanuwanta sukayi jajir saboda kukan da tayi yasa Fatima cewa. “Subhanallahi, maman boy meyake faruwa?” Hakan yasa Dr fitowa daga cikin motar yana kallonta had’e da qoqarin rufe marfin motar, qarasowa wajensu yayi kafin yace. “Maman boy lafiya?” Yanda sukaga ta sake fashewa da wani kukan yasa Fatima riqo hannunta zata shiga cikin gidan da ita da sauri taja baya tare da tirjewa. “Don ALLAH uncle ku kaini naga ya Nuraddeen, Ina son ganinsa Ina so nahad’u dashi Amma su baffa sunqi amincewa,” “Kamar ya Rashida?” Dr.nura ya tambayeta cikin rashin sani. “So sukeyi su raba aurena dashi uncle kuma Ina son mijina, bayada laifi, akan abunda yafaru amma gaba d’aya sun kasa fahimtar hakan! don ALLAH ko sau d’ayane kataimaka akaro nabiyu ka had’ani da mijina kamar yanda kahad’ani da iyayena.” Maganar takeyi tana kuka had’e da game hannayenta waje d’aya, Alama yayiwa Fatima dasu shiga motar sannan yajuya shima yashiga had’e da tayarwa, hannunta Fatima tariqa tabud’e gambun bayan motar tasata ciki sannan tarufe itama tashiga yaja motar sukabar qofar gidan, “Ina muka nufa?” Ya tambayeta adaidai lokacin da suka fito qauyen. “Bebeji.” Tabashi amsa ataqaice tana goge hawayen da suka jiqa mata fuska sharkaf, Tafiya mai d’an nisa sukayi kafin su iso gaba d’ayansu Babu wanda kecewa wani uffan, tuqi yakeyi da hannu d’aya, hannun d’aya kuma ya azoshi saman tagar qofar yariqe hab’arsa dashi ita kuma Fatima sai faman jujjuya kwalin wayar dake hannunta takeyi wacce dama itace dalilin zuwan nasu saboda kewarta da tayi mata yawa kullum cikin zancenta ita da little yasa Dr yasiyowa Rashida wayar don suriqa gaisawa sai gashi sun tarar da ita cikin wannan halin. Bini bini take juyowa takalleta cike da tausayi kafin Dr yamiqo mata wayarsa. “Kamomin Yaya maryam” Scrolling contact d’insa ta farayi har takai ga lambar Yaya Maryam da yayi saving da Ya Maryam kano takirata. Bugu d’aya ta d’aga muryarta a hargitse. “Dr.” “Na’am, anwuni lafiya.?” “Lafiya klw, yanzu nake zancen kiranka na nemi Rashida sama ko qasa narasa saboda nayi mata fad’a.” “Karki damu tana tare damu, dama shine kiran dana yimaki.” “Tirqashi Amma wannan yarinyar anyi shashasha, shine zata fita fisabillahi bazata fad’amun ba, gaba d’aya duk tabi ta tayarmun da hankali?.” “Kiyi haquri, Bata kyauta ba gaskiya amma yanzun nan zamu dawo tare in Sha ALLAH.” Kasancewar akwai cikakkiyar yarda tsakaninsu yasa bata damu sosai ba duk da abun ya b’ata mata rai, asalima gaba d’aya ranta bai kawo mata cewa Rashida zatayi tunanin zuwa tahad’u da Nuraddeen ba balle har ta taka da kanta taje garin nasu, STORY CONTINUES BELOW  Koda suka iso angama sallar isha’i suka samu gefen wani shago sukayi parking, Fitowa tayi cikin motar suma suka biyo bayanta har suka iso inda za’a iya hango gidan, “Inane gidan Rashida?” “Wancanne uncle.” Tafad’a tana nuna gidan da yatsa. “To muje ko.” “A’a uncle bazan iya ba, kawai ni shi kad’ai nake son nahad’u dashi.” “Bari to naje nasa ayo mani sallama dashi.,” Yafad’a tare da tunkarar gidan. Tsaye kawai take duk qafafuwanta sunyi sanyi tanaji tamkar basu imata, kallon anguwar takeyi d’aya bayan d’aya, Kafin tahango Yusuf tafe yanufo inda suke gefen wani tsoho dake saida kalanzir saman d’an teburinsa, “Lado abani kalanzir na naira ashirin?” “Ahhh… yusufa d’an gidan yayansa nura, Wai ina yashige ne kwana biyu nadena ganinsa.?” “Laah…ashe lado bakasan yaje qasar waje ba?” “Kai yusufa!, Kace wlh.” “Wlh lado da gaske nakeyi.” “Kai ALLAH ban yarda da kaiba, shi nuran d’an mahaukaciya ne da zaibar qasar nan bayan matarsa da tsohon ciki tab’ata, sai kace wanda bedamu da ita ba,” “To ni kabani kalanzir d’ina kada innar mu tabugeni, ai sai katambyi mutane kaji, yanacan yaje k’aro karatunsa.” “Tirqashi! Amma gaskiya be kyauta ba.” Kukan da Rashida ke qoqarin dannewa ne yaci qarfinta had’e da kucce mata. Da sauri Yusuf daya miqa hannu zai karb’i kalanzir d’in da lado kemiqo masa suka d’ago kai tare jin kukan da suka jiyo agefensu. “Yaa rasulu manzon ALLAH, ke baiwar ALLAH lafiya.?” Lado yafad’a had’e da sakin kalanzir d’in yana kallon Fatima da Rashida dake tsaye hasken k’wan shago na yadosu, da hannu Yusuf ya shiga nuna Rashida don fuskarta bazata tab’a b’oye masa ba aduk inda tashiga, kasa magana yayi sai faman ja da baya yana fad’in. “Aun..aunt..auntyyy..” Yaruga aguje yabar wajen had’e da nufar gida yana k’walawa su baffa…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/24/2020, 10:40 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___59💎 Baffa, baffa, baffa ga aunty tadawo, abunda Yusuf kefad’a kenan har ya isa bakin qofar shiga gida, karo yaci da mahaifin nasa wato baffa Ali shida Dr. nura dake qoqarin barin wajen fuskarsa a cunkushe babu alamun walwala atattare da ita, kad’an yarage Yusuf yafad’i garin kallon Dr nura daya ga yanufi inda su Rashida suke, da sauri ya riqo hannun baffa Ali yana jansa had’e da nufar inda ya gasu Rashida yana nuna masa wajen da hannu, gaba d’aya Yusuf ya rud’e ya manta da cewa ba mahaifinsa yakamata yasan da dawowar taba sanin irin matsayin da take dashi awurinsa. Baffa Ali kuwa binsa yayi har suka isa wajen lado mai kalanzir, lokacin kuwa har su Rashida sunbar wajen saboda irin amsar da Dr nura nura yazo masu da ita, STORY CONTINUES BELOW  “Lado Ina aunty?” “Kai yusuf wace aunty kuma?.” “Haba lado! Anan fa nabarta ita da wata mata, nan wajen!.” Yaqare maganar yana nuna masa inda suka tsaya. “Aiho nan naga sunbi suda wani mutum.” Lado yafad’a yana d’aure ledar daya zubawa wata yarinya kalanzir. Dagudu Yusuf yabi hanyar baffa Ali shima yabi bayansa don yatabbatar da da hakan, Suna kawowa su Rashida naqoqarin shiga mota ya shiga qwala mata kira. “Aunty, auntyyyy..” Juyowa tayi tana goge hawaye harya iso wajen, da sauri baffa Ali yab’oye bayan wani kango yana hangosu don kada taganshi. “Aunty ina zaki tafi kuma, kizo muje gida don ALLAH, ya nura nason ganinki shida su baffa da Inna bilki, kowama nason ganinki munyi kewarki sosai don ALLAH kizo muje kinji aunty.” “Yusuf me zanje inyo agidanku Bayan wanda nazo don shi gaba d’aya yabar qasar, zantafi Kuma bazan sake dawowa acikin gidanku ba saboda bakwa sona.” Tafad’a tana kuka tare da juyawa zata shiga motar, riqe hijab d’inta yayi shima yana kukan yace. “A’a aunty muna sonki don ALLAH kada kitafi.” Hannunta tasa tacire hannunsa daga riqon daya yiwa hijabinta sannan tafad’a cikin motar Dr. Nura yaja sukabar wajen. Kuka Yusuf keyi kamar ransa zai fita had’e da nufar hanyar zuwa gidan baffa, da sauri baffa Ali yafito daga mab’uyar daya shige yatare gabansa had’e da kamo hannunsa, “Kai Yusuf ina zakaje ne acikin daren nan?” Ya tambayesa had’e da d’aure fuska yana kallonsa. Cikin sheshshekar kuka Yusuf yace. “Gidan baffa zanje.” “Kaje kayo ubanmi acan?.” “Zanje infad’a masa Aunty tadawo amma ta tafi kuma tace bazata sake dawowa ba.” Saida ya sakar masa wani mugun ranqwashi akai sannan yace. “To uban waye ya aikeka? idan Auntyn tadawo qanwar uwarka ce kota ubanka da zakaje kasanar dasu tunda tace bazata koma dawowa to meye naka aciki.?” Qoqarin bud’e baki yayi don ya bashi amsa sai Kuma yayi saurin rufewa da hannunsa sanadiyar yanda ya murd’e masa kunne so had’e da cewa. “Karka sake inji kafidda wannan maganar waje kaji nagaya maka, inba haka ba yanda Yaya hawwa ta b’addata kaima haka zansa a b’adda kai, kaga shikenan baka ba ganin kowa naka wata qilama kamutu gaba d’aya ahuta, shashashan yaro kawai, har kamanta akanta akaje aka kullemu ni da mahaifiyarka, babu kalar azaba da kuma dukan da bamu sha ba ahannun ‘yan sanda kuma duk ta dalilinta, to bari kaji duk kasake naji wannan maganar abakin wani sai nayi maka d’an banzan duka kuma wlh kadena cin abincin gidana kenan har kamatu, shegen yaro da bansan halin waye kad’auko ba, maza kawuce gida kafin in jijjimaka anan” Sosai Yusuf ya tsorata dajin kalaman da baffansa ya fad’a masa don haka yanufi gida yana kuka kamar ransa zai fita, kasa shiga d’akin mahaifiyarsa yayi yakoma saman barandar part d’insu ya Nuraddeen dake rufe ya had’a kai d guiwa yanaci gaba da kukansa, tun qarfe takwas yake zune wajen yana kuka har wucewar goma da rabi nadare kan kace me tuni zazzab’i ya taso masa ya fara rawar sanyi, Inna Bilkisu ce tafito zata zagaya bayi tagansa wajen a kwance had’e da cewa. “Kai Yusuf lafiya kazo nan ka kwanta ko sanyin nan bakaji?, Maza tashi kawuce d’aki kar mura takama ka” Ba tare data tsaya sauraren amsar da zai bata ba tawuce bayi don yin lalurar data fiddota, koda tadawo ta tarar har lokacin yana a wajen kwance ko motsawa baiyi ba daga inda tabarshi STORY CONTINUES BELOW  “Ikon ALLAH, wai bakaji me nace maka bane Yusuf.?” Tafad’a tare da qarasawa wajen tana d’agosa, yanda taji jikinsa ya gashe da zafi sai faman rawar sanyi yakeyi yasa tayi saurin rungumosa ajiki tana daddafa kansa. “Subhanallahi, Yusuf dama baka lafiya shine kazo nan ka kwanta.” ‘Dago kansa yayi yana qoqarin yimata magana saiga baffa Ali ya shigo shida baffa Usman, ai yana ganin haka da sauri yaqarasa wajen yana fad’in. “Kai Yusuf mekakeyi wajen? Ko munafuccin ne kaima zaka koya.” Ya zata maganarce yake fad’a mata, Inna Bilkisu najin haka tacire Yusuf daga jikinta had’e da zaunar dashi saman barandar tanufi inda mijinta yake tsaye yana jinjina irin kalaman da d’an uwansa ke alqanta iyalinsa dasu, shi kuwa baffa qiiiii…yaja hannun Yusuf har yana neman fad’uwa yana fad’in. “Wannan yaron anyi mai kunnen qashi, ina dai kasan abunda nace maka shine zakazo nan kasaki baki don rashin jin magana” hed’e da jefasa saman gadonsu d’an bono bayan sun shiga d’aki, ••• ••• ••• Dr kuwa banda tunanin kalaman da baffa yafad’a masa babu abunda yakeyi, wannan wace irin rayuwace muke ciki aduniya?, Wanda ma kayarda dashi alokaci d’aya sai ya sauya maka, ancuci yarinya kuma ankoma ana binta da sharri, a iya saninsa inzai tuna Rashida tafad’a masa cewa mahaifin mijinta na qaunarta Amma sai gashi maganganun daya fad’a masa akanta sunsha banban da irin kalaman daya dace afad’a ga wanda ake so, saita madubinsa yayi yana kallon yanda hawaye ke tsiyayowa daga cikin idanuwanta dake rufe ya saki wata irin ajiyar zuciya, tabbas ta cancanci tayi kuka ba kad’an ba, ko kad’an bazai hanata tayi shiba awannan karon saboda abubuwan sunyi mata yawa, a qaramcin shekarunta bai kamata ace tafuskanci irin wud’annan damuwowin ba donma Allah yataimaka ansamu jininta yakoma normal da tuni qila zuciyarta tabuga, duk da dai bai sanar da ita gaskiyar abunda yafaru tsakaninsa da baffa Ali ba daya nuna masa cewa shine mahaifin Nuraddeen, kawai dai ya fad’a mata cewa ance baya nan yabar qasar. Tare suka shiga gidan da ita lokacin da suka iso yaya Maryam na tsaye tsakar gida tana jijjiga little da sai faman kuka yakeyi tun d’azu. Miqa hannunta tayi ta karb’esa kanta naduqe aqasa batare data bari sun had’a ido da yaya Maryam ba data zuba mata ido tana kallo. ‘Daki tawuce, su kuma suka tsaya suna gaisawa da ita, “Sannu Dr har kin dawo.?” “Eh ya gida yaya Maryam.” “Gida Alhamdulillah Dr, kunbarni da yaro sai faman tsula Mani kuka yakeyi?” Murmushi yayi had’e da cewa. “Afuwan ai gamu mun dawo, dama kwana biyu Fatima tadameni da zancen ta shine nace bari muzo dubata sai gashi munci karo da ita, ganin babu alamun walwala atattare da fuskarta yasa nace bara muje da ita wani wurin taraka mu, I fatar za’ayi mana afuwa bisa wannan kuskuren?” Yafad’i hakanne saboda yasan ran Yaya Maryam b’aci zaiyi idan tasan gaskiyar inda sukaje. “Ba komai Dr, ai kaga Fatima gaisawa kawai mukayi tabi bayansu saboda sukad’ai tadamu dasu” Shiru yayi na tsawon wasu ‘yan sakanni kafin yace. “Amm! Dama yaya maryam cewa nayi yakamata ariqa kwantarwa da Rashida hankali saboda yanayin damuwowin da suka tarar mata azuciya don kar takoma shiga wani halin, nasan kuna qoqari sosai tunda gashi naga cikin kwanakinnan tacanza ba kamar yanda muka zoba saboda yanayin natsuwar da tasamu, amma don ALLAH aqara bata kulawa, sha’aninta akwai bantausayi aciki sosai.” “Ikon ALLAH!, Ai dama nasan dole qara tace zata kai wajenka Dr tunda muna ganin mutuncinka, yakamata ace rashida ta fahimci abunda muke guje mata faruwarsa saidai takasa gane hakan…” STORY CONTINUES BELOW  Nan takwashe komai tafad’a masa akan abunda yafaru ba qari balle ragi, sosai Dr yashiga rud’ani daya auna maganganun guda biyu, da wud’anda baffa yafad’a masa da kuma na yaya Maryam yagano akwai wani abun aqasa wanda ba daidai ba, ko meye kuma ALLAH kad’ai yasani.” Haquri yabata tare da sake roqonta a lallab’ata in Sha ALLAH da sannu zata fahimcesu sannan ya koma bakin motarsa yana jiran fitowar Fatima. Rashida kuwa saida taba little nono yasha ya qoshi Fatima na gefenta tana dad’a bata haquri tare da rarrashinta sannan tamiqa mata shi ta kwanta saman qatuwar katifar dake cikin d’akin nata, anan maganganun da suka faru tsakaninta dashi a daren ranar suka shiga dawo mata a kwakwalwa, tabbas ita ta qarfafa masa yin wannan tafiyar kuma ko kad’an hakan da yayi ba laifi bane, Amma meyasa ya aikata hakan batare daya sanar da iyayenta ba.? Meyasa baiyi tunanin abunda zai iya faruwa ba akan wannan kuskuren da yayi, kamata yayi ace ya fahimci cewa komai na duniya kan iya sauyawa idan aka samu sauyin al’amurra, kama daga ra’ayi, buqata, lafiya, wajen zama da kuma yanayi na yau da kullum, gashi yanzu yaje yabar baya da qura, babbar damuwarta shine rashin sanin har tsawon wane adadin lokaci zai d’auka kafin yadawo. Jitayi Fatima nafad’in “maman boy zamu tafi, yana waje yana jirana, don ALLAH kimaida al-amurranki agaresa kidena kukannan bayada amfani, ga wannan wayace uncle d’inki ya siya maki zamu rinqa magana, akwai lambata da tashi aciki kuma na saka maki ta yaya maryam data aunty marwiyya saiki kirasu, kada kiyarda inkira injita akashe, ko yaushe ina son ki kasance tare da ita kinji ko?.” ‘Daga mata kai tayi sannan tajuya zata tafi tana d’auke da little. “Au! yau babu rakiya maman boy?” Ta juyo tana kallon rashida dake qoqarin tasowa alokacin. Har bakin mota ta rakata tare da yiwa Dr.nura godiya sosai tamiqa mata Little sannan suka wuce… _Darasi: ‘yar uwa ki guji aikata laifi komai qanqantarsa domin bakisan iya adadin mutanen da Zaki iya cutarwa ba ta dalilinsa, wanda hakan kad’ai na iya zamowa dalinlin tsanantar hukuncinki awajen ALLAH, domin shi mai yafe haqqinsane amma banda haqqoqan rayukan da kika cutar, laifi d’aya yaya hawwa ta aikata akan rashida amma mutane da yawa sun cutu adalilinta, ciki kuwa harda qaramin yaro (yusuf) dake fuskantar damuwa da kuma barazana ta dalilin hakan._ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/26/2020, 10:51 PM] FARI’S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___60💎 Tunda Rashida ta tabbatar da cewa Nuraddeen yabar qasar taji gaba d’aya komai na duniya ya tsaya mata, Babu abunda ke mata dad’i haka kuma babu abunda ke burgeta arayuwar duniya, kallo d’aya zakayi mata kafahimci tsantsar damuwar da take ciki saboda yanda duk tabi ta susuce, batada wani aike sai kuka, na safe daban na rana daban hakama na dare daban, duk tabi tarame tayi baqi, rashin iyayenta namatuqar damunta musamman yanzu da take cikin wani hali marar misaltuwa duk da kuwa Yaya maryam da baffa sunyi qoqarin nuna mata sun sauko daga dokin naqin da suka hau saboda yanda sukaga tana nemanfita hayyacinta sai dai aransu ba haka bane. Baffa Usman kuwa da baffa basu san abunda kefaruwa ba , gaba d’aya sun maida hankalinsu kocokom ga nemawa Yaya hawwa magani har zuwa lokacin da aka d’ibar masu nazuwa a d’auketa, ranar nayi misalin qarfe sha biyu na rana motar asibitin ta dira abakin qofar gidansu baffa, lokacin suna tsaitsaye da alamu dama suna jiran dakon isowarsune tun d’azu, wasu ma’aikatan lafiyane su biyar da kuma wani mutum yasha suit, da alama shine babbansu, Saida suka gaisa dasu sannan baffa Usman yayi masu jagora zuwa cikin gidan inda Yaya hawwa take ya bud’e masu d’akin, STORY CONTINUES BELOW  Cikin qwarewar aikinsu suka shiga cikin d’akin yayainda Yaya hawwa tayi wani irin kukan kura tayo kansu. Ba qaramar wahala suka shaba kafin su samu damar rirriqeta tana keta wani irin ihu daya karad’e ko ina tana fizge fizge, sai da sukayi da gaske sannan suka sakata cikin mota suma suka shiga. Wajen motar baffa yatako yana hango ta glass d’in motar yanda jami’an lafiya ke qoqarin yimata allurar da zatasa tayi bacci kafin su isa yasa hannu ya goge k’wallan da suka zubo masa a idanuwansa yana mai addu’ar Allah yabata lafiya, gaban motar ya koma saiti gefen driver inda babbansu yake ya saukar da glass d’in motar yamiqa masa hannu suka sake gaisawa yayi masu godiya sannan motarsu tabar wajen, ahankali dandazon mutanen da suka taru qofar gidan suka fara watsewa cike da tausayin halin da sukaga anfito da Yaya hawwa aciki saboda yanda tayi baqi da rama sosai fiye da tunani, inba wanda yasanta sosai ba bazaka tab’a ganinta kace itace ba. Adai dai lokacin baffa Ali yadawo daga gona rataye da fartanyarsa a kafad’a yana rera ‘yan waqoqinsa, yana hango su baffa Usman ya murtuqe fuska tunkafin ya iso har zai wuce abunsa sai kuma yadawo baya had’e da kallon gungun wasu yara dake tsaye abakin gidan. “Kai me kukeyi anan naga kun had’e kanu kamar d’iyan awaki?” “Wlh Yaya hawwa ce akafito da ita za’a kaita asibitin mahaukata abun gwanin tausayi.” Wani yarone daga cikinsu yafad’a hannunsa na tallab’e da kuncinsa. Batare da baffa Ali yadamu da ‘yan uwansa dake wajen ba yayi tsaki had’e da cewa. “ALLAH yaraka taki gona, ai mun huta da gayyar tsiya kullum ana hanamu bacci ana tsorata iyalinmu da yaranmu,” Juyowa baffa yayi ransa amatuqar b’ace yace. “Karka damu Aliyu, SANNU SANNU ai bata hana zuwa…kamar dai yanda hawwa ke girbar abunda tayi haka kaima zaka girbi naka in alkhairi in kuma sharran.” Guntun tsaki yaja batare daya damu da abunda baffa yace masa ba yashige cikin gida yana cigaba da rera ‘yan waqoqinsa… ••• ••• ••• Kimanin satinsu Dr nura uku kenan da dawowa kano kawo Rashida, wanda sun jima hakanne sanadiyar Fatima data nace akan suyi zamansu sai qarshen wata saisu koma gaba d’aya tunda dama yakusa d’aukar hutu (annual leave), saidai hakan bazai yuyu ba saboda maganin little Nuraddeen da za’a karb’o masa gashi bayason idan yaje qarshen watan yasake dawowa har sai hutunsa yaqare, Hakan yasa cikin satin da zasu koma kafin ranar tazo yayi sakko yaje borno ya karb’owa little maganinsa wanda idan yasha shine naqarshe, Yana isa garin kai tsaye yawuce gidan iyayensa saboda akwai saqon da mahaifiyarsa tace yaje ya karb’owa Fatima na maganin da takesha, Yana isa yatarar da mahaifinsa shima yadawo lokacin yana zaune kan dining table yana cin abinci, qarasawa yayi bakinsa d’auke da sallama yaje ya d’an russuna gabansa had’e da gaishesa. Sake da fuska yamiqa masa hannu yana fad’in. “A’a bokan turawa saukar yaushe?” “Yanzunnan dady, mun sameku lafiya?” “Lafiya klw dady, ya kasuwar.” “Kasuwa Alhamdulillah muna nan muna tattab’awa musanmman sabon shagon dana bud’e, abun Masha ALLAH gaskiya.” “ALLAH yaqaro bud’emai albarka, dady ammie fa?” “Tana ciki, yanzu tabar nan inaga ankirata ne awaya.” Yana rufe baki tana fitowa, babbar mace ce mai cikar zati da kamala, farar mace ce sosai mai yawan fara’a da son mutane, kallo d’aya zakayi mata kafahimci hutu na tattare da ita, da sauri yanufi wajenta had’e da gaishesa, rungumosa tayi ajiki kai kace bashine d’anta nafarin ba suka nufo wajen dadyn tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Oyoyo mutanen kano ta dabo tumbin giwa yaro koda mekazo anfika, Amma inada tabbaci akan ba’afi yaron nawa ba saidai ayi gogayya dashi ko ba haka ba alhaji?” Taqarasa maganar had’e da jawo kujera ta zaunar da Dr nura. Dariya sukasa shida dady kafin yace. “Mezance hajia fareeda tunda kinriga kin fad’a, ai ko ba haka bane ta zauna, uwa da d’anta kome tace akansa ai babu wanda ya isa musa mata.” Suka sake sa dariya. “Son ya hanya da ‘yata Ina fatar kuna lafiya?” “Lafiya klw ammie, tace agaisheki sosai.” “Muna amsawa, injin tana amfani da maganin yanda yakamata? Nasan halinku na ‘yan boko baku fiye ba maganin nan namu na gargajiya muhimmanci ba.?” “Ahh ammie banda Fatima tana kulawa sosai da lokutan shansa yanda yakamata,” “ALLAH sarki baiwar ALLAH, ALLAH yasa adace, yarinyar nabani tausayi sosai, tanada matauqar juriya da haquri wlh, badon haka ba idan irin ‘yan matan nan namu na zamani ne da yanxu tabi ta tayar maka da hankali dama kanta ga abunda Babu mai iya baku sai ALLAH, kuci gaba da haquri, in Sha ALLAH lokaci nazuwa da ijaba zata sauka, muna nan muna yimaku addu’a,” “Hakane nura! Kaci gaba da haquri kana kwantarwa da iyainka hankali, da SANNU ALLAH zai duba lamurranku ya share maku hawayenku, akoda yaushe addu’ar mu natare dake.” “Dady, ammie nagode da kulawar da kuke bamu tare da addu’o’inku, koda ALLAH bai bamu aihuwa ba ku kad’ai kun isa farinciki agareni domin babu abunda yakai samun nagartaccin iyaye aduniya muhimmanci, sune kad’ai farincikin da idan katuna zaya dad’a sanyaya maka zuciya.” Daidai lokacin umma tafito daga kitchen don tagama kammala komai zata koma part d’insu, “umma gafa d’anki da d’azu nake fad’a maki cewa yana kan hanya ya iso.” Dama tuni umma tadawo wajen hajia fareeda da aiki kamar yanda dady ya umurta kuma tanajin dad’in aiki da ita sosai don kusan komai atare sukeyi cikin girmamawa, sab’anin hajia nafeesa da saidai ta nad’e qafafuwa tana bada umurni, murmushi tayi had’e da qarasowa wajen tace. “Sannu da zuwa..” Bata qarasa ba sakamakon juyowar da yayi suka had’a ido, cikin i’ina tace. “Kaine?” “A’a baba kece anan kuma.?” Yafad’a yana nuna baba da hannu, binsu da kallo su ammie sukayi cike da mamakin ganin sunsan juna, nan Dr nura yabasu labarin ynda yasanta har yana qarawa da tambayarta cewa. “Baba ina wanda naganku tare.” “Yana can shagon da alhaji yabashi yariqa kulawa dashi, ai shi d’in mijinane” Tafad’a akunyace tare da komawa kitchen, Dariya su dady sukayi kafin sushiga bashi labarin zuwansu ataqaice amma basu fad’a masa cewa sanadiyar b’atan ‘yarsu sukazo garin ba. Dawowa tayi d’auke da wani qaton try da suka shirya masa abincin da yafiso ita da ammie wato tuwon semolina da miyar kub’ewa d’anye, da sauri ammie taje tariqo mata tana fad’in. “Kai umma ai dabari kikayi nazo na d’auko masa.” Sannan ta ajiye abincin agabansa, yana bud’awa yaga best food d’insa ba shiri yature jikkar gabansa yana qoqarin fara zubawa yaci, d’an mangararsa ammie tayi aqeyar kai tana fad’in. “Bazaka bari kafara watso ruwa ba.?” “Awshh….ammie bara nagama cin abinci tukuna, ALLAH yawuna har sun tsinke.” Yafad’a yana shafa inda ta mangaresa, dariya umma dake tsaye tana kallonsu cike da burgewa tayi tana goge ‘yan hawayen da suka zubo mata tunawa da tata ‘yar sannan tabar wajen. STORY CONTINUES BELOW  Bayan ya kammala cin abincinsa yaje ya watso ruwa sannan yaje wajen hajia nafeesa matar babansa ya gaisheta daga can kuma yawuce wajen malamin da yake karb’o maganin Little Nuraddeen awajensa ya karb’o sannan yadawo gida lokacin kusan qarfe biyu na rana yawuce kai tsaye d’akin ammie tana zaune tana tilawar alqur’ani, Saida takai aya sannan tarufe taje ta d’auko wata leda cikin drower d’in madubi tadawo inda yake zaune gefen bedside d’inta ita kuma ta zauna agefen gado. “Ungo wannan ka kaimata, don ALLAH kace takula da shansa tunda safe kafin taci komai, shi wannan ganyen koba don haihuwa ba yanada kyau adinga tafasashi ana sha da ruwan tea kafin aci komai da safe, yana wanke duk wata datti dake cikin jikin mutum har zuwa mara, hakama yana wanke dattin mahaifa sosai, hatta wannan tumbin da kake ganin kafara azawa idan kuna shansa tare zaya rage sosai, don haka kukula, shi magani da kuke gani dace ne bamusan ta ina ALLAH zaisa adace ba, ALLAH yabamu rayayyi masu albarka.” “Amin ammie, amma shi wannan ganyen mene ammie?” “Ganyen guava ne.” “Guava fa kikace ammie!, Wannan guava dai dana sani.” “Eh mana, Ina tabbatar maki idan kuka gane shan tea da ita, bazaku tab’a bari ya tsinke maku va agida, da kanku zaku kirani kusanar dani amfanin da kukaji tayi maku ajiki.” “To ammie shikenan mungode.” “Yawwa ALLAH yayi albarka kuma yakiyaye hanya.” “Amin ngd.” Yafad’a had’e da miqewa ya kama hanyar komawa kano bayan yayi sallama da mahaifinsa. ••• ••• ••• Kimanin kwanaki uku Yusuf ya d’auka kwance yana fama da zazzab’i, baya fita ko ina daga d’aki sai d’aki har ALLAH yasa yasamu sauqi, baffansa nafita zuwa gona ya iske baba Usman a d’aki yana shiryawa zaije gidan baffa zasu koma wajen baba balarabe su sake bashi haquri akan abunda yafaru, dama Inna ruqayya tafita anguwa Inna Bilkisu kuwa tana waje tana share wajen dabbobinta da yayi datti, baffa Usman na gyara zaman hularsa akai yaji anriqo rigarsa, juyowa yayi had’e da cewa. “A’a Yusuf ka taso? Yajikin naka da sauqi ko?” “Eh baffa Usman naji sauqi sosai.” “Masha ALLAH, ALLAH yaqara sauqi , to ya akayi ne.” Duba gefe da gefe yayi sannan ya leqa ta qofar shigowa d’aki yaga ba kowa ya matso dab da inda baffa yake zaune a gefen gado a kunnensa yace. “Baffa aunty Rashida matar ya nura tadawo, naganta da idona Amma karka gayawa baffana.” A razane baffa Usman yamiqe had’e da cewa. “Kai Yusuf bana son shashanci, a Ina kaganta ne?” Hannu Yusuf yasa had’e da rufe baki yana qwalalo idanuwa ya juya yana kallon qofa, Furzar da iska baffa Usman yayi had’e da kwantar da hankalinsa ya matso inda Yusuf ya dafa kafad’unsa. “Yusuf ka kwantar da hankalinka, Babu wanda zaiji kaji ko?, Yimun bayani a Ina kaganeta.” “Bana son baffana yaji yace idan nafad’a nima zai b’addani kuma bazai sake bani abinci ba.” “Bazaiji ba nayi maka alqawari kaji ko?” Nan Yusuf yayiwa bayanin baffa komai had’e da roqonsa don ALLAH kada yafad’awa baffansa shi yafad’a masa, jikinsa na rawa yabar d’akin shima baffa Usman jikinsa asanyaye yabar gidan yanufi wajen baffa yayi masa bayanin abunda Yusuf yafad’a masa, yayi matuqar shan mamakin cewa wai har yanzu baffa ali na adawa da Rashida, tsanar da yakeyi masu har takai girman da zai sake cillasu awata damuwar, tare suka fito suka nufi gidan lado mai kalanzir suka tambayesa abunda yafaru ranar tsakaninsa da Yusuf na zancen ganin matar da Yusuf ya tabbatar masu da cewa Rashida ce. Sun samu amsa daidai da zancen Yusuf don haka ba b’ata lokaci suka nufi gidan baba balarabe. Sai yanzu baffa yasake fahimtar dalilin fushin da baba balarabe yayi sosai, ya tabbata akwai maganganu da baffa Ali yafad’a masa marasa dad’i wud’anda sune suka tunzurasa, haqiqa ko shine malan balarabe zai d’au zafi fiyema da hakan domin d’a baifi d’a ba. Duk qoqarin da yakamata su baffa suyi wajen yiwa baba balarabe bayani yanda zai fahimci komai sunyi amma gaba d’aya Sam yaqi saurararsu balle yafahimce su, da suka d’auko masa zancen ganin Rashi da akace anyi kuwa buga kai yayi ga qasa yace shi baima san da zancen ba, Dole suka haqura suka koma gida, kusan ko yaushe cikin kiransa suke awaya da isko shi gida suna son tabbar da zancen amma ko kad’an yaqi barin hanya ko kad’ance da zasu iya gane hakan, musamman suka turo abokanansu da mutanen da suke da kima abashi haquri ko zai sauko yafad’a masu cewa Rashi tadawo. Amma baba balarabe yakafe akan bashida masaniyar hakan, ayanayin yanda yake sakin fuska da tarbar wud’anda suke turowa yasa bazasuqi amincewa da zancensa ba, gaba d’aya baffa yasake shiga damuwa har ya soma ramewa. A kullum bayada lokacin kansa saina bin hanyar zuwa gidan baba balarabe, baya can baya gidan Yaya Maryam, hakama aunty marwiyya, duk inda yake sa ran zai samu tabbacin labarin zuwan Rashida yana biye dashi Amma k sunqi bud’e baki sufad’a masa gaskiya. Duk zafin da aunty marwiyya ta d’auka akan maganar saida yasoma bata tausayi saboda irin yanda taga yana kaida komo gidanta shida d’an uwansa kawai saboda su sani ko Rashida ta dawo amma idan ta tuna cewa fada masu shine zai sake zamowa silar da Rashida zata koma acikin ahalinsu da Babu zuciyar tausayi ko Imani atattare da wasunsu sai taji zuciyarta ta karye, musamman idan ta tuna da rashin ‘yar uwarta da tayi akusa da ita ta dalilin haka. Ganin irin kai da komowar da baffa keyi a tsakankanin gidajen nasu su uku yasa suka yanke shawarar had’a Rashida dasu Dr nura su koma da ita acan borno domin hakan shi zai fimasu kwanciyar hankali tunda sunsan inda take, koba komai itama zata d’an rage damuwar da take ciki tunda har yau taqi sakin jiki kullum cikin qunci take. Wata nakaiwa qarshe Dr nura sunzo yimasu bankwana yaya maryam takira baba balarabe da aunty marwiyya suka roqesa akan buqatarsu tasu koma da Rashi acan yafi masu kwanciyar hankali indai hakan bazai zamo takurawa agaresu ba har zuwa lokacin da ALLAH zai qaddari dawowar iyayenta, Sun matuqar jin dad’i yanda suka basu yarda haka tare da amice masu akan ‘yar tasu duk da babu wata alaqa inbata musulunci ba a tsakaninsu musamman Fatima da tunkafin Dr nura ya amsa cewa sun amince tace. “Babu wata matsala sun amince ba komai.” Har tana karb’ar little a hannun aunty marwiyya cike da farinciki. Rashida kuwa babu yanda ta iya domin ta dad’e da tabbatarwa kanta da cewa batada wani sauran iko akanta tunda tarasa iyayenta akusa da ita, komai yanzu sai yanda akayi da ita, sunjima agidan kafin Yaya maryam taje ta har had’o mata kayanta dana little, aranar ma Rashida tasha kukan rashin iyayenta sosai tare da fawwala dukanin al’amurranta ga ALLAH tana mai addu’ar ALLAH yasa wannan qaddarar da zata d’auketa ta maidata garin da tabaro tazame mata alkhairi, ahalin yanzu ko kad’an bata ganin laifin tafiyar Nuraddeen, saidai takanji wani irin zafi da qunci azuciyarta Idan ta tuna dashi wanda batasan dalilin faruwar hakan ba. Haka sukayita bata baki da rarrashinta sannan suka d’auki hanyar komawa borno ita dasu Dr. Gidan iyayenta kuwa tuni Yaya Maryam da baba balarabe suka yanke shawarar saka ‘yan haya aciki kafin randa ALLAH zai dawo dasu sai suna jujjuya masu kud’in… Pls comment, vote and share👏 *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___61💎 Ba qaramar rawar gani Dr nura da Fatima ke takawa ba wajen kula da farinciki da kuma walwalar Rashida ba ita da d’anta, duk wani abu da take buqata basa bari har saita kai ga furta cewa tana so suke yimata, mutanene su day sukasan haqqin zaman takewa da kuma sanin kimar d’an Adam, ko kad’an abunsu baya rufe masu idanuwa balle ya had’a ka dasu, sosai suka nuna mata cewa dasu da ita duk abu d’aya ne babu wani banbanci don haka tanada ‘yancin tayi rayuwarta yanda takeso acikin gidan ita da yaronta matuqar hakan bai sab’awa musulunci ba.+ Hakan yasa tafara sakewa kamar yanda suke buqata saboda taga tasasu farinciki yanda suke qoqarin sata itama. Sunada sati d’aya da dawowa Dr nura yaje ya sanar da iyayensa batun zaman Rashida agidansa da irin taimakon da yayi mata wanda daga qarshe har danginta suka roqesa akan tazauna wajensu nawani d’an lokaci kafin ALLAH yadawo da mijinta lafiya. Sun jinjina al-amarin sosai har ammie nayi masa fad’an meyasa tun farkon faruwar al’amarin bai sanar dasu ba sai yanzu, gashi sanadiyar banzar tunaninsa ya haifar mata da rasa iyayenta wanda da ansanar dasu dawuri da duk haka bata faru ba, haquri yabata tare da fad’a mata iya qoqarin yin hakan da yayi alokacin amma ALLAH beyarda ba sanadiyar wannan rubutacciyar qaddarar daya tsaro masu. Dady kuwa tunda Dr yafara bada labarin yake ganin kamancece niyarsa da nasu umma duk da dai bakomai yafad’a masu ba, jin dayayi Dr nura ya ambaci cewa ita mijin nata na qasar waje yaje karatu yasa ya janye hankalinsa daga wannan tunanin, a tsammaninsa ma yarinyar ‘yar masu kud’ice don haka sai dai kawai ya nuna masa yanda yaji dad’in taimakon da yayi da kuma qara qarfafa masa wajen sanin kima da kuma darajar d’an Adam, ya sake horonsa akan ya taimaki duk wani mabuqaci shima ALLAH zai taimakesa domin shi alkhairi aduk inda kayishi to tabbas zai biyoka aduk inda kake. Haka ammie itama ta sake gargad’insa akan yariqa sanar dasu duk wani abu dayasan yinsa zai iya basa wata matsala ko akasin haka saboda suriqa bashi shawarwarin daya kamata harma da taimako idan akwai buqatar yin hakan, yadena yin gaban kansa akan wasu abubuwa matuqar suna raye dominsu har yanzu yaro yake agaresu, ya matuqar jin dad’in nasihohin da suka yimasa kafin yayi madu sallama yawuce gida suna masu sanya masa albarka da addu’ar ALLAH ya albarkacesa da zuri’a d’ayyaba. Zama mai cike da girmamawa da kuma mutunta juna ke tsakaninsu da Rashida, basuda matsala da ita haka itama batada wata matsala dasu, rayuwarsu sukeyi mai tsabta inganci da kuma nagarta har little Nuraddeen ya cika wata goma aduniya lokacin har yafara takawa Babu inda bai zuwa, yayi wayau sosai gwanin ban sha’awa dashi ga surutu, koda yafara iya magana da gwaggo yake kiran Rashida saboda sunan da yaji ana kiran mai aikin gidan dashi kenan sai yazata itama sunanta kenan yake kiranta dashi, Amma yanayin shaquwa da sabon da yayi da Fatima ita mama yake kiranta shi kuma Dr da Abba yake kiransa saboda tunda suka dawo kusan duka renonsa a hannunsa yakoma, iyakar Rashida dashi bashi nono sai wasu lokutta da idan uzuri ya gittowa Fatima sai tayi masa wanka da gyarashi, hatta bacci wani lokacin awajensu yakeyi ataqaice duk wata kulawa daya dace uwaye suyiwa ‘ya’yansu su suke yimasa, kallo d’aya zakayi masa kasan d’an d’an ‘yan gayune saboda irin gyaran da yake samu daga wajensu, wata irin mahaukaciyar soyayya sukeyi marar misaltuwa daga shi har mahaifiyarsa, idanko zasu fita sau goma ayini yadinga ihu kenan yana zallo har sai sun tafi dashi, ita abun har mamaki yake bata don ba qaramin shaquwa yayi dasu ba, Babu abunda ma yafi bata mamaki irin kud’in da suke kashikke masa aduk lokacin da suka fita dashi sai take tunanin kamar tad’ora masu hidima sosai akansa, lokacin data roqesu surage yimasu hidima kada abun yayi yawa nan take suka b’ata rai had’e da nuna mata rashin jin dad’insu akan haka, dole tabasu haquri taci gaba da yimasu addu’a suma ALLAH yakawo masu nasu ‘ya’yan masu albarka kusa kusa kamar yanda tasaba akoda yaushe. STORY CONTINUES BELOW  Hakama dady da ammie suna matuqar son yaron sosai don duk lokacin da Dr zasuje tare suke zuwa dashi, shi kuma baba randa yafara ganin yaron saida gabansa yafad’i saboda yanda ya hango tsantsar kamarsa da ‘yarsa da kuma ummanta atare dashi, yadad’e yana tunanin anya wannan yaron ba jininsa bane kuwa?, Amma sanin cewa jikane ga alhaji tunda baisan alaqar dake tsakanin yaron da kuma Dr ba yasa yakama bakinsa yayi shiru daga bayama sai yashiga tambayar kansa taya hakan zai faru tunda yasan kosu waye iyayen yaron?.duk lokacin daya ga yaron sai yaji gabansa na tsananta fad’uwa, ji yake tamkar Rashidarsa ce hakan yasa yafara qoqarin jan yaron ajiki, Dady ma ranar daya ga little kai tsaye yacewa ammie yana kama da umma tayi dariya had’e da cewa. “Ikon ALLAH dama haka abun yake, qila idan anyo taliyo yanada alaqa da ita tunda dama mutane ‘yan uwan junane idan an bincika.” Basu wani d’auki maganar da muhimmanci ba shiyasa suka barta abakin nan batare da tayi tsayi ba. Yau da misalin qarfe biyar na marece Fatima tafito riqe da hannun little suna takawa ahankali kamar yanda take tafiya yasha manyan kayansa irin na cikakkun hausawa hadda babbar riga da hannuwa masu clips kai karantse kace babban mutumne, kansa saye da ‘yar madaidaiciyar hula irin mai qube d’innan da takalma have cover yayi matuqar kyau sosai har yagaji, murmushi Rashida tayi had’e da cewa Masha ALLAH aranta kafin tace “Haba aunty, uncle fa nawaje yana jira kin tsaya biyewa tafiyar wannan yaron da sai magrib tawuce baku qaraso ba,” “Eh munji dai, ai SANNU SANNU bata hana zuwa ko my boy.” Taqarasa maganar had’e da d’aukeshi sannan taqaraso wajen tana d’agawa Rashida gira tana dariya had’e da kallon little tace. “To ya kikaga yarona?.” “Ba kyau, kuma am jealous.” Rashida tabata amsa had’e da wucewa gaba tana dariya. “Lallai ma maman boy, kawai kice dai jealous d’inne yahana kiga zallar kyan dake zuba anan.?” Saida suka iso suka shiga cikin motar sannan itama Rashida ta shiga sukabar qofar gidan, bayan sun hau titi sunfara tafiya Dr nura ya kalli Fatima yanda tayi kyau ita da little tamkar ace d’anta ne yace. “Wow..Masha ALLAH, matar yau kincini tukuici, wannan wankan na takwara dole yahau Instagram, yaro sai kace donsa aka halitto kayan nan na hausawa, gaskiya badon kar ace nayi sonkai da yawa ba da nace maman boy kinfi kowace uwa azamanin nan dacewa da kyakkyawan yaro kamar takwarana.” “Kai uncle to ai wannan zancen naka ga mamansa nan azaune ita kad’ai zata iya fahimtarsa amma nikam yanzu haka nahango yaron daya fishi kyau da komai akan titin nan.” “Jealousy jealousy..” Fatima tafad’a tana dariya. “Yawwa maman boy yaufa wajen su ammie zan kaiki kugaisa, tun satin can take cewa na kaiki wajensu kugaisa amma ko yaushe sai namanta saboda abubuwa da sukayi mani yawa, Yauma matar ce tatuna mani ganin Ina shirin tafiya can nida takwara shine nace tafad’a maki kigyara sai muje gaba d’aya, Ina fatan bamu takuraki ba ko?” “Laaa..uncle wace irin takurawa, ai nima matsayin iyaye suke agareni kuma kamata yayi ace tuntuni nayi wannan tunanin na zuwa nagaishesu lura da irin saqon gaisuwar da akoda yaushe suke aiko mana dashi amma rashin kammaluwar cikakken tunani irin nawa yasa nakasa yin hakan, babu komai kuma naji dad’i sosai koba komai naje naga mahaifiyar da tayi sa’ar samun nagartaccin ‘ya’yaye kamarku, inada yaqini akan cewa tafi kowa sa’ar samun surukar qwarai irin aunty Fatima kuma nasan tana alfahari da ita sosai. “Hakane maman boy, mahaifiyata nason Fatima fiye da son da takeyimun, a kullum tana fad’a cewa itace cikar farincikin mu kuma hasken gidana.” Yaqare maganar yana kallon Fatima data qura masa idanuwa had’e da d’aga mata gira. STORY CONTINUES BELOW  Haka sukayita firarsu har suka isa qofar gidan wanda yayi daidai da shigowar baba yanufi sashen da aka basu. ••• ••• ••• Baffa kam tuni yagama haqura tare da fitar da rai akan komai, yanzu tunaninsa gaba d’aya yakoma akan d’ansa da tunda yatafi baya samunsa awaya kuma shi bai kiraba gashi yanzu kimanin watanni bakwai kenan da tafiyarsa, Ganin baffa na neman shiga wata damuwar yasa baffa Usman yakoma wajen iyayen matarsa Inna Bilkisu akan zancen auren ‘yar yayarta da akayi da baffa mai suna nusaiba, nan take aka fara shire shiren biki nan da sati mai zuwa, fenti marar tsada baffa Usman ya siyo don yanzu bashida isashshin kud’ad’en a hannunsa saboda lalurorin da sukayita fuskanta yasa akaje akayowa baffa awancan gidan inda yake zaune lokacin yana kasuwa, koda yadawo yatarar da anyi fenti kuma anmaida komai yanda yake ya tambayi baffa Usman yafad’a masa cewa ai zancen auren sane yatashi, tabbas yasan yanada buqatar natsuwa ahalin yanzu saidai bayada tunanin ta inda natsuwar zata zo masa, dole yana buqatar taimako takowace irin fuska don haka dole yasawa d’an uwansa ido yayi abunda yakamata wataqil hakan shine zai sama masa natsuwa. Inna Bilkisu kuwa ‘yan kud’in adashinta data karb’a tayiwa baffa magana yaqara mata wasu duk da kuwa basuda yawa tasa aka sawo mata akwati d’an madaidaici ta sayi atamfuna guda biyar masu sauqin kud’i da leshi d’aya mai d’an kyau da takalma kala d’aya da jikka d’aya sai hijab da mayafi shima qwaya d’ai d’aya, foda, turare, sabulu da ‘yan sauran kwantsammai da basu taka kara suka kawo ba daidai gwargwado irin kayan auren da aka sani anayi aqauye takai amatsayin lefen da baffa yayiwa yarinyar. Duk da kayan basuda yawa an amshesu hannu biyu cike da farinciki anata saka albarka. Baffa Ali kuwa da Inna ruqayya yanda kukasan auren da baffa zaiyi abun kunyane haka sukabi gari duk inda suka zauna basuda tsogumin daya wuce wai baffa zai auri qaramar yarinya tsofai tsofai dashi don abun kunya bai isheshi ba, haka sukayita yad’a wannan maganar har ta zagaye garin, yayinda wasu ke kallon abun ba wani abune tunda ansaba yin hakan a qauyen wasu kuma suke kallon auren amatsayin abun kunyane agaresa. Wannan dalilin yasa ranar d’aurin auren d’aruruwan mutane na qauyen da kewayensa suka halarci taron d’aurin auren bisa sadaki naira dubu ashirin laqadan ba ajalan ba, Sosai innna Bilkisu da iyayenta sukayiwa yarinya kayan d’aki daidai arziqinsu kuma suka yima baffa hidima sosai don fitar da ita kunya. Bayan angama d’aurin auren aka wuce gidansu baffa usman inda yahad’a ‘yar qwarya qwaryar walima, abincine jalop da sob’o yasa Inna Bilkisu da qawayenta na mutunci suka dafa ‘yan d’aurin auren kowa yaci ya sha yaqoshi sannan suka kama gabansu suna masuyiwa baffa addu’a da fatar ALLAH yazaunar dasu lafiya yabasu zuri’a masu albarka… Acan cikin gida kuwa Inna ruqayya sai gud’a takeyi tana yadawa Inna Bilkisu magana wai anyi abun kunya an aurarwa da ‘ya mijin kishin sauri, da dai sauran suruttan da no zasu iya tunzurata, amma taqyaleta ko cikanki bata cemata ba, dama dai munduwa biyu ka amo.. Bayan anyi sallar la’asar mutanen dake zoma Inna Bilkisu sun watse tajawo d’akinta tarufe sannan taje qofar rumfar Inna ruqayya yace. “To uwar muneera kizo mutafi yowa yayan mijinki bikon amaryarsa, duk da dai nasan zallar kishi bazai barku ba qaramar yarinya ta aure maki wan miji kuma ko ba’aso dole abata girmanta idan ansan girman manya sai akirata da matar Yaya ko kuma Yaya nusaiba. Tana gama fad’ar haka tafice tabar Inna ruqayya tana d’ura ashar tare da kumfar baki. Ana gama sallar magrib ‘yan kai amarya suka raka nusaiba har gidan mijinta dake can farkon gari Inna Bilkisu nariqe da hannunta sai faman kuka takeyi, nasiha tasake yimata sosai sannan suka baro gidan yarage daga ita sai Aisha yarinyar baffa Usman da yusuf, suma Inna Bilkisu tace da zaran baffansu yadawo sudawo gida. Shikuwa baffa tunda aka gama sallar magrib yayi zaunensa masallaci yakasa motsawa ko nan da can, juya al’amarin kawai yakeyi a k’wakwalwarsa wai yau shine da sakeyin aure bayan tsawon shekaru kusan talatin da wani abu da aurensa na farko, abunda ko amafarki bi tab’a kawowa aransa ba. Baffa Usman na kalle dashi tun d’azu har akayi kiran sallar isha’i, tare sukabi jam’i har aka gama baffa yasake komawa inda yake zaune d’azu ya zauna yana tunani. “Ikon ALLAH, Yaya a Ina katab’a ganin ango ya zauna yana tunani haka?, Don ALLAH katashi katafi wajen matarka nasan yanzu haka tana can zaune ita kad’ai.” “Usman wlh abunnan nauyinsa nakeji, sai naga kamar maganar dasu Aliyu kefad’a gaskiya ce, wlh abunne da kunya sosai.” “ALLAH ne yahana?” “Ko kad’an.” “To donme kake jin nauyi ga abunda ALLAH ya halasta maka?, Katashi katafi matuqar baso kakeyi tun yau kafara d’aukar haqqoqan amanar yarinyar mutane da aka baka ba.” Shiru baffa yayi kafin yamiqe ya rungumesa yana fad’in. “Nagode d’an uwana, kayi Mani sutura kala kala arayuwa da bazan iya saka maka ba, a matsayinka na qane agareni kazamemani uba kuma aboki acikin rayuwa, ya ALLAH ka kula da dukkanin al’amurranka dana iyalanka ya shirya mana d’an uwanmu shima yayi maka fiye da abunda kayi mani.” “Amin Yaya, ai wannan shi d’inne ake kira da zumunci, allah yabamu ikon cigaba da haquri da juna.” Shi yarakasa har gida sannan ya juya batare daya shiga ba yana yimasa Saida safe, yana shiga suma su Aisha d Yusuf suka gaishesa tare da yimasa saida safe suka nufi gida.. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭[8/29/2020, 4:20 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Thank you guz for d warmest comment you did on a previous page, all jazakumullahu bikhair, fillah i feel so much appy💃🏼bless to be with you & always proudly to have you🥰_ Page___62💎 Yajima tsaye abakin qofar d’akin kafin ya tattaro d’an sauran kuzarin dake jikinsa had’e da tira qofar d’akin sannan yashiga bakinsa d’auke da sallama. A tsakiyar gado ya hango yarinyar kwance ta lullub’e da alama bacci ya soma d’aukarta ya qarasa wajen yana qara rafka wata sallamar da d’an be qarfi tayanda zatajishi,+ Cikin yanayin baccin dake cinta ta tashi da sauri tana murtsuka idanuwa had’e da amsa sallamarsa, kasancewar akwai hasken wutar lantarki a d’akin yasa baffa qura mata idanuwa yana kallon irin kyawon da ALLAH yayi mata, kallo d’aya zaka yimata ka tsinkayo asalin kyawo ‘ya’yan fulani dake tattare da ita, farace tas dake da dogon hanci da kuma manyan idanuwa farare tas da suka d’an zurma d’auke da zara zaran gashi a samansu sai kuma yalwataccen gashin girar daya kwanta luf asaman idanuwannata, bakinta kuwa d’an qaramine dake d’auke jajayen labb’a masu matuqar d’aukar hankali, tanada lotsawa a gefen bakinta(dimple) musamman idan tayi dariya wanda shike qara fitar da tsantsara kyannata, ataqaice dai tubarkallah masha ALLAH amaryar baffa sai sambarka, batada wani tsayi ko girman jiki daya d’ara qananun shekarunta don haka dole baffa yayi mamakin qanqancinta a kansa. Ganin yayi tsaye ya kasa qarasowa inda take yasa ta sauko daga saman gadon tare da takawa zuwa inda yake ta durqusa tana fad’in. “Ina wuni baffa?.” Wani irin murmushine ya kuccema baffa da yasa haqoransa bayyana a lokaci d’aya yasa hannu ya d’agota daga duqen da take gabansa ya zaunar a bakin gadon sannan shima ya zaune gefenta had’e da cewa. “Lafiya klw nusaiba, bakiyi bcci ba.” “Nafarayi sallamarka ta tasheni.” Tafad’a tana murza d’ayar ijiyarta. Shiru yayi na tsawon wasu mintuna kafin can yajuyo qafarsa d’aya akan gadon itama yajuyo da ita suna fuskantar juna. “Nusaiba kinsan ya nake dake?” Yafad’a yana kallonta, saida tad’anyi jim sannan tace. “Yakumbo tace matsayin uba kake awajena ingirmamaka hakama kaka dasu baffa sunce kai shugabana ne inyi maka biyayya.” ‘yar dariya yayi don yafahimci metake nufi, anyimata nasihane data girmamasa saboda dattijantakarsa ta isa ya haifeta komanta zarta haka, sannan annuna mata shugaba take awajenta kasancewarsa mijinta wanda hakan zaisa dole tayi masa biyayya, wannan wata hikimace da nagartaccin iyaye keyi don d’ora ‘ya’yayensu bisa turbar yin bautar gidan aure cikin ladabi da biyayya da koma girmama maigida, aransa yaji cewa tabbas yayi sa’ar nagartaccin ahalin mata awannan karon. Ajiyar zuciya yayi sannan yaciga da tambayarta cewa. “Me ake nufi da shugaba a gidan aure nusaiba?” “Mijin gidan.” tabashi amsa hankalinta kwance. Yanda take amsa tambayoyin nasa cike da yarinta duk da dai tana fad’a daidai yasa yaqara gasgata qanqantarta don haka yaci gaba da tambayarta akan abunda yashafi karatun addini, kama daga tsarki da kashe kashensa, arwala, farillai, sunnoni da kuma mustahabbanta, yanda ake sallah da abubuwan data qunsa, wanka da kashe kashensa, banbancin Haram da halat acikin rayuwar auratayya duka saida ya tambayeta, yayinda kashi cas’in da twakwas bisa d’ari batasan komai ba sai ‘yan qalilan daga ciki musamman ta b’angaren wanka, anan baffa ya fahimci cewa akwai aiki gabansa don dole tasan wud’annan abubuwan kafin komai yashiga tsakaninsa da ita, koba komai zuwa lokacin tasaba dashi kuma taqara sanin ko meye matsayinsa awajenta. STORY CONTINUES BELOW  Yana wannan tunanin ne yaji anbubbugo qofar gida yamiqe had’e da ficewa yabar d’akin dama yanzu yake zancen zuwa yarufe don har qarfe goma tayi. Yana zuwa yatarar baffa Usman ne a qofar gidan riqe da ledoji a hannunsa ya miqo masa yana fad’in. “Yaya aini namanta da tsiren amarya har sai dana kwanta kuma nasan baka shiga da komai ba shiyasa nace Bari nafitu nan anguwarmu wajen habule mai nama inkarb’o maka tunda anan dai anguwar kusa banga tukubar mai nama ba, gashi ammafa aro nabaka kud’in.” Yafad’a had’e da miqa masa ledojin yana dariya. Murmushi baffa yayi yakarb’a. “A gaida qanen nusaiba, ai gaba d’aya shaf ni namantan da wannan zancen, shine zaka fito awannan daren ai da kabarshi.” “Inaa..ai ba’ayi hakan ba tunda sunna ce.” “Hakane kuma, to nagode sosai ALLAH yabar zumunci, kud’inka kuwa har qari zanyi maka in Sha ALLAH.” Saida Baffa Usman yayi dariya sannan yace. “Inaaa..kud’ina daidai zan karb’a bana son qari, salon kace ace nabada aron bashi na karb’i ruwa (bashi da ruwa)..” haka sukayita raharsu kafin yawuce shi kuma baffa yarufe gida. A inda yabarta anan yasameta tana gyangyad’i ya ajiye ledojin gefe tare dad’an girgiza kafad’arta, zumbur tamiqe tsaye cikin gigin bacci tanufi qofar fita yariqo hannunta ya shiga toilet d’in dake cikin d’akin yace tayi arwala, Bayan sunfito yarufa mata mayafinta ya jasu sallah raka’a biyu sannan suka sallame, jawo ledojin yayi naman kazane qwaya d’aya da cire sai lemun Coca-cola na gora guda biyu ya tura mata agabanta yace taci, Citake tana rufe idanuwa had’e da sandare hannu cikin naman alamun har lokacin bacci nacinta don haka yasa hannunsa tare dayin bisimillah yana d’ebo naman yana tura mata abaki, haka yayita bata idanuwanta arufe tanaci har taqoshi don taci fiye da rabi saboda yunwar da takeji sannan yabud’e coke d’in ya azamata bakin gorarar abaki tafara sha, da sauri tabud’e idanuwa had’e da cire bakinta saboda yanda sanyi da gas d’inta suka shigar mata a hanci. “Bana shan wannan naqoshi.” Tafad’a tana qoqarin zamewa takwanta anan inda take. Aje lemun yayi had’e da d’agata yaje ya wanko mata hannunta yabata ruwa tasha yakaita saman gadon takwanta ya lullub’eta sannan yadawo ya zauna ya canye ragowar naman yasha lemunsa sannan yafidda ledojin awaje. Yajima zaune yana tunanin abubuwa uku da suka yimasa kututu azuciya, nafarko rashin sanin halin da Nuraddeen ke ciki, na biyu zancen Rashida da aka tabbatar masa da cewa tadawo na uku rashin sanin inda amininsa yashiga wato mahaifin Rashida. ganin bayada tudun dafawar da zai samun mafita akansu yasa yamiqe yafara salloli yana kwararo addu’o’i akan ALLAH yakawo sassauci acikin jarabawowin rayuwarsu. ••• ••• ••• Baba na wucewa sashensu Rashida nafitowa cikin mota, jitayi gabanta ya tsananta fad’uwa da sauri tayi ta’awizi saboda korar shed’an, dama tunda taga annufo gate d’in gidan gabanta yasoma fad’uwa amma saita laqantashi da kyan gidanne da tsaruwarsa yasa tajin hakan, a hankali takebin ko Ina da kallo har zuwa lokacin da Fatima ta zagayo zuwa inda take tsaye tana d’an d’unguzarta da kafad’a. “Kai maman boy.” Tafad’a tana d’an harararta. Dariya tayi had’e da cewa. “A’a aunty barni in kalli wannan aljannar duniya, tunda nake ban tab’a shiga cikin irin wud’annan gidajen ba koda kuwa a mafarki ne saidai in hangosu a tv.” Hannunta Fatima taja tana d’auke da little sukabi bayan Dr nura daya wuce yana murmushi, “ALLAH kidena wannan qauyancin, idan ba haka ba kuwa nida yarona bazamu sake fita tare dake ba kada ki kofsa mana ko little?.” Taqarasa maganar tana dariya had’e da kallonsa. STORY CONTINUES BELOW  Dariya yayi tamkar wanda yafahimci metake fad’a yana qoqarin zillewa ya sauka qasa ganin annufo part d’in ammie, dama haka yakeyi duk sanda sukazo yafiso a ajiyesa yashiga da qafafuwansa, haka kuwa akayi ta ajiyesa da gudu yanufi cikin falo tana fad’in. “Little kadena gudufa?” Ita kuwa Rashida dariyar gudun nasa tashigayi tana fad’in “Wayyo ni ALLAH Rashida, wlh aunty yaronnan naki idan naganesa da daddare sai gudu, kingasa kuwa qurqur dashi sai kace d’an aljanu.” ‘Dago kai tayi tana kallonta had’e da harararta sannn tace. “Mungode, wato nida Dr mune aljanun ko?, Bari mushiga ai zanfad’awa uncle d’in naki abunda kikace.” Hango ammie sukayi da tuni dr nura daya shiga yasanar da ita zuwan nasu tafito cikin shiga ta alfarma tad’auke little Nuraddeen da sai faman wangalar dariya yakeyi yana d’aga hannuwa. “Wowwww…Masha Allah, oyoyo maigida, wannan wanka haka gaskiya nasayeshi, iyyeeeee yaron Abba kasha kyau tubarkallah yau nikam auren dakai nakeyi.” Shi kam banda dariya da gwarancin maganarsa da ba’a fahimta babu abunda yakeyi, d’ago kai ammie tayi lokacin da suka qaraso tana fad’in. “Maraba da ‘yata takaina, kice yau tafe kuke da manyan baqi, bisimillah sannunku da zuwa” Tawuce gaba suna biye da ita har suka qaraso cikin falon, Bayan sun zazzauna suka shiga russunawa suna gaisheta cikin girmamawa yayinda shi kuma Dr nura kecan gefe zaune riqe da remote yad’ora qafa d’aya akan d’aya yana kallon wani shiri a tv. Gaba d’aya ammie ta manta dashi sai faman firarta takeyi dasu Fatima suna dariya kai kace ba surukarta ceba idan kaga yanda sukeyi, Rashida kawai ce bata wani saki jiki sosai ba, “Rashida kisaki jikinki mana, kemafa ‘ya na d’aukeki tamkar su Fatima, don haka kid’auka nan gidanku ne har zuwa lokacin da zama zaiyi halinsa tsakanin mu dake kinji ko, koda inafatar ko hakan tafaru zumunci bazai tsinke a tsakaninmu ba ko?” “Insha ALLAH.” Tabata amsa tana murmushi, Ganin sukayi Dr Nura yataso yana kumbura fuska ya d’auki little dake jikin Rashida yana faman jaye mata mayafi da alama nono yake son sha. “A’a son Ina zakaje kake qoqarin d’aukar Nuraddeen” don ita haka take kiran little, acewarta wai qara ariqa kiransa da cikakken sunansa yafi akan litte d’in. “To ammie fita zamuyi tunda yau gaba d’aya kin manta dani ta ‘ya’yanki kawai kikeyi.” “Ikon ALLAH, shine kake kumbura fuska haka?” “Eh mana, Nima ai da umma nan nasan zata kulani dani tunda kin shareni.?” “To da batanan fa?” “Nazama so lonely, waima Ina take ne? Yafad’a yana duba gefe gefen kitchen. “Aw sai yanzu kake tambayarta?, Ina tunda kashigo baka nemeta ba kuma kasan inhar dai tananan bazata barka haka ba idan kazo ko?” “Wlh shirincan ya d’aukemun hankali, ina tajene ammie?” “Babu inda taje, zazzab’i ke damunta yau shiyasa baka ganeta ba, Amma dai da sauqi don ban jima dabaro wajenta ba” “Ya Salam! ALLAH yasawaqe, Bari muje nida maigidanta mudubota.” “To ai shikenan ka kyauta kuwa, kagaisheta idan kunje.” ‘Daukar little daketa faman rigimar shan nono Rashida tayi kamar bata fahimta ba yayi suka fice, Fatima tad’an harareta sannan tamaida kallonta ga ammie tace STORY CONTINUES BELOW  “Kingata ko ammie?, Yaro nason yasha nono tahanasa shida kayansa, sai kace jiqawa zatayi tasha, ALLAH haka takeyi masa ko agida tayi kamar bata san rigimar me yakeyi ba.” “A’a Rashida kidena yimasa haka, yaro fane sosai ina watansa goma akace ko?” “Eh.” Tafad’a a kunyace. “Haba ai har yanzu yana buqatar ruwan nonon ajikinsa don sunada matuqar tasiri wajen basa garkuwa ga lafiyar jikinsa data qwaqwalwarsa, kidena ganin wannan girman d’an jikin da wayau da ALLAH yayi masa tunda bai shekara ba kina bashi nono isashshe yana sha kinji ko?.” “Ai zakiga wasu yaran da wata tara har sun iya tafiya ga kuma d’an banzar wayo atattare dasu amma sukai har kusan shekaru biyu iyayensu na basu nono batare dasun damuba balle shi dake da wata goma da ‘yan satukka akai.” Dr nura kuwa d’auke da litte yanufi sashensu umma yayi sallama a bakin qofar shiga d’akin baba dake ciki ya amsa masa tare da bashi izinin shigowa, koda ya shiga kwance ya iskota lullub’e kanta na bud’e ya gaisheta tare da yimata ya jiki, shi kuwa little wajen baba yanufa ya d’aukesa yan dariya. “Kai babban mutum wannan gayun dai bazai burge amaryar kaba tunda kwance take tana fama da zazzab’i, abunda kawai za’ayi kabani kayannan naka sai in lallab’a maka ita ta tashi kugaisa.” Baba yafad’a d’auke dashi yan gyara masa zaman hular kansa shi kuma sai hannuwa yake turawa cikin babbar rigar yana wasa da ita.” Dariya yaba baba yace. “A gaisheka alhajin baka jeba, kodai alkhairi zakamun intaro hannu.” Hatta umma dake kwance saida suka bata dariya, batasan meyasa yaron ke matuqar shiga ranta ba, ita dai har ga ALLAH jitake tana yimasa wani irin so nadaban, tana wannan tunanin taji ya hayikke jikinta yana qoqarin leqo fuskarta, shi kuma Dr nura suka fita tare da baba suna gaisawa yana tambyar mike damunta. Zaune umma ta tashi ta jawosa ajiki tana kallonsa, haka kurum taji tafashe da kuka wanda bako shakka kukan tunawa da ‘yarta data hango kamarsa da itane, shin taya wannan yaron ya zamo jinin alhaji bayan jikinta da kamanninsa nafad’a mata akwai alaqa mai qarfi tsakaninsa da ita, wannan shine tmbayar da tashiga yiwa kanta tanaci gaba da kuka. Acan waje kuwa kud’d’i Dr yaba baba yace yaje yakai umma asibiti adubata saboda bai kamata ta zauna da zazzab’in ba tunda ba’asan meke damunta ba. Godiya yayi masa sosai sannan yakoma cikin d’akin ya d’auko little daya isko lafe ajikinta yana kallo yanda take kuka. Bayan Dr nura yawuce ya taimaka mata tashirya yana yimata fad’an tacire damuwa aranta kar azo ace itace keneman yimata barazana a lafiyar jiki sannan suka wuce asibitin. Basubar gidan ba sai bayan isha’i ammie tarakkosu har part d’in hajia nafeesa don su gaisheda dady tunda a part d’inta yake. Dr nura yafara shiga kafin su ammie da Fatima su shigo suma yana zaune shida hajia nafeesa da yaranta suna kallon wa’azin shaikh Ahmad tijjani Yusuf a tashar Sunnah tv, dama matuqar yana part d’inta to tashar ake kalla gaba d’aya saboda tarbiyar yaransa, idan kuwa baya part d’in basuda aiki sai kallon tashoshin waqe waqe da cartoon, Sallama d’auke abakunansu suka shiga aka amsa masu. Yaranta ko gaisuwa Babu suka mimmiqe zasu shiga d’akunansu dady ya katsa masu tsawa. “You stupid, bakuga mutane bane zaku shige baku gaishesu ba? Maza kudawo kugaisheshu.” Yafad’a ransa a b’ace, kumbure fuska hajia nafeesa tashigayi tana binsu da harara har yaran suka duqa suka gaishesu suka tafi, Ita dai ammie naganin haka tagaida dady tare da d’aga wayarta da ake kira tafita don bazata juri walaqanci ba ko kad’an, Gaisheta dr. dasu Fatima sukayi ta amsa ciki ciki tana wani hurar hanta, Dr ya d’auke kansa daga kallon da yake yimata zuwa ga mahaifinsa yace. STORY CONTINUES BELOW  “Am dama dady Rashida ce tazo gaisheku, kullum tana son tazo ALLAH bai yarda ba sai yau.” “Af ikon ALLAH, maman little Nuraddeen kuke kiransa ko wa?” “Eh baffa.” “ALLAH sarki, sannu kinji Rashida, ayita addu’a ana jurewa kowace irin jarabawa in sha ALLAH komi zai zama tarihi.” “Hajia nafeesa kinga maman wannan yaron da kike tambaya kwanaki kina ganin Dr nashigowa tare dashi.” “Au sannunki, ai nazata wlh agidan reno suka d’aukosa har ina cewa ALLAH dai yasa ba shege bane.” Da sauri Dr suka d’ago kai su duka suna kallonta kafin dady ya girgiza kai cike da takaici yace. “Nafeesa kenan, to bahaka bane, da uwarsa…” Kafin yaqarasa yaji tace “Ai to baza’a gane hakan ba tunda ba’asan kowaye uban sa ba, Ina tsintar uwarsa akayi ko?.” Bata qarasa ba ya katsa mata tsawa had’e da cewa ta tashi tabashi waje. Bayan tatafi dady yayita ba Rashida haquri kamar zaiyi kuka ita kuma tanuna ko ajikinta tunda tasan yanada ubansa, kawai dai dole zataji ba dad’ine ko kad’an, Fatima kuwa harda hawaye tana ganin da ace tana haihuwa baza’a tab’a jifarsu da zuwa gidan reno d’auko d’a, juyowa yayi gareta yaci gaba da cewa. “Fatima kada kibari kalaman auntynku suyi tasiri azuciyarki, ALLAH shi yake badawa bai manta daku ba in sha ALLAH jikina nafad’amun rabonku na kusa kusa domin akoda yaushe bamu cire qauna ga rahamar ALLAH ba, don haka kuyi haquri, kuyi haquri kunji ko?” K’wafa Dr yayi tare da miqewa yafita ransa ab’ace, dama shiyasa tun farko baya shiga sha’aninta ko kad’an saboda gujewa irin wud’annan matsalolin, dama albarkacin mahaifinsa takeci amma daga yau tagama. Sallamar Fatima yayi yarage daga shi sai ita da kuma little sannan yakira hajia nafeesar tafito daga d’aki, nuna mata kujera yayi ta zauna tana wani shashshan magani yace. “Nafeesa kinsan ALLAH.” “Eh” ta amsa masa ciki ciki. “Wlh idan baki ba yarinyar nan haquri ba bisa abunda kika jefeta dashi narantse da ALLAH abakin aurenki kenan!” Da sauri Rashida tad’ago kai had’e da cewa. “A’a dady wlh babu komai nahaqura, ni batama yimun laifi ba idan ma tayi naya…” Bata qarasa ba sanadiyar juyowar da yayi fuskarsa a d’aure ya d’aga mata hannu da sauri tayi gum takama bakinta. “Zaki iya zab’an duk abunda yayi maki arai, amma hukuncin da nayanke yana nan babu ja da baya,” Har zai miqewa yafita yaji muryar hajia nafeesa tace. “Kiyi haquri.” Ciki ciki tana Mai jin wata iriyar tsanar Rashida da d’anta aranta. “Jeki Rashida, ALLAH yayi maki albarka.” Yafad’a tare da ciro kud’i da batasan ko nawa bane yamiqawa little a hannu. Bayan tafita yakalli hajia nafeesa yace. “Kiguji duniya nafeesa da qyalqyalin dake cikinta, wannan rayuwar da kika d’auka bamai b’ullewa dake zuwa ga kyakkyawan qarshe bace shiyasa nake qoqarin aduk lokacin da kika tozarta wani agabana innuna maki kuskurenki saboda ko meye yazo maki da sauqi.” “Amma alhaji..” “Rufemun baki.” Yakatsa mata tsawa had’e da ficewarsa. Lokacin da Rashida kuwa tafito ta samesu tsaitsaye ammie nabasu haquri akan abunda yafaru don taji komai da kunnenta, haquri tasake ba Rashida sannan tace. “Son yakamata suje sugano umma kafin suwuce.” “No… ammie tun d’azu suka wuce asibiti ita da baba saidai idan munqara dawowa.” STORY CONTINUES BELOW  “Ok son kuyi haquri don ALLAH kasaki fuskarnan taka, bana son inganeku cikin damuwa kinji ko ‘yatah kuyi haquri.” Murmushi sukayi kusan atare sannan sukayi mata sallama zukatan kowanensu ba dad’i kafin su shiga mota subar gidan, motarsu nafitowa daga cikin gate napep d’insu baba nawutowa sun dawo daga asibitin, kusan saida sukayi clashing da juna sannan napep d’in ta ajiyesu sukuma suka wuce. 🤪 *Target bend*🏃🏻‍♀️ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/30/2020, 11:39 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___63💎 Tunda suka hau titi babu wanda yacewa wani uffan har suka isa gida, kowanensu ya lula duniyar tunani akan yanda rayuwa zataci gaba da tafiya dasu bisa linzamin qaddarar da suke akai, musamman Dr nura da yake ganin gaba d’aya cinmutuncin da matar mahaifinsa tayi akansa yaqare, don haka akwai buqatar ya d’auki matakin yiwa abun tufqa tunkafin yayi tsayi. Gaba d’aya sai sukajidaren ranar yazo masu abai baice, hatta ‘yar firar da suka sabayi a kowane dare kasawa sukayi kowane ya shige part d’insa ya kwanta, haka ma da safe kusan yanda suka kwana haka kowane yatashi fuskarsa babu wata walwala har suka zauna wajen karyawa ba wanda yace wani abu bayan gaisuwa, miqewa Rashida tayi bayan tagama nata Karin zata wuce d’akinta taji muryar Dr yace. “Koma kizauna maman boy ina son zamuyi magana dake.” Bamusu takoma ta zauna yayi gyaran murya had’e da cewa. “Ina mai baki haquri bisa abunda yafaru jiya, da nasan hakan zata kasance wallahi da ban d’aukeki nakaiki gidan muba, gashi hakan da nayi na neman sauya walwala da kuma farincikin gidannan gaba d’aya, naroqeki kimanta da abunda yafaru domin haka zaisa rayuwarki taci gaba da inganta kamar yanda tafaro, tabbas Bata kyauta ba data cutar dake ta hanyar munanan kalamanta batare da tasan koke waye ba! kuma ko kad’an batayi maki adalci ba a matsayinta na uwa da tasan irin zafin da akej idan aka aibatawa mutum d’a, Amma duk da haka Ina nema mata afuwa a matsayinta na matar mahaifina, ina tabbatar maki da hakan bazata sake faruwa ba in sha ALLAH kinji.” “Uncle kenan! bazance banji komai araina ba akan abunda yafaru jiya kasancewar yazamo silar jefaku cikin halin da tunda nake zaune daku ban tab’a ganinku acikin koda makamancinsa ba, ba ina damuwa bane akan abunda tayi mani ba, kawai damuwata tabayyana ne adalilin yanayin da nake kallon fuskokinku aciki, kalamanta abune da babu tushe, asali ko kuma inganci aciki da har zan damar da kaina. amma shi b’acin ranku da kuma damuwarku tamkar wutace dake cin zuciyata idan Ina ganinku acikinsa wanda natabbata bazata dena ciba har sai lokacin da naga farinciki yabayyana fuskokinku, kuyi haquri domin nima nazamo sila wajen sa ajefeku da kalaman da suka cutar da zukatanku.” Kallon Fatima Dr yayi had’e da cewa. “Kijifa abunda take fad’a!, taya za’ayi tazamo silar cutuwar zukatanmu bayan laifin ita akayiwa.” “Hakan nafaruwa kuwa Dr, musamman ga zukatan da basu fiye son kansu ba kuma suke kallon damuwar wasu amatsayin tasu, don haka damu da ita mu manta da komai mu fuskanci gabanmmu.” “Shikenan ALLAH yaqarawa zukatanmu haquri kuma yabasu girman d’auke duk wata jarabawa da kuma gwagwarmayar rayuwa.” “Amin ya rabbi.” STORY CONTINUES BELOW  Suka fad’a tare suna murmushi, nan suka dasa rankon sabuwar firar da basuyi ba jiya, Bayan wata uku little yaqara wayau Rashida ta yanke shawarar yayesa saboda ganin irin girma daya taso masa kuma babu abunda bai iya ciba. Ana saura sati d’aya tayayeshi suna zaune ita da fatima tace. “Aunty nifa wani sati cire yaronki zanyi amama, ALLAH nagaji da tsutsannan da yakeyimun.” “Kai maman boy, shekararsa d’aya da wata d’aya fa kenan?” “ALLAH nagaji aunty zalina yakeci sai yayita cizona da haqoransa masu kaifin tsiya sai kace reza.” dariya Fatima tayi had’e da cewa. “Aikuwa baki isa ba, sai yayi 2years tukuna, haquri kawai zakiyi kema wayasan yanda ummanmu tayi fama dake.” “ALLAH sarki umma, ai da zaku had’u kika tambayeta Allah zata fad’a maki bata wani sha wahalar renona ba saboda da kanta take fad’a cewa ni ‘yar baiwa ce.” “ALLAH!?” Fatima tafad’a tana dariya hadde da zaro idanu, gwaggo mai aiki dake goye dashi tana mopping tace. “Gaskiya hajia ta yaye yaron nan tunda ya iya cin komai, tubarkallah qato dashi gayanan yana neman karyamun baya,” “Laaa…gwaggo har dake?, Zo kawomun yarona indai goyone daga yau yadena son naki.” Qarar wayar rashidane data jiyo rurinta ad’aki ya katse firar tayi saurin miqewa don ta d’auko gwaggo tace “A’a Bari nad’auko maki, Amma cin hancin yaye d’an hajia ne zan baki.” “Aikuwa angama gwaggo.” Rashida tafad’a tana dariya “Ai sai kuyi bari abbansa yadawo zan fad’a masa ai.” koda gwaggo takawo mata wayar har tayi missed call, murmushi tayai ganin lambar Yaya Maryam da kullum saita kira idan bataji takirata ba taji ya lafiyarau take ita da litte, saurin kiranta tayi don kada tasake kiranta bugu d’aya ta d’aga. “Rashida ya kike? kuna lafiya.” “Lafiya klwa gwaggo ya wajensu baba balarabe?” “Kowa lafiya Rashida, Ina maigida.” “Gashinan ya hayewa gwaggo mai aiki baya, dama yanzu nake zancen zan yayesa da aunty saboda mugun tsotsans.” “Kul! Karki fara, kibari koda wata biyar ne nan gaba yad’an qara qwari kinji nafad’a maki ko?” ‘bata fuska tyi kamar zatayi kuka had’e da cewa. “Kai gwaggo kinga yanda yazama wani tulele dashi, ALLAH bazan iya da tsutsar saba.” “Cit d’inki, kenan ummanki sau uku tana zancen yayeki amma saboda qulafucin nono saita fasa har saida kika shekara biyu cif sannan ta yayeki, shima d’in haka kika dingayi kamar zaki mutu duk kikabi kika tada mana da hankali.” “Nid’in gwaggo!?” Tafad’a tana kallon fatima dake jin duk abunda Yaya Maryam kefad’a tana gumtse dariyar dake neman kucce mata. “Ked’in fa, some some nawa kikayi?, Banda ALLAH yayi zakinfita ai da yanzu saidai labarinki, don haka kibari sai nan da wata hud’u idan ALLAH yasa munada rai.” “Shikenan gwaggo, ya labarinsu ummana?” “Kiyi haquri Rashida har yanzu bawani labari akansu, amma munanan muna addu’a ALLAH ya karkato hankalinsu sudawo gida.” Wata gauruwar ajiyar zuciya tayi kafin suyi sallama tana dubon inda Fatima ke zaune, kashe mata ido d’aya tayi had’e da d’aga mata gira tana dariya tace. “To ‘yar baiwa ya akeyine?.” “Ummaaa!..” tafad’a cikin sigar damuwa. “ALLAH sarki, ummanmu gaskiya baqaramin so da tausayinki take ba, amma ke shine kike so kicuci yaronmu, to ALLAH yakama ki duk naji abunda Yaya Maryam tafad’a, ashe haddasu some some akayi akan nono, oh ni Fatima! gaskiya umma taga jalala.” taqare maganar had’e da tintsirewa da dariya tana tafa hannuwa, tayi hakanne saboda tadaqile tasirin damuwar dake shirin ziyartar Rashida akan zancen rashin dawowar iyayen nata da suka gama da Yaya Maryam. STORY CONTINUES BELOW  Binta da kallo Rashida tayi tana murmushi, a zuciyarta tana mai addu’a, Allah ya dawwamar da irin wannan farinciki da Fatima ke ciki atattare da ita nahar abada. Dr kuwa tunda yaji zancen Rashida na Shirin yayen little shima yafara shire shiren nema mata takardun shedar kammala primary, dama sun tab’a maganar karatun da ita tafad’a masa primary ne kawai tayi har take basu labarin yanda tahad’u da abban little a sanadiyar rashin son karatunta sunata dariya, bai wani sha wahalar samun takardun ba saboda yanda komai ya lalace zaka iya samunsu matuqar akwai kud’i atare dakai, kafin kace me har yagama had’a takardun da cike mata form d’in shiga makarantar gaba da primary na wannan shekarar tare da taimakon Fatima batare da sanin Rashidar ba, akoda yaushe Rashida cikin farinciki take natakusa yaye little Nuraddeen tahuta da tsutsa ita kuma Fatima nayimata dariyar maida ita makaranta da suke shirinyi bada saninta ba, wanda ALLAH kad’ai yasan yanda za’a kwashe matuqar har yanzu tana nan akan bakanta na rashin son karatu. Satin yaye little nakamawa tahad’a gaba d’aya sauran kayansa dake hannunta takaiwa Fatima suna tayi mata dariya ita da Dr. “Ikon ALLAH, maman boy wannan wace irin korace haka akeyiwa takwara, anharhad’o komai nasa sai kace zai bar gari” “Uncle sunanta kora da hali, gaba d’aya nayi handing over dashi, gashi ga mamarsa kar akoma cewa ansanni, yabarni inhuta abuna ko d’akina kada yakoma leqawa har sai jinin jikina yadawo.” “E’em kedai! karfa ayi haka bayan kwana biyu kice kinyi missing d’insa.” “Cab! Uncle little d’in?, Ai yanda take addabar rayuwata da daddare babu wani missing d’insa da zanyi.” “Kika ce?” Tayi dariya kawai had’e da juyawarta tabar falon fatima nafad’in. “Muna nan dake zakizo ganinsa muma muyi maki handing over.” Randa akayi yayen little kuwa ba qaramar rigima suka shaba duk daya saba kwana wajensu amma sai kace wanda aka fad’awa yayesa za’ayi haka yadinga yimasu kuka cikin dare, sunyi lallashi har sungaji amma yaqiyin shiru, idan tayi tagaji taba Dr shima yayi nashi lallashin amma kamar ana sake sake turashi, ALLAH sarki Rashida tun tana iya sauraren kukan har takasa tasa pillow ta dad’e kunnuwanta amma bata dena jiba, tashi tayi tayi zaune tsakiyar gadon tanajin kukan nasa har cikin ranta batasan lokacin da itama tafashe da kuka ba, batasan meyasa ba ko kad’an bata iya jurar kukansa gashi bazata tab’a iya fita da sunan taje taduba saba, d’aga hannuwanta tayi sama ahankali tafara yimasa addu’a. “Ya ALLAH Kai kake karb’ar addu’ar mahaifiya ga d’anta, ALLAH kasa masa dangana, ya ALLAH kamar yanda yabar nono na ayau ALLAH karabashi da duk wani musibar rayuwa tun daga qanqantarsa har zuwa girmansa, ALLAH kasa yazamo mai juriya da haquri acikin rayuwarsa kuma ka albarkaceshi kasa amfani mai tarin yawa acikin wanda yasha na tsawon wannan lokacin.” Tana gamawa takoma takwanta tana cigaba da saurarar kukan nasa, ahankali tafara jin sautin kukan nasa na ragewa har tadena ji gaba d’aya, ajiyar zuciya tayi sannan tagyara kwanciyarta har bacci b’arawo yazo ya saceta. Haka sukayi ta fama dashi har kwana biyu duk da qarfin hali kawai ne Fatima keyi itama kullum da zazzab’i take kwana, amma saboda shi take jurewa, arana ta uku ne safiya nawaye koda Dr nura yatashi yaganta a qudundune cikin bargo jikinta sai faman rawa yakeyi, “Subhanallahi, Fatima bakida lafiya ne?” Yafad’a yana yaye bargon, yanda yagata ba qaramin tayar masa da hankali yayi ba da sauri ya Ida cire bargon yatada ita had’e da rungumota ajiki yana tattab’a wuyanta da goshinta, “Fatima ko ciwon kanne?” Yafad’a arud’e da sauri ta d’aga masa kai had’e da cewa. “Inajin sanyi sosai.” STORY CONTINUES BELOW  Yatabbatar da haka don gaba d’aya jikinta yayi zafi sai rawar sanyi takeyi, First-aid d’insa yatashi ya d’auko yaciro maganinta na ciwon kai da take yawanyi ya b’alla mata yabata tasha ya had’a mata dana maleria sannan ya maida ita ta kwanta ya lullub’a mata bargo yana yimata addu’a. _As’alallahul azhim, rabbil arshil azhim, anyashfiki, laa ba’asa d’ahurun in sha ALLAH_ Ya tofa mata had’e dayi mata sannu sannan yayi kissing d’inta a goshi yabar d’akin, bayan mintuna biyu yadawo ya d’auki little dake sharkar baccinsa hankali kwance dama haka yakeyi, ya hanasu bacci da daddare da safe kuma yayita sharkar abunsa har rana, yanufi wajen Rashida dashi yace tagyarashi zai kaishi wajen ammie Fatima batada lafiya, nan take Rashida taji ba dad’i aranta sai take ganin kamar rigimarshi ta haifarwa da Fatima rashin lafiya. “Uncle baka ganin zai dami ammie sosai tunda baya bacci da daddare.” “Nooo..Bakomai ki gyarashi, ai taso akaimata shi tun farko mu mukaqi ganin zaifi sauqi tunda yafi sabawa damu, amma yanzu tunda ga dalili sai akaimata shi, koba komai zata sama mashi maganin da ake ba yara na yaye tunda mu bamuyi dubarar haka ba?” “Shikenan uncle.” tafad’a tare da karb’arshi agurguje tashiga shiryashi, koda yadawo d’auke da akwatinsa har tagama shiryashi yakarb’esa sannan yanufi wajen ammie dashi. Satinshi biyu a hannun ammie kuma yana samun kulawa sosai wajenta da kuma umma da kusanma yayen awajenta yake, don matuqar dady na part d’in ammie to awajenta yake kwana, little kam har zazzab’i yayi shima kusan sau biyu amma Rashida bata tab’a zuwa dubosa ba saidai Fatima da Dr suje duk da har yanzu itama tana fama da zazzab’in, babu yanda fatima batayi da Rashida ba akan taje taduboshi don har saida aka kwantar dashi asibiti na kwana d’aya amma taqi zuwa. Baba balarabe kuwa da aka sanar dashi safiya nawayewa yaje ya sanar da Yaya Maryam suka yanke shawarar zasuje ganinsa idan ALLAH yakai ranmu gobe,….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [8/31/2020, 11:38 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___64💎 Cikin daren Yaya Maryam takira aunty marwiyya tasanar da ita zancen tafiyar zuwa borno tace. “Bazata samu dama ba saboda itama mai gidanta bayajin dad’i, Amma don ALLAH idan sunje su gaishesu sosai.” Kasancewar son sukeyi suje ranar sudawo yasa tunda sassafe suka shirya, aron mota baba balarabe ya samo masu su hud’u, dashi da alhaji ubale mijin Yaya Maryam, sai ita da kuma matar baba balarabe guda wato uwar gidansa sukasa mai sannan suka d’auki hanyar zuwa borno… ••• ••• ••• *FEDERAL NEUROPSYCHIATRIC HOSPITAL (KWARE) SOKOTO.* canne asibitin da Yaya hawwa ke jinya, duk wani qoqari da yakamata ayi wajen bata kulawa anyi amma abun sai sake hab’b’aka yakeyi, allurori, magunguna da gwaje-gwaje don gano matsalarta da kuma yimata maganinta kullum cikin yimata ita ake, baffa yakashi kud’i da baisan iya adadinsu ba amma babu wani sauyi ko cigaba da aka samu, kullum al’amarinta jiya iyau, kimanin shekara d’aya da watanni kenan yanzu. Duk wanda yasan Yaya hawwa duniya ya kalleta ba lallene ya iya ganeta ba saboda yanda tabi talalace haukan dake saman kanta yafi hauka muni don hatta mahaukatan dake tare da ita sunfara tsoronta saboda tana cutar dasu, hakan yasa aka killace ta ita kad’ai batare da kowa ba, idan abun ya motsamata saidai jami’an lafiya suga tana lallaqe ailin da bango tamkar wata halintar daba mutum ba, sunaji suna gani zata dinga buga kanta ga jikin bango har sai yayi jini kuma duk wanda yaje cetonta in sunkai su goma suna fitowa da wata kamar tadaban daba tasu ba, kasancewar ma aikatan lafiya mutanene masu matuqar qoqari da kuma jajircewa wajen ganin sunyi yaqi da duk wata cuta dake damun marasa lafiyarsu batare da sun nuna gazawarsu ba yasa gaba d’aya likitocin suka zauna suka yanke shawarar had’a taron gaggawa na qarawa juna sani daga b’angaren mabanbanta likitoci kamarsu daga wasu asibitoci da sauran garuruwa akan wannan sabuwar cutar da Yaya hawwa ked’auke da ita wacce suke tunanin tana nema tafi qarfinsu don samun mafita mai d’auke da topic _HOW TO TREAT PATIENT WITH UNKNOWN NEUROSIS.._ STORY CONTINUES BELOW  Cikin qanqnen lokaci taron ya wakana, manyan likitoci daban daban sun tashi sunyi bayani kala kala akan wannan matsala tare da samun solution d’aya da suke tsammanin shine qarshen matsalar, Haka kuma tundaga sokoto wani babban likitansu yaje kano don samun cikakken bayanai akan asalin yanda lalurar tasami yaya hawwa, da baffa Usman suka fara cinkaro kasancewar sun sanshi tunda sune suka kaita asibitin, duk wasu tambayoyi da suka yimasa qin amsa masu ko d’aya yayi har saida ya aika aka kira baffa, gefe suka keb’e dashi yayi masa bayanin abunda ya kawo likitan, d’ari bisa d’ari baffa yayi masu bayanin cewa cutace kawai da suka wayi gari suka ganta da ita, wacce bazasu iya cewa ga dalilin daya haifar mata da itaba, duk yanda likitan yakai qwarewa wajen ganin yasamu wani labari da zai iya basu haske aikai bisa tattaunawar da sukayi wajen taron qarawa juna sani cewa cutar nafaruwa ne tadalilin wasu kalolin halittu masu tsananin tsoratarwa dake bijirowa marar lafiya daga nan sai tasirin ya halbu ga qwaqwalwarsa tayanda zata riqa juyawa tana qara d’auko masa hoton abubuwan, daga nan kuma sai zuciya tafara aiki da sauri sauri saboda tsananin tsora sai kuma suriqa ganin duk wani abu da zai fuskantosu to cutar dasu zaiyi daga nan kuma sai tana tunzura jiki wajen baiwa kai kariya ko kuma neman kub’uta daga inda mutane suke zuwa wani wajen da suke ganin shine zai basu kariya idan sun kad’aita, duk hakan nafaruwane ta dalilin yawan mu’amalar da marar lafiya yayi da wajajen dake d’auke da abubuwan ban tsoro inda ba’afiya samun mutane awajen ba da kuma mu’amala da wani abun da kake tsoron zai iya cutar dakai alokaci d’aya ko rasa wani abun da kake so, amma baffa yaqi cewa komai akan haka, saboda yana kallon fallasa dalilin faruwar haka agareta amatsayin zubar da kimarsa da kuma ta d’ansa. Haka likitan yaqari masu tambayoyin yagama amma bai samu wani haske akan wancan bayaninba balle sutabbatar da hakan, har zai tafi saiga baffa Ali shida matarsa sun dawo daga wani wajen da ako yaushe suke zuwa tare, tsabar gulma shida bawani shiri yake da ‘yan uwan nasa ba amma saboda yaga babban mutum d’an birni tare dasu yanufi wajen. “Assalamu alaikum, ahhh baqo akayi?” Yafad’a yana kallon baffa Usman, eh, yabashi amsa ataqaice yana qoqarin jan hankalin likitan subar wajen, d’an matsowa baffa Ali yayi yana kallon likitan had’e da goge hannunsa ga rigarsa sannan yamiqa masa yana fad’in. “Assalamu alaikum, sannu bawan ALLAH, yanzu ake tafe.” Kallonsa likitan yayi kafin yamaido kallonsa gasu baffa yan tambayarsu shima tare yake dasu saboda ganin yanda sukayi kama su ukun sosai, baffa ya d’aga masa kai, cike da qyanqyamin yanayin da yaganshi na qazanta likita yamiqa masa hannu suka gaisa yana washe baki donshi yazata wani alkhairi ne zasu samu shima ya lakata. “Ok ko zan iya tambayarsa ko yanada wani bayani d’aya sani akai tunda tare kuke a gida d’aya?” “A’a Dr iya bayanin da muka yimaka shikenan daga shi babu wani abun, Aliyu zaka iya wucewa.” Baffa Usman yafad’a yana tura baffa Ali cikin gidan, rigima suka soma yi baffa yariqe masa hannu. “Barshi Usman, Aliyu zo kafad’i abunda kasani. Cikin jin haushi baffa Ali yagyara rigarsa yana hararar baffa Usman, tambayarsa likita yashigayi akan matsalar Yaya hawwa ko akwai abunda yasani ai kuwa baffa yabud’e baki yanda kukasan indararo yanata zubawa likita bayani akan zuwan Yaya hawwa dajin qare kukanka har zuwa silar haukacewarta. Sosai likitan yaji dad’i kuma yasamu amsar da suke buqata yayi sallama dasu yawuce, ahasale baffa Usman yayi kan baffa Ali yakai masa naushi yafad’i qasa bakinsa yafashe da jini, cikin b’acin rai yashiga nunasa da hannu da hannu yana fad’in. “Anya wai kai mutun ne?, Wace irin zuciya gareka mai cike da son cutar da ‘yan uwanka, wai kaima d’an uwane koko d’an wuta?..tir da halinka wlh kahi hasarar rayuwarka aliyu matuqar baka canza ba.” STORY CONTINUES BELOW  Wani naushin yasake kaimasa lokacin daya taso yana son fad’a masa magana yasake fad’uwa yabishi qasa zai dakai baffa yayi saurin riqe masa hannu, idanuwansa na zubar da qwalla yace. “Don ALLAH Usman ka qyalesa, kada kabiyeshi duniya ta zagemu a matsayin munfito ciki d’aya muna wannan hasuma, meye laifinsa ga abunda yafad’a Usman?, Wannan shine sakamakon abunda yakamata yamayarwa da hawwa bisa tonawa da binnewar da sukayi atare, wataqil inhar yad’a labarin suke sonyi akan cutar dake damunta don mutane su kiyaye sai yazame mata kaffara tahanyar rage mata zunubanta, kuma tazamo silar d’aukar darasi ga duk wani mutum mai hali irin nata ko son aikata abunda tayi don gujewa gobensa, ka qyalesa zo mutafi.” Yafad’a tare da jan hannunsa sukabar wajen. Tofar da yawu cike da jini baffa Ali yayi yashiga d’ura masu zagi kala kala yana fad’in daga yau babushi babu su. haqiqa ba qananan kud’i asibitin suka kashe ba wajen ganin sun yaqi wannan lulura da suke ganin kamar wata sabuwar cutace kuma suke fatar asibitinsu tazamo tafarko wajen kauda ita kafin ta watsu ga duniya, Nan take manyan kafafen yad’a labarai a qasar nan da kuma gidajen jaridu sukayi dandazo a asibitin don samun tattaunawa da manya manya likitocin da suka jagoranci wannan shiri nakawo qarshen cutar da suka rad’awa suna _neurosis2020_ kan kace me tuni cikin qanqanen lokaci labarin lalurar haukar yaya hawwa yazaga ko ina ta kafafan yad’a labarai tahanyar fira da babban likitan asibitin yana wayarwa da mutane kai akan lalurar ana bayani ana nuno Yaya hawwa da irin yanayin da take ciki da wanda take shiga idan yamotsa, wasu idan sungani tabasu tausayi wasu kuma suyi ALLAH wadda da ita, wasu kuma subita da addu’a. Nan take suka maida kud’ad’en da suka kashe har riba tabiyo baya, kuma Alhamdulillah bisa sabuwar kulawar da aka koma bata tamusamman sun fara ganin canji akan gwaje-gwaje da suka sake yimata daga baya duknda dai har yanzun akwai sauran rina akaba. ••• ••• ••• Su baba balarabe basu isa garin borno ba sai kusan qarfe d’aya na rana, baba balarabe yakira Dr yasanar dashi zancen isowarsu lokacin yana zaune sungama shiryawa shida Fatima suna fama da ita akan taje ta sako mayafinta suje ganin little Nuraddeen agidansu ammie amma taqi, sai da taga Dr yad’aga wayarsa yana fad’in. “Na’am baba har kin iso, eh to kutsaya adaidai junction ganinan zuwa.” Waro idanuwa waje tayi had’e da cewa “laaa uncle wane baban?” “Baba balarabe.” Yafad’a in I don’t care d’innan yana fad’in Fatima ta tashe suje don dama bai sanar da Rashida batun zuwansu ba su ammie kad’ai ya fad’awa. “Aunty dama zasu zo shine baku fad’an ba.?” “Eh to, aiba wajenki zasu zoba shiyasa ma ba’anan zasu sauka ba, gidansu ammie zamu saukesu tunda yarona sukazo dubawa kuma kinga ke kince baki zuwa shiyasa ban fad’a maki ba.” “Amma dai zasu zo ko?” “Ina, Ina kibar wannan zancen kawai, idan kina son ganinsu kizo mutafi idan kuma bakya so to kizauna warki anan, mu muntafi” Dr yafad’a yana gumtse dariyar shi had’e da ficewa Fatima nabiye dashi abaya. Ganin hakan yasa taje ta d’auko mayafinta ta lullub’a tana turo baki itama tabi bayansu. Suna kawowa titi yayi parking da motar yace Fatima tajesu sutafi shi zai hau mashin yaje yazo dasu baba balarabe. Cike da kunya Rashida tashiga gidan tana wani nonnoce kai qasa Fatima sai dariya take yimata har suka isa, Kuda suka shiga part d’in ammie tana kitchen suna girki ita da umma, Kai tsaye Fatima taja hannunta suka wuce bedroom d’in ammie saboda warin girkin da taji yabugar mata hanci, “Kai aunty meye bazamu tsaya a falo ba har sai munzo d’aki.” “Maman boy bana son qamshin abincin, mu zauna warmu anan bari nakirata awaya.” tafad’a tana ciro wayarta cikin jikka. STORY CONTINUES BELOW  “Hello ammie mun iso gamu a bedroom d’inki?” “Ok Ina zuwa.” Tabata amsa, tana shigowa sukayi ido biyu da Rashida databi yanda d’akin yatsaru da kallo, da sauri ta jid’ar da kanta qasa tana wasa da ‘yan yatsun hannunta. “A’a ‘yata kice yau bikon maman Nuraddeen kika yomana, koda yake nasan badon mijina tazo ba don taga iyayenta ne ko Rashida.” Ammie tafad’a tana dariya. Saukowa daga zaunen da suke kan doguwar kujerar dake cikin d’akin sukayi had’e da duqawa har qasa suka gaisheta tadafa kansu tana fad’in. “Lafiya qlw ‘ya’yan albarka, kutashi ku zauna ALLAH yayi maku albarka.” Itama ta zauna bakin gado. “Agaisheki Rashida sarkin fulanin duk duniya, wato haka kika yiwa maigidana sai yau don kinji su gwaggonki zasuzo ko?” Murmushi kawai Rashida tayi batare data tanka ba har lokacin kanta naduqe aqasa. “To ai shikenan kin kyauta, ALLAH yarabaki da wahala, ‘yatah ya jikin naki da sauqi ko?” “Eh ammie, kawai yanxu baccine ke yawan damuna.” “To may be rankon wanda bakiyi bane kwanakin baya, Ina son take?” “Yaje tahowa dasu Yaya maryam.” “Au har sun iso? Bari make muqarasa aikin kafin su iso, Rashida kinemi kud’in da zakifa biyamu kafin mugwada maki maigida naga sai warar idanuwa kikeyi kina bid’ar inda zaki hangoshi.” Cike da tsokana ammie tafad’ima rashida haka sannan tafice tana dariya. Koda su Dr suka iso su ammie na a harabar gida ita da dady suna jiran isowarsu ita kuma umma nacan tagama shishshirya abincin da sukayi tana gyarawa little daya qara wayau yayi kyau sosai, tawai tashiga yimasa tana fad’in. “Maigida mai raki, d’an Fatima mai kukan yaye, mijin hajiya mai babbar kyauta.” Baba kuwa dake gefe zaune yana kallonsu sai faman dariya yakeyi, shima little d’in dariya yakeyi harda qyaqyatawa riqe da marfin mai yana wasa dashi. Cike da farinciki su ammie suka tarbesu had’e da yimasu iso zuwa part d’in nata, bin gidan su baba balarabe sukayi da kallo suna jinjina ki had’e da mamakin yanda suka fita daban acikin masu arziqi wajen girmama d’an Adam da kuma karrama shi har suka iso cikin falon, Yaya Maryam kam kusan lumfashinta d’aukewa yaso yayi saboda irin qamshi da sanyin a.c daya bugi fuskarta, ji tayi jiri na neman d’ibarta da sauri tariqe hajia Aisha matar baba balarabe, juyowa tyi takalleta had’e dayin murmushi cikin murya qasa qasa tace. “Yawwa Yaya riqeni, nima nan jiri d’ibata yakeyi ina neman fad’uwa” “Bari Aisha! wannan shi ake kira da aljannar duniya, anbasu duniya kuma ga dukkan alama lafira ma zasu samu” Bayan sun zazzauna ammie taje da kanta ta d’auko masu ruwan swan masu sanyi a tire tana jero masu sannu, bayan ta ajiye masu ruwan takoma ta d’auko wasu had’e da kofuna tanufi d’ayan parlon da dady yaja su baba balarabe, Saida ta ajiyema kowanensu agabansa sannan tanemi d’aya daga cikin kujerun tazauna tana gyara mayafinta dake qoqarin zamewa fuskarta asake. “Sannunku da zuwa, ya hanya?” Saida mijin Yaya Maryam ya ajiye cup d’in daya tsiyaya ruwan yasha sannan suka had’a baki shida baba balarabe suna fad’in. “Yawwa hajia, hanya Alhamdulillah, mun sameku lafiya?.” “Lafiya klw wlh, ya kuka baro mutanen gida.” “Kowa lafiya klw hajia, since agaisheki sosai da d’awainiya ALLAH yasaka da alkhairi.” “ALLAH sarki ai Bakomai yiwa kaine, ” “Hakane gaskiya angode sosai, yau ALLAH yanufa kun ganemu agarinku waccan rangon saurayinnan naku ya taddomu cikin wannan rana saboda rakinsa sai kace ba namiji ba.” STORY CONTINUES BELOW  “Aikuwa dai ya kyauta tunda gashi yasa anyi zumunci.” “Hakane gaskiya, tofa angode da d’awainiya sosai Ubangiji ALLAH yabiya kuma yasaka maku da mafificin alkhairi.” “Amin ya ALLAH.” Ta amsa masu had’e da miqewa tanufi wajensu Yaya Maryam ta barsu nan tare dasu dady suna qara gaggaisawa. “Hajiya sannunku fa da hanya, don ALLAH kuyi haquri nabarku zaune ko?” tafad’a lokacin da take qoqarin shigowa inda suke. “Ai babu komai hajia, ya gida munsameku lafiya.” “Lafiya klw Alhamdulillah.” “Ya ‘yan yaye sarakunan raki da jiki, muna zaunenmu yatado damu muda angwayenmu saboda rakinsa.” “To ayi haquri hajia, ba raki bane kewarku ce tayi masa yawa shiyasa shi zazzab’i, gashi kuma tunda kuna son maigidan kun rugo ko kuwa?” “A’a indai mazan rakine mun barmiki namu sun ishemu, mukam dai albarkacin ‘yarmu mukazo gani ba shiba.” Yaya Maryam tafad’i hakan tana dariya. “A’a fa hajia, karfa yazo kugansa kuce baza kubi su alhaji ba ku kunga wurin zama inda maigidanku yake.” Rashida kuwa tunda taji muryar su Yaya maryam take qoqarin fitowa Fatima tariqeta had’e da cewa tabari sugama gaisawa tukuna suma sufita gaishesu. Muryar ammie sukajiyo tana qwalawa Fatima kira da sauri tamiqe had’e da amsawa sannan tacewa Rashida tazo sutafi. Tare suka fito da gudu Rashida taruga qiris kad’an ta ture fatima tana fad’in “oyoyo gwaggona nayi kewarki sosai.” Dariya duk suka aza mata Yaya Maryam nafad’in. “Oh ni maryama ko yaushe Rashida zakiyi hankali.” “Kai gwaggo da hankalina fa, kawai dad’i nakeji naganku, ina su baba?” “Gasucan awancan d’ayan falon ammie tabata amsa tana mamakin irin sakewar da tayi, amma d’azu gaba d’aya tabi duk ta takura, sai alokacin Rashida ta tuna da ashe ammie nawajen cike dajin kunya tamiqe tanufi inda su baba balarabe suke cike da farinciki. Murmushi Fatima tayi lokacin da take qarasowa wajen tana girgiza kai tare da duqawa tagaishesu tana yimasu sannu da zuwa. Bayan sungama gaisawa ammie tace. “‘yata jeki kikira umma tazo takawo masu Nuraddeen, naga matan nan nasa sai hararata sukeyi.” Gaba d’aya sukasa dariya suna fad’in. “A’a hajia indai wannan maigidan nakine mai kukan yaye mun barmiki kiyita kaya basai yazo ba.” Suna rufe baki umma nashigowa d’auke dashi yana wasarsa cike da gwalamniya, kasancewar taqofar baya tashigo yasa Rashida dake qoqarin fitowa daga wajen su baba balarabe tana dariyar labarin da suke bawa dady nata lokacin da aka yayeta tayi ido biyu dasu, kasancewar bataga fuskar umma daidai ba saboda tajuya tana yimasa wasa should kad’ai tahango gasu ammie a tsakiyarsu tasan bazata rasa ganinta ba yasa tayi saurin sadda kanta qasa, can kamar an tsinkaleta tayi saurin d’ago kanta tunawa da gefen fuskar wacce tagani, turo idanuwa tayi ganin wai ummanta ce agabanta d’auke da little, jitayi lumfashinta na neman d’aukewa da sauri tace. “Um..um..ummah..” tana nunata da hannu, Da qarfi umma ta d’ago kai jin muryar ‘yarta tilo da bazata tab’a mantawa da ita ba, yayinda gaba d’aya su ammie suka miqe suna kallon abunda ke shirin faruwa, Ganin umma na neman sandarewa a inda take tasaki little yasa Fatima qarasawa da sauri takarb’esa tana kallon ikon ALLAH, Rashida da tuni hawayen farinciki suka jiqa mata fuska tafara takowa cikin rashin kuzari jikinta har wata tsima yakeyi cikin rawar murya tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Um..mata ni..ni..ce Rashida, nice Rashida ‘yarki data b’a..b’a.ta.” Kafin taqaraso tuni qafafuwanta suka kasa imata tafad’i qasa tana kukan da babu shakka zata iya cewa na farinciki ne, haka umma gaba d’aya kasa motsawa tayi saboda qafafuwanta da suka yimata nauyi Saida taji su Yaya Maryam sunce. “Aisha..” atare sannan tasamu wani irin qwarin guiwar qarasawa wajen ‘yar tata dake jan qafafuwa tana neman isowa inda take ta rungumeta tana wani irin kuka mai cike da ma’anoni kala kala, “Ina kika tafi Rashida kika barmu, munyi kuka mun shiga damuwa marar adadin duk ta dalilin rashinki, Ina kika tafi baki nememu ba kika sa gaba d’aya mukabar kowa namu Rashida saboda rad’ad’in rashinki akusa damu?.” Kasa amsawa Rashida tayi sai sake naniqe mahaifiyarta takeyi cikin jiki tanajikamar lumfashinta zai fita saboda tsabar farinciki, daqyar tasamu cikin wata irin murya mai ban tausayi tace. “Kuyi haquri, kuyu haquri umma, son zuciya da biyan buqatar rayuwa tasa aka rabani daku, akanisantani da farinciki na aka nemi salwantar da rayuwata batare da andubi halin da nake ciki ba, saidai tsananin addu’arku agareni ya kubutar dani ga shiga duk wani irin gararin rayuwa, ya haskakamun dukkanin lamurrana, ya damqani a hannayen da babu son zuciya balle son kai acikin al’amurransu, d’ago kai umma tayi fuskarta jiqe da hawaye tariqe fuskarta tana goge mata hawaye da manyan ‘yan yatsunta. “Kidena kuka ‘yata, muyi godiya ga ALLAH daya sake had’a fuskokinmu ba tare da yad’au rayukanmu ba, haqiqa dukkanin bawan da yayi Imani kuma yayi haquri ubangiji bazai tab’a bari ya tozarta ba.” “Hakane umma, nayarda da ALLAH shike jarabta rayuwar bawansa kuma yayi masa mafi qololuwar sakayya alokacin daya maida dukkanin al’amurransa agaresa, nayi kuka mai yawa lokacin dana koma agareku ban taradda kuba, saidai yau dukkanin kukana yaqare umma tunda gani gaku.” Tare suka juya suna fuskantar alqiblah had’e dayin sujudush shukur sannan suka juyo Rashida ta sake rungumeta tana fad’in. “Ummahhh nayi kewarki” Murya suka jiyo a bakin qofa ana fad’in, “Ummanki kad’ai kikayi kewarta bada abbanki ba ‘yata?.” juyowa Rashida tayi daqarfi jin muryar mahaifin nata dake tsaye fuskarsa jiqe da k’walla yana takowa izuwa garesu yana bin ‘yan uwansa daya gani a tsaitsaye da kuma ‘yar tasa tilo da tuni yagama fidda ran cewa zasu sake had’uwa, “Babaaa..!” Rashida tafad’a tare da rugowa da gudu tayi tsalle ta hayesa had’e da rungumesa, wani irin sanyi taji aranta da yasa ta runtse idanuwa tsabar jin dad’i hawaye naci gaba da kwaranyo daga cikin idanuwanta. “Nayi kewarka baba..” “Kika ce?” “Nayi matuqar kewarka sosai babana.” Murmushi yayi cike da farinciki yasa hannu ya goge hawayen dake zubowa daga cikin idanuwansa, sake rungumeta yayi sosai tamkar wanda za’a k’wacewa itama tashige jikinsa tanajin wani farinciki marar misaltuwa atattare da ita. Wannan al’amari da yafaru ba kad’an yasa dukkanin wud’anda ke cikin falon hawaye ba, musamman baba balarabe da Yaya Maryam da sukafi kowa jin dad’in faruwar haka idan aka cire Rashida aciki. Ganin taqi saukowa daga jikin baba yasa baba balarabe da tuni duk suka hallara afalon jin abunda kefaruwa ya qaraso wajen yad’an tulli bayanta kad’an had’e da cewa. “To cikamun d’an uwana haka kada kiqarasamun shi.” Lokaci guda duk sukasa dariya kowane nagoge qwallan da suka zubo masa, rungumesa baba balarabe yayi yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Meyasa d’an uwa?.” Baba daya kasa tsaida hawayen farincikin dake yimasa zarya a fuska yace “Tsarin alqalamin qaddara d’an uwana.” D’agowa baba balarabe yayi had’e da cewa “Baka kyauta ba ko kad’an kuma kada kasake yin hakan?, ko kamanta cewa mu muna buqatarku idan har ku bakwa buqatarmu da har zaku yanke hukuncin guduwa kubarmu batare dakun fad’a mana inda kuka jeba?” Duk da shine Yaya akansa hakan bai hanashi bashi haquri ba, Yaya Maryam kuwa koda yanufi wajenta d’an marin fuskarsa tayi hawaye nazubo mata had’e da cewa. “Zaka sake?” Kafin yabata amsa tasake kaimasa wani d’an marin agefe d’aya tana fad’in. “Zaka sake guduwa kabarmu.?” Cikin kukan farincikin irin son da suka nuna masa yace. “Kiyi haquri Yaya Maryam bazan sake ba.” Yasa hannu yagoge mata hawayen farincikin dake kwance a fuskarsa. Nanfa dady yayi gyaran murya had’e da cewa. 😅 *HOPE YOUR MISSION IS ARCHIVED?* *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/2/2020, 11:31 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___65💎 Nanfa dady yayi gyaran murya had’e da cewa. “Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah, inaga yakamata ace kowa yanemi waje ya zauna hakanan tunda ubangiji ya nuna ikonsa yanda yake so, alokacin da yake so kuma adaidai inda yake so, duk da dai azahirance wannan abun daya faru abun mamakine da kuma ban al-ajabi agaremu saidai bazai kuma hanamu fahimtar ko meye ke wakana awannan wajeba duba da kuma la’akarin yanda alokaci d’aya ALLAH ya dunqule ahalin da muke tunani biyu ne atare damu yakoma ahali d’aya, wannan abun farincikine da kuma murna agaremu, don haka ina mai neman alfarmar kowa yanemi waje yazauna ko don baqinmu da suka shawo hanya na tsawon awanni akwai buqatar ace sunci, sun sha kuma sun huta tukuna sai acigaba da jajantawa juna wannan al’amarin inaga hakan shiya kamata.” Takowa baba yayi zuwa wajen alhaji ubale fuskarsa d’auke da farinciki marar misaltuwa yamiqa masa hannu suka gaisa, murmushi alhaji ubale yayi tare da riqe hannun har suka nemi waje suka zauna yana fad’in. “A gaisheka mai gayya mai aiki.” Juye juye baba yafarayi yana neman Dr nura wanda shine yaje yakirawosa ganin abunda kefaruwa, cike da mamaki ya hangosa ajikin qofa yanad’e hannayensa aqirji yana tunano ranar daya fara ganinsu baba, sai yau yatuna da muryar umma dako yaushe idan yai yake tunanin inda yasanta ashe ta maman boy ce, lalle ALLAH gagara misali ne kuma huwarrahmanu yau yaqara imani akan cewa tabbas duk yanda bawa yakai maqura wajen son had’a abu aikin banza yayi matuqar ba ALLAH da kansa yaso hakan ba, yamatuqar sha wahala wajen neman iyayen rashida don ya had’asu amma ALLAH bai yarda da hakan ba sai yau da yaga dama, sai gashi cikin sakanni ya had’asu da kansa, haqiqa al’amarinsa abun girmamawa ne kuma duk wanda baiyi imanin cewa shi kad’ai keda iko wajen had’awa da kuma rabawa ba, ansa da hanawa, qaddartawa da kuma jarabtawa, iko akan komai aduk lokacin da yake so, ayanda yake so,a kuma inda yake so haqiqa yayi asara duniya da lahira. STORY CONTINUES BELOW  Da hannu baba yayi masa alama da yaqaraso daga ciki sannan yabaro wajen yana murmushi, duqawa yajeyi agabansa da sauri ya rungumesa yana fad’in. “Nagode sosai dr.” Rashida kuwa gaba d’aya ta naniqe ajikin umma takasa bari tamatsa konan da can, so take ta tashi tariqowa ammie abinci ashigo dashi amma itama shauqin soyayyar ‘yar tata yahanta motsawa wajen, gani take kamar inta saketa zata sake dawo ta tadda bata nan, gashi bazata iya barin ammie taci gaba da kaida kawo ita kad’ai ba, don haka sai tamiqe riqe da hannunta kamar wacce za’a kwacewa tanufi kitchen d’in da ita, gaba d’aya falon sukabita da kallo musamman Dr. da yau yamatuqar qara gaskata kamar dake tsakaninta da umma da kuma little dake hannun fatima yana zallo ta d’aukesa da sukazo wucewa taqi. Suna kaiwa bakin qofar shiga kitchen sukaci karo da ammie ta d’auko kuloli da sauri umma tamiqa hannuwa zata karb’a tace. “A’a umma, ai kuma yanzu shikenan wannan aikin yadawo hannun maishi dama taimaka mani ne kikeyi, gashi da alama yau maman boy bazata bari ko lumfashi kiyi ba.” Sai alokacin umma talura da yanda ta k’wak’wume hannun Rashida sosai da sauri tasaketa cike dajin kunya tana karb’ar kulolin hannun ammie sannan tabar kitchen d’in. Ganin ammie naqoqarin d’auko wasu kayan yasa Rashida itama ta taimaka aka jejjere abincin kowa yaci ya qoshi, Bayan sun kammala aka shiga maida maganganu inda Dr yashiga basu labarin adadin mayannun da yayi wajen nemansu da had’uwar da yayi dasu atasha da irin halin daya tsinci Rashida aciki tare da irin ciwon da little yayi tamkar bazai rayuba, duk dasu baffa da daddy sunsan da labarin tawani b’angaren yanzu su baba yake baiwa hakan bai hanasu jin tamkar yanzu suka fara jinsa ba, umma da baba sun zubar da hawayen cike da tausayawa ‘yarsu sosai kafin baba yamiqa hannu yakarb’i little Nuraddeen dake hannun Dr. “ALLAHU akabar, duk wannan abun daya faru anyisa ne saboda kada kazo duniya karayu, amma da yake kai alqawarin ALLAH ne saida ya tsaro fitowarka tahanyar jarabta mahaifinka da mahaifiyarka, haqiqa rashin sani yafi dare duhu sannan alqawarin ALLAH tabbatacce ne ko ana so ko ba’a so, badon haka ba dabanyi kwad’ayin aurar da mahaifiyarka abagiren da ba’a buqatar taba duk da dai nasan cewa matsalar ba daga mahaifin kabane.” ‘Dago kansa yayi had’e da yima Dr godiya marar adadi kafin suma su dady yayi masu godiya sosai shida sauran ‘yan uwansa san mazan suka tashi suka tafi wajen sallah su kuma matan suka tsaya nan part d’in ammie sukayi tasu, Rashida kam bin umma tayi sashenta sukayi sallarsu atare, addu’o’i sosai da washi da yabo umma tayi ga ALLAH tana mai godiya daya maido masu da ‘yarsu agaresu cikin qoshin lafiya, haka shima baba har kowa yafito masallaci aka barosa shikad’ai yanata yiwa ALLAH godiya. Bayan sun dawo suna zazzaune falo ana sake maida firar yaushe gamo can sai ammie dake zaune tare dasu ummu taqara volume d’in makekeyir tv d’in dake laqe a bango tana fad’in. “Alhaji gafa maimaicin shirin da kake so nakiwon lafiya uwar jiki, da baka samu ka kalla jiya ba.” “Af sun fara?” Dady yafad’a had’e da maido hankalinsa ga tv sannan yace. “Ai inaga saidai nahaqura wannan karon tunda banida lokaci, ki saurar inyaso anjima saiki maimai tamani tunda naga kema yanzu kina son shirin.” “Eh gaskiya Ina so saboda akwai abubuwa masu muhimmanci da ake qaruwa dasu ciki ko umma?” Taqarasa maganar tana kallon umma dake zaune ita dasu Yaya Maryam suna fira, Rashida kuwa nacan d’aki ita da fatima da little. Sosai ammie tanatsu tana sauraren bayanin da likita keyi akan wata cuta da matar da ake nunowa wadda ke d’auke da ita su kuma sunaci gaba firarsu. “Yawwa ‘yata zo kiga maimaicin labaran jiya da nakiraki na fad’a maki cewa yau ki kalla saboda it’s very important to all the marry woman.” STORY CONTINUES BELOW  Ammie tafad’a tana kallonsu Fatima dake fitowa daga cikin d’aki, Wata irin qara sukaji Rashida dake bayanta tasaki had’e da cewa. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, umma..uncle.baba.” Gaba d’aya duk tabi duk ta rud’e ta kasa yin magana sai nuna tv takeyi da ake nuno irin yanayin da Yaya hawwa keshiga idan ciwonta ya tashi. Kafin kace me duk sun maido hankalinsu akanta Fatima na rirriqetatana tambayar ko lafiya, yanda sukaga hankalinta ya tashi yasa suka maido hankalinsu ga tv suma suna son fahimtar ko meye dalilin da yasata firgita hakan, iya kallon da zasuyiwa matar da ake nunowa a tv sunyi amma basu gano komai ba saboda da yawansu ma basu santa ba balle su iya ganeta cikin wannan lalurar da take ciki. Saida aka d’au d’an lokaci ammie dake riqe da hannun Rashida jikinta har tsima yakeyi tace. “Alhaji inaga bari akashe kallon nan, domin yarinyar nan jikinta har wani cira yakeyi.” Har tamiqa hannu zata kashe Yaya Maryam tace. “A’a hajia dakata, kibarshi muga irin sakayyar da ALLAH keyiwa bayinsa wud’anda suka cutar da wasu bayin nasa, wannan matar da kuke gani ba kowa bace face surukar Rashida data nemi salwantar da rayuwarta data d’anta saboda son zuciya, ya ALLAH Ina godiya agareka da keke gaggauta yin wani hisabi tunduniya saboda sauran bayinka su wa’aztu.” Wata irin zabura baba yayi had’e da miqewa tsaye yana sallallami yana kallon Rashida don tabbatar da abunda yayar tasu kefad’a, jinjina kai Rashida ta shigayi tana kallonsa itama had’e da cewa. “Baba innar mu ce, meye yasameta haka!?” Tana kuka. “Anya Rashida itace?, Innarku fa kikace mahaifiyar mijinki Nuraddeen? don ALLAH ki kalla da kyau kada kitayar mana da hankali.” “Wlh baba itace, bazan tab’a mantawa d fuskarta ba, innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, nashiga uku umma Ina ya nura yatafi haka yabar Inna acikin wannan halin?, wayyo ni ALLAH baba, meye yasami Inna haka.” Duk wanda ke falon binta yayi da kallo cike da mamakin lafuzzan dake fitowa daga bakinta, musamman Yaya Maryam data soma hasala ganin kukan da takeyi, cikin b’acin rai ta katsa mata tsawa had’e d cewa. “Kirufa mana baki ko inzo intakaki awurin, munji mungani itace, sai akayi me kuma da zaki azawa mutane kuka?” “Haba gwaggo! Haba gwaggo, uwar mijina face!, Surukata kakar d’an dana haifa, taya bazanyi kuka ba tana cikin wannan yanayi, gwaggo kidubi fa yanda takoma, dubi irin wahalar da take sha, don me baza’a tausaya mata tunda rayuwace itama.” “Rashida fita d’akinnan kafin na sab’a maki, gwaggon taki ke fad’a kema kina fad’a?” Baffa yafad’a ransa a b’ace. “A’a bashar, ba dakai takeyi ba don haka kabarni da ita.” Shiru baba yayi had’e da komawa yasamu waje ya zauna jikinsa a mace, haqiqa ubangiji Mai jujjuya al’amurransa ne aduk lokacin da yaso, yau gashi ‘yarsu da akaso ajefa cikin wani hali a haukatar masu da ita ALLAH yakareta ita kuma wacce taso hakan agareta ALLAH yajuyar da al-amarin akanta dama haka rayuwa take _(aljaza’u min jinsil amala)_ sakayya nazuwa daidai da irin abunda ka aikata. Muryar matar baba balarabe hajia Aisha yajiyo tana fad’ar.”Banda abunki Rashida meye na kuka awannan al-amarin? abunda ta aikatane ya koma mata, to tawane dalilin za’a tausaya mata, kiduba adadin mutanen data jefa cikin wani hali fiye da shekara d’aya, su kwana cikin qunci da baqincikin rayuwa duk ta dalilinta, ke kanki da mahaifanki harma damu duka sai yau ALLAH ya yaye mana d’inbin damuwar dake dasqare acikin zukatanmu, taya za’ayi ALLAH yabarta da wud’annan haqqoqa data d’aukarwa kanta batare da anbima bima masu sub?, Ai addu’armu d’aya itace ALLAH yakaremu da son zuciya irin nata.”+ STORY CONTINUES BELOW  “Kar kice hajia mama,” da yake haka suke kiranta. “Dukkaninmu bayi muke ga ALLAH, kuma babu wanda yawuce ajarrabi rayuwarsa da khairan ko kuma akasin haka kuma bawai don namanta da abunda tayi manine ba nake tausayin wannan halin da take ciki, kawai ina tausaya matane saboda darajar haihuwa da tayiwa mijina koba komai ma ai baza’a tab’a canjawa tuwo suna ba, matsayinta na kakar jininku baza’a tab’a kankaresa ba, kuma idan kun duba itama rayuwace kamar mu, wlh hajia mama indai akan abunda ta aikata agareni ALLAH ke azabtar da ita haka nayafe mata duniya da lahira.” Bud’e baki Yaya Maryam tayi da niyar yin magana maigidanta alhaji ubale yayi saurin dakatar da ita. “Haba Maryam, don me zakiyi qoqarin tirsasata bijirewa kyakkyawar zuciyarta, wlh bana tantama akan yarinyar nan bazata tab’a walaqantaba duniya da lahira saboda akowane irin yanayi dake samunta arayuwa takan kasance mai tsarkakakkiyar zuciya da kuma haquri, ni inaga ku k’yaleta, tanda ikon yafewa duk wanda taga dama, tazubar da hawayenta aduk lokacin da take so kuma ta tausayawa duk wanda taga yadace domin ita take da iko akan zuciyarta, kamata yayi kuyi alfaharin samunta a matsayin ‘ya tagari ba kuyi qoqarin chanzata izuwa kangarariyar ‘yaba.” Saida Yaya Maryam tawatsa mata wata iwar harara tukuna sannan tace. “To ai shikenan saita shirya muwuce mukaita wajenta tazauna tayi jinyarta, inaga haka shiyafi kuma shi zatayi tanunawa duniya kyawon zuciyarta da kuma tausayinta.” Murmushi dady da tund’azu ya mayar da hankalinsa ga tv yana mamakin irin yanayin da yaya hawwa take ciki kuma har ahalinta suka tsaya b’ata lokacinsu wajen zuwa asibiti, duk wanda yakalleta da abubuwan da takeyi yasan ba komai ke damunta ba illa matsalar jinnu ce, duk abubuwan da suke fad’a yana jinsu kawai yayi shirune saboda atunaninsa ba huruminsa bane, amma yanzu kalaman Yaya Maryam dake nuni da yanda ranta yab’aci su suka sakashi murmusawa har yake tunanin yakamata yace wani abu awannan gab’ar, musamman idan yayi la’akari da cewa akwai rashin cikakkiyar wayewa atattare dasu wanda yasa har suka iya irin wannan musayar bakin a inda bai kamata ba, kamata yayi ace sun ajiye wannan matsalar a tsakaninsu idan sun koma gida domin sirrin suce amma yanayin qaramcin wayewa dake tattare dasu yasa sun kasa fahimtar hakan. Saida yayi gyaran murya sannan yafara basu haquri akan su ajiye wannan matsalar daga baya saisu zauna su tattauna akanta domin hakan shine sirri agaresu sannan yayi masu nasiha sosai sannan ya sake tayasu farincikin had’uwa da junansu da sukayi. Sai alokacin baba balarabe da duk jikinsa yagama sanyi yayi ajiyar zuciya tare da sake miqa godiyarsu agaresu shida d’ansa bisa taimakon da sukayiwa ‘yarsu da d’an uwansu da kuma matarsa. Saida akayi sallar la’asar sannan su baba balarabe suka kama hanyar komawa, sunso a haukarsu su koma dasu umma da baba amma sai Dr ya roqesu subari idan an kwana biyu sun shirya tsaf sai yawuce dasu tunda wurin aikin sane, Haka suka tafi cike d’inbin alkhairin da dady da ammie sukayi masu suna masu yabawa nagarta irin tasu, haka Dr nura shima ba’a barshi abaya ba don yayi masu alkhairi sosai harda suturu ya siya masu da sauran kayayyakin da zasuyi tsaraba dasu, saida yarakasu har suka fita gari sannan yajuyo ya koma can gida suka shiga tattaunawa da dady akan qudurinsa na mayar da Rashida makaranta da yayi gashi kuma yanzu da alama iyayenta bazasu barta anan ba idan suka tashi komawa. Murmushi dady yayi had’e da cewa. “Haba nura, ai kayi wauta, taya daga baka amanar yarinya zaka d’auko zance maida ita makaranta bayan kasan akowane lokaci zata iya komawa hannun iyayenta, bayan haka karka manta yarinyar nan tanada aure bai kamata ace kai tsaye kana zartar da abubuwa akanta ba, don haka ka ajiye maganar komawarta makaranta, iya taimakon daya kamata kayi kayi basai kashiga hurumin da ba naka ba kaji ko.” “Eh dady.” Yafad’a yana mai yaba hangen nesa irin na mahaifinsa, sai yanzu yafahimci gaba d’aya shirmene yaso tabkawa, nan suka cigaba da tattaunawa akan sauran alamurran dake gabansu kafin akira sallar magrib suwuce masallaci, bayan anyi sallar isha’i yashigo part d’in na ammie Fatima na kwance ta tattake da bargo ita kuma ammie na zaune tana karatun alqur’ani bayan tagama sallah, gaisheta yayi had’e da yimata seda safe sannan yace Fatima tafito suje gida. STORY CONTINUES BELOW  Cikin qarfin hali tamiqe had’e da yima ammie saida safe itama sannan tabi bayansa, sashensu umma suka nufa tana biye dashi, “Sweety don ALLAH kabarni anan zan kwana, gaba d’aya banajin qarfin jikina.” Juyowa yayi had’e da d’an dawowa baya yariqo hannunta. “Kiyi haquri Fatima bazan iya bacci acikin gidan canba idan har bakya nan kuma kinga ammie bazata barni na kwanar mata ad’aki ba da sai inyi kwanciyata anan nima. Cikin qarfin hali tayi murmushi had’e da cewa. “Haba dr! Ai kaima kasan kayi girma da kwanar mata d’aki.” “Ok, to kinga sai kiyi haquri kawai muje gida gaba d’aya tunda nayi girma.” Da haka suka iso sashen dasu umma suke sukayi sallama abakin qofa kafin umma tabasu izinin shigowa, kwance suka isko Rashida bisa qafafuwan umma shi kuma little nagefe yana bacci sai faman firarsu sukeyi hankali kwance, suna shiga ta tashi zaune tare da matsawa jikin umma ta d’ora kanta saman kafad’arta, sau d’aya Dr yakalleta ya d’auke kai had’e da gaisheda umma yana tab’o little dake bacci. “Takwara yau har anyi bacci dawuri ahaka!” “Aikuwa kaganshi nan inba ALLAH yatsare muba sai tsakar dare yatashi ya hanamu bacci da shegen kukannan nasa.” I’m tafad’a tana qoqarin zame kafad’arta daga kan da Rashida ta aza mata, “Maman boy kitashi muje ko.” Fatima tafad’a tana zolayar Rashi don tasan babu yanda za’ayi tabisu. Shiru tayi batare data amsa ba Dr. Yamiqe yana yima umma Saida safe, “Rashida tashi kuke ko?” Yanda Dr. Nura yaga ta shagwab’e fuska kamar zatayi kuka yasa yayi ‘yar dariya had’e da cewa, “Kai maman boy saki fuskarki da wasa Fatima keyi, dama nazo muyi saida safe kuma muga yaronmu don nasan yau babu mai cewa ya rabaki da umman nan taki yasan ko waye ya aikesa.” Dariya duk suka sannan suka wuce bayan itama tayi masu seda safe. Kusan ranar rashida da ummanta zaune suka kwana shikuwa baba masallacin dake cikin gidan yayi tafiyarsa ya kwanta bayan sun gama firar dashi kusan qarfe d’aya na dare. _kuyi haqnayi manage ne nayi maku typing, sai ahankali wlh yikawai nayi, don ALLAH Ina baran addu’arku kada kumanta dani😰🙏🏻_ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/5/2020, 10:02 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___66💎 Kasa bacci baba yayi, inbanda juye juye babu abunda yakeyi, da zaran yarufe idanuwansa babu wacce yake tsinkayowa sai Yaya hawwa da suka gani a cikin tv d’azu, tambayar kansa ya shigayi. Shin meke faruwa da matar aminin nasa kuma surukar ‘yarsa?, shin gaskiyane ita d’ince idanuwansu suka gane masu acikin tv ko kuwa?, Idan har gaskiya ne itace meye silar fad’awarta a cikin wannan mummunan halin da gaba d’aya duniya ta shaida shi, Ganin yakasa samun amsoshin tambayoyinsa ya yanke shawarar isko aminin nashi da shikad’aine zai iya bashi amsarsu, miqewa yayi yafito daga cikin masallacin lokacin qarfe ukku saura kwata yanufi fanfunan dake jikin masallacin yayo arwala sannan yanufi sashensa saboda hasken wutar d’akin daya hango wanda shine ya tabbatar masa da cewa har yanzu su umma basu kwanta ba. STORY CONTINUES BELOW  Knocking yayi abakin qofar d’akin Rashida tagwalo idanuwa waje tana kallon umma da gaba d’aya jikinta yayi sanyi akan labarinsu Dr da take bata na rashin haihuwarsu da soyayyar da suke nunawa little Nuraddeen, yanda tayi da idanuwa yaba umma dariya don kana gani kasan tsorone kwance fal a qasan zuciyarta, jin baba na sake bubbuga masu qofar ahankali muryarsa qasa qasa yana fad’in. “Maman Rashida wace irin firace haka kukeyi har qarfe uku takusa kuna zaune, da haka kutashi kufuskanci ubangiji mana kufad’a masa buqatocinku inaga yafi wannan b’ata daren da kukeyi a banza” Yasa umma saurin cewa. “To malan dama yanzu nake tunanin haka.” “Yawwa to ai yafi, kutashi.” Baba yafad’a tare da juyawarsa yakoma masallaci yana mai fuskantar ubangijinsa yana mai godiya tare da sake miqa d’imbin buqatunsa agaresa. Haka ta b’angaren aunty marwiyya tsabar farinciki hadda sadaka tayi lokacin dasu Yaya maryam suka isa gida suka sanar da ita zancen had’uwarsa dasu umma da sukayi acan garin, rawa tadinga kwasa tanayiwa ALLAH godiya, duk da bata san taya had’uwar tasu ta kasance ba itama harda k’walla tayi. A b’angaren baba balarabe ma bacci yayi yana tunanin ko meye gaskiyar abunda yafaru ga iyalin baffa?, Kenan maganar da d’an uwansa yafad’a masa ba gaskiya bace? Idanko haka ne yatabka babban kuskure abunda yayi masu, Tsaki ya dingayi naba adadi yana ALLAH waddai da zuciyar data tunzurasa yakasa banbance qarya da gaskiya tsakanin maganganun da su baffa suka fad’a masa da kuma wud’anda d’an uwansu yafad’a masa. Matsuwa baba yayi safiya tawaye don yad’au alwashin komawa garinsu saboda sanin halin da aminin nasa keciki, a iya saninsa yasan shi da kansa yace masu susa asako yaya hawwa da d’an uwan nasa da kuma matarsa, yana tsoron kada ace garin d’aukar matakine ya jefa iyalin tasa cikin wannan halin. Tunda akayi sallar asuba baba yagama karanta azkar d’insa ya hau shirye shiryen tafiya, kasancewar dady part d’in ammie yake yasa bayan ya kammala shirinsa yace umma taje ta sanar da ammie yana son magana da dady idan yatashi bacci, yanda yace haka umma tayi sannan tadawo tana goye da little Nuraddeen tace. “Wai malan lafiya naganeka kamar cikin damuwa? Ga alama ko bacci baka samu kayi ba jiya, Kuma yau tunda sassafe kahau shiri, meke faruwa da kaine kuma Ina zakaje?” Taqare maganar damuwa kwance a fuskarta, ganin haka yasashi d’an murmusawa had’e da cewa. “Babu komai maman Rashida, zancen bacci kuwa ai bani kad’aine banyi ba….” “To naji basai ka qarasa ba, amma ina zakaje? Ko yau zamu koma.” “A’a bana tunanin haka domin idan nace zan koma banyiwa alhaji adalci ba don gaba d’aya amanar sabon shagonsa a hannuna ya damqata, zandai je kano ne Ina son in had’u da alhaji Idris akan abunda muka gani jiya dangane da iyalinsa? Kinga bai kamata ace nagani nayi shiru ba matuqar ita d’ince kamar yanda Rashida tafad’a.” “ALLAH ya kiyaye.” Umma tad’an fad’a kamar cikin jin haushi zatabar wajen. “Dakata mana, Ina Kuma zakije muna magana.?” “Ai mungama magana tunda kafad’a mani inda zakaje.” “To meya b’ata maki rai aciki maman Rashida naga zakibar wajen rai a b’ace.” “Bakya son natafi ne?” Shiru tayi batare data tanka saba tana d’an jijjiga little dake mutsu mutsu yana neman tashi, murmushi yayi don yasan dole hakan zata faru, mawuyacin abune ga uwa ta iya manta wanda ya cutar mata da d’a, musamman idan taga ana damuwa da al amarinsa alokacin da shima ya jarabtu sai taga kamar ita annuna rashin so akan nata ne da aka kasa nuna masa haka a lokacin da ake cutar dashi. STORY CONTINUES BELOW  Lumfasawa baba yayi had’e da cewa, ” kiyi haquri maman Rashida abunda zuciyarki ke tunani ba haka bane, iya sanina matuqar zamuyi koyi da mafificin halitta to bazamu rama cuta da cuta ba domin shi yakan rama cuta da alkhairi ne ga wanda yacutar dashi sannan karki manta da irin d’imbin alkhairin da d’an baiwar ALLAHn nan da mijinta suka yimani, koba komi tunda suka qaunaci ‘yarmu sunngama mana komai arayuwa.” “Amma kuma meya biyo baya malan?, Cutarwa da kuma neman salwantar mata da rayuwa, yakamata kafahimci hakan kabarsu suma da tasu jarabawar suji idan akwai dad’i, ‘yarmu aka cutar amma rad’ad’in da zafin akanmu yaqare muda muka haifeta, don haka dole suma suji irin wannan zafin alokacin da take cutuwa duk da kuwa basu ke cutuwar ba.” “Ashsha! Kada kibari ‘yarki tafiki hankali da tunani, karki manta mu da muka shiga cikin tamu jarabawar ai ba qyalemu sukayi ba, qarfinsu, lokacinsu da kuma kud’insu harma da mutuncinsu duka sunyi amfani dasu wajen nuna mana damuwa akan halin da muke ciki, shine yanzu zakice mu muwofantar dasu saboda sun zamo silar cutuwarmu data ‘yarmu?, Kiyi haquri mumanta da abunda yafaru tunda ALLAH ya maido mana da ‘yarmu duk da nasan hakan abune mai wahala amma zamu iya matuqar mukaci gama da yawan tuna alkhairansu.” Sosai jikinta yayi sanyi kuma b’acin ran da takeji akansu yad’an rage sosai, “Shikenan ALLAH yasawaqe yasa kaje lafiya kadawo lafiya.” “Amin ya rabbi, bari naje inaga kiran alhaji ne qilan yafito.” yafad’a yana ciro wayarsa dake ruri a gaban aljihu. Qarasa shiga cikin d’aki tayi shi kuma yanufi sashen ammie. Sida suka gaisa cikin girmamawa sannan yasanar dashi zancen tafiyar da yake so yayi yau, duk da ko kad’an dady baya son yayi nesa dashi haka yadaure yabashi goyon bayan yin tafiyar tare da ciro dubu goma yamiqa masa yace yayi na mota. “A’a alhaji da ka barsu wlh, akwai kud’i a hannuna sosai.” “Ai nasani, ka karb’a ni nabaka kaqara, kud’i ai basa yawa ga matafiyi.” Karb’a yayi had’e da yimasa godiya sannan yami zaifita, har yakusa kai bakin qofa alhaji ya kirasa had’e da cewa. “Am..malan bashar me zai hana kabari zuwa jibi sai mutafi tare don zanje sayo kaya, kasan duk kayan namu sunyi qasa.?” Sosa kai baba yayi had’e da cewa. “Ai da kabarshi alhaji, so nake yau ko gobe in juyo idan ALLAH ya yardar mana.” “To shikenan ALLAH yakiyaye hanya, dama nafi samun natsuwa idan kana kusa lokacin da zan tafi, don ALLAH ka gaishe mana dasu.” “In sha ALLAH zasuji mungode.” Abakin qofa sukaci karo da Dr nura yana qwalawa ammie da dady kira, kallo d’aya zakayi masa kasan cikin farinciki yake saboda wani annuri dake fita a fuskarsa, d’an sunkuyawa yayi yana sosa k’eya ya gaida baba, fad’ad’a murmushinsa yayi had’e da amsa gaisuwar daya yimasa yana fad’in. “Agaida likita bokan turai kuna lafiya?..” Bai qarasa magana ba yaga Fatima na qoqarin shigowa itama tajawo hijab d’in jikinta yarufe mata fuska, ganin yayi tarugo da gudu hango ammie nafitowa tafad’a jikinta tana kuka. “Subhanallahi.. Dr lafiya?” Baba yafad’a yana kallon Dr nura da shikam sai faman washe haqora yakeyi, gaba d’aya 34 d’insa sun kasa rufuwa, Saida ya d’an sinne kai qasa had’e da kallon Fatima ta wutsiyar ido sannan yace. “Baba lafiya klw ku qyaleta kukan dad’i ne takeyi, addu’arku da kuka dad’e kunayi ne ALLAH yakarb’a mana shine fa tunda likita yafad’a take wannan kukan.” “Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah…” Gaba d’aya falon tundaga ammie dake faman rarrashinta har baba da dady suka fad’a atare, sai alokacin Dr yaji wata irin kunya tarufesa da sauri yajuya batare daya qaraso cikin falon ba. STORY CONTINUES BELOW  Maida jiki gabas ammie tayi had’e dayin sujada hawayen farin ciki nazubo mata tace. “Lakal hamdu ala maqadait, walakash shukru ala man a dait, tabarakta ya zaljali wal ikram.” Sannan ta tofa tashafe a fuska. Dady kuwa Banda murmushi Babu abunda yakeyi, nan take yaqudurta aransa zai yiwa baba dake tsaye wata kyauta a matsayin godiyarsa ga ALLAH bisa wannan ni’imar daya yimasu duk dako ba itace ta farko ba, Hajia fareeda wato ammie itace matar dady tafarko kuma uwar gidansa tanada yara uku dashi kuma sune manyan ‘yayansa agidan, Dr nura shine babban d’ansa sai kuma qanensa faruq, saurayine Amma zaikai shekara ashirin da bakwai haka, sannan qanwarsu Khadija dake da shekaru ashirin da hud’u, tayi aure bayan shekaru uku da suka wuce bayan ta kammala karatunta a fannin lafiya wato (nursing), kuma ALLAH ya albarkaceta da samun yara biyu Shahid da Shahida idan kaganesu zaka d’auka tagwayene amma ba haka bane saboda haihuwar rurrutsa tayi, tana ilorin acan take aure saboda mijinta soja ne basu fiye zama waje d’aya ba, yau in suna wannan garin to gobe kuma suna waccan garin, wannan dalilin ne yasa dady cewa ba itace ni’ima tafarko da ALLAH yayi masu ba. Tun daga nan ammie bata sake haihuwa ba kuma hakan bai tab’a damun dady ba, acewarsa sukad’ai idan ALLAH ya raya masa sun isheshi, amma da yake ammie macece mai tsananin alkunya da kuma son mijinta ta tirsasa masa cewa dole sai yaqara aure saboda yasamu qarin zuri’a ita kanta tana sha’awar yara qanana gashi ga dukkan alamu haihuwar ta tsaya mata, don haka tayita rarrashinsa har tasamu ya amince ya auro hajia nafeesa, ‘ya ga amaninsa da suka tashi tare ya rasu yabarsu su takwas ga mahaifiyarsu, rashin wadatar da suke ciki don shi sana’ar noma yakeyi, sai gashi ALLAH yamasa rasuwa yasa dady ke tsananin tausaya masu kuma yake taimakonsu sosai, daga nan ammie tabashi shawarar ya auri nafeesar saboda hakan zai qara bashi damar taimakon ‘yan uwanta sai gashi tazamo butulu ta hanyar walaqanta duk wani dake tare dashi matuqar bayada arziqi, musamman hajia fareeda data d’auka wata maqiyiyarta aduniya. Dawowa cikin falon baba yayi fuskarsa d’auke da farinciki ya taya su hajia murna had’e da fatan ALLAH ya sauketa lafiya sannan yajuya yafita. Miqewa dady yayi shima had’e da cewa. “Dota congrat, ALLAH yakawo mana rayayyi masu albarka.” Sannn shima yajuya yafice, ammie na dariya tasa hannu ta d’ago fuskar Fatima da tayi sharkaf da hawaye tana fad’in. “Kai ‘yata wannan duk kukan farincikine ko kuma na shagwab’a ne akeyiwa ammie ankusa zama mama.” Kasa tanka mata tayi saima faman share qwallar da takeyi tana wasa da gefen hijab d’inta had’e da sissinne kai qasa, karo nafarko kenan arayuwarta data fara jin kunyar ammie irin haka, arayuwa babu abunda take b’oyewa ammie, ta d’auketa tamkar uwar data haifeta da cikinta, hatta wani abun cikin rayuwr aure idan Bata sani ba ita take tambaya tafad’a mata, haka ab’angaren kayan jiki na gyaran mata duka ammie nahad’a mata tabata kuma tayi mata bayani batare da taji kunyarta ba, sai gashi yau gaba d’aya takasa d’aga kai takalli ammie su had’a ido. Murmushi irin na manya ammie tayi had’e da cewa, “ikon ALLAH, karmuyi haka dake ‘yata, kisaki jikinki ni mahaifiyarkice don haka dena wani jin kunya akan wannan abun farinciki daya kamata muyi sharing happiness d’inmu atare, let celebrate together my dota bawani abubane, show me how much appy you feel about this, i will support you and make you enjoy it better kinji ko?.” Ahankali tad’ago kai tana kallon ammie hawaye nazubo mata afuska. “I couldn’t believe ammie, ammie ashe nima zan haihu ba juya bace ni kamar yanda ake fad’a, Ashe nima zan zama uwa am…?” Kasa qarasawa tayi sakamakon kukan farinciki da yaci qarfinta, Bata tab’a kawowa kusa cewa zata haihuba, Bata tab’a sama ranta tana da ciki ba duka da dai Bata tab’a cire tsammani da rahamar ALLAH ba, ako yaushe cikin sa rai take komai daren dad’ewa zata haihu itama in ALLAH ya yarda. STORY CONTINUES BELOW  Cike da tausayinta ammie tajawota ajiki ta rungume tana fad’in. “Ya isa haka ‘yatah, just blieve it, dama haka ALLAH yake, yakan lullub’e bayinsa da rahamarsa a lokacin da basu tab’a tsammani ba, kuma yakan dubi zukatan bayinsa da sukayi Imani dashi suka kyautata al’amurransu ya share masu hawayensu, wannan shine abunda nayita fad’a maki cewa idan lokaci yayi bazato ba tsammani zakiga abun kamar qyaftawar gira, Kuma nafad’a maki tunda dai har akece lafiyanki qalaw to kiyi haquri domin SANNU SANNU bata hana zuwa….gashi naki ALLAH yakawo ijaba har kin iso ko kuwa?” Tafad’a tana d’an turo idanuwanta kad’an tana dariya alamar tana jiran amsa. Jijjiga kai tashigayi alamar tabbatar mata da cewa hak ne ammie tace. “To mugodewa ALLAH ba kuka zakiyi ba kinji ko?, Yanzu fad’amun me kike son ci?” Rufe fuska tayi ammie nadariya tamiqe tana fad’in. “Ko zakici wainar fulawa nayi maki?” Ta girgiza kai had’e da cewa. “A’a ammie eba dai zanci.” Turo idanuwa ammaie tayi had’e da cewa. “Tofah, kice maigidan nawa d’an yarbawa ne?” Duk sukasa dariya harda Dr nura da tun d’azu ke tsaye abakin qofa yace. “Ai kuwa ammie da yaci sunan qudusu” yafad’a kamar yanda yarbawa ke kiran sunan suka sake sa dariya atare, can batare daya ankareba ammie takamo kunnensa had’e da murd’ewa tana fad’in. “Son yanzu rashin kunyarka har yakai da kanka kake fad’an ‘yata nada juna biyu kuma ka taso mani ita agaba, To Ida cikashe rashin kunyar taka ka fad’amun ko how many month ne?,” Fatima na ganin haka ta tashi tashigewarta bedroom d’in mom tana murmushi, komai na surukar tata cike yake da burgewa da kuma ban sha’awa, ko kad’an batada wata matsala komai nata tanayinsa da cikakkiyar wayewar da babu qazanta acikinta. “Awwwshhh..ammie da zafi fa.” “Nasani mana, bakai rashin kunya ba?” “Kai mom, albishir nefa nayi maku, ALLAH badon baba ba sai kun cike mani check tukuna zan fad’a, Ashe laifine nayi bansani ba, amma ita data azawa mutane kuka Ina gani sai wani lallashinta akeyi ana murmushi.” Yafad’a yana turo baki sai kace wani qaramin yaro. Murmushi tayi had’e da sakinsa tace. “Srry kaji ko son, tsantsar farincikinne har yayi mani over shiyasa nanemi regesa akanka, congrat soon zaka shiga next level arayuwa, wato mtakin zama uba bayan magidanci, ubangiji ALLAH yayi maku albarka yabamu rayayye.” “Amin ammien mu” yafad’a yana rungumeta. Baba kuwa koda yakoma sashensa acan ya tarar da Dr nura suna gaisaw da umma da Rashida yana basu labarin jiya a asibiti suka kwana saboda zazzab’in daya tasowa Fatima har saida aka qara mata ruwa, baikai ga fad’a masu zancen cikin ba baba yashigo yamiqe zai fita baba ya tsayar dashi yake sanar dashi batun tafiyar da zaiyi kano, nan take Dr yaji tafiyar bata kwanta masa ba, yayi iya qoqarinsa naganin ya hana baba tafiyar har zuwa banda gobe idan zaije wajen aiki suwuce tare amma yakafe kai da fata shidai ya barshi ya tafi ai yau zai dawo, hakan yasa babu yanda ya iya dole sukayi sallama akan idan zai tafi ya aika Rashida yakirawosa zai koma wajen ammie sai ya ajiyeshi tasha sannan yabar sashen yanajin wani irin. Baba kuwa zaunawa yayi suka sake d’an tab’a hira dasu umma yanata zolayarta wai yanzu idonta sun bud’e tadena kunyar Rashida amatsayinta na ‘yarta tafari ashe b’oyewa takeyi tana sonta sosai sunata dariya. Daga nan kuma yajuya akalar firar tasu izuwa yimasu nasiha akan rayuwar duniya sai kace wanda akace idan yatafi bazai dawo ba, bayan yagama umma tayi ajiyar zuciya had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Malan nifa duk jikina yamutu wlh, nidai don ALLAH kabar zancen tafiyarnan har zuwa wani lokacin.” Murmushi yayi had’e da cewa “Karki manta sau da yawa bama son abu sai kiga ALLAH yasanya alkhairi sosai acikinsa, kika San alkhairan da wannan tafiyar zata jawo mana, qilama ‘yar qanwa zan samomaki shiyasa duk kikabi kika tada hankalinki akanta.” Yaqarasa maganar cikin sigar zolaya yana dariya had’e da miqewa yana d’auke da litte, “Rana nayi bari na hanzarta yau nake son nadawo in sha ALLAH, Rashida jeki kikira Dr ni kam nad’au harma.” Gaban Rashida ne taji yafad’i da sauri tace. “Baba kayi haquri kuwuce da uncle banda gobe.” “Ikon ALLAH, har dake Rashida? Bakyason sanin halin da mijinki da surukarki suke ciki halan?” “A’a baba, ni kawai…” Saurin dakatar da ita yayi tahanyar cewa “maza jeki kice Ina jiransa.” Har takusa fita yakira sunanta had’e da cewa. “Dawo nayi maku albishir ni namanta, maman Rashida matar Dr fa tasamu qaruwa.” “Da gaske baba?” Rashida tafad’a cike da farinciki tare da ficewa da kad’an ma tafad’i garin sauri, umma kuwa Alhamdulillah tace tana fad’in “ALLAHU AKBAR, ALLAH maji roqon bayinsa, kai madalla bari naje nataya hajia murna.” Kusan tare da ita suka fita yana maijin wani sanyi aransa saboda yanayin farincikin da yaga ya bayyana a fuskarsu wanda hakn baqaramin tasiri yayi ba wajen qara masa natsuwa azuciya….. _Godiya agareku masoya masu karamci da halacci bisa bibiyar lafiyata da kukayi, nagode sosai ALLAH yabar tare, maman ameera da ummu sauda ban manta daku ba, kunnuna kulawa agareni kuma jazakumullahu bikhair, fatan alkhairi aduk inda kuke👍🏻_ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/7/2020, 1:07 AM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___67💎 Da gudu Rashida tashiga part d’in ammie tana kiran fatima. “Aunty, aunty..” da kad’an sunyi karo da ammie dake qoqarin shiga kitchen, d’an ja da baya tayi cike da farinciki kafin tasake matsowa kusa da ita tarungumeta tana fad’in, “Ammie kitayamu murna auntynah zata haihu.” Murmushi ammie tayi cike da mamakin irin sakewar da Rashida tayi dasu tsakanin jiya da yau sab’anin yanayin da take ganinta abaya, tabbasa iyaye wani jigone da rashinsu kan kawowa ‘ya’ya tawaya maigirma arayuwa, “Iyyeeeeee….to ina tayaku murana kice little yakusa zama big zai samu d’an qane..” Ko qarasa maganar ammie batayi ba Rashida ta saketa tanufi bedroom d’in ummie don tasan tana ciki tunda bata ganeta a falo ba, girgiza kai ammie tayi tana kallon Dr nura da yabi Rashida da kallo cike da mamakin tsantsar farincikin da yaga tashiga, juyowa yayi suka had’a ido da ammie yace. “Gaba d’aya ta canza tsakanin jiya da yau, kinga farincikin dake tattare da ita ammie sai kace wacce aa biyawa makka.” “Haba son!, ai dole tayi farinciki, iyaye fa rahamana sosai ga kuma wannan batun data tsinta alokaci d’aya, matuqar ita d’in masoyiyar kuce dole kaga fiye da wannan farincikin atattare da ita, ni yarinyar na burgeni sosai saboda sanin yakamatar ta” STORY CONTINUES BELOW  “Ehm..gaskiya hakane, Rashida kam akwai hankali.” Da gudunta taqarasa shiga cikin d’akin tafad’a jikin fatima dake zaune bakin gado ta tallafe fuskarta da tafin hannuwanta guiwowinsu na akan cinainanta. “Yeeew…auntay na congrat, agaskiya Ina cikin farinciki marar misaltuwa ayau, bayan duk wasu fad’i tashi da suruttan mutane yau ALLAH zai bamu namu d’an, Ina farinciki sosai auntynah ALLAH ya inganta yaraba lafiya.” Duk wannan surutun da Rashida keyi cikin farinciki Babu abunda Fatima keyi in banda kallonta, d’aga mata idanuwa Rashida tayi tana juya hannunta had’e da cewa. “Me akayi ne aunty?” Rungumeta tayi tajawo hannunta ta d’ora akan cikinta tana fad’in. “Maman boy I can’t believe so soon zan haifa maki baby, thank you so much for supporting me, haqiqa babu abunda yakai qarfin addu’a tasiri arayuwa, nagode bisa addu’o’in da kika d’orani akai da kuma wud’anda kikeyi mani ba dare ba rana, tabbas anasamun warakar kowace irin matsala tahanyar jajir cewa dayin addu’a, ALLAH ne yace anemi maganin kowace irin matsala amma ana samun warakane bisa qarfin addu’o’inmu agaresa, maman boy kinzamo wani haske acikin rayuwarmu da bazamu tab’a iya mantawa dake ba, yanda kika faranta mana kema ina roqon ALLAH daya faranta maki acikin dukkanin lamurrank, Ina miki albishir da cewa idan ALLAH ya saukeni lafiya zamuyi maki takwara da yardar ALLAH idan aka samu macce, wannan shine tukuicin zamowarki sila wajen tsaida hawayen da muka dad’e suna yimana kwaranya a idanuwa.” Taqarasa maganar had’e da riqo hannayen Rashida ta d’ora saman idanuwanta dake fitar da qwalla. “Kai aunty meye haka kikeyi?, Haba ya isa kidena wud’an maganganun don ALLAH, dukkaninmu ALLAH yakamata mumiqa godiyarmu agaresa, inada tabbin dama lokacin da zaki haihu yayi koda kuwa banbaki wud’an nan addu’o’inba, kawai sun zamo silane bisa wanzuwar qudurar ALLAH agareki, don haka kidena damuwa akan wannan, koda babuni acikin rayuwarku zaki haihu kamar yanda ALLAH ya tsaro, ita addu’a da kike gani ai makami ce babba da idan bawa yariqa duk nisan lokaci zai riskesa da yardar ALLAH.” “Zancen yimani takwara kuwa ALLAH ban yarda ba, sunan yazama local, ni kaina dariyarsa nakeyi wani lokaci.” “Commonnnn…” Fatima tafad’a tare dakai mata d’an duka agefen hannu tanaci gaba da cewa. “Waya fad’a maki sunanki local name ne, ai sunan Rashida da kike gani sunane mai girma, is drive from the one names of ALLAH dt’s (AL-RASHID), Ma’ana mai shiryarwa, asalin sunan ubangijine sai akayi amfani dashi ta hanyar qara harafin (a) yazama (RASHIDA) sai ma’anarsa ta tashi daga Mai shiryarwa zuwa shiryayyiya, don haka kiyi alfahari da sunnki akoda yaushe, domin sunane da bazai kusuba ga wud’anda sukasan asalin ma’anar inda aka ciro sunan, hikimace kansa iyaye nasakawa ‘ya’yayensu ire iren wud’annan sunayen saboda fatan ma’anar dake tattare dasu tad’ore akan ‘ya’yan masu.” “Laaa…kinsan ALLAH aunty! Hankalina bai tab’a kawomun wannan tunanin araina ba, atak’aice ma mantawa nakeyi da akwai sunan acikin jerin sunayen ALLAH da har zan iya tsinkayo ma’anar dake tattare da sunan nawa, kawai nidai tunda banji ana yayin sakawa jarirai sunan ba to sunan dane agurina, d’ai d’ai kune acikin yaran dake tasowa nake ji da irin wannan sunan, amma yanzu tunda kinfahimtar dani ma’anarsa da inda aka samo asalinsa Ina alfaharin kasantuwa ta da sunanan RASHIDA.” Gyaran murya ammie tayi abkin qofa tana fad’in. “Agaida qanwar aunty, dama aikoki baban naki yayi shine kikazo kikayi zaunenki?” “Laaa…. ALLAH na manta ammie, bari naje nafad’a ma uncle.” “Zauna abunki, ai ummanki data shigo tayamu murna tafad’a masa gashican har yafita.” “ALLAH shaf ni namanta sai yanzu bari naje nabashi haquri daga nan nayi masa ALLAH yakiyaye.” Tana gama fad’ar haka tamiqe tafita, ammie tace,”Kinga mutuniyarki tasaki jikinta sosai yanzu ko?” “Eh wlh ammie kuma naji dad’in hakan sosai, kinga kafin sutafi zata qara koyamun wasu addu’o’i sosai.” “Wlh ammie tun watan da kika aikamun da wannan ganyen guava kikace mudinga sakawa cikin ruwan tea muna tafasawa muna sha kafin muci komai da safe tun alokacin nafara jin canji da kaina ajikina, ranar muna zaune nida ita sai take cemun akwai wasu addu’o’i acikin alqaur’ani da yakamata na dingayi wud’an annabawan ALLAH sukayi da bai basu haihuwa ba kuma daga baya yabasu, hakan zai taimaka wajen sanya maganin duk da nake amfani dashi yayi tasiri ajikina sosai saboda qarfin addu’a, ammie kamar da wasa ta nunnuna manisu acikin alqur’ani nafarayi, yanzu kimanin watanni biyar inyinsu kenan sai gashi cikin yardar ALLAH ijaba tasauka, tabbas ammie ilimi nada dad’i aduniya kuma yawane dashi da bazaya tab’a qarewa ba sai randa bawa yakoma ga mahaliccinsa, Kuma duk yanda kake taqama dashi sai kaga wanda yafika shi.” “Dama hakane ‘yata, koda kuwa wanda baikai darajarka bane ko kuma yafika zakaga yasan wani abun dakai baka sani ba, duk da nasan wasu daga cikin addu’o’in ‘yata kifad’a mani sauran naji domin inada wata qawa yanzu kusan shekaru talatin kenan bta haihu ba, kuma tana matuqar son haihuwar kamar taqwato, babu gwaje gwajen da batayi ba, qasashen waje kuwa sunje ba iyaka amma har yau ba’a dace ba, kuma duk da hakan bata gaji ba har yanzu tana kan neman magani cike dasa ran wata rana zata dace, zanji matuqar dad’i idan tasamu irin wannan farincikin da ayau muke ciki kuma hakn zaisa nayi alfaharin tarayyata da ita nahar abada.” “Ai kuwa ammie bari nafad’a maki don gab d’aya nahardace su akai, ba ita kad’ai ba, ina fatar duk wanda kecikin irin wannan matsalar ya amfana dasu domin samun waraka kusa kusa matuqar zai dage dayinsu cike da yaqinin ALLAH zai amsa masa.” “To bara nad’auko biro da takarda narubuta ‘yata, kinsan qwaqwalwar taku da tamu yanzu ba d’aiba.” Takarda ammie ta d’auko Fatima tafara karanto mata addu’o’in daki daki kamar haka. ( _Rabbi laatazarni fardan wa’anta khairul warithiyn,_) ( _Rabbana hablana min azwajina, wazurriyaatina, qurrata a’ayunin, waja’alna lil muttaqina imama_) ( _Lillahi mulkussamawati wal’ardi, yakhluqu maa yasha’u, yahabu liman yashaa’u inasan, wayahabu liman yashaa’uzxukur.._) ( _Rabbi habliey minladunka zurriyatan d’ayyibatan, innaka sami’uddu’ah_) ( _Wa’inni khiftul mawaliya minw waraa’i wakanatimra’atiy aaqiran fahabliey minlladunka waliyya_.) ( _wayumdidkum bi amwalin wabanieyn.._) ( _wamaa tahmilu min unsaa wala tada’u illa bi ilmihi.._) ( _izhaa qada amraan fa’innama yaqulu lahu kun fayakuun.._) ( _qala kazalika qala rabbuka huwa alayya hayyinun waqad khalaqtuka min qablu walam taku shai’a_) ( _Yaa zakariyya Inna nubashshiruka bigulaminismuhu yahya lam naj’allahu min qablu samiyya_) ( _Rabbi habli minasswalihieyyn_). ‘Dago kai ammie tayi had’e da cewa. “‘yatah har yanzu addu’o’in basu qareba, naga har nacika takardar nan.?” Saida Fatima tayi dariya sannan tace. “Dayawa ko ammie?, Ai dama mai bid’a dole sai ya daure, balle ace d’an mutum kake so ai Dole sai an nace kuma anjajirce kafin akai ga gaci, ni ada nake ganin yawan addu’o’in amma daga baya da ALLAH yataimakeni na haddace wasu wasu kuma ina dubawa ga takardar dat rubuta mani wallahi sai nadena jin wahalarsu, kinsan ammie abun sa kaine, idan kad’auka da sauqi sai yazo maka cikin sauqi, duk yawannan nasu da kike gani idan natashi da daddare nayi raka’a biyu na sallame nakan maimaitasu fiye da sau goma wani lokacin kuma nakanyi ko sau d’ayane bayan nayi istigfari da washi zuwa ga ubangiji sannan nayiwa annabi salati tare dayiwa ALLAH godiya bisa wasu ni’imomin da yayi mana nadaban. Idan na kammala sai nakoma bacci, wani lokacin tare ma dashi mukeyi gaba d’aya idan anyi sallar asuba rana tafito sannan mukoma bacci, wani lokacin ammie ko sallarma bamayi, arwala kad’ai mukeyi muzauna muna bitar addu’o’in har bacci yana d’an fizgarmu wani lokaci.” STORY CONTINUES BELOW  “Tirqashi! Tabbas ‘yata kunkoma ga Wanda kad’ai ya isa yabaku kuma yabaku, ubangiji ALLAH ya inganta yabaki rayayyi masu albarka, albarkacin miqa wuyan da kukayi agaresa.” “Amin ammie nagode.” ‘Dan hararta ammie tayi akn godiyar data yimata, dariya tayi had’e da cewa. “Natuba ammienmu kiyi haquri.” “Shikenan, ammafa kada kiqara.” “Baran qara ba ammie..” “Shikenan addu’o’in nakirata taturo akarb’ar mata?” “Eh ammie, tun yanzu Zaki aika mata?.” “Eh mana, ai qara abugi qarfe da zafinsa.” “To ammie ALLAH yasa adace, Amma ammie kice tayi duka addu’o’in cike da yaqinin cewa ALLAH zai karb’a mata, kinsan yana d’aya daga cikin abubuwan da kesa ubangiji ya gaggauta amsar addu’ar bawa idan yayita da yaqini.” “Ai zama tayi ‘yata saboda akullum batada burin da yafi wannan, kinga kuwa dole zata dage, bari naje nadubo maki abinda kikace kina so.” Ammie tafad’a tare da linke takardar ta ajiye akan madubi sannan tabar d’akin, miqewa tayi had’e da shafa cikin nata dako motsi bai fara ba tayi murmushi, gaba d’aya ganin ranar takeyi kamar mafarkine takeyi sannan itama tabi bayan ammien. Rashida kuwa koda ta isa baba na qoqarin shiga mota har lokacin little na ahannunsa, qarasawa tayi wajen baba yamiqo matashi, har tamiqa hannu zata karb’esa cike da zolaya yaja baya dashi yana fad’in. “Bazaki bari naje dashi ba nakaishi wajen kakansa, nasan zaiji dad’in ganinsa fiye da irin dad’in da mukaji.” Murmushi Rashida tayi had’e da cewa. “Shikenan baba, kaga nida ummata dasu ammie mun huta da fitinarsa, sai yaje can yad’an tab’awasu baffa da inna Bilkisu suji yanda mukaji.” “Wai hakane mai sunan babansa?.” Baba yafad’a yana kallon little dake faman tafi da hannuwa yana kallonta, dama Dr nura naganin taqaraso wajen yad’an basu waje yana amsa waya, maida kallonsa baba yayi ga Dr da har lokacin wayar yakeyi ya basu baya sannan yace. “Rashida don ALLAH ku kula da bayin ALLAHn nan, mutanene masu karamci da halacci, duk abunda suke so kufisu sonshi wanda kuma basa so to kifisu qinsa, inaso kiriqesu tamkar mu da muka haifeki kuma ki kyautata masu iya qarfinki hakan zaisa kirage wata kunyar hidimar da suka yimana kinji ko.?” “In Sha ALLAH baba, ALLAH yasa kaje lafiya kadawo lafiya.” “Amin ya rabbi, ALLAH yayi maki albarka dake da duka zuriar da zai baki.” Yaqare maganar yana shafa kan little had’e da miqa mata shi yana murmushi. A daidai lokacin Dr yadawo fuskarsa cike da walwala ya shafa kan little had’e da cewa. “Takwara nazata dakai baba zaije?” “Yawwa uncle don ALLAH kuje dashi shima yarakashi.” Karb’arsa yayi yayi sannan yashiga cikin motar yarufe gambun yana qoqarin tada motar tace. “Laaa…uncle congrat, little yakusa samun qane, ALLAH ya inganta uncle yabamu rayayye mai albarka nima narama abunda ake yimani akan d’an wasu.” Batare daya kalleta ba yana key d’in motar yace. “Amin ya rabbi, Thank you so much maman baby, amma ko kunrama bazaku iya ramawa ba kamar yanda muka yimaku ba ko takwarana?” Da haka yatada motar had’e dayin ribas ya juya motar suka fara tafiya, binsu tayi tana d’agama baba hannu shima yana d’ago mata har suka fita, haka kurum saita tsinci kanta da fashewa da kukan da batasan dalilin yinsa ba, Saida ta tsaida kukan sannan tajuya tanufi sashen na ammie, umma tahango jikin qofa tsaye itama taqurawa gate d’in idanuwa tana mai addu’ar ALLAH ya saukeshi lafiya, STORY CONTINUES BELOW  “Umma ya nagaki a nan tsaye?” Rashida tafad’a jikinta ba qwari. “Wlh Rashida nidai tafiyannan tashi bata kwantamun ba, daya bari har sai an kwan biyu tukuna tunda muma jiyan nan muka fita alhinin rashinki.?” “Kai umma, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH zaije lafiya kuma yadawo lafiya.” Rashida tafad’i hakan saboda takwantarwa da umma hankali don ita kanta tanajin ba dad’i akan tafiyar tasa. Dr nura bai baro tasha ba har saida yaga motarsu baba nashirin tashi sannan yanufi inda motarsa take, da sauri yajuyo ya tsaida motar had’e da leqawa tagefen tagar da baba yake yace. “Baba akwai waya a hannunka nasa maka lambata idan ka isa saika sanar damu don hankalinmu ya kwanta.” “Likita kenan! ai inada lambarka tun satin can da alhaji yasaya mani wayar ya saka mani ita, in Sha ALLAH da zaran na isa zankiraku.” “To shiken baba, amma ka kirani sai inga lambar taka nayi saving tunda banida ita.” Nanfa fasinjoji suka fara suruttai suna qorafi akan suna b’ata masu lokaci amma kota kansu Dr baibi ba har saida baba yakirasa yaga lambar sannan yabar wajen, Saida yaga motar tasu tawuce sannan shima yaja tasa ya nufi gida. Ba’afi mintuna talatin da isar Dr gida ba saiga kira ya shigo ga wayarsa, lokacin duk suna zaune kan dining table suna lunch yana faman jinini wai ammie tabiyewa Fatima anyi masu eba kuma shi baya sonta, ita kuma ammie tace dole yacita don ita kad’ai tadafa kuma bazaibar gidan da yunwa ba, hakan yasashi tusa abincin yana wani b’ab’b’ata rai da kumbura fuska sunata yimasa dariya, ganin wayar tasa naruri yaqi d’agawa yasa dady tsaida dariyar tasa had’e da cewa. “Sorry son, qyale dota da ammienka, zamu rama kaji ko.” “ALLAH dady babincinnan na garin kwaki bayada dad’i ko kad’an, ci kawai nakeyi badon Ina so ba.” “Ajiye hakanan, kad’aga wayar da akeyi maka tun d’azu.” Kallon wayar tasa dake famn ruri akaro na uku yayi had’e da qoqarin d’agawa yana fad’in. “Kai, Ashe baba ne ke kira tun d’azu, Assalamu alaikum, Eh nine, eh, yanzunnan fa ta tashi” “What?” Yafad’a da qarfi yana turo idanuwansa had’e da miqewa da qarfi. Hakan yasa su dady sakin cokullan dake hannunsu suna kallonsa. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun.” Shine abunda Dr keta nanatawa kafin yakalli dady dake tambayarsa ko lafiya yace “Dady wai motarsu babace tayi had’ari acan qauyen dake kan hanya idan anfita gari kad’an.” Gaba d’aya sukasa sallami da sauri ammie tariqo hannun Fatima tayi d’aki da ita had’e da kwantar da ita kan gado tace. “‘yata kinkwantar da hankalinki, kinsn yaron ciki kejikinki in sha ALLAH Babu abunda yafaru.” Koda ammie tafito har dady da Dr sun fita. Sallallami tashigayi tana zagayar falo batare da tasan mezata aikata ba alokacin. Gaba d’aya su dady basuyi wta doguwar tafiya ba suka cimma inda akayi had’arin ashe suna fita daga cikin garinne sukayi karo da wata qaramar mota garin drivern ya kauce mata motarsu tayi cikin daji takife, kasancewar lambar Dr nura itace ta qarshe da baba yakira yasa lokacin da aka ciccirosu aka sami wayar ajikin baba da ko qwarzane baiyi ba amma rai yayi halinsa, kallo d’aya zaka yiwa gawarsa kasan mutumen kirkine saboda wani irin haske da qyalqyali da fuskarsa kefitarwa. Suna isa suka isko an jejjere gawarwakinsu agefen titi da sauri suka isa wajen, tsabar yanda hankalin dady ya tashi saida jiri yad’ebesa yayi baya baya zai fad’i Dr ya tarosa, gefe ya zaunar dashi sannan yanufi wajen ‘yan sandan dake tsaitsaye suna korar mutane yayi masu bayani tare da nuna masu gawar baba dake kwance an lullub’a masa ganyen bedi akai ya nuna masu i.d card d’insa ta asibiti, suna tsaye motar asibiti ta iso aka kwashi gawawwakin kusan mutun uku wud’anda suka rasu biyar kuma sun samu raunuka, bayan motar su dady sukabi zuwa asibiti akayi ‘yan bincike binciken da za’ayi ma gawawwakin da zai tabbatar da cewa mamatan sun rasu sukuma wud’anda suka jimu akayi masu treatment sannan akabasu dady gawar baba sukayo gida da ita, STORY CONTINUES BELOW  Baqaramin tashin hankali su baba balarabe suka shiga ba lokacin da saqon rasuwar d’an uwan nasu ya isa garesuba, yayinda Yaya Maryam tadinga sabbatu tana fad’in. “Ba gaskiya bane, jiya mungansa, munhad’u dashi, munyi magana, mun yi fira da maganganu masu tsayi dashi, wara haka duk muna tare dashi taya za’ace yamutu, inaa banyarda ba, bashar bazi mutu yanzu ba bayan jiya jiya muna tare dashi, ya ALLAH kasa wannan zancen ba gaskiya bane, bashar mutumen kirkine, baikamata ace yamutu yanzu ba..” haka tayita sabbatu tana kuka har saida aka dinga rufe mata baki. Nan take baba balarabe da mijin yaya Maryam da wasu ‘yan uwansa sukayi mota d’aya babba suka d’auki hanya cike da alhini. Duk da baba baifi shekara d’aya da watanni acikin garin borno ba babu inda mutuwarsa Bata kaiba, kuma duk wanda yab’ud’a baki fad’ar mutuncinsa da alkhairansa yakeyi, Umma kuwa da Rashida gaba d’aya sun fita hayyacinsu saboda sumar da sukayi, koda suka farfad’o itadai Rashida bata cewa komai si hawaye dake zubar mata tana kallon ammie da Fatima dake faman basu baki. Umma kuwa miqewa tayi tace akaita inda gawarsa take tana so taganesa, rirriqeta ammie da maqwabtanta da suka shigo sukayi suna fad’in don ALLAH tayi haquri kada take, ganin haka yasa Rashida tasowa tace. “Ammie don ALLAH kubarta taje.” Matsowa tayi takama hannun umma tace “Umma zaki iya ganinsa.” Kad’a mata kai tayi tariqe hannunta suka nufi wani d’aki dake gefen sashen ammie da alama d’aya daga cikin d’akunan dasu Dr sukayi zamane, suna kawowa zasu shiga faruq qanen dr yahanasu. “Don ALLAH kuyi haquri idan bazaku iya ba.” yana qara tare bakin qofar idanuwansa cike da qwalla, duk da shi bai fiye shiga shirgin mutane ba saboda haka yake kamar yanajin warin mutane shiyasa baya mu’amala da kowa, amma duk da haka yana mauqar shiri da baba sosai don acewarsa shi mutumne nadaban ko acikin mutane, tasowa Dr yayi yasa hannu yajaye faruq gefe yana fad’in “Umma kushiga matuqar hakan zai rage maku rad’ad’i arai, saidai Ina so kutuna, ba’ayiwa mamaci kuka irin na jahiliya balle ga irin baba da mukeyiwa kyakkyawan zaton cewa ya dace.” Yana gama fad’ar haka haka yad’an ja da baya yabasu hanya yana goge hawayensa, suna shiga sukaga baba kwance anlullub’esa, da sauri Rashida tarirriqe umma tana kuka tare da toshe bakinta. Duqawa umma tayi daidai fuskarsa tayaye lulub’in da aka rufa masa, ayanda taga fuskarsa tayi haske yaqara kyau tamkar yana dariya duk da tana cikin rad’ad’in mutuwarsa yasa tayi farinciki sosai. “Alhamdulillah malan, naji dad’in yanayin dana ganeka aciki, inafatar wannan qanwar dakace zaka samo mani tayimaka kyakkyawar tarba da kulawa kafin na iskoka, tsakanina dakai babu komai sai alkhairi idan ma kuma katab’a yimani wani abun nayafe maka duniya da lahira inafatar kaima baka tafi dani da komai acikin ranka ba kuma ina roqon ALLAH daya tsarowa rayuwarmu haka akan wannan bawa naka daka jiqansa da rahama, kagafarta masa ka amintar da rouhinsa.” Rashida ta amsa da amin. Tana gama fad’ar haka tagoge hawayen idanuwanta sannan tamiqe suka fito, ayanayin da tafito kad’ai idan ka kalleta zaka tabbatar da cewa tagamsu da yanda taga mijin nata kuma tana yimasa kyakkyawan zato.. _karku manta mutuwa wajibice ga duk wanda keraye, azahiri ma idan munyi tunani soyayyarmu ko kuma qiyayarmu ga wata rayuwa bazata hana idan lokacinsa yayi ba ALLAH yakarb’i abunsa balle littafi, dayawan lokuta ALLAH yafi karb’e mana mutanen kirki aduniya fiye da na banza, da son samune nafiso baffa Ali yamutu fiye da baba amma ayanayin labarin mutuwar baba kad’aice zata haifar da rabuwar da Nuraddeen yayi da mahaifinsa har ya girma kamar yanda kuka gani a farkon littafi, Amma matuqar yana raye dattakonsa bazai bari hakan tafaru ba, don haka kuyi haquri da yanda labarin yake plzzz, ALLAH YAJIQAN BABA DA RAHAMA_👏 STORY CONTINUES BELOW  *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/7/2020, 11:33 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___68💎 Saida ‘yan uwan baba suka iso sannan akayimasa wanka aka sallaci gawarsa aka kaishi gidansa nagaskiya, a yanda mutane suka taru sukayi dandazo wajen sallar jana’izarsa kai ka dauka wani riqaqqen mai mulkine ko sarauta ko kuma wani hamshaqin malami, ALLAHU AKBAR, shiyasa akoda yaushe akeson mutum yazama mai sanyin hali da kyautata zamantakewa dtsakaninsa da mutane, duk da baba ba d’an asalin mazaunin cikin garin bane, kyakkyawan halayensa sun biyosa har zuwa qasarsa inda aka rufesa, bayada wani tarin arziqi kuma bai kasance wani sananne ba acikin garin da shekara d’aya kacal yayi acikinsa amma soyayyarsa ga ALLAH da kuma kyautata zaman takewarsa ga mutane yasa ubangijinsa ya soshi kuma yasa al’ummah ta soshi, babban abunda zaisa a kyautata masa zato shine yanda ruwa ke bulbulowa awajen haqar kabarinsa, har kusan sau biyu ana canza masa wani kabarin amma kowane aka haqo haka ake riskarsa, a dole aka d’aukesa akasashi hakanan acikinsu mutane namasu yabawa da ni’imarsa da ALLAH yayi masa tun akabari, duk inda kaduba cikin maqabartar cike yake da mutane ta ko ina da sukazo kawosa. Bayan andawo su baba balarabe sukaje sukaa yimasu umma nasiha akan sud’au haquri da tsarin qaddarar da ALLAH yayi masu akan d’an uwan nasu domin yanda yasamu jama’a suna kyautata masa zato had’e da yima junansu gaisuwa. Kwanan su baba balarabe uku sannan suka fara maganar komawarsu tunda anyi masa addu’ar uku, lokacin da sukaje wajen dady yimasa sallama akan zasu tafi kuma suna son suwuce da iyalan marigayin tunda dama shine jigonsu nazama garin kuma ALLAH yakarb’i abunsa sai dady yayi gyaran murya had’e da sake yimasu gaisuwar rashin d’an uwan nasu akaro na ba adadi sannan yace. “Malan balarabe Ina son in roqeki wata alfarma awajenku idan zaku iya” “Munaji alhaji ALLAH yasa batafi qarfinmu ba.” “Eh to! Banace haka ba amma Ina son ne idan har kun amince kubar iyalan marigayi anan har zuwa lokacin da zata gama takaba, nayi maku alqawarin cewa zan kula maku dasu bisa amana har zuwa lokacin idan ALLAH yabamu aron rayuwa.” Shiru baba balarabe yayi kafin yace to yabari sud’an shawarta tsakaninsa da sauran ‘yan uwansa da suka zo tare, hakan yasa dady miqewa shida dr sukabar d’akin, bayan sun fita baba balarabe ya tambayi ‘yan uwan nasa had’e da kirawo Yaya Maryam da aunty marwiyya dake can shiyar ammie da yake suma wan saheken rasuwar suka iso suda matan baba balarabe sannan yasa aka kirawo suma su umma sukayi shawara, nan take kowa ya amince da hakan don alkhairin da yayi masu bazasu iya hanasa wannan ‘yar qanqanuwar alfarmar ba, umma kuwa dama cewa tayi duk shawarar da suka yanke akai tayi daidai batada ja, don haka koda suka nuna amincewar tazauna d’in batayi musu akaiba asalima yanzu tafijin garin aranta saboda mijinta dake ciki fiye da wancan garin da suka baro, gaba d’aya yafice mata arai batada sauran sha’awar komawa cikinsa. Sosai dady yaji dad’in amincewarsu da buqatarsa yayita yimasu godiya tare da fatan ALLAH ya saukesu lafiya, har bakin motocinsu gida biyu dake wajen gate yarakasu sannan suka wuce shi kuma yadawo gida yana mai jinjinawa qoqarinsu akan amincin da suka bashi. ••• ••• ••• Baffa da baffa Usman kuwa basusan abunda kefaruwa ba har akayi zaman ukkun baba basuda labari akan rasuwar tasa sai bayan kusan sati biyu sannan suka sani, baffa yayi kuka sosai akan mutuwar aminin nasa wanda d’an uwansa yakasa sanar dashi saboda wata ‘yar rashin fahimta data shiga tsakaninsu, babu abunda yafi qona masa rai irin ace ALLAH yasa har ansan inda suka tafi amma akaqi sanar dashi har ta ALLAH ta faru akansa, yamatuqar jin zafi da Kuma rad’ad’i azuciyarsa fiye da abubuwan da suka faru abaya, hakan yasa yaqudurce aransa bazaya koma waiwayarsu baba balarabe ba akan maganar da tasa suka yanke ganawa tsakaninsa da aminin nasa idan har suna tunanin hakan tafarune da son ransa ko kuma da had’in bakinsa har sai lokacin da ubangiji yatashi bayyanar da gaskiyar al-amarin, duk da wannan matakin daya d’auka hakan bai hanashi had’a waau daga cikin ‘yan uwansa mata ba da wasu abokanansa da ‘yan uwansa maza kusan mota biyu sukaje har gida suka yowa baba balarabe gaisuwa, aranar baba balarabe yaji kunyar da bai tab’a jiba aduniya, so yake yakeb’ance da baffa suyi magana amma tsananin b’acin ran dake zuciyar baffa yasa ko bari bayayi su had’a ido dashi balle suyi wata magana, gaisuwa dai ce takawosa kuma yayi masa fatanshi d’aya ALLAH yajiqan aminin nasa kuma ya lullub’esa da rahama, haka sukabar gidan batare daya samu keb’ewa dashi ba ko kad’an, wannan abun yaqara saka baba balarabe cikin nadama da dana sanin abunda yayi don yatabbata shima baffa yayi fushi akan zancen rasuwar da ba’a sanar dasu ba, STORY CONTINUES BELOW  Su baffa nafita nan suka nufi gidan Yaya Maryam da aunty marwiyya suka yomasu gaisuwa, nanma baffa bai nuna masu komaiba banda gaisuwar da sukaje yimasu ba sannan suka koma gida. Suna isa gida baffa yanemi waje yakwanta sboda wani irin zazzab’i daya rufesa, kallonsa matarsa nusaiba tayi had’e da cewa. “Baffa don ALLAH kafidda damuwar wannan abun aranka, karka manta duka mai rai mamacine, koda kasan da maganar ganinsu bazaka iya hana mutuwarsa ba tunda lokaci yayi, haka kuma koda ansanar dakai zancen rasuwarsa dawuri bazaka iya canza komai ba akan abunda yafaru, don haka kayi haquri muma nan duk ita muke jira, babu wanda kezuwa har sai lokacinsa yayi, su day suka tafi basuyi gaggawa ba mukuma da bamu tafi ba bamuyi jinkiri ba, ubangiji ALLAH kasa muyi kyakkyawan qarshe.” “Amin.” baffa yafad’a yana kallon d’an qaramin cikin dake jikinta yataso kad’an, murmushin da yafi kuka ciwo yayi yanajin wani irin zugi aransa, anan yaqudurta azuciyarsa idan ALLAH yasauketa lafiya matuqar namiji tahaifa zaiyiwa aminin nasa takwara, ganin yanda takafesa da idanuwa kamar zatayi kuka tana fad’in. “Baffa kayi haquri kaji.” Don haka take kiransa har yanzu, yayi yayi da ita tadena amma taqi, hakan yasa yaqaqaro murmushin qarfin hali had’e da cewa. “Nusaiba to me akayi naga kina b’ata fuska, ai dole nahaqura tunda yariga ya tafiyarsa, amma inajin rad’ad’in rabuwata dashi sosai,” “To kayi masa addu’a,” “Zanyi masa nusaiba amma kema zakiyi masa takwara idan kika haifi namiji?” Cike da yarinta tasa hannuwa tarufe fuskarta, don har lokacin bata cika shekaru goma sha shida ba aduniya kuma ALLAH ya albarkaceta da samun ciki wata hud’u kenan ynzu da kwanaki, yana matuqar jin dad’in zama da ita duk da zamowarta yarinya da mafiya al-amurranta shirme sunfi yawa, amma takan nuna damuwarta aduk lokacin data ganesa cikin damuwa kuma tana bashi kulawa daidai iya qarfinta naqaramar yarinya dad’in dad’awa ma ladabi da biyayyar da take yimasa badon ‘yan matsalolin dake tattare dashiba dake hanasa samun cikakkiyara natsuwa da yace gaba d’aya bai tab’ajin dad’in rayuwar aure ba sai yanzu, qaramar yarinyace mma tanada kiyayewa sosai wajen iya zama da miji bisa turbar da yake koyar da ita, hakan yasa duk yanda damuwa tayi masa yawa idan yaga hakan zai haifar da tasirinta wajen cutar da yarinyar yake dannewa, hakan yayiko yanzu yadanne duk abunda yakeji yashiga zolayarta tana dariya. Bayan kwana biyu baffa yaje can gidansu baffa Usman ya isko ‘yan sanda sunyi cirko cirko aqofar gidan wai zasu kama muneera akan tafasama wani saurayi dutsi a ijiya har saida ta tsiyaye gaba d’aya. Inspector najida yagani a tsaye jikin motar fuskarta ba walwala tana jira ashiga akamo muneerar, wajenta yanufa tana ganinsa tasaki fuskarta had’e da qarasawa wajensa kafin ya iso, d’an russuna kai tayi tagaishesa had’e da cewa. “Baba ya gida ya kwana biyu?” “Alhamdulillah ‘yata injin dai ko lafiya?.” “Lafiya lau baba, yaron kune yafasawa wani ijiya shine aka kaimana qararsa.” “Subhanallahi wakenan.” “Muneera baba, yarinyar nan batajin magana sau biyu kenan ana kaimana case d’inta amma saboda kai sai nasa asulhunta abun, amma awannan karon dole mukai case d’in kotu.” “Haba ‘yatah, don ALLAH karkice haka ai shi taimako ba’a gajiya dayinsa.” “A’a baba! Haka ya isa batajin magana da yawa, koda zamuyi wani abun dole sai munje kotu da ita.” “Shikenan!, ‘yatah ALLAH ya kyauta, zamu biyo bayanku in Sha ALLAH muji yanda za’ayi.” Har inspector najida tajuya zata tafi sai kuma tasake juyowa ta tsaida baffa tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Baba nikam nace wai yabatun tsohuwar matarnan taka Yaya hawwa, injin tasamu sauqi?.” Saida Baffa ya sinne kai yana d’an sosa qeyarsa saboda nauyin maganar da yaji sannan yace. “Ehmm! Da sauqi zamuce, Amma har yanzu tana kware anaci gaba da bata kulawa aqarqashin jami’an lafiya.” “ALLAH sarki, ALLAH yabata lafiya, kwanakima nayita neman lambarka awayata narasa lokacin da naga ana nuno yanayin da take ciki a tv, abun yabani tausayi sosai sai natuna da zancen bokan da take zuwa wajensa dake asibiti, shaf namanta nakiraka na sanar dakai cewa bayan angama bashi treatment yafarajin sauqi da sati d’aya ashe shima yasamu matsala aqwaqwalwarsa, abun mamaki koda akayi masa gwaje gwaje sai aka samu qwaqwalwarsa lafiya take Amma yanayin abubuwa irin na miyagun mahaukata dake iya illata kowa, asibitin na shirin sallamarsa sai aka samu ya gudu, yanzu haka zaka ganesa akan tituna tsirara haihuwar uwarsa ko akan juji yanacin lalataccen abinci marasa kyau kamar yanda mahaukata keyi a wani lokacin kuma sai kagansa da sutura ajiki yana bin mutane yana bara abashi abincin da zaici, rayuwa yakeyi gatanan dai, shi ba dabba ba kuma ba cikakken mutum ba, hakan yasa nayi tunanin cewa wataqila matsalarsu d’aya da tsohuwar matarka, Ina nufin qwaqwalwarsu lafiya klw take saidai suna azabtuwane ta dalilin miyagun aljanun da suka shiga jikinsu su sukesa sunayin wud’annan abubuwan dakesa anayi masu kallon mahaukata, shine nayi tunanin kiranka nafad’a maka ko zaku koma gwada maganin musuluncine tunda yanzu kusan shekara d’aya da watanni kenan ana fama dana asibitin ba’a dace ba.” Shiru baffa yayi yana maimaita kalaman inspector najida a qwaqwalwarsa, tabbas maganarta akwai qamshin gaskiya aciki dole yayi nazari akanta sosai ko ALLAH zaisa adace. “Shikenan ‘yata in Sha ALLAH zamuyi tunani akan haka nida ‘yan uwana, dama qarfina yafara qarewa akan wannan matsalar tata, kullum cikin kashin kud’i ake, kuma duk da binciken da sukayi akanta suka yad’a aduniya ankasa samun tallafi daga ko ina.” “ALLAH yasawaqe baba, har yanzu ita matar d’an naka ba’a ganta ba ko?” Saida Baffa yayi ajiyar zuciya sannan yace. “ALLAH kad’ai yasani ‘yatah..” Ananma yake bata labarin rasuwar aminin nasa wato mahaifin matar d’ansa, tamatuqar tausayawa tare da yimasa addu’ar ALLAH yajiqansa da rahama, suna tsaye ‘yan sanda suka fito da muneera duk anbubbuge mata fuska saboda taurin kan da tasa wajen kamota, su kansu ‘yan sandan sai nishi sukeyi saboda wahalar dasu da tayi suna sake jibgarta da kulaken dake hannuwansu Inna ruqayya nabiye dasu tana d’ura masu zagi, juyowa inspector najida tayi da qarfi jin zagin da takeyi masu, Inna ruqayya naganin haka ta arta dana kare don bata manta irin azabar da tasha ahannun taba, ana qoqarin tura muneera mota tarugo da gudu ta lab’e bayan baffa da yayi tsaye yana kallon ikon ALLAH tana fad’in. “Wayyo baffa ka ceceni, wlh ba laifina bane, innace tace naje wajen salele na karb’o mata saqo ashe wai iskanci zaiyi dani ya bata kud’i, shine ni kuma na doka masa wani qarfe yafad’a akan wani abu nasamu nayi guduwata, shine akace wai nafasa masa ijiya, don Allah baffa kataimakeni bana son zuwa.” “Yi haquri munneera jeki ku tafi yanzu nida Usman zamu biyo bayanku, Ina shi baffan naki yake?” “Ya gudu baffa, kuma wlh har dashi ke karb’ewa salele kud’i wai zaya aura mani shi ni kuma bana sonsa, kuma baffa ya…” “Ashsha muneera yishiru haka jeki kinji zamuzo yanzunnan?” ‘Bare baki tayi tana kuka had’e da susar kai ‘yan sandan sukazo suka cakumeta tanata tsalle tsalle da ihu suka sakata aciki, yaran anguwa da suka taru sai faman dariya sukeyi, girgiza kai baffa yayi sannan yabar wajen don ya tabbata Usman baya cikin gidan shi Kuma mahaifin nata sakaran wofi da rashin kunyarsa akansu kad’ai ta tsaya yayi guduwarsa… Daqyar baffa Usman da baffa suka samu sukayo belin muneera batare da anje kotu ba saboda ijiyar yaron batayi komai ba amma yace sai ambiyasa kud’insa. STORY CONTINUES BELOW  Don haka sukaje suka kama d’aya daga cikin shanun baffa Ali suka sayar batare da yasani ba aka biya salele kud’insa sannan akayi masu tsakani da ita, sauran kud’in kuma baffa yakai masa, baffa Ali sai faman wasar baki yakeyi duk d’aukarsa a banza aka bashi kud’in, Saida yagama murnarsa sannan baffa Usman yafad’a masa yanda aka samu kud’in, wayyo ranar yini baffa Ali yayi yana d’ebe masu albarka tare da zunduma masu zagi, yaran gida duk Wanda ya matsosa saidai yaji ya falla masa mari yana d’ura masa ashar, daga qarshe da yaji rad’ad’in yaqi d’ebe masa yasa muneera d’aki yasata yayita jibgarta yana tsina yana fad’in sai yafidda kud’in naggensa ajikinta.Baffa Usman dake zaune yana shan fura yayi dariya had’e da cewa+ “Oho dai, inma kasheta zakayi ka kashe ai ‘yarka ce, ayanda kake marar hankalin nan da tunani babu abunda yakamata ace kayi illa kanunawa duniya cewa nagge tafi ‘yarka muneera awajenka, shasha kawai, mudai bazamu doku ba awajenka, ubangiji ALLAH kashiryar mana dakai kada baqincikinka yasa murasa rayukanmu *BAYAN SHEKARU ASHIRIN DA BIYAR* Abubuwa da dama sunfaru wud’anda duk wani mumuni ya ishesa d’aukar darasin duniya matuqar babu ta’bewa da ‘bata acikin rayuwarsa…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/8/2020, 11:21 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___69💎 Musamman acikin rayuwar Rashida da mahaifiyarta da idan kazauna kayi nazari zaka fahimci dalilin daya hana Rashida yin karatu tace aure take so har ta auri Nuraddeen mahaifiyarsa ta turo mata aljanu suka d’auketa suka kawota garin borno, har hakan taja iyayenta suka baro garinsu cikin qaddarawar ALLAH kuma aka sake had’asu gari d’aya da inda ‘yarsu take kuma ta ALLAH tazo ta afku akan mahaifinta da aka tsaro cewa nanne qasar da za’a rufesa, don bayan umma takammala takaba sai dady yasake bijirowa da buqatar d’ansa akan yana son Rashida ta tsaya anan taci gaba da karatu har lokacin da ALLAH zai dawo da mijinta, badon su baba balarabe naso ba suka sake amince masa akaro na biyu bisa sharad’in duk lokacin da mijin nata yadawo dole zata ajiye karatun takoma hannunsu don su mayar masa da ita, wannan dalilin yasa itama umma tace bazata komaba zata zauna da ‘yarta don itama tabata tata gudun mawa wajen cikawa baba burinsa naganin tayi karatu mai zurfi kamar yanda yaso, kasancewar tanada ‘yancin kanta yasa babu wanda ya tilasta mata akan sai takoma suka bisu da fatan alkhairi Cikin sati biyu Dr nura ya ida kammala shireshiren komawarta makarantar tare da sama mata Mai lesson na musamman da zai taimaka mata don j.s.s 3 yace akaita duk da kuwa qoqarinta bai kai can ba, nan take tafara karatu ka in da na’in cikin jajircewa da qaunar cikawa mahaifinta burinsa, Ammie kuwa tuni ta dakatar da umma batun aikin da takeyi mata tasa aka samo mata wata sai ya zamana umma bata aikin komai agidan inba kula da gyara shiyar da suke ba da kwanciya don ko girki ammie kesa ana kaimasu nasu daga sashenta idan andafa, dady kuwa akoda yaushe cikin kulawa dasu da yimasu hidima yake, kwatsam ranar yasami ammie da zancen yana son ya auri umma saboda shidai yana tsananin tausayinta aransa don tunda baba yarasu har yanzu takasa komawa daidai, kuma shi agani sa idan yayi hakan yiyi jahadi sosai tunda batawuce yin aure ba to baiga amfanin tazauna ahaka ba, asalima yana tunanin idan har tanada sha’awar yin aure Wanda zai iya damqawa amanarta kuma yariqeta hannnu biyu, hakan yasa azuciyarsa yaji ya amince d’ari bisa d’ari don tabbatar daya riqe amanarsu hannu biyu kamar yanda ya d’auka, zuciya batada qashi kuma shi kishi gaskiya ne don haka awannan lokacin ammie sai taji badad’i aranta amma saita danne zuciyarta tabashi goyon baya tare da qarfafa masa wajen aikata hakan, STORY CONTINUES BELOW  Kwana biyu tayi tunda dady yayi maganar bata barin su had’u da umma saboda abunda takeji nataso mata aqasan zuciya saboda kada tayi abunda ba daidai ba, daga qarshe kuma tasaki taroqi ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi, Hajia nafeesa kuwa da taji Babu irin maseefar da batayi ba da habaice habaice tun umma batasan abunda kefaruwa ba don bai riga ya sanar da ita ba har tasani, ta matuqar girgiza had’e da nuna qin amincewarta amma ammie tayita lurar da ita da lallashinta har saida ta amince, ba’a wata samu matsala ta b’angaren ‘yan uwanta dana baba ba sboda ganin dattako da cancantar dady suma suka amince, nan take dady yasa aka rushe sashen da take da wasu wurare cikin gidan itama aka fitar mata da part d’inta abunka ga mai arziqi cikin sati biyu aka kammala komai har d’aurin aure ta tare abinta, Duk wannan abun daya faru bisa amincewar Dr da taimakonsa dady yayis hakan kuma dashi har Fatima sunyi farinciki sosai ba tare da wata hiyana ba, Rashida ce kawai kullum take cikin jin kunya tana ganin kamar hakan da akayi ba’a kyautawa ammie ba, bayan duk taimako da halaccin da tayi masu ita da d’anta har saida ammie tazaunar da ita tanuna mata hakan ba illa bane tunda musulunci bai hana ba sannan tafara samun sakewa daidai, duk da ako yaushe idan hajia nafeesa tahad’u da ita har mahaifiyarta cikin jifarsu take da miyagun kalamai cewa wai Rashida tayi cikin shegene shiyasa tagudo suma da abun kunya ya ishesu sun kasa gano uban d’and’an dake cikinta sai suka biyo bayanta, hatta ma little da baisan komai ba kullum cikin kyararsa take tana aibantasa agaban ‘ya’yanta tana kiransa da shege wanda ba’asan ubansa ba, hakan yasa har ‘ya’yanta ma ke kiransa da haka amma da yake baisan komai ba baya damuwa. Haka rayuwa taci gaba Rashida nasamun kulawa da kuma gudun mawa sosai wajen karatunta da ita har d’anta ta b’angare biyu wato dady da kuma Dr, don tuni shima little Dr yasashi makaranta lokacin itama Fatima har tahaihu tasamu qaton d’and’anta suka rad’a masa suna basheer wato sukawa baba takwara, wannan ba qaramar kima da daraja yaqara jawo masuba a idanuwan umma da Rashida harma da ‘yan uwansa, sunyi matuqar farinciki da jin dad’i sosai aransu harma suna ganin aduniya yanzu basuda masoya da suka fimasu su dady da Dr nura ba. Rashida kuwa tun tana dakon dawowar mijinta izuwa gareta ita da d’anta har tacire rai, gaba d’aya ta tattara wata rayuwar aure data tab’ayi abaya dama auren ta ajiyesu gefe taci gaba da karatunta ita da yaronta, saidai duk da hakan daidai da rana d’aya Bata tab’a yarda tayi wani abun da zaya keta mata marta da kuma darajar auren taba har ta kammala secondary lokacin little na primary 2 amma babu wani labarinsa, a lokacin fatima har tayaye basheer da suke kira (abbaty) tasake samun ciki ta haifi ‘yan biyu duka mata saidai rurrutsa ce tayi a tsakaninsu, inda aka barsu da sunayensu na asali wato hassana da hussaina, murna kam awajen Dr da fatima bata misaltuwa, gashi dai SANNU SANNU cikin iyawar ALLAH suma sunfara tara nasu ‘ya’yan da suke matuqar qauna a cikin shekaru uku kacal ALLAH ya arzuttasu da ‘ya’ya uku, Babu wata wahalar reno da fatima kesha saboda Rashida nanan, duk wata kulawa da yaran zasu buqata tana basu tamkar ita tahaifesu. Shekarar Rashida d’aya tana jiran saka makon jarabawar tasu tafito kuma cikin taimakon ALLAH tayi nasarar lashe kowane darasin da kyakkyawan sakamako wato exelent gaba d’aya, ranar da ita har umma sunyi kuka sosai cike da son inama baba nada rai yaga yanda tafara taka mataki na biyu akaratu da kyakkyawan sakamako, godiya kuwa sunyiwa Dr da dady da ammie ba adadi har saida suka farajin kunya. Umma da ammie kuwa bazaka tab’a ganinsu kace kishiyoyi bane domin akwai tsantsar fahimta da mutunta juna atsakaninsu, hakan yaqarawa hajia nafeesa tsanar umma da rashida dama little gaba d’aya. ••• ••• ••• A b’angarensu baffama acikin shekarunne ALLAH ya sauki nusaiba matarsa lafiya saidai ba’a samu namiji ba kamar yanda yaso ALLAH ya arzuttasu dai da samun ‘ya mace kyakkyawa kamarta sak da nusaiba baffa ya rad’a mata suna Rashida, yana matuqar son yarinyar fiye da tunani saboda sunan data zauna, sau da dama yakan tuna da baba da Kuma ‘yarsa Rashida aduk sadda aka ambaci sunan ‘yar tasa da taci sunan Rashida, wannan yasa ko kad’an baya son jin kukanta balle abunda zai b’ata mata rai, hakama gaba d’aya yakasa mantawa da gudan jininsa daya kasa samun labarinsa, lokacin daya tuntubi ma’aikatar da aka turasu qasar waje don qaro karatu akan labarinsa sai suka b’oye masa ainahin halin da d’an nasa ke ciki, domin koda Nuraddeen suka isa qasae waje bayan anbasu wajen zama sai yanemi wayarsa sama da qasa yarasa, gashi gaba d’aya wud’an da aka had’asa dasu zama ‘yan jahohin kudu ne acan nageria babu wanda yasani acikinsu, asalima gaba d’ayansu babu ruwansu dashi saboda shikad’aine bahaushe sai suka nuna mashi halinsu qarara na qyamar jinsin da banasu ba musamman ma ga musulmi d’an arewa duk da kuwa qasarsu d’aya, hakan yasake jefasa acikin wata damuwar akan wacce yake ciki yana son yasan halin da ake ciki anan gida nageria amma bayada waya, kud’ad’ensa ma daya zo dasu gaba d’aya an sace balle yasamu ya sayi wata, wata irin wahalalliyar rayuwa yafarayi aqasar da kud’in ma da zai samu yayi amfani dasu babu, ana haka d’aya daga cikin qabilun da yake tare dasu yafara qoqarin jawosa jiki yana son taimaka masa da sunan tausaya masa, amma azuciyarsa bashine dalilin silar taimakon da yake yimasa ba kawai yana so ya d’orasa akan hanyar da zata hanasa karatune balle yasamu yayi abunda yakawosa har yakoma qasarsa ana alfahari dashi sai dai duk da haka Nuraddeen bai tab’a wasa da karatunsa da tuni suka fara yiba a fannin koyon likitanci na psychiatric musamman idan yatuna da halin daya baro mahaifiyarsa aciki sai yaji yaqara samun qwarin guiwar maida hankali sosai, hakan yasa yazamo kusan shine zakara kuma zaqwaqurin da yafi kowane d’alibi amakarantar, tun daga kan fararen fata har zuwa ‘yan uwansa baqaqe, wannan abun yaqara baqantawa natare dashi rai ganin shi bakowa bane acikinsu amma ace ya zartasu qoqari acikin aji, don haka suka sake d’aukar d’amara wajen ganin sun durqushesa tahanyar jansa ga jiki, sunyi amfani da yawan damuwar da yake shiga wajen ganin sun jawo ra’ayinsa tahanyar zagayawa dashi wajaje masu ban sha’awa da d’aukar hankali aqasar wanda nan take suka fara zuwa club club dashi suna nuna masa hanyoyin shaye shayen qwayoyi da barasa da sunan zasu taimaka masa wajen rage damuwar da take ciki, yau da gobe babu abunda tabari, tun Nuraddeen najin bazai iyayin hakanba har yafara sha’awar aikatawa batare daya ankara ba, akoda yaushe yakan zauna yana qoqarin tunano gida da abunda yafaru sai yaji yakasa tuna komai, sab’anin da da kullum cikin tunaninsa da abunda yafaru tsakaninsa da matarsa yake, wani abu daya sake d’aure masa kai shine yanda bayason tuna qasarsa gaba d’aya balle ahalinsa shiyasa nan take suka samu nasarar juyar dashi yanda suke so, idanma yace zai zauna yatuna wani abu akansa sai yaji kansa na matuqar sara masa da yimasa ciwo, bazaiji yasamu sauqin hakan ba har sai ya d’auki barasar da tuni ya amince da takan rage masa damuwa yasha. STORY CONTINUES BELOW  Gaba d’aya rayuwarsa tagurb’ace amma wani ikon ALLAH babu abunda ya sauya ta b’angaren karatunsa, zai iya sha yabugu sosai sannan yaje aji suyita yimasa dariya yana wartsakewa zaije yanemi topic d’in da akayi yayi reasarch akai kuma nan take yafahimta, idanma yakasa zaije yanemi malamin duk inda yake ya sake yimasa bayani, malamai da yawa na mamakin halin da yaron yajefa kansa aciki wanda shi da kansa idan an tambayesa bazai iya fad’ar daliliba, iya abunda zai iya fad’a akai shine baya son tuna komai akansa, ahalinsa da kuma qasarsa, idan kuma yayi yunqurin hakan to halin da zai tsinci kansa aciki shine zai haifar masa da shan barasa don yasamu magancesa.. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [9/10/2020, 11:15 PM] S WHITE💎: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Masha ALLAH, a gaskiya zafafan comment d’inku akan yanayin da Nuraddeen keciki sun tafasa k’wak’walwata, da banyi niyar cewa komai ba but yazama dole nace wani abun wataqil hakan zaisa kud’an fahimceni, A iya sanina qarfin imanin mutum qarfin jarabawar da ALLAH zai yimasa😅alkawarin ALLAH ne cewa duk wanda yace yayi imani to dole za’a jarabcesa tako ina arayuwarsa don atabbatar da ingancin imaninsa, don haka kuyi haquri da halin da Nuraddeen ya tsinci kansa aciki, ba burina ku karanta littafin ku nishad’antu dashi kawai neba, a’a ina son kutsinci darussan dake cikine tare da fahimtarsu, karku manta alqalamin marubuci bayana ta’allaqa kawai bane akan nishad’antarwa da burgewa, dole yazamo ansamu ilmantarwa, fad’akarwa da kuma luraswa aciki, hakan shi zai bashi damar isar da saqon da ake son isarwa ya yanda yakamata, da fatar nima kun fahimceni yanda yakamata_🥰 Page___70💎 Haka rayuwar Nuraddeen taci gaba da kasancewa acan batare da mahaifinsa sun san komaiba, sukuma jami’an dake kulawa da lamurran karatunsu babu abunda basu sani ba, duk iya matakan daya kamata su d’aukar masa suna iya qoqarinsu amma hakan tafaskara, ganin yana karatunsa yanda yakamata d’abiarsa ce kawai yagagara gyarawa daga yanda take yanzu zuwa yanda take ada yasa suka qyalesa, a qa’ida tsarin karatun nasu shekara shida zasuyo acan sannan su kammala, amma bayan shekara uku zasu dawo gida hutun wata d’aya sannan sukoma su ida qarasa sauran shekaru uku. Lokacin da suka shekara uku acan aka tashi dawowa hutu Nuraddeen kafewa yayi kai da fata shi babu inda zaije, Babu irin yanda ba’ayi dashi ba yace shi gaba d’aya baya buqatar hutun balle har yakoma qasarsa, kasancewar yanada matuqar qoqarin da tun daga d’aliban makarantar har zuwa malanta Babu wanda bai sanshi ba, don haka sai ‘yan uwansa mazauna kano da sukazo tare sukaje suka sanar da wani malamin halin da ake ciki, koda yaje shima yayi masa magana irin amsar daya basu ya bashi, nan take malamin yaje ya sanar da shugabar makarantar da yake macece (Miss Florence Jackson) tasa aka kirawo matashi tayi masa magana, tayi iya juyin duniya akan yabi ‘yan uwansa amma yaqi amincewa daga qarshe ma sai yafara riqe kai irin alamun maganar na neman saka mashi damuwa, don haka sai tace subarshi zatayi magana da jagororinsu na nan qasar zai zauna awajenta saboda su awajensu kowa nada ‘yancin kansa yayi duk abunda yakeso, hakan kuwa akayi gaba d’aya d’alibban da sukaje tare dashi suka dawo gida cike da farinciki zasuga ahalinsu da iyalansu bayan tsawon shekaru uku da suka sharikke awaccan qasar. Baffa nasamun labarin dawowarsu cike da farinciki ya sanar da baffa Usman, Kwana da yini sukayi suna jiran isowarsa gida amma shiru wannan dalilin yasa baffa ya isko baffa Usman har gida cike da damuwa ya sanar dashi cewa tunda sukaga bai iso gida ba to tabbas ba lafiya yakamata suje su tuntub’i manyannasu suji meke faruwa?, STORY CONTINUES BELOW  Ba qaramin tashin hankali baffa yashiga ba lokacin da akayi masa bayanin abunda yafaru na cewa Nuraddeen yaqi amincewa yadawo wai har sai sun kammala karatun gaba d’aya nan da wasu shekaru uku masu zuwa, kusan fad’uwa zaune yayi daga tsayen da yake saida Baffa Usman yayi saurin riqosa, ba abunda kefita bakinsa inba. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, qadarallahu wama sha’a fa’ala.” Tabbas jikinsa yanzu nabashi akwai abunda kefaruwa akan d’ansa wanda aka b’oye masa, Aikuwa daya matsa lallai sai ansanar dashi dalilin da yasa hakan zata faru sai suka sanar dashi gaskiyar halin da Nuraddeen keciki don bazasu iya cigaba da b’oye masa ba a matsayinsa na uba awurinsa kuma suka sanar dashi cewa yana cikin qoshin lafiya sannan kuma yana maida hankalinsa ga karatunsa sosai don haka yakwantar da hankalinsa. Awannan ranar gaba d’aya guiwowin baffa saida suka sare had’e dayin sanyi kuma ya yadda cewa tabbas rayuwar mumini kullum cikin jarabta ta akeyi, idan yafita wannan jarabawar sai kuma wata takunno kai, yashiga kwararo addu’a ALLAH yabashi qwarin guiwar da zai rinjayi zuciyarsa har zuwa lokacin da ALLAH zai canye dukkanin jarabawowinsa. Bayan sun dawo suna tsaye a qofar gida suna tattaunawa akan yanda zasu b’ullowa matsalar, baffa Usman nata rantsuwa cewa tabbas koma meye akwai abunda badaidai ba don yayi imanin bazai tab’a aikata abubuwan da akace ba, idanko har gaskiya ne to tabbas bayin kansa bane, Ashe duk abunda suka fad’a Inna ruqayya da zata fitowa tajisu don haka sai takoma cikin zaure ta lab’e tana saurarensu. Tsabar farinciki da jin dad’in abunda kunnuwanta suka jiyo mata nassa taji wani irin sanyi azuciyarta kuma ta gamsu cewa tabbas haqarsu ta cimma ruwa kuma abunda suka dad’e suna dakon jira amatsayin fansar da suke son d’auka ya tabbata, fasa fitar tayi takoma cikin gida fuskarnan tata tamkar ambiya mata makka tashige d’aki tana tiqar rawa had’e da cewa da SANNU SANNU zakuga aikina da ciwa, kad’an kuka gani ai indai ina raye saina qumsa maku baqincikin da kuka qumsa mani nida ‘yata akan yaronku, tashi baffa Ali da bai jima da kwantawa ba yayi yana kallonta cike da mamaki, dama dawowarsa kenan daga d’aukar hatsinsu da suka girbe ta tambayesa kud’i ya hanata shine tafita tana kumburar fuska wai zataje ta aro wani wuri, sai gashi bata jima da fitar ba yaga kuma tadawo fuskarta d’auke da farinciki tana dabsar rawa, tun kafin ya tambayeta ta shiga zayyane masa abunda taji ‘yan uwan nasa nafad’a akan halin da Nuraddeen keci acan qasar. Nan shima fa yatayata har yana fad’in wai anzo wajen!, sai su baffa sunyi dana sani da nadamar turasa qasar waje yaqaro katu, don bazaya tab’a dawo masu amatsayin wanda yayo karatu ba, sai dai yadawo masu a matsayin d’an iska lalatacce da baza’a iya tab’a banbance tsakaninsa da arna ba tunda suka zab’i turasa can akan aurar masa da ‘yarsa, bayan duk walaqancin da akayi masu da wanda Yaya hawwa tayita masu alhalin ansamu damar da za’a iya aura masa ita, yazama dole yaje yabiya malan bakada imani don yanzu kam yatabbata yayi masu aikin daya dace, fatanshi kawai ALLAH yaqara duhu don girman d’ib. Ashe duk wannan abun daya samu Nuraddeen aikinsu ne, su suka kaishi wajen malamin tsibbu sukace ayi masa asarin da zai lalace kuma idan yabar qasar ya manta da kowa nasa, asamashi tsanar qasarsa gaba d’aya yadena sha’awarta balle ma yatuna da iyayensa ko matarsa, duk wata hanyar da zatasa yaci gaba a dwad’e masa ita hatta karatun da akace zaije yi ya kasa yinsa, aganinsu yin hakan shine kad’ai zaisa su d’aukar fansar abunda baffa yasa akayi masu, fansar da batada wani tushe balle asali. Ba’ayi wata da faruwar hakan ba su baffa sukaje sokoto asibiti wajen karb’owa Yaya hawwa sallama don ba laifi tafara samun sauqi, duk iya qoqarin su naganin ambasu sallama aranar hakan ta cutara daga qarshema sai ankace suje sai bayan sati biyu su dawo, ko kad’an basuso hakan ba amma babu yanda suka iya dole suka koma gida, sati biyu nacika suka sake komawa, awannan karonma saida sukayi da gaske sannan aka basu sallamar, itama d’in da sunan transfer ne akayi masu izuwa asibitin PSYCHIATRIC dake can kano sannan aka d’aukosu da motar asibitin. STORY CONTINUES BELOW  Inna Bilkisu ita tagyarawa Yaya hawwa d’akinta kafin su iso, acan asibitin aka kaisu sukayiwa wani babban likita bayani akan suna son komawa da ita gida sugwada yimata maganin hausa idan ALLAH baisa aka dace ba sai sudawo, cikin sa’a da yake bahaushene kuma musulmi ya amince masu tare dasa hannu akan file d’in nata sannan aka aai aka ajiyesa inda yakamata, kuma ya fad’a masu aduk lokacin da buqatar kawota asibiti takama ba matsala sukawota in Sha ALLAH za’a dubata, data dai takowace irin hanyace ALLAH yabata lafiya, sunyi matuqar jin dad’i bisa karamcin daya yimasu kafin suyi masa godiya suwuce da ita gida. Qwararrin malamai masu ruqya suka samo akayi mata ruqya, inda nan take mugun aljanin dake jikinta ya bayya yana wata qara da kururuwar shi bazai fita ajikinta ba tunda tasa aka azabtar dashi, aka naqasa shi tare da illata masa rayuwa don haka shima bazai gusheba yana azabtar da ita acikin jiki ba har sai lokacin da ruhinta ya rabu da gangar jikinta, babu irin magiyar da ba’ayi masa ba amma yaqi don haka malaman sukaci gaba da yimata karatu ana watsa ma aljanin ruwan magani yana wata irin muguwar qara saboda zabar qonasa da akeyi har saida yaqone tas, nan take jikinta ya saki malaman suka yima ALLAH godiya daya basu nasarar qona aljanin batare daya naqasa taba, sannan suka bada maganukkan da za’a dinga bata tare da tabbatar masu da cewa in sha ALLAH tasamu lafiya musamman idan aka dage da kulawa wajen bata maganin. Cikin iyawar ALLAH da aka dage wajen kula da bata maganin sai gashi tafara samun sauqi sosai, duk wasu kuwace kuwace da wasu caccanza halittarta da akeyi tadenayi, tadena bugu balle maqura, haka kuma tana iya gane duk wanda yazo wajenta maganace kad’ai bata iyayi, yanayin yanda idan Inna Bilkisu tashiga kaimata abinci ko bata magani take kuka hawaye nazuba a idanuwanta shike qara tabbatar da cewa tasamu lafiya, don kallo d’aya zakayi mata kasan cewa ba kukan komai ne takeyi ba illa na tarin nadama, don gaba d’aya cinta, shanta, kula da tsaftaceta duka ita keyi ita da yaranta su Aisha, musamman idan basa komai d’akinta duk suke zuwa azauna ayita fira saboda kada subarta cikin kad’aici, wani lokacin saidai taqura masu idanuwa tayita kallo batare data tanka masu ba, duk da aranta babu wanda take tunani take son tambayar Ina yake kamar d’anta ya nura amma babu bakin magana saidai tazauna tayita kuka Inna Bilkisu na faman rarrashinta da bata magana. Haka baffa ma idan yazo ganinta, Babu abunda takeyi sai kuka wanda kukan ya tabbatar masa da cewa na nadamane takeyi don haka sai yanuna mata tadena damuwa, kamar yanda yafad’a mata ashekarun baya cewa yayafe mata duniya da lahira har yanzu hakanne aransa, Kuma yasa nusaiba ta shirya ranar sukaje tare ya gabatar mata da ita a matsayin matarsa tare da ‘yarsa Rashida da har tafara tafiya, sannan yayi mata bayanin duk halin da d’anta Nuraddeen keciki saboda amatsayinta na mahaifiyarsa ta tayashi yimasa addu’a, ranar Yaya hawwa kwana tayi tana kuka azuciyarta tana roqon gafarar ALLAH da kuma yayewa d’anta halin da yake ciki, tana so ta tambayi Rashida matar d’anta amma ba halin haka domin bataga fuska ga kowa ba da zata iya tambaya, Babu mai d’auko mata zancenta ita kuma babu baki balle ta tambaya. Su baffa Ali kuwa tamkar babusu acikin gidan don sau d’aya sukaje dubata, qarama muneera takan d’anje tadubota wani lokacin shima idan basa nan. ••• ••• ••• Rashida kuwa tuni antaka matakin manyan mata don tuni an takammala karatunta na jami’a aqarqashin kulawar Dr da mahaifinsa, tasha karatu sosai fiye da tunanin mai karatu a fannin law wato shari’a, yanayin yanda tamaida hankali sosai ga karatun yasa tasamu nasara acikin kowane mataki data taka, tanada wata baiwa tamusamman da ALLAH yabata wajen jajircewa ga dukkanin abunda tasa agaba wannane yasa take nasara acikin dukkanin al’amurranta, bayan ta kammala Dr yayi sha’awar sama mata aiki Amma sai dady yahana, acewarsa hakan badacewa bane tunda tanada aure kuma dole amartaba igiyar aurenta sai kuma idan kotu za’aje araba auren tunda har yanzu mijinta bai waiwayeta ba, hakan yasa Rashida tace tahaqura duk da tanada sha’awar yin aikin, Amma har yanzu qauna da soyayyar mijinta na kwance azuciyarta da bata tunanin zata iya rayuwa da wani idan bashi ba, tasha alwashin bazata koma wani auren ba koda hakan na nufin tarabu da mijinta kenan har abada domin gaba d’aya tadena sha’awar auren, don haka sai dady yabata kud’ad’e masu tsoka sosai tafara gudanar da business, acewarsa zaifi kyau ta dogara da kanta domin ba’asan halin rayuwa ba, sosai Rashida tamurje tayi kyau tazama ‘yar gayu, idan kaganta bazaka tab’a cewa wai Rashidar nance ta qauyen yarimawa matar malan nura ba. Ana haka ranar labari ya iso mata cewa ai su Nuraddeen sun dad’e da kammala karatunsu da sukaje yi tun shekarun baya amma shi yaqi amincewa yadawo, zamowarsa qwarare a fannin daya karanta namasu fama da matsalar neorology da gaba d’aya qasar basu tab’a samun d’aliba mai hazaqa kamar saba yasa qasar tariqesa har tabashi goyon baya d’ari bisa d’ari bisa muradinsa da kuma ra’ayinsa, nan take suka bashi aiki tare da yanka masa albashi mai tsoka, ayanayin da yake aciki lokacin koda bazasu bashi komai ba yafi son ya zauna acan qasar fiye da yadawo, da gwamnatin jahar tasu tanemi tsaurara al_amarin qasar ta d’auko maqudan kud’i tabasu, kasancewar yanda qasar tamu idonta yariga ya bud’e wajen ansan rashawa da cin hanci da Kuma rashin sanin ciwon Kai ya sukayi mui basu koma tada zancenba, baffa yayi kuka da baqincikin abun sosai amma daga baya ya haqura yaci gaba da addu’a tare da yaqini akan ko yaushene zai waiwayesu, Yaya hawwa ma duk da bata um balle u’um aranta tana yimasa addu’a tare da fatar ALLAH yadawo dashi kafin ta ALLAH takasance akanta, wannan labari ya matuqar girgiza Rashida duk da aqasan zuciyarta bata gamsu cewa zaiyi hakan ba sai indai akwai wani abu aqasa da bata sani ba, amma koma meye tayi alqawarin zata zauna zaman jiransa komai daren dad’ewa, kwatsam ranar tana kallon BBC news taga ana fira da wani likita mazaunin qasar malesia amma haifaffen d’an qasar Nigeria ne, qura masa idanuwa tayi saboda ganin yanda yake matuqar kama da habibynta amma azuciyarta sai tace shi wannan yafi habibynta qiba da kuma haske sosai asalima daka kallesa kaga d’an gayu wanda hutu ya zauna masa ajiki, badon ma yanayin haskensa dana mutanen can akwai banbanci ba da bazaka tab’a cewa shi ba d’an qasar bane, tana wannan tunanin ne taji ana tambayarsa sunansa… Qara volume d’in tv tayi had’e da juyowa tana kallon yaransu Dr dake zaune suna wasa wato (walida da sultan) wud’anda aka haifa bayansu shahid da Shahida, walida ita ke bimusu twins sunan ammie ne da taci shiyasa ake kiranta waleeda sai sultan shi kuma sunan dady ne aka saka masa ana kiransa da sultan, tace masu suyi shiru, gabanta ne yafad’i jin da tayi likitan yace Sunana…[2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___71💎 Sunana Nuraddeen Idris Aliyu wanda akafi sani da Dr N.I Aliyu wato qwararren likita a fannin lafiya daya shafi matsalolin qwaqwalwa… Waro idanuwa Rashida tayi had’e da qurawa masa idanuwa cike da farinciki, alokaci d’aya tashiga qwalawasu Fatima kira, aunty, aunty, aunty kufito kuzo kugani ga abban little a tv ana fira dashi, pls aunty kufito kugansa, habiby ne wlh, kufito don ALLAH kada agama firar dashi.+ Tadinga fad’a tana k’walamasu kira, ayanda take kiran nasu yasasu fitowa da sauri ba shiri, musamman Dr. Nura har yana shirin fad’uwa sanadiyar tuntub’en da yayi, ita kuma Fatima daqyar take takawa saboda nauyin da tayi, gashidai girma nadad’a tarar masu amma har lokacin haihuwa bata tsaya masu ba tasamu daqyar ta qaraso ciki, Saida takai jikin tv tasa yatsa adaidai gefen da aka nuno hotonsa tana fad’in uncle wannan shine mijina, shine abban little aunty, Dawowa tayi tariqa Fatima tana cewa, kuzauna aunty kusaurari firar da za’ayi dashi, gaba d’aya ya canza saida nakallesa da kyau da sunan sa daya fad’a sannan zuciyata ta gamsu da cewa shid’inne, taqare maganar had’e da zaunar ita saman kujera, kaima uncle kazauna tafad’a lokacin da take qoqarin zaunawa itama had’e da qura masa ido, wani irin farinciki take jin kanta aciki marar misaltuwa, addu’a tadingayi azuciyarta akan ALLAH yasa yafad’i cewa zai dawo garesu nan kusa bada jimawa ba, Wayarta tajawo ta lalubo lambar umma lokacin tarako dady zai fita riqe da hularsa tana yimasa addu’a, kasancewar wayar na nan falo saman kujera yasa umma tad’auko tare da d’agawa, Saida tayi murmushi sannan tace Rashida kuna lafiya, cikin zumud’i ta amsa mata tana cewa umma ku kunna tv a tashar BBC ana fira da mijina, gaba d’aya tamanta da umma take magana saboda hankalinta gaba d’aya na wajen firar da akeyi da Nuraddeen yana bada amsa, jin da tayi umma tayi tsaki had’e da cewa marar kunya yasa takashe wayar tana girgiza kai yasa tayi saurin toshe baki tana dariyar da da zaran ka kalleta zaka fahimci tsantsar farincikin dake tattare da ita taci gaba da kallonta Dady ne yatambayi umma ko lafiya yaga tayi tsaki, tace kabarni da yarinyarnan marar kunya wai ni take fad’awa na kunna tv tashar BBC ana fira da mijinta inba tsabar rashin ta ido ba sai kace mijin nata yadamu da itane, dariya yayi tare da matsawa ya d’auki remote d’in tv dake kunne yana fad’in, to meye abun kunya aciki, idan bata fad’a maki ba wa kikeso tafad’awa?, ko Qaryane tafad’a shid’in ba mijinta bane? yaqare maganar daidai lokacin da yakamo tashar BBC, juyawa tayi zatabar wajen don batasonma ganinsa gaba d’aya dady yariqo hannunta had’e da cewa don ALLAH tsaya suji ko zasu samu wata hujja acikin firar da akeyi dashi wacce tahanasa dawowa, dama tuni ita umma tafara jin haushinsa tun lokacin da suka tsinci labarin cewa yace bazai dawo qasar ba yafiso yayi zamansa acan, shene abun yaqona mata rai har take ganin kamar yayine don yacutar mata da yarinya data kafe kai da qafa saishi duk da yashafe shekaru masu yawa acan batare daya tab’a tunanin waiwayo taba. Babu yanda ta iya dole suka zauna suna kallon fira. Gaba d’aya b’angaroran biyu sun shagala da irin firar da akeyi dashi har zuwa lokacin da ake tambayarsa dalilin daya hanasa komawa qasarsa yabada gudun mawarsa duk da zamowar gwamnatin qasarce ta d’auki nauyin karatunsa da komai nasa har zuwa lokacin daya kammala, yajima shiru yana tunanin amsar da zai bayar amma daga qarshe yace bayada wani dalili, kawai yafi sha’awar yayi zaunensa acan ne, da aka sake tambayarsa cewa ko yayi hakanne saboda kud’in da can qasar za’a bashi anan qasar baza’a tab’a iya bashi koda makamancinsu bane amma bud’ar bakinsa sai cewa yayi koda qasar bazata biyashi ko sisi ba yafiso ya zauna acan, shi kawai baisan abunda yasa hakanba amma yafi son zama acan har iya qarshen rayuwarsa fiye da yakoma qasarsa. STORY CONTINUES BELOW  Tirqashi! Nan take Rashida taji wani dimmmm! akanta tanajin gaba d’aya duniyar tayi mata nauyi saboda maganganun da taji suna fitowa daga bakin wanda zuciyarta tagama bashi aminci da yarda, d’ago kai tayi tana kallon irin yanda yake b’ata rai da nuna damuwarsa qarara afuska adaidai wannan gab’ar wanda farkon fara firar dashi ba haka yake ba duk da akwai sauyesuyen da tagani atattare dashi alokacin na rashin walwala da sakin fuska da ada Bata sanshi daau ba, amma da akazo daidai wannan gab’ar sai taga sauyin yasake lunkuwa atattare dashi, nan take jikinta yayi sanyi tashiga jerowa kanta tambayoyi akan me hakan kalamansa ke nufi?, shin ko yamanta da ita ne?, meye ma’anar zai zauna acan har abada?, Shin a Ina ya ajiye auren nasu?, Idan kuma zancensa ya tabbata meye makomarta?, Meye makomar rayuwarta?, wane hali zata kasance aciki?. Kafin ta lalubo amsar wud’annan tambayoyin sai taji ansake jefo mata wata tambayar da tayi daidai da d’ai daga cikin tambayoyin da tayiwa kanta, shin kamar yanda kafad’a kafi son kazauna acan qasar nahar abada to ya zancen iyalinka da kuma sauran ahalinka?, Sai daya murza goshinsa da yatsun hannuwansa na tsawon daqiqu biyu sannan ya d’ago kansa idanuwansa sunyi jawur yana kallon wanda keyi masa tambayoyin yace iyali? Ahali?, Kamar ya?, Abokin firar nasa yayi d’an murmushi yana jujjuyawa akan kujerar da yake zaune akai sannan yace Ina nufin matarka da ‘ya’yanka, iyaye harma da ‘yan uwa, bud’ar bakinsa ba abunda yace sai iyaye, ‘yan uwa? bansani ba, yaqare maganar cikin yanayin ko inkula. Wata irin razana Rashida tayi had’e da miqewa tana girgiza kai tana ja da baya, tsaye tayi cak lokacin da taji yana cewa mata da ‘ya’ya shi bayada ko d’aya bayan ansake jefa masa wata tambayar akansu, durqushewa tayi wajen tare da fashewa da kuka tana fad’in, Kada kayi hakan malamina, iyaye, mata, ‘ya’ya, ahali duka kana dasu, idan har zaka manta dani baici kamanta da iyaye da kuma d’anka da muka rabu ina d’auke dashi, safe, rana, dare soyayyarka bata tab’a fita azuciyata ba, idan kuwa zakayimun halacci ban cancanci kamanta dani ba balle har kafurta babuni acikin rayuwarka gaba d’aya, duk iya shekarunnan narayune da igiyoyin aurenka akaina batare da nadamu da qananan shekaruna ba ina dakon jiran dawowarka agaremu, na b’ata duka lokacina wajen baka yardata da kuma soyayyata amma acikin qananan mintuna gaba d’aya ka rosamunsu. Wani irin kuka tasaki tare da rugawa tashige d’akinta tasa makulli, adaidai lokacin little Nuraddeen yadawo daga makaranta, ya isko su Dr da gaba d’aya sun kasa motsawa daga inda suke zaune yayi sallama, ganin hawaye daga idanuwan Fatima da tausayin mamansa yasata kuka yasa ya jefar da jikkarsa abakin qofar shigowa falon yazo ya duqa agabanta yana goge mata hawayen tare da tambayarta meyasata kuka, riqo hannunsa tayi tana shafa kansa had’e da kallon tv tana hango kamarsa acikin fuskar Nuraddeen da ake concluding firar da akeyi dashi, tabbas jini jini ne duk da kamannin little gaba d’aya na mahaifiyarsa ne amma akwai na mahaifinsa kad’an atare dashi, ganin tana kallon tv yasa shima yamaida hankalinsa ga tv, qurawa Nuraddeen idanuwa da ake nuno qaton hotonsa had’e dayin d’an taqaitaccen sharhi akan bayanin da yayi cikin firar da akayi dashi, maido kallonsa yayi ga fatima had’e da cewa, wayeshi mama?, Meya samesa naga ana nunosa kina kuka?, Kasa amsa masa tayi saidai Dr nura yace yamaza yaje yacire uniform d’insa yayi wanka sai yazo yaci abinci. A lokacin little nada shekaru goma sha biyar aduniya kuma yana matakin aji na hud’u a makarantar secondary. Umma kuwa murmushin da yafi kuka ciwo tayi had’e da kallon dady tace kagani, kawai ita kad’aice ke hauka akansa, gaba d’aya ya manta da ita balle abunda ke cikinta, dafari na d’auka yanda suka nuna damuwa akanta koda tabbaci suka samu akan tamutu bazasu manta da itaba, nayi tunanin son da suka nuna mata zaisa susamu tawayar farinciki atatattare dasu don nuna damuwarsu akai, amma sai gashi cikin wannan yanayin da ake ciki yasamu qwarin guiwar barin qasar, naji ba dad’i lokacin da aka sanar damu amma marigayi yalurar dani na fahimci hakan ba laifi bane, sai gashi akaro nabiyu da ranta bata mutuba sun wofantar da ita kuma nasan cewa dole zasusan cewa anganeta daga wajensu balarabe da sauran mutanen gari, hakan da sukayi shima babu kyautawa aciki, sai kuma gashi anxo mana da labarin yace bazai dawo qasar saba alokacin da tagama sa burin cewa zai dawo zuwa wajensa, shima d’in banji dad’i ba araina don Babu uwar dake burin ta zauna tana kallon ‘yarta agabanta kuma da sunan tanada aure musamman yanda ake sheganta mata yaro, amma kazauna ka lurar dani cewa ba lallene abunda aka fad’a yatabbata ba, ka hana zuciyata ta gasgata zancen sai gashi yau agabanka, da kunnuwanka ka gani kuma kaji abunda yafad’a da bakinsa, Wai bayada mata da ‘ya’ya gaba d’aya saboda rud’in duniya da abun duniya daya d’ebesa, alhaji shin shima wannan ba gaskiya bane?, shima suruttaine it na mutane kada I gasgata?, STORY CONTINUES BELOW  Sau d’aya kabani gamsashiyar amsa amatsayina na uwa kuma macce dake d’auke da zuciya irin ta d’an adam da batada qashi shin yakamata raina yab’aci kuma naji zafi akan wud’annan abubuwan ko kuwa?, *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___72💎 Shiru Dady yayi gaba d’aya yakasa yin magana saboda yanda jikinsa yayi sanyi akan kalaman da Dr Nuraddeen yayi, yajima zaune yana nazarin maganganunsa dana umma yanaso yagano dalilin da zaisa Dr Nuraddeen yayi hakan, amma duk iya nazarinsa da zurfin tunaninsa kasa samun dalili d’aya yayi da yasa ya aikata hakan, abu d’aya zai iya cewa shine kodai k’wakwalwarsa tasamu matsalane ko kuma rud’in duniya, Amma wane irin abune zaisamu aduniya da sukafi iyayensa da iyalansa da sauran ‘yan uwansa aduniya, yatabbata dole dai akwai abunda ba daidai ba acikin wannan al-amarin, wanda qoqarin gyarashi izuwa daidai d’in baqaramar wahala zaiyiba, dole koma meye yazamo d’aya daga cikin wud’anda zasu fahimci rad’ad’in da umma keji aranta fiye da yace zaiyi qoqarin fahimtar da ita kuma awannan karon, domin hakan zai saka mata wani shakku arai tayi tunanin kondon bashi yahaifi Rashida ba tunda ranta yariga da yagama b’aci, Saida ya sauke wata irin gwauruwar ajiyar zuciya sannan ya kashe tv had’e da kallon umma dake sharar qwalla da gefen hannunta yafara qoqarin bata maganada kuma kwantar mata da hankali, A matsayinki na mahaifiya tabbas nasani dole zakiji badad’i bisa abubuwan dake faruwa domin UWA DA ‘DA sai ALLAH, ayanayin daya fitar da lafuzzansa babu kyautawa aciki ko kad’an kuma beyi adalci ba, mussamman ga iyayen da suka haifesa, anan yakamata kiyi tunani,abubuwane marasa dad’i kefaruwa akan Rashida kikaji ba dad’i aranki to mekike tunani ga iyayensa da suka haifesa daya nunama duniya baisan komai akansu ba alokacin da akayi masa zancensu, wannan abu mai girmane da akwai buqatar ace anbinciki qwaqwalwarsa da zuciyarsa kafin a amince da kalaman da yayi, anawa tsammanin indai wud’annan maganganu da yayi dagaskenke yakeyi to tabbas yarasa hankalinsa ne, idan kuma da hankalinsa yayisu to rud’in duniya ne kuma zaiyi nadama akai ko yaushene, don haka Ina so kiyima Allah kicire komai aranki uma ki kwantar da hankalinki muje can garin iyayen nasa muji ko meye kefaruwa don asamu maslaha aciki. Maslaha! Maslaha dadynsu? Wace irin maslaha za’aje nema awurin iyayen da suka cutar da ‘yar wasu kuma suka nemi gyara rayuwar nasu d’an don ALLAH yamayar masu da aniyarsu?, ai shi ALLAH baya zalinci kuma abunda duk kayi sai anyi maka, saboda haka babu inda zamuje tunda hatta su kansu yanuna baya buqatarsu balle suyi darajar da zasu iyayin wani abu akansa, umma tafad’a cikin b’acin rai da nuna tsantsar baqincikin daya tarar mata azuciya, ganin haka yasa dady ya d’auki hularsa dake gefenta had’e da cewa ALLAH yasawaqe yabar gidan don yasan duk bayanin da zaiyi mata alokacin bazata fahimceshi ba, asalima zai dad’a qaramata wani rad’ad’ine azuciya idan ya matsa mata, duk da shima wani sashe nazuciyarsa nafad’a masa Nuraddeen yayi kuskure mai girma amma acan qasan zuciyarsa yahanasa gasgata hakan domin shi mutumne mai yawan yiwa mutane uzuri. ALLAH sarki rayuwa kenan, shi rashin sani yafi dare duhu, kuma sanin gaibi sai ALLAH duk jarumtar umma da alkunyarta dole zata ajiyesu agefe tayi duk abunda take ganin ya dace akan ‘yar tata tilo da take kallo amatsayin sauran farincikin da yarage mata aduniya, saboda rashin sanin ainahin abunda kefaruwa ga Nuraddeen da batayi ba , ba itaba hatta iyayen nasa dake tare da wud’anda suka aikata son ransu akansa basu san abunda kefaruwa ba, Basu san abunda akayi masa ba har yakoma haka balle ita, abune gaibi dabai bayyana agaresu ba, amma komai nisan dare gari zai waye kuma SANNU SANNU bata Hana zuwa…in Sha ALLAH da sannu ALLAH zai bayyana komai kuma yawarware dukkanin wani qullin da basuda masaniya akansa, ya haskake duhun dake gabansu suka kasa ganosa kuma ya yaye masu duk wani shamakin daya zamo silar wanzuwar wannan qaddararriyar matsalar data cutar masu da d’a. STORY CONTINUES BELOW  A b’angarensu Rashida kuwa little nawucewa Fatima tanufi d’akinta tana bubbuga mata qofa tana kiran sunanta, tanajin yanda sautin kukanta ke tashi alamun tana jinta amma taqi zuwa tabud’e qofar, tasowa Dr nura yayi yadafa kafad’arta ta juyo ya girgiza mata kai alamun ta qyaleta tace amma Dr tana buqatar wani akusa gareta dazai rarrasheta kuma kasan tana fama da matsalar bp nan kada yazo ya tasar mata, jawota Dr yayi yana fad’in, ki k’yaleta babu abunda zai sameta, ahalin yanzu tafi buqatar kad’aici fiye da komai, mubarta tazubar da hawayen shine zai sama mata sassauci azuciya fiye da ace anhanata fitar dasu, wallahi matar Ina tausayin rayuwar yarinyar nan, tun daga lokacin datayi qoqarin sauya ra’ayin mahaifinta akanta yayi mata abunda takeso ALLAH ke jarabtarta har zuwa wannan lokacin, idan tafita wannan saita shiga waccan kuma duka adalilin rayuwar auren da tayi iqirarin cewa tana so, ubangiji nayi mata hakanne saboda yagwada qarfin imaninta agaresa, kinga kuwa tanada dalilin zubar da hawayenta ko don tasamu qarfin canye jarabawarta, sau da dama kukan da mukeyi akan damuwarmu yana taimaka mana wajen yaqi da ita sab’anin shirunmu dake mummukar zuciya har yasanya mana raunin da zamu iya yaqi da damuwar tamu balle mucanye jarabawowin mu. Suna nan zaune afalo har little yayo wanka yadawo fatima tasa shahida da alokacin tanada shekaru goma sha biyu ta zibo masa abinci, Saida yaci yaqoshi sannan yafara dube dube yana tambayar Fatima ina gwoggonsa wato Rashida, don yasan idan tana nan to tabbas bazataji dawowarsa daga makaranta ba kuma taqi fitowa, kasancewar har lokacin bata fitoba balle taci abincin rana yasa Dr yace yaje ya had’a mata abincin ranarta yakai mata tana d’aki, yayi hakanne don yasan ahalin yanzu shikad’aine zata iya saurara kuma ya kusanceta taji sanyi aranta. Shahida ce tayi saurin riqa masa tray d’in daya d’auko da abinci tabi bayansa dashi, sau kusan uku yana qwanqwasa mata bata bud’e ba kafin can yasoma kiranta, gwaggo, gwaggo kibud’e qofa yaci gaba da fad’a yana dukan qofar, tanajin murayarsa da sauri ta taso tabud’e qofar, qura mata idanuwa yayi ganin yanda sukayi ja had’e da kumburewa kafin yajuyo yakarb’i tray d’in ahannun shahida yana fad’in sannu sister, sannan yashiga daga ciki had’e da sake tura qofar da qafa tarufe, Saida ya ajiye tray d’in a saman gado daga gefe sannan yadawo ta gabanta ya zauna, yanaci gaba da kallonta cikin natsuwa yanason karanto damuwarta, little yarone Mai matuqar natsuwa da sanyin hali, koda yatashi baiyi irin qiriniyar nan ta yara ba saboda rashin son hayaniyarsa, yanada matuqar tsinkaya da kuma fahimtar abubuwa da sauri, musamman ga mahaifiyarsa da akoda yaushe yake jinta har tsakiyar ransa, duk da bawata shaquwa bace sosai tsakaninsa da ita saboda gaba d’aya kulawarsa ta ta’allaqane akansu Dr da kuma su umma da ammie, amma yana jinta aransa tun daga lokacin da yasan cewa itace mahaifiyarsa wacce tahaifesa da cikinta, saboda kulawar da yake samu awajensu Dr baisan cewa basune suka haifesa ba sai lokacin da hajia nafeesa taci masa mutunci tare da zazzagesa shida umma, anan ne yagano cewa yanda yake d’aukar ammie amatsayin kakarsa dady kuma kakansa ashe ba hakan neba, umma daya d’auka amatsayin matar dady kawai ashe itace kakarsa, gwaggo kuma itace ‘yarta wato mahaifiyarsa basu Fatima da Dr ba, Cikin natsuwa yace waya b’atawa gwaggona rai haka har ta zubar da hawayen da suka kumbura mani idanuwanta?, d’ago kai tayi ta kallesa sai taji wasu sababbin hawaye sun zubo mata tasake fashewa da wani kukan tare da jawosa tarungumesa, sunjima ahaka kafin tatsaida kukan nata had’e dasa hannu tana share hawayen da suka jiqa mata fuska tana fad’in, kana so kasan wanda yab’atama gwaggonka rai? Da sauri ya d’aga mata kai yana gogen ‘yan hawayen da suka zubo masa sanadiyar kukan da yaga tanayi, wani irin nishi mai sanyi tayi sannan tace dashi, abbanka ne little, abbanka shi yasani wannan kukan da naga kanayi. Cikin farinciki yamiqe yana dudduba ko ina cikin d’akin had’e da cewa, abbana yadawo ne gwaggo? A ina abban nawa yake?, yaushe yadawo ne gwaggo amma kikak’i kirana?, Abba, abba.., ya shiga kiransa yana qoqarin fita. Saurin dakatar dashi tayi tana kallonsa had’e da cewa, kadena kiran sunansa don bazai amsa ba, kadena nemansa don bazaka tab’a ganinsa ba kuma kadena tunanin zaka had’u dashi nan kusa kamar yanda nake fad’a maka don bazai dawo ba, STORY CONTINUES BELOW  Dawowa yayi ya zauna kusa gareta yana fad’in, Amma gwaggo ke kike bani labarinsa akullum tayanda zuciyata tacika da qaunarsa da kuma son ganinsa da jin muryarsa, ke kika sanya mani tunanin cewa zanga mahaifina nan kusa alokacin da ake shegantani, gaba d’aya mafarkina da kuma muradaina sun ta’allaqane alokacin da zan had’uwa da mahaifina kamar yanda ako yaushe kike fad’amun cewa nan kusane bada jimawa ba amma meyasa yau zaki rusa mani su tahanyar cewa nadena tunanin abubuwan da nake fatan zuwansu gareni akoda yaushe?, duk wannan maganar da yake cikin tausasawa da kuma sanyin murya yakeyi matasu, Riqo hannunsa tayi tace, nasan ni nasa maka wannan tunanin da kuma shauqin soyayyar mahaifinka dason ganinsa, duk nayi hakanne cike dasa ran cewa zai dawo agaremu, amma sai gashi yau da bakinsa yafurta cewa bazai dawo agaremu ba har abada, yazab’i yarabu damu ya zauna acan wata qasar shida wud’anda yake ganin sun fimu saboda rud’in abun duniya, dakansa yasanya wuqa mai tsananin kaifi ya kashe alaqar dake tsakaninsa damu sannan yayi amfani da kalamai mafi d’aci da kuma quna da rad’ad’i ya tunb’ukemu daga cikin rayuwarsa, don haka a matsayina na mahaifiyarka bana son kasake yimani magana akansa da kuma abunda ya shafesa, ina son ka kashe duk wasu mafarkai naka da kuma muradanka matuqar nina haifeka. Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, gwaggo idan nayi hakan meye makomar rayuwata?, Wace sheda zan bayar ga mutanen dake shegantani?, wane irin qwarin guiwa zan samu wajen martabaki a matsayinki na mahaifiyata bayan kinsa sharud’d’a masu matuqar nauyi agareni da zasu hanani tsayuwa ako ina inbugi qirji cewa ni d’an halak ne?, A razane tamiqe had’e da d’aukesa wani irin zazzafan mari hawaye nazubo mata a fuska saboda jin d’acin kalmar da yayi taqarshe sannan ta nunasa da yatsa tana cewa, ko kayarda ko karka yadda kai d’in d’anane kuma kai d’an halak ne ba shege ba kamar yanda mutane suke fad’a, kuma yazama dole kasa a ranka kuma kayarda da hakan azuciyarka. Ganin yanda b’acin ya bayyana a fuskarta qarara da kuma tsantsar qaunarsa a idanuwanta yasa yariqo hannuwanta ya zaunar da ita yana share mata hawaye had’e da cewa, kiyi haquri gwaggo idan nab’ata maki rai kuma kiyafe mun, na amince da sharad’inki nafarko amma don Allah kijaye nabiyun, kibarni in rayu da mafarkaina nason had’uwa da mahaifina da kuma muradaina akansa domin zasu tsaya mani wajen yaqar duk wasu kalaman cutarwa akaina, Hannunta ta aza a kuncinsa had’e da cewa, katabbata haka yarona?, Yace sosai gwaggo, tayi murmushin da iya saman d’eb’enta ya tsaya sannan tashiga labarta masa irin firar da akayi da mahaifinsa kamar yanda talabarta masa rayuwarsa da ita acan baya kafin abubuwa suzama hakan, wani wajen tana fad’a masa tana ‘yar dariyar da tafi kuka ciwo wani wajen kuma idan takawo fad’a masa tana hawaye, duk da qananan shekarunsa haka yayita bata magana don yana nuna mata yanayin yanda rayuwa kezoma bawa kamar yanda akoda yaushe take lurar dashi, don kam gwargwado yasamu gatar ilimi da tsantsar tarbiya daga garesu, saida yaga damuwar da take ciki tad’an ragu sannan yajawo abincin daya shigo dashi ya zubata tare da miqa yana cewa, kici abinci gwaggona, jarumar uwa, d’aya tamkar da dubu, linzamin rayuwata kuma hasken idaniyata, kinsan da ALLAH kuma yasan dake shiyasa yake shiga dukkanin lamurranki har yake jarabtarki aci, kiqara haquri in Sha ALLAH ranar cikakken farincikinki nazuwa, ahankali nake maki fatan canye duk wata jarabawarki da qaruwar imaninki had’i da lafiyarki, SANNU SANNU dai Bata hana zuwa..da yardar ALLAH sai kinzamo zakaran gwadin dabi aduniya, Ina sonki sosai mahaifiyata kuma inafatar zakici gaba dayi mani addu’ar cimma mafarkaina domin duk halin abbana shima Ina matuqar sonsa. Wani irin sanyi taji azuciyarta tare da yima ALLAH godiya daya batashi amatsayi d’anta, ko ahaka aka tsaya ta tabbata batayi asarar auren da qurciya tasata iqirarin sonsa ba ba tare da tasan qalubalen dake ciki ba wanda ayanzu take nadamar yinsa arayuwa. Bayan kwana biyu dady dasu umma da ammie sukazo gidan saboda tattaunawa akan matsalar don tun ranar bai koma d’auko zancenba sai yau saboda bayason abun ya haifar masu da damuwa tsakaninsa da umma. STORY CONTINUES BELOW  Bayan duk angaggaisa dady yayi bayani sosai tare da fad’a masu cewa shi yana ganin atuntub’i magabatansa kawai aji ba’asi idan har abunda yafad’a ta tabbata shikenan sai anemi maslaha aciki, idan zasu sa yadawo ya d’auki matarsa da d’ansa sukoma tacan qasar tareni walillahil hamd, idan kuma sawaqe mata zaiyi shikenan, anan umma takafe kai da qasa tace bata amince da hakan ba, Babu yanda za’ayi su iskesu bayan su yakamata ace sunyi hakan, kuma koma meye suna sane amma suka share saboda basa qaunarta don haka ita kawai aje kotu araba auren faqat shi yafi sauqi, don ita dama bata shirya sake rabuwa da ‘yarta ba akaro na biyu. Nan fa rigima takucce tsakaninta da dady tafad’i yafad’i saboda yanda tad’au zafi, anan Dr yacewa umma a musulunce bazai yuyu araba auren ba har sai in akwai magabatansa aciki sunsan da maganar don haka tayi haquri aje can d’in, nanma kasa fahimtarsa tayi had’e da fashewa da kuka tana fad’in, bazasu fahimci yanda abun yake ba don ALLAH subar mata ‘yarta, Hakan yasa Rashida da tun d’azu batace komai ba ta d’aga kai tana kallon yanda mahaifiyarta take kuka tacewa dady don ALLAH indai donta zasuje kada sutafi, tafiso abar zancen domin zuwan nasu ba lallaine yayi wani amfaniba tunda baza’a iya tirsasashi dawoba, aslalima yariga daya fad’awa duniya cewa baisan komai ba game da ahalinsa da iyayensa to meye amfanin cewa sai angamsar da duniya cewa yana dasu tahanyar tirsasa masa abunda bayada muradi ko qoqarin cewa sai anje kotu domin araba auren, Saida tashare qwalla sannan taci gaba da cewa ita tana ganin yin hakan zai iya zama qalu bale agaresa ga wud’anda basu san gaskiyar al’amari ba tunda shi yanzu yazama wani shahararre da aka sani awannan lokacin, za’a iyayin amfani da wannan damar ayi qoqarin tab’a mutuncin d’ansu kuma masu sheganta mata shi su samu qwarin guiwa da wata damar cigaba da walaqantasa had’e da tozartasa, koba komai ita yanzu batada wani sauran buri akansa amma akwai mafarkai da dama da d’anta kedasu akansa don ALLAH kada hakan yazamo mafarin rushewarsu. Murmushi dady yayi irin nasu na manya domin gaba d’aya kalamanta sun gama bayyanar da cewa har yanzu akwai sauran soyayyar mijinta aranta, koma meye b’acin rai yasa takasa iya jure abunda yayi kuma yagamsu da maganganunta saboda tarin hujjojin da keciki, dama shi babban burinsa amincewar yarinyar amma tunda tabuqaci ayi hakan shikenan ALLAH yasanya alkhairi, nan yanuna mata cewa shikenan baza’aje ba matuqar hakn zai faranta mata rai sannan suka koma gida. Akan sa’insar da umma tayi dashi saida yayi kwana biyu yana fushi da ita duk da bawai har azuciyarsa bane, kawai yayine don yanuna mata kuskurenta kuma tabashi haquri suka daidaita, tun lokacin dady ya d’auki alwashin saka Nuraddeen acikin addu’o’in sa akan ALLAH ya yaye masa abunda ke kansa ya dawo da hankalinsa ga iyalinsa kodon tarin d’imbin qaunar da take yimasa. ••• ••• ••• Yaya hawwa kuwa kullum cikin addu’a take da kuka ALLAH yadawo mata da d’anta agareta, kullum cikin kiran sunansa take tana istigfari akn abunda ta aikata, baya da haka bata aikin komai sai kuka, abinci ma sai Inna Bilkisu tayi da gaske takeci, tsananin rad’ad’in da takeji akan rashin d’anta har ji take yana neman sa lumfashinta ya d’auke, sai yanzu takejin rashin kyautawarta nasa a salwantar da rayuwar ‘yar mutane ashe haka akejin zafi alokacin da aka raba iyaye da d’ansu ko masoyi da masoyinsa, tayi dana sani sosai tare da nadamar abunda ta aikata. Baffa ma gaba d’aya yamiqa lamurransa ga ALLAH yanaci gaba da addu’a ALLAH ya karkato masa da hankalin yaronsa izuwa garesa yadawo gida, don shima yasamu labarin firar da akayi dashi da abunda yace, Wanda hakn yasashi komawa can wajen shuwa gabannin da suka turasu yace sutaimaka abashi lambar da zai iya samun d’ansa yana son magana dashi, ai kuwa cikin sa’a saiga wani daga cikin wud’anda sukayi karatu yanada contact dashi Nuraddeen d’in aka samu lambarsa a hannunsa donsu cewa sukayi basada ita, Cike da farinciki baffa ya amshi lambar wayar yaje da ita yasa kud’i masu yawa yawa yakirasa, Tajima tana ringin kafin ad’aga cikin wata iriyar miskilalliyar murya aka amsa sallamar, muryar da Nuraddeen dake kwance yaji tasashi miqewa zaune yana qoqarin tunano wani abun amma yakasa, shikuwa Baffa sai fad’in yake Nuraddeen meyake faruwa dakai?, Kana lafiya?, Kayi magana mana idan kaine, meyasa zaka zab’i yin bauta awata qasar bayan qasarka data taimaka maka?, shin I tarbiyarka tatafine har ka I manatawa damu iyayenka?, don ALLAH kadawo hakanan kaga mahaifiyarka kuma kayi qoqarin gano inda matarka take, jikina nafad’a mani cewa tana raye aduk inda take, sarawa kansa ya shigayi yana son tunano muryar amma hakan tafaskara saboda wani juyawa da ciwo da kansa keyi, cikin qarfin hali yace, bab..kafin ya qarasa yasaki wata irin qara tare da buga wayar ajikin bango ta watse saidai baffa yaji tayi d’if, yanata faman hello hello daga nan bai qara jinsa ba yasake kiran lambar yafi aqirga amma sai yajita akashe hakan yasa yahaqura yaci gaba da yimasa addu’a kuma yana qoqarin sake gwada kiran lambar akoda yaushe amma kashe STORY CONTINUES BELOW  A b’angaren Nuraddeen kuwa nan take alokacin ciwon kai mai tsanani ya rufesa yadafe kan da hannuwa yanata juye juye daga tsayen da yake cikin d’akin saiga wani abokinsa d’an can qasar yazo gidan, shiya taimaka masa ya d’aukesa yayi asibiti dashi, bayan ya farfad’o yafara qoqarin tunano abunda yafaru da muryar da har lokacin sautin amonta yakeji akunnuwansa amma yakasa tunowa, hakan yasa da kansa yasa akayi masa allurar bacci don da kansa yanzu yafara rage shan barasar da yakeyi gaba d’aya, tun daga lokacin yakasa komawa yanda yake saboda qarar sautin baffa dake damunsa a kunnuwa wanda yaja gaba d’aya yanzu bayason abunda zai had’asa da waya balle d’aga kira daga ko Ina, hakn yasama gaba d’aya bai komabi takan wayar tasa data tarwatseba. ••• ••• ••• Haka rayuwa taci gaba da tafiya har zuwa lokacin da little yagama secondary, sau da dama yakan so yayi zancen mahaifinsa da mahaifiyar tasa amma idan yatuna yanayin da take shiga nadamuwa akan haka da alqawarin da yayi mata na bazai koma yimata zancensa ba sai yafasa, ana qoqarin nema masa makarantar da zaici gaba da ita wato jami’a yahad’u da wata kyakkyawar yarinya da ALLAH ya jarabceta da mugun sonsa Mai suna *BATOOL*, ‘yace ga yayan mahaifiyar hajia nafeesa dake can garin kano wato mahaifar iyayensa, sun had’une sanadiyar hutun da take zuwa nan gidan dady wajen ‘yar uwar tata da take matsayin abokiyar wasanta, tunda ALLAH yad’ora idanuwanta akansa taji duk duniya babu wanda takeso sama dashi, wani irin so takeyi masa da batasan iya adadinsa ba wanda hakan yahaifar mata da yawan zuwa hutu garin saboda shi, tun tana b’oye son da take yimasa har takasa haqura ta bayyana masa, aranar kwana yayi yana juye juye don bako shakka bazai yi qarya ba shima yana sonta, saidai tunani matsayinta ga wacce duk duniya babu macen daya tsana sama da ita saboda yanda take amfani da halshenta wajen cutar dashi da mahaifiyarsa harma da kakarsa yasa yakejin bazai iya soyayya da itaba don gudun kada allura ta tono masa bakin galma… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___75💎 Tun cikin daren batool tahau shirin kayanta, hajia nafeesa dai nabiye da ido tana kallonta, saida takammala tsaf sannan tashige toilet ta watso ruwa, kallo d’aya zakayi mata tabaka tausayi saboda yanda idanuwanta suka kukkumbure akan kukan da taci amma sai qoqarin sakin fuskarta takeyi tana son nuna babu wani abun da yake damunta, kitchen tawuce ta had’oma kanta ruwan Lipton saboda yanda takejin bata sha’awar sama cikinta komai tadawo falo ta zauna tana kurb’a ahankali batare data tankawa qananan yaran hajia nafeesa dake faman mugun wasanni atsakiyar falon ba, shakur ne yashigo fuskarsa ba d’igon walwala ko kad’an yanemi waje kusa da ita ya zauna yana faman shinshinar qamshin body spray d’in dake tashi ajikinta, Wata uwar harara ta zabga masa had’e da miqewa takoma d’ayar kujerar taci gaba da kurb’ar ruwan Lipton d’inta hankali kwance, Miqewa yayi yasake binta zuwa inda take zaune shima ya zauna yana qare mata kallo tun daga sama har qasa yana lasar baki, sake miqewa tayi zatabar wajen yayi saurin sa hannu a fusace yariqo hannunta yana fad’in. Wai yane malama dana zauna saiki tashi, meye kika gani ajikina da bakya so, kallonsa tafarayi sannan takalli hannunsa daya riqe nata dashi alamun yacikata amma yaqi hakan ya fusatata ta yadda cup d’in a saman center carpet d’in dake tsakar d’akin don dama ta shanye abunda ke ciki ta d’aukesa wani irin azababben marin da yasa ya saketa ba shiri ya dafe kuncinsa, cikin halin ko inkula ta d’auke cup d’in had’e da juyawa tanufi kitchen zata mayar da sauri ta tsaya sanadiyar jin da tayi yabiyo bayanta, STORY CONTINUES BELOW  Cikin takaici tajuyo tana kallonsa tace, lafiya malan kake biyata. Kamar sakarai Shakur ya amsa mata da, batool ni kika mara don kinga ina sonki?”. Eh, yanzuma zan sake marin naka idan ka sake yunqurin tab’ani, anfad’a maka so haukane? Ko ko anfad’a maka ana so dolene?, To bari nafad’a maka ni ba sa’ar kabace don matsayin uwarka naka tunda qanwar mahaifiyarka nake, don haka kadena ganin ka girmeni sosai wannan girman dole kabani shi ka ajiye shashanci agefe, ni banida lokacin yaro irinka. Tana rufe baki taji hajia nafeesa nafad’in, eh lallai batool d’an nawa kike neman yaqunawa haka?, Shi kike kira yaro bayan yabaki shekaru d’aid’ai har goma sha d’aya aduniya?, to shikenan naji shi yarone, shi kuma wancan shegen fa da kike tsaya kulawa, shi kuma menene?. Oho! bazan iya ganewa ba don tarbiyarsa Bata barni na iya fahimtar ko shekarunsa nawa ba, ban damu ba koma jaririne shi amma kijawa yaronki kunne, karya kuskura ya sake tab’ani idanko ba haka ba…bata ida qarasawa ba hajia nafeesa ta d’aga hannu zata kaimata mari tayi saurin riqe hannun tana cewa. Daga lokacin da kika kira mahaifina kika sanar dashi qarya da gaskiya akan masoyina, daga lokacin ne nima nadaina ganin duk wani mutunci naki da kuma kimarki, daga lokacin kika rasa dararjar da har zaki iyasa hannu ki dakeni in qyaleki, ko wancan marin da kika yiwa masoyina, rad’ad’insa dana dad’e inaji ajikina bai barni na iya haqura ba har saida narama masa ga d’anki, gashinan kuma ki tambayesa, yanzu idan yayi qoqarin sake maimaita abunda yayi mani, to tabbas shima wancan dayan marin da kikayi mani to tabbas kuwa zan sake ramashi akansa, kitsaya a iya huruminki nake ‘yar uwatace ko ince ‘yar uwar mahaifina, kada kisake kice zaki sake qoqarin shiga rayuwata domin bakida hurumi akanta, har yanzu lokaci bai qure maki ba domin akwai sauran burbishin kimarki da nake gani sanadiyar zamowarki silar dana had’u da farincikina, idan kuwa ba haka ba to ina baki tabbaci akan zan zubar da sauran kimar taki dake idanuwa na nayi maki abunda sai kinyi dana sanin shiga gonata, kuma kamar yanda kikace Abu sumayya yarabu dani to zaiyi hakan ammafa nawani d’an lokaci, shima d’in bisa umurnin mahaifiyarsa ne don kada ki d’auka cewa kinyi nasarar rabamune idan kinga hakan, Ina so ke kuma idan har kin isa ga d’anki kuma yatabbata shi d’in d’an halak ne to kice yarabu dani, yadena bibiyata domin bana sonsa kuma bana qaunarsa. Shaqo wuyanta shakur da tuni yakai qololuwa wajen fusata yayi yana huci ya had’ata da jikin bangon kitchen d’in data nufa yana fad’in. Kinyi qarya kice zaki walaqantani akan wani shege da ba’asan aslinsa ba, halama waye ubansa da zaki zab’esa akaina?, to bari kiji nafad’a maki duk duniyar nan idan ta taru babu wanda ya isa yarabani dake, shi d’in wa da zaki fifitasa akaina?, Yaron daya tashi agabana cikin inuwar d’an uwana data mahaifina da suka yimasa sutura shi zaki nemi had’awa dani? to bari kiji in fad’a maki, idan ma mafarki kikeyi toki farka don narantse bakida miji aduniya saini, don haka kizuba mugani…., yana kaiwa nan ya jefar da ita gefen kujera yawuce fuu…kamar zai tashi sama yabar wajen, har ya kusa kai bakin qofar fita cikin qarfin hali ta tashi tare da cewa, kai sakarai, Cikin b’acin rai yajuyo tayi murmushi had’e da cewa, Ashe kasan sunanka?, to bari nima in buga maka kashedi akaina kamar yanda kayimun, nunasa tayi da hannu had’e da murza ‘yan yatsunta har Saida sukayi qara sannan tace, karubuta ka ajiye, ni d’innan mallakin Abu sumayyace wato ‘yar da zan haifa mana nida shi don haka kadena wannan mafarkin nacewa zaka zamo mijina, waye kai kuma wa kake dashi da kake tunanin zai tsaya maka? Aunty nafeesa ce dake qoqarin amfani da zafin ran mahaifina? Ko kuwa zuciyarka da batada qwarin guiwar da zata iya fighting da tawa har taci galaba akanta?, to bazasu iya ba domin ni inada tsayayyu a hannun damata da kuma haguna, sannan zuciyata jarumace da zata iya fuskantar duk wata matsala kuma ashirye nake nabada rayuwata akan wannan d’an yaron daya tashi aqarqashin inuwar gidannan aka yimasa sutura, don haka ni dakai shege kafasa. Kanta yayo a fusace da sauri hajia nafeesa da tayi tsaye tana kallon tsantsar rashin kunyar da batool ke zuba masu tariqesa tana fad’in. Qyaleta shakur, jeka d’akinka kawatsa ruwa ka huta, duk rashin kunyarta kaine zakayi maganinta, tayi iyayinta don SANNU SANNU Bata Hana zuwa, in Sha ALLAH sai tazo hannunka a matsayin matarka kayi duk yanda kake so da ita kaji ko?, STORY CONTINUES BELOW  Mere baki batool tayi had’e dayin tsaki tabar wajen tana fad’in, lallai kuwa iska na Shirin wahalda mai kayan kara. Wani irin naushi yakaiwa bango yana huci yace, mom nifa bazan iya jurewa irin wud’annan walaqancin ba, kinajin yanda yarinyar nan ke fad’in maganganu amma kice duka na haqure, bazan iya ba. Yaqare maganar a fusace had’e da barin wajen zuciyarsa na tafarfasa. Bayan sati d’aya lokacin har little yawuce makaranta ita kuma batool takoma gida, tun ranar da takoma mahaifin nata kefushi da ita saboda abunda hajia nafeesa tafad’a masa kuma daya tambayeta kai tsaye ta amsa masa da cewa maganganun da hajia nafeesa tafad’a gaskiyane tana soyayya dashi saidai ba shege bane kamar yanda tafad’a kawai hassada ce da tsabar baqinciki dake cinta yasa tafad’i hakan don tab’ata masa suna. A maimakon yafahimceta saima d’auketa mari da yayi yana fad’in bata isa ba tagurb’ata masu jini da yaron da ba’asan asalinsa ba, tunda har aka fara jita jitar cewa shid’in bad’an halak bane to tabbas akwai qamshin gaskiya aciki, don haka dole ta yakicesa azuciyarta don bazaya tab’a barin ta auresa ba koda shikad’aine namijin daya rage aduniya dole tahaqura tarabu dashi, kasancewar yariga daya b’ata batool tun farko saboda soyayyar daya nuna mata fiye data sauran ‘ya’yan da yake dasu yasa takasa saurararsa ballema har tafahimci abunda yake cewa tabar wajen aguje tana kuka, ta tabbata irin soyayyar da yake yimata ita zatasa ya sauko idan tayi hakan don baya qaunar b’acin ranta balle kukan ta gashi takafe kai da fata batacin komai sai kuka duk don yasauko daga dokin naqin daya hau. Amma sai taga abun yasha banban awannan karon don ko kad’an baibi takanta ba balle tayi tunanin zaibarta tayi abunda takeso kamar yanda yasaba mata akoda yaushe, mahaifiyarta kuwa hajia salmah da suke kira da hajia mama tayi lallashi har tagaji amma batool taqi saukowa kullum sai kuka, qaramar yarinyace da anriga ansabo mata rayuwarta cikin gata da sangartawa don tun tanada shekara biyar aduniya duk abunda tace tanaso ayi agidan shi akeyi, idan kuma tayi fushi taqi cin abinci shikad’aine ke zuwa ya lallasheta yabata abaki sannan taci kuma har tagirma haka take shiyasa duk girman mutum bata shakkar tsayawa agabansa tafad’i abunda keranta don yariga daya saba mata da hakan, inda kawai rayuwarta take da sauqi shine batayin fad’a ko wata rigima sai da dalili, bata son reni shiyasa batayar da tasa qarya acikin sha’aninta ba, takan girmama babbane idan ya got kansa amma daga lokacin daya bari yayi abunda zai jawo zubewar girmansa agareta to komai tsufansa zata iya tsayawa tayi masa tas akan gaskiyarta, wannan halayyar tata natab’awa hajia mama rai amma idan tayi magana sai mahaifin nata da take kira da Abba yace a qyaleta ai yarinyace, ita kuwa hajia mama babu abunda take tsoratarwa rayuwar ‘yar tata kamar gidan wani zata ace tanada kafuwa da rashin d’agawa kowa qafa indai tana bisa gaskiyarta ita kuwa rayuwa ba haka take ba musamman ta gidan aure da kanaji kana gani da gaskiyarka za’a take maka ita kuma dole ka haqura, sai gashi yau tun ba’aje ko ina ba zata fara shan wahalarta a hannun wanda shine ya d’orata akan tarbiyar, Da kuka hajia mama taje ta iskesa tafad’a masa halin da batool d’in ke ciki amma duk da yaji badad’i haka yaruntse idanuwa yace ta tafi tabashi waje, matuqar bazata haqura dayaron nan ba to saidai tamutu, hakan yasa takoma wajensu uncle h tasanar dasu halin da ake ciki, Uncle hassan da kansa yaje qofar d’akin nata ya bubbuga had’e da kiran sunanta, lokacin tana kwance sai faman juye juye takeyi saboda yunwar data isheta, daqyar ta tashi taje tabud’e gambun tare da b’are baki tafad’a jikin uncle hassan tana kuka, da yake yanada sanyin hali ba kamar uncle Hussain ba ya d’agota yana sallallami yace da hajia mama. Kingani ko hajia abunda muke fad’a masa akan yarinyar nan yakasa fahimta!, don ALLAH dubi yanda baqar sangarta da kafiya irinta yarinyar nan daya d’orata akai kenema ta illatata babu gaira balle dalili, meye amfanin wannan rayuwa haka? Qara lafewa jikinsa tayi tana kuka saiga uncle Hussain shima yashigo, tsawa ya katsa mata had’e da cewa tanemi waje ta zauna, wani kukan tasake sawa da qarfi da yasa abban nata fitowa, yana ganin ‘yan uwan nasa tare da ita yajuya zai koma uncle Hussain yace. STORY CONTINUES BELOW  Ina kuma zakaje? Ai sai kaqaraso ka ida aikin naka tunda mun fiddo maka da ita, da sauri hajia mama taje ta d’auko abinci ta ajiye a tsakar falon uncle hassan yaja hannunta yaje da ita ya zaunar da ita gaban abincin. Ganin yanda ta canza cikin kwana biyu ba yanda take son ganin taba yasa Abba d’an sassabtowa daga fushin da yayi ya matso kusa da ita, tana ganin haka tamiqe zatabar wajen yayi saurinsa hannu ya riqeta, Batool yanzu saboda naqi amincewa ki jefa kanki cikin quncin rayuwa da yaron da baida asali kike nema ki illata kanki, yafad’a yana qare mata kallo yanda tad’an fad’a cikin kwanaki, juyawa tayi tana kallon uncle Hussain had’e da cewa, kaji ko uncle?, Fuskarta kamar zatayi kuka,tsabar takaici da bazai iya tsayawa yana kallon wannan kayan haushi ba yasa uncle hussain yayi tafiyarsa, haka hajia mama da uncle hassan suma bayansa sukabi suka ficewarsu suka barshi daga shi sai ita suyi yanda suke so… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___73💎 Ganin abun zai zame masa damuwa yasa ya miqe yaje ya d’auro arwala ya fara nafilfili yana mai addu’ar ALLAH kazab’a masa abun duk da yafi zama alkhairai arayuwarsa. Tun daga lokacin yad’an fara d’ad’d’aurewa batool fuska duk da kuwa tarin d’imbin soyayyar da yake yimata atunaninsa hakan shine mafita amma ako yaushe soyayyarta sai qara nitso takeyi acikin zuciyarsa, musamman yanda yaga tana faman bibiyarsa, sannu ahankali batare daya ankara ba yafara bata damar da bai tab’a tsammani ba azuciyarsa, gashi tuni angama shire shiren wucewarsa jami’a wato BUK dake nan cikin kano inda Dr nura ya cikashe masa fannin computer science bisa shawarar mahaifiyarsa da Fatima a lokacin yanada shekaru ashirin da d’aya aduniya, wasa wasa shaquwa mai tsanani tashiga tsakaninsa da batool da sati d’aya yarage mata takoma gida can kano don hutunsu yaqare. Tunda umma tafahimci alaqar dake tsakanin little da batool ta zaunar dashi tanuna masa cewa yafita hanyar yarinyar kodon su tsira da mutuncinsu tunda yasan Babu wata jituwa tsakaninsu da ita Kuma yasan koba komai yanzu karatune agabansa ba zancen aure ba don haka ya fad’ama yarinyar gaskiya, amma da yake yariga ya kurb’i giyar soyayya duk da qananun shekarunsa sai yanuna mata cewa shifa yana sonta kuma itama tana sonsa don haka shi baidamu da duk abunda hajia nafeesa zatayi ba domin yariga da tunfarko kafin sufara soyayya yaba ALLAH zab’i akan yazab’a masa duk abunda yafi zama alkahiri tsakaninsa da batool, don haka tunda har yaji ALLAH naqara samasa sonta kuma har suka fara soyayya to yatabbata akwai alkhairi tsakaninsu kuma babu abunda hajia nafeesa zata iya sai abunda ALLAH yaso, duk iya qoqarin da tayi wajen lurar dashi qin fahimta yayi don haka saita sanar da mahaifiyarsa tun kan abu yayi nisa. Fad’a Rashida tayi masa sosai tare da umurtarsa ya ajeyi zancen duk wata soyayya agefe har sai lokacin daya kammala karatunsa domin bayada gatar data fimasa karatu alokacin, kasancewar yana matuqar yimata biyayya tare da martabata acikin duk wani umurni da zata bashi yasa ya amince da maganarta kuma yayi mata alqawarin zaiyi yanda tace matuqar hakan zai faranta mata rai, sannan yanemi alfarmar tabashi izinin sake had’uwa da batool d’in sau d’aya daga nan bazai sake kulata ba dama duk wata mace har sai zuwa lokacin daya kammala, taji dad’i sosai tare da saka masa albarka kafin ta shiga sanar dashi saqon Dr ya barmata cewa ta fad’amasa yaje wajen dady yakarb’o saqo ya ida kammala shireshirensa in sha ALLAH jibi zai wuce makaranta don har anfara karatu satin daya wuce ya amsa mata da cewa anjima da daddare zai tafi, sun jima suna firarsu irinta d’a da uwa kafin akira sallar la’asar yayi arwala sannan yanufi masallaci, ana gamawa ya dawo sukaci gaba da firarsu alokacin harda fatima da yaranta gaba d’aya, Rashida na tsokanarsa wai yazama kiyashe ja abunda yafi qarfinka had’e da labartawa Fatima abunda kefaruwa anata dariya, d’an sosa kai yashigayi saboda jin kunya Fatima tace, Kai qyaleta big son, haushi takeji nakusa zama suruka kafin ita, in sha ALLAH indai batool ce kad’auka har tazama matarka komai daren dad’ewa, ai SANNU SANNU bata hana zuwa….kamar gobene zakaga ka kammala karatunka musha buki, ranar aga b’arin nera awajen Fatima surukar Fatima uwar ango da kanta. STORY CONTINUES BELOW  Taqarasa maganar tana dariya, d’an kallon Rashida yayi ta qasan idanuwa data mere baki itama tana dariyar yace, wlh ko mama, ranar saidai su gwaggo surab’e agefe sai inkinga dama kince su shigo adama dasu kuma mama kinsan meyasa nake son batool?, A’a big son sai kafad’a, Fatima tafad’a tana kallon Rashida da alamu tafara gajiya da shirmen nasa da tabiye masa sunayi yace, saboda kawai sunanki da take dashi, kinga sai adinga cemani d’an fa….bai qarasa fad’ar abunda zaice ba Rashida ta d’auki throw pillow d’in dake gefenta ta jefesa dashi tana fad’in, ungo nan marar kunyar yaro yatashi da gudu yana dariya yabar falon, maido kallonta tayi ga Fatima had’e da cewa, ALLAH yaron nan naki idan yayi wani abun har mamaki yake bani, duk wannan shiru shirun nasa da nike gani idan yaganki awaje haka yake sake baki yayita zaro suruttai cike da rashin ta ido sai kace bashi ba. Ah to! barshi yayi, shida mamansa ne balle ayi masa gori, ni kaina mamakinsa nakeyi, zuwa nan da anjima kuma in kika gansa bazakice shine ba, musamman idan dadynsu na awaje, sai kiga gaba d’aya ya tattaro natsuwarsa waje d’aya, yana matuqar girmamasa fiye da lissafi, Ai aunty shiyasa in za’a kwana ana kawoma uncle laifinsa bazaya tab’a yarda ba, Fatima tace. Ai kuwa wlh, yo inama yai laifin balle har afad’a masa ya yarda, Hmm! aunty kenan!, Rashida tafad’a tana murmushi, Shikuwa bai jima da fita ba aka kira sallar magrib don haka saida yawuce masallaci yayi sallah sannan yanufi gidan dady, yana shiga batool nafitowa daga cikin part d’in ammie, dama yau tayi mayannu sunfi aqirga part d’in don tagansa tasa bayada wajen zama idan ba canba, cike da farinciki tanufi inda yake tana sakar masa wani qayataccen murmushi, ta qasan idanuwa yake kallonta yana susar gefen idonsa har taqaraso, zagayarsa tashigayi hanuuwanta duka nazube abayanta kafin tadawo gabansa ta tsaya tana qare masa kallo tundaga sama hara qasa, shima kallon nata yashigayi yana ‘yar dariya sannan yafara zagayarta kaman yanda tayi masa had’e da cewa, ALLAH bazan yarda ba kishanyemun jini nima sai narama, hakan yasata sakin dariya had’e da d’aga hannu kamar zata dokesa, d’an kaucewa yayi had’e daja da baya, tace, kai ko?, Ina kashigane yau tun safe nake nemanka ban ganeka ba kasa gaba d’aya har bugun zuciyarta na neman tsayawa?, taqarasa maganar had’e dasa hannuwa a qugun tana kallonsa, Saida yasa hannuwansa guda biyu ga kunnuwa yariqe yana d’an yatsina fuska sannan yace da ita, tuba nake gimbiya, yau wajensu gwaggo naje shiyasa baki ganeni ba, amma zuciyata da kuma rouhina gaba d’aya suna nan wajenki, zo muje nafad’a maki wani sak’o kafin dare yayi inwuce. Kana nufin yauma ba’a gidannan zaka kwana ba?, nida nake son musha firarmu har mugaji sai kuma kace haka!, taqarasa maganar tare da juya baya tana turo baki had’e da qoqarin barin wajen, bayan nata shima yabi yana cemata, Ke gimbiya!, Ina kuma zakije daga magana, Dena cemun gimbiya ni, kawai kace mun batool d’ina tunda munyi fad’a dakai, ‘yar dariya yakama yimata tare da cigaba da binta yana fad’in. Kai yaushe kuma akayi haka?, to tsaya mushirya mana, Inaaa!, tafi kawai. Shikenan! Bari kawai natafi, kicewa su ammie Ina gaishesu. yajuyawarsa kamar zai koma, da sauri tajuyo tabiyoshi baya da gudu shima yad’an ruga saida yaga yakusan kai bakin gate tana qoqarin cimmasa sannan ya baud’e mata tare da nufar gefen da wasu fararen kujeru suke kakkafe tsakankanin part d’in umma dana hajia nafeesa ya zauna yana dariya, tana qarasowa wajen tayi tsaye kamar zatayi kuka tana kallonsa da sauri yamiqe had’e da qamewa ya d’aga qafa yabuge qasa sannan ya Sara mata da hannu yana fad’in, sorry mah! Bushewa tayi da dariya ganin yanda yawani qame tare da zaunawa saman d’aya daga cikin kujerun har tana riqe ciki, Saida tayi dariyar mai isarta yana kallonta shima yana murmushi sannan yanemi waje ya zauna, cikin wani irin kallon qauna takallesa had’e da cewa. Abu sumayya a gaskiya zakayi kyau da soja sosai, ka ganka kuwa dake qame d’innan? STORY CONTINUES BELOW STORY CONTINUES BELOW  A’a gimbiya, amma tunda ke kingani ya wadatar, saidai ni bana sha’awar duk wani aiki na kaki saboda bana qaunar duk abunda zaisa nayi nesa da mahaifiyata, karatunnan ma da zanje garinku inyi saboda babu yanda na iyane kuma ita tagoyi bayan hakan da babu inda zanje.+ ALLAH sarki, shiyasa nake qara sonka abu sumayya saboda kana matuqar girmama magabatanka musamman gwaggo, ya ALLAH kabani ikon qara qarfafa maka hakan idan munyi aure. Amin gimbiya, wai nikam na tambayeki?, Cikin kashe murya tana kallonsa tace, Ina jinka Abu sumayya. Meyasa kike kirana da Abu sumayya?, tunda muka had’u dake ban tab’a jin kin kirani da sunana ba, meyasa? Shiru ta d’anyi kafin tace, sunanka nada matuqar nauyin da bazan iya kiranka dashi ba, kaga sunan abbanmu ne sannan kuma sunan babban Yaya agidannan so bazan iya kiran sunan gatsau ba, Abu sumayya kuwa da nake kiranka dashi mafarkina ne da kuma burina da nake fatan ya tabbata idan munyi aure muka haifi ‘yah Ina son taci sunan sumayya, Ina matuqar son sunan tun lokacin da malamin islamiyarmu yayi mana tarihin irin gwaggarmayar da tasha acikin musulunci, to tun alokacin nak’uduri cewa idan nahaifi ‘yata sumayya zan saka mata kuma duk mijin da zan aura komai dad’insa ni da Abu sumayya zan kirasa. Iyyeee to idan shi kuma baya so fa?, Saida ta d’an d’aure fuska sannan tace dashi, Dole ma yaso tunda nima naso sunan da yake yimani, murmushi yayi sannan yace da ita, To shikenan, ubangiji ALLAH yacika mana burinmu na alkhairi, ni kaina inajin dad’in sunan sosai kuma Ina sonsa fiye da yanda kike sonshi, tace dashi ALLAH? Ya amsa mata da sosai kuwa. Saida suka sha firarsu sosai sannan yabijiro mata da maganar da sukayi da mahaifiyarsa kuma ya tabbatar mata da cewa zaibi umurninta koda hakan na nufin zai mutune, duk inda hankali ke tashi hankalin batool yatashi, nan take tafara girgiza kai hawaye nayimata zarya a fuska, Don ALLAH abu sumayya kada kayimun haka, Ina tsananin sonka kuma saida kai zan iya rayuwa, don ALLAH kataimakeni kada karabu dani har bayan cikar mafarkaina, idan ba haka ba zan iya lalacewa. Haba gimbiya, meyasa zaki fad’i haka, taya za’ayi in saka idanuwa inaji Ina gani ki lalace adalilina, yakamata ki fahimceni gimbiya, bawai ina nufin murabu bane, ina so mujingine wannan maganar agefene har zuwa lokacin daya kamata, aduk fad’in duniya ban tab’ajin zuciyata zata iya son wata da sunan aure ba daidai da second d’aya, ke ce kad’ai azuciyata kuma ke kad’ai nakeda wannan buri akanki, amma hakan bazai yuyu ba har saina gama cika burin tawa mahaifiyar. Amma mekake tunani zai haifar akaina lokacin da muka jingine wannan maganar agefe?, ita fa macce ba iyaye na renonta bane don d’ai su zauna suyita kallonta ko su ajiyeta ba har zuwa lokacin da cikar burin wani zaya gama cika, don ALLAH kafahimci wannan abun da kake shirinyi ba komai bane illa kuskure da kuma ganganci da zai jawo rabuwarmu d juna akowane lokaci, kasani ina sonka tun daga zuciya, jinin jiki, rouhina da kuma dukkanin sassan jikina, Abu sumayya zan iya rantse maka akan cewa kaine bugun kowane lumfashi nawa dake fita daga jikina. Nasani gimbiya, amma nima Ina so kisani mahaifiyata da kuma cikar kowane muradi nata sune rayuwata, don haka kiyi haquri mu ajiye wannan soyayyar agefe har lokacin da zan kammala karatuna, nayi maki alqawarin cewa bazan kula kowace macce ba da sunan soyayya balle aure kuma zan reni soyayyarki cike da tausaya da kulawar da bazan tab’a bari wani abu ya tab’ata ba balle har tasamu wata tangard’a tamkar yanda mahaifiya kerenon ‘ya’yanta har zuwa lokacin da zasu girma su koma ga ALLAH batare data bari wani abu yatab’a mata suba bisa son ranta, Ina fatar kema haka?. Yana gama fad’a yajuya zaibar wajen qwalla nazubo masa, durqushewa tayi had’e da saurin kamo qasan rigarsa, ya rufe idanuwansa da sauri. Cikin sheshshekar kuka taci, shikenan katafi izuwa cikar dukkani muraddan mahaifiyarka ni kuma zan jiraka komai daren dad’ewa, zan kula da soyayyarka har sai natabbata ta lullunku fiye da yanda zaka tafi kabarta, zan tanada maka kaina batare da gazawa ba har zuwa lokacin da zaka dawo gareni. STORY CONTINUES BELOW  Sosai yaji tabashi tausayi, yatabbata soyayyarta agaresa mai girmace da darajar data lunka darajar lokaci, yatabbata tana yimasa son da ko rabinsa baya yimata kuma in sha ALLAH shima ya d’auki alqawarin da SANNU SANNU zai rama mata dukkanin qaunar data nuna masa. Ahankali ya sauke wata irin ajiyar zuciya had’e da juyowa yana kallon yanda take sheshshekar kuka, kan ya ankara yayi qoqarin rarrashinta da bata magana kawai yaga ansa qafa anshureta, ransa ab’ace yajuya don yaga wane marar imanine ya aikata mata haka shima yaji an d’aukesa wani irin zazzafan mari. Hajia nafeesa ce sai faman huci takeyi kamar zata fashe ashe tun d’azu tana tsaye abakin part d’inta tana kallon duk abunda ke faruwa sakamakon hasken qwayaqwayin daya mamaye harabar gidan, ganin batool da tayi durqushe agabansa shiya fusatata tanufo wajen cike da takaici har tayi masu haka?, Cikin wani irin matsiyacin kallo dake nuna tsantsar tsanar da take yimasa tace, meye alaqarka da ‘yar uwata, koso kakeyi kajawomun irin abun kunyar da kayo gado tun asali don kana butulu marar halacci?, to bari nafad’a maka, wlh hanyar jirgi daban take data mota, kuma ruwa ba sa’an kwando bane sannan kaje katambayi magabatanka kaji, akwai tsantsar banbanci tsakanin d’an halak da kuma shege, koda yake ba lallai bane ace sunsan haka, balle har su iya fahimtar da kai, daga yau bakai ba ‘yar uwata domin ita jininta halastacce ne ba gurb’atacce ba, inba haka ba duk abunda yafaru dakai kai kajawo… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___74💎 Murmushi yayi tare da juyawa yana kallon batool data kasa tashi sannan yace, gimbiya kidaure kitashi, lalle ayau nafara hango gwagwarmayar da zakisha wajen tattala mani soyayyarki, kidaure komai za’ayi maki akaina kijure matuqar zuciyarki tayarda da cewa nid’in zan cika maki alqawarin dawowa agareki da kuma zamowa Abu sumayyarki da kike mafarki akaina, ni kuwa ina tabbatar maki da cewa zanja daga kuma nayi d’amarar yaqi da duk wani da zai shiga tsakanina dake, Bubbuga saiti zuciyarsa yayi sannan yaci gaba da cewa, wannan zuciyar ta Abu sumayya takice ke kad’ai gimbiyata, zagi da aibantawa basu isa suhanata qaunarki ba, kisa aranki ina sonki, Ina sonki, Ina sonki kuma ina qaunarki fiye da tsammani, cike da wani irin farinciki tamiqe tsaye tana murmushi tare da dawowa gabansa tana kalonsa tace, da gaske kakeyi kana sona?, kana qaunata? Kamar yanda kafad’a?. Sosai kuwa gimbiya, fiyema da kalaman da bakina suka fad’a, kisa aranki nid’in nakine kuma kema tawace komai tsanani komai wuya, ba gudu baja da baya kinji ko?. Nayarda, na amince kai d’in zaka zame mani tamkar wata fitila da zata haskake duk wani duhu dake tare dani kuma zaka zamo ruwa da zasuyi maganin duk wata datti da zata demeni aduniya, maida kallonsa yayi ga hajia nafeesa data koma tamkar wani mutum mutimi tsaye agabansu bud’e da baki tana kallon batool data daddage tana zarowa masoyinta kalaman da zasu dad’asa ya yadda da tsantsar soyayar da takeyi masa d’ari bisa d’ari sannan yacewa batool, kinyi alqawari? Nayi alqawari Abu sumay…, Bata qarasa ba sakamakon buge mata bakin da hajia nafeesa tayi had’e da jan hannunta tabar wajen da ita, shidai baice da ita uffan ba saima kallon batool d’insa da take faman ja yakeyi itama tajuyo tana kallonsa had’e da sakar masa wani sassanyar murmushi mai cike da tarin ma’anoni kala kala shima yana mayar mata har sukabar wajen, STORY CONTINUES BELOW  Wata irin ajiyar zuciya ya sauke had’e da cewa, coming home Abba, hakan d’ai zai bani damar mayar da duk wani martani ga waccan baiwar ALLAH, Ai baka isa ba, domin duk wanda yasai rariya yasan zatayi zuba kuma ita halak ana barinta ko don kunya, kuma dama ai duk wanda yaqiji bayaqi gani ba, ummace kefad’ar haka da itama tun d’azu tafito da taji halshen hajia nafeesa tana koro kalamai marasa dad’in ji data tabbatar da cewa da jikan natane takeyi. ‘Dan sosa qeyar kansa ya shigayi yana kallonta taqasan idanuwa ita saima yabata dariya, don gaba d’aya kamanninsa basu nuna yadamu da kalaman da hajia nafeesa tayi masa ba, mere baki tayi had’e da juyawa zatabar wajen tana fad’in, to ai shikenan duk tsuntsun da yajawo ruwa shi zasuci, yayi saurin cimmata had’e da d’ora kansa asaman kafad’arta yariqe hannunta yana cewa, kiyi haquri ‘yar tsohuwa, ya zanyi da cutar data riga tashigeni kuma narasa magani, Ai sai kayi indai Aishatu ce tana gefe iya karta dakai addu’a, Yawwa kakata takaina, indai addu’arki natare dani nasan Babu abunda zai shiga gabana tunda tariqe gwaggona cikin amincewar ALLAH. Sarkin salo, to ai saika cikani kuma ka d’agamun kafad’a kada angona ya shigo ya hangoka. Eyyeee! lallai ummarnan karkisa kishina ya motsa yau aja daga tsakanina da shi, har kinada wani ango daya wuceni?. Soqo tayi masa ga kai har zata sake kai mas na biyu yayi saurin d’auke kansa daga kafad’arta tare da sakin hannunta yabar wajen aguje yanufi sashen ammie yana dariya, tace ja’irin banza kawai sannan tawuce part d’inta. Cike da sheshshekar shaqiyanci yashiga falon na ammie yafad’a kan kujera yana dafe qirjinsa, ammie dake zaune tana karatun qur’ani ta d’ago kai tana kallonsa bayan takai aya had’e da cewa. Maigida lafiya?, Ummace ke neman saka qwaqwalwata ababireshon saboda wani soqo data kaimun, shinefa zata qara nagudo wajenki don nasan ke tattalina kikeyi. Saida tayi murmushi had’e da rufe alqur’anin sannan tace, to halama kai mekayi mata ne? Banyi mata komai ba, wai kawai don nace batada angon daya fini kuma sai naja daga da tsohon mijinnan nata shinefa take nema tasaka qwaqwalwata awaqi’a.. Ai kafin yarufe baki itama ammie ta d’aga hannu zata sakar masa wani soqon tana fad’in, to bari natayata nima tunda qashinka yagi daya girma shiyasa kake neman jan daga da gudan alhajin namu, da sauri yaruga yana cewa, kai ashe gudun gara nayo..saiga dady yashigo had’e da cewa, ai kuwa ka fad’awa zago, fad’amun meka aikatawa matan nawa suke nema yau sukarya munkai, ga hajia nafeesa can nabaro tun daga bakin gate najita tana fad’a da yarinyar nan da tazo wajenta, sai gashi dana shiga kuma takawomun qararka, yaqare maganar tare da azo hannunsa saman kafad’arsa suka dawo cikin falon, Cike dajin kunya yazube qasa bayan ya zauna shikuma dady nakan kujera ya sunkuuar da kai tare da gaishesa ya amsa yana kallonsa yana dariyar abunda hajia nafeesa tace masa azuciya, wai takamashi zai b’ata mata ‘yar uwa, to gaba d’aya nawa yaron yake kuma cikin gidan inane da wurin da hakan zata iya faruwa batare da angansa ba, ahankali yafurta ALLAH yakyauta yana sauke wata irin ajiyar zuciya, sannu da zuwa tayi masa tare da kallon little Nuraddeen tace, to katashi kugwada mana, sum sum yamiqe yafita dady yace dawo ka zauna. Tambayarsa ya shigayi meye tsakaninsa da batool, yayi masa bayani sosai batare daya b’oye masa komai ba, hatta yanda sukayi da umma da kuma mahaifiyarsa Rashida duk saida yafad’a masa, jinjina kai dady yayi sannan yace dashi, katabbata kana son yarinyar?, noce kai yayi had’e da cemasa eh dady. Dady yayi murmushi tare da shafa kansa yace, shikenan! Kaje kayi karatunka da kyau kuma kafito da babban sakamako ni kuma nayi maka alqawarin matuqar Ina raye zan nemo maka auren batool in Sha ALLAH kaji ko.? STORY CONTINUES BELOW  Little ya amsa masa cike da farinciki. Kud’i yafiddo masu yawa yabashi yace yaje ya ida qarasa sayayyar abubuwan da suka rage masa kan yawuce jibi in ALLAH yakaimu, godiya yayi masa sosai sannan yamiqe zai fita dady yace. Zauna abunka ni fita zanyi, kaidai kabi umurnin mahaifiyarka kuma ka kula da amanar da kad’aukarwa yarinyar mutane domin abun tambaya ce agareka, ni kuma nauyine akaina incika maka wannan alqawarin dana yimaka, maida kallonsa ga ammie yayi had’e da cewa, ranki shidad’e akwai wani abun? don dama part d’in umma yake kawai ya shigone yaga ya take da kuma intana buqatar wani abun kamar yanda yasaba ako yaushe in yana part d’in wannan to idan yadawo duk sai yashiga na saura tukuna zai shiga inda yake, girgiza kai ammie tayi alamun babu yace, to Masha ALLAH, ALLAH yamiki albarka, qoqarin ficewa yayi yana dariya had’e da cewa ashe ke hajia nafeesa abokin garawar nan tawa ganin yayi duk kun tsufa shiyasa yake neman d’auko maku wata shine like neman sakashi awaqi’a ko Nuraddeen? Sosa kai yashigayi cike da jin kunyar ashe duk yaji abunda take fad’a, Bayan yafita ammie ta tadashi agaba tanata yimasa Sheri wai yaro dashi yana neman yatadasu tsaye da zancen biki yanata dariya had’e da cema yadaiji duk cikin kishine shiyasa tafad’i hakan, sun jima suna fira da ammie yaci abincinsa yaqoshi sannan yayi mata saida safe, part d’in umma yakoma da yake dady yasanar da ita duk abunda yafaru tanata fad’a har tana cewa wai duk laifinsa ne daya biye masa har yake d’aure masa gindin nemo masa aure shida baida komai nayin auren inbanda baqar rigima irin tasa, saida yace mata ai bayanzu take nufi ba sai nan da idan yagama karatu sannan yabar fad’an, harar Nuraddeen d’in daya shigo yimata Saida safe tayi sannan tafiddo wani saqo ta ce yakaiwa Fatima tana gaishesu da yaran gaba d’aya sannan yawuce Hajia nafeesa kuwa cikin daren takira mahaifin batool ta sanar dashi cewa takamata tana soyayya da wani yaro agarin dake neman ya lalatata, Kuma yaron kowa yasani agarin shegene, gaba d’aya takwashe qarya da gaskiya ta sanar dashi har tana qarawa da cewa yu takamasu yaron yana neman lalatata, badon ALLAH yakawota ba da batasan iya abunda zai faru ba don haka yaturo a d’auketa gobe gobe, tsabar makirci irin na hajia nafeesa hadda fashewa tayi da kuka Wai tanajin tsoro tinda wajenta tazo kada wani abun ya sameta. Shi kuwa mahaifin na batool wato alhaji umar fari Wanda ya kasance d’aya daga cikin jerin masu kud’in da za’a iya lissafowa dashi a garin daidai gwargwado ranshi ya b’aci sosai yanata fad’a, daga qarshe ma yace tabashi batool d’in, Duk da tarin soyayyar da yakeyi mata haka yarufe idanuwa jin cewa tana tare da yaron da shegene bayada uba yaci mutuncinta sosai tare da cewa ta harhad’a inata inata gobe zai turo a d’auketa sannan ya kashe wayarsa yanaci gaba da masifa, ‘yan uwansa dake zaune tare dashi suka zura masa ido suna kallon ikon ALLAH, Abu kad’an ke tunzura yayan nasu yayita fushi yana fad’a batare dayayi bincike ba, d’aya daga cikinsu wanda shike bimasa duk da dai qannen nasa ‘yan biyune wato Hassan ya kalli d’an uwan sa hussaini sannan yamaida kallonsa ga yayan nasu alhaji umar fari yana fad’in, Haba Yaya ko meye dai kayi haquri tunda kayanke hukuncin da kake so, sai kajira idan tadawo kaci gaba da yimata fad’an, Amma yanzu ko Ina ana jinka kuma ba’asan koda waye kakeyi ba ai kaga babu dad’i, cike da zafin rai yajuyo yana fad’in, za’a San koda waye nakeyi idan nasa ankamo Mani wancan shegen yaron marar uba dake bibiyar ‘yata, Murmushin takaicin kalaman daka fitowa daga cikin bakin yayan nasu husainin yayi had’e da cewa, ashsha yaya, duk meyayi zafi haka da kake aibanta yaron mutane?, Kai kasan cewa duk duniya babu wanda ake haihuwa bada uba ba inba annabin ALLAH isa da adamu (a.s.w) ba, sannan idanma har aka haifi yaro tahanyar daba daidai ba to kuskurene akirasa da shege domin bashine shegen ba, iyayen da suka haifesa tahanyar daba daidai d’in ba sune shegun, kuma fa duk wannan fad’an da kakeyi ni banga amfanin saba tunda bakada tabbaci akan abunda aka fad’a, don ALLAH ka kwantar da hankalinka idan batool d’in tadawo sai ka binciketa kaji idan har gaskiyane, STORY CONTINUES BELOW  Kubarni da ita, ganin Ina nuna mata soyayya shiyasa take nema ta kwasomun abun kunya agida kuma wlh hakan bazata tab’a yuyuwa ba, taya zata fad’a mani gaskiya tunda son yaron akace tanayi kamar jela, harfa kuka akace tanayi masa tan faman duqawa agabansa don tsabar sakarci, tir, tir halan Bata san cewa wutsiyar raqomi tayiwa qasa nisa ba? Haka yaci gaba da suruttansa ko gajiya bayayi, ganin bashida ranar denawa yasa suka yimasa saida safe suka tafiyarsu batare da sun zauna sunci gaba da firar da suka sabayi dashi duk dare ba. Batool kuwa ranar kwana tayi tana kuka tare dajin tatsani ‘yar uwar tata dake nema tarusa mata dukkanin farincikinta, akaro nafarko kenan arayuwarta da mahaifinta ya taba yimata irin wannn fad’an harda zagi batare daya saurareta ba, Ita kuwa hajia nafeesa wani irin farin cikine taji kwance azuciyarta, aganin tasamu hanyar da zatasa awalaqanta umma da ita har shegiyar zuriar tata kamar yanda take fad’a… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___76💎 Binsu Abba yayi da kallo har suka fice kafin yadawo inda take zaune tajuya masa baya ya riqo hannunta, juyowa tayi tana kallonsa idanuwanta cike da hawaye ya girgiza mata kai alamun tayi shiru, yanayin yanda taga jikinsa yayi sanyi ya tabbatar mata da cewa ya sauko daga fushin da yakeyi, batare data yimasa musu ba tamiqe tabiyo bayansa har lokacin yana riqe da hannunta suka nufi wajen dining table inda hajia mama ta ajiye mata abincin ya jawo mata d’aya daga cikin kujerun dake wajen ya zaunar da ita sannan shima yajawo wacce ke kusa gareta ya zauna ya bud’e abincin ya zuba a plate, miqewa yayi yaje ya wanko hannunsa sannan yadawo ya zauna ya dinga d’ibar abincin yana bata abaki, ci take tana zubar da hawaye saboda ganin irin girman soyayyar da yakeyi mata, a d’ayan b’angaren zuciyarta kuwa tunani takeyi yanda zata iya haqura da soyayyar da takeyiwa Abu sumayyanta don tabiya mahaifinta d’imbin qaunar da yake nuna mata. Ba tare daya cire hannunsa a plate d’inba har saida yaga tacinye abincin dake cikinsa tas don yasan baqarama yunwa take jiba sannan jawo gorar ruwa da lemu yayi ya tsiyaya mata a cup tasha sannan yasa hannu yagoge mata hawayen dake neman bushewa a saman fuskarta had’e da cewa. “Meye kuma na kuka yanzu?.” Riqo hannunsa tayi da dukkanin hannayenta biyu tana fad’in. “Don ALLAH Abba kayi hak’uri, ba Ina nufin zan bijire maka neba ko kuma na b’ata maka rai, kawai nidai ina son..” Saurin dakatar da ita yayi kafin taqarasa tahanyar d’aga mata hannu had’e da cewa. “Bana son jin komai tunda kinzab’i rayuwa da Wanda bakisan asalinsa ba, don haka tunda kin girma yanzu bakya son farincikina kamar yanda nake son naki, na amince kije ki auresa?” “A’a Abba ba haka nake nufi ba,” “Ya isa, kice yazo Ina nemansa.” “Abba bazai yuyu ba.” “Saboda me?” “Karatu yakeyi, kuma mahaifiyarsa tace ya ajiye zancen soyayya ko wani aure agabansa har sai ya kammala.” STORY CONTINUES BELOW  Shiru Abba yayi yana kallonta cike da mamaki, wata gwauruwar ajiyar zuciya ya sauke cike da takaici yace “To ya kike so ayi?, Nidai bazan zauna dake agabana Ina kallonki ba Dole ashekararna zanyi maki aure, shi kuma kince karatu yakeyi kuma mahaifiyarsa tace ya ajiye zancen aure agefe, to ya kike so ayi?” “Abba ayi haquri yagama, ni zan jirasa har ya kammala ko kuma nima naci gaba da karatun idan jarabawarmu tafito?” “A ina?, Ke wace yarinya kika tab’a ganin mun bari taci gaba da karatu a makarantar gaba da secondary acikin gidannan?” “Abba Babu, Amma ai kamawa takeyi wlh Abba shi kad’ai ne nake tunanin zan iya rayuwa kuma insamu isashshen farinciki atare dashi kuma kaima nasan zaka so hakan agareni, don ALLAH Abba ka amice mani” “Zanyi tunani akai, Amma idan aka samu qamshin gaskiya akan zancen da ‘yar uwarki hajia nafeesa tafad’a mani koda kuwa makamancinsa ne acikin rayuwarsa to bazaki auresa ba koda kuwa hakan na nufin zaki qarasa rayuwarki me acikin d’aki baci ba sha.” yafad’a tare da miqewa yabar d’akin ransa duk adagule, kawai ya amince da hakanne saboda bayason taci gaba da zama cikin yanayin da take ciki, amma aransa ya d’au alwashin tunda har mahaifiyarsa bata buqatar aurensa nan kusa to zaiyi amfani da wannan damar ya aurar da ita ga wanda ya dace acikin shekarun kafin lokacin da zai sake waiwayarta yayi. Binshi tayi da kallo har yafita, aranta tana mai shakkun abubuwan daya fad’a don kar tasan mahaifin nata, tunda har ya furta baya son shi to babu yanda zai iya fahimtar abunda zayatarrar akan kowaye masoyinta don kusan tasan duk wasu abubuwa akansa bai b’oye mata ba, musamman data tambayesa dalilin da yasa hajia nafisa ke kiransa da shege akoda yaushe, amma dai ko meye zataci gaba da rayuwarta yanda tasaba batare data ba wani fuskar da zai iya tunkararta da maganar soyayya ba har zuwa lokacin da Abu sumayyanta zai kammala karatunsa yadawo gareta. Tun daga lokacin tamanta da duk wani Abu dake faruwa tacigaba da gudanar da harkokinta yanda tasaba amma akullum safiyar ALLAH son da takeyiwa Abu sumayya sake lunkuwa yakeyi a zuciyarta, wanda hakan ba qaramin farinciki ya saka hajia mama ba dama shi abban da kansa, Amma ta qarqashin qasa yasa wani amininsa dake can borno ya binciko masa komai akan Abu sumayya da mahaifiyarsa, inda ya tabbatar masa da cewa tabbas ba’asan mahaifin yaron ba kawai anwayi garine anga mahaifiyar tasa da iyayenta acikin garin ne, mijin ‘yar uwar tasa hajia nafeesa shike kula dasu shida babban d’ansa, yasamu qeshe qashin labarin cewa su d’in ‘yan asalin nan kano ne amma bazai iya cewa sud’in konsuwaye ba, yanzu haka dai mijin hajia nafeesa shike auren kakar yaron saboda ALLAH yayiwa mijin nata rasuwa, ya tabbatar masa da cewa iya gaskiyar abunda yasamu kenan acikin binciken da yasa yayi masa, kusan mutum biyu Abba yasake sa suka sake yimasa bincike amma dai duk amsar d’ayace Babu banbanci, hakan ya matuqar b’ata masa rai, wai yau ‘yarsa da yakeso fiye da sauran ‘ya’yan da take dasu tarasa wanda zata soyayya dashi sai shege wanda ba’asan asalinsa ba, kuma har tanace akan cewa wai shi kad’aine zai iya bata farinciki aduniya, wata irin tsanar little marar misaltuwa yasake ji aransa, tabbas koda zai rasa ‘yarsa ne bazaya tab’a bari da girmansa da mutuncinsa ba tazubar masa da kima acikin garin, zai bita yanda take so har zuwa lokacin da take tsammanin cewa zai d’auketa da hannunsa ya damqawa wanda bayada asali, inyaso alokacin zai nuna mata cewa shi d’in ubane da soyayyar da yake yiwa d’a bata Isa tahanasa yanke hukuncin daya dace akansa ba. ••• ••• ••• A b’angaren little kuwa tuni yafara karatunsa cikin maida hankali da kuma qwazo da son ganin ya cikama mahaifiyarsa burinta, kamar dai yanda akoda yaushe batool ke kwana da tashi da soyayyarsa azuciyarta haka shima ta b’angarensa Babu wani banbanci, yana yimata so da bazai iya misaltashi ba, musamman yanzu da basa tare da juna kuma sukayiwa kansu alqawarin nesanta da juna har zuwa lokacin da suke tunanin mafarkinsu zai cika, A campus d’in makarantar gwaggo wato Rashida mahaifiyarsa taso ya zauna amma sai Dr yace a’a agidan baba balarabe zai zauna don har yagama magana dashi, ko kad’an rashida bataso hakan ba Amma babu yanda ta iya dole tahaqura, sosai baba balarabe yaji dad’in zamansa wajensa koba komai yana tunanin zai iya gyara kuskuren daya aikata na tsawon shekaru duk da ba’ason ransa ba, yaso tuntuni yaje ya sanarwa da baffa cewa anga Rashida da kuma qaruwar d’a da Allah yabata tsakaninta da d’ansa amma sab’anin daya nemi b’arkewa tsakaninsa da ‘yar uwarsa tilo data rage masa aduniya shiya haifar masa da kama bakinsa akoda yaushe, yayi kuka ba adadi kuma marrar misaltuwa lokacin da qaddara tasa yasanar da ‘yar uwar tasa yaya Maryam cewa yana son xuwa yaroqi baffa gafarar abunda yafaru daga nan kuma ya sanar dashi cewa Rashida da abunda tahaifa naraye basu mutu ba saboda yanda yaga ransa yab’aci lokacin da suka zo gaisuwar aminin nasa amma sai tanuna masa bata amince da hakan ba saboda ita aganinta babu wani kuskure da suka aikata aciki da har zai d’auki zafi akan abun yanuna ransa ya b’aci don duk iyaye nagari zasuyi fiye da abunda sukayi akan ‘yarsu, sannan tunda d’ansu baya gari meye amfanin sanar dasu?, Zasu iya yunqurin cewa takoma d’akinta zasu kula da ita tunda bai saketa ba idan kuma suka nuna qin amincewarsu suce abasu jikansu wanda duk duniya idan zata nad’e wlh bazata bari araba Rashida da d’anta ba don haka inhar zasu sanar dasu komai to sai d’ansu yadawo qasar tukuna kuma shima d’in bawai don takoma dasu ta zauna bane, a’a sai don araba igiyar dake tsakaninsu ne, ita kad’ai tarage masu da zasu kalla amatsayin d’an uwansu suji sanyi don haka babu yanda za’ayi subarta a inda za’a iya sake salwantar mata da rayuwa tunda ba surukar tata kad’ai bace bata sonta ance harda wasu ‘yan uwan mijin nata, idan kuwa yaje yasanar dasu wani abun akan Rashida da d’anta bata yafe masa ba a matsayinta na ‘yar uwarsa kuma wlh babushi babu ita saidai ya sake wata ‘yar uwar, da yayi yunqurin nuna mata muhimmancin fad’a masu musamman ko don d’an uwansa da sanadiyar hakan yarasa rayuwarsa sai tafashe masa da kuka wai yana son surasa marainiyar ALLAH kamar yanda suka rasa mahaifinta, duk iya qoqarinsa naganin tafahimta amma takasa sai nanata take duk ya aikata hakan to babu shi babu ita, wannan dalilin yasa babu yanda ya iya ya haqura saboda tsoron kada zumuncinsu ya lalace itama ya rasata, amma kullum cikin addu’a yake ALLAH yadawo da Nuraddeen yahad’u da iyalinsa ko wannan nauyin zai rage masa azuciya, a kullum cikin bibiyar al’amurran ahalinsu baffa yake asirrance koda zai samu labarin dawowarsa amma shiru, hatta auren da baffa yayi duka yaje, haka lokacin da yasamu labarin abunda yafaru da Yaya hawwa shima d’in yaje amma duk bai samu ganinsuba sai dai ya aika yaro yace aje ace balarabe daga yarimawa yace yana gaida marar lfy, saidai bayada masaniya akan saqon na isa ko kuwa, damuwarsa taqaru alokacin da yaji labarin cewa wud’anda sukaje karatu da Nuraddeen sun dawo amma shi yace bazai dawo ba sai daya yasa yasake komawa yaroqi Yaya Maryam akan don ALLAH tabari bawan ALLAH nan yahad’u da jininsa ko yasamu sassaucin halin da yake ciki saboda shi mutumne mai matuqar muhimmancin da bai cancanci ace ya amshi irin wannan sakamakon daga wajen suba amma for taqi amincewa saima cewa da tayi karya sake nufota da wannan maganar tunda har d’an nasa yace bazai dawo ba kenan yanuna cewa ya manta da yanada wani ahalin anan qasar don haka suma dole su manta dashi kamar yanda ya manta dasu, alokacin yakira umma yasanar da ita hukuncin da Yaya Maryam ta yanke kozata roqeta ta sassauto ko don cikawa marigayi burinsa, amma da yake itama alokacin cike take da b’acin rai akan abun sai tabashi amsa da cewa ai ‘yar tace tanada iko akanta kamar yanda shima yake da iko akanta don haka ita babu abunda zatace akai, hakan yatabbatar masa da cewa itama umma tad’au zafi akan lamarin yanzu baida yanda zaiyi dasu, sun sha had’uwa da baffa akasuwa amma banda sallamar musulunci da gaisuwar mutunci babu abunda keshiga tsakaninsu, yana so ya sakijiki da baffan Amma saboda yanda baffan ya d’auka da zafi musamman akan rasuwar aminin nasa da sukaqi sanar dashi yaqi samun fuska daga wajensa, hakan kesa aduk lokacin daya tuna yazauna yayita kukan rashin d’an uwansa don ya tabbata idan yana raye hakan bazata faruba duk da kuwa gaba d’ayansu qanne suke agareta amma saboda suna su biyu shi zaisa su iya galaba akanta, yanzu kuwa zamowarshi shi kad’ai yasa masa raunin da bazai tab’a iya jayayya da ita ba, Yauma kamar kullum ya zaune a zauren gidansa idanuwansa na zubar da qwalla saiga little ya dawo daga makaranta sargahe da jikkar littafansa da laptop d’insa daya azo daga saman wuyansa zuwa gefen hannusa na dama ta sauka a qarqashin kafad’arsa, yana ganinsa yayi saurin kauda kansa gefe yana sharar qwalla, murmushi little yayi kafin yaqarasa wajen yana fad’in “kai d’an tsoho mai ran qarfe” da yake hakan yake kiransa dashi saboda yanda ya manyantar da yayi, “meyake damunka d’an tsohona har kake qwalla, fad’amun idan matan can nawane naje nabasu saki uku uku su barmu muhuta.” Dariya baba balarabe yayi saboda yanayin yanda little yayi maganar cikin kwaikwayon yanda ‘yan daaga ke magana ya kaimasa d’an naushi a gefen kafad’a yana fad’in. “Kaganka ko! ALLAH yarabaka da wahala.” Little na dariya yashafa wajen yana cewa. “Awwwshhh…Ashe kakan nan nawa da sauran qarfinsa, kai! ai sai ka b’allamun kafad’a irin haka kabarni jinya a hannun wud’an can tsofaffin matan naka jinya.” Baba balarabe nata dariya, ba ko shakka zuwan little a gidan alkhairi ne agaresa domin yana rage masa rad’ad’in dake damunsa azuciya, kuma yana d’ebe masa kewar d’an uwansa sosai, little bai bar wajen ba har saida yaga damuwar daya iske qarara a fuskarsa ta b’ace sannan yamiqe had’e da cewa. “Yawwa d’an tsohona bari naje na watso ruwa sai na d’auko abincina anan inzo inci kana bani labarin jarumin yayan nan naka mai mata d’aya tilo kamar rai.” Jawo carbinsa yayi ya d’aga zai dka masa da sauri yabar wajen yanufi cikin gida yana dariya, “Ja’irin banza daya gado taqadirancin gyatumarsa.” Yafad’a tare da komawa ya kishingid’a ga pillow d’in dake gefensa ajiye ya cigaba da tunanin rayuwar duniya da kuma qalubalen dake cikinsa. Ba’a wani jima ba little yadawo d’auke da plate d’in shinkafa da miyar tasha baqin kifi da kuma salad, gefen sa yaje ya zauna tare da fara motsa abincin ya d’ebo a cokali had’e da kai masa abaki yana fadin. “Ungo naga tunda nashigo kake kallon plate d’in duk yawunka sunbi sun tsinke.” Ba musu baba balarabe yabud’e baki yasa masa abincin yana dariya. “ALLAH bazan qara maka ba, ashe da gaske zakaci.” “Anfad’a maka nasan gatsene! Yimaza kaci kagama muyi magana dakai, so nake idan ALLAH yakai ranmu gobe karakani kasuwa kaji ko?, Saida ya had’iye lomar abincin daya saka abaki sannan yace. “Aikuwa da naji dad’i kamar kasan ina son zagayawa cikin garinnan Amma narasa Wanda zai rakani, su uncle hassan basa zama gida balle naroqesu, gaskiya d’an tsohona naji dad’i sosai dama gobe bamuda lectures sai zuwa qarfe d’aya. sai naje na bud’ikke qeyar idanuwana.” “A’a fa lele (little) nifa ba yawo nace zaka rakani ba, kasuwa nace karakani don haka kama kahutar da kanka zancen d’ebe qeyar idanuwa.” “Kai d’an tsoho, sunan nan nawafa little ne ba lele ba.” “To meye banbanci, ai shima d’in lele ake nufi dashi, saboda haka ni da lele zan kiraka tunda iyayenka suka saka maka sunan da ban iya ba.” Duk sukasa dariya, little nafad’in to ai shikenan, haka sukaci gaba da firarsu cikin tsantsar soyyayya ai in kagani kace shine kakan nasa na ainahi. Tunda sassafe baba balarabe bayan yagama karyawa yasa uncle Hussain kamar yanda little ke kiransu ya kirawo masa shi, dama tuni yayi shirin wucewa kasuwa shikad’ai yake jira….. *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___78💎 Shikuwa ashe lokacin ko barci bai tashiba don gaba d’aya ya shafa’a da zancen fitar da zasuyi, kwance yake yana baccinsa hankali kwance uncle hussain d’in ya d’an bubbugi qafarsa ya tashi yace dashi. “Kaje baba na kiranka tun d’azu ya shirya kai kad’ai yake jira.” Yana gama fad’ar hakan ya juya yafita da sauri yamiqe yafad’a toilet yayo wanka, bai tsaya wani abuba yana tsane jikinsa yaciro qananan kayansa yasa had’e da zura takalminsa yafito, a tsakar gida ya samesa yafito daga cikin d’aki matan nabiye dashi suna yimasa addu’ar ALLAH ya kiyaye ya gaggaishesu cikin girmamawa had’e da karb’ar ledar hannunsa yana gaishesa shima.+ Kallonsa baba balarabe yayi tun daga sama har qasa bayan ya amsa masa gaisuwar had’e da cewa. “Kar kace dani yanzu katashi bacci Naga kamar akwai sauransa acikin idanuwanka.” “Aikuwa dai, don gaba d’aya na sha’afa da zancen tafiyar nan, koda uncle Hussain yaje bacci nakeyi.” “To kawo ledar, maman ‘yan biyu jeki kizubo masa abun karya warsa.” “A’a d’an tsohona mutafi, idan naje can sai na karyar.” “Anya zaka iya kuwa?” “Eh mana, muje tunda ba noma ne zanyi ba.” Su maman ‘yan biyu nata yimasa dariya had’e da tsokanarsa wai kar yaje yadawo masu kamar a hurasa yafad’i, murmushi kawai yayi masu had’e da juyawa yafita baba balarabe yabi bayansa suna biye dasu suma suna yimasu ALLAH ya kiyaye. Suna isa kasuwar bayan ya taimakawa baba balarabe yabud’e shagonsa na kayan d’unki da yadukkan mata da yake saidawa suka gama jejjera komai sannan yasamu waje ya zauna yana kallon yanda d’aid’aikun mutane ke shigowa cikin kasuwar da sauran masu shagunan da suka fara bud’ewa, dariya baba balarabe yayi had’e da cewa “Yaufa mazan boko ne akasu sai faman raba idanuwa sukeyi, ko yazata kaya dasu?” “Sa ido kagani, zaka sha mamakin mazan bokon nan sosai, don yau zakayi cinakin da baka tab’a yiba.” “Ah..to madallah ai haka akeso, bara ni naje can nadawo.” Yafad’a tare da ficewa yabar shagon, wajen wani mai saida tea da biredi yanufa yace ya bashi leda d’aya ta biredi da madarar ruwa gwangwo d’aya sai bonbita itama sachet d’aya sannan yasa ya soya masa qwai guda ukku tare da ruwan tea a cup ya karb’a yanufo shago dasu, a daidai bakin qofar shiga shagon nasa da yake akan hanya wucewa cikin kasuwar yake yaci karo da baffa d’auke da kondon kajinda yake sayarwa shida yaransa da suke biye dashi d’auke da sauran kwandunan kaji suna shigowa saboda tuni yakoma sana’arsu adalilin qarewar da dabbobin nasa da ada yake kasuwancin saye da sayarwa dasu, gashi badamar ya rabke hannuwa tunda iyali sun riga da sun taso masa don yanzu Masha ALLAH, ALLAH ya albarkacesa da ‘ya’yaye har biyar aduniya, yanada ‘yan mata hud’u da kuma namiji d’aya wanda shine qarami yanzu yanada shekaru biyar aduniya, hakan yasa yakoma sana’ar kiwon kaji acan gida irin buloros d’innan kuma yana zuwa dasu anan kasuwa yana saidawa kuma balaifi yana samun cinaki sosai da yake rufawa kai asiri dashi, da sauri ya qarasa wajensa fuskarsa asake yamiqa masa hannu yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Barka da shigowa malan Idris anshigo?” Baffa da kallo d’aya zakayi masa ka tabbatar da ankwana biyu aduniya shima yamiqa masa hannu fuskarsa ba yabo ba fallasa yana fad’in “Yawwa malan balarabe, ALLAH yanufa, assalamu alaikum.” “Wa’alaikissalam, ya iyalin? Yau kam kayi sakko da yawa?” “Wlh kuwa, kasan idan kasuwa naja to baikamata ayi zaune gida ba, iyali duk suna lafiya, ya taku kasuwar?” “Alhamdulillah.” “To masha ALLAH, ALLAH yadatar damu a sa’a.” “Amin summa Amin.” Har zai wuce da sauri baba balarabe ya qwallawa little kira. “Kai lele, zo kariqawa baffanku kayannan.” “A’a kabarsu kai kuwa ai yanzune zamu qarasa.” Baffa yafad’a yana qoqarin wucewa, adaidai lokacin little yafito yana d’an yatsina fuska sanadiyar hasken ranr daya bugar masa idanuwa had’e dayin miqa don tuni yasoma komawa baccinsa dayaga bedawo ba, kamar ance baffa ya d’ago kai sukayi ido biyu da little gabansa yayi wani irin mugun fad’uwar da har saida kwandon dake kansa ya soma fad’uwa, da sauri little yaje ya riqesa tare dasa hannu yatare kwandon yana binsa da kallo, sunfi minti biyu ahaka baba balarabe na tsaye yana kallonsu cike da tausayi, tabbas jini jinine duk inda naka yake ko kuma yashiga kana ganesa, goge ‘yan qwallan da suka zubo masa yayi had’e da qoqarin shigewa shagon riqe da kayan tea daya karb’o masa ya karya dake neman hucewa yana fad’in. “Ka amsar masa kayan mana kutafi kada ka gajiyar dashi garin kallo irin naka.” Yayi maganar cikin d’aga murya batare daya sake juyowa ya kallesu ba, karb’ar kwandon little yayi tare da azawa saman kai yacewa baffa. “Mutafi kaka.” Wani irin yarrr…baffa yaji ajikinsa har kafafuwansa na neman rinjayarsa, gaba d’aya babu wanda yake gani atattare da yaron sai d’ansa, musamman da yayi magana, sak irinta d’aya data d’ansa Nuraddeen, kamanninsa ne kawai suka rinjaya izuwa na Rashida wacce sanin alaqarta da baba balarabe yasa yayi tsammanin ko cikin ‘ya ‘yansane, juyawa yayi yana kallon baba balarabe da yayi saurin noce kansa kamar yana wani abun lokacin da yaga yajuyo, amma ganin hankalinsa baya wajen yasa yawuce gaba shi kuma little yabisa baya, bini bini baffa ke juyowa yana kallon little dake biye dashi yana ‘yan kalle kallen yanda yanayin wajejen kasuwar yake har suka isa, gaba d’aya hankalin baffa yatashi don jikinsa nabashi wani Abu akan wannan saurayin saidai kuma meye?, shine abunda bai sani ba. Bayan ya ajiye kwandon yajuyo yana kallon baffa had’e da cewa. “To kaka sai anjima, ALLAH yabada kasuwa mai albarka, Amma kadena d’aukar irin wannan kwandon gaskiya akwai nauyi, koba don kajin dake ciki ba ynayin girmansa kad’ai ya isa yasa nauyin ya gijyar da mutum balle ga kajin sunfi a qirga aciki, ga yanayin tsufa uma qara kadinga axowa yara kana biya, ni kaina da nakeda d’an qarfi yanzu haka nagaji balle kai da shekaru suka ja ga wajen da d’an nisa sosai” don can qasan kasuwar rumfarsa take inda ‘yan kaji ke tsayawa. Tunda little yafara magana baffa ke kallonsa har yakai aya ya juya zai tafi, da suri baffa yakirasa yaciro d’ari biyu a aljihu yana kallonsa ya miqa masa had’e da cewa. “Karb’a kasha ruwa nagode kaji ko?, Nima ba’a son raina nake wannan wahalar ba yanayin rayuwarce tazo mani ahaka, ga qananan iyali da suka taso kaga ai saida neman nakai ko.” “Eh kaka da gaskiyarka, Amma kada awahalda kan da yawa idan akwai makarkata ko kuwa?, Kabar kud’inka kaka nagode.” Har yajuya zai sake tafiya baffa yasake cewa. “Karka maida hannun baiwa mana, ai saka makon kyautatawa kyautawa.” Ko kad’an baffa baya son yadena jin muryar yaron, wani irin farinciki yakeji marar misaltuwa idan yana saurararsa shiyasa baya son yabar wajen yake jawo wata maganar. STORY CONTINUES BELOW  Murmushi little yayi had’e da dawowa yana kallon baffa, shima kansa ji yake kamar tuncan ya sanshi ko kuma yasaba dashi, koma dai meye shidai tsohon yayi masa kuma ya matuqar kwanta masa arai, amsar kudin yayi ya koma mayar masa ga aljihu had’e da cewa. “A maimakon wud’annan kud’in da zaka bani kaka, kasa mani albarka mana.” A wannan karon dariya baffa yayi idanuwansa cike da hawaye yana fad’in. “To shikenan ALLAH yayi maka albarka yasa kagama da duniya lafiya.” “Amin kaka, nagode sai anjima, idan zakaje gida ka aika akirawoni idan baka samu wanda zai riqa maka sauran kayan ba, kada ka d’auka da kanka zanxo in d’aukar maka” sannan yabar wajen, Tsaye baffa yayi yana binsa da kallo har ya b’ace sannan yayi wata irin ajiyar zuciya aransa yana maijin dole zai ajiye alqawarin daya d’auka abaya ya sake tunkarar baba balarabe akaro na ba adadi bayan tsawon shekaru, ayanzu yanaji yayi kuskuren fusata a wancan lokacin daya dena bibiyar labari akan matar d’ansa da abunda ke cikinta, akwai buqatar yamaido komai baya don yasan ko waye wannan yaron?…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶🏽‍♀️ 🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___79💎 Saida little yagama zagaye kasuwar sannan yasamu daqyar yagano hanyar da zai komawa shagon nasu, lokacin har qarfe sha biyun rana tagamayi, a wahalce ya dawo tare da fad’awa akan kujerar rubar dake ciki yana fitar da nishi a hankali, kallonsa baba balarabe yayi had’e da cewa. “Ina katsaya ne tun d’azu naketa faman jiran dawowarka kazo ka zauna ka karya najika shiru, ga abincin nan dana anso maka har ruwan tean sun huce gaba d’ai” “Bari kawai d’an tsohona, gaba d’aya nan agajiye nake ga yunwar cikina ta isheni, gaskiya kasuwarnan da girma take, ai kad’an yarage in b’ace ALLAH ya taimaka nadawo kan hanya.” “Kace ashe ka kuru?, Ai nazata kanacan wajen malan idris d’in ne?” “A’a, ai tund’azu nabaro wajensa ina zazzagayawa cikin kasuwar saboda na d’ebe qeyar idanuwana, Amma dattijon nan gaskiya yakamata ace yazauna gida ya huta saboda ya manyanta sosai, halama bashida manyan ‘ya’ya mazane suka barshi haka yana faman shan wahalar rayuwa?.” Saurin kauda zancen baba balarabe yayi had’e da d’auko masa biredi da wainar qwai yamiqa masa yana fad’in. “Ungo nan nidai kaci abinci kar qwalsa(ulcer) ta kamamin kai, ga ruwan tea nan saika had’a dasu haka nan ka kora” Yafad’a yana miqo masa cup d’in. Karb’a yayi had’e da cewa. “Bari naci biredin kawai ya isheni.” Miqewa baba balaraben yayi tare da d’aukar sauran kayan had’in tean daya sawo ya mayarwa mai tiredar shayin yace yabashi lemu mai sanyi da ruwa a maimakonsu da yake mai tiredar na sai dasu duka saboda masu buqata idan masu sayayyar kaya sunzo masu sannan yadawo ya kawo masa ya had’a dasu yaci abinshi ya qoshi. Baba balarabe na ganin qarfe d’aya har da mintuna tayi yaciro d’ari biyar yamiqawa little had’e da cewa ya tashi yawuce makaranta tunda yace sunada lectures, sallama sukayi dashi sannan yamiqe zai tafi yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Zan dawo tanan idan mun tashi zuwa qarfe shida na marece.” “A’a kabarshi sai kuma wani jiqon saboda daqyar mukai k’arfe shidan?” “Kashh!…gashi kuma nacewa dattijon can ya aiko akirani idan zai tafi sai nariqa masa kayan,?” “To saidai kayi haqura har zuwa wani lokacin don suna ma riganmu tashi saboda ba’a gari d’aya bane su samu su isa gida dawuri.” “Shikenan bari naje!” Har yayi nisa sai kuma yadawo had’e da cemasa, “Bari dai naje nafad’a masa kada ya aiko kuma asamu bana nan, kasan bakyau karya alqawari ko kuwa?” Ya wuce batare da yajirayi jin amsar da zata fitowa daga bakinsa ba, Yana zuwa ya iskosa tare da wasu manyan mutane da sukazo sayen kajin har angama cinaki sun bashi kud’in yana qirgawa, sallamar da yayi tasa baffa juyowa yana kallonsa kafin yayi qoqarin qarasa qidaye kud’d’in ya sallamesu sannan yamaido hankalinsa ga little d’in daya nemi waje ya zauna. “A’a lele kadawo?” Baffa yafad’a yana kallonsa had’e da tura kud’in cikin aljihu, Saida little yayi murmushi sannan yace “Eh kaka, dama zanwuce makaranta me yanzu saina tuna nayi maka alqawarin cewa ka aika akirawoni idan zaku tashi zanriqa maki kaya, shine nace bara nazo na sanar dakai kada ka aika saboda tafiya zanyi, Ina fatar hakan ba damuwa ko kaka.” “Ikon ALLAH, to nikam meye abun damuwa anan, ai nasaba karaka wani damar da kanka kaji.” “A’a nidai kam bana son yanda ka manyanta haka kana d’aukar wud’annan abubuwan, don ALLAH kasamu wud’anda zasu dinga riqa maka zuwa titi ko biyansu ne sai kadinga yi?” Shiru baffa yayi yana kallonsa irin yanda yanuna damuwa qarara a fuskarsa tabbas yasan dole akwai wani abu b’oyayye tsakaninsa da wannan yaron, haka kurum baza’a samu irin wannan tausayin ba har sai in akwai alaqa mai qarfi tsakani, “Shikenan jikana in Sha ALLAH bazan d’auka ba, zan riqasa akaimun duka abakin titi Ina biya.” “Yawwa kaka, hakan yafi gaskiya, bari intafi lokaci na qulewa ALLAH yaqaro kasuwa.” “Amin ya rabbi.” Har zai tafi baffa yakirasa had’e da cewa, “Yarona yau kafara ganina amma kana matuqar tausayina da kuma girmamani, ko meyasa haka?” “Nima ban sani ba kaka, Amma nasan shi tsoho na kowane, yanada kyau ace duk inda yake angirmamasa ko badon wani dalili ba?” “Hakane, to shikenan nagode sosai, amma zaka tafi baka fad’amun sunan kaba?” Shiru yayi na tsawon wasu daqiqu tare dayin murmushi da alama wani abun ya tuna sannan yace “Kaka sunana Abu sumayya.” “Abu sumayya.? Kanada aure ne?” Ya maimaita sunan cike da mamaki. “A’a kaka, Ina dai son akirani da sunanne saboda wani dalilin amma sunana na gaskiya…” Bai qarasa ba sakamakon wayar baffa da tayi qara yayi saurin cirota daga cikin aljihunsa had’e da d’aga masa hannu alamun ya tsaya don yasamu ya amsa kiran, kasancewar kiran daga gidane wajen iyalinsa nusaiba yasa yabar wajen zuwa can gefe inda babu hayaniya sosai ya d’aga kiran, shi kuwa little naganin haka ya shiga duba agogon hannunsa yaga lokaci na neman qurewa gashi akwai tazara sosai kafin yasamu yakoma gida har yayi zancen shiryawa ya wuce makarantar, wani saurayi dake nan gefe zaune da alama yaron baffane dake taimaka masa ya kalla tare da cemasa” “Dan ALLAH idan kaka yadawo kace masa nawuce saboda nakusa makara.” Gyad’a masa kai saurayin yayi sannan shi kuma yawuce yana d’an d’aga qafa saboda yasamu yayi saurin isa da wuri. STORY CONTINUES BELOW  Baiyi mintuna biyar da barin wajenba baffa yadawo yana tambayar saurayin ko ina yake? ya bashi amsa da cewa ai yawuce yace afad’a masa cewa sauri yakeyi yakusa makara shiyasa. Ba haka baffa yaso ba don yaso ace yasan ainahin sunansa ko don mutuncinsa tare da kulawar daya bashi, amma duk da haka in sha ALLAH zai tambayi baba balarabe yafad’a masa tunda shi kullum suna tare a kasuwar. Da lokacin tashinsu baffa yayi yasa masu yin dako suka d’aukar masa kwandunansa suka kaimasa bakin titi inda zai samu mota ya biyasu kamar yanda yayiwa little alqawari sannan ya d’auki kaji uku cikin sauran kajin da suka rage masa yanufi shagon baba balarabe dasu da niyar yabashi aba little amma ga mamakinsa sai ya isko shagon arufe da alama har ya rigashi tashi, Bai kawo komai aransa ba yawuce abunsa duk da aransa ba hakan yaso ba saboda dama wasu lokutan akwai lalurar da zata iya tasowa ya rigashi tashi ko shi yarigashi tashi, duk da dai su sunfi rigansu tashi saboda yanayin sana’ar tasu da kuma gari daba d’aya ba. Baffa na isa gida bayan yawatsa ruwa yaci abinci yashiga labartawa matarsa nusaiba zancen saurayin daya gani d’an gidansu baba balarabe muryarsa da tafiyarsa sak ta Nuraddeen d’insa, kallo d’ayazakayi masa kaga banbancin farincikin daya samu yau fiye dana kullum, yaqare zancen yana fad’a mata cewa tabbas duk yanda akayi wannan yaron jininsa ne, amma zai tuntub’i balaraben yaji gaskiyar maganar don shidai jikinsa yabashi hakan. Murmushi tayi itama fuskarta d’auke da farinciki saboda ganinsa cikin yanayin da tadad’e tana son ganinsa aciki tace. “To kodai jita jitar da Yusuf yafad’a maku ashekarun baya gaskiyane cewa sunga yarinyarsu?” “To banida tabbaci akan haka sai naje natuntub’esa tukuna, ada na musanta zancen na Yusuf saboda atunanina bazai yuyu ace anga yarinyarnan kuma akasa sanar damuba a matsayinmu na iyayen mijinta, koba komai muma munada haqqi musan halinda take ciki duk da mungaza wajen nemota, amma yanzu ganin yaron nan jikina yabani kamar akwai wani b’oyayyen al-amari da fushin zuciyar da nayi yasa nakasa saninsa.” “To koma dai meye ALLAH yasa hasashenmu yazamo gaskiya.” “Amin, maman Rashida, Ina suka shigane suda aminina.” “Sunje gidan baffansu gano Inna hawwa? Shikuwa amininka yana d’akinsa yana bacci.” Tafad’a tare da qwallawa bashar da suke kira da Abba kira. Amsawa yaron yayi had’e da shigowa da gudu dama tund’azu ya matsu yaji kiran nata saboda yasan amininsa yadawo kuma tabbas yazo masa da wani abun. “A’a Abba meye haka! Bazakayi tafiya ahankali ba sai kaje kajima kanka ciwo kabar mutane da wahala.” “Nadena Babar mu.” Yaron yafad’a tare da nufar inda baffa yake yana dariya, hannu yabasa suka gaisa yana fad’in. “Sannu da zuwa baffanmu kasiyo mana alewar?”. “Yawwa aminina, nasiyo maka kai kad’ai bada kowa ba.” Rungumesa yaron yayi yana kallon nusaiba dake d’an harararsu cike da tsokana tana b’ata rai tace. “Sufa ‘yan matan nawa?, Adenafa yimasu ‘yan ubanci akan aminin marar jin magana.” taqare maganar tare da kaimasa ranqwashi akai, b’ata rai yayi zaiyi kuka baffa yace. “Qyale babarku, ‘yan matan nata ai sunyi girma da yawa baza’a basu ba, badon yayanku da baya nan ba da yanzu na aurar da Rashida itada zainaba, kaga narage maka abokan takara, ya rage daga asiya sai Bilkisu ko?” “Yaya zai dawo baffa in Sha ALLAH ko?” “Eh aminina kunadai yimasa addu’a ko?” “Eh baffa.” Yaron yafad’a baffa yaciro sweet da biskit d’in daya siyo masu yabashi nashi sannan yace yaje yajirasa a waje sutafi gidan baffa Usman. ‘yan maganganu suka qarasa da baba nusaiba sannan yafito yariqa hannunsa suka nufi wajen baffa Usman da shima yanzu ya manyanta sosai, Sun jima suna fira dashi akan zancen da yasanar da baba nusaiba na yaron daya gani tare da baba balarabe daga qarshe suka yanke shawarar zasuje masa a mutum su sake tuntub’arsa zancen Rashida don susan gaskiyar lamarin. STORY CONTINUES BELOW  Baffa Ali kuwa ba’a maganarsa don tun shekaru biyar da suka wuce yaje gona maciji ya saresa a qafa har sau biyu, babu maganin daba’a nema masa ba amma ba’a dace ba, gaba d’aya qafar ta sundule masa baya zuwa ko nan da can, a d’akinda baffa yayi jinya ashekarun baya anan shima yake jinya, gaband’aya yayi baqi yarame amma babu wani sauyi da aka samu na halinsa, kullum cikin baqinciki yake na zaman da yakeyi waje d’aya baya zuwa ko Ina, duk iya taimako da kulawar dasu baffa keyi masa baya gani kullum cikin tsinarsu yakeyi, shi baya iya fita ya bid’o idan kuma sun kawo masa Inna ruqayya sai tace baza’a amsa ba tafiso tafita tayo bara da takarb’i abin hannunsu gori yayi masu yawa nan gaba, haka kuwa akeyi, bakunya ba tsoron ALLAH take Jan muneera sufita bara tana fad’in ataimaka mata mijinta ne ke cikin mugun yanayi gashi yabarta da d’iya, ‘ya’yanta sunyi fad’a har sun gaji amma taqi bari, Yusuf da har ya girma shima yayi fad’an da rarrashi da ban magana Amma takasa fahimtarsa, idan yaje yayo ‘yar buga bugarsa yanemo yakawo masu sai tace baya isarsu, haka ya haqura ya zuba masu ido duk da bai dena abunda yakeyi ba, in safiya tawaye haka zata kama hanya ita da muneera sufita bara tana yimata jagora basa dawowa sai bayan la’asar, abinci ma sai Inna Bilkisu ta samma baffa Ali dake jinya yayita qorafi an bashi kad’an ko yace badon ALLAH aka bashi ba, Kuma hakan bai hana yaci, Inna Bilkisu saidai ta kallesa tagirgiza kai domin tuni tagama d’aukar darussan rayuwa aduniya, acewarta ita yanzu batada lokaci inba nata qara neman kusanci ga ubangijinta ba saboda yanda shekaru sukaja, Amma su ko yaushe mugun nufi, qyashi da kuma hassada basubar zuciyarsu ba, halin da baffa Ali ke ciki idan shi mai hankaline ya isa yad’au darasi aciki domin qarara isgilin da yayiwa d’an uwansa ne ALLAH yamaido masa akansa amma yakasa fahimtar hakan, don ma ALLAH yataimakesa da samun d’a irin yusuf dake da matuqar jinqai da tausayi, akoda yaushe shike tare dashi yana bashi kulawa daidai gwargwado duk da baya yaba masa daga tsiga sai zagi da kuma ganin la’ari. ••• ••• ••• Baba balarabe kuwa tun ranar da yadawo kasuwa zazzab’i mai nauyi yarufesa, Saida yayi sati biyu bai koma leqawa kasuwa ba saidai su Hassan da hussaini suje, hakan yasa su baffa basu samu yin magana dashi ba, sunso iskosa gida da maganar amma da sukaji zancen bashida lafiya sai suka fasa, little kuwa gaba d’aya karatu ya d’auke hankalinsa, bayada wani lokacin zuwa kasuwa sai baka rasa ba kuma duk yaje sai yashiga wajen baffa, baffa na matuqar jin dad’in irin kulawar da yaron kebasa wanda hakan yaqara saka masa son sanin kowaye shi, Wata irin shaquwace sosai tsakaninsa da shi da bazai iya kwatanta taba duk da dai bako yaushe suke had’uwaba, ana haka baba balarabe yasamu sauqi ranar da kansa ya shirya yaje har garinsu baffa bebeji don little nafad’a masa irin kyautatawar da yake yimasa, da yawan tambayar lafiyarsa da yakeyi wanda hakan ya tabbatar masa da akwai abunda take zuciyarsa yake son tambayarsa Kuma yad’auki alqawarin koma me zai faru zai sanar da baffa duk abunda yakamata yasani ko zai rage nauyin dake cikin zuciyarsa, saidai zaiyi hakanne tare da roqonsa alfarmar daya tabbata ba lallene yasameta ba amma yana fatar samunta ko don kaucewa lalacewar zumuncinsa da ‘yar uwarsa… _Bazance komai ba, Amma Ina mai roqonku don ALLAH da girmansa kuyi mani afuwa bisa jini da kukayi shiru, in Sha ALLAH bada jimawa ba zamu kammala littafin nan kusa kusa da yardar ALLAH ngd sosai👏🤝_ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  Page___80💎 Kyakkyawar tarba su baffa sukayiwa baba balarabe da yake shi kad’ai yaje bada kowa ba, a can gidansu baffa Usman aka share zauren aka yimasa shimfid’a baffa yaba d’aya daga cikin yaran gidan kud’i aka siyo masa ruwa masu sanyi sosai tare da fura da nono Inna Bilkisu tadama masa fura aka kawo masa, tunda baba balarabe ya zauna idanuwansa ke qasa yakasa had’asu da nasu baffa saboda tsananin kunyarsu da yakeji saida baffa Usman yayi gyran murya had’e da cewa. “Malan balarabe ya hanya da kuma kasuwa? Kwana biyu dad’a mun datse zumuncin dake tsakaninmu, har qara shi Yaya kuna had’uwa kasuwa dashi amma nikam ai bana iya qirga adadin shekaru ba sharabonmu da juna.” ‘Dago kai yayi suka had’a ido da baffa yaji wasu hawaye sun kwararo masa ga idanuwa saboda tausayinsa yanda yaga tsufa yataso masa ga rashin mataimaki atare dashi, alokacin d’aya yaji haushin kansa na biyewa zuciyarsa bisa yarda da abunda aka fad’a masa wanda bayada tabbaci akai kuma ya hau, gashi sanadiyar hakan yazamo silar rushewar wani sashen farincikin bawan ALLAH n nan bisa rubutacciyar qaddarar da ALLAH ya tsaro akansa, murmushi baffa yayi yana kallonsa had’e da cewa. “Ashsha malan balarabe meyayi zafi haka?, duk wani tsanani da kake gani aduniya ai yana tare da sauqi, kafad’a mana dalilin zuwanka anan domin wannan kukan naka zai iya jefamu cikin wani rud’ani da kuma tashin hankali.” Saida yasa hannu ya share hawayen da suka kwanta masa afuska had’e da jan majinan dake neman toshe masa kafafen shaqar lumfashi a hanci yana sake qoqarin danne wasu hawayen dake neman zubo masa sannan cikin sanyin muryar dake nuna tattare yake da nadama da damuwa yace. “Da farko ina so nafara baku haquri bisa abubuwan dana aikata maku ashekarun baya bisa son kaina da kuma sharrin zuciya dana biyewa, haqiqa nayi dana sanin yin hakan tun bada jimawa ba awancan lokacin sai dai aqoqarina naganin nagyara wannan kuskuren da nayi sai kuma nasake b’atawa don kub’utar da zumuncina da tsoron rasa abunda muke tunanin shikad’ai yarage mana aduniya da zai rage mana rad’ad’in wani sashe da muka rasa arayuwarmu….” Nan baba balarabe yashiga basu labari tun daga abubuwan da suka faru alokacin da d’anuwansa da iyalinsa sukabar gari har zuwa dawowar Rashida da rigimar da sukayi da Yaya Maryam da aunty marwiyya akan sanar dasu dawowar Rashida da da yace zaiyi da kuma abunda yafaru lokacin da yazo garin domin sanar dasu da komawar Rashida acan garin da aka tsinceta da had’uwarsu da mahaifanta sanadiyar zuwansu gano d’an data haifa lokacin data yayesa, da rasuwar mahaifin nata washe garin ranar a qoqarin sa na zuwa wajensa har ya yahad’u da hatsarin da yazamo sanadiyar rabasu dashi da tsatstsauran hukuncin da yayar tasu tayanke alokacin da yayi yunqurin cikawa d’an uwansa burinsa da abunda ya sake fusatata na rashin dawowar Nuraddeen da yanda sukayi da umma mahaifiyar Rashida saboda lafuzzan da taji yafurta qarara a tv cewa bayada iyali har dai zuwa qarshen duk abunda yasan yafaru wanda shine yazamo silar b’oye masa duk wata gaskiya da yayi, daga qarshe yace. “Wannan yaron da kagani ranar atare dani, yaron da kake matuqar kyautatawa, yaron da qarfin jini ya sanya shaquwa da kuma soyayya mai tsanani tsakaninka dashi acikin d’an qanqanin lokaci ba kowa bane face jikanka, jinin d’anka Nuraddeen kuma d’a ga Rashida, shine wannan cikin data b’ata dashi har muke kokonton yana raye ko akasin haka, ALLAH yanufa tahaifesa kuma har ya girma batare da mun bari kun sanshi ya sanku ba, sanadiyar karatun da yakeyi anan jami’a wajena yasa nayanke shawarar had’asa dakai kasanshi yasanka a matsayin kakansa, Ina roqonka da kayi haquri kayi mani afuwa bisa b’oye maka wud’annan abubuwa da nayi tun farko dakayi bibiyar sanin hakan, ALLAH shine sheda duk tsawon shekarunnan da aka kwashe ina rayune cike da qunci da damuwar hakan azuciyata, nayi kuka nayi da nasani yafi aqirga amma nakasa samun rangwamen nauyin da nakeji azuciyata har sai yau da ALLAH yabani ikon fad’a maka, wataqil hakan nanufin cewa nima zan amshi tawa jarabawarce tahanyar rabuwa da ‘yar uwata kamar yanda ta alqawarta, koma dai meye ashirye nake da nakarb’i duk wani sauyin rayuwa da zaizo mani matuqar hakan da nayi zai kawo maka wani sassaucin qunci da damuwar daka dad’e dasu acikin azuciyarka.” STORY CONTINUES BELOW  Hawaye nazuba a idanuwan baffa Usman yace. “Hak’ik’a kun cika mafiya son kanku da yawa kuma ko kad’an bakuyiwa yayana adalci ba bisa fad’i tashin rayuwa daya dingayi wajen nemo maku ‘yarku da kuma bimata haqqinta, yayi kukan safe, rana dare a sanadiyar b’atanta, yarasa duk wani abu daya mallaka ta sanadiyar b’atan ‘yarku, farin cikinsa da walwalarsa gaba d’aya duk saida yayi bankwana dasu ta sanadiyar b’atan ‘yarku, meyasa zakuyi masa hakan bayan ya kasance mai tsananin kamanta adalci agareku?, Yarabu da matarsa, dukiyarsa, d’ansa, d’an uwansa, da duk wani farinciki nasa aduniya saboda kawai yaga ya qwatowa ‘yarku haqqinta, amma shine ku kuka zab’i cigaba da cutuwar da zuciyarsa ta hanyar b’oye masa gaskiya alokacin da ‘yarku ta bayyana agareku wanda natabbata da kun sanar dashi da yasamu craguwar damuwarsa kaso 99 bisa d’ari, haqiqa kune mutane mafiya son kai dana tab’a gani aduniya, maganar gaskiya bakuyi masa adalci ba kuma kun cutar dashi da yawa sai….” Saurin dakatar dashi baffa da shima hawayen yakeyi yayi ta hanyar d’aga masa hannu had’e da cewa. “Kar kace haka Usman, awani b’angaren sunada gaskiya d’ari bisa d’ari a matsayinsu na iyaye, kuma ko nine su zan d’au mataki fiye da hakan, saidai bazan d’auka akan iyayen mijin ‘yar tawa ba, tsatsauran matakin da zan d’auka zai kasance ne akan shi mijin nata shi dake da iko akanta kuma na d’auki duk wani hukuncin da nake tunanin shine zai zamo maslaha tsakanina dasu don in late ‘yatah, sai dai shi tunanin kowa da kake gani daban yake aduniya kuma babu wanda yafi qarfin kuskure, haqiqa naji ba dad’i ga yanda wud’annan abubuwa suka kasance, musamman rashin aminina da nayi aqoqarinsa nazuwa ya bayyana mani abunda yakeda tabbaci akan cewa narasa natsuwata akansa, Amma babu komai tunda babu yanda na iya dole nayi haquri kuma nagodewa ubangijina daya sama mani wani aminin daga jinina da zan riqa kalla a matsayinsa ina jin sanyi duk da rashinsa agareni babbar illace sosai arayuwata…” Kasa cigaba da maganar yayi saboda kukan dayaci qarfinsa adaidai wannan gab’ar, haqiqa ALLAH shiyake halittar bayinsa kuma yadubi zukatan da suka dace da juna sai yajefa soyayya mai tsanani a tsakaninsu, tunda yake bai tab’a had’uwa da mutum wanda ALLAH yasanya masa soyayyarsa arai ba kamar baba mahaifin Rashida, yana matuqar sonsa ba ga zuciyarsa kad’ai ba hatta sassan jikinsa da kuma rouhinsa, sai gashi kwatsam arana d’aya mutuwa tayi masu yankan qauna a lokacin da suke matuqar buqatar junansu, ya tabbata da yanada rai bazai bari hakan tafaru ba, hatta d’ansa daya zab’i yayi nesa dashi yanada yaqinin cewa da yana raye duk hanyar da zaibi wajen ganin yadawo dashi agaresa sai yabi don tunkud’e masa duk wata damuwa da zata ziyartarsa, gashi sanadin rashinsa aduniya damuwowi da yawa sun nemi su durqusar masa da rayuwa, donma ALLAH yabashi jajirtaccen d’an uwa daya tsaya masa, badon haka ba da tuni shima yarasa tashi rayuwar. Saida yayi kukansa mai isarsa sannan ya d’ago idanuwansa da sukayi jajir yana kallon baba balarabe yace. “Nayafe maka komai meye kayimun kaida ‘yan uwanka, tasiri da girman soyayyar dake tsakanina da d’an uwanka bazai iya bari nariqeku azuciya ba tunda har ka iya takowa kazo kanemi yafiyata had’e da sanar dani gaskiyar abubuwan da suka faru, haqiqa naji dad’i da hasashena yazamo gaskiya Abu sumayya ya kasance tsatsona, tabbas nagartaccin iyaye suke haifar da nagartacciyar zuri’a kuma babu tantama uwa tagari ita kad’ai ke iya haihuwar d’ah nagari, a nagarta naga jinina atattare dashi a b’angaren kamanni, tarbiya, tausayi da kuma sanin yakamata sak nahango mahaifiyarsa rashiday atare dashi, Ina so ka kwantar da hankalinka akan abunda ‘yar uwarka tace, zumunci abune mai girma kuma bazan bari naku ya lalace ba ta sanadiyata ba duk da dai shi hankalin mata yasha banban da namu saboda qarancin tunani da suke dashi amma ni har ga ALLAH banga laifinta ba kuma kaima da kabi umurninta banga naka ba anan, domin shi bin nagaba bin ALLAH ne mun riga da mun taso bisa tarbiyar da iyaye sunka yimana akan muyiwa manyanmu biyayya shiyasa ka gagara bijire mata, ba ita kad’ai ba hatta nidana haifi Nuraddeen naji zafi da rad’ad’in kalaman daya furta nacewa baisan komai ba akan maganar iyayensa da kuma iyalinsa, don haka banga laifinta ba nacewa sai lokacin daya dawo sannan za’a bayyana dawowar Rashida da abunda ta haifa, domin ko an bayyana hakan kafin yadawo bayada amfani tunda baya nan kuma bazai yuyu muriqeta tazauna zaman jiransa ba tunda bashi kad’aine namiji ba aduniya, gayanda kuma abubuwa suka faru akan Rashida ta b’angarenmu dole aji tsoron dawo da ita da abunda tahaifa awajenmu don kada asake qoqarin salwantar da ita da d’an nata kamar yanda akayi abaya, don haka nayi maka alqawarin zanci gaba da b’oye wannan gaskiyar har zuwa lokacin da yaji zai iya dawowa garemu.” “A’a malan Idris kada ayi hakan, asanar dashi komai inaga hakan zai iya karkato dashi yadawo gida.” Baba balarabe yafad’i hakan tare da riqe masa hannu. Murmushin da yafi kuka ciwo baffa yayi had’e da girgiza kai sannan yace. “Hmm malan balarabe kenan!, Karabu da d’an yau kawai, ada zuciyata na kokonton cewa Nuraddeen zai iya d’aukar dogon lokaci da ransa da lafiyarsa da kuma hankalinsa ba tare damu ba, amma tunda aka d’auki tsawon wud’annan shekarun bai waiwayo muba bayan nakirasa kuma yaji muryata har ya ambaci sunana yaji irin tashin hankalin da nake ciki na rashin dawowarsa amma ya kashe wayarsa saboda baya buqatarmu ya kuma toshe duk wata hanya da zamu iya samunshi nacire wannan kokonto da kuma tabbacin da nake dashi akai, wanda yayi hakan tawace hanya kuma kake tunanin zamu iya sake samunsa balle har mu sanar dashi?,” Kallon baffa Usman yayi da tun d’azu yazuba masa idanuwa shima yana kallo saboda mamakin kalamn dake fita daga bakinsa, yatabbata idan shine bazai tab’a yafe masu ba akan wannan abun da suka yimasa amma shi alokaci d’aya ya yafe masu har yana qoqarin b’oye laifinsu ya bayyana na d’ansa, a gaskiya qarfin imanin yayan nan nasa yayi yawa, yana wannan tunanin ne yaji yace. “Kaga d’an uwana nan, Babu wahalar da bamuyi ba wajen ganin munsamu hanyar da zata sadamu dashi Amma hakan ta faskara, haka nakoma tamkar wani mahaukaci kullum riqe da waya a hannuna Ina qoqarin kiransa ko ALLAH zaisa in samesa amma hakan ya cutara kuma ina tsammanin shine yaqi bada damar da hakan zata yuyu saboda yasamu duniya da wasu mutanen da yake tunanin sun fimu.” “Haba Yaya kadena fad’ar hakan?, Wlh nasan ba haka kurum yaqi dawowa ba, wannan abun akwai sharrin shed’anu aciki.” “Hmm Usman kenan, sharrin shed’anu ko kuma sharrin zuciya?, ALLAH dai ya yaye masa abunda kedamunsa amma mudena azawa shed’an da shed’anu laifukanmu akoda yaushe muma kanmu muna aikatasu da kanmu da kuma saninmu sai mufake da cewa shed’anne ko kuma akasin haka, nayi imani akan cewa innamal a’amalu binniyat.” Wud’annan kalamai na baffa su suka fahimtar da baffa Usman cewa izuwa yanzu ran d’an uwan nasa yafara b’aci game da rashin dawowar d’an nasa wanda alamu sun nuna bai yarda cewa wani yayiwa Nuraddeen wani abuba daya shafi magani ko sammu, amma shi zuciyarsa d’ari bisa d’ari tayarda baya bisa hankalinsa kuma ba kowa yake zargi ba sai d’an uwansu, don haka dole yaqara tashi tsaye akan matsalar ko ALLAH zaisa adace awannan karon duk da dama ko yaushe cikin addu’a suke kuma yanada yaqinin tana karb’uwa ijaba kawai ce bata sauka ba…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___81💎 Duk iya qoqarin da baffa Usman zaiyi awajen don ya gamsar da baffa cewa Nuraddeen ba’a bisa hankalin kansa yaqi dawowa qasarsa ba qinyarda yayi daga qarshema ya shashantar da maganar tahanyar yiwa baba balarabe da shima yake had’a baki da da baffa Usman wajen qoqarin lurar dashi nuni da kwanon furar dake gabansa yana fad’in. “Bisimillah malan balarabe kasamu ko furar ce kasha maqoshinka yabud’e sannan kaci abinci tunda naga nema kake ka ida dallashesa bayan kukan da kasha.” Yaqare maganar cikin zolaya gaba d’aya sukasa dariya. ‘Daukar kwanon furar yayi yasha sosai har saida yakusa shanyewa sannan ya ajiye baffa yace.+ “Yawwa ko kaifa, yanzu fad’amun ya labarin ‘yatah Rashida da mahaifiyarta?, Suma suna fushi damu ko?” “Gaskiya banace haka ba, Amma dai ita mahaifiyarta taji ba dad’i sosai musamman da yarinyar taqi amincewa da hukuncin da shi mijin mahaifiyarta yayi yunqurin d’auka naganin yazo in akwai hanyar da za’abi don samun maslaha abi idan kuma babu sai aje kotu taraba auren, acewarsa bazai yuyu ta zauna da aurensa ba kuma bayanan.” “ALLAH sarki, dole zataji hakan ai, abubuwanne sunyimata yawa akai, Kuma bai kamata abiyewa ra’ayin yarinyar ba tunda ko musulunci bai yarda da hakan ba, kaga dai har yau babu wanda aka cutar acikin wannan al’amarin kamar ita Rashida, mtsss kwata kwata wannan abun beyi dad’i ba, wlh da anje kotun anraba auren da duk sai yafi akan wannan zaman da tayi tab’ata quruciyarta gaba d’aya ga wanda baisan darajar aure ba.” Baffa yaqare maganar cike da damuwa d’auke a fuskarsa, bashar (Abba) ne yashigo shida yayunsa asiya da Bilkisu riqe da jikunkunan littafansu na leda zasuje islamiya baba nusaiba tabakkasu abinci ga kwano sukawowa Yaya hawwa, kasancewar shine agaba yana hango baffa yarugo yafad’a ajikinsa, nan take duk damuwar dake tattare afuskar baffa ta b’ace ya d’agosa cike da fara’a yana fad’in. “A’a aminina har anfito zuwa makarantar?” “Eh baffa, Ina wuni?” “Lafiya klw aminina, injin babarku tabaka abinci kaci ka qoshi.” Yaqarasa maganar yana dariya tare da d’an mammatsa cikinsa. Dariyar shima yayi sannan ya juya yaje wajen baffa Usman yabashi hannu suka kashe don shine gaisuwar tasu yana fad’in “Ina wuni baffanmu?.” “Lafiya klw malan bashar, za’a makarantar ko?” “Eh..” “To madallah, Allah yabada ilimi mai albarka.” “Amin.” Yaron yafad’a tare da juyawa wajen baba balarabe daya hangosu asiya duqe agabansa suna gaishesa shima yaje yamiqa masa hannu sukayi sallama sannan ya gaishesa, dariya sosai yabawa baba balarabe ganin yanda yamiqo masa hannu suka gaisa batare da tsoro ba kamar yanda sauran yara keyi, yace “Agaida yayana aminin baffansa, ALLAH yayi maku albarka.” Ya amsa da amin mungode sannan yabi bayan ‘yan uwansa da suka nufi cikin gida yana tsalle tsalle. “Aminina kenan!, ALLAH yasa kagado mai sunanka da dukkanin nagartarsa.” Su baffa Usman suka amsa da Amin, aranar baba balarabe yaga irin tsantsar soyayyar da baffa keyiwa d’an uwansa don gaba d’aya firar tasa komawa tayi akan rayuwar da sukayi da abokin nasa alokacin da yake raye, wani wuri yana basu labari yana dariya wani wuri Kuma saidai ya girgiza kai ya goge qwalla had’e da cewa ALLAH yajiqansa. STORY CONTINUES BELOW  Suna zaune bayan sun dawo daga masallaci sallar la’asar saiga kiran little ya shigo awayar baba balarabe, yana dubawa yaga kusan 21missed call daga mabanbantan lambobin daban daban saboda a silent wayar take, yana d’agawa little yafara fad’a dashi yana fadin. “Haba d’an tsohona, a Ina ka shigane yau tun safe aketa nemanka ba’a ganka ba kuma anata faman kiran lambar wayarka kaki d’agawa sai yanzu?, ga wannan rigimammiyar tsohuwar nan yayarka tazo dubaka da jiki ta tadda baka nan, a maimakon tajira kadawo sai masifa takeyi da tsofaffin mutane wai ansan bakada lafiya akabarka kafita, duk inda ya kamata nadubaka na dubaka amma ban sameka ba, yanzu haka ganinan kasuwa nazo shima baka nan su uncle hassan kawai na isko, har a rumfar kaka naje nanma baka nan, Ina kajene gaba d’aya duk kabi ka tada mana da hankali?” Maganar yakeyi batare da yabashi damar da zai amsa masa tambayoyin da take yimasa ba, hakan yasa baba balarabe yayi murmushi had’e da katse wayar, ko ajiyeta beyi ba yasake kira awannan karon cikin girmamawa yace. “Yihaquri d’an tsohona, hankalinmune yatashi kasan bazamu iya jurar wani abun ya sameka ba, kana inane ranka yadad’e baban gwaggonah.” “Canake ko inbari harka gama fad’an tukuna sai na amsa maka tambayarka ko kuwa.” “A’a d’an tsohona Yihaquri natuba fad’amun inda kake inzo in d’aukeke.” Rage murya baba balarabe yayi kamar mai tsoron wani abu yace. “Kana inane kai yanzu.” “Ina nan kasuwa,” “To I akwai kud’i a hannunka kaje tasha inda kake rakiyar dattijon nan abokina kashiga mota kazo ina nan qauyen nasu, Idan kazo sai kakirani, kuma kada kafad’awa kowa kaji?” Gaban little ne yafad’i cikin sarqewar murya yace “e.e.eh naji, amma meyake faruwane?, me kajeyi acan? lafiya d’an tsohona?” “Lafiya klw lele, kaidai kazo, Idan kazo zaka samu dukkanin tambayoyinka acan, maza ina jiranka, kaga marece kenemanyi” Bai bari yasake jefo masa wata tambayar ba ya kashe wayar tare da sauke wata it ajiyar zuciya. Little naji ya kashe wayar da sauri yakoma shagonsu ya karb’i dubu d’aya a hannun uncle hassan don d’ari uku kacalce a aljihunsa ya nufi tashar da ake shiga motar bebeji, yana zuwa shine naqarshe ya shige sukabar tashar gabansa kuwa sai faman fad’uwa yakeyi shi kuma yana cigaba da karanto addu’o’in daya sani abakinsa. Kasancewar drivern motar na gudu yasa suka isa cikin qanqanin lokaci ya kirasa had’e da sanar dashi cewa sun iso, kallon baffa usman yayi tare tambayarsa Ina zai cemasa akawosa ya fad’a masa sannan ya sanar dashi, saida yanemi mashin ya hau ya fad’a masa sunan inda zai kaishi yaji yafad’a daidai sannan yakashe wayarsa, Kallonsa baffa keyi yanajin wani farinciki marar misaltuwa aransa, wai yau jikansane da aka fita da cikinsa acikin gidannan zai sake tako da qafafuwansa bayan tsawon wasu shekaru, tabbas ALLAH mabuwayine acikin al’amurransa don in bashi ba babu wanda ya isa yayi hakan, shikad’aine ya isa yanuna ikonsa ga yanda take buqatar wanzuwar abubuwa alokacin da yakeso kuma alokacin da yaga dama, bini bini baffa yakai kallonsa ga abakin qofar zaure yana jiran isowarsa, gaba d’aya ya matsu sai mutsinniya yakeyi tamkar wani yaro kai kace yauce rana tafarko da zai fara had’uwa da little d’in, murmushi baffa usman yayi yana kallon yanda fuskar baba balarabe kefidda annuri, shima sai kallon baffa yakeyi da alama yasamu farinciki sosai da gamsuwa akan abunda ya aikata yau. Tsayawar Mai mashin aqofar gida yasa baffa Usman saurin fita ya samu yana sallamar mai mashin d’in, har little yaciro wayarsa zai kiran baba balarabe sai yaga baffa Usman ya nunasa da hannu had’e da cemasa. “Abu sumayya?” Kamar yanda yaji baffa nakiransa dashi. Murmushi little yayi tare da d’an russunar da kansa qasa yace. STORY CONTINUES BELOW  “Eh, Ina wuni?” Fad’ad’a murmushin sa baffa Usman yayi tare da qarasowa wajensa yayi saurin miqa masa hannu tare da yimasa sallama, cike da yaqinin cewa tabbas wannan jinin d’an d’an d’an uwansane baffa Usman ya amsa masa sallamar yana qare masa kallo tare da tunano kammannin Rashida acikin fuskarsa. Kusan secod biyar suka kwashe ahaka kafin can baffa Usman yayi firgigit kaman wanda yafarka daga bacci yajawo hannnunsa su shiga ciki, tunda suka shigo baffa ke kallonsa har suka qarasa, shidai little sai bin ko ina nagidan yakeyi da kallo kafin can ya ajiye idanuwansa akan baba balarabe, ajiyar zuciya ya sauke yana fad’in. “Kai wlh ALLAH tsohonnan yau ka wahalsheni da yawa, gaba d’aya ka tada mani da hankali gabana sai fad’uwa yakeyi.” “To ai seyadena yanzu tunda gani kagani cikin qoshin lafiya.” Matsawa yayi inda baffa yake had’e da zaunawa kusa dashi yasa hannu ya dafo kafad’unsa, “sannu kaka, anwuni lafiya?” “Lafiya klw Abu sumayya, ya kake?” “Ina lafiya kaka, yanaga kamar jikinka a sanyaye..” Muryarsa na rawa ya juyo duka jikinsa yana fuskantar little tare dasa hannayensa yariqo fuskarsa dasu yace, “Farincikine yahaifar da haka jikana tare da samun kyakkyawan albishir daga bakin da bazai tab’ayimun qarya ba akan cewa kai d’in jinina ne, katuna nasha fad’a maka inada wani d’a tafiyarka da maganarka sak irin nasa, har kake tambayata yana ina? Kana so kasanshi katuna,” Kasa amsa masa yayi saboda yanda yaji gaba d’aya jikinsa ya mutu yana kallonsa, juyowa yayi yana kallon baba balarabe ya jinjina masa kai alamun tabbatar mas da zancen baffan. “Hakane Nuraddeen, wannan shine kakanka wanda yahaifi babanka, nazab’i nahad’aka da sune batare da sanin mahaifiyarka ba da kuma ‘yan uwana saboda gudun lalacewar zumunci tsakanina da ‘yar uwata, koba komai ni kaina na sauke wani nauyi da d’an uwana yamutu yabarni dashi aransa, Little baisan lokacin da wasu hawayen da zai iya kira dana dad’i ba suka zubo masa da sauri yataso ya rungume baba balarabe yana fad’in. “Nagode d’an tsoho da kazamo nafarko wajen cika mani muradai na da kuma mafarkaina, kayi mani abunda duk duniya Babu Wanda zai iya yimani, ka haska mani rayuwata alokacin da take cikin duhun rashin sanin makomarta anan gaba, ba shakka kakana yafi kowa sa’ar samun d’an uwa aduniya, yayi saurin tafiyane saboda yanada yaqinin cewa goben ahalinsa zatayi kyau a hannun d’an uwansa, nagode maka nagode maka sosai d’an tsohona mai ran qarfe, ka dad’e kayi qarko har zuwa qarshen ahalinmu.” Yasake rungumesa sosai kamar zai tsaga jikinsa ya sakasa, “Kai meye haka? Meye haka kakeyi lele? Cikani mana kasan ba qwarine da qashina ba yanzu, wannan abu haqqine akaina duk da nasan hakan zai iya haifarmun da matsala, amma nayi farinciki sosai, wannan addu’ar taka bana fatar karb’uwarta domin banaso qarkona yawuce lokacin da zanga jininka, don haka kama dena fatar hakan kaji ko?” Yaqarasa maganar qwalla nazubo masa a fuska, d’agowa little yayi daga jikinsa yasa hannuwa yagoge masa hawayen fuskarsa yana fad’in. “Kadena kuka mana d’an tsohona, kayi Abu mai kyau, ka sada yaron da akeyiwa kallon shege da danginsa na uba, ka gyara zumuncina don me da ALLAH zai tsaida rayuwarka ga iya ganin jinina bayan shi yafad’awa manzonsa cewa duk wanda ya kiyaye game da sha’anin zumunta zaiyi masa tsawon rai tare da gyara gobensa?, Natabbata koda baka kai lokacin da nakeyi maka fata ba in Sha ALLAH zaka wuce lokacin da kai kake fata, na dad’e da dason sanin dangin mahaifina, amma yanayin da mahaifiyata keshiga da alqawarin dana d’aukar mata akan bazan sake tambayarta abunda zai sakata cikin damuwa ba shi suka hanani tsaurara son sanin hakan saboda gudun na kaucewa umurninta duk kuwa da shegantani d’in da akeyi” STORY CONTINUES BELOW  Miqewa yayi yakoma wajen baffa da duk wata kalma da yake ajewa ke dad’a tunkud’o da fitar hawayenta saboda tausayinsa da yakeji da kuma rad’ad’in kalmar da yaji ana jifarsa da ita, kamo hannuwansa yayi yana murzawa ahankali tare dayin murmushi alokaci d’aya kuma hawaye na zubo masa yace. “Kakana kaima kuka kakeyi?, Kaida zakayi farincikin bayyanar jikanka agaresa mezai saka kuka Kuma?” Sa hannuwansa yayi akan fuskarsa shima yagoge masa hawayen dake zubowa sannan yaci gaba da cewa. “Kana kewar mahaifina kamar yanda nima nake matuqar kewarsa ko?.” Girgiza masa kai yayi had’e da saurin rungumesa yana cewa. “Ko kad’an jikana, kai kad’ai nake kewa da kuma mahaifiyarka, ka manta dashi tunda bayada buqatarmu na tabbata zaka maye mani gurbinsa.” “A’a kakana, zaiyi matuqar yimani wahaka na iya maye maka gurbinsa, kayi haquri kada kayi fushi dashi, duk da Ina son jin muryarsa, Ina son ganinsa, Ina son na rab’i jikinsa nayi fira dashi na fad’a masa damuwata nayi kuka ya sharemun hawayena amma nakasa samun haka saboda yayi nesa damu banyi fushi dashi ba, natabbata SANNU SANNU bata hana zuwa..kamar yanda bamuyi tsammanin zamu had’u da juna ba sai gashi ahankali ba zato ba tsammani ALLAH yahad’a fuskokinmu shima in Sha ALLAH da sannu zai dawo garemu, da kanshi zai cike gurbinsa da kake tunanin zan maye maka da yardar ALLAH.” Wani irin sanyi baffa yaji na ratsa zuciyarsa jin kalaman jikan nasa, d’ago yayi daga jikinsa little yayi saurin maidashi yana fad’in “Rowa zaka yimun bazaka barni naji d’imin jikinka ba?” Gaba d’aya duk sukasa dariya, baffa ya cikasa yana fad’in nawa kad’ai bazai wadatar da kaiba har sai ka had’a dana wannan kakan naka.” Yaqare maganar yana nuna masa baffa Usman da bakinsa yakasa rufuwa saboda farincikin da yakejin kansa aciki, haka little yaje ya rungumesa shima tare da d’an tsokanarsa sannan suka shiga wata firar mai cike da jin dad’i kowannensu naji tamkar karsu fita cikin wannan yanayin, saidai ita rayuwa haka ta gada wani lokaci farinciki wani lokaci baqinciki, Abu d’aya baya tabbata balle sudawwama acikin wannan yanayin. Sun jima suna shawarwarin yanda cigaban rayuwar zata kasance inda baffa da kansa ya roqi little akan cewa subar wannan zancen a tsakaninsu har zuwa lokacin da mahaifinsa zai dawo, yasani bayada matsala ta b’angaren baffa Usman haka ta b’angaren baba balarabe shima bazai bayyanata ba kodon gudun lalacewar zumuncinsa da Yaya Maryam har zuwa lokacin data buqata, little d’in dai yake tsoron yabud’e sirrin shiyasa yaroqesa, abunda bai sani ba shima kansa baya buqatar fitar zancen saboda gudun b’acin ran mahaifiyarsa har sai lokacin data buqaci ita da kanta tahad’asa dasu sai ya bayyana mata gaskiya, nan yayiwa baffa alqawarin zai riqe wannan sirrin har zuwa lokacin da ALLAH yayi nufin bayyana komai batare da matsala ba tunda dai yasamu wani sashen farincikinsa kamar yanda yake mafarki, Shiru baffa yayi kafin can yace, “Saidai yakamata ace Ali yasani tunda shid’in d’an uwana ne bazai yuyu ace na waresa daga sanin hakan ba.” “Idan nima d’in d’an uwanka ne dana isa ga dukkanin abunda yashafeka to nace harshi bazai san komai basai ranar da gaskiya zatayi halinta.” Baffa Usman yafad’a cikin b’acin rai. “Saboda me Usman, karka manta shimafa jinin mune, duk mugun halinsa dai bazamu iya cire jininsa daga namu ba kamar yanda shima bazai iya cire namu anasa ba.” “To nidai nafad’a Yaya, wlh baza’a fad’a masa ba kaji kuma na rantse.” Daga haka baffa bai sake cewa komai ba ya qyalesa, little yayi dariya don yafahimci kakan nasa baiji dad’in hakan da d’an uwansa yace ba. “To nidai ku taimaka ku gwada mani amaryata, itama ina kewarta Ina so naganta.” ‘Dago kai baffa yayi yakallesa don ya fahimci kakarsa yake nufi wato Yaya hawwa, aransa yace ALLAH sarki gaba d’aya sak d’abi’unsa na mahaifiyarsa ne, matuqar yasan abunda tayiwa mahaifiyarsa har take buqatar ya had’u da ita to tabbas yacika d’a nagari mai ramakon alkhairi ga mugunta, nan shima baba balarabe yabuqaci yashiga ya dubota ita da baffa Ali suka miqe gaba d’aya suka shiga cikin gidan. STORY CONTINUES BELOW  Ita Yaya hawwa saboda tsananin kukan da takeyi ako yaushe yasa idanuwanta gaba d’aya sun dena gani ga yanayin tsufan da taqarayi duk ta nad’e waje d’aya kai ka d’auka ba mutum bace, don ma ALLAH yasa tana samun kulawa gwargwado, tsabar tausayinsa da little yaji da suka shiga harda kukansa, koda suka shiga babu abunda takeyi sai kuka tana kiran nura.nura.nura, da qyar Inna Bilkisu dake zaune gefenta ta rarrasheta sannan tasamu tayi shiru suka gaisa da baba balarabe tare da yimasa yajiki, little kuwa sunan mahaifinsa da yaji tana kira yasa yakasa yin magana saboda kada ta ida rud’ewa idan taji muryarsa tayi tsammanin shine, bayan sun fito ita dai Inna Bilkisu sai kallon little takeyi saboda kamarsa da Rashida gashi har taji zasu tafi ba’ace komai akansa ba, hakan yasa zuciyarta tabata cewa qilan cikin ‘yan uwanta ne tunda gashi tare yake da qanen mahaifinta malan balarabe, A hankali lokacin da suka kawo wajen shiyar da Nuraddeen da Rashida sukayi zama baffa Usman ya rad’awa little a kunne, nan ne mahaifiyarka da mahaifinka suka zauna ka ganshi nan tunda suka barshi sau d’aya aka bud’asa har zuwa yau. Juyawa little yayi yakalli wajen da kyau kawai sai ya tsinkayo mahaifinsa da mahaifiyarsa tsaye abakin qofar, murmushi yayi tare da shafa kansa sannan suka wuce ta can d’ayar qofar inda baba Ali ke jinya don awancan zaurenne na qofar baya suka zauna shiyasa ma Basu samu wurgewar mutane ba sosai balle asan abunda yafaru. Suna shiga baffa Ali yayi ido hud’u da baba balarabe dake shigowa bayan baffan Usman da sauri ya noce kansa qasa saboda tunawa da abubuwan daya fad’a masa ashekarun baya, gaba d’aya sai yashiga gashi gabansa yashiga fad’uwa yayi tunanin sunzo ne domin su turkesa akan abunda yafad’a amma abunda bai sani ba gaba d’aya baba balarabe bai fad’a masu maganar daya fad’a masa ba, don yasan idan yayi hakan to zai iya tab’a masu zumunci musamman daya fahimci irin soyayyar da baffa keyiwa ‘yan uwansa ta hanyar kalamansa, kawai sai ya b’oye gaskiyar yabar duka laifi akansa don baya buqatar ya lalata zumuncin tsakaninsu da shima yake neman gyara nasa, yatabbata komai daren dad’ewa gaskiya zata bayyana domin ita SANNU SANNU bata hana zuwa…, Girgiza kai kawai yayi sannan suka shiga gaggaisawa tare da yimasa yajiki, ba qaramar razana yayi ba da yaji muryar little wanda saida hakan ta bayyana qarara a fuskarsa. Kowanensu yi yayi tamkar bai lura ba har suka gama gaisawa sannan suka fita, tambayar kansa ya shigayi wanene wancan yaron to?, me sukazoyi a gidan?, Kardai ace sun kashe macijine basu sare kansa ba!, Idan kuwa hakane duk d’aukar fansarsu tazamo ta banza domin bahaka suke buqata ba, yafiso labarin nura harma da tarihinsa su shafe adoron qasa tayanda mahaifinsa zaifi jin rad’ad’i aransa. Saida sukayi sallar magrib sannan baba balarabe da little suka wuce bayan sunje can gidan baffa sun gaisa da nusaiba kuma little yaga qannen mahaifinsa, itama konkad’an basu bayyana mata kowaye little ba duk da yasaki jiki suna fira da ita da yaran sosai Amma kasancewar Bata san Nuraddeen ba balle Rashida yasa bata gano komai ba, Little da baffa kuwa ji sukayi tamkar garsu rabu aranar saboda wata irin sabuwar soyayyar junansu da sukeji na taso masu. Haka little wanda gaba d’aya yanzu ya maida sunansa Abu sumayya saboda soyayyar batul d’insa da yake dako azuciyarsa yaci gaba dayin rayuwarsa cikin jin dad’i, yana matuqar taimakawa kakannin nasa guda biyu aduk lokacin da yasamu dama, haka tab’angaren karatunsa yana maida hankali sosai duk da kuwa akwai wud’anda suka fishi qoqari tare da jajircewa hakan bai hanasa qasa a guiwa ba yana iya qoqarinsa na ganin shima yasamu abunda yasamu koda bai kaisu ba, har baya son hutu ya qare saboda farincikin da yake samu awajen kakan nasa, haka ya kammala shekarun karatunsa hud’u a tsakanin b’oyayyiyar gaskiyar da sukayi alqawarin b’oyewa a tsakaninsu har zuwa ranar da gaskiya zata bayyana, Kuma yayi nasara samun kyakkyawan sakamako a mataki na biyu wato second class.. A ranar daya amshi saka makon jarabawarsa aranar yaquduri aniyar zuwa gidansu batool domin ya gabatar da kansa awajen mahaifinta bayan yanemo izini da kuma sa albarkar mahaifiyarsa kamar yanda ta alqawarta masa, Kuma ysha alwashin koda za’a rabasa da rayuwarsa aranar sai ya tabbatarwa da batool cewa shi d’in nata ne ita kad’ai kuma ita kad’ai ya tanadawa zuciyarsa da kuma gangar jikinsa… STORY CONTINUES BELOW  *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___82💎 Ba gwaggo Rashida kad’ai ba hattasu Dr da dady sunyi farincikin sakamakon daya zomasu dashi tare da sanya masa albarka, nan take Rashida tashirya masa ‘yar qwarya qwaryar walima don nunama ALLAH godiyarta daya gwada mata wannan lokacin, Bayan ankammala walimar ne data samu halartarsu dady, ammie umma harma dasu Dr. da Fatima da suka kasance masu masaukin baqi, cikin zolaya Dady ya kalli Rashida had’e da cewa. “To Rashida, tunda yanzu ALLAH yanufa ya kammala karatunsa lafiya sai kiqara dagewa wajen yimasa addu’a domin ba anan nake son karatunsa ya tsaya ba in Sha ALLAH har sai ya had’a master’s d’insa, inda nake son turasa qasar Lebenon shida d’an uncle d’inki wato qaninsa Abbaty,” d’ansu dr nafarin da akayiwa marigayi baba takwara. Zaro idanuwa tayi tana kallon dady, da sauri su Dr da fatima harma da su ammie dake kallonta suka qumshe dariyar da tanemi kuccikke masu ganin kallon da takeyi masa suna kallonta, ganin yanda kowa ya tsuro mata idanuwa yasa ta had’iye maganar dake neman fitowa daga bakinta had’e da maida kanta qasa, Dady da shima dariyar ke neman fito masa yayi saurin had’iyeta had’e da cewa. “Rashida naji kinyi shiru bakice komai ba?” Saida ta runtse idanuwanta saboda yanda maganar ta dirar mata a lokaci d’aya cikin zuciya tare da tuna mata da mijin nata da har yanzu takasa mantasa aranta sannan yace. “Duk yanda kukayi dady ai kuma kuna da iko akan shi, banida ja ga duk hukuncin da kuka yanke akansa.” “To Masha ALLAH, in ALLAH ya yarda nan da wata uku zan…” Bata bari yaqarasa ba tayi saurin d’ago kanta tana kallonsa had’e da cewa. “A’a Dady! Agaskiya nidai bana sha’awar hakan ko kad’an, nafiso ya zauna anan gida tare damu yaci gaba da karatunsa ko kuma idan aure yake so sai yayi aurensa, hakan zai fimun kwanciyar hankali sosai fiye da yaje qasar wajen nan qaro karatu!” Awannnan karon gaba d’aya kasa riqe dariyarsu sukayi duk suka kece da dariya don dama da biyu dady yayi hakan, yana so ne yaje kano nemawa Abu sumayya auren batool kamar yanda ya alqawarta amma baya son Rashida tadakatar dashi ta hanyar qin amincewarta saboda sanin matsayin da take dashi awajen ‘yar uwar yarinyar da kuma qanqantar shekarunsa, don lokacin shekarunsa ashirin da biyar bai dad’e da shiga cikin ta ashirin da shida ba, wanda zata iya lab’ewa tanan tace abari sai nan gaba ko kuma tace tafiso yaci gaba da karatun, murmushi dady yayi sannan yace. “Taya zayayi aure tunda bakyason ya had’a karatu da soyayya, kuma kinsan matuqar yana nan qasar dole sai ya had’asu tunda qara girma yakeyi, inaga zaifi sauqi yaje can yayi karatunsa kinga idan ya kammala sai yazo nan yayi aurensa hankali kwance kamar yanda kika buqata.” ‘Bata rai tayi kamar zatayi kuka tana kallon dr had’e da cewa. “Don ALLAH uncle kace wani abun, gaba d’aya dady bai fahimceni ba.” Ware hannuwa Dr yayi alamun babu ruwansa ta kalli umma itama ta kauda kai gefe, wajen ammie tanufa tariqo hannunta tare da cewa. “Ammie don ALLAH kicewa dady ko duka biyun zai had’a masa na amince amma kar ataurasa wajen nan, wlh tsoro nakeji kar yaje shima…” STORY CONTINUES BELOW  Saurin rufe mata baki ammie tayi tana dariya sannan cikin muryarta dake nuna manyantar da tayi tace. “Kenan kin amince yayi aurensa ko yaci gaba da karatunsa.?” “Duka na amince ammie idan ma biyu yake so ya had’a amma anan qasarsa.” Dariya ammie ta kwashe da ita sauran mutanen dake wajen na tayata tace. “Ja’ira, ai dama ansan halinki shiyasa aka b’ullo maki ta hakan, ni Ina ganin nakai ga maigida ya isa aure tunda yanada masoyiyarsa amma duk kikabi kika riqe masa mara kika hanasa fitsari, to yanzu tunda yagama karatunsa lafiya saiki sakar masa ita in Sha ALLAH wani sati alhaji zaije can kano su had’u aje gidansu yarinyar nan a nemo masa aurenta, Ina dai kin amince ko?” Wata irin kunya ce tarufeta da sauri ta tashi tashige cikin gida sunata yimata dariya, gaba d’aya yau d’an kawicin nata da takeyi masu akn yaron soyayyarsa takasa bari tayi masu don bilhaqqi har qasan zuciyarta bata buqatar yaronta yafita kowace qasa da sunan karatu koda kuwa da gaske sukeyi bazata amince ba saidai aga rashin kunyarta. Fatima data bita da kallo tana dubin yanayin jikinta, Inka ganta bazaka tab’a yarda cewa ita tahaifi Abu sumayya ba tace. “Ina ruwan auntyn yara, ai banga laifinta ba nikam, tama d’an jure data iya saurararku, don da nice wlh bori zan azawa, dady ai ko abbaty bazan yarda yaje waje karatuba wlh balle ita da take ganin sanadiyar hakan mahaifin little yabarsu gaba d’aya.” “Da gaskiyarki kema my dota, ALLAH dai yaraya manasu kuma yanuna mana shima mahaifin nasa yadawo, wannan abun da yafaru yana d’aya daga cikin rashin amfanin fita wajen karatu, kawai bama ganewa ne, Amma babu abunda zakaje can qasarsu ka karanto da bazaka iya karantarsa anan qasarka ba, ko tsabar son kai irin nasu nasa suriqe mutum acan saboda basa son cigaban tamu qasar.” dady yafad’a cike da takaicin abun. Ita dai umma tunda taji an d’auko zancen mahaifin little batace komai ba saima komawarta gefe da tayi ta zauna tana kallon samarin dake har had’a kujerun da akayi walima dasu wasu kuma na warware rumfar da aka kakkafa, gaba d’aya bata son jin zancen Dr ko kad’an saboda duk daren ALLAH sai tayi kukan halin da ‘yar tata keciki, wanda badon haka ba da yanzu itama ta tara nata zuri’a a gabanta kamar yanda su Fatima da Dr keda su, don yanzu ‘ya’yansu bakwai aduniya, bayan haihuwar abbaty, shahid da shahida, walida, sultan da kuma jidda fatima ta sake haihuwar zainab wanda yanzu tanada shekaru goma aduniya saboda haihuwarsu da takeyi kusa kusa daga ita kuma bata sake haihuwa ba. Ganin haka yasa little yaje inda take ya zauna tare dasa hannuwansa ya tallafe fuskarta yana kallonta, d’an harararsa tayi takai masa ranqwashi akai had’e da cewa. “Lafiya?” Saida ya d’an sosa wajen yayiwa fuskarsa kamar zaiyi kuka sannan yace. “Da zafi umma.” “Ai Kai kajawa kanka, meyakawo nan!” “Haquri nazo nabaki, Naga kamar kinajin haushin mahaifina ne har yanzu?” Jin tayi jikinta yayi sanyi saboda yanayin yanda yayi maganar sai taji yamatuqar bata tausayi, hannunta ta d’ora akan nasa tana d’an mummurzawa a hankali alamun ban haquri sannan tace. “Kayi haquri amma Ina matuqar jin haushin mahaifinka saboda yanda yasa mahaifiyarka ta b’ata duka qurciyarta akansa, dole naji ba dad’i ko kad’anne domin bana son ace yanda take ‘yah tilo awajena itama yazamana taqare rayuwarta kai kad’ai awajenta, duk da wannan hurumine na ALLAH amma ina fatar ace ita tatara zuri’a fiye dani.” Sosai little yafahimci pain d’in da takeji a matsayinta na uwa, don haka sai yayita fad’a mata kalamai masu matuqar sanyi da kuma dad’i da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga tasaki takoma daidai yanda take d’azu sannan yabarta da yake su dady najiranta suka wuce gida. STORY CONTINUES BELOW  Bayan anyi sallar la’asar little ya iske mahaifiyarsa cikin shirinsa na manyan kaya yayi matuqar kyau har yagaji, murmushi tayi data kallesa tare dayin hamdala tana Mai godewa ALLAH acikin zuciyarta da yayi mata ni’imar samunsa a matsayin d’ah, murmushi ya sakar mata ganin rin kallon da takeyi masa itama tana murmushi yace. “Gwaggona barka da marece, anwuni lafiya?” “Yawwa little, lafiya klw, wannan irin gayu kuma sai Ina?” Saida ya sosa kansa sannan yayi qasa dashi had’e da cewa. “Kano zanje in Sha ALLAH.” “Tohh!..injin dai lafiya?, Ina yau d’in nan da safe kadawo?, to kuma me zakaje yowa a can yanzu?” Shiru yayi batare daya bata amsa ba yanaci gaba da sosa kansa har lokacin kan nasa na aqasa tayi murmushi don tafahimci inda zancen yanufa!. “Au shiyasa tun dawuri kaje ka kai qarata gunsu dady akayi mani shigo shigo ba zurfi?” Dariya yayi tare da d’ago kansa yace, “haba dai mamana!, ALLAH yatsareni da son duk wani abu da zaisa har inkai qararki ko awurin waye kuwa, shi dady kawai alqawari yayimun shiyasa yayi hakan, ni kuma bisa umurninki nayi mata alqawarin bazan sake waiwayarta ba har sai ranar dana cika maki burinki, shiyasa yau dana tabbatar da hakan nake qoqarin itama naje nacika mata alqawarinta.” “To kayi haquri ranka yadad’e har zuwa gobe tukuna kaga yanzu marece yayi, yaushe har ka isa kuma har kace kaje zakaje wajenta, ai kamata yayi ace yau kafin kazo kafara zuwa saboda kada jewad’in yayi yawa.” Zaunawa yayi ya tanqwashe qafafuwansa agabanta kamar mai shirin d’aukar karatu sannan yace. “Duk duniya Babu wanda yakamata yafara sanin nasarar dana samu inba keba hakan yasa nafara zuwa agareki domin neman sa albarkarki da kuma addu’o’inki kafin naje wajenta, idan hankalinki yafi kwanciya dana bari sai gobe zanyi hakan don faranta maki koda kuwa zuciyata bata so.” “Eh bawai nafi son hakan bane, kakirata kaji idan tayarda kabari sai goben shikenan don kada ta d’aukeka cikin masu karya alqawari.” Murmushi yayi had’e da cewa. “Dame zan kirata gwaggo bayan tunda muka rabu da ita bamu koma waya ba balle muhad’u da ita, asalima har nasoma mantawa da muryarta saboda nadad’e banji ba, wataqil itama ta canza lambar waya tunda jiya ba yau ba.” Riqe kunnensa tayi had’e da cewa. “Da kuwa kazamo gajiyayye a fannin soyayya domin komai dad’ewar masoya basu had’uba idan da halacci bazasu manta muryar juna ba matuqar akwai amana a tsakani.” “Kiyi haquri mamana da abunda zance, kenan hakan na nufin har yanzu kema baki manta da muryar abbana ba?.” Jikinta a sanyaye tasaki kunnensa da take riqe dashi fuskarta na mai sauyawa daga yanayin farinciki da take izuwa damuwa, da sauri yayi nail down had’e da cewa. “Kiyafemun idan fad’ar hakan ya b’ata maki rai, akoda yaushe Ina mai qoqarin nesanta kaina da duk wata kalma data shafi mahaifina saboda nafaranta maki kamar yanda kike buqata amma hakan ba yana nufin na manta dashi bane a matsayinsa na uba awurina, kiyi haquri bana gaji bane da bin umurninki kawai yau natsinci kaina da fad’ar hakanne sanadiyar abunda kika fad’a, don ALLAH kada kiyi fushi dani akan haka” Ganin yanda yadamu yasa tad’an saki fuskarta tare da d’aga hannu kamar zata maresa sannan ta ajiye tana fad’in. “Bakayi laifi ba amatsayinka nad’a don ka ambaci mahaifinka, nakan ji ba dad’i kawaine aduk lokacin da aka tuna mani dashi, amma taya kake tunanin zan manta da muryarsa bayan a kullum inajin muryarka?, Hakan zai kasancene kawai idan rouhina yarabu da gangar jikina, tashi katafi, ALLAH yasa kaci galaba a soyayyarka kuma yabaka ikon shiga gaban duk wani Abu da zai shiga tsakaninka da ita, ya hanaka zubar da qwalla acikin soyayyarka kamar yanda nayi.” STORY CONTINUES BELOW  “Amin ya rabbi gwaggo, Amma nafasa tafiyar sai gobe in Sha ALLAH, bazan iya tafiya nabarki da b’acin ran da nine silar sakaki acikinsa ba koda da qwarar zarra ne.” Wani farinciki taji ya dirar mata azuciya saboda jin kalamansa, tabbas tasan yana iya qoqarinsa wajen faranta mata, don haka itama dole taso duk abunda zai faranta masa, ko kad’an bata tab’a sa tsammanin biyayyarsa tayi girman da zai datse duk wata alaqa da abunda yake matuqar so ba musamman waya da baza’a iya yiwa kowane mutum shamaki akanta ba, murmushin daya fassara masa irin farincikin dake zuciyarta ta sakar masa had’e da cewa. “Tashi kaje marece nayi Abu sumayya, ALLAH ya tsare hanya, kuma kagaishemun da ita sosai kaji ko.?” Cikin qwarin guiwa yamiqe yanajin farinciki shima aransa tare da yimata sallama sannan yabar d’akin, part d’in Fatima yanufa itama yayi mata sallama had’e da kama hanya yana mai fatar samun masoyansa cikin qoshin lafiya. Bashi ya isa kano ba sai zuwa qarfe takwas da rabi na dare, kai tsaye ya nufi anguwar su batool batare daya biya ko Ina ba don ko baba balarabe da baffa bai sanar dasu zancen zuwansa ba saida ya iso sunata mamakin abunda ya dawo dashi bayan sunsan yau yakoma, A anguwar sharad’a phase 1 little yasa Mai mashin d’in daya d’aukosa ya ajiyesa kamar yanda batool ta tab’a fad’a masa. Bayan ya sallami mai mashin d’in yanufi qofar wani gida daya hango mai gadin gidan awaje shida wani mutum saman kujeru, hannu yamiqa masu duk suka gaisa sannan yashiga tambayarsu don ALLAH a ina ne gidan Alhaji umar fari, Tasowa d’aya daga cikinsu yayi ya d’an matso kusa dashi tare da nuna masa wani gida can gaba kad’an da yatsa yana fad’in. “Kaga wacan gidan mai gate kalar ruwan qwai?, to ka matsa gaba canne gidansa?” “Alhaji umar fari nake tambayarka fa?” “Eh! Kaje mana canne gidan, halan kai baqone agarin?” “A’a! kawai dai bansan gidan bane.” Little yabashi amsa had’e da miqa masa hannu yayi masa godiya sosai sannan yawuce. Bakin gate ya tsaya lokacin daya isa qidan yana qarewa girmansa da had’uwarsa kallo, gabansa ne ya soma fad’uwa da sauri ya dafe qirjinsa tare da isa jikin gate d’in ya d’an qwanqwasa mai gadin ya leqo had’e da cewa. “Waye?” “Amm..nine?” “Kaine wa?” “Baqon batool ne.” Bud’e masa yayi tare da cewa ya shigo, bayan yashiga ciki maigidan yadinga qare masa kallo tun daga sama har qasa sannan yace. “Jira, Bari afad’o mata.” A daidai bakin qofar shiga falon part d’insu batool ya tsaya tare dayin sallama, Cikin sa’a kuwa yaji muryarta ta amsa lokacin ita kad’aice a falon kwance tana faman karanta wasiqar jaki, gaba d’aya tashin hankalin da take ciki akan mazajen da mahaifinta ke kawo mata ta aura tana bijirewa yasa ta manta cewa shekarar da take zaman jira ta shigo har taqare batare data sani ba, gaba d’aya tarame ta lalace saboda matsi da takurar mahaifinta, Babu wani farinciki da take samu awajensa yanzu saboda gazawar da tayi wajen yimasa biyayya, gashi bai saba mata da hakan ba sai abun ya kashe mata biyu, agefe d’aya tunanin masoyinta da d’imbin soyayyarsa dake qara cika tana timbatsa acikin zuciyarta ad’aya gefen kuma takura da kuma damuwar da take cikine sai sukabi suka tasota agaba tabi duk taqare, Yauma saida mahaifin nata yayi mata duka saboda b’acin ran da tasashi aciki na walaqanta d’an amininsa da yazo wajenta bisa umurnin mahaifinsa akan zasu had’asu aure kuma yaganta yace yana so, zaune suke a Paris hutun da aka samu yadawo dasu nageria, ai kuwa tayi masa tas, tabuga masa warning akan ya nesanta kansa daga mafarkin dake nuna masa cewa yanemi soyayyarsa domin itad’in mallakin wani ce, gaba d’aya rouhinta, da kuma gangar jikinta na masoyinta ne kuma koda zai shekara d’ari yana bibiyarta bazata tab’a amince masa ba balle yasa ran zata auresa, da taga yanace yana son takurata harda riqe mata mayafi ta zabga masa mari had’e da cemasa yayi kuskuren aikata mata hakan domin hatta abubuwan da suke mallakinta mutum d’aya ne keda hurumin tab’asu, shine masoyinta, cikin gida tashiga ta d’auko ashana tare da kalanzir ta canzo wani mayafi tazo da wanda tacire ta jefasa agabansa tasa masa kalanzir ta cinna masa ashana yaqone, Saida yagama qonewa sannan ta d’ago kanta had’e da cemasa, “kamar yanda kaga na qona wannan mayafin haka zan qona duk wata zuciya da tayi qoqarin tunkarata da kalmar so, zaifi sauqi agareka ka manta da wannan kalmar agareni acikin rayuwarka ni kuma nayi maka alqawarin zanci gaba da kallonka a matsayin Yaya Kuma nabaka girma a matsayinka nad’an aminin mahaifina, ai kuwa tana rufe baki taji an d’auketa zazzafan marin da saida taga wuta, ashe duk abunda yafaru mahaifinta nacan daga gefen corridorn bayan d’akinsa yana hangota, shinefa har ya iso bata sani ba ya d’auketa mari, da gudu tayi cikin gida yabita yayi mata shegen duka, da Kuma yasanarwa da mahaifiyarta shine itama tayimata fad’a sosai kuma ta d’auki fushi da ita. STORY CONTINUES BELOW  Tana tunanin wud’annan abubuwanne taji mai gadin yace. “Wai anayiwa batool sallama.” “Je kace bata nan.” Tabashi amsa ataqaice cike dajin haushi. Bayan mintuna biyu ya sake dawowa yace. “Wai yace don ALLAH kizo ba dad’ewa zaiyi ba kawai yanaso yagane kine.” “Kaje kace masa bana buqatar hakan koshi waye.” A hasale ta taso lokacin da taji yadawo tana fad’in. “Idan kasake dawowa nan wlh saina tabbatar abakin aikinka.” Cikin rawar murya mai gadin yace. “ALLAH yabaki haquri ranki shi dad’e ai har ya tafi, Amma yace afad’a maki Abu sumayya ne daga borno..” Ai kafin yarufe baki da gudu tafito cikin falon har tana turesa gefe da kad’an ya fad’i tanufo bakin gate tana fad’in… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Awannan gab’ar alqalamina bazai iya cigaba da rubutu ba har sai ya miqo saqon gaisuwa tare da jinjina had’e da fatan alkhairi agareku, *AUNTY MAIJIDDA MUSA* da kuma *AUNTY FAREEDA MUHAMMAD ABBAS* Bisa zallar karamci, k’auna da kuma halacci da kuka nuna mani wajen jajircewa bibiyar wannan littafi nawa duk da kuwa irin tafiyar hawainiyar da yakeyi hakan baisa kuka nuna qosawa ko kuma gazawarku ba, kun qara mani qwarin guiwa tare da addu’o’in fatan alkhairi agareni da sukasani himmatu da kuma samun quwwar cigaba da rubuto wannan littafin cikin nasara, Ina yimaku addu’ar dukkanin alkhairan ALLAH su lullub’eku tare da ahalinku, nagode sosai da samun goyan bayanku acikin kowane rubutu nawa, ubangiji ALLAH yatsare mani ku kuma yakula mani daku aduk inda kuke👏, Fillah! akoda yaushe zuciyata na matuqar yabawa d’imbin karamci irin naku tare da yimaku son so na har abada😍_ Page___83💎 Tana fad’in “Abu sumayya!” Cike da kokwanto hakan aranta har ta qarso da gudu bakin gate d’in, daidai lokacin ya aza qafarsa zai fita taja wani irin burki had’e da tsayawa tana fidda lumfashi d’aya bayan d’aya saboda gudun da tayi. Cikin wani irin salo takira sunansa tace. “Abuu.. sumay..yaaa.” Cak ya tsaya da qafarsa had’e da lumshe idanuwa jin dirar sautin muryarta da yanda takira sunan acikin kunnuwansa, a hankali yajuyo da duka gangar jikinsa izuwa gareta suna fuskantar juna, lokaci d’aya idanuwansu suka sarqe suna isar masu da wani saqo dake fassara tsantsar soyayya da adadin kewar da suka yiwa junansa, Wata irin dariya had’e da kukan farinciki taji sun kucce mata alokaci d’aya ta durqushe agabansa saboda qafafuwanta da taji na gagarar imata tace, “Wannan wace irin bazatace mai cike da burgewa da kuma qayatarwa Abu sumayya?, Ka qaraso izuwa gareni kafin tsantsar farinciki yasa lumfashina d’aukewa.” Taqarasa maganar tare dasa hannuwanta ta rufe bakinta hawayen farinci na zubo mata a fuska, nad’e hannuwansa yayi akan qirjinsa yana kallonta yana murmushi, duk da ayanayin da ya ganta baiyi masa dad’i ba Amma farincikin ganinta yasa yakasa matsawa kusa da ita saboda nauyin da qafafuwansa suka yimasa, sunfi mintuna biyu ahaka kafi yafara takowa izuwa gareta yana cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Haba gimbiyar Abu sumayya! Wannan kukan da kikeyi ai saikisa hawayen dake zubowa daga idanuwanki su narkarmun da zuciya, kitashi mana na kalleki da kyau naga ko kin kula mani da kanki kamar yanda kika alqawarta mani kinji ‘yan matanaaaa…” Yaja qarshen cikin wani salon sigar lallashi da yasa batasan lokacin data saki dariya ba had’e da miqewa tana rufe fuska. “Sannu da zuwa annurin zuciyata, farincikina kuma uban ‘ya’yanah.” tafad’a cikin murmushi tana jifarsa da wani kallo mai cike da tarin ma’anoni kala kala. Tsabar jin dad’in kalaman da yaji na fito daga bakinta ya sashi d’aga kansa yana murmushi tare da kallon fitillun da suka haskaka harabar gidan, gyara tsayuwarsa yayi idanuwansa na akan fuskarta yana kallonta sanna yace. “Yawwa uwar ‘ya’yana, makullin zuciyata da kuma mabud’inta, Ina fatar dai nasameki cikin amincin ALLAH da kuma yardarsa.” “Sosai kuwa, domin badon amincin ALLAH dake tare dani ba da tuni kewarka da rashinka sun kaini kushewata.” Saida yayi dariya sannan ya d’ago kai yana kallonta yace. “Godiya ta tabbata agaresa daya tsare mani ke daga zuwa kushe don tseratar da rayuwar Abu sumayya daga fad’awa gararin duniya nahar abada, ya kike gimbiyata?. “Ina lafiya yanzu tunda gani ga ka kuma.” “Alhamdulillah, nayi farinciki sosai duk da dai naga kamar kinyi k’wabron kula mani da kanki, Ina fatar akwai banbancin kulawar da ajiyar dana baki acikin zuciyarki.” “Babu buqatar tabbatar maka da hakan domin ance labarin zuciya atambayi fuska, ai tsantsar kula da ajiyar kane dake cikin zuciyata ya haifarwa da gangar jikina shiga cikin wannan hali, kaine kawai na shiga taraddadin cewa ka kula mani da tawa ajiyar ko kuwa?.” “Haba ‘yan mata!, Ai wanzuwata awannan lokacin tare dake shine zai baki tabbacin cewa naba ajiyarki cikakkiyar kulawa, Alhamdulillah yau na karb’i sakamakon dake tabbatar da na kammala karatuna bayan adadin shekaru hud’u dana d’auka inayi cike da tarairayar qaunarki acikin zuciyata, hakan yasa na gaggauta dawowa agareki adaidai wannan lokacin da zimmar zamowa mijinki ke kuma mata kamar yanda na d’aukar maki alwashi, inafatar zaki amsheni hannu biyu ki maidani a gurbin da tun farko kika bani.” “Kash!..a gaskiya bazaka samu hakan ba domin na dad’e da cireka a wannan gurbin.” Tafad’a cike da zolayarsa tare da d’aure fuska ta juyar da kanta gefe, cikin fad’uwar gaba ya koma ta gefen data maida kanta yana kallonta. “Kamarya! Ban fahimceki ba gimbiya?, Wai kina nufin kin d’aukeni daga wannan gurbin kin bawa wani.. how? ” yafad’a yana tsareta da idanuwansa da suka soma canza kala. Kwashewa tayi da dariya harda tafa hannuwa tana nunasa, sake d’aure fuska yayi yana binta da wani irin kallo da yasa dole ta tsaida dariyar had’e da cewa. “Afuwan Abu sumayya!, Ba haka nake nufiba, taya kake tsammanin zan iya cireka ga wuri har in aza wani?, Wannan abune da bazai yuyuba kama dena tunanin hakan.” “Taya tunanina bazai bani hakan ba bayan da bakinki kikace..” “Don ALLAH kayi haquri da wasa nakeyi..” Kafeta yayi da idanuwa kafin yayi wata irin ajiyar zuciya ya juya mata baya. “Pls kayi haquri mana..” “Em’ehm..ni nayi fushi, dama d’azun kin b’atan rai da kikace natafi bakya buqatar ganina, sonki ne da yayi mun yawa yasa na iya dawowa garemu da kika fito” “Wayyo…kayi haquri mana, plsss…” Tafad’a tare da komawa gabansa tariqe kunnuwa, Dariya ya saki sannan yace. STORY CONTINUES BELOW  “Shikenan nahaqura, bari natafi dare ya somayi.” Nan take kamannin fuskarta suka sauya daga farinciki zuwa damuwa. “Meye gimbiya?” “Bana son katafi Abu sumayya, gaba d’aya shekarunnan hud’u a jigace na qarar dasu saboda rashinka da kuma ganinka, ka qaramun lokaci mana ko hasken daya d’iga azuciyata zai qara yawan da zai haskamun yau zuwa gobena.” “Kamar ya gimbiya?, So kikeyi na kwana anan ne? Ko bakiga lokaci naqara qurewa bane?” Saida ya duba agogon dake hannunsa sannan yace. “Kin gafa har goma da rabi takusa, gashi akwai nisa da inda zanje gidan baffan mamana, in dai akaina ne ki kwantar da hankalinki yanzu kullum muna tare kinji ko?” “Ka kasa fahimtata ne, Taya hakan zai faru abbana na nema ya aura mani duk wanda yaga dama naqi amincewa, sanadiyar hakan ya sanya mani tsauraran matakai,” “To kinga ya kamata ace natafi yanzu kamin ya sameni, na tabbata ko yanzu don baya gida shiyasa muka samu wannan damar, don haka kiyi haquri kinji ko?” ‘Daga masa kai tayi idanuwanta na tsiyayar da hawaye yacire hankacif daga cikin aljihunsa yamiqa mata. “Ki share wud’annan hawayen bana son ganinsu.” Karb’a tayi tayi kamar yanda yace sannan tamiqa masa ya karb’a ya mayar cikin aljihu, “In fad’a maki wani Abu?” Kad’a masa kai tayi yace “to yi murmushi mana tukuna, idan ba haka ba sai nafasa fad’a.” Murmushin da seda haqoranta suka bayyana tayi shima ya mayar mata had’e da cewa. “Yawwa gimbiyar Abu sumayya, ummu sumayya, haka nake son akoda yaushe ki kasance, in Sha ALLAH su dady na nan tafe gobe su nema mani aurenki, saboda haka kidena damuwa soon zan d’aukeki izuwa duniyar farincikinDana tanada mana kinji ko?” Saboda yanda farinciki ya rufeta batasan lokacin da tayi tsalleba had’e dayin dariya tana fad’in “da gaske Abu sumayya?.” “To kijira mana gobe kigani.” Ciro wata leda yayi a aljihunsa ya miqa mata sannan yace “Ina wayarki?” “Tana cikin nabaro.” “Ok ungo saka mani lambarki nasan yanzu kin canza layi ko?” “Eh amma ni ai inada naka, kaje kawai zan kiraka” “Nima fa na canza layi ‘yan matana” “Eh nasani mana.” Sallama yayi mata sannan yawuce saboda ganin takafe tanada sabon layinsa, wanda yake ganin abun da kamar wuya… Ai kuwa bai qarasa gida ba sai gashi yaga ankirasa da sabuwar lamba, Sanin yanda sukayi da ita yasa bai wani b’ata lokaci ba ya d’aga, muryarta yaji tace. “Kasamu abun hawa kuwa?” “Eyyeeee ashe da gaske kikeyi gimbiya, nasamu gashi har mun kama hanya.” “To Allah ya saukeka lafiya ya karemun kai daga sharrin qarfe, mutum da kuma aljani.” “Amin gimbiya,” yafad’a cike dajin dad’in addu’arta. ••• ••• ••• A can borno kuwa hajia nafeesa najen qesheqeshin cewa dady zaije nemawa little auren batool hankalinta ya tashi, tasan tabbas ba abunda zai hana dady zuwa sai in baya raye kuma duk yanda zaiyi ya wanke little daga kashin kajin data shafa masa awajen mahaifin batool sai yayi, don haka takasa zaune ta kasa tsaye har saida dady ya shigo, da yake yau zai dawo part d’in nata, ALLAH ALLAH tadingayi yayi sauri yagama cin abincin don ta maganta masa abunda ta qudurta aranta. STORY CONTINUES BELOW  Yana kammalawa tace. “Am Alhaji nikuwa Ina son yin magana dakai idan ka amince.” “Ina jinki hajiya nafeesa, injin dai ko lafiya?” Yafad’a tare da d’aukar jarida yakoma can saman kujerun dake tsakiyar falon ya zauna, biyo bayansa tayi ta zauna kusa dashi had’e dayin shiru na ‘yan mintota be sannan yace. “Shin kasan ko yaron nan shima son batool yakeyi naji ana zancen zakaje nemawa wanda bayada asali ita.” Kar ya fahimci inda zancenta yanufa amma sai yabasar yana qoqarin bud’o wani shafin jaridar yace. “Wane yaro kike zancen kuma wace batool d’in.” ‘dan muskutawa tayi daga zaunen da take sannan tace. “Shakur mana da batool ‘ya gidan kawuna alhaji umar fari dake zaune kano, yanzu hakan yana can kwance baya jin dad’i saboda yaji kana shirin zuwa nemoma wani bare ita gashi shi daya jima yana sonta, wlh alhaji zai iya rasa rayuwarsa akanta, shiyasa nace bari nafad’a maka don ya kamata kaduba wannan al’amarin. Cigaba yayi da bud’a jaridarsa batare daya tankata ba har natsawon mintota da tagaji tace. “Haba Alhaji!, Dakai fa nake magana kayi mani shiru..” “Mts..shin mema kike cewa?” Duk da ranta ya b’aci haka tasake daurewa ta maimaita masa tanaji kamar ta qwalla ihu saboda abunda yayi mata, ajiye jaridar yayi sannan ya aza qafarsa d’aya akan d’aya yana kallon yanda tacika tayi fam, yasan kad’an take jira yanzu tafitinesa ta hanasa bacci mai dad’i don haka sai yace. “Shikenan naji, Kuma in sha ALLAH kafin muje zanyi tunani akai, idan naga yafi dacewa da ita shikenan sai ayo maganar dashi, duk da shima yaron da kikacewa bayada asali kakarsa na acikin gidannan kuma a matsayin matata baza’a ce abawa daji gida bai qoshi ba, don haka in sha ALLAH za’ayi abunda ya dace, Ina shi shakur d’in?.” Washe baki tayi saboda taji dad’in yanda haqarta zata cimma ruwa anata tunanin sannan tace. “Yana can sashensa kwance tun safe ba inda yaje.” “Ok Bari nadubosa.” “Ai daka bari har nan da zuwa safiya, don inaga yasamu yayi bacci yanzu kada atashesa.” Tafad’a gabanta na fad’uwa don bata masan inda yaron nata take ba tana qoqarin dakatar dashi, cigaba yayi da tafiyarsa yana fad’in. “Eh bara dai nadubosa, ai kamata yayi tun wuri ki sanar dani, yanzu idan har ciwon yayi masa tsanani ya cutar dashi ban sani ba, sai kice a’a.” Yasa kai ya ficewarsa. Da sauri taje ta d’au wayarta takira shakur lokacin yana zaune yana game da wayarsa hankali kwance. “Kai shashasha, me kakeyi yanzu?” “Zaune nake Ina game awayana lafiya mom?” “Maza, maza, kanemi waje ka kwanta kuma katabbatar ka lullub’a, nafad’awa dadynku cewa bakada lafiya saboda kaji zaije nemawa wannan shegen auren batool, shine zaizo dubaka, maza ka kwanta kafin ya qaraso.” “Mom nifa Ina da..” “dallah rufamun baki sakaran banza, kayi abunda nace kawai.” Jefar da wayar yayi agefe tare da komawa yakwanta saman gadonsa ya lullub’e yana qunquni, kasancewar qofar d’akin abud’e take kuma ga fitila akunne yasa har dady yaqaraso bai sani ba, Shikuwa dady qunqunin da yakeyi ya tabbatar masa da cewa idanuwansa biyu, shigowa yayi ciki ya tako har gaban gadon nasa ya zauna wajen gefen kansa cikin muryar dake tabbatarwa da Shakur bawasa atattare da mahaifin nasa yaji yace. STORY CONTINUES BELOW  “Kai Shakur tashi!” Aikuwa kamar jira yakeyi yayi zumbur yamiqe yayi zaune tsakiyar gadon idanuwansa wuqiwuqi babu alamun ko ciwon kai yayi balle zazzab’i, Saida dady yaqare masa kallo sannan yayi murmushi had’e da cewa. “Meyake damunka ne?” “Ba.ba.babu komai dady zazzab’ine kawai” yafad’a cikin rawar murya yana b’ab’b’ata rai, d’aure fuska dady yayi sosai had’e da cewa “Ok. To meye alaqarka da batool qanwar mahaifiyarka, naji ance kamar kana sonta, meye gaskiya?” Har zaiyi magana dady ya nunasa da yatsa yana zaro masa idanuwa. “Ka tabbatar kafad’amun gaskiya, idan nace gaskiya Ina nufin magana qwaya d’aya tilo wacce batada tabiyu, samuwar ta biyunta kan iyasa na d’auki mummunan mataki akanka, Ina saurarenka!” Wani qugi Shakur cikinsa yayi don yasan halin abban nasa, idan yace abu to tabbas zaiyisa, wani irin zufane ya keto masa ya shiga sharewa tare da kallon mahaifinnasa yace. “Dady maganar gaskiya ni bana son batool, asalima bamu fiye jituwa da ita ba, mom ce ke matsamun akan innemi aurenta saboda dani tafi dacewa ba little ba, nayi qoqarin nuna mata banison yarinyar saboda cin mutuncin da take jawowa tana yimani amma taqi ta fahimta, Dana matsa matsa mata da zancen sai tace idan har nakoma musa mata akan maganar zan fuskanci fushinta, shiyasa kawai nahaqura Ina qoqarin cusawa zuciyata yarinyar.” Murmushi dady yayi had’e da bubbuga bayansa sannan yace. “Gud, kanada wacce kake so yanzu?” “Eh dady, amma mom bata son na aureta.” “Wacece ita?, kuma meyasa bata sonta?.” “Qanwar matar ya faruq ce dady, sunanta hafsat amma ana kiranta iman, mom Bata sonta ne wai saboda ammie tunda yayarta surukar tace.” Tsaki dady yayi saboda gaba d’aya alamurran hajia nafeesa ba komai acikin Inba tarin hauka da shirme ba, bata tab’a tanadar qwaqqwarar hujja cmai ma’ana sai shirme, “Katabbata yarinyar na sonka kamar yanda kake sonta?” Dady yafad’a yana kallonsa. “Eh dady.” “Shikenan! Koma ka kwantawarka, Kuma katabbatar kayo arwala ka kashe fitilar d’akin kafin ka koma kaji nafad’a maka.” “To dady nagode saida safe.” “ALLAH yatashemu lafiya, ubangiji yayi maku albarka.” “Amin dady” Shakur yafad’a tare da yaye bargon daya lullub’a dashi ya sauko daga saman gadon tare da wucewa toilet yana maijin wani sanyi aransa, dama duk abunda yake yiwa batool mom d’insa ke sashi, shi kuma sai yana amfani da wannan damar don ya tunzura batool taqara tsanarsa aranta yanda koda ance za’a had’a aurensa da ita bazata yarda ba. Koda dady yakoma bai cema hajia nafeesa komai ba yayi shirinsa na kwanciya ya kwanta yana mai addua’ar ALLAH yatashesa lafiya. Da sassafe yakira faruq qanen dr, yace yaturo masa lambar mahaifin surayya matarsa, bayan yaturo masa sukayi magana mai tsawo sannan yakashe yakira dr, shima nan sun d’an jima kafin yakashe yafad’a toilet yayo wanka. Misalin qarfe 9:30 na safe dady yagama shirin tafiyarsa kano yashiga sukayi sallama dasu umma da ammie sannan yadawo itama hajia nafeesa sukayi sallama batare daya nuna mata komai ba, so take ta taddo masa da zancen amma ayanayin da tagansa ciki sai tad’auka haqartace ta cimma ruwa. Koda yafito tana biye dashi ta rakoshi Dr da faruq na tsaye bakin mota suna jiran fitowarsa don tare zasu fita tawani galla masu harara aranta tana mai jin kamar takamo su tashaqe tsabar tsanar da tayi masu. STORY CONTINUES BELOW  Kai tsaye gidan iyayen matar faruq suka nufa su uku lokacin mahifinta shima yakirawo ‘yan uwansa su uku sun iso suka nemawa shakur auren hafsat (iman), iyayen nata sun tarbesu hannu biyu kuma sun amince da maganar don seda suka tambayeta tace eh tana sonsa sannan suka bashi ita, yarage sadaki da sa rana yarage, saida sukayi masu godiya sosai sannan suka baro gidan suna yabawa nagartar sarakanan na faruq. A bakin titi suka ajiye faruq su kuma suka kama hanyar kano. Suna Isa misalin qarfe uku na rana suka nufi gidan baba balarabe kai tsaye suka samu anhad’a masu ‘yar qwarya qwaryar liyafa don dama yasan da maganar. Bayan sunci sun sha sun qoshi baba balarabe ya d’auko masu zancen mahaifan little ta b’angaren mahaifinsa inda ya nuna masu bai kamata aje nema masa aureba bada suba saboda haqinsu ne, asalima sun fisu qarfi dashi, nan dai yazauna ya labarta masu duk abunda yafaru da yanda yahad’asa da dangin mahaifina nasa tacikin sirri, sun matuqar gamsuwa tare da fahimtarsa, kuma sunyaba masa bisa qoqarin da yayi inda suka d’aukar masa alqawarin cewa suma zasu riqe wannan sirrin batare da sun bari umma da Rashida sunji ba har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta, anan yake sanar dasu cewa ai yariga daya fad’amasu baffa zancen yanzu haka shi little yana can tare zasu dawo dasu. Ana kiraye kirayen sallar la’asar su baffa suka iso gidan baba balarabe, sunji dad’in yanda ya nuna muhimmancinsu acikin sha’anin tare da yimasa godiya sannan baba balarabe ya gabatar masu dasu Dr. Yauma baffa seda yayi kuka yanata sakawa Dr albarka bisa taimakon da yayiwa Rashida da kuma gudan jininsa little alokacin da suke matuqar buqatar sa, hakama suka taru shida baffa Usman suka dinga yiwa dady godiya har saida yafara jin kunya don kusan duka sun girmesa, musamman baffa, Dr kuwa shidai mamakine ya ishesa da aka nuna masa baffa amatsayin mahaifin baban little wanda yasan ranar da sukaje qauyen shida Rashida bashine sukayi magana dashib amatsayin kakan little, asalima gaba d’aya baya cikin su biyun don haka sai yafara tunanin tabbas akwai wata aqasa acikin al_amarin Wanda su Basu sani ba, koma dai meye shi Wanda yagani tabbas yanada nasaba dasu don ga kamanninsu da shi nan, yana wannan tunanin ne suka miqe zasu tafi can gidansu batool d’in, saidai awannan karon qin binsu yayi saboda aganinsa su hud’un sun wadatar a matsayinsu na manyan iyaye agaresa. Dady shike jan motar sai baffa Usman a gefensa, baba balarabe kuwa da baffa suna baya sannan suka bar qofar gidan tare da nufar unguwar sharad’a phase 1. Dama tuni little ya sake kiran batool ya jaddada mata zancen zuwan iyayen nata don itama ta sanar da nata iyayen, cikin farinciki batare da wani shakku ko shayi ba taje ta iske su uncle Hassan da Hussain lokacin suna zaune tare da mahaifin nata da ko kallo bata ishesa ba a harabar gidan tasanar dasu, Murmushi uncle Hassan yayi had’e da cewa. “To yaushe!” “Yanzu uncle h.” Tafad’a tana dariya tare da kallon mahaifin nata, tsabar takaicinta da irin fand’arewar data yimasa yasa yayo kanta da niyar mammaketa da sauri suka rirriqesa ita kuma taruga da gudu cikin gida. Subhanallahi Yaya wai meye haka?, Shekarunka fa jasukeyi kadena biyewa yarinyar nan saboda duk abunda tayi kaine sila kuma kai ka d’orata akai, don haka yazama dole kayi haquri da yanda halinta take ko kuma da kai har ita kudinga ba juna wahala. “Meye laifin da nayiwa yarinyar nan da gaba d’aya take son maidani wani shashasha, meye zunubina agareta da bazata hakura da zab’inta ba tabi nawa?, meyasa?, Ko don taga na nuna mata soyayya fiye da sauran ‘yan uwanta shine zata nemi tozartani da gwada mani iyakata, ni zatayiwa taurin kai da kafiya don akan wani banza dabata san ainahin ko waye shiba?, To wlh tallahi hassan nafiso in kakkaryata nazubata akwandon sharah dana aura mata wannan yaron da bayada asali.” Cikin b’acin rai uncle hussain ya sakesa daga riqon daya yimasa had’e da cewa, “Ai shikenan, jeka gata can ka kakkaryata in kaga dama ma karabata da lumfashinta yaya, wai har kamanta lokacin da muke lusar dakai illar soyayayar da kake gwadama yarinyar nan, kamanta yanda gaba d’aya kanuna mata fifiko fiye da sauran ‘ya’yanka daka haifa sai kace su bakai ka haifesu ba?, kamanta yanda kai tsaya kafad’a mana cewa babu abunda zata bid’a aduniya ka hanata shi matuqar kana raye?, To wlh anzo wajen! Saboda tu tana qaramarta kasaba mata da yimata duk abunda take so koda kuwa ba daidai bane, katuna anan cikin gidan kake nuna ba ‘yan uwanta kad’ai ba hattamu dake matsayin iyayenta zaka iya haqura da duka ra’ayinmu dama naka ra’ayin kabi nata, ahaka tarayu bisa turbar da kake buqatar tarayu da ita, shine kwatsam alokaci d’aya zakace ta canza, kaima kasan abune da bazai tab’a yuyuwa ba, koda kuwa zai yuyu to bata hanyar wannan tsanar da kuma tsaurarawar da kake yimata ba, ka lallab’ata kamar yanda kayi tun farkon tasowarta wataqil ALLAH zai taimakeka tacanza koba duka ba, da kake zancen kafiya da kuma taurin kai ai jininka keyawo ajikinta badon haka ba qila data sauko tabi naka ra’ayin.” Yana gama fad’ar haka yabar wajen ya wuce part d’insa kamar zai tashi sama, hajia shafa matarsa na kitchen tana girkin abincin dare yakira sunanta da sauri tafito saboda yanda taji muryarsa cikin b’acin rai. “Ki qara abinci saboda zamuyi baqi.” Haka kawai yafad’a yajuya yawuce d’akinsa ransa ab’ace, sosai idan batool d’in tayi wani abun yake son hukuntata amma daya tuna yanda mahaifinta yanuna masu zai iya samun matsala da kowa akanta da irin yanda ya sangartata sai yaji yakasa, saboda kwatakwata batada laifi, kome tayi shiya jawo da hannuwansa don haka yake zuba mata idanuwa matuqar abun bazai cutar da itaba don kawai yayan nasu ya d’auki darasi kuma yagane illa da kuskuren daya aikata abaya ko don nan gaba ya kiyaye. Abba kuwa kallon uncle Hassan yayi had’e da cewa. “Kaji me d’an uwanka kefad’a mun?, Kaji maganganun dake fitowa abakinsa akaina, meye kuskuren da nayi da zaiga laifina?, Waye baya son d’ansa?, Waye baya buqatar ririta d’ansa da kuma nuna masa gata idan hakan tasamu da zaiga laifina cikin kulawar dana bawa batool?” “Ashsha wannan shine laifin naka yaya kai kuma ka kasa fahimta!, A al’adar malan ba haushe yarinya najin nauyin tunkarar iyayenta da maganar za’azo neman aurenta, Amma saboda sangartawar da kayiwa batool da nuna mata duk abunda tayi daidaine shiyasa bako kunya tazo kai tsaye tafad’a mana kuma agurinta wanan daidaine ba wani abuba, don haka ni atawa shawara ka lallab’a yarinyarnan hakan zai iyasa tafahimci me kake nufi.” STORY CONTINUES BELOW  “Au kenan kaima kana goyon bayanshi kenan?, Ya zauna yafad’a mani magana sannan kaima kabiye masa?, Shikenan naji na b’ata batool, nayi alqawarin zanyi qoqarin gyarata tahanyar zab’a mata wanda yadace da ita tayanda gobenta zatayi kyau, don haka wlh kaji narantse kada ‘yan iskan da suka zo mani gida, kaje kafad’a mata cewa takirasu tasanar dasu ni mahaifinta nace kar inga kowa agidana.” Sheqeqe uncle Hassan ya kallesa kafin yace. “Tunda kaine mahaifinta kamar yanda kafad’a mezai hana kaje da kanka ka sanar da ita, kasani muna matuqar girmamaka da kuma yimaka biyayya Amma hakan bazaisa mu walaqanta mutane ba don sunzo neman abu wajenmu tunda ba gadon iyayenmu bane, alqawari d’aya zanyi maka shine, bazamu bayar maka da ‘yaka ba tunda baka buqatar hakan.” Yana gama fad’ar haka shima yabar wajen. Safa da marwa Abba ya shigayi a qarqashin ‘yar rumfar dake gefen harabar gidan tasha tayils da kujeru na alfarma, bini bini ya kalli agogon hannunsa tare da bakin gate d’in, gaba d’aya yakasa zaune kuma yakasa tsaye, yaqi komawa part d’in nasa yana dakon isowarsu, yaci alwashin ko suwaye suka zab’i maida yaron da akace shegene izuwa d’ah don a yaudaresa tahanyar aurar masa da ‘yarsa sai yasasu sunyi nadamar zuwa gidan, ji yakeyi gaba d’aya baya buqatar wakilcin ‘yan uwan nasa shi da kansa zaiyi abunda yake ganin shine daidai kuma shi zai sama masa salama azuciya. Aikawa uncle Hassan yayi aka kirwo masa uncle Hussain ya fad’a masa abunda yayan nasu yace da kuma shi amsar daya bashi, shiru uncle Hussain yayi zuciya na cinsa kafin yace. “Kace ya rantse kar wanda yashigo masa gida?” “Eh, yanzu banma san ko meye abunyi ba.?” “Ka qyalesa ai gidan ba shikad’ai keda shiba, sannan ‘yar tasa ma da yake zance muma munada haqqi akanta don haka zasu shigo kuma tabbas dole yayi kaffara.” “A’a hussain kada kayi haka, muqyalesa mana, bana son mubiye masa har yakai ga yayi wani rashin mutunci da zai shafi ita yarinyar, saboda idan ya walaqantasu kamar ya kafa mana wani mummunan tarihine agida, mutane zasuji shakkun koma dawowa gidannan da sunan neman aure kaga kuwa maganin ayi kar afara.” “Shikenan Hassan, amma matakin da zan d’auka naqarshe kar kace komai akai, idan zuciya Yaya ke taqama da ita ai duka Abu guda yayimu dashi don haaka jeka ka shirya ance suna isowa, zansa ayi yanda yakamata.” “A’a hussain..” “Don ALLAH katafi hassan nasan meya kamata kuma nafahimci abunda kake nufi, bazanyi abunda zai jawo zubewar kimar gidannan ba, kawai jeka ka gyara kafin su iso.” Kallonsa uncle Hassan yayi don yasan indai zuciyace to d’an uwan nasa yadama yayan nasu ya shanye, shi kanshi yanada ita amma ba irin tasu ba sai idan ankaishi bango yake nuna tashi, murmushi yayi sannan yace. “Shikenan uban d’iya, ALLAH ya huci zuciyarka.” Dariya uncle Hussain yayi sannan yakoma part d’in nasa. Qarfe biyar nabugewa motarsu dady natsayawa qofar gidan, Abba kuwa sai raba idanuwa yakeyi yana jiran yaga shigowarsu, abunda bai sani ba kuwa tuni Uncle Hussain yasa aka yimasu shimfid’a a qarqashin inuwar fulawowin da sukayi rassa ajikin katangar gidan daga can waje, qatuwar darduma aka shimfid’a tare da kujeru qattunan timatimai irin na sarauta d’in nan yasa aka qawata wajen dasu sannan yasa aka kai abincin aka shirya masu da lemuna da ruwan goruna masu sanyi, duk anyi hakanne ba tare da sanin Abba ba saboda ta wancan d’ayan gate d’in da ba’a fiye bud’ewa ba dake ca qarshen gidan uncle yasa akabi da kayan Kuma suma tacan sukabi suka fita, kallon wajen uncle Hassan yayi ya kwashe da dariya had’e da cewa. “Banda fitina irin na yayanmu da rufin asirinmu zai samu wannan tonon silili awaje kowa sai yagama da ganinmu, gaskiya wannna abun baiyi dad’i ba duk da dai konan d’in ba laifi ma fake da sunan shan isaka.” STORY CONTINUES BELOW  Murmushi uncle Hussain yayi had’e da cewa, “Ai duk laifinka ne da kake neman abisa ahankali, wlh indai Yaya ne sai anyi wuta da wutane dashi sannan za’a daidaita, Ina girmamawa awannan sha’ani ai andaiji kunya in anjita.” Haka suka yita firarsu suna dariya har zuwa yanzu dasu dady suka iso, cike da girmamawa suka taso suka tarbesu tare da yimasu iso zuwa inda shimfid’ar take, yanayin su baffa da baba balarabe da suka gani baisa sukaji komai aransu ba balle surena arziqinsu sukuma hakan da suka gani an ajiyesu awaje Bai kawo masu komai arai ba, dady kad’aine ransa yaso bashi wani abu amma sai ya basar, cikin mutuntawa da karrama juna suka gaggaisa kafin uncle Hussain ya mammatso masu da kayan abincin yana fad’in. “Bisimillah.” “Murmushi baffa yayi had’e da cewa Alhamdulillah, mungode sosai amma aqoshe muke.” “Haba alhaji ai ba’ayi haka ba ko ruwane yakamata kusha kafin mushiga maganar abunda ya taramu anan, akace baqonka ai annabinka ko kuwa?” Uncle Hassan yafad’a duk sukasa dariya. Dady yafara d’aukar ruwa ya tsiyaya a cup tare da lemu yasha sannan suma su baffa suka sha, hakan kuwa baqaramin dad’i yayiwa su uncle Hussain ba. Cikin tausasa murya da girmamawa duk da kuwa dady ya girmesu yayi masu bayanin abunda ke tafe dasu cewa sunzo nemawa d’ansu ne izinin neman auren ‘yar wajensu batool daya had’u da ita acan gidansa lokacin da taje hutu wajen matarsa hajia nafeesa, saboda bawani sanin dady sukayi sosai ba suna dai yimasa kallon sanine yasa sai alokacin suka gane cewa ashe shid’inne mijin hajia nafeesa ‘yar qanwar tasu da suke qoqarin tunano inda suka san fuskarsa. Bayan yagama yimasu bayani uncle Hassan ya sauke ajiyar zuciya had’e cewa. “To masha ALLAH, kaga ashe kai surukin mune, munata faman laluben inda muka sanka duk ta dalilin rashin qarfafa zumunta, lokacin da kuka iso naso na ganeka amma a Ina shina manta tinda andad’e ba’a had’u ba, zumuncinne yanzu sai ahankali mutane bamu cika bashi muhimmanci ba.” ‘Dan russuna kai dady yayi had’e da cewa. “Wlh kuwa, abubuwane da sukayi yawa gashi ba gari d’aya ba saidai ayita haquri.” “Eh da haka kuwa, ALLAH yayi taimako.” “Amin ya rabbi alhaji.” “To alhamdulillah munji abunda ketafe daku kuma munji dad’i da har ALLAH yasa d’anku yaso jininmu, kaga zumunci zai qara qarfafa idan ALLAH ya daidaita abun, saidai wani hanzari ba gudu ba, kinsan ita maganar aure anfiso ayita bisa kan gaskiya da gaskiya, ni da kuka gani tare da d’an uwana annan, qannene ga mahaifin ita wannan yarinya da d’anku keso, ita kuma matarka ya nuna dady, ‘yace ga qanwarmu kasani uwa d’aya uba d’aya duk muke ba inki bawai, don haka bazamu b’oye maku gaskiya ba maganganu sun zo mana ko ince sunzo Kai tsaye ga kunnuwan mahaifin yarinyarnan cewa yaronku bayada asali wanda hakan yasa mahaifinta har yayi mata tsakani dashi bayan yasa anyi masa bincike acan garin antabbatar masa da cewa yaron nan bayada uba, kuyi haquri kada kuga nayi maku cin fuska, muna so musan sahihancin maganar ne don shi yayan namu yakafe akan bazata auresa ba sai gashi kuma yarinyar ta sanar damu zancen cewa zakuzo nema masa aurenta, hakan yasa mukayi tunanin zaunawa musaurareku don jin gaskiyar zancen.” Wani irin dimmmmm…baffa yajiya aransa duniyar ta shiga jujjuya masa saboda kalmar da yaji cewa wai jikan nasa shegene bayada uba, badon ALLAH yasa yana zaune bane to da Babu abunda zai hanasa fad’uwa adaidai wannan lokacin, wasu zafafan hawayene suka zubo masa a fuska da sauri yasa hannu yagoge yanajin wani qunci tare da takaicin d’ansa aransa. Dady kuwa gabansa ne yafad’i jin kalmar da duk duniya mutum d’ayane yaji nayiwa little ita wato matarsa hajia nafeesa wacce baya tantama akan komeye yafaru itace ta assasashi. STORY CONTINUES BELOW  Ganin duka yanayin da suka shiga yasa uncle Hussain jin badad’i aransa Amma ya za’ayi dolene suyi haka don susan yanda zasu kamo bakin zaren, cikin tausasa kalamansa yace. “Ina nemawa d’an uwana dani kaina yafiyarku idan maganganunsa sun tab’a maku zuciya, har ga ALLAH ba muna nufin zamu yimaku walaqnci bane don kunzo neman alfarma wajenmu, a’a kuyiwa maganar kyakkyawar fahimta akan muna so kai tsaye mu binciki sanin kowaye yaronku tawajenku saboda munyarda daku, kuma Ina zaton ko a misulunce hakan ba laifi bane, idan bakwa buqatar hakan kuma to muna baku haquri tare da cewa kubamu d’an lokaci kafin muje muyi bince akai.” Da sauri baba balarabe yace. “A’a babu buqatar hakan, asalima godiya yakamata muyi maku dakai tsaye kuka fuskancemu da wannan magana batare da kunje waje wurin neman sanin gaskiyarta ba, ni sunana malan balarabe qane ga mahaifin uwar yaron, Ina zaunene awani qauye da ake kira yarimawa, wannan kuma ya nuna baffa sunansa malan Idris Aliyu wato mahaifin baban yaron tare dashi kuma akwai qanensa malan Usman Aliyu, su kuma suna zaunene a qauyen bebeji, shi ya haifi uban wannan yaro da ake shegantawa ni kuma amatsayina na qanen mahaifin mahaifiyar yaron ni nabada aurenta a hannun wannan qanen mahaifin babansa bisa sadaki naira dubu hamsin, zaku iya zuwa atsakankanin wud’an nan qauyukka guda biyu kuyi bincike akan munda maganar alaqarmu don tabbatar da hakan.” A yanayin da yake yimasu bayani duk daqiqancin mutum dole yafahimci cewa yana fad’in gaskiyar zancene daga qarqashin zuciyarsa. A hankali baffa ya d’ago kai tare da fara basu labarin dalilin da yasa aka jingina jikan nasa da cewa shegene, tun daga farko har zuwa qarshe batare daya b’oye masu gaskiya ko d’aya ba har yana zubar da qwallah, dady me ya d’ora masu cigaban labarin daga qarshe yakira Dr. yace yazo maza maza yana son ganinsa tare da bshi address d’in inda zai iskosu, ba’a jima ba saiga Dr ya iso dady yace ya sanar dasu kowaye little da mahaifiyarsa, kallonsu yayi d’aya bayan d’aya yace “Meke faruwa dady?, Bazasu bashi auren tabane har sai an bayyana masu abunda yafaru akan mahaifiyarsa?, Ganinku bai isa ya gamsar dasu ko waye Nuraddeen d’inmu ba?, Idan ko hakane inaga babu buqatar hakan saboda babu yaddar da zata jawo auratayya a tsakani.” “Ya isa, kayi abunda nace maka.” Dady yafad’a in a serious tone, ganin babu wasa a fuskarsa yasa yafara labarta masu halin daya tsinci mahaifiyar little har zuwa lokacin data had’u da iyayenta agidan mahaifinsa, anan dady yafad’a masu yanda akayi har yasan mahaifin Rashida wato kakan little, lamba da address d’in abokinsa da marigayi ke karb’ar takalmi awajensa Wanda nanne yahad’u da baba yabasu yace suje wajensa suqara yin bincike akai. Gaba d’aya duk inda ilahirin jikin uncle Hassan da Hussain yake saida yayi sanyi, sosai kunya da dana sanin tambayoyi da kalaman da sukayi masu tarufesa, sun matuqar tausayawa rayuwar baffa tare da jinjinawa qarfin imaninsa haka sun girmamawa karamci irin na surukin nasu wato dady da d’ansa, da za’a samu irin wud’annan mutanen aduniya to tabbas za’a zauna lafiya cikin wadatuwa da ni’imar ALLAH. Muryar baffa Usman suka jiyo yana fad’in. “Little dake son yarinyarku ba shege bane kamar yanda kuka jiyo daga bakin qananun mutane dake yiwa alamari hawan qahura, su zauna akai suyi sharhin abunda basuda masaniya akai, mune iyayen babansa kuma da izininmu yaje karatu waje, qaddarawar ALLAH da kuma jarabtawa da wanzuwar alqalamin qaddara akan yaronsa tahanasa dawowa qasarsa zaku iya zuwa can ma’aikatar ilimi a b’angaren qananan malamai dake da rauni data taimaka musu ku bincika don kutabbatar da hakan domin ita taturasu qasar, bamu fidda rai da dawowar mahaifinsa ba a kowane lokace kmar yanda bazamu dena cigaba da rayuwarmu ba har sai lokacin da ALLAH ya dakatar mana da ita, Kuma in Sha ALLAH kusa ko nesa zai dawo garemu don tabbatarwa da duniya cewa d’ansa ba shege bane da yardar ALLAH.” Cikin sanyinyin murya uncle Hussain yace. “Kuyi haquri, kuyi haquri, shikad’ai zamuce, damu bawai mu muka sheganta yaronku bane, kawai munfad’i abunda mukajine daga bakin wasu, amma yanzu mun gamsu da bayaninku d’ari bisa d’ari, dama haka ubangiji yace, ” _yaa ayyuhallazina amanu injaa akum fasiqun binaba’in fatabayyanu antusibu qauman bijahalatin fatusbihu ala maa fa’altum nadimuun_” ma’ana ” _yaku wud’anda kukayi imani!, Idan fasik’i yazo maku da wani babban labari, to, kunemi bayani, domin kada kucuci wasu mutane acikin jahilci, saboda haka ku wayi gari akan abin da kuka aikata kuna masu nadama_, Shiyasa dashi yayan namu yayi nasa binciken mukaga yadace mu tuntub’eku da maganar kamar yanda ALLAH ya umurta don kaucewa aikata abunda zamuzo muyi nadama akai kuma alhamdulillah bamu d’auki wani matakiba koyin abunda zaisa muyi nadamar abunda muka aikata, don haka a matsayinmu na iyayen batool mun ba Nuraddeen dama yaci gaba da nemanta har zuwa lokacin da zamu sake waiwayarku akan batun aurensu,” STORY CONTINUES BELOW  Cike da farinciki baffa ya d’aga hannu sama yayiwa ALLAH godiya sannan suka had’a baki shida dady dake murmushi sukace. “Bakomai mungode, mungode sosai ALLAH yatabbatar da alkhairi.” Nan suka shiga musabahar hannaye kowanensu fuskarsa na nuna jin dad’in yanda abun yakasance, suna qoqarin tafiya aka kira sallar magrib, don haka uncle Hassan yaroqesu akan subari sai sunyi sallah sunci abinci sannan sutafi, haka kuwa akayi anan saman dardumar baba balarabe ya jasu limanci sukayi sallah sannan sukaci abincin, cikin qanqanen lokaci suka saba da juna har sukayi musayar lambobi sannan suka wuce cikin yaba nagartar juna da fahimta. Suna wucewa Abba na isowa wajen kamar zai tashi sama, kallo d’aya sukayi masa dariya ta soma kuccikke masu da sauri suka gintse, “Nagode da maidani d’an iska da kukayi a matsayina na yayanku, wato ni Ina can zaune ina jiran isowarsu ashe ku har kunyi mani yanda kuke so sai dai cikin anguwa atareni ana tambayar halama yau baqi nayi?, Yau kun nuna mani cewa ba bakin komai nake ba agareku kuma ban isa gareku ba.” Sannan yajuya yanufi cikin gida, ayanda yayi maganar yasasu jin cewa kamar basu kyauta masa ba don haka suka bi bayansa suna bashi haquri, Kusan sati ya d’auka yana fushinda kowa agidan, hatta abincin gidan bayaci, haka kuma baya wuni agida bacci kad’ai ke dawo dashi gidan shima safiya nawayewa zai tafiyarsa, sun matuqar damuwa da hakan ganin yanda gaba d’aya gidan yakoma ba dad’i suka dinga binsa suna bashi haquri, saida suka had’a gaba d’aya gidan har matansu da yaransu sukayita bashi haquri sannan suka samu daqyar ya hanqura saidai yatabbatar masu cewa ya haqura kad’aine bisa laifin da suka yimasa amma akan zancen auren batool da wannan yaron har yanzu yana nan kan bakansa. Qoqarin fahimtar dashi da yimasa bayani sukayi amma sai yaqara birkice masu akan wai shi be yadda iyayensa bane saboda anfad’a masa cewa had’in bakine akayi da mijin hajia nafeesa aka d’auko hayar mutanen da sukazo a matsayin iyayensa. “Ya ALLAH! Yaya wa Kuma ya sanar dakai haka?, wlh qaryane yaya, mahaifinsa na qasar waje sun riqesa daya gama karatu, don ALLAH Yaya ka tausayawa yaran nan tunda suna son junansu” Uncle Hassan daya tsani tashin hankali yafad’i hakan cike da damuwa, shi dai hussain tsoron ALLAH ma yahanasa cewa uffan sai kallon yanda yayan nasa ke kumfar baki yakeyi…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Gaisuwa da fatan alkhairi agareki Auntynah *AUNTY RASHIDA GARBA 😍* sincerely i rilly dont know how to start thanking you for all what you did to me, you have encouraged me so much in my difficult time when i lost hope that i could ever do something like this, you were the one to push me on things, i am really grateful that i have such a wonderful sister like you in my life, and i just want to express my gratitude and my thanks to you. You are truly wonderful sister so thank you for the support, like, luv and everything to me..haqiqa karamcinki agareni mai girmane da bazan tab’a iya mantawa dake ba, i pray almighty ALLAH to give you a wanderful charming husband dt will luv you, care with you, support you and Charis you for ever in life,👏 *LSM AUNTY RASHIDA*_ STORY CONTINUES BELOW  Page___86💎 Komawa yayi akan kujerar kusa da ita ya zauna ahankali yace. “Gimbiya tah, meya jimaki a goshi?” Yana nuna wajen da yatsa inda yaga filista da hajia mama tasa mata jiya inda goshinta ya fashe. ‘Dan shafa wajen tayi had’e dayin murmushi sannan tace. “Abu sumayya ya kake?” “A yanzu lafiya klw nake tunda gani gaki.” “Kaga yanda rayuwa ta sauya mana ko, meyasa hakan take faruwa damu, musamman ni da zuciyata gaba d’aya yakasa hango mun kowa sai kai, gashi sai wahala rayuwa ke bamu, mahaifina na matuqar sona, ya kula dani sosai, yabani farinciki fiye da tsammaninka, saidai yakasa karanto zuciyata yafahimci irin tsantsar qaunar da nake yimaka, d’ago kanta tayi tana kallonsa idanuwanta sun cika da hawaye tace. ” _Wish that i spend some time with you only the time where there would be two of us looking at the sky and gazing at the stars, wish that we would just run away from here and run away so far, i was thinking about this the whole day and i just want to say that my love for you is so true, no matter what the hardest time it’s i will be thinking of you, when i think about you, my mind goes numb, i am not me, i become so dumb, because our love was so strong, It was to me you belong, then why all this happened, I miss you so much Abu sumayya_” Kallon cikin kwayar idanuwanta ya dingayi yana karanto tabbacin gaskiyar duk wata kalma da take fad’a, yarasa wane irin so ne takeyi masa haka, yarasa dalilin da yasa ta qaunace haka, tabbas shima ya cancanci yabata dukkanin irin wannan soyayyar da take nuna masa koda hakan na nufin zai rasa farincikinsa da natsuwarsa nahar abada, wani sassanyan murmushi ya sakar mata lokacin data kai qarshen kalamanta had’e da cewa. “Karki damu gimbiyata, a halin yanzu ina rayuwane wa sonki da qaunarki, nayi maki alqawarin zan iya bada rayuwata domin ceto soyayyarmu, ba ina nufin zanmutu bane akan soyayyarmu ba, Ina nufin na shirya tsaf akan zan fuskanci duk wata matsala ko qalubale don naga na killaceki a inda yakamata, zan rayu don in cika maki duk wasu burikanki da mafarkanki akaina, zan biya soyayyar da kika nuna mani da zallar halacci da kuma karamci don haka kidena damar da kanki, tun asali qaunace ALLAH yasaka tsakanin ni da kuma ke, so ya biyo baya ne kawai, kiyarda dani zan baki duk wata kulawa, zan maye maki farinciki da wannan quncin da kike ciki, zan share maki wud’annan zafafan hawayen na maye maki gurbinsu da sanyayyun hawayen farinciki, Ina so kisa aranki gimbiyata, Abu sumayyanki na sonki kuma yana qaunarki har zuwa fitar lumfashinsa naqarshe,” Sun jima suna fad’awa junansu kalamai masu dad’i da kuma sanyaya zuciya da suka sake basu qwarin guiwar cewa komai rintsi komai wuya zasu rayune kad’ai idan suna tare a qarqashin inuwa d’aya, ganin lokaci na dad’a ja gashi Rashida tace dole yau yamaidata gida yasa yamiqe yaje kitchen ya d’ibo abinci ya zauna agabanta yana ci. Cin abincin yakeyi yana kallonta tana yimasa dariya har ya canyesa tas batare daya ankara ba sannan yamaida plate d’in kitchen yadawo inda take yace. “Gimbiya bari naje na watso ruwa mutafi kafin gwaggo tafito tasameni.” “Shikenan ka kula mani da kanka.” Bayan ya gyara cikin wata farar shaddarsa giznah da tamatuqar yimasa kyau yanufo falon bakinsa d’auke da sallama, tsabar kyawon da yayi batool batasan lokacin da ta sakar masa murmushi tare da cewa, “kamatuqar yin kyau Abu sumayya.” “Nagode oum sumayya.” Yafad’a shima yana mayar mata da murmushi, kusan atare Rashida da Fatima suka fito daga cikin d’akunansu Fatima nariqe da makullin motar dasu little zasu tafi da ita tace. “Har anfito little?.” “Eh mama.” “Ungo to ga makullin motar ubangiji ALLAH ya tsare hanya, don ALLAH akula da titi da kyau kaji?” tamiqa masa tana kallon batool da har lokacin kezaune kanta na aqasa, jitake kamar ta fusa ihu domin gaba d’aya bata buqatar komawa gida saboda abunda zata tarar. STORY CONTINUES BELOW  Murmushi tayi had’e da cewa. “Takwarata tashi kuje lokaci na tafiya kuma don ALLAH kihi haquri kibarwa ALLAH dukkanin lamurransa, kada kikoma yunqurin yin jayayya da mahaifanki domin hakan kuskurene kinji ko.?” “In Sha ALLAH.” Batool tafad’a muryarta na kakkarwa alamun tana so tayi kuka. Dafata Rashida tayi had’e da cewa. “Ashsha batool, kukan zaki komawa bayan nafad’a maki cewa kuyi hak’uri, bawa baya iya tab’a canza qaddararsa aduk inda yake don haka kuka bayada wani amfani ga abunda zartar maka dashi za’ayi bakai zaka zartar dashi ba, ungo wannan littafin hisnul Muslim ne, kintab’a amfani dashi.?” “Eh dashi mamana tayi koyamun addu’o’in safiya da marece.,” “Masha ALLAH, kiduba cikinsa akwai babin addu’o’in hammu wal hazan, kije ki laqancesu in Sha ALLAH zaki samu sassaucin quncin zuciya dana baqinciki da damuwa kinji ko.” Hannu biyu tasa takarb’a hawaye na zubo mata, Rashida tace. “Au bazaki dena kukanba.” Cikin sake d’aga sautin kukanta tace “Ina matuqar jin tsorone gwaggo.” Shiru Rashida tayi kafin tace “shikenan, share hawayen naki kibani lambar shi mahaifin naki.” Fad’a mata tayi ta copy digit d’in awayarta sannan tace, “Maza jiki yana jiranku, Allah yayi maki albarka kuma ya kaiku lafiya.” Amin batool tafad’a sannan tafice tana sharar qwalla, wani gauron nisha Fatima tayi had’e da cewa Rashida. “Yarinyar nan tabani tausayi, wlh tana matuqar son little sosai, ALLAH yakawo mata d’auki don girman qur’ani, “Amin.” Rashida tafad’a sannan sukabi bayanta, Saida sukaga tashinsu sannan suka dawo cikin gida bayan Rashida ta tabbatarwa da little cewa yakula da batool sosai kuma yaje ahankali. Kusan awanni biyar suka shafe akan hanya kafin su iso gida, tafiya ce sukayi mai cike da nishad’i da kuma jin dad’i wacce gaba d’aya ta mantar dasu halin da suke ciki saboda yanda suka d’ebawa juna kewa sosai, atarihin rayuwarsu wannan rana itace da bazasu tab’a mantawa da itaba soboda lokacin da suka samu wajen qara bayyanawa juna sirrin dake zuciyarsu. Rashida kuwa saida ta kwatanta sun kusa isa sannan takira mahaifin batool, lokacin yana kwance gaba d’aya duniya tayi masa zafi saboda neman batool da aka shigayi tun safe ba’a ganta ba, Wanda hakan yasa ‘yan uwansa suka fito masa da b’acin ransu qarara akan cewa duk abunda yasamu batool laifinsa ne kuma ALLAH zai kamashi dashi, a matsayinsa na mahaifi bashi kad’ai ALLAH yad’orawa haqqin ‘ya’yansa ba, hatta qannensa, yannensa da mahaifiyarta da qannen mahaifiyarta da qannenta duk sunada haqqi akanta don haka sun gaji da zuba masa idanuwa yana neman cilla ‘yarsu cikin halaka, ada sunyi tunanin barmasa ‘yarsa kamar yanda yake iqirarin cewa ‘yarsa ce, Amma ayanzu zasu had’a qarfi da qarfe suyi mata abunda take so, zasu bata zab’in ranta matuqar shine kwanciyar hankalinta koda hakan na nufin zai yakicesu daga jikinsa, sun shirya tsaf wajen nuna masa cewa suma ‘yarsu ce kuma zasu bata gatar daya kasa bata ayanzu, Maganganu masu zafi suka yab’a masa kafin su sake tabbatar masa da cewa zasu je su nemo ‘yarsu da kansu amma ya tabbata yazare hannunsa acikin lamurranta don su suna buqatarta idan shi baya buqatarta, baban abunda yafi b’ata masa rai shine a gabansa suka kira wanda yayiwa alqawarin aurawa ita suka sheda masa cewa yayi haquri yazo yakarb’i kayansa, dayayi yunqurin magantawa gaba d’aya suka had’a masa baki wajen cewa matuqar yasake dakatar dasu akaro nabiyu acikin sha’anin ‘yarsa to bazasu sake amsa sunan cewa su qannensa bane, Kuma zasu barmasa gidan suda iyalinsu in yaso yayi yanda yake so, sannan suka fice suka barsa cike da damuwar matakin da ‘yan uwan nasa suka d’auka, STORY CONTINUES BELOW  Jin da yayi wayarsa naqara yasashi tashi zaune had’e da miqa hannu ya d’auko wayar dake kan kujera, ganin sabuwar lambar da yayi yasa ya maida wayar ya ajiye tare da komawarsa ya kwanta fuskarsa na kallon sama, Sake kira Rashida tayi akaro na biyu amma har ta tsinke bai d’aga ba sai akaro na uku taji ya d’aga. Sallama tayi masa a mutunce cikin girmamawa ya amsa sannan tace. “Sunana barrister Rashida bashar maitakalma, ni haifaffiyar cikin garin kano ce awani qauye da ake kira yarimawa amma yanzu ina zaunene agarin borno ni da mahaifiyata da kuma mahifina da ALLAH yayiwa rasuwa duk anan borno d’in. Wata zabura Abba yayi daga kwancen da yake had’e da miqewa tsaye yana bin wayar da wani irin kallon tsana kai kace ita d’ince Rashida, jin da yayi taci gaba da magana had’e da cewa “ni…” Yasa yayi saurin dakatar da ita cikin b’acin rai tahanyar cewa. “Kece uwar wannan yaron da bayada uba, yaron da bayada asali, yaron da duniya tasan rauninsa da rashin nagartarsa, yaron da ba’ada tabbaci akan koshi waye?, Yaron daya nacewa ‘yata yake neman lalatata izuwa tahanyar da aka samosa, meye dalilin kirana?, meyasa bazaki jawa yaronki kunnuwaba daya nisanta kansa da ‘yatah?, meyasa bazaki lusar dashi cewa wutsiyar raqomi tayiwa qasa nisa?, meyasa amatsayinki na uwa bazaki zaunar dashi kinuna masa banbancin aya da tsakuwa ba?, oh! Wato kinaso yaronki ya zama kiyashi ja abunda yafi qarfinsa saboda son zuciya da sakarci irin naki, me kike so akiraki uwa ko kuma uwar kawai tunda kin kasa banbancewa d’anki tsakanin fari da baqi?, To bari nafad’a maki yayi kuskuren neman aure a inda bai dace da shiba kuma da sannu zan nusar dashi wannan kuskuren da yayi tunda ke kin kasa.” Tunda yafara magana Rashida batace dashi komai ba har saida ya dasa aya sannan tashare qwallan da suka zo mata, aduk lokacin da aka aibanta mata yaro sai taji wani qululu yataso azuciyarta ya tokare mata wuya, zafi da zugin da zuciyarta keyimata kuwa suke saka hawaye saurin kwaranya daga idanuwanta, murmushin qarfin hali tayi wanda saida ta tabbatar yaji sautinsa akunne sannan tace. “Alhamdulillah daka fad’amun kowane irin mahifine kai batare dana b’ata lokacina wajen fahimtar dakai abunda nake da tabbaci ayanzu cewa bazaka tab’a fahimtarsa ba, sanin kima da darajar mutuntaka yasa nayi yunqurin kiranka don tunatar dakai girman qudura ta ubangiji akan abunda shi yake da iko akansa, amma yanzu nafahimci baka buqatar hakan!, Naji yarona bayada uban kmar yanda kace ko, bayada asali shima, yarona bayada nagarta da kima a idanun duniya musamman ga irinku to duka naji kuma nayarda da hakan, Amma Ina so kasani ayanzu yarona, shine rayuwar ‘yarka!, shine kimar gidanka!, shine abun so ga dukkanin nakusa gareka!, yarona shine zab’in fatincikinka da kafi so aranka! Kuma shine wanda take alfahari dashi data jingina wanzuwar rayuwarta bisa samunsa!, Bana buqatar sanin abunda ke faruwa acikin gidanka domin ‘yar taka da kake cewa yarona na bibiya tana tare damu, zuciyarta takasa amince mata ta zauna atare dakai saboda gazawarka wajen sama mata farinciki, hakan yasa tazo garemu cike da so da qauna kuma mun karb’eta hannu biyu dommu nuna mata yanda rashin uba ke iya samar da gata fiye da masu uba.” “Ka kwantar da hankalinka babu abunda zai sami ‘yarka don nafahimci karazana da jin hakan, izuwa yanzu ‘yarka na gab da isowa wajenka domin nasa yarona ya maido maka da ita, koba komai wannan inganci nasa da nagartarsa da duniya takasa ganewa kai ka ganota, sannan kasa aranka kausasan kalamanka basu isa susa infad’a maka waye ubansa idan har baka sani ba ko in rabasa da ‘yarka domin nasan ko banyi hakan ba ina da tabbacin soyayyar da ‘yarka keyi masa kawai ta isa tasa d’ana yayi nasara akanka wajen aure ‘yarka, yawwa! Sannan naji kamar kace zaka nusar dashi kuskurensa ko? To Ina jiran hakan domin idan ka kuskura kayiwa d’ana wani abun ko kuma yadawo naga qwarzane ajikinsa to tabbas zan manta da cewa ni uwace in d’auko tsofaffin kayan da suka dad’e ajiye nasa don bimasa haqqinsa, Kuma Ina tabbata maka cewa idan nafara shari’a dakai bazan bari ba har sai na tabbatar da nima na nuna maka kuskurenka natab’a mun d’a da kayi, saboda haka kada kafasa ga fili ga mai doki, ni na barka lafiya.” STORY CONTINUES BELOW  Takashe wayarta tun kafin yayi qoqarin cewa wani abun zuciyarta fal cike da farincikin ta mayar masa da baqaqen maganganun daya yimata daidai shi. Wani irin qugi Abba yayi tare da ture dispenser d’in dake gefensa a kan fridge yana mai jin d’acin kowace kalma d’aya da Rashida ta mayar masa, wanda ya ta’allaqa hakan da walaqanci da kuma cin zarafi da ‘yarsa ta cikinsa tajawo masa takowane b’angare. Qarar motar daya jiyo daga wajen gate ya sashi saurin fita tsakar harabar gidan yana huci ya d’auka su d’inne suka iso kamar yanda Rashida tafad’a, sai gashi ashe su uncle h ne suka dawo daga wajen nemanta agajiye rayukkansu duk ba dad’i saboda babu wani labari da suka samo akanta, har hajia nafeesa sun kirawo acan borno suji ko batool d’in taje can amma saboda batada wata masaniya akan zuwan nata yasa tace masu bata ganeta ba. Har ya juya zai komawa ciki ya hango mota na kunno kai cikin gidan da sauri yadawo yanufi wajen motar tamkar wani zararre, hannu batool ta shiga yarfawa hawaye nazubo mata a fuska hango mahaifin nata da tayi ya tunkaro wajen motar tasu, sudai su Uncle h zura idanuwa sukayi suna jiran fitowar wanda ke cikin motar, qafar macce da suka gani tafara azowa lokacin da suka bud’e gambunan motar yasasu saurin qarasowa wajen motar suma, batool na ganinsu da sauri taqarasa fitowa jikinta narawa tanufi inda suke tana fad’in. “Nashiga uku, uncle don ALLAH kuyi haquri ku yafemun kada kubari Abbana ya dukeni, wlh Abba natuba bazan qara guduwa ba..bayansu ta b’uya tana kallon idanuwa abban nata da sukankad’a sukayi jawur kamar an watsa masa barkono, cikin fushi yanufi wajen da little yake tsaye yariqe gambun mota shi bai qarasa fitowa ba shi baikoma ciki ba yana kallonsu uncle h da suka juya suna kallonta cike da mamaki. Wata irin cakuma Abba yayiwa little had’e da shaqo wuyan rigarsa ya had’asa da jikin motar tasa yana fad’in. “Kai d’an gidan uban waye da zaka d’aukemun ‘yah?, ubanme kaje kayimata ana saura kwanaki a d’aura mata aure?, Kafad’amun uban me kaje ka aikata mata?” Yanda yake kakari yasa batool rugowa tariqe masa qafa tana fadin. “Abba ka qyalesa, don ALLAH aba karabu dashi, ba abunda yayi mani asalima ninaje na iskosa har gidansu, Abba naroqeka kabarshi kada kacutar dashi don ALLAH.” Ko kad’an little baiyi yunqurin kwatar kansa ahannun abba ba saboda kada yace yayi kokuwa dashi duk kuwa da azabar da yakeji Kuma bawai bayada qarfin bane kawai ya shiraya rayuwa ko mutuwane akan masoyiyarsa. Yanda batool takoma qoqarin cire hannunsa ga wuyan little tana kuka yasa Abba sakinsa tare da riqo hannunta ya d’auketa wani irin zazzafan marin da saida takife wajen asume, da gudu little yayi kanta yana kiran sunanta had’e da cewa. “Kada ki karaya batool, wannan shine qalubalen da soyayyarmu tazo mana da ita, don ALLAH kitashi kada kibari wani abun ya sameki, bazan juri hakan ba, batool batool tun yana qeqqegar tab’ata har yasoma aza hannunsa akafad’arta yana jijjigata, a fusace Abba yasake yowa takansa ya shuresa gefe amma hakan bai hana little tasowa ba yana kuka yana kiran sunanta, qafa Abba ya d’aga zai sake shuresa uncle Hussain yazo ya jayesa yana fad’in. “Ta b’angaren sa ya isa haka domin idan ma laifi yayi na d’aukarta kacire wannan rad’ad’in azuciyarka, ayanzu bakada hurumin sake tab’asa sai dai ko ‘yar taka gatanan agabanka zaka iya qarasata idan kana buqata,” Yana gama fad’ar haka ya juyawarsa riqe da hannun little ya shige part d’insa dashi, shi kuma sai waiwayen batool daya hango uncle Hassan na yayyafa mata ruwa yakeyi yana sharar hawaye, Tana farfad’owa tafara waige waige tare da nufar art d’insu tana kuka ahankali tana kiran sunansa, Karki kuskura qafafuwanki sutaka mani cikin gida domin ya haramta daga gareki, yanda kika fita kika barsa Ina so ki kama qafafuwanki kifice daga cikin gidannan kafin nacireki daga cikin ‘ya’yana, tunda har kikasa aka ci mutuncina kika zubarmun da kima a idanuwan duniya kikasa ‘yan uwana suka juyamani baya to nima daga yau babuni babu ke, kije can kinemi wasu iyayen da suka fimu Amma mu bama buqatarki, STORY CONTINUES BELOW  “Madalla daka fad’i hakan, idan har kai baka buqatarta to mu muna buqatarta, gida kuwa tanada ikon ta zauna tunda tana damu, batool share hawayenki in Sha ALLAH daga yau sun dena zubowa, idan har shi yayi maki gata kina qaramarki to mu zamuyi maki ita ayanzu da kike da girmanki tahanyar aura maki wanda kike so” Uncle Hassan yafad’i hakan tare da riqo hannun batool yawuce part d’in uncle Hussain da ita shi kuma Abba yawuce fuuuuu..zuwa nasa part d’in…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___85💎 Duk iya qoqarin su uncle h wajen ganin sun fahimtar dashi hakan ya cutara don gaba d’aya ida birkice masu ma yayi tamkar wata birkitacciyar kaca, shiru duk sukayi suna sauraren yanda take masifa yana qarawa har yayi mai isarsa yagama sannan suka miqe rayukkansu a ‘bace sukabar wajen. ••• ••• ••• Dady kuwa tunda suka koma shima ya canzawa hajia nafeesa, gaba d’aya baya shiga al-amurranta saboda yanda ransa yab’aci, ya tabbatar babu wanda ya shiryawa mahaifin batool wannan qullalliyar ta cewa little bayada uba sai ita wanda hakan baiyi masa dad’i ba ko kad’an, shiyasa ya d’auki fushi da ita don ya nuna mata kuskurenta, amaimakon ta fahimta sai itama ta sharesa tafita batunsa kamar yanda yake yimata, Saida taji tagaji don kanta sannan yau daya shigo part d’inta da daddare don ya duba yaransa saboda a part d’in ammie yake ta tsaresa akan lallai sai yafad’a mata dalilin da yasa yake fushi da ita har na tsawon sati biyu. Waje yanema ya zauna fuskarsa a d’aure babu alamun walwala atattare da ita sannan yace “Meye dalilinki na shegantawa Rashida d’ah da kuma shiga rayuwarsu?, meye yadameki da zuwam mu nemawa yaronsu auren da kikaje kika fad’i maganganun da zasu iya lalata komai?” Wani irin sheqeqe ta d’ago takallesa had’e da cewa. “Au dama akan wannan kake fushi dani?, Tirqashi! Ai wallahi da nasan akan wannanne dalilinka da ko kallonka bazanyi ba balle har indamu da fushin da kakeyi, Kuma da kake zancen shiga rayuwa dani dasu waya shiga rayuwar wani?, meye alaqarsu dakai da har zaka tambayeni zance sheganta yaronsu, yo ina uban nasa yakene da har don na shegantasa zakaga laifina?, Ina ganinsu kawai mukyi dashi tsakar rana shida da uwarsa da suka gudo ita da kakannisa batare da munga ubansa ba?, To don me an tambayeni bazan fad’i gaskiya ba?, Kama ajiye duk wannan agefe, kai kasan dolene ma nab’ata wannan auren tunda aka munafucceni akan za’a nemowa d’ana yarinyar sai akaje aka nemawa wanda ba’asan asalin saba saboda bid’ar suna, kaga kuwa koba komai yanda natsani kakarsa wlh in akwai abunda yafi lalata aure zan iyayi masu don bazan bari muhad’a jini dasu ba balle ace sunyi nasara akaina?.” “Haka kikace!?” “Eh haka nace, nafad’a kuma naqara fad’a, indai ina raye wlh bazan bari wannan yaron ya auri ‘yar uwata ba!.” “To shikenan, bari naqyaleki tukuna kafin hukuncin da zanyi maki akan wud’annan maganganun da kikayi tsaye kina fad’amun da abunda kika aikata yabiyo baya mugani idan zaki iya dakatar da abunda ALLAH ya tsaro, mugani idan kinada girman shaqiyancin da zaki iya ja da ikon ALLAH, ni dai natabbata wud’annan bayin ALLAH da kike gani ALLAH ne garkuwarsu kuma babu wani abu da zai samesu face yazamo alkhairi agunsu, sunyarda da Allah kuma shi suka riqa acikin al-amurransu, don haka nasan shine zai tayasu wannan fad’an da basuma san kinayi ba, kije ki binciki qarshen wacce tafiki fitsara da tanemi yimasu kaidi yanda ALLAH ya mayar mata dashi akanta!” STORY CONTINUES BELOW  Yana gama fad’ar hakan yafice abunsa ya barta da tarin tambayoyin da batada mai amsa mata su. Bayan sati uku da faruwar hakan dady ya kirawo Dr da qanensa faruq sai shakur don sune manyan ‘ya’yansa maza ya kuma aika aka kirawo masa little, bayan duk sun hallara ya d’auko takardun wasu gidaje guda biyu d’aya takardun gidan dake laqe dana faruk ne, d’aya kuma takardun gidansa ne dake can laqe da shagonsa wanda marigayi baba yayi tsare masa kafin yarasu, kallon Dr yayi yace. “Nura kaine babban d’ana, kuma kasani cewa dukkaninku ni nabaku gidajen da zaku zauna lokacin da zakuyi aure, don haka yanzuma Ina so inbawa d’an uwanku shakur nasa saboda sati nasama nakeso da yardar ALLAH muje muyo maganar aurensa asamana rana da kuma sadaki.” Ciro takardun gidan dake kusa dana faruk yayi yamiqa masa had’e da cewa. “A matsayina na mahaifinka nabaka wannan gidan dake kusa dana faruk halak malak kamar yanda nabawa sauran ‘yan uwanka alokacin da zasuyi aure, saboda haka daga yanzu zaka iya zuwa kayi ‘yan gyare gyaren da kake buqata kafin lokaci yayi, Kai koma saidashi kake da ra’ayin yi kasai wanda kake so zaka iyayin hakan nakane babu wanda zai hanaka.” Godiya Shakur yashiga yiwa mahaifin nasa yana wasar baki tare da kallon ‘yan uwansa yace. “Broth’s kutayani yiwa dady godiya ALLAH yaqara bud’i.” Duk suka amsa da Amin har da little dake gefe zaune yana kallonsu, saida suka gama yimawa dady godiya gaba d’ayansu sannan ya ajiye takardun d’ayan gidan dake hannunsa agabansu had’e da cewa. “Wud’annan takardun kuwa na gidan dake laqe da shagon da marigayi bashar kakan little yayi tsare mani ne, ALLAH shine sheda tun ranar da kai Dr inbaka manta ba kazo kasanar damu cewa matarka Fatima tasamu juna biyu yana tsaye araina naqudurta cewa zan bashi wannan gidan ya d’auki iyalinsa sukoma can saboda yiwa ALLAH godiya akan ni’imar da yayi mana takarb’uwar addu’o’inmu da yayi kaima ya nuna maka naka jinin aduniya, sai gashi kuma ALLAH yayi nashi ikon akansa, ganin hakan yasa naquduri cika wannan niyar tawa ga iyalinsa, nan ma ALLAH bainufi hakan tafaru ba dalilin kasantuwarsu aqarqashin inuwarmu, don haka yau Ina son ALLAH da mala’ikunsa da kuma ku ‘ya’yana kuzama sheda ko bana raye na mallaka wannan gidan halak malak ga jikansa don cika wannan alqawarin dana d’aukarwa kakansa cewa zan bashi wannan gidan tun farko,” “Dady mun sheda hakan uabangiji ALLAH ya saka maka da alkhairi ya lullunka maka da gidan aljannah,” Shakur yafad’a yana dariya tare da jujjuya nasa takardun gidan dake hannunsa, duk da dai faruk bai tanka ba da zaran ka kallesa yanayin fuskarsa zai tabbatar maka da cewa baiji dad’in hakan da mahaifinsa yayi ba. Takarda da biro dady yaciro yayi rubutu akai sannan yafara ba Dr yace yasa hannu shida ‘yan uwansa, bayan sun sa ya amshi takardun yamiqawa little dake zaune tamkar andasa shi, banda hawaye babu abunda ke zubo masa saboda ganin irin gatar da dady yayi masa tamkar yanda yayiwa ‘ya’yansa, wannan bawan ALLAH wane irin mutunne shi da kokad’an babu qyashi da hasada acikin al’amurransa, yana karb’a yafashe da kuka hannunsa na kakkarwa, “A’a Dady ban cancanci haka ba daga wajenka, abubuwan da kukayi mana nida mahaifiyata da kakannina kawai sun wadatar don ALLAH kabar takardun gidannan.” “A’a! Little meye haka?, Wannan kyautar tun asali cancantar kakan kace shiyasa tazo hannunka, shi kuma alkhairi danqone idan kayishi watarana zai dawo maka, bamusan me gobe zata haifar ba, abunda muka bayar shine namu wanda Kuma mukayi amfana dashi sharar banzane, rabon bawa kuwa duk inda yake bai wucesa don haka kawai ka amsa kayiwa ALLAH godiya domin shine yabaka ni kawai nazamo silane sai kayi mani addu’ah” Godiya yayita zuba masa tare da sake miqawa Dr takardun ya amsa ya sanya masu albarka tare da miqo masa yana fad’in. “Karb’a amma kafin nan bari nima amatsayina na uba agareka infad’a maka irin abunda dady yafad’awa Shakur d’insa, wannan gida nakane halak malak kaje idan akwai gyare gyaren da zakayi kayi kafin lokaci yayi, idanma bakada ra’ayinsa zaka iya sayar dashi kasai wanda kake buqata babu wanda zaice kayi laifi.” STORY CONTINUES BELOW  Gaba d’aya dady dasu shakur sukasa dariya, sun d’an jima awajen suna tattaunawa akan maganar auren kafin dady yasallami kowanensu yana maijin farincikin sauke wannan nauyin alqawarin daya dad’e dashi acikin zuciya har na tsawon shekaru, faruq baiji dad’i ba ko kad’an amma da yaje wajen ammie yana qunquni ya sanar da ita fad’a tayi masa sosai tare da nuna masa cewa idan mutum ya tallafi bayan wani to shima ALLAH zai tallafi bayansa, alkhairi kuwa danqone baya fad’uwa qasa banza, sucire qyashi da son duniya suyi koyi da mahaifinsu wajen taimakon wanda bayada, musamman shi faruq d’in don ta tabbatar Dr yariga daya gama hawa kyakkyawar turbar mahaifinsa shi kad’aine yamzu kansa ke rawa wani lokacin don haka yatsaya yayiwa kansa fad’a domin duniya ba wajen zama bace, Dole ya sauka daga dokin naqin daya hau ya bata haquri tare da tabbatar mata da cewa zai kiyaye. Rashida kuwa har gida ta isko dady da guntayen hawayenta tayi masa gdy bisa kyautar da yayiwa little, umma kuwa ba’a magana don haka ta tashi cikin dare tayita zuba masa addu’a bayan tayi masa godiya, gawata kulawa ta musamman da riritasa data qarayi tamakar qwai a faranti. ••• ••• ••• Acikin sati ukun da aka kwashe kuwa banda qara cikakken bincike akan bayanin dasu baffa suka basu uncle h babu abunda sukayi saboda maganar da yayan nasu yazo da ita cewa wai hayar mutanen da sukazo amatsayin iyayen little akayi, sunyi hakanne don qara tabbatar da zancensu baffa akan hukuncin da suka gama yanke shawarar d’auka akan yayan nasu, kafin sukai ga zartar da hakan kwatsam saiga wani Abba yakawowa batul akan shi zata aura nan da sati biyu kuma ba gudu ba ja da baya, wayyo ranar batul qaramin hauka kawaine batayi ba, tayiwa mahaifinta kuka tayi masa magiya kamar ranta zai fita amma yaqi saurararta, kwana d’aya da zancen aka kawo lefe set d’in akwati uku, duk inda ran su uncle h yake ya b’aci don gaba d’aya bai bid’esu ba shi kad’ai ke sha’aninsa. Haka batul ta dinga kuka tare da isko su uncle h tana riqon qafafuwansu akan kada subari abbanta ya aura mata wanda bata so amma saboda b’acin rai akan abunda yayi masu suka kauda kai akanta, ganin yanda sukayi biris da ita yasa ta iske iyayenta mata tana roqonsu akan su dakatar da mahaifinta kada yayi mata auren dole nan ma suma suka qyaleta, matar uncle Hassan ce da bazata iya jurewa kukan nataba tana hawaye tariqo hannuntata nufi d’akin Abba da ita, yana zaune falo tayi sallama suka shiga lokacin yana waya har dasu qyaqyatawa da alama yanajin dad’in firar wanda suke waya dashi, yana gamawa ya d’ago kai yana kallon matar uncle hassan d’in da hawaye ke kwance a fuskarta yace. “Lafiya hajia Naga kamar hawaye afuskarki? Meyake faruwa?” Nuna batool data durqusar masa agabansa tayi had’e da cewa. “Bakaga wud’annan hawayen na wannan yarinyar ba data kwashe kwanaki tana zubarwa akan abunda kanada ikon tsayar mata dasu tahanyar dakatar da qudurinka sai nawa?, Haba Yaya wannan wace irin zuciyace da kai da bata tausayawa abunda ta dad’e tana iqirarin tana so?, Naroqeka kayiwa ALLAH da girmansa ka amincewa yarinyar nan ta auri wanda take so don ALLAH yaya?” “Shegen?, Marar asali.” “Kodai waye shi kabarta ta aura, ai ita zata zauna dashi bamu ba, sannan idan ma shegenne to meye laifinsa?, Iyayensa sune masu laifi kuma sune shegun bashi ba, katausaya mata kabata zab’inta.”Saida ya hard’e qafarsa d’aya akan d’aya sannan yace. “Ni kuma nawa zab’in fa?.” “Ka haqura dashi mana, haba yaya don ALLAH kada karusa mata rayuwa.” Cikin b’acin rai yamiqe tare da katsawa matar uncle h tsawa yace. “Ke wace da zakice nahaqura da zab’ina da nake ganin shine daidai akan ‘yata, tuntuni ban rusa mata rayuwa ba sai yanzu da take ganin duk gatar da nayi mata bata yimata ba saboda tana butulu.?” Cikin kuka batool ta had’a hannyenta had’e da cewa. “Abba ba butulci bane nayi maka, abunda zuciyata kawai keso nake qoqarin fad’a maka kamar yanda abaya kafad’a mun cewa in sanar dakai dik wani abu aduniya da naji zuciyata naso zaka nemomin, Abba kayi mani duk wata gata aduniya da nake tunanin babu wani mahaifi da zai iya yiwa ‘yarsa ita kuma ban rena hakan ba, ayau Ina sake roqonka a karo na ba adadi daka cikashe mani wannan gatar da kakeyimun tahanyar bani zab’ina, wlh Abba nagartaccen zab’i nayi maka, Nuraddeen d’an halak ne ba shege ba, yanada asali yanada tarbiya da duk wata nagartar mutuntaka, don ALLAH kada kahanani samunsa Abba domin bayan kai shi kad’aine ke iya bani irin kulawar daka bani, Ina sonsa Abba Ina son sa fiye da tunani, hanani shi zai iya dakatar da bugun zuciyata da kuma lumfashi na, Abba kaji tausayina ka aura mani shi ina matuqar qaunarsa sosai.” STORY CONTINUES BELOW  Taqarasa maganar tana kuka tare da d’ora kanta asaman qafafuwansa daga tsayen da yake, hanb’areta gefe yayi har saida kanta yabugi qarfen center table d’in dake tsakiyar falon yafashe da sauri matar uncle hassan tajuyar da kanta gefe had’e da runtse idanuwa tana fad’in. “Shikenan, zaka iya kasheta ai ‘yar kace kai kake da hasarar hakan,” sannan tabar d’akin itama tana sharar qwalla. Karo tayi da hajia mama ta d’auko abinci a try bakin qofar d’akin taja burki tana share hawayenta tace. “Yanzu bazaki iya dakatar dashi daga qoqarin illata maki ‘ya da yake shirin yiba?, kinfiso kirasata tahanyar biyewa zab’in da mahaifinta yayi mata.” Cikin dauriya don ita kad’ai tasan irin damuwar dake cunkushe acikin azuciyarta hajia mama tace. “Ai ita tajawa kanta, mezanyi mata bayan addu’a, mahaifintane yanada iko akanta, ni kuma matarsa ce dole inbi duk wani umurni nasa, don haka ALLAH yayi mata magani kuma yarabata da wahala, gadone tariga tayisa, yanda baza’a iya saukar dashi ya sauka ba haka itama baza’a saukar da ita ba ta sauka,” Tana gama fad’ar haka tawuce ciki daidai lokacin yana fad’in. “Koda zaki mutu kina dawowa batool ni bazan tab’a d’aukarki naba wanda bayada asali ba, yarage naki kihaqura da zab’inki kibi nawa saiki zauna lafiya, idan Kuma kikace a’a to tabbas hawayenki zasu qare aduniya ba tare da ni nabi naki zab’in ba, shashashar banza da wofi.” Ko kallon gefen da suke hajia mama batayi ba taje ta jere abincin akan dining table tana qoqarin maida qwallanda suka zo mata, Har zata fita dady yace. “Zo kifice Mani da ita ad’aki kafin na kakkarya ta.” Dawowa tayi tasa hannu tariqo batool zata miqar da ita batool tariqe qafar Abba d’aya tana fad’in. “Wayyo Abbana, nice batool d’inka, katuna lokacin da kake sakani dariya idan zaka kaini makaranta Ina kuka kana fad’amun cewa inyi shiru kukan da nakeyi na tab’a maka zuciya!, katuna lokacin da idan aka sakani kuka anan gidan kake cewa da ab’ata mani rai kafison a b’ata maka naka!, Abba ka tuna cewa tun ina qarama kasaba mani da nema mani duk abunda nake so kuma ka riqemun shi yanda bazani tab’a kukan rasa shiba, Abba don ALLAH kada yau da kanka ka nosantani da abundanake so, kada ka bari narasa Nuraddeen domin daidai yake da rasa rayuwata.” Hannunsa yasa yacire hannunta daga riqon da tayi masa ya juya mata baya, haka hajia mama tayita jan hannunta tana kuka tana kiran Abbaaa. Duk da yanajin damuwa aransa na kukanta amma yafiso yayita saurarensa akan dawwama da zuciyarsa zatayi cikin damuwar aura mata wanda take so da yake yiwa kallon shege da bayada uba. Ganin abbanta naci gaba da shire shiren auren nata gashi fushin zuciya yasa su uncle h fita batunta yasa batare da sanin kowa ba ta tsere tabar garin tanufi borno, kai tsaye gidan Dr ta sauka wajen Rashida mahaifiyar little don dama tasan gidan, suna zaune ita da Fatima tashiga bakomai ahannunta tana daga ita sai kanta tana kuka, sun matuqar firgita ayanayin da suka ganta don tarame tayi baqi tamkar wacce batada galihu aduniya. Tana zuwa ta zube agabansu tana fad’in. “Gwaggo don ALLAH da girmansa kije kiyiwa mahaifina bayani, gwaggo bazan iya rayuwa babada Nuraddeen ba, shi kad’ai nake so kuma zan iya bashi rayuwata, mahaifina, mahaifiyata, baffannina, gaba d’aya sun juya mani baya, sunnkasa karantar zuciyata balle susan irin zafi da qunar da take yimani, kitaimaka kifad’awa abbana kece mahaifiyar little, kafad’a masa mahaifinsa naraye wataqil zai…” Bata qarasa ba sanadiyar fad’uwar da tayi daga durqushen da take tasuma, kallo d’aya zakayi mata kafahimci irin jigatar da tayi. Ruwa Fatima ta d’ebo ta yayyafa mata tare da tada ita zaune, d’ago kai tayi tana kallon Rashida da tayi tagumi da dukkanin hannayenta hawaye na zubar mata saboda tsananin tausayin yarinyar, wato haka ita rayuwa ta gada kowane irin mutum da tasa jarabawar rayuwar, ayau taqara jin zafin mahaifin little a ranta domin duk shine silar faruwar wannan abun ga yaronta da kuma wacce yake so. STORY CONTINUES BELOW  Ganin batool naqoqarin yin magana yasa tagoge hawayenta had’e da dakatar da ita da hannu, cikin sanyin murya tace da ita. “Kina son little?” Da sauri batool tashiga kad’a kai kamar qadangaruwa had’e da cewa. “Eh..” “Zaki iya zama dashi aduk yanayin da take?” “Eh?” “Kingamsu da cewa shid’in d’an halak ne gaba da baya?” “Eh.” “Wane yaqini kike dashi akansa?” “Zai kula dani har qarshen rayuwarsa.” “Wace tabbaci zaki bani akan soyayyar da kike yimasa?.” “Ban saniba, amma nasan Ina sonsa domin ALLAH, kuma Ina qaunarsa har zuwa fitar lumfashina naqarshe!.” Wata ajiyar zuciya rashida tayi had’e da cewa. “Shikenan, share hawayenki, kina sonsa domin ALLAH, shima haka, don haka narantse da wanda lumfashina yake a hannunsa a matsayina na mahaifiyarsa Ina tabbatar maki da cewa matuqar ALLAH nanifin alkhairi acikin aurenku kamar yanda akoda yaushe nake roqa maku to tabbas babu abunda zai hana ku auri junanku, sai dai tabbas bazaku gujewa tsarin qaddarorin da za’a jarabceku dasu aciki ba, girman imaninku da yaqininku ga ALLAH shi zai tseratar daku daga kaidin dukkanin masu kaidi, kisa aranki in Sha ALLAH, ALLAH zai kawowa soyayyarku d’aukin da bazaku tab’a rabuwa ba, ni inajin haka ajikina.” “Yanzu dai ba wannan ba ke gwaggon yara, inashi little d’in? Yakamata akirashi.” Fatima tafad’a tana kallon Rashida. “Kwana uku kenan shima yana d’akinsa baida lafiya sanadiyar kiran da tayi masa ta sanar dashi halin da ake ciki, na hanasa bayyana hakanne saboda kada yatayarwa da dady hankali, kina ganin yanda shekarunsa keja bai kamata acika kai masa duk wani abu da zai jefasa cikin damuwa ba, mubi komai a sannu ALLAH zai kawo mafita” Yanda Rashida ke maganar cikin kwarin guiwa shiya dad’a kwantarwa da batool hankali domin itace last hop d’inta akan soyayyarta shiyasa tayo wajenta atunaninta nacewa ita kad’aice zata iya gamsar da mahaifinta, sai gashi tasamu qwarin guiwa da gamsuwa daga wajenta, murmushi Fatima tayi had’e da cewa. “Anya kina ganin hakan zai yuyu?” “Sosai kuwa, ai SANNU SANNU bata hana zuwa….” “Shikennan! Amma dai taci abinci ta watsa ruwa sai a sanar dasu dady da Dr kokuwa?” “A’a basai anfad’a masu ba, zansa shi da kansa ya d’auketa yamaida ita gidansu.” “Anya Rashida kina ganin hakan yayi?.” “Eh mana, hakan shine daidai.” Bayan tayi wanka taci abinci wanda sharabonta dashi har ta manta Fatima takira little awaya tace yazo tana son ganinsa,ba’afi mintuna biyar ba sai gashi yashigo tamkar a hura sa ya fad’i cikin ‘yan kwanaki uku kacal da yayi acikin damuwa, yana d’ago kansaya hango batool d’insa zaune kusa da fatima tana wasa da ‘yan yatsun hannunta. Da sauri yaqarasa wajen gaba d’aya ya manta ko wacece awajen had’e da cewa “Gimbiya, waya kawoki nan?, ya akayi kika zo nan?, Meya sameki haka gimbiya?.” Kasa maganatayi saboda wani nauyi da takeji, sab’anin d’azu da Bata masan kalaman da take fad’a ba saboda tsananin halin da take ciki, “Kice dani wani abu mana, dama nasan bazaki barni ba, pls gimbiya kiyi…” Bai qarasa maganar ba Rashida dake shigowa lokacin tace. “Rufe mana baki marar kunya, agaban maman taka kake wud’annan suruttan?” STORY CONTINUES BELOW  Sai alokacin ma yatuna tana wajen cikin rashin qwarin jiki yaje ya zauna qasan qafafuwanta yana kallon batool qasa qasa. Murmushi Fatima tayi had’e da cewa. “Dama na kirakane saboda kazo kaganta ku gaisa, idan kun gama gaisawa sai kaje kawatso ruwa ka d’auki motar Dr ka maida ita gida.” ‘Dago kai yayi kamar zaiyi kuka Rashida tace. “What ever the situation is..Dole yau d’innan kaje ka maida ita wajen iyayenta kaji nafad’a maka.” Sannan suka miqe sukabar falon yarage daga shi sai ita….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Gaisuwa tare da fatan alkhairi agareki, haqiqa kulawarku agareni ta musammance da bazan tab’a iya mantawa daku ba, *NANA RUKAYYA GUMMIEY, DOTA HADIZA ZAINU (KUBRA), NAJIDA ALIYU🐒, MUM NUSAIBA, TEEMAH M SANI, HAFSAT HASSAN USMAN, SA’ARBUKAR RABI’U CE, ABLAH SORPEEEY, UMMUL ADNAN, ZAINAB GARBA FARUK, SHAMA HALLIRU, UMMI ABIL BAITY, XEEEE, JAMILA YUSHA’U* Ina godiya bisa qwarin guiwa da kulawar da kuke yimani dama littafina, fatana amincin ALLAH da kuma yardarsa ya lullub’eku kuma yabaku aljannah da rahamarsa👏Fillah Ina matuqar girmama karamcinku agareni, ngd ngd ngd sosai 😍🤝_ Page___87💎 Abba bai zame ko Ina ba sai tsakar falon hajia mama wato mahaifiyar batool, kira yadinga qwala mata tamkar wacce tayi wani laifin, tafito daga kitchen riqe da ludayin miya da alama girkine take qoqarin qarasawa, kallo d’aya zakayi mata ka hango tsantsar damuwar da take qoqarin b’oyewa daga cikin idanuwanta, wanda ko shakka babu kasan hakan yasata zubarda qwalla ba adadi lura da yanda idanuwanta suka kumbura, cikin sanyin murya yace. “Gani alhaji lafiya?” “Bana buqatar jin wannan tambayar daga bakinki, Ina so daga rana mai kama tayau karki sake kisake barin yarinyar nan tashigomin part domin nadad’e da cireta daga cikin ‘ya’yana, don haka dole tanisanta da duk wani abun daya shafeni kuma yazamo mallakina, wannan umurnine nafad’a maki, qoqarin sab’ashi kuma zai iya jawo b’annar rayukka tsakanin ni dake, ban haifi d’iyar da zatazo tana walaqantani agaban idanuwan duniya ba kuma har in zauna da ita, wlh bazai yuyu ba, ta zab’i wani akaina duk irin gatar dana bata saboda kawai cikar nata burin, tayi fatali akan cewa wane irin hali zan iya shiga a matsayinta na ‘ya tilo mafi soyuwa araina don haka taji tayi duk yanda take so nacire hannuna a al_amurranta, nayi qoqarin ganin nabata gata tare da inganta rayuwarta amma takasa fahimtar hakan, amma shikenan taje, in dai duniyace ta isheta riga da wando, in Sha ALLAH da SANNU SANNU…” Bai qarasa ba tayi saurin d’aga masa hannu idanuwanta na hawaye tace “Ya isa haka, ya isa haka nace, bazan ja akan duk wani hukunci da zaka yankewa ‘yarka ba, amma Ina so kasani zanyi maka biyayya iya gwargwadon yina amatsayina na matarka saidai Ina roqonka kadaka aibatamun ‘yata agabana, domin hakan zai iya jawo duk girmamawa da kimarka da nake gani su zube, idan kace zaka koreta agidanka bazan hanaka ba matuqar zata samu cikar burinta, idan kace indena kulata zan dena matuqar farinciki da kuma addu’a ta natare da ita, amma bazan iya yin shiruba matuqar zaka cutar da ita ta lafuzzan bakinka dake iya aibata mani ita nahar abada agabana domin yin hakan kuskurene kuma illoline masu yawa da zaka jawowa yarinyata, don ALLAH da girmansa kayi haquri kayafewa ‘yarka idan zaka iya idam kuma bazaka iyaba Ina roqon ALLAH daya tsare mani ita kuma ya albarkaci rayuwarta yakare mani ita ga shiga dukkanin baqincikin duniya dana lahira, no bana ganin laifin yarinyata kokad’an domin kaine kad’orata akan wannan tarbiyar, don haka fushinka bazaisa na d’au fushi da itaba, saidai zanyi qoqarin dakatar da ita ga dukkanin abubuwan daka fad’a tare da bin umurninka akan wud’anda basu sab’awa ubangijina ba.” STORY CONTINUES BELOW  Tana gama fad’ar hakan tajuya ta shigewarta kitchen taci gaba da aikinta, wayyo Allah yau ina wuta Abba yakad’ata, tana jinsa yana bambaminsa da fad’ace fad’acensa tayi tamkar ma bata jiyosa ba, don izuwa yanzu yafara kaiwa qarshen haqurinta. Su uncle h kuwa gaba sukasa batool da little sukayi masu fad’a sosai akan yanda suka tsanantawa kansu soyyayyar junansu dake nema tajefasu cikin mawuyacin hali har suna lurar dasu cewa idan sun kasa jurewa arabasu lokaci na zuwa da ALLAH zai d’auki ran d’aya yabar na d’aya, shikenan sai d’ayan ya kasa rayuwa saboda an d’auke ran d’ayansu? Yakamata su sassautawa ransu yanayin son da sukeyiwa juna izuwa tubalin rayuwa bisa qaddaruwar kyakkyawar qaddara ko akasinta akansu domin hakan shine zaisa su iya canye duk wata jarabawar da ALLAH zai yimasu, kallon batool uncle Hussain yayi had’e da cewa. “ke kuma ina son kisani cewa kuskurene mai girma bijirewa zab’in iyaye matuqar mai nagartane, haka kaima Nuraddeen taya mai laifi aikata laifinsa shima kuskurene babba domin ALLAH ya haramta sab’awa iyaye.” Gaba d’ayansu banda hawaye babu abunda ke zuba ga idanuwansu saboda jin kalaman dake fitowa daga bakinsa, wani irin tsorone ya ziyarci zukatansu akan rashin sanin ko wane hukuncin zasu zartar masu lura da irin nasihohin da suke yimasu, sun tabbata duk abunda suka fad’a gaskiyane amma taya zukatansu zasu amince sukarb’i wannan gaskiyar dakeda matuqar d’aci azuciyoyinsu, suna wannan tunaninne sukaji uncle Hussain yaci gaba da cewa. “Sai dai kuma shi fiyayyen halitta kuma annabin rahama yayi mana hani da muyiwa ‘ya’yayenmu auren dole sannan yaqara mana da cewa idan wanda muka aminta da addininsa da d’abi’unsa to mu aurar masa dashi, idan mukaqi kuwa hakan zai jawo fitina da fasadi mai girma a doron qasa, bisa wud’annan hujjoji yasa muka zab’i mu aurar daku ga junanku, domin fifita umurnin manzon ALLAH s.a.w akan na yayanmu saboda kaucewa abunda ya tsoratar mana, badon haka ba wlh tallahi kunji na rantse maku koda rayukkanku nafita suna dawowa bazamu tab’a barin ki sab’awa mahifinki ba, bazamu tab’a bari kicutar da zuciyarsa ba saboda ra’ayinki domin muna sonsa fiye da soyayyar da kuke yiwa junanku, saidai son da mukeyiwa manzonmu yasa dole mu ajiye soyayyar da muke yimasa muyiwa ALLAH da mansonsa biyayya.” Kallon little yayi idanuwansa cikin nasa yace. “Shin ko kashirya kanada muhalli mu aurar maka da batool.” Tun kafin yarufe baki little yashiga kad’a masa kai had’e da cewa. “Eh uncle.” “Yaushe?” “Yau…” Little yabashi amsa tamkar anqwato muryar tasa da qarfi tafito, hakan yasa su uncle h sakin murmushin da Basu tashi yiba, ba ko shakka yamatuqar basu dariyar da Saida uncle Hassan yakasa tsaida murmushin nasa yakoma dariya, yana dariyar yace. “Anya malan Nuraddeen kashirya ayau d’innan? Halama so kake mu d’aura maku aure kawai kawuce da matarka?. Murmushi ya shigayi yana sosa qeyar kansa saboda wata kunya da yaji ta lullub’esa, baima san ya akayi ya furta hakan ba sai yanzu da uncle ya tambayesa, murmushin itama tayi kanta na duqe qasa tana kallonsa. Dariya irinta manya uncle Hassan yayi don yana kalle dasu kafin yace. “To kayi haquri, bazamu d’aura maku aure ayanxu ba domin kada ka d’auka cewa ‘yarmu batada gata, batool da kake gani ‘yar gatace gaba da baya fiye da yanda kake tsammani saboda haka yanzu kahuta kaci abinci sai kawuce gida, in Sha ALLAH da kanmu zamu nemi iyayenka tunda ka shirya nan da sati biyu sai a d’aura aure idan ALLAH ya yardar mana.” Wani irin murmushi yasaki, lokaci d’aya suka d’ago kai shida batool suna kallon juna tare da yin hamdala acikin zuciyoyinsu, babu ko shakka ayanzu sunada yaqinin cewa sunfara tako matakin nasara nafarko wajen cika burinsu, murmushin itama tayi sannan tamaida kanta qasa, haka su uncle suka cigaba da fira dasu wacce rabinta kusan duk nasihohine masu ratsa zuciya akan auratayya suka yimasu, kafin uncle Hussain yace batool tashiga cikin gida takawo ma little abinci da ruwa, sosai shikam little yasaki jikinsa dasu uncle h sukasha firarsu har tadawo d’auke da tray abinci wanda tanan suka sake fahimtar wani Abu akansa tare da yabawa nagartarsa da Kuma tarbiyarsa. STORY CONTINUES BELOW  Tana shigowa su uncle h suka fita sukabar falon yarage daga ita sai shi, Saida tafara zuba masa ruwa a cup yasha sannan tazuba masa abincin a plate ta tura masa agabansa tare da komawa gefe tayi zaune tana kallonsa, tankwashe qafafuwansa yayi tamkar mai shirin d’aukar karatu tare da matsowa da abincin kusa dashi yafaraci, Saida yayi kusan cokali uku tukuna ya d’ago kansa had’e da kallonta yace. “Gimbiya ke bazakici abincin bane?” Girgiza masa kai tayi tana kallonsa alamun taqoshi sai shima yature plate d’in dake gabansa had’e da cewa. “Shikenan Nima naqoshi.” Yafad’a had’e da qoqarin miqewa daga inda yake, da sauri tasauko daga kan kujera tana fad’in “A’a’ah…don ALLAH kazauna zanci Nima.” “Kin tabbata?” “ALLAH zanci, kaidai kawai ka zauna kaci naka.” Ta sake turo masa plate d’in abincin agabansa,” Qinci yayi har saida yaga tazuba nata a plate ta soma ci sannan yayi murmushi had’e da d’aukar cokali yaci gaba dacin nasa, Bai bar gidan ba sai bayan sallar magrib sannan yayi masu sallama yanufi gidan baba balarabe don bazai iya komawa borno ba alokacin. Su uncle h kuwa tuni suka kira dady suka sanar dashi zance auren wanda suka ajiye nan da sati biyu, yayi matuqar farinciki dajin dad’i kafin yace yana son subashi dama ya tuntub’i su baba balarabe da baffa idan sun amince da lokacin harma da mahaifiyar yaron kuma sun amince masa da hakan inda sukace yabari da kansu zasu kira baffa su sanar dashi, hakan da sukayi yasashi qarajin dad’i ganin sun martaba wanda shine matsayin mahaifin yaron ayanzu don haka shi sai yakira baba balarabe da Rashida ya sanar dasu komai, ita dai Rashida tasan abunda yafaru tsakaninta da mahaifin batool don haka zuciyarta tashiga kokwanto cewa daqyar idan har da amincewarsa za’ayi wannan auren azahiri kuwa amsawa dady tayi da ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi, baba balarabe ma yayi farinciki sosai had’e da addu’ar ALLAH yasanya alkhairi, baffa kuwa amaimakon farinciki damuwace ta sake bijiro masa na ganin jikan nasa zaiyi aure ammababu mahaifinsa alhalin yana raye bai mutu ba. Washe gari dady yasa Dr yagyara don yana fama da zazzab’i shi bazai iya tafiya ya bashi dubu d’ari yace yaje can kano yasami su baba balarabe da baffa ayanka masu sadaki su biya kafin lokaci yayi, Bayan Dr yaje ya dawo yamiqawa dady kud’insa had’e da cewa. “Dady gashi su baffa sunce ayi maka godiya sosai sunayi maka ya jiki da addu’ar ALLAH yabaka lafiya, sunce agaisheki sosai.” “Madalla duk dai kasamesu lafiya ko?” “Alhamdulillah, kowa lafiya,” “To ya akayi ka dawomun da kud’in?” “Eh to, lokacin da aka yanka mana sadaki dubu saba’in ina qoqarin ciro kud’in sai shi kakan little wato baffa yaciro kud’in ya bayar, kaga kuma bazai yuyu nagardan tamasa anan ba saboda yanada haqqi akan jikansa fiye damu,.” “Eh to balaifi hakan ma yayi, haka ake son mutum yakasance mai tsayawa da kuma jajircewa ga dukkanin al-amurran ahalinsa, ubangiji ALLAH yafaranta zuciyar wannan bawan ALLAH bisa nuna godiyarsa agaresa ya maido masa da d’ansa agaresa ko zai samu farinciki.” “Amin dady, wlh dattijon nan kam mutumne, yanada matuqar qana’a da kuma zuciyar yi duk kuwa da qaramcin yalwatuwar da take da ita.” “Sosai kuwa, kaga sanin little jininsa ne kuma babu wanda yake Dole agaresa kamar shi yasa bai tsaya jiran kowa ba yayi abunda yakamata, kaga yanzu sai kaje da wud’annan kud’in kakira little idan akwai wani Abu ahannunsa ka karb’a abawa ita Fatima taje tahad’o masa lefe da sauran abubuwan daya kamata, sannan Ina son gobe kuje kaida d’an uwanka da alhaji sabiu, aminina ayankawa d’an uwanku shakur sadaki shima, idan son samune ma kuroqa amadadina akan abarshi shima nan da sati biyu saboda Ina son ayishi lokaci d’aya dana little, zan kira shi alhaji sabiun in fad’a masa inyaso sai kuje ku samesa can gidansa kutafi, shima shakur d’in ka lalubesa kaji idan akwai wani abun ahannunsa sai akarb’a ahad’o masu lefen atare don bazai yuyuba ace komai yimasu za’ayi kar akashe masu zuciya.” STORY CONTINUES BELOW  “To dady, Nima zanbasu dubu d’ari shida, faruk kuma yabasu hud’u sai ahad’a da abunda aka samu ahannunsu aje ahad’o lefen.” “Masha ALLAH Dr, ALLAH yayi maka albarka, haka ake son babba akoda yaushe ya zamana dashi naqasanshi zasuyi koyi, ALLAH yaqara had’a mani kawunanku baki d’aya yakareku daga sharrin maqiya.” “Amin dady, bari intafi” Dr yafad’a had’e da miqewa yana maijin dad’in addu’o’in daya yimasa, Bayan kwana biyu kamar yanda dady yace yayi haka yayi har sun biya sadakin da aka yankawa Shakur dubu hamsin sannan ya kuma had’a kud’ad’en wajensa dana faruq, little ma dubu d’ari biyu ya bayar da taimakon mahaifiyarsa Rashida sai Shakur shima yabada dubu d’ari uku don har soma yayi abarshi ya had’a lefensa da kansa Dr yace a’a yayi haquri anriga angama magana Fatima zataje Legos tahad’o duk abunda yakamata, yabari idan tadawo yaga abunda baiyi masa ba sai yaqara da wanda yake so, da yake akwai fahimta da girmamawa tsakaninsu sai ya hanqura, Fatima na shire shiren tafiya Legos had’o kayan lefen Rashida tafiddo da sababbin akwatuna set uku tace ga nata gudum mawa nan, basai ansayi akwatunan ba kowane qwaya hud’u da jikkunan sama guda biyu, akwatunan sunyi kyau sosai har sun gaji, kowane na ukun set aciki tacikosu da kayan kwalliya da shafe shafe masu matuqar kyau da tsada, abu ga masu abun dama sana’ar da takeyi kenan. Ko kad’an su dr da Fatima basuyi mamaki ba tunda dama tanada abunyinta don haka sukayi mata godiya sosai kai kace ba d’ansu ne tayiwa hidimar duk da dai akwai qanensu aciki amma ai yiwa kaine, su ammi da dady da umma ma sun kirata ga waya suka yimata godiya sosai tare da saka mata albarka, ita kuma hajia nafeesa gaba d’aya kusan zaucewa tayi jin abunda kefaruwa, tayi bala’in tayi maseefar har tagaji akan an munafucceta anhad’a d’anta da wacce bata dace dashi ba gaba d’aya amma babu wanda ya tankata dole tahaqura itama tafara shire shiren hidimar biki tana mai ayyana abubuwan da zasu faru da sai anyi dana sanin aurawa d’anta ‘yar gidan matsiyata da akayi… _INA GODIYA WUDANDA SUKA KIRANI DA WUDANDA SUKA YIMANI FATAN ALKHAIRI TA MESSAGE DA KUMA CHART BISA QARUWAR DA ALLAH YABAMU, MASU JEGO DA BABYS SUNA GODIYA DA ADDU’OINKU NA ALKHAIRI AGAREKU ALLAH YABAR TARE, BABU KALMAR DA ZATA IYA ISAR DA BAN HAQURINA AGAREKU, AMMA INA SO KUSANI NA SAKAKU A QUNDIN ZUCIYATA DA BAZAN IYA MANTAWA DAKU BA, HIDIMOMINNE BA KADAN BA KUMA BA AGARI ‘DAYA BA SHIYASA KUKAJI SHIRUN YAYI YAWA, INA FATAR ZAKUCI GABA DA AMSAR UZURUKKANA BATARE DA KUN GAJIYA BA, NGD SOSAI ALLAH YABAR TAREWA A TSAKANINMU👏🤝_ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _😅Bazan manta da kuba domin nakan taka salon kowace rawa tawa da bazarku, *AISHAFAREEDA, OUM AMEERA, AINA’U BASHIR (MAMAN UMMU SALMA), MURJA TSAFE, MAMAN MUHAD, KUBRA, HIJJA YAKS,MAMAN KHALEEL, MY SIDIYA, AISHATU MJ, @AISHABALA37, UMMIEY ALKALI SANI, BODINGA, HAUWA’U A AUWAL SARINA, BILQEESU LAMEEN, PRINCESS NANA, UMMU KHALIL, NASMI🥰, MOMYN AMATULLAH, RUQAYYA YUNUS, MAMAN SALEEM, MAMANBAFFA, MAMAN FATI,* wash… a gaskiya kunada yawan gaske da bazan iya ida lissafeku acikin wannan page ba, Ina miqo gaisuwa tare da fatan alkhairi agareku bisa lokacinku da kuke bayarwa wajen nuna gamsuwarku ga saqon da nake son isarwa har kuke bibiyarsa tare da addu’o’in fatan alkhairi agareni, nagode sosai ina fatan ubangijina ya yalwata rahamarsa agareku da dukkanin ahalinku, haqiqa Billy s fari takuce kuma kuma d’in natane, Ina mai addua’ar ubangiji ALLAH yabar tarenmu har a aljannah.🤞🏻ALWAYS ONE LUV NI DA KU😍_ STORY CONTINUES BELOW  Page___89💎 Su uncle h su suka d’auki batool cikin mota tare da matansu suka d’auki hanyar zuwa borno, momy kuwa matar Abba dasu Yaya Maryam da aunty marwiyya da d’aya daga cikin matan baba balarabe motarsu abbaty da akazo biko da ita suka shiga tare dani bayan motarsu uncle h sannan sauran motoci suka bi bayansu, misalin qarfe uku na rana suka miqi hanya amma basu isa ba sai qarfe takwas da rabi na dare, Kai tsaye gidan dady aka nufa da amarya lokacin ankawo imana amaryar Shakur itama, haka dady da matansa da Dr suka had’asu tare suka yimasu nasiha, nan ma saida batool ta sakeyin kuka don ta tabbata tarabu da iyayenta kenan sai Kuma idan ALLAH ya sake had’asu in tatafi kosu in sunzo wajenta, bayan an gama masu nasiha hajia nafeesa tayi gyaran murya zatayi magana dady ya dakatar da ita had’e da cewa “kutashi kutafi ALLAH yayi maku albarka kuma ya zaunar daku lafiya da mazajenku yabaku ‘ya’ya nagari.” Suna fita dady ya juyo ya kalli hajia nafeesa had’e da cewa. “Karki kuskura koda wasa naji kin shiga hurumin yaran nan har sai lokacin da kikayi hankali..” Su umma najin haka suka miqe ita da ammie sukabar d’akin don basuda alaqa da maganar da yake qoqarin yi, batare daya dakatar dasu ba yaci gaba da cewa, “Ayanzu bakida wani iko akan batool tunda takoma qarqashin inuwar mijinta wato Nuraddeen, dama nafad’a maki cewa duk abunda zakiyi baki isa ki dakatar da qudurar ALLAH akan wud’annan bayin nasa ba domin yana tare dasu, to kinga ya nuna maki d’aya daga cikin ikonsa wanda da kinci gaba da tsaurarawa to da tabbas kin jawowa kanki matsowar ajalinki kusa don shi rabo Kashi yakeyi, sai maganar hafsat wato iman, ban yarda koda wasa wani abu marar dad’i ya shiga tsakaninki da itaba don tana auren d’anki, kitsaya matsayinki in ba haka ba tsattsauran hukunci zai biyo bayanki kinji nafad’a maki.” “Amma meye dalilinka na hanani yin magana amatsayina na uwar miji ga surukata da aka kawomun kuma agabanta bayan kowa ka barshi yayi magana? Wannan ai salon arainani ne da kuma cin fuska.” “To koma dai meye kinji abunda nafad’a maki don haka sai ki kiyaye kafin tab’atar mana ni dake.” Yana gama fad’an haka yafice ya samu su uncle Hussain awaje suka sake gaisawa tare da damqa masa amanar batool ahannunsu don tuni baffa da mijin yaya Maryam suna tare dasu tunda suka iso, Ita dai iman gidanta aka wuce da ita, ita kuma batool gidan Dr aka nufa da ita inda Rashida, cike da farinciki Fatima ta taso ta tarbosu tana rungumota ajiki, “Oyoyo takwarata, sannunku da zuwa kunsha hanya.” A mai makon Fatima tabarta ta zauna aqasa saita zaunar da ita akusa da ita tana riqe da hannunta suka shiga gaggaisawa da mutanen da sukazo kawota, matar uncle hassance tace. “To iyayen batool, don yanzu kam kune iyayenta bamu ba, batada wasu agarinnan da suka fiku, gata nan mun kawo maku bisa amana, intayi ba daidai ba alurar da ita, ayimata afuwa bisa kuskurenta domin qaunar d’anku tasata rabuwa da iyayenta, don ALLAH muna roqonku daku d’auketa a matsayin ‘ya ba suruka ba hakan zai taimaka mata wajen jajircewa agidan aurenta, muna roqon ALLAH daya bata ikon kyautata maku tare da yiwa mijinta biyayya har ace qara da ankayi.” “Amin ya ALLAH,” Rashida dake zaune can gefe sai faman murmushi takeyi tafad’a, gaba d’aya yau wani farinciki takeji a tattare da ita marar misaltuwa, wai yau itace aka kawowa suruka had’e da damqa mata amanarta, tabbas duk abunda yayi farko zaiyi qarshe, tana roqon ALLAH daya sanya tarin albarka mai yawa acikin rayuwar auren d’anta ya karesu daga dukkanin sharrin mutum da kuma aljani, nan dai itama tayi mata nasiha sosai ita da Fatima wadda tamatuqar faranta rayukkan matansu uncle h kuma sun samu natsuwa d’ari bisa d’ari akan cewa batool zata samu ingantacciyar rayuwa acikin wannan ahali data jajirce wajen zab’awa kanta domin nagartasu ta tabbatar masu da cewa batayi zab’en banza ba, daga nan aka d’auki amarya batool aka wuce da ita gidanta da sai tashin qamshi yakeyi kana gani zaka san cewa ya dace da masu shi. STORY CONTINUES BELOW  Su uncle h kuwa tuni suka d’auki harmar komawa kano su da su baffa da kuma mijin Yaya Maryam, babu yanda Dr da dady basuyi dasu ba akan subari sai gobe saboda dare yayi amma sukace a’a sudai yimasu addu’a, hakan yasa dady cewa to subar matan su su kwana anan har zuwa gobe, kasancewar sun san da zancen walimar da za’a gudanar yasa suka amince da hakan don bai kamata ace ba’a bar wani nata anan ba. Saida su Uncle Hassan sukasa dady yayi masu sallama da hajia nafeesa suka sheda mata cewa suna sane da duk abubuwan data aikata don haka ga ‘yar uwarta nan sun kawo mata suna son tayi qoqarin aikata abunda yafi wanda ta aikata abaya, sukuma suzo suyi mata aika aikar da bata tab’a tsammani ba, suka dai yimata fad’a sosai tana tafaman nonnoce kai qasa saboda wata irin kunya data rufeta, gaba d’aya batayi tsammanin sunsan da abunda kefaruwa ba don tasan halinsu ba itaba ko mahaifiyarta tayi ba daidai ba a matsayinsu na yayunta zasu iya zuwa su b’ab’b’allata balle ita, Saida suka tabbatar sunja Mata kunne sosai saboda karsu tafi subar baya da qura sannan uncle hassan yakira matarsa awaya ya sanar da ita cewa si zasu wuce, hakan yasa ta tattaro sauran ‘yan uwa suka nufo gidan dady a tsammaninta tare zasu wuce, don haka gidan yarage amarya ce kad’ai aciki tana jiran angonta, Suna isa uncle hussain yayi masu bayanin anan zasu kwana sukuma zasu wuce, addu’a sukayi masu tare da fatan ALLAH ya kaisu lafiya sannan suka wuce sukuma suka shige nan gidan dady wanda mafi yawancinsu a part d’in ammie suka sauka, aunty marwiyya da Yaya Maryam kawaine suka kwana apart d’in umma a zaune suna firar yaushe gamo, wacce rabinta duk akan Nuraddeen sukeyinta wato mahaifin little. ••• ••• ••• Cikin wata shadda milik d’unkin babbar riga little yashiga d’akin da acan ne yake tsammanin batool d’insa na ciki shida abbaty daya rakkosa riqe da leda, bakinsa d’auke da sallama ya shiga tana zaune akan sallaya tagama ranka sallolin da ake biyarta da batayi ba, qasaqasa ta amsa sallamar batare data d’ago kai ba har sai da taji muryar wani abayanta, da sauri ta juya taga abbaty ne yana murmushi ya ajiye ledar dake hannunsa had’e da cewa. “Kar dai har kin tsorata matar qaramin baba?, To kwantar da hankalinki nasan matuqar kina tare da wannan mai sunan dadyn nawa babu abunda ya isa ya matso kusa dake ya cutar dake, so yayyarki agaresa ta Isa ta wadatar dake wajen samun kariya har iya qarshen rayuwarki, Ina fatar zaki kula mana dashi sosai had’e da gusar masa da duk wata kewa taki data kasance a tattare dashi na tsawon shekaru.” sosai kalaman abbaty suka yimata dad’i tare dayin murmushi tace dashi. “ALLAH yabani ikon aikata hakan!” Ya amsa mata da cewa.”Amin ya rabbhi, Bari naje dare nayi, ALLAH yabaku zaman lafiya tare da zuria masu albarka.” Saida yakalli little da tun d’azu ita yake kallo yana murmushi sannan yace. “To sarki! Yau fa gaka ga gimbiyarka, ubangiji ALLAH yasa adaren yau ka amsa sunan nan naka na abu sumayya.” Yaqarasa maganar cike da shaqiyanci tare dayin dariyar qeta sannan yafice, girgiza kai kawai little yayi yana dariya tare da bin bayansa yayi masa Saida safe sannan yarufe gidan had’e da tofa addu’a. Koda yadawo ya tarar batool tamiqe akan sallayar da tayi sallah tana lunkewa yace. “A’a keko gimbiya, kibar mana ita muyiwa ALLAH godiya bisa wannan burin soyayya tamu daya cika mana mukayi aurenmu na sunnah koba haka ba?” Murmushi kawai tayi masa ta maida sallayar ta shimfid’a a inda ta tashi shi kuma yashiga toileta yayo arwala suka kabbarta sallah. Raka’a biyu sau biyu yayi masu yana sallamewa sannan yayi addu’ar neman alkhairan ALLAH acikin aurensu mai tsawo, yayiwa ALLAH washi da kirari, yayi masa godiya tare da yiwa annabi salati, sannan ya roqesa daya dawo masa da mahaifinsa agaresu ya tsawaita masa rayuwar mahaifiyarsa ya kuma sanyawa aurensu albarka albarkacin girman haquri da ktawakkalin da mahaifiyarsa ke dasu, yayi hakanne saboda yanada yaqini akan duk abunda mutum yayi tawassali dashi matuqar anyisa domin ALLAH to ALLAH na amsawa yabiya buqata. STORY CONTINUES BELOW  Jawo ledar yayi sukaci naman dake ciki atare tare da lemun hollandia sannan yaje yacire kayan dake jikinsa ya watso ruwa tare da kakkashe fitillun dake gidan, Gab da zai shiga d’akin batool tayi saurin kashe fitilar yayi murmushi tare da tura gambun qofar sannan ya hau gadon, a tsammaninsa zai jita saman gadon a kwance amma yana lalubowa yaji wayam, hakan yasa ya zabura da sauri yamiqe yana kiranta a hankali, “Gimbiya,gimbiya, Ina kike ne, Ina kika shigene?” Tana jinsa tayi shiru had’e da shan jinin jikinta a bayan gambun qofar, tun yana kiranta ahankali yana lallalubowa har yasoma d’aga murya. “Pls batool, where are you ne?, Kada kisafa jinin abu sumayya ya hau ko zuciyarsa tabuga, zo mana gimbiyata, sanyin idaniyar abu sumayya,..” Maganar yakeyi yana qoqarin kamo abubuwan dake cikin d’akin ko zaici sa’ar damqota ita kuwa tanayi tana qara maqewa ajikin bango dariya na neman kuccikke mata, duk taku d’aya da zaiyi sai yafad’i kalmomi masu matuqar tsada da isar mata da saqon irin tsantsar qaunar da yake yimata, tun yana saran zai kamota har ya gaji ya nufi inda makunnin fitilar zai kunnawa, tana ganin haka tayi saurin juyawa tare da aza fuskarta ajikin ginin taba d’akin baya har lokacin tana saye da hijab d’inta. Yana kunna fitilar haske ya mamaye d’akin ya hangota awajen, dariya yayi tare da sakin wata ajiyar zuciya sannan ya sake kashe fitilar ya taka ya iskota har wajen, azo kansa yayi asaman kafad’arta had’e dasa hannuwansa ya rungumota yana shaqar qamshin dake fitowa daga tsakankanin wuyanta, lumshe idanuwa yayi had’e da cewa. “Gimbiya ni kaka shammata haka?, Wato kina so ki auna girman soyayyarki awajena ne ko kuma kina son irin wannan wasar tajawo narasa raina ne?.” Da sauri tajuyo had’e da aza yatsanta a saman lab’b’ansa tana girgiza kai, “Kadena fad’ar haka Abu sumayya, mutuwa bazata ziyarcemu awannan lokaci d’aya zame mana mafi tsada acikin lokutanmu, idanma zatayi hakan to na tabbata anan gabane kuma atare zata d’aukemu, tsananin soyayyarka tasa na aikata hakan Amma idan na b’atama kayi haquri kayafeni.” Taqarasa maganar had’e da d’ora kanta asaman qirjinsa, shafa bayanta ya shigayi tare da lumshe idanuwansa sannan yace. “Ina fatar hakan zata kasance atare damu, yanda muka rayu atare kuma mumutu atare, zuciyata nafad’amun cewa soyayyar da muke yiwa junanmu bazata bari d’ayanmu ya rayuba matuqar babu d’aya, ” “Idan ma hakan tafaru Abu sumayya to tabbas rayuwar wanda aka Bari bazatayi amfani ba domin Babu mahad’inta aduniya, Ina matuqar tsoron zuwan wannan ranar domin bazan juri rashinka ba Abu sumayya.” “Haka nima gimbiya bazan iya rayuwa babu keba.” “Da gaske?” “Fiye da gaskiyarma idan akwai yafad’a tare da sake jawota ajikinsa suka nufi saman gadon” suna dariya. _Ina ganin haka nafito aguje had’e da cewa Saida safe duk da ba lallaine su jini ba tunda basu san dani ba_😅🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️asuba tagari. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ STORY CONTINUES BELOW  _Gaisuwar fatan alkhairi agareka d’an qanina M.K, *MUHAMMAD KAREEM* haqiqa bazan tab’a iya mantawa da d’imbin kyautatawarka agareni ba no matter how in life!, kadamu da sha’anina ka tayani isar da saqona saboda kyakkyawar zuciyarka, bana haufi da tantama akan cewa samun irinka adoron duniya abune mai wahala dake buqatar sai an tona, akullum addu’ata gareka shine, ALLAH yashiga cikin lamurranka kuma yasa kafi qarfin dukkannin abunda yafi qarfinka, ALLAH ya zamemaka jigon rayuwarka aduk inda kashiga kuma yasa kazamo mai cin galaba ga dukkanin abunda ke baka tsoro, ngd ngd sosai da d’imbin karamcinka agareni ALLAH yabaka aljannah da rahamarsa👏 Auntyn MK na fatar zamowarka cikin alkhairan ALLAH safe, rana, dare da dukkanin lokutan da rayuwa zata aramaka, STAY BLESS🤝_ Page___88💎 Haka akaci gaba da shire shiren buki cikin farinciki da jin dad’i ta kowane b’angare, inda tuni matan su uncle h suka d’auki harmar gyara amarya batool ciki da wajenta, haka hajia mama da kanta take zuwa har part d’in uncle Hassan don tuni batool takoma hannunsa tayi mata duk abunda yakamata sannan ta komawarta, gaba d’aya an watsar da sha’anin Abba agefe su uncle sai shire shirensu sukeyi hankali kwance suda sauran matan gida yayin da shikuma kullum yana d’akinsa cike da baqinciki da damuwar wargaza masa lissafi da Kuma buri da ‘yan uwan nasa da bayanda zaiyi dasu sukayi. Tuni ankai lefe akwatuna takwas da jikkuna qanana guda biyu, duk wanda ya kalli lefen sai yayi sha’awar sake kallo saboda yanda ya tsaru, akwatunan kad’ai ma abun kallone balle kayan dake cikinsu, don ba qaramin qoqari Fatima tayi ba wajen tsayawa kai da qafa tahad’a kayan sosai yanda zasu burge kowa, kama daga kan suturu, takalma da jikkuna, kayan shafa, sarqoqi, turarukka, mayafai da sauransu duka tsadaddi ta saka masu matuqar kyau kuma komai iri d’aya tazuba cikin kayan lefen na little da kuma na Shakur babu wani abunda ta banbanta inba colours ba, shima ita takira kowanensu tace su kira amaren nasu su tambayi kowacensu best colour d’in data fiso, wannan shine dalilin da yasa aka samu banbanci wajen colours d’in akwatunan da kuma kayan da keciki, Su baffa kam babu wani dogon shiri da sukeyi duk da dai anan gidansa za’a wankan ango kafin yaje d’aurin aure, wanda D.r ne yaso yayi hakan dady yace a’a yabarwa baffa domin shine yafi cancanta da yayi hakan koba komai zai rage masa rad’ad’i da damuwar da yake ciki. Batool kuwa anbuga an raya akan ta d’anyi wani program daya kamata kafin d’aurin aure amma tace ita bata buqatar yin komai inba walima ba, itama tafiso sai bayan ankaita da kwana d’aya sai agudanar da ita acan kamar yanda annabi keyi wanda hakanma yayi daidai da ra’ayin little shima, acewarsa yafi buqatar yayiwa ALLAH godiya bisa mallaka masa abunda bai tab’a tsammanin cewa halin daya shiga ciki zai iya bari ya samesa ba da yaje garin murna su aiwatar da abubuwan da zasu jawo masu fushin ALLAH acikin rayuwar aurensu. Suma su uncle sun amince da hakan duk da dai akwai su ‘yar walimar da suka shirya bayan angama d’aurin aure wacce itace matsayin taron yinin biki da za’ayi, both ango da amarya zasu halarci walimar ana gama d’aurin auren a babban gidan gwamnati da d’aya daga cikin aminan Abba ne ya d’auki nauyinta gaba d’aya, taron zai kasance mata da maza, manya da yara zasu iya halartarsa batare da wata damuwa ba don akwai qwaqqwaran tsaro da aka tanada awajen kuma walimace da aka tanadi b’angaren mata daban na maza daban inda malamai da dama zau halarci walimar wacce za’a fara qarfe goma sha biyu na safe bayan angama d’aurin aure zuwa qarfe d’aya na rana. Shakur kuwa da amaryarsa iman tuni sun fara gudanar da programs d’insu inda kamu suka farayi sannan dinner sai kuma walima da zasuyi ranar juma’a Dr yace suyi haquri ita ahad’a data little da za’ayi bayan ankawo amarya, basuso hakan ba amma dole suka haqura, hajia nafeesa kuwa tun tana kumburi har tagaji tadena tashige itama uwar ango Shakur ana damawa da ita. Rashida kuwa kusan halin da baffa yashiga itama cikinsa take don a ‘yan kwanankin nan da suka rage batada aiki kullum sai kuka, taso ace wannan ranar zata riske sune tare da habibynta amma sai gashi yau ita kad’ai ke gudanar da shagalin d’ansu alhalin yana raye ba mutuwa yayi ba, lura da hakan yasa Fatima ta dinga qoqarin janta cikin mutane ‘yan buki da suka zo saboda takawar mata da damuwar amma duk da hakan bai hana cikin dare tazauna tayi kukanta mai isarta sannan tamiqawa ALLAH al_amurranta tare da addu’ar ko meye akan habibynta ALLAH ya yaye masa shi yakarkato hankalinshi izuwa garesu, musamman Fatima tasa aka d’unkawa little kayan cin buki kusan kala goma tsadaddi masu kyau ta d’unka masa ga wasu da Rashida itama tayi masa, shi kansa kusan kala biyar ya d’unka sai gashi ana gobe d’aurin aure Dr yazo masa da wasu shaddodi bugaggi masu shegen kyau da tsada kusan kala uku d’unkin babbar riga shida Shakur da zasu saka wajen d’aurin aure amma kowanensu kalar nasa daban, qwaya d’aya ne wata farar shadda gizna da tasha aiki har tagaji yayi masu kala d’aya da alamu su zasu saka wajen d’aurin auren, aikuwa murna da farinciki agun little ba’a magana kamar zai taka kan jariri, ji yakeyi yazama d’an gata gaba da baya baya da inyace yana fama da maraicin rashin uba akusa dashi yayi qarya saidai kawai yace yana fama da kewar rashin ganinsa ne kawai, godiya shada Rashida suka taru sunata yiwa Dr da fatima har ba adadi, Dr yayi murmushi had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Haba maman little ai inaga izuwa wannan lokacin godiya bata kamata ba a tsakaninmu saidai addu’ar ALLAH yaqara mana danqon zumunci, inhar godiya tazamo dole a tsakankaninmu to mune yadace muyi maku ita domin kun zamo mana haske acikin gida, tunda kuka shigo rayuwarmu ALLAH yaqara bud’a mana tare da saukar mana da ni’imar ‘ya’ya da muka dad’e d’auke da quncin rashinsu tattare a zukatanmu, haqiqa komai na duniya yanada sanadi gashi asanadiyarku rayuwa tazo mana da sauqi, don haka dole mufaranta zukatan da suka zamo silar farincikinmu don nuna godiyarmu ga ALLAH, don haka bana buqatar irin wannan godiyar agareku ko kad’an, addu’arku kawai ta isa kumata wadatar.” “Shikenan uncle mundena, ALLAH yayi maku sakayya da farincikin duniya da kuma na lahira, mungode sosai.” Murmushi Dr yayi had’e da d’ora kansa saman kan kujera fuskarsa na kallon rufin falon yace. “A haf! Indai kece nasani bazaki dena wannan godiyar ba data riga ta aurar maki baki.” Duk suka kwashe da dariya har da Fatima. “Nagode Abba, ALLAH yaqara bud’a da tsawon rai” shima little yafad’a yana kallonsa yana dariya. Miqewa Dr yayi kamar zai fita yariqo kafad’ar little dake qoqarin tashi shima had’e da d’an matsesa kad’an ya d’aga hannu kamar zai dokesa yana cewa “Kai ko!” ‘yar qara little yayi had’e da cewa. “Awwsshh…mama!” Irin yad’anji zafi kenan! Fatima na dariya tace, “A’a’a’ahhh.. Dr cikamun yaro kada ka b’allashi yana shirin zama ango gobe.” “Haba matar, ina ni Ina karya wannan zabgegen saurayin naki, ko bakiga yanda yake neman kereni da tsawoba?, Anya ma tuwon gidannan kawai yake ci bada na gidan umma ba?, kodai d’aki kike sashi kina qara masa da wani bamu sani ba?” “Eh tam, kodai nayi ai banyi laifi ba, naga wasu yini sukeyi suna d’urawa yaran nasu abinci ba dare ba rana, to meye don nima nayiwa nawa d’an jaririn haka? Ka cikashi tsautsayin angwanci nake tsoro ga yarona ko little.?” Ba kunya little ya d’aga kai Rashida tayi murmushi had’e da d’auke kai tana qoqarin barin wajen tace. “Wayaga god’ai god’ai, ALLAH yatsari jariri idan haka yake!,” Yanda tayi yasa Dr sakinsa tare da bushewa da dariya yana fad’in. “A’a maman little banda cin gira fa kusa ga ido, har yanzu takwarana jaririne, zo muje kafad’amun idan akwai sauran abubuwan da kake buqata kafin gobe.” Yaja hannunsa tare da ficewa. Rashida kuwa girgiza kai kawai tayi tana ‘yar dariya taqarasa shigewarta batare da tabi takansu ba. Gidan amare kam yasha kyau musamman na batool da gaba d’aya saida su uncle suka cika mata d’akunan da kayan d’aki masu kyau don duka kayan nawajene hatta kayan kitchens d’inta suma daga waje su Uncle h sukasa akayo odarsu, duk wata gata da suke tunanin mahaifinta nada niyar yimata sunyi mata fiye da hakan, babban falonta kad’ai saitin kujeru biyu aka zuba mata aciki, qarami kuma saiti d’aya, sai kayan gado d’aki biyu aka samata su tare da wata qatuwar katifa a d’an qaramin d’akin dake cikin gidan Wanda kamar an tanadesa ne saboda yara ko baqi da doguwar wadrobe had’e da cheat of drawer aciki, komai dai yaji Masha ALLAH, nera tasha kashi sosai don su uncle sun bud’e bakin aljifansu duk da ba itace ‘ya tafarko da suka fara aurarwa agidan ba, amma amatsayinta na ‘yar gaban goshin yayan nasu sun nunama duniya cewa tabbas itad’in ‘yar gatace, duk wanda ya shiga gidan yafito sai kaji yana fad’in albarkacin bakinsa, wasuma har suna kiran little ya tako arziqi, hakama a b’angaren iman iyayenta sunyi qoqari matuqa sunsa mata komai daidai qarfinsu, inda Shakur ya sake zage damtse wajen ganin yasa duk abunda yaga batada shi saboda gudun ‘yan gutsuri tsoma musamman da yaji mahaifiyarsa na zancen irin kayan da aka narkawa batool agidan little, har tana fad’in da yanzu suke dasu ankayi masu baqinciki saboda sonkai. STORY CONTINUES BELOW  Kwanci tashi ba wuya awajen ALLAH haka ita SANNU SANNU bata hana zuwa saidai adad’e ba akai ba, abunda duk aka sawa rana kuma to tabbas qararrene, yau misalin qarfe 12:30 na rana dubban mutane suka sheda d’aurin auren NURADDEEN NURADDEEN IDRIS ALIYU (LITTLE) DA AMARYARSA FATIMA UMAR FARI, a nan anguwar sharad’a phase 1 dake cikin kano inda yasamu halartar manya manyan baqi ciki harda mataimakin gwamna jahar da ciyamoma da manyan ‘yan kasuwa na cikin gida da waje don babu wanda su uncle h basu gayyato ba, kama daga kan abokanan yayan nasu(Abba) har zuwa nasu abokanan, ‘yan uwa da abokan arziqi, mutanen anguwa, mutanen gari nakusa dana nesa hakan yasa anguwar tacika maqil ko masokar tsintsiya babu, duk inda ka duba manyan motocine sai huci sukeyi tamkar ana cidasu, abunka ga sanannen mutum wanda akasan dashi nan take ‘yan gidan redio da television suka isa wajen suna d’aukar rahoton yanda ake gudanar da d’aurin auren, duban irin karamci da halaccin dasu dady suka yiwa jininsa yasa baffa yaroqi dady daya zamo wakilin ango ma’ana ya karb’ar masa auren batool a hannun iyayenta, shi kuma dady sai yace yabarwa baba balarabe, nan shima yace a’a yabar masa ya amsa kawai, ganin abun nasu yakoma jayayya yasa baffa Usman yace, Dr nura yaje yakarb’o masa auren sun nad’asa waliyin ango dama shiyafi dacewa don shine ubansa su duka karambanine zasuyi, ba tare da bata lokaciba kuwa nan take yaje aka gudanar da d’aurin auren dama tuni anbada sadaki don haka sai abun bai wani d’auki dogon lokaci ba. Ana kammalawa motoci suka fara kwasar mutane zuwa d’akin taron da za’a gudanar da walima, sai dai shi baba balarabe da baffa Usman da bashar(abbaty) d’and’an Dr wanda shine babban abokin ango tunda bawani girme masa yayi ba dasu Hassan da Hussain ‘ya’yan baba balarabe su suka tsaya wajen gudanar da walimar tare da ango, su kuma su dady, Dr, baffa, juyawa sukayi suka koma borno don misalin qarfe 2:30 na rana za’a d’aura auren Shakur da amaryarsa hafsat (iman) dama booking d’in jirgi sukayi ya kawosu Kuma shi zasubi su koma saboda yanayin lokaci mota bazata bari su isa dawuri ba, da da baba balarabe za’aje sai dady yace akwai buqatar ace iyayen ango sun halarci walimar, don haka sai ya tsaya akaje da baffa da mijin aunty marwiyya. Suna Isa kai tsaye suka nufi wajen d’aurin auren Shakur don har lokaci yasoma qurewa dama dady yabar amininsa da faruk su tsaya tare da Shakur koda sunyi lattin dawowa, suna zuwa aka fara gudanar da d’aurin auren wanda anan ma Dr shiya karb’arwa qanensa shakur auren iman. Bayan an kammala d’aurin auren mutane suka hallara zuwa qofar gidan Dr wanda sai alokacin Rashida takira Dr tafad’a masa akwai reception d’in data had’awa ‘yan d’aurin aure anan gidansa idan an kammala, wanda ita ta shiryashi da kud’inta batare da sanin kowa ba si Fatima data fad’awa don komai odarsa tayo a restaurant, nan take Dr ya sanar da dady akayi sanarwa akwai reception a anguwarsu Dr. dama dakon mutane kenan kamar yanda abun yasoma zama al’ada yanzu don haka suka nufi gidan Dr wanda tuni ankafa qatuwar rumfa da kujeru awajen, wasu kuma mutanen suka tafiyarsu saboda wasu uzurukka nasu, bayan kowa yaci yasha ya qoshi shakur yashiga har cikin gida yayiwa Rashida godiya sannan shida abokanansa suka nufi gidansu iman don d’aukar hotuna. ••• ••• ••• A can kano kuwa saida aka gama kwashe kowa aka kai can inda za’ayi walima sannan su Uncle h suka zo suka d’auki amarya batool, matar uncle Hussain da amaryar Abba wato kishiyar hajia mama su suka riqota har zuwa cikin mota, sanye take da royal blue lace yasha fararen fulawowi masu fad’i ajikinsa anyi mata d’unkin riga da sket, sai wata qatuwar alkibba fara tas itama daga saman kai ayi mata aiki da royal blue d’in zare haka agaban rigar da bayanta an qawatashi shima, kallo d’aya zakayi mata ka hango tsantsar farincikin dake tattare da ita don takasa b’oye hakan, kasancewar ita d’in kyakkyawa ce ta ajin farko yasa bata wani bari aka cika mata fuska da irin kwalliyar nan da ake yayi ba sai dai ‘yar kad’an data qara fiddo mata da kyanta na asali sai qamshi take zubawa tayi matuqar kyau tubarkallah masha ALLAH abunka ga farar macce da blue d’in abu ke matuqar amsa. Batare da b’ata lokaci ba uncle Hussain yaja motar suka bar wajen, Abba kuwa dake can bayan corridor d’akinsa zaune bisa resting chair idanuwansa arufe miqewa yayi yakoma cikin d’aki yarufe yanajin wani irin rad’ad’i azuciyarsa, tabbas yau ya yarda da bahaushe dake cewa son zuciya b’acin zuciya..Wai yau ‘yarsa da yafi so fiye da komai aduniya itace ke farinciki bayan baqin cikinsa, itace tazab’i bijire masa akan zab’inta, ta yarda tarasa gatar da yake bata taje ta zauna da wani marar asali matsiyaci da baisan darajarta ba, ta zauna da mutanen da basuda wata kima da daraja a idanuwan mutane, idan kuwa hakane dole a matsayin sa na mahaifi daya reneta cikin kulawa har takawo wannan girman yanuna mata kuskurenta na fifita wasu akansa. STORY CONTINUES BELOW  A can wajen walima kuwa tunda aka shiga da ita idanuwan little ke kanta ko qyabtawa bayayi, ganin an nufo wajen da ita yasa little qoqarin miqewa da sauri abbaty yaja rigarsa yakoma ya zauna. “Little meye haka?, Duk idanuwan taron nan fa na akanka, ina zakaje idan katashi?” Sai alokacinma little yafahimci ko meyake son yayi yayi saurin duba gefe da gefensa yana murmushi tare da sunkuyar da kansa qasa yana sosa qeyar kansa, qasa yayi da muryarsa had’e da cewa. “Old man.” Don haka yake kiransa saboda sunan marigayi baba dake garesa. “Ya akayi?, in baka waje zaka tafine?” “Haba! Bahaka nake nufi ba, bakaga yanda gimbiya tayi kyau bane!, Sak tafito a gimbiyarta wanda kamata yayi ace awannan lokacin nazama srki, ya kake tunanin abun zai kasance.” Saida abbaty yaui dariya sannan yakai bakinsa wajen kunnensa had’e da cewa. “Abun zai matuqar burgewa, Amma kayi qoqarin farkawo daga mafarkin da kakeyi inba haka ba ko yanzu kazamo sarkin marasa kunyoyi awajen nan!” Da sauri ya juyo suka had’a ido dashi ya kad’a masa kai alamun tabbatar masa da abunda yafad’a had’e da d’an turo masa idanuwansa. Hakan yasa yayi saurin tattaro natsuwarsa zuwa ga sauraren wa’azin, bini bini yake juyawa ya kalli batool dake can kan kujera saiti dashi a gefen da mata suke, malamai sunyi wa’azi sosai akan zamantakewar aure da kuma neman aljannah, mutuntaka da kuma girmama rayuwar d’an Adam, muhimmancin riqo da addinin da kuma kariyar da take bayarwa acikin aure, tausayi tsakanin ma’aurata da taimakekeniyar juna, yiwa juna uzuri tare da fahimtar juna, kyakkyawar zamantakewa da iyaye da kuma ‘yan uwa had’i da mutanen gari, haquri, juriya da Kuma yiwa juna uzuri acikin rayuwar aure, duk da ba awaje d’aya suke zaune ba alokaci d’aya zukatansu sun quduri riqe junansu amana bisa wud’annan kyawawan nasihu da suka fito daga bakin manyan malamai tare dayin alwashin aiki da duka nasihohin da suka saurara. Ana kammalawa mutanen da aka tanada saboda su kula da jin dad’in baqin da suka halarci taron had’e da ci da shansu suka fara zagayawa da abintayye kala kala suna a’ajiyewa tare da gorunan ruwan sha masu sanyi da kwalayen lemuna kala kala, ga kaji da snacks suma sai abunda mutum kesonci zai zab’a yaci, _😅acan nahango mutanena su aunty fareeda da meamah dasu teemah gabs anbaje anata Jan gara, aunty fareeda kam sai tura kaji takeyi acikin jikka wai zata riqawasu arfatu, gani awaje an hanani shiga sai ta taga nake samun d’auko maku rahoto, nahadiyi yawu yafi a qirga amma babu wanda yakulani sai aunty maijidda data hangoni a jikin taga ta taso saye da hijab d’inta tundaga sama har qasa riqe da take away guda biyu duka naman kajine aciki ta miqomun tana fad’in, My billy ungo kirage zafi da wannan tunda sun hanaki shigowa, kece da naci komai sai kice sai kin d’au rahoto kin fad’awa mutane shiyasa suka saka maki idanuwa suka hanaki shigowa, ALLAH idan bakibi hattaraba ko motar kai amaryar ma baza’a bari kigani ba sai dai kawai kiji ance ta haihu nace, to aunty Maijidda taimakon da ruwa da lemun mana, ga samosa can da tsinken tsire guda hud’u ki had’omun dasu, dariya tayi had’e da d’aukomun tace, yo my Billy kice ke kinfima wud’anda suka samu shigowa murewa_ Saida kowa yaci yaqoshi hani’an mari’a sannan motocin suka sake kwashesu suka mayar dasu gida wasu kuma daga nan suka wuce gidajensu suna masu yiwa ango da amarya fatan alkhairi da kuma samun zaman lafiya da zuri’a masu albarka. Batool nakomawa gida su uncle sukace aje agyarata yanzu za’a wuce da ita gidan mijinta, ai nan take jikinta yafara rawa hawaye suka soma zubo mata tashiga dube duben inda zataga mahaifinta ahankali tana kiran sunansa. “Abba, abba, abbanah, momy Ina abbana?” Tafad’a tana kallon matar mahaifin nata, dafata tayi sannan tace STORY CONTINUES BELOW  “Ki kwantar da hankalinki kizo muje kigyara zan kaiki har inda yake kinji ko?” Kamar wata samna batool tace. “To..” tare da bin bayanta. Bayan angyarota tana tashin qamshi tako Ina ajikinta mom takaita indasu uncle h suke tanzaunar da ita, hud’uba suka sake yimata kamar yanda iyaye keyiwa ‘ya’yansu idan zasuyi aure sannan sukasa aka kira hajia mama ta sake yimata. Cikin dakiya tace. “Batool haqiqa yau kin samu cikar burinki duk da kin sab’awa mahifinki awani b’angare, Amma Ina roqon ALLAH kada yakamaki da wannan laifin ya yafe maki, Ina roqonki da kibi mijinki sau da qafa fiye da yanda nake yiwa mahifinki, ki girmama masa iyayensa fiye da yanda kike girmama naki, kishiga gidanki da niyar bautar aure ba kasuwanci ba, kaji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH Kuma kiriqe ibada da kuma addininki, wannan shine nasihata agareki, du abunda kika yimani kuwa nayafe maki duniya da lahira, ALLAH yayi maki albarka yabaki zuri’a d’ayyaba yakareki da sharrin mutum dana aljani da kowace irin halitta, dafa kanta tayi had’e da karanto mata addu’a ta tofa mata sannan tabar d’akin da sauri saboda kukan dake neman kuccikke mata, batool kuwa tsananin kukan da takeyi ko fita sautinsa bayayi saidai sheshshekar da take famanyi kamar za’a cire ranta, ‘Dagota uncle Hussain yayi had’e da riqo hannunta na dama uncle Hassan yariqota a gefen hagu suka nufi part d’in Abba inda d’akinsa yake, suna zuwa suka tarar da qofa kulle suka bubbuga yaqi bud’ewa, sunfi mintuna biyar suna magana amma bai tanka suba balle susa ran zai bud’e hakan yasa suka juyo da ita tana kuka tana waiwayen qofar d’akin had’e da kiran sunansa amma yaqi bud’ewa. Ganin har zasubar part d’in bai bud’eba yasa ta kwace hannuwanta da gudu takoma bakin qofar d’akin tana kuka tana bubbugawa. “Abbana don ALLAH kabud’e, Abbana, Abbana to kayimun magana ko zan samu albarkarka kaji Abbana, Abbana don ALLAH kabud’e na sake ganinka ko sau d’aya ne..” Yana jinta yayi banza da ita harsu uncle h suka gaji suka dawo suka riqeta, wani irin kuka tafashe dashi had’e da cewa. “Wayyo Abbana..za’a tafi dani don ALLAH kafito, abba, Abba..” Ganin bazai tankata ba yasa taroqi su uncle subarta ko sau d’aya tayi magana dashi, bakin qofar takoma ta jingina tana fad’in. “Abbana ina matuqar qaunarka, nasan cewa kana fushi dani bisa bijire maka da nayi amma don ALLAH ka yafemun, zan tafi cike da d’imbin kewarka azuciyata, ban sani ba zan dawo agareka ko kuwa rai zaiyi halinsa kafin nadawo gareka idan ka dena fushi dani, zan rayu cike da tsammanin cewa wata rana zaka waiwayeni da idanuwanka na rahama da kuma tausayina, Abba kacire damuwa akaina, natabbata cikin ‘yan uwana da yawansu zasu share maka hawayen wannan halin dana saka, kayi haquri nakasa sarrafa zuciyata tafi qarfina akan abunda take so, Ina sonka abbana, Ina roqon ALLAH daya tabbatar da kai cikin amincinsa ya cika qirjinka da farincikinndan kasa sakaka aciki.” Tana rufe baki uncle Hussain yaja hannunta suka fita da ita kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita har suka kai bakin motar da zata shiga, tana aza qafarta da sauri ta dawo da ita had’e da juyowa jin takun tafiyar da tasan ta mahaifinta kawai ce, shine yafito yana nufato inda suke fuskarnan tasa ba walwala aciki da gudu tanufi wajensa zata rungumesa yayi saurin dakatar da ita, tahanyar d’aga mata hannu, cak tsaya batare daya damu da wud’anda ke tsaye wajen ba yace. “Nayafe maki Fatima Amma bisa sharad’i d’aya.” Da sauri ta d’aga masa kai tana qoqarin qarasowa inda yake ya sake dakatar da ita, alokacin su uncle h suma suka matso don sauraren me zaice suma ya dakatar dasu ta hanyar cewa. “Ina buqatar yin magana da ita kad’aine ba daku ba, kunyi yanda kuke so naqyaleki, kun nuna isarku akanta na amince da hakan ayanzu kuma Ina so in nuna maku tawa isar akanta har ma daku gaba d’aya” STORY CONTINUES BELOW  “Batool kije nayafe maki Amma bisa sharad’in karki sake tako qafarki anan gidan har sai lokacin dana barsa ko kuma raina ya rabu da gangar jikina, idan kuma kika kaucewa hakan to kitabbatar babuni babu ke kuma nafiddake a matsayin ‘yata, Zaki iya had’uwa da duk wanda kike so ciki harda mahaifiyarki Amma ba’a cikin gidanan ba.” Yana gama fad’ar haka tajuya yanaci gaba da cewa. “Wlh wlh duk Wanda yasa takarya wannan umurni nawa acikinku to yakarya dangantakar dake tsakanina da ita na uba da ‘ya kunji nafad’a maku.” Bud’e da baki suke kallonsa don Basu tab’a tsammanin cewa zuciyarsa zata kasa lanqwasawa ba da kalaman da ‘yarsa tayinmasa sai yanzu, asali ma da sukaga yafito sun zata ya saukone ashe wata baqar zuciyarce tasa taso, ai kan su juyo batool tazube awajen some sukayo kanta aguje. Hajia mamace tafito tana hawaye riqe da cup da ruwa aciki ta yayyafa mata ta farfad’o, tana bud’e ido tafad’a jikin mahaifiyarta tana kuka, d’agata tayi tariqata takaita har cikin mota sannan tace. “Batool indai ni nahaifeki Ina roqon kibi umurnin mahaifinki tunda yace hakan kad’aine zaisa ya yafe maki, kici gaba da addu’a nima zanyi maki ALLAH ya sassauta masa zafin rai, addu’a ta Kuma natare dake duk inda kika shiga in Sha ALLAH dakansa zai nemeki, b’acin rai yasa dole yayi haka Amma Ina roqon saukowarsa akoda yaushe, kidena kuka kinji ko Nima zanci gaba da rarrashinsa har zuwa lokacin da zai sauko.” Ta share mata hawaye sannan tanufi cikin gida itama tana share nata hawayen da suka jiqa mata fuska… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 [2/13, 10:37 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___90💎 Ana fara kiraye kirayen sallar asuba little ya miqe daga kan gadon don dama baiyi bacci ba, tun faruwar abubuwan da suka wakana tsakaninsa da ita adaren jiya ya kasa rumtsa idanuwansa sai albarka yake samata, wani irin farinciki da nishad’i marar misaltuwa ya tsinci kansa aciki, tabbas batool alkhairice sosai agaresa domin adaren yau kad’ai ya gamsu da kasancewarta acikin rayuwarsa, kallon yanda take fidda lumfashinta hankali kwance tana barci yayi had’e dayin murmushi yana shafa fuskarta had’e da cewa. “Waye yafi Abu sumayya samun mata ‘yar baiwa kamarki, waye zai kaini sa’ar samun mace tagari a duniya? Gaba d’ayanki komai naki yiyi d’ari bisa d’ari bakida wata matsala, fatana ALLAH yabani ikon kulawa dake sosai ta yanda zanci gaba da alfaharin kasantuwata dake nahar abada.” A hankali tafara bud’e idanuwanta har suka sauka akan kyakkyawar fuskarsa, murmushi ya sakar mata itama ta mayar masa tare da d’ora hannunta akan nasa dake saman fuskarta. “Lafiya Abu sumayya?” “Ina fa lafiya nayiwa gimbiyata laifi!” “Hmm! Ai duk abunda zakayiwa gimbiyarka bazakayi laifi awajenta ba matuqar kayi hakanne don kasamu farinciki.” “ALLAH gimbiya ta?” “Sosai kuwa.” Tafad’a had’e da rufe idanuwanta kamar mai shirin komawa bacci, jawo hannunta yayi ya sumbata sannan yace. “Nagode sosai gimbiyata ALLAH yayi maki albarka, kin sakani acikin farinciki da bakina bazai iya misaltasa ba kuma komai zsn baki aduniya bazai iya biyan wannan daren alkhairin da kika tanadarmun ba, amma nayi maki alqawarin cewa matuqar muna tare araye zan bautawa soyayyarki har iya qarshen rayuwata, zan kula dake kuma nabaki gatar da bazan tab’a bari hawaye su kwaranya awud’annan kyawawan idanuwan naki ba, Ina sonki da qaunarki acikin zuciyata, rouhina dama dukkanin gangar jikina.” STORY CONTINUES BELOW  Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tashiga bud’e idanuwanta ahankali tana kashe masa su had’e da cewa. “Idan kayimun haka kagama mani komai Abu sumayya, ka biyani dukkanin dakon qaunarka da nakeyi azuciyata har kabiyoni bashi.” “To kid’auka hakanma tafaru matuqar ina raye, yanzu muje na taimaka maki kiyo wanka kafin a kirayi kiran sallah na biyu.” “Karka damu zan iya da kaina, kaje kafarayi karka rasa jam’i.” Baiyi mata musu ba ya miqe had’e da shigewa toilet ya tsarkakikke jikinsa tare da d’auro arwala ya fito ya zura babbar rigarsa sannan yanufi masallaci, bayan yafita itama tamiqe taje tayo wanka tayi sallah, tana sallamewa tasamu katsar watsar tayi azkar saboda baccin dake damunta tamiqe ta kakkab’e gadon taqara gyarasa sannan takoma ta kwantawarta tana mai jin wani irin farinciki ya mamaye mata dukkanin zuciya. A b’angaren Shakur dai shima kusan hakan ta kasance, yasamu iman d’insa ayanda yake buqata yayita sanya mata albarka, kuka kam tashashi sosai tare da zuba masa shagwab’a shikuwa sai nan nan yakeyi da ita. Da safe umma ta tashi dawuri ta shirya abun karyawa lafiyayye tasa shahida ‘yar su Dr da yake anan gidan dady takwana tace taje takai masu, Saida tafara biyawa gidansu Shakur takai masu nasu sannan tawuce gidansu little, lokacin yana kwance a falo donnkoda yadawo daga masallaci ya isko takoma bacci, saboda bayason takurata yasa ya dawowarsa falo ya kwanta don inhar ya kwanta inda take to ya tabbata bazai iya qyale taba, gashi tamatuqar shan wahala jiya amma saboda jarumtarta takasa hanasa har saida ya samu gamsuwa, don haka bazaiso ya takura taba yanzu. Jin ana bubbuga qofa had’e dayin sallama yasa ya tashi yaje ya bud’e, d’an rissinawa shahida tayi ta gaishesa sannan tawuce ciki ta ajiye kwandon abincin, tsaye tayi tana murmushi yace. “Yaya aunty batool fa?” “Bacci takeyi shahida ko a taso tane?” “Eh yaya, Ina son mugaisa ne sai in fad’a mata saqon umma.” Tsura mata idanuwa yayi kafin yace. “A tasota fa kikace shahida! Cab gaskiya saidai ki haqura anjima kidawo, fad’an saqon na umma sai nafad’a mata idan ta tashi.” B’ata rai shahida tayi had’e da turo baki tana fad’in. “Yaya wato rowar auntyn tamu zaka yimani, ALLAH baran sake dawowa ba idan kace haka?” “Eh naji! jeki abinki baza’a tashetan ba, haka kawai zakice atasheta tana bacci don ki ganta, Ina ai shikenan yanzu kullum tana tare daku? to meye na neman takurata awannan lokacin?” “Lalle Yaya, Aikuwa saina fad’awa gwaggo wlh.” “Eh kifad’a mata, nasan ai itama bazata so atakurawa ‘yarta ba.” Yana rufe baki batool nafitowa daga cikin d’akin ta taso saboda muryoyinsu data dingaji sama sama wanda sune suka tasheta daga baccin, dariya shahida tayi tare da qarasawa inda take tana fad’in. “Auntynmu barka da safiya. Ina kwana” Har lokacin idanuwanta nakan little dake faman zabga mata harara. Cikin sanyin muryar dake nuna tashinta daga bacci kenan tace. “Yawwa! lafiya klw shahida ko?” “Eh aunty.” shahida tafad’a tana qara fad’ad’a murmushin dake kan fuskarta, qarasowa cikin falon batool tayi tana d’an yayyamutsa fuska saboda d’an zafin da takeji qasanta duk da dai ba irin sosai d’innan ba shahida nabiye da ita ta zauna akan kujera, kallon little dake faman binta da kallo tayi tare da sakar masa murmushi sannan tace. “Barka da safiya ranka shidad’e, antashi lafiya.” “Lafiya klw gimbiya, am sorry wannan talkative d’in ta tayar mani dake ko?” STORY CONTINUES BELOW  Fuskarta na d’auke da murmushin tajuyo tana kallon shahida da tuni sun gama burgeta tace. “Shahidaya gida yasu gwaggo da mama?” “Lafiya klw suke duk da dai ba’a can nakwana ba gidansu dady.” “ALLAH sarki, to yasu umma dasu ammie da aunty?” “Kowa lafiya, umma cema ta aikoni nakawo maku abun kari, tace na gaisheki sosai kafin tazo?” “To kice nagode shahida, Ina amsawa sosai nima ina gaishesu.” “Zasuji aunty, bara natafi kafin idanuwan Yaya su fad’o qasa.” tafad’a had’e da miqewa tana dariya, Hannu ya d’aga kamar zai mata soqo tafice aguje tana yimasu sai anjima. Da kansa yajawo kwandon abincin zaiyi mata saving ta dakatar dashi, d’aki takoma tayo brush tafito shima yaje yayo nasa sannan ta zuba masu a plate be d’aya sukaci suka qoshi ta kwashe kayan da suka ci abincin taje ta d’auraye sannan takoma d’aki ta sake kwantawa, Hakan yasa yashiga gyaggyara duk inda yakamata duk da bawani datti yayiba sannan shima yakoma inda take ya kwanta tare da jawota ajikinsa suka koma baccin atare. Basu tashiba sai kusan qarfe sha d’aya na safe, shima d’in abbaty ne yakirasa awaya ya sanar dashi cewa Dr yace su shirya za’azo a d’aukesu zancen walima an mayar qarfe sha biyu na rana zuwa qarfe d’aya saboda mutanen kano da zasu koma don dama da marece aka shirya yinta to saboda su ‘yan kano da sukazo kawo amarya dady yace ayita da Sha biyun zuwa d’aya saboda su samu su tashi dawuri donsu isa gida cikin lokaci. Kasancewar lokaci yaqure yasa agurguje sukayo wanka suka fito little yafiddo mata da wasu sababbin kaya da batama san dasu ba rigar naja har qasa tasaka, sosai tayi mata kyau shima yasa nashi kala iri d’aya da nata, sun matuqar yimasu kyau sai faman qyallin amarci sukeyi, Kallon juna suka shigayi saboda kyan da sukayi atare sukace kinyi kyau itama tace kayi kyau har suna rigegeniyar fad’a, a hankali ya tako zuwa inda take yariqo goshinta ya sumbata yana fad’in. “Masha ALLAH, matata tafi takowa! Gimbiya kinga yanda kika sake had’uwa kuwa!, Gaskiya nafiye sonkai da yawa da nayiwa maza zarra nayi masu wayon mallakarki nikad’ai, na tabbata da sunada dama da sun dingi yanka Naman jikina d’aid’ai saboda takaicin hakan ko zasu rage zafi.” “ALLAH Abu sumayya! Karfa kafasa mani kai kasa nakasa kallon kowace mace a matsayin macce awurinka inba niba.” “Da zakiyi hakan da nayi maki tukuici mai tsoka don kin gama cika mani burin dake Raina.” Odar motar da suka jiyo awaje lokaci d’aya kuma wayar little tad’au ruri yasasu tsaida kalamansu, ganin abbaty ne yasa little riqo hannunta batare daya d’aga kiranba suka fito suna taku d’aid’ai, kana ganinsu ko ba’a fad’a maka ba kai kasan sababbin amarene dake matuqar son junansu, bud’e mata baya yayi tashiga sannan shima yashigaya zauna agefenta ya rufo qofar, “Ahh! Driver zan koma maku little dad!?” Abbaty yafad’a yana qoqarin tayar da motar had’e da juyowa yana kallonsu, Masha ALLAH yafad’a azuciyarsa ganin yanda sukayi kyau sosai sannan ya gaida batool ta amsa masa a kunyace, kallon Little da idanuwansa ke kansa yayi shima ya gaishesa ya amsa masa da cewa. “Lafiya lau, barka da safiya old man! tazurun gidan Abba?” “Iyyeeee, lallai Abu yakawo ga ma’iya, Bakomai indai da rai wata rana jaririma angone! Lokacinmu nazuwa in Sha ALLAH.” Haka suka dingi fira suna tsokanar juna har suka isa, lokacin su Shakur har anmanta da an iso yana gefe inda aka tanadar masu shida amaryarsa sun had’a kai sai qusqus sukeyi ko kunyar idanuwan mutane basaji. Manyan malamai Dr yakira sukayiwa ma’auratan nasihohi masu ratsa zuciya akan haqqoqan junansu dake kansu sannan aka rufe taro da addu’a aka watse, wasu dalleliyar mota guda biyu Dr yabawa shakur da little bayan anwatse lokacin daya gama yimasu nasiha gaba d’aya, sunji matuqar dad’i sosai sunata yimasa godiya har saida yagaji da amsawa yakoma yimasu murmushi kawai. Rashida kuwa dasu umma da dady saida suka had’awa matansu auncle h shatara ta arziqi sannan suka d’auki hanyar zuwa gida suna masu yabawa zallar karamci da irin da cewar sarakanan arziqi da batool tayi bayan sunyi mata nasiha tariqe mijinta hannu biyu da danginsa tanata kuka da zasu tafi. ••• ••• ••• A b’angaren b’angarensu Inna ruqayya da baffa Ali kuwa halinsu na nan Babu abunda ya sauya, ita dai Bata daina yawon baran da take fita tare da muneera ba duk da kuwa irin taimakon da suka samu daga wajensu baffa Usman da baffa, ga Yusuf shima sai tashi fad’i yakeyi dasu amma duk bata gani tafiso tafita baran, shi Kuma baffa Ali qafa takumbure har tafara fidda ruwa tana wari amma hakan yaqara sashi komawa fitinanne fiye da da, kullum cikin tsinar d’iyan gida yake idan sun wulga ta d’akinsa yana d’ebewa iyayensu albarka, gani yakeyi kamar wani ya azo masa lalurar da yake ciki, musamman ganinsa da yakeyi zaune kullum cikin gida shikad’ai, sai yawuni a d’aki babu wanda ya leqasa saboda masifarsa inba Yusuf ba wanda hakan ke matuqar qona masa rai har yake tunanin tabbas yayan nasu ba qaramin juriya da haquri yayi ba lokacin da ALLAH ya jarabcesada had’arin daya samashi lalurar zaman gida ba tafiya kamarsa. 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___91💎 Yauma kamar kullum Inna ruqayya tafito zataje wajen baran data saba tajawo qyauren qofar d’akinta tana rufewa had’e da gyara mayafinta saiga baffa Usman yafito daga cikin d’akinsa shima, kallo d’aya yayi mata ya d’auke kai muneera na kwance bakin qofar d’aki tasa qafa ta zungureta tana fad’in.+ “Ke kasa uwar bacci tashi muje inda mukafi wayau don indai zamu yini mukwana acikin gidannan saidai takaici ya kashemu don babu abunda za’a iya tsinana mana yanda muke so, tunda ubanku yanzu bayada mamora kullum yana can kwance.” Tafad’i hakanne saboda tab’atawa baffa Usman rai data gani wajen a tsaye, muneera da itama yanzu tad’an miqe hanyar da zaka iya fahimtar takwana biyu aduniya tunda babu wata cikakkiyar kulawa da za’ace tana samu ta tashi zaune tana buga hamma had’e da cewa. “Inna wai don ALLAH fita baran nan dolene?, Wlh nagaji da yawon nan bana sonsa, muyi haquri da taimakon da muke samu daga hannun ‘yan uwan baffanmu in Sha ALLAH zai wadatar damu.” Batare data tanka taba tajawo sandarrta da kwanon da suke fita baran dasu sannan ta d’auki wata jikka irin ta d’unkawar nan tayi majalmajal ta rataya tamiqi hanya, saida takawo saiti da baffa Usman sannan tajuya tana cemata. “Inzaki taso mutafi sai kitaso in bazaki taso ba kuwa sai kiyita zama anan, yunwa da baqinciki su zasu illataki acikin gidannan kigano cewa da dangin uban naki da kike fad’in suna taimaka maki basuda amfani don wlh saita kasheki batare da ankula kiba, banda abunkima to me nasama yaci balle yabawa naqasan sa da har kike iqirarin suna taimakonmu, mu inba tarin baqinciki ba me alaqa dasu tahaifar mana tunda basa son ubanku basa qaunarsa basa bid’ar had’a jini dashi don tsabar baqinciki, ai saiki zauna cikin gidan kigani in zasu iya tsinana maki wata tsiyar shasha da batasan kanta ba ni kinga inda nayi” “To Inna kijirani mana.” Muneera tafad’a tana b’ata rai, shidai baffa Usman ko kallonta beyi ba balle yasa ran zai iya tankata, jin abunda muneera tafad’a yasashi d’ago kai yana kallonta kafin yakira sunanta. “Muneera..” Juyowa tayi tana qoqarin saka takalummanta had’e da cewa “na’am baffa Usman.” “Kina buqatar fita tare da ita?” Ya tambayeta fuskarsa a d’aure. Saida takalli fuskar Inna ruqayya dake tsaye ta aza kwanon saman kanta sannan ta maido kallonta ga baffa Usman had’e da girgiza masa kai tace. “A’a baffa, wlh nagaji da yawon barar nan, banda walaqancin mutane da tozarci babu abunda muke fuskanta, wani zubinma har zagi ake had’a mana dashi.” Baki bud’e Inna ruqayya ke kallonta kafin tace. “Don uwaki don ubaki amma ai muna samo kud’i ko?, Yo zagi zai laqekine ko zai fito maki ajiki.” “Amma Inna..” Saurin dakatar da ita baffa Usman yayi had’e da cewa. “Bashi nake son jiba muneera, kinada ra’ayinne ko bakyada shi Ina so na sani a matsayina na yayan mahaifinki.” STORY CONTINUES BELOW  “Bana ra’ayi baffa nafi son inzauna gida abina,” “Shikenan komawarki ki zauna, daga yau naharamta maki zuwa bara kuma duk wanda ya tilastaki to ‘yan sanda zasu shiga tsakanina dashi saboda inada iko akan ‘ya’yan d’an uwana.” “Baffa Inna bazata bani abinci ba…” “Bana son shashanci muneera, indai kinyarda yayan mahaifinki nake to kibi abunda nace batare da sab’awa ba, ni kuma nayi maki alqawarin zanyi maki duk abunda yakamata ace yayi maki.” Washe baki muneera tayi don tasan halin baffa Usman fad’a da cikawa ne, qarasawa tayi kusa dashi had’e da cewa. “ALLAH baffa zanyi yanda kace, amma harda aure zaka yimun?” “Zanyi maki muneera inkina buqatar hakan kuma kinada wanda kike so…” “Uban kuturu yayi kad’an wlh, ba wanda ya isa hanani fita bara da ‘yata, Ina ni nahaifi abita ba wani ba? Maza kitaso muje kafin na sab’a maki” Inna ruqayya tafad’a tana laqame kwanon acikin hamuttatta, baffa Usman bai tankata ba yashige d’aki abinsa don yasan kowace muneera, batada babbar damuwa duniya irin ahanata abincin da zataci kuma tunda har taji yafurta cewa zai yimata komai tofa babu wanda ya isa ya sake tirsasata batun zuwa yawon bara tunda dama bata so tagaji, qarasawa muneera tayi kusa da ita takarb’i kwanon baran da jikkar da sandar Inna ruqayya tazata binta zatayi sai taji tace. “Inna ki ajiye batun fita baran nan don ALLAH kizo mukoma cikin gida, su baffa zasu taimaka mana kinga koba komai zamu muhuta da cin mutunci da mutane keyi mana” Tun kafin yarufe baki Inna ruqayya ta wafce jikkarta tare da kwanon, zata karb’i sandar muneera ta ja baya da ita had’e da cewa. “Babu inda zaki jefa Inna kawai kihaqura, fisabillahi dubeni yanda nabi duk na tsofe akan titi nakasa samun koda d’an qauyene balle d’an birni ya aureni saboda son zuciya irin taku, izuwa yanzu yakamata ace kun zubar da makaman yaqinku, donni kukeyi kuma tuntuni nace nahaqura meyasa ku bazaku haqura ba, duniyar nan takarantar dani darussa da dama wud’anda a matsayinki na iyayena kun kasa fahimta, ada ana yimani kallon shashasha, sakarai, samna da batasan inda duniya tanufa ba, ana kallon cewa na cika hauka da shirme amma ayanzu inada gwargwadon hankalin da zan iya banvance qarya da gaskiya, Inna baran nan bayada amfani don girman ALLAH kihaqura dashi, bayin ALLAH nan su ake cutarwa amma duk da haka akoda yaushe suna iya qoqarinsu na ganin sun sauke haqqin zumuncin dake tsakaninmu dasu sai muyita shurewa hakan!, Yau ina roqonki don ALLAH da darajarsa kihaqura da zancen bara mukula da baffanmu da ‘yar gudun mawar da zamu samu daga wajen ‘yan uwansa kafin lokaci ya qule mana, munyi abubuwa da yawa da yakamata mu natsu munemi yafiyar bayin ALLAH n nan…” Ai kafin taqarasa ta qwace sandar jin zata b’allo masu ruwa sannan tace. “Ya isa haka, sai kikeki ki zauna, zanga tsiyar da za’a yimaki kuma wlh kika sake kika bud’e baki akan wata maganar da ta shafemu saina tsine maki, jeki ni bazan iya zamaba don ALLAH baiyini da matacciyar zuciyar da zan zauna sai wani yabani ba.” “Assha innarmu, ai inaga duk tafiyar d’aya ce, dama dama wannan shida ba roqa zakije kiyiba, taimaka makine za’ayi acikin gidanki a matsayinki na uwa kuma matar d’an uwansu wanda sune dolenmu.” “Dallah tafi can, nadai fad’a maki ni kinga tafiyata.” Ta ficewarta tanata maseefa da ita, har takusa fita tadawo tanufi d’akin da baffa Ali ke jinya, tana kaiwa bakin qofar kafin ta d’aga labule yajefo wata gora dake gefensa tabugeta ga qwabri yana fad’in. “Wane d’ebabben albarkane abakin qofar d’akinnan, tsinannin yara, d’iyan abun kware!, Magulmata da basuyi gadan mutunci ga iyayensu ba, wanene anan?” Muryar Inna ruqayya yajiyo tana fad’in. “Kai ka kai ka kai!, Ali yau maseefar taka akaina zaka saukar da ita?, Ni kake jifa da gora salon nima ka kaini kabaro gaba d’ayanmu mukoma zaune ana nunamu, to wlh kaga inda nayi nafasa shigowa, wannan muguwar gora dad’a so kakeyi ka karya mun qafa da ita, to nafasa shigowar sai anjima idan na dawo.” STORY CONTINUES BELOW  “Haba ruqayya, are bansan ke bace, nazata shashashun yarannanne masu kaida komowa da d’an kai suna regena, Yi haquri kiwhigo mana muyi magana.” “ALLAH da sai in tafiyata abuna, wannan ai mugunta ne” tafad’a tare da d’aga labulen ta tura kanta aciki, ai kafin ta ida shiga tayi saurin dawowa baya sanadiyar wani irin wari daya bugi hancinta tana fad’in. “Nashiga uku ni ruqayyatu, Ali mezanji haka! Kardai kace bayan gidane kayi azaune yake wannan d’oyi haka!,” “Haba kekuwa! ya za’ayi nayi bayan gida bayan Ina iya motsawa da kaina, ga yaronnan Yusuf kinsan bazai barni cikin qazanta ba.” “To nikam narantse maka da ALLAH bazan iya minti d’aya a d’akinnan ba saboda warin da yakeyi, yanzu ma ALLAH yagani ka cuceni da kasa nashigo ciki bayan kasan akwai irin wannanazababben wari aciki, wai! To nidai zani wajej bid’o maka abunda kaci tunda yanzu ba kada mamora, kakoma mani cima kwance.” “Ikon ALLAH, yanzu da bakinki kike fad’ar haka bayan kinsan irin wahalar da nakeyi daku lokacin da ina lafiya?” “Yo yanzu kuma aimuke wahala dakai tunda bakada lafiya, ka jika da wani zance, Ina ai gaskiya nafad’a ba qarya ba zaka wani yab’omun gori, yanzu shekararka nawa ahaka zaune? Ai inaga ko ban biyaka ba duka nakusa biyanka wahalar da kayi damu, kajimun zancen banza da wofi, nikam tin wuri wlh ka sawwaqemun indai qafarnan takace ke wari don bazan iya cigaba da rayuwa dakai ba.” Tana gama fad’ar haka tabar wajen batare da tsaya sauraren abunda zai cewa ba duk da tana jiyo sautin kiran sunanta da yakeyi amma ta tafiyarta. Haka rayuwa taci gaba da gudana tsakaninsu, muneera dai su baffa sun hanata zuwa bara don da sukaga ma tana nema ta tilasta mata baffa Usman yasa takwashe kayanta takoma gidan baffa inda baba nusaiba, kuma tana samun kulawa daidai gwargwado don har makarantarsu nusaiba ta islamiya da daddare take binta, kuma ba laifi tana fahimta, duk da tagirmema baba nusaiba tana bata girmanta daidai gwargwado a matsayinta na matar wan mahaifinta kuma itama tana jin dad’in zama da ita sosai, gaba d’aya muneera ta canza daga muneerar shekarun baya da batasan ciwon kanta ba izuwa kamilar muneera data san ciwon kanta yanzu, duk wani taimakon aikin gida takan riqawa baba nusaiba batare da tajira ance tayiba kuma tana kula da qannenta su Rashida cikin so da qaunar juna. Hakan yasa su baffa sukayi tunanin samamata mijin aure duk da kuwa shekarunta sunja sosai, inda akwai wani abokin baffa Usman dake gadi acan cikin birnin kano agidan wani alhaji, amma d’an asalin nan qauyensu ne yanada mata biyu da yara goma sha hud’u donnhar ya aurar da wasu ya tab’a ganin muneera tun lokacin da dad’ewa yayiwa baffa Usman maganar yana so yabashi aurenta, Amma saboda matsalar iyayenta da rawar kanta alokacin baffa Usman yabashi haquri saboda kada su samu matsala a abokan takarsu ta sanadiyar aurenta, don haka sai ya iskesa ya sake tuntub’arsa akan maganar idan har yanzu yanada ra’ayinta kuma cikin iyawar ALLAH yanuna masa shi bai damu da tsufanta ba har yanzu yana sonta indai za’a aura masa ita, nan take su baffa sukace suma sun amince yaje yaganta suyi magana, yana zuwa kuwa muneera ta amince masa ba b’ata lokaci don dama abunda ta dad’e tana jirane ALLAH bai kawo mata ba sai yanzu, iya darasin duniya dai izuwa yanzu ta d’aukesa don haka babu abunda take buqata yanzu inba samun abokin zaman da zata ida sauran rayuwarta da shiba. Duk da yanayin da baffa Ali yake ciki hakan bai hanasu bashi haqqinsa ba na zamansa mahaifi agareta duk da kuwa babu abunda zai iya attakawa alokacin saboda yanzu ciwon qafar har yakai yafara shafuwar lafiyan jikinsa, ya rame sosai tamkar ba shiba, babu yanda ya iya illa yabi abinda sunka zomasa dashi don ko yace yaqi amincewa tofa bayada qarfin da zai iya dakatar dasu, Inna ruqayya kuwa tayi maseefa tayi jidalinta har tagaji lokacin da zancen yazo mata wanda zuba idon da baffa Ali yayi ya matuqar tab’a mata zuciya har ta d’auki fushi dashi tadena kulasa dama can Kuma ba wata kulawar take basa ba tunda tafahimci halin da yake ciki, acewarta bazata iya zaman shaqar wannan warin qafar tasa da yake fama da ita ba. STORY CONTINUES BELOW  Yusuf kuwa kullum cikin aikin gini da labaranci yake yana tara kud’ad’e don yasamu yakai mahaifinsa asibiti hakan yasa baya samu ya wuni gida sai da marece zuwa dare, baffa Ali yayita zaginsa yana fad’in wai shima gudunsa yakeyi shiyasa baya zama gida da rana, tsiga kuwa sai wacce yamanta, haka Yusuf zai zauna yayita kuka yana basa haquri amma tamkar yana sake turasa. Bayan sati biyu aka tsaida zancen auren muneera tare dasu baffa da Yusuf da iyayen baba aminu mai gadi da sukazo nema masa auren nan da wata mai hita in ALLAH yakaimu, inda su baffa suka koma fad’i tashin kayan aurenta batare da sun jira komai daga kowa ba inba Yusuf da ako yaushe yake bibiyar yanda abun zai kasance ba matsayinsa na d’a babba daya rage masu abokin shawara agidan, Tsananin tausayinsa da baffa keji yasa ya tambayesa in yana son ‘yarsa muneera ya aura masa ita ko yasamu natsuwa akan yanayin da yake ciki, Yusuf na matuqar son Rashida amma daya tuna matsalar mahaifiyarsa da mahaifinsa sai ya nunawa baffa cewa bayada halin yin aure yanzu asali ma baida inda zai aje matar, baffa yayi murmushi had’e da cewa. “Indai wannan itace matsalarka babu damuwa in Sha ALLAH, ALLAH bazai hana yanda za’ayi ba kashirya in Sha ALLAH zan aurama Rashida indai kana sonta, shekarunka naja yakamata ace kaima kamallaki iyalinka izuwa yanzu.” Shiru Yusuf yayi yana jinjina halayyar baffa wacce ahalin yanzu tayi qaramci, a koda yaushe yana qoqarin rama cuta da alkhairi kamar yanda annabi keyi, bayan duk cutawar da iyayensa suka yimasa amma gashi zai d’auki ‘yarsa yabashi wannan wace irin kyakkyawar zuciya yake da ita da batada riqo balle qoqarin rama cuta da cutar da aka yimata, kuka yafashe dashi tare da zayyane masa gaskiyar dalilinsa naqin auren baffa yace bakomai, in Sha ALLAH baya hango komai sai alkhairi acikinsa don haka ya kwantar da hankalinsa, baffa Usman kuwa kafe kai yayi akan bai yarda ba Kuma bai amince da had’inba saboda Inna ruqayya, yasan Yusuf baida wata matsala don kusan halayyarsa irin ta ya nura ce Amma abun dubawa shine halin da zasu jefa yarinyar aciki, Kar azo a maimaita abunda yafaru ashekarun baya ga yarinyar mutane abubuwa duk sukabi suka lalace, Inna Bilkisu ce tayita lurar dashi har ya amince amma yace ba yanzuba kamar yanda baffa ke buqata sai idan takammala karatunta na sakandiri, yanzu tana aji hud’u don se daga baya baffa yayi tunanin sasu makarantar saboda yanda bokon gaba d’aya yafice masa arai, badon baffa yaso hakan ba ya yarda tunda har ya samu ya amince. Bayan wata d’aya su baffa aka fara shore shiren auren muneera don dama a satin farko na sabon wata yakama, duk abunda yakamata uba yayiwa ‘yarsa sunyiwa muneera Kama daga kan kayan d’aki har zuwa na aikin gida da sauransu, muneera kam tayi kuka ba iyaka da nadamar biyewa iyayenta da tayi tun tana cikin qurciyarta ta kasa riqe ‘yan uwan mahaifinta da kyau si gashi yanzu sunyi mata gatar da bazata tab’a mantawa ba, baba nusaiba da Inna Bilkisu ma sun tsaya mata sosai wajen gyara kanta duk da tana nocewa, Amma suka nuna mata aishi aure ba ruwansa da tsufan mace matuqar tanada rai da lafiya dole tagyara kanta don samun natsuwar mijinta, Inna ruqayya kuwa ko ajikinta don har ranar da aka d’aura auren muneera Saida ta tashi fita baran Saida Yusuf yayi da gaske sannan tahaqura shima Saida yabata dubu uku tukuna, gaba d’aya haukan tsufa yaqara tarar mata akai da rashin arziqi takoma wata birkitacciyar tsohuwa sai dai ace ALLAH yakyauta. Alhamdulillah anyi auren muneera lafiya an watse lafiya batare da wata hayaniya ba ko tashin hankali, acan cikin kano inda baba aminu ke gadi cikin wata anguwa ya kama mata hayar d’aki d’aya a wani gidan haya mai d’akuna barjik aka kaita har zuwa lokacin da zai kammala mata nata d’akin acan bebeji inda matansa suke.. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 STORY CONTINUES BELOW  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___92💎 Haka rayuwa taci gaba da kasancewa a b’angaren su baffa wani lokaci farinciki wani lokaci kuma baqinciki musamman idan sun kalli halin da d’an uwansu ke ciki yanda rayuwa ke basa wahala amma yakasa fahimta, ga matarsa gaba d’aya ta gujesa yanzu, babu wata kulawar da yake samu daga wajenta saboda yanda ta qara kwand’arewa a lokaci d’aya, Babu Wanda ya isa gareta kuma babu maiyi mata magana taji sai abunda take so, ta maida bara umrun azhimun tare da bashi muhimmanci fiye da komai arayuwarta, duk iya qoqarinsu baffa na ganin sun dakatar da ita hakan ya cutara dole suka haqura suka zuba mata idanuwa amma abun na matuqar cimasu tuwo aqwarya, Ganin irin yanayin da baffa Ali ke ciki na rashin samun cikakkiyar kulawa yanda yakamata duk da d’ansa Yusuf na iya yinsa yasa suka yanke shawarar kaisa asibiti saboda basuda lokacin zaunawa subashi kulawar data dace tunda kowanensu na wajen kasuwancinsa matarsa kuma batada lokacinsa tana can wajen bara, gashi magani akeyi amma kamar ba’ayi, saboda tsananin baqar zuciya baffa Ali ya nuna masu baya buqatar taimakonsu, sunyi sunyi dashi har sun gaji amma fir yaqi amincewa dole suka haqura shima suka saka mashi idanuwa don kowacce duhu to baiji zawo ba, Wasa wasa qafar baffa Ali ta sake kumburewa wasu ruwa nafita daga cikinta masu shegen wari, tun baffa Ali yana haquri da jurewa har yakai yafara kuka saboda tsananin azabar ciwon dake damunsa, reras yake zaunawa yayita kuka Amma babu wanda ke kulasa sai yusuf, baffa Usman kuwa dama yayi zuciya yafita al’amurransa yana jiran lokacin da zai gano cewa shayi madarane yakawo kansa da kansa in taqamarsa kafiya da mugun riqo azuciyarsa, Da daddare yau baffa Usman na kwance yajiyo ihun d’an uwansa na kuka yana qarawa saboda azabar data kaimasa karo yana kiran sunansa yazo ya taimakesa ya kawo masa d’auki, yaso ya qyalesa har sai yaqara gano kuskuren da ya aikata amma qarfin jinin zumunci dake gudana a tsakankaninsu yasa yakasa aiakata hakan, saukowa yayi daga saman gadon da yake kwance tare da jawo wayarsa ya zura aljihu sannan yabud’e d’aki yanufi d’akin da baffa Alin yake lokacin qarfe uku da minti biyar na dare, koda yashiga ya isko yusufa rungume dashi shima yana kuka had’e da tofa masa addu’a, yana ganinsa yafara qoqarin qwace jikinsa daga yusufa tare da riqo qafafuwan baffa Usman yana fad’in. “Ku taimakeni Usman ku kaini asibiti, mutuwa zanyi don ALLAH ku taimaka mani kada narasa rayuwata, wayyo Usman qafata zan mutu.” Duqowa baffa Usman yayi saiti dashi had’e da cewa. “Bazaka mutuba Ali said dai idan dama lokacinka yayi, kaga abunda muke guje maka tun farko rayuwarka, d’an uwanka kuma yayanka uwa d’aya uba d’aya ka zauna kana goranta masa don ALLAH ya jarabcesa da lalurar da tazaunar dashi waje d’aya kana yimasa dariya da kuma isgilanci, to yau gashi kaima ubangiji ya damqeka, Ina waccan lafiyar da kake tinqaho da ita?, Ina alfaharin da kakeyi na kanada qarfin yawatawa duk inda kake so don ALLAH ya aramaka lokaci?, Dubeka kagani yanda ALLAH yayi da kai yanzu wa gari yawaya tsakanin kai da kuma shi da ka dinga yiwa dariya?” Wasu zafafan hawayene suka sake karyikkewa baffa Ali yana kuka yace. “Kadubi ALLAH da girmansa kutaimaka mani ku kaini asibiti, inajin tamkar ana jawo lumfashina daga qasan qafata izuwa bakina, yanzu haka kokuwa nakeyi dashi ta yanda banida tabbaci akan zaici galaba akaina ko kuma ni naci galaba akansa, kutaimakeni, kutaimakeni, kutaimakeni, kutaimakeni ‘yan uwana fisabilillahi badon halina ba.” Shidai Yusuf banda kuka babu abunda yakeyi, tausayinsa yasa jikin baffa Usman macewa yaciro wayarsa a aljihu yakira baffa ya sanar dashi halin da d’an uwan nasu ke ciki, cikin daren baffa ya taso ya bud’e qofa yanufi gidansu baffa Usman jikinsa na rawa ba tare da yadamu da yanayin daren da ake ciki ba sai addu’a yake abakinsa har ya isa, baffa Ali naganinsa ya sake bud’e baki kai kace qaramin yarone yana gumza saboda azabar ciwo. STORY CONTINUES BELOW  “Yaya kutaimakeni, qafata, zan mutu, zan mutu yaya, wayyo qafata,” Kasancewar baffa mutumne mai raunin zuciya nan take zuciyarsa ta karye ganin yanda qanen nasa ke kuka shima yafashe da kukan. “Innalillahi wa Inna ilaihirrajiuun, Ali kayi haquri, ka kira ALLAH in sha ALLAH bazaka mutu ba, yusuf bani ruwa a kofi.” Yafad’a tare da zaunawa gabansa saman wata kujera dake jikin bango don bayada qarfin iya jurewa tsayuwa hawaye nacigaba da zubo masa. Baffa Ali kuwa sai nishi yakeyi yana fad’in. “ALLAH!, ALLAH!!, ALLAH!!!..” Kamar yanda yaji baffa yace yakira ALLAH yadena ihu da kukan da yakeyi baffa Usman natsaye yana kallonsa, aransa yana tunanin dama akwai ranar da d’an uwan nasu zai ajiye baqar zuciyarsa ya nemi taimako daga wajensu?, Tabbas ALLAH shine mabuwayi acikin al’amurransa maiyin yanda yake so alokacin da yake buqata, muryar baffa yaji yana fad’in. “Usman karb’i ruwan nan katofa masa addu’ar da ada Rashida tayi tofamun a ruwa Ina sha alokacin da ina fama da lalurarnan, zaka tunata?” Ko rufe baki baiyi ba sukaji baffa Ali yayi carab ya riqe sunan Rashida yana fad’in. “Rashida, Rashida, kiyimani addu’a, Rashida, Rashida Ina kike, don ALLAH kitaimakeni, yaya, yaya, Yaya ku kira mani ita tayi mani addu’a, don ALLAH yaya ku kirata ta taimakeni.” Gaba d’aya zafin ciwo yasa yarud’e yafara fitar da sabbatu, amsar ruwan baffa Usman yayi yana girgiza kai, aransa yana fad’in ko shegema da ranarsa, wato yau Rashidar da suka tsana yake neman tazo ta taimakesa, duk da dai yana jin tausayin halin da yake ciki amma yana ganin koma meye ya samesa shi yajawowa kansa kuma dama ita SANNU SANNU bata hana zuwa…duk abunda mutum ya shuka sai ya girbesa, tofa masa addu’ar yayi aruwan ya duqa ya bashi yasha sannan baffa yace yad’an yayyafa masa aqafar, wani irin qara yasaki lokacin da ruwan suka saukar masa saman qafa don jiyayi tamkar an watsa masa ruwan zafi, ataqaice dai ranar su baffa basu koma runtsawa ba dasu harshi, kwana sukayi suna abu guda sanin cewa ko sun fito alokacin bazasu samu abun hawa ba, nan take baffa Ali yafita hayyacinsa banda sabbatu babu abunda yakeyi har aka kira sallar asuba, baffa yafara zuwa shida Yusuf sukayi sallah sannan da suka dawo baffa Usman yaje yayi tasa. Duk wannan abun dake faruwa Inna ruqayya na d’aki abinta kwance tana sharqar bacci saboda baqin yawon baran da tasha, gaba d’aya batasan me akeyiba kai in kaganta tamkar wacce aka yanke sai faman kakari takeyi sai da Inna Bilkisu da itama baccin yayi mata qaura a idanuwa taje ta qwanqwasa mata qofa, shima d’in tafi mintuna biyar kafin ta taso tabud’e tana yatsina fuska cike da gajiya, “Lafiya dukan qyaure a tsakar daren nan?” Tafad’a tana sakin wata uwar hamma kamar zata had’iyeta, d’anja baya Inna Bilkisu tayi sannan tace mata. “A’a ba dare bane ruqayya, asubace ni Ina kukan Ali ya tadake tun d’azu kina can, sai yanzu na lura da ashe d’akin rufe yake bacci yayi maki nauyi baki farko ba.” “Eh! to meya samu Alin ne?” “Inaga zazzab’insa ne yad’an motsa nima yanzu zanje wajen naga yanda suka tashi.” “Mtss.! Nagode ALLAH da banji ba, da yanzu ya hanani d’an baccin nan, wlh yafiye rakine, meyasa lokacin da Yaya yayi jinya shi bai ishi mutane ba har ya warke, saishi zaizo ya fitini kowa, ALLAH Toni bazan iya ba?.” Tsabar tsoron ALLAH yasa Inna Bilkisu takwashi jikinta tabar wajen tanufi d’akin Yaya hawwa tana mamakin yanda mata ke iya juyawa mijinta baya haka bayan tarabasa da kowa nasa, ta izasa wajen kashewa da kuma binnewa ga abubuwan da basu kamata ba ace yanzu ta juya masa baya, koda yake ba wannan ne farau ba agidan saidai ace ALLAH yasawaqe. STORY CONTINUES BELOW  Tana shiga d’akin Yaya hawwa ta iskota zaune tana can carbi, kasancewar gaba d’aya idanuwan Yaya hawwa sun dena gani tuntuni yasa tana jin motsi tafara tambayar waye awajen don ba laifi yanzu tana d’an iya magana duk da bawani fita maganar keyi sosai ba. “Nice Yaya!” “Kece wa?” Yaya hawwa tafad’a cikin muryar dake nuna antsufa sosai. “Nice Bilkisu tawajen Usman, nazone inga ko kin samu tashi kiyi sallah!.” “Aiho! Balkisu ce?, Natashi tun d’azu, sautin kuka nakeji shiya hanani bacci.” Saida Inna Bilkisu tanemi waje ta zauna sannan tace. “Bari Yaya, Ali ne ciwon nasa ya tashi wlh gwanin tausayi, gaba d’aya jiya basu runtsa ba.” “Waye?” “Ali nace” “Wane ali?.” “Ali na nan gidan.” “Bayada lafiya ne?.” “A’a! keko Yaya har kin manta ai yafi shekaru dashi ko kin manta.?” “Namanta balkisu, shi take wannan ihun?” “Eh, kinsan kuwa abun yayi masa nauyi ace babban mutum yana kuka da ihu irin haka ai kasan shi kad’ai yasan yanda yake ji, ALLAH dai yabashi lafiya.” “To Amin balkisu, ALLAH yakyauta Kuma ya rabamu da son zuciya.” “Amin Yaya, Bari naje na duboshi.” “To kigaida shi.” Yaya hawwa taqare maganar cikin irin yanayin yanda tsofaffi ke magana, ta tabbata cewa wannan na cikin hukuntawar da ALLAH keyi masa bisa abubuwan da suka aikata tare da ita, don ita gaba d’ayama bata san abubuwan daya aikata shida matarsa daga baya ba. Inna ruqayya nakaiwa Yusuf da baffa Usman da wani abokinsa sun tallabo baffa Ali da baimasan inda kansa yake ba baffa na biye dasu don bayada qarfin da zai iya riqa masu shi zasu je asibiti. Fashewa tayi da kuka tana sallallami baffa yace taje takirawo Inna ruqayya ta sanar da ita kuma tadena wannan kukan don kada ta tayarwa da mutanen gida hankali. Koda tafad’owa Inna ruqayya cewa tayi taje tajiya zata bisu daga baya ita baccin bai isheta ba, girgiza kai kawai Inna Bilkisu tayi tare da cewa. “ALLAH ya sawaqe,” tabar wajen, Koda suka isa asibitin dake nan cikin qauyen don yanzu anqara gyarata sosai fiye da shekarun baya da sauri aka amshesa, gwaje gwaje suka fara yimasa kafin suyi masa wani abun inda suka tabbatarwa dasu baffa saidai akaisa can asibitin cikin gari saboda gaba d’aya qafar tarub’e. Jiki narawa baffa yakoma gida ya sauyo kaya tare da d’auko d’an sauran canjin da take dasu ajiye, hankalinsa atashe ya sanar da baba nusaiba halin da ake ciki cike da damuwa, ganin yanda duk yabi ya hargitse yasa tashiga kwantar masa da hankali tana gaya masa cewa yayi Imani da ALLAH shiya jarabcesu sai suyi qoqarin canye jarabawar ta hanyar qarfafa zukatansu da kuma imaninsu, sosai yasamu raguwar damuwarsa ta d’auko masa abunnkarinsa da rarrashi da ban magana tasamu ya karya daqyar sannan yafice yana mai addu’ar ALLAH yasa takasance abokiyar rayuwarsa har a aljannah. Yana komawa asibiti ya tarar shima baffa Usman har yaje ya dawo ya d’auko tashar mota suka d’auki baffa Ali sukayi general hospital dake cikin gari dashi, Suna isa likitoci ska amshesa aka shiga yimasa gwaje gwaje nan take suma suka tabbatar masu da cewa qafar tasa tarub’e tun daga tafi har zuwa Rabin cinyarsa wanda yazama dole acire qafar gaba d’aya har cinya in ana so ya samu lafiya, idan kuma ba haka ba to ciwon zaici gaba da tafiyane har can cikin jikinsa, idan sun amince ga takarda nan sai susa hannu saboda agaggauta yimasa aikin kafin ciwon yakai inda ba’a buqata bayan an fad’a masu wasu maquddan kudd’i da zasu biya. STORY CONTINUES BELOW  Basu tsaya wata doguwar shawara ba nan take sukasa hannu atakardar sannan sukaje sukasa wata babbar gonarsu da suke da ita su uku ta gado akasuwa wanda daqyar suka samu aka basu rabin kud’in ak’asa sauran kuma sai nan da kwana uku za’a basu suka karb’a sukayo asibiti, kasancewar kud’in na isa ayi aikin har su rage yasa suka amince suka karb’o kud’in suka biya aka yimasa aikin. Tsawon kwana uku baffa Ali yayi kafin ya farfad’o Amma sau d’aya Inna ruqayya ta tab’a zuwa dubasa shima d’in tabiyo ta asibitin ne tana bara tahad’u dasu Rashida d’ayan baffa napep ta ajiyesu sunzo kawo abincin, shinefa tabisu suka shiga tare lokacin yana bacci, kasancewar baffa ne awajen yasa baima kulata ba balle yayi mata fad’a akan abunda ta aikata, shi kuwa baffa Usman dake cike da ita baya samunta gida ko yakoma balle yayi mata zancen, dama yanda sukeyi yau idan baffa yawuni asibiti sai baffa Usman yaje kasuwa, gobe kuma baffa yaje kasuwa baffa Usman ya zauna a asibiti shi Kuma Yusuf da wani abokinsa suke kwana anan. Tsabar daqiqancinirin na Inna ruqayya kai tsaye tanufi wajen kan baffa Ali dake bacci tana bubbugawa had’e da kiran sunansa. “Ali, Ali, Ali katashi, nifa da akwai inda zani yanzu, bazaka tashi ba?, Shikenan ALLAH yasawaqe, dama naji ance karasa qafarka kaga dole naqara maida himma wajen nemo mana abunda zamuci, shikenan an qara mayar mana dakai cima kwance gurgu da bayada amfani dama haka ake son ganinmu, wlh dai ALLAH ya isa ga Wanda yasa aka cire maka qafa, da Wanda yabada kud’i aka cire qafar da wanda ya tuqo motar da aka d’aukoka da qafafuwanka aka mayar dakai gurgi, da wanda yasayi motar da wanda ya gina asibitin da wanda yakarantar da shegennlikitan yanda ake cire qafar duk ALLAH ya isar mana.” Taqare maganar had’e da fashewa da kuka tana sharar majina da mayafinta, shi kam baffa abunma dariya yabashi don yaga haukan natama yayi yawa. Ganin bai tankata ba yasa taja qafafuwanta tabar d’akin, tana fita tafara bin mutanen dake jinya tana kuka wai su taimaka mata aiki aka yiwa mijinta anka cire masa qafa basuda kud’in magani, haka tazagaye asibitin tana fad’a tasamu kud’inta sannan tafito ta tabar asibitin tana harhad’a kud’in da tasamu, daidai zata fita bakin gate d’in taga wani dattijo a tsaye da alama wani yake jira, ai kuwa tayi tsaye tana roqonsa, kallo d’aya yayi mata ya d’auke kai har wacce yake jira ta qaraso cikin napep ta sauketa. Da d’an sauri ta qaraso tana fad’in kayi haquri maigida, napep d’in tamuce ta tsaya muje ko, Amarya idan kinada hamsin d’an taimakawa tsohuwar nan tun d’azu ta nace tana bara kuma banida canji, irin ‘yar jikkarnan qarama ta hannu da ake d’unkawa tabud’e taciro d’ari tana fad’in. “Bari nima nabata hamsin sadaka gami da taka d’ari kenan, ALLAH yaba baffana lafiya.” ‘Dago kan da zatayi suka had’a ido biyu da mahaifiyarta wato Inna ruqayya, da sauri takarb’e naira d’arin sannan tace, “ja’ira nice…” *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___94💎 Batare data damuba tasa qafa taficewarta daga gidan, waje yanema ya zauna d’aya daga cikin kujerun dake wajen ya dafe kai, gaba d’aya yarasa wace irin rayuwace ga hajia nafeesa wacce batada lissafi da kuma sanin yakamata, ko kad’an bata gajiya da fitina arayuwarta duk kuwa yanda za’a jamata kunne, yana iya qoqarinsa wajen ganin yayi haquri da halayyarta har zuwa lokacin da zata canza amma hakan ya cutara har saida taqure haqurinsa tasa ya aikata abunda bai tab’a aikatawa tun qurciyarsa sai yanzu da manyanci ya kamasa. STORY CONTINUES BELOW  Haka ya qarashi tunane tunanensa har yagaji yamiqe yakoma cikin gida yana mai Shan alwashi akan cewa koda zai amince tadawo masa gida saita gane gaba d’aya kurakuran data dad’e tana aikatawa tukuna, Kimanin watanni takwas kenan da aurensu su little kuma adadin watannin cikin batool, zaune take tamimmiqe qafafuwanta tana faman yatsinar fuska saboda nauyin da cikin yayi mata, gaba d’aya duniyar tayi mata zafi ji take kamar ta fasa ihu, kallon little tayi dake mammatsa mata qafafuwanta alokaci d’aya kuma yana d’ibar wainar fulawa ga cokali yana bata abaki tace. “Abu sumayya, agaskiya ‘ya’yaye na d’auke da haqqin iyayensu sosai, sai yanzu nake jin tsananin rad’ad’in rashin kyautawar da nayi abbana azuciya akan kafiyar dana yimasa, da nabi komai ahankali da yanzu abbana bai haramta mani kusantar saba, wayyo…ni wannan karauniyar ce da akeyimun cikin ciki bana so wlh, Awwshhhh…ya ALLAH kabiya iyayenmu da alkhairi wlh da wahala renon cikin nan sosai, Tafad’a had’e da d’an muskutawa tana qoqarin jinginawa a jikin kujera, cike da tausayinta ya d’anyi murmushi had’e da cewa. “Ayya!, Yihaquri gimbiya, dama dole ai zakiji haka, kema ALLAH yabiyaki ya saukeki lafiya, idan summynmu tazo saina qwangare mata kai tunda ta wahalar mun da gimbiyata haka” ‘Dan b’ata rai batool tayi tana turo baki gaba had’e da cewa. “Karma kafara don bazan lamunta ba, yarinya ‘yar gwal ‘yar baiwa zaka dokanmun ita, ai kuwa da anjimu ko sumayya tah.” Taqare maganar tana shafar cikin nata tana murmushi, murmushin shima yayi mata tare da cewa. “Kice akwai match agidannn don na lura sumy a partyn adawa zata zomun Kuma bazan yarda ba.” “Shikenan tunda kace haka, damankasan ita zatayi wining match d’in shiyasa kake adawa da ita, ni kama dena kiranta da sumy kana b’atawa yarinyata suna, sumayya take baiwar ALLAH.” “O’oh Anya gimbiya!, to shikenan nadena ranki shi dad’e ummu sumayya ALLAH ya saukeki lafiya.” Ta amsa da amin tana dariya. Bayan sati d’aya da yin hakan takira mahaifiyarta hajia mama suka gaisa sannan tayi mata batun komawarta gida wajen wankan jego, ai kuwa nan hajia mama tayita yimata fad’a had’e da cewa tayi haquri ta zaunawarta gidan mijinta ta haihu babu abunda zai faru da ita in sha ALLAH tunda tana samun cikakkiyar kulawar da koda itace ke tare da ita iyakar ta zata bata, duk da bata so hakan ba haka ta haqura don kuwa ba k’arya gwargwado babu abunda tanema tarasa a fannin kulawa tun daga kan mijinta har zuwa mahaifiyarsa da sauran natare da ita, sun zame mata uwa da uba kuma sunyi mata gatar da bata tab’a tsammani ba aduniya don haka dole ta haqura da ra’ayinta tabi umurnin mahaifiyarta, haka taci taci gaba da renon cikinta yau ciwo gobe lafiya har watan haihuwarta ya kama, Ranar tana zaune taga little yashigo kai tsaye yawuce d’aki yaje ya harhad’o mata kayanta cikin akwatuna biyu ya fiddosu falo sannan yakoma ya d’auko mata mayafinta yana fad’in. “Gimbiya tashi muje..” Binshi tayi da wani irin kallo dake cike da tarin tambayoyi kala kala da take buqatar ya amsa mata kafin sutafi yayi murmushi had’e da cewa. “Easy madam! Bafa Saida ki zanyi ba, wannan irin kallo haka ai sai kisa ‘yan kayan cikina zubikkewa.” Saida tayi dariya sannan yace. “Ahh.. to! Ba dole ba naga notice tsakar rana bazato ba tsammani.” ‘Dan matse fuska yayi kamar mai shirin kuka had’e da cewa. “Yana iya gimbiya! Gwaggo tace nakawo mata ‘yarta yau d’innan ba sai gobe ba tunda watan haihuwarki yakama bazai yuyu kizauna ke kad’ai agida ba, nace zan ajiye aikina mu zauna gidan tare tace a’a, nace aturo maki Shahida shima tace bata amince ba, kinga kuwa dole na cika umurninta.” STORY CONTINUES BELOW  “Aw! Akan wannan abun d’an abun kake b’ata rai?, Lallei Abu sumayya kice kashagwab’e da yawa yanzu, Ina can d’in ba baqonka bane tunda bawani waje za’a kaini ba, ni danaso komawa kano gaba d’aya nahaihu can da sai kayi qaqa?” “Tab inbiki mana!” “Da kuwa katabbata bita zaizai gaskiya.” Taqare maganar had’e da tuntsirewa da dariya can kawai yaga hawaye na zubo mata dariyar takoma kuka, da sauri yaqarasa kusa gareta ya zauna tare da jawota ajiki yana fad’in. “Gimbiya menene?” Ta d’ora kanta aqirjinsa had’e da cewa. “Abbana, Ina son naga Abbana ko sau d’ayane, bana son namutu ban ganesa ba.” “Yaa salaam! Gimbiya meya kawo zancen mutuwa kuma, bazaki mutuba har sai muntarawa Abba jikoki da yawa da zaiyi alfahari dasu, kinsan ko jiya saida likita yafad’a maki cewa kirage damuwarnan da yawa tana tab’a lafiyar babynmu, shine kike kuka yanzu bakya son yafito very healthy ne?” “Ina so mana, Amma bazn iya dena damuwa akan Abbana ba, Ina so naji muryarsa pls Abu sumayya ko a’ane.” Ganin yanda duk tabi tarikice masa yasa yaciro wayarsa had’e da kallonta yace. “Idan kikaji muryarsa kinyimun alqawarin zaki dena wannan kukan?” Da sauri ta d’aga masa kai yayi murmushi had’e da shafo kanta dake saman qirjinsa sannan yakira Abba da d’ayan layinsa na (data) da yake using dashi, don tunda ya gwada kiransa bayan auren sau d’aya suka gaisa yagano shine yadena samunsa daga baya idan yakira, may be ya kulle masa layine ta yanda bazai iya samun saba. Bugu d’aya Abba ya d’aga yana fad’in. “Hello, hello assalamu alaikum.” Can yayi tsaki jin ba’a amsa shiba had’e da kashe kiran, d’ago kai tayi ta kallesa hakan yasa yasake kiran lambar yana murmushi. “Assalamu alaikum.” Abba yafad’a awannan karon tare dayin shiru yana jiran a amsa masa a d’aya b’angaren, jin ba’a amsashi ba yasa ya sake tsinke kiran little yasake kira akaro na ukku. A hasale abba ya d’aga kiran yana fad’in. “Wai wayene halan? Idan ba’ada abuncewa kar asake kira, shashancin banza da wofi.” Amai makon ya katse kiran saiya ajiye wayar yaci gaba da fad’ansa yana fad’in. “Wannan ai shashancine akira waya akasa magana, mutane sun d’auka yanda basada abunyi kowama baya dashi, saika rufesu da fad’a akama srry is wrong nomba.” Dariya batool takamayi ita da little tana goge hawayen da suka zubo mata, azahirin gaskiya taji dad’in jin muryar mahaifinta sosai amma aqarqashin zuciyarta wata irin kewarsa ce ta sake rufeta, tana matuqar son mahaifinta fiye da tsammani saboda tsananin shaquwar dake tsakaninsu abunma ba’a magana, qaddarowar son dake tsakaninta da little tajawo mata rabuwa dashi badon ranta yaso ba, cikin dubaru had’e da so da qauna little ya dinga fad’a mata kalamai masu sanyi da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga damuwar dake fuskarta ta gushe daga nan kuma ya karkata akalarsa izuwa muradinsa har saida suka farantawa juna rai sannan ya taimaka mata tayo wanka tashirya, akwatunan tajawo tasake gyara duk abunda take da buqata sannan yafito dasu yasa cikin mota, tana qoqarin fitowa yaja hannunta suka koma cikin d’aki shima ya d’auko wata jikka ya dinga jidar kayansa yana zubawa. Turo idanuwanta tayi awaje tana dariya tace. “Abu sumayya ya haka!, Ina zuwa da wannan uwar jikka haka kake ta loda kaya.” “Tab..ai wlh qafarki qafata bazan zauna ba, mezanyi agidan nima can zan koma ai inada nawa d’akin.” Dariya ta dinga yimasa har tana riqe ciki had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Ashe ko kaida gwaggo.” “Eh naji dai, amma bazan zauna anan ba ke kina acan sai kace wani mara gata.” Yaqarasa maganar yana kulle zip d’in jikkar suka fice tare yanaci gaba da jinini tana dariya. Satinta uku da komawa gidan Dr wajen Rashida wanda gaba d’aya duk kulawar daya kamata tasamu Rashida nabata wand idan kagani kai karantse kace ‘yartace ba suruka ba, yauma kwance take saman gadon bayan sallar magrib Rashida na gefe tana jan carbinta sai kawai taga ta zabura, da sauri ta katse lazumin had’e da miqewa tanu wajenta ganin tariqe kunkuru, “Batool lafiya?.” “Wash..gwaggo bayana.” “Subhanallahi sannu ko haihuwarce?” Bata tsay jin amsar da zata bata ba da sauri tajawo wayarta takira little sannan tayi cikin gida ta sanar da fatima.” Kan kace me gaba d’ayansu hankalinsu yatashi suka nufi d’akin da sauri, dur qushe suka iskota gefen gado tana yarfi da hannuwa tana cizon baki, ga wani zufa daya tartso mata alokaci d’aya saboda tsananin azabar naquda, ganin haihuwarce zangu zangu yasa Rashida ta d’auko wata qatuwar leda ta shimfid’a mata tare da zane sabo sannan suka kamata ita da fatima suka maida wajen, tun batool na juriya har azabar zafin ciwon naquda tasa tafara kiran abbanta tana fitar da wani iska abaki, Wani irin tausayinta yarufe Rashida tunawa da irin yanda azabar haihuwa take da tayi, safa da marwa ta shigayi tana karanto addu’o’in da tasani abaki tare da nema mata sauqin rad’ad’in da take ji, bini bini tajuyo tayi mata sannu fatima kuwa tuni tafita taje takirawo Dr, yana zuwa yasa suka riqota suka kaita a mota daidai lokacin little shima ya iso hankalinsa atashe Dr yace yashiga motar ya shiga sannan yaja suka nufi asibiti bayan Rashida takoma ciki ta d’auka kayan da za’a iya buqata. Ko mintuna ashirin basuyi da Isa ba batool ta samb’alo qatuwar ‘yarta kyakkyawa jawur da ita, ho ho zo kaga murna a wajen little ba’a magana don gaba d’aya bakinsa kasa rufuwa yayi musamman da aka fiddo yarinyar daga d’akin haihuwa Dr yamiqa mashi ita, gaba d’aya kamarta sak da batool d’insa babu ta inda tabarota tun daga kan hasken fata har zuwa kamannin fuska. Kallon Rashida yayi yana dariya yace. “Gwaggo kinga yarinyar nan gaba d’aya mamanta ta d’auko ko tayimun ‘yar kara nima tayi kama dani.” Murmushi kawai Rashida tayi batare data tanka saba tanajin wani irin farinciki marar misaltuwa na mamaye mata zuciya, soqo Fatima tayi masa akai had’e da cewa. “Lallai little ashe rashin kunyarka har takai haka ban sani ba, bazaka bamu ‘yar ba kakame kariqe sai kace wanda za’a qwace mawa sai kamanninta kake fad’a mana.” “Kema dai kyafad’a, bana fad’a maki baida kunya ko kad’an ba kikace a’a, to ai gashi yau kingani da idanuwanki.” Saida yayi mata hud’uba ya rad’a mata sunanta da tunkafin tazo duniya mamanta ta rad’a mata wato (sumayya) sannan yamiqawa Fatima ita yana fad’in. “ALLAH yaraya mana sumayya.” Had’e da gyara mata d’an bargon da aka nad’ota dashi aciki daya d’an rufe mata fuska. Baki bud’e Rashida ke kallonsa tare da mamakin rashin ta idonsa kafin taji Fatima tace “Aikam little kabushe fitilarka, ALLAH dai ya shiryaka, in dai wannan narkakkarce badon kar in saketa tafad’i ba ace kishine nakeyi ai dana sakar maka abukka qasa.” “Mama kice dai kinga zata anshe maki Abba shiyasa kikace haka, dama tunda yafito da ita naga yanata kallonta da alama yagama qyasawa.” Taji muryar abbaty daya biyo bayansu yafad’a yana wasar baki shima, hannu yaba little suka tafe had’e da cewa. “Congrat real Abu sumayya, ubangiji ALLAH yaraya mana.” “Amin” duk suka fad’a kafin dady yasake dawowa ya fad’a masu cewa batool na buqatar jini sai an qara mata don jininta yayi qasa, nan take suka nufi lab shi dasu abbaty da little cikin sa’a kuwa ana auna na little yazo daidai da nata aka d’ibi leda d’aya aka qara mata, STORY CONTINUES BELOW  Sosai batool tasamu sauqi don anata fira da ita ‘yan uwa da abokanan arziqi dake zuwa dubata, murna awajensu uncle h ba’a magana suda hajia mama da sauran mutanen gida, abbanta ma da aka sanar dashi saida wani annuri ya bayyana a fuskarsa har zaiyi magana sai kuma yayi saurin d’aure fuska yaci gaba da duba jaridarsa batare daya tanka ba, baiso tankawa ba azancen sai kuma yaji ya tsinci kansa da cewa, “ALLAH yara itama yabata lafiyar shayarwa.” Wannan addu’ar da yayi tasa kowa jin cewa tabbas nan kusa bada jimawa ba zai daina fushi da ‘yar tasa kuma yadawo da ita cikin rayuwarsa kamar yanda take ada. Bayan kwana biyu su uncle h zasuje dubo batool bayan an sallameta daga asibiti hajia mama tacire kunya agefe tabisu taje tadubo ‘yarta da kuma baby sumayya, taji dad’i matuqa ayanda taje ta isko ‘yartata cikin kulawa da walwala da kuma soyayyar uwar miji da sauran ahalinsa, kusan yini sukayi acan kafin sufara yunqurin juyowa su dawo gida bayan sun ajiye mata kayayyakin da suka jemata dasu masu uban yawa kama daga kan suturarta data baby, kayayyakin abinci da kayan qarin jini da kud’i masu yawa sukace taqara tayi hidima dasu kafin suna, kuma sauran ‘yan uwanta da iyayenta nanan tafe ranar suna sannan suka yiwa Rashida dasu Dr da iyayensa godiya sosai suna masu nuna masu farincikin da sukaji na had’a zuri’a dasu da kuma yabawa qoqarinsu wajen kulawar da sukaba ‘yarsu wanda hakan baqaramin dad’i yayi masu dady da dr ba suma, koba komai sun samu natsuwar cewa sun kula da amanar batool da suka basu d’ari bisa d’ari tunda har suka yaba ayanda suka ganta. Ranar suna kuwa batool tasha mamaki don taga gata kala kala kama daga wajen ‘yan uwanta har zuwa ‘yan uwan mijinta da nasu Dr abun saidai tace alhamdulillah, anyi taron suna lafiya an watse lafiya na kusa sun koma gidajensu na nesama sun kama hanya saidai fatan ALLAH ya saukesu gida lafiya. A ‘bangaren hajia nafeesa kuwa har lokacin bata saduda ba don tanada abunda zata iya kula da kanta koda babu abunda za’a bata agidansu, Shakur nazuwa akai akai wajenta ya gaisheta tare da abun kyautatawa da ALLAH ya hore masa, yayita qoqari wajen lurar da ita kuskuren da tayi tare da nuna mata cewa yanda take d’aukar umma ba haka suke ba mutanene masu karamci da dad’in zama amma taqi fahimta saima masifar da take rufesa da ita wai shima ambashi ya canye kamar yanda aka yiwa mahaifinsa, hakan yasa ya haqura dayi mata nasihar saidai addu’a da kullum yake yimata akan ALLAH ya ganar da ita, wasa wasa tun ana qidayar watannin da tayi batanan yanzu har takusa shekara amma taqi ta hankalta hakan yasa ‘yan uwa da abokanan arziqi aka shiga ba Abba haquri akan yabari tadawo d’akinta tunda ba sakinta yayi ba shima yabuga kai ga qasa yace bazai bari ba har sai tayi hankali, kawai aqyaleta taci gaba da abunda takeyi ai SANNU SANNU bata hana zuwa…lokaci zaiyi wanda idan taji wutar gashinta da kanta zata gano kuskuren da tayi kuma tanemi gyarawa. _BAYAN SHEKARU BIYAR_ Abubuwa da dama sun faru ciki har da rasuwar ‘yarsu Abu sumayya da gimbiyarsa lokacin tanada shekara d’aya aduniya wanda hakan ya matuqar tayar masu da hankali, musamman Rashida da little da suka d’auki son duniya suka azawa yarinyar don little kam har da zazzab’i yayi na tsawon sati d’aya, batool kuwa gaba d’aya ta dangana tabarwa ALLAH ikonsa acewarta shikad’ai yasan dalilin amsar yarinyar, yarinyar nada matuqar kwarjini da kuma shiga ran mutane sosai wanda hakan yasa mutuwarta tagirgiza mutane da yawa, ciki kuwa harda hajia nafeesa da tuni tayi nadamar abubuwan data aikata saboda ba kad’an tasha wahalar zaman gida da tayiba sanadiyar gobarar da sukayi gidansu yaqone qurmus da mahaifiyarta aciki saidai aka tattara tokarta data cinye aka sallaceta aka rufeta, ita kuma gaba d’aya jikinta yaqone fuskarta kawaice bata qone ba itama gefe yafara qonewa aka kaita asibiti da taimakon dady inda daqyar likitoci suka ceto rayuwarta don babu wandama yayi tsammanin cewa zata rayu, sai gashi cikin iyawar ALLAH da yardarsa da take kwana basu qare ba tasamu sauqi bayan takwashe watanni kusan uku tana jinya a asibiti, alokacinne tagane cewa duniya ba abakin komai take ba kuma idan mutum yasan farkonsa da qarshensa to baisan tsakiyarsa ba don kusan duk jinyar tata batool dasu ammie ne sukayi, tayi kuka sosai akan abubuwan data yimasu daga qarshe ta roqesu gafara kuma suka yafe mata umma kawaice bata fiye shiga harkar taba don har ga ALLAH bata son abunda zai jawo mata wani walaqancin awajenta, abunda bata sani ba kuwa shine hajia nafeesa tayi nadama sosai har cikin zuciyarta don har little da Rashida saida tanema gafara kuma takira abban batool tafad’a masa cewa duk abunda tafad’a akan little ba gaskiya bane, tayine saboda kwad’ayin d’anta shakur ya auri batool da kuma tsanarsa saboda soyayyar da mijinta ke nuna masu shida kakarsa da mahaifiyarsa kuma tayi nadamar hakan don ALLAH ya yafeta, alokacin Abba yayi nadamar d’aukar maganar hajia nafeesa da yayi sosai amma sai zuciyarsa ta nuna masa cewa koma meye ai bai kamata duk irin d’imbin soyayyar daya nunawa ‘yar tasa ba ace tagujesa ta bijirewa umurninsa da zab’insa ba saboda son zuciyarta, tazab’i ta b’ata masa don tafarantawa kanta da masoyinta don haka baiga dalilin da zai koma bata wata soyayyar tasa abanza ba, kuma yayiwa ita hajia nafeesar kaca kaca had’e da cewa shi yanzu bayada case da wannan maganar don haka da ita da batool d’in da mijinta suje can suqarasa, STORY CONTINUES BELOW  Wannan dalilin yasa hajia nafeesa ta qudiri riqe ‘yar uwarta batool hannu biyu tare da kyautata mata tana yimata addu’ar samun daidaituwa tsakaninta da mahaifinta kota rage alhakinta data d’auka kuma ta dinga jan sumayya ajikinta sosai tana kula da ita had’e da cewa adinga kawo mata ita tana tayata reno, kusan ko yaushe cikin sayen ‘yan kayayyakin yara take tana aika mata dasu tare da kayan wasa da sauran abubuwa wanda nan take Abu sumayya da gimbiyarsa suka manta da abunda tayi masu, dama ita uwa samnace da zaran kaso d’anta to shikenan ka gama da ita, duk girman laifinka zata iya mantawa dashi adalilin soyayyar daka nunawa d’anta kamar dai yanda suka manta da laifin da hajia nafeesa tayi masu suka saki jiki da ita suna kaimata baby sumayya da zuciya d’aya wanda hakan yajawo shaquwa mai tsanani tsakaninta da yarinyar shiyasa lokacin da yarinyar tarasu tana cikin wud’anda mutuwar ta jigata sosai. Sunji damuwa matuqa akan rashin yarinyar amma daga qarshe suka fawwalawa ALLAH komai kamar yanda mahaifiyarta batool tayi, bayan watanni bakwai da rasuwarta ALLAH yasake bawa batool wani ciki, murna awajen little kam ba’a magana kai ka rantse kace shine cikinta nafarko, don farincikin daya nuna fiyema da wanda yayi ne alokacin da tasamu cikin sumayya tana tayi masa dariya, tun cikin na qarami idan yafita sai yakira fiye da sau bakwai kafin ya dawo yana tambayar ya unborn d’insa yake har ya tsufa ko gajiya bayayi, musamman da taje scanning d’inta na farko aka tabbatar mata tana d’auke da cikin ‘yan biyu duka mata, ai sai kulawar ta sake lunkuwa har zuwa lokacin da zata haihu,….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___93💎 Cike da mamaki muneera tabi mahaifiyar tata da kallo tana fad’in, “innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, Inna wai kece?” “Eh nice nan! lafiya kike rafkamun uban salati haka sai kace wacce ta canza maki?, waima bari na tambayeki, dana ganki anan ke kad’ai ina shi mijin naki da tunda yazo sau d’aya gaishemu shima d’in da daddare har yanzu bai sake komawa ba saboda mugun hali don kar yace mana ungo.” Kallon kallo suka shigayi shi da ita kafin tace. “Maigida innace fa!” Da sauri ya duqa qasa yana gaida Inna ruqayya data saki baki tana kallonsa kafin tace. “Yanzu muneera wai wannan shine mijin naki?” “Eh Inna.” Muneera data rasa yanda zatayi da ita tafad’a tana kallonsa, jitayi mahaifiyar tata nafad’in. “Tirqashi! Kaico muneera, kice baki rabu da wahala ba, tsiyace ta taradda tsiya don wannan tsohon dagani babu tsiyar da yake tsinana maki, ana mutum haka hannuwa duk aqwaq qwange ba ko wannan ungo ta alkhairi! tun d’azu nake miqa masa hannu kusan mintuna biyar amma bawan ALLAH nan yayi biris dani ya d’auke mani kai don d’ibar albarka, Ina in bazai bani ba sai yafad’amun intafi abina sai yabarni tsaye ina miqo hannu, kaganka wallahi da gani bakada kir..” Bata qarasa ba muneera tayi saurin cewa. “Haba inna meye haka kuma!, Ai baisan ke bace kuma baya canji Shiyasa bai baki ba.” “Ke rufamun baki, samna wannan ai qwanda kiyita baranki daki zauna dashi, mutum bazaice ungo ba ta alkhairi sai dai yayita karkace karkacen kai yana duqe duqen banza.” STORY CONTINUES BELOWTa qarasa maganar tana zura wuya tana kallonsa daga duqen da yake har ya gaji dajin maganganunta yamiqe yana mummurza hannayensa had’e da cewa. “ALLAH yabaki haquri Inna.” “Innooo!, nace ba Inna ba innooo..don tsabar mugunta tsofai tsofai dakai ka kalleni kace mani Inna, haka aka Inna ba ungo ta alkhairi..” Jin kalmar ungo da taketa maybe maitawa yasa mijin na muneer tura hannu a aljihu ya ciro naira d’ari biyar had’e da d’an rissinawa yamiqawa Inna ruqayya, tsabar sauri takarb’a har yakusowa tayi da hannunsa tana fad’in. “Ikon ALLAH, to ko kaifa! da arziqinka kanemi maida kanka marowaci, to ALLAH qara bud’i kaji, agaisheka maza munneer kishiga ciki dashi kin barshi a tsaye don sakarci da rashin iya kula da miji, kushiga cika mana baffan naku nacan dad’a a guntule qafa abun gwanin tausayi.” Taqarasa maganar had’e da fashewa da kuka tasa mayafi tana sharar qwallan da suka zubo mata. Muneera da tsabar baqin ciki da takaici sun rufe mata idanuwa tayi fuuu…tawuce abunta batare data qara bi takanta ba, bayanta mijin nata yabi yana kiran sunanta har ya cimmata ya tsaida ita, ganin da yayi idanuwanta sun cika tab da qwallah ya sashi cewa. “Subhanallahi, muneera meye abun kuka!.” Cikin b’acin rai tabud’e baki zatayi magana yayi saurin dakatar da ita don yasan dole taji ba dad’i aranta, Amma ya zatayi? Mahaifiyar tace dole tayi haquri da ita, d’an murmushi yayi kafin yaci gaba da cewa. “Baikamata ace kin nuna b’acin rankiba har kiyi fushi kitafiyarki kibarta awajen, ita uwa uwace baza’a tab’a canza taba komai lalacewarta, don haka kijeki idan kinada abun kyautata mata ki kyautata mata tare da magana mai dad’i cikin girmamawa, hakan zaisa nasamu natsuwar cewa koda nan gaba nayi tsufan da zan buqaci taimakonki to bazaki tab’a wofantar dani ba.” Dama damuwar muneera shine kar mijin nata yaji ba dad’i ko yayi qoqarin walakantata akan wannan abun da mahaifiyarta tayi, amma da taji yafad’i hakan sai tasamu wata irin natsuwa da sauri tabi bayan Inna ruqayya dake tafe can gefen titi tana faman qirga ‘yan kud’ad’enta da bata gajiya da qirgarsu, “Inna..” munnera tafad’a lokacin data cimmata tare da riqo hannunta suka koma cikin inuwar wata bishshiya. “Lafiya muneera, ko saqo mijin naki ya sake turowa ki kawo mani?” Murmushin da yafi kuka ciwo muneera tasaki had’e da cewa. “Inna kenan!..” sannan tasa hannu cikin ‘yar qaramar jikkarta ta hannu ta d’auko kud’ad’e aciki ta harhad’a, d’ari uku ne da saba’in aciki tamiqa mata had’e da cewa. “Ga wannan Inna ni nabaki, kiyi haquri banida kud’i wannan ma sana’ar saida ‘yan kayan yaji nakeyi d’an cinakin dana samune nahad’o da niyar inba baffanmu ko lemu asiya masa, Amma tunda kina so gashi saiki qara, in Sha ALLAH zan dinga kawo maki masu yawa idan ALLAH ya bud’a mani.” Rawa Inna ruqayya tafara kwasa awajen cike da farinciki kafin ta amshi kud’in tana fad’in. “Kai a dai gaisheki muneera, ALLAH yayi maki albarka, haka nake son gani kullum don haka kiriqe mijinki hannu biyu yanda zaya yita baki kina bani kinji ko.?” “To inna, Amma naroqeki don ALLAH kidena wannan baran bayada amfani ko kad’an, yanzu kinga abunda yafaru tsakaninki dashi ai baiyi dad’i ba badon ma yanada tunani ba sai hakan yasa wata rana ya koro makini, amma kiyi haquri Idan hakan dana fad’a ya b’ata maki rai.” Taqarasa maganar tana hawaye tare da riqo hannunta. Fisge hannunta tayi daga riqon da tayi mata had’e da d’aure fuska tace. “To naji, maza kijeki yana jiranki.” STORY CONTINUES BELOW  “Kiyi haquri inna…” “Nikam muneera yaushe kika lalace haka?, nace kijeki naji ba shikenan ba?.” Jiki a sanyaya muneera tabar wajen tanayi tana juyowa tana kallonta tana tafiya harta b’acema ganinta sannan ta ida shigewa ciki tana mai addu’ar ALLAH yaganar da mahaifiyar tata. Bayan sati uku baffa Ali yaji sauqi sosai saboda yana samun kulawa wajen likitocin da kuma ‘yan uwan nasa yanda ya kamata, babu wani rad’ad’i da yakeji kamar da sai abunda baka rasa ba, yanzu babbar damuwarsa d’aya shine yanda zai kalli ‘yan uwansa inya tuna da walaqanci da kuma abubuwan daya tayi masu abaya amma duk basu dubi wannan ba sukayi tsaya wajen ganin yasamu lafiya, duk yatuna da wannan yana sashi dana sani da zubar da hawaye sosai, musamman idan yatuna yanda son zuciya da baqin hali yasashi biyewa matarsa ya raba yayan nasa da d’ansa na tsawon shekaru sai yaji gaba d’aya ya tsani kansa. Yauma zaune suke duk su duka tare dasu baba balarabe sunzo dubasa da mijin Yaya Maryam anata fira ana dariya, shikam banda murmushi babu abunda yake iyayi don rad’ad’in cutar dasu da yayi dake zuciyarsa bazai bashi damar yin walwalar da zai iya dariya ba, wasu zafafan hawaye yaji sun zubo masa a fuska lokacin daya dubi yayan nasa yaga yanda tsufa ya dabai bayesa gaba d’aya don baida baqin gashi ko kad’an a jikinsa inba jefi-jefi gashin gaba d’aya yakoma furfura gwanin ban tausayi, kukane ya kufce masa ya shiga sheshsheka yana share majina, nan take gaba d’aya hankulansu suka dawo kansa, da sauri baffa Usman ya riqesa ganin yanda jikinsa ke rawa daga kan gadon yana qoqarin fad’owa saboda tsananin kukan dake nema yafi qarfinsa. “Haba Ali!, shin har yanzu bazaka haqura kadena wannan kukan haka ba?, Duk fa mai rai dole ajarabcesa don agwada imaninsa, kai kamata ma yayi ka godewa ALLAH da yasa qafa d’aya aka cire maka, adaidai wannan lokacin akwai wanda gaband’aya dukkanin qafafuwan nasa yarasa, sai yace me?, Ana rayuwa haka ace Babu tawakkali?, Fad’amun naji shin wannan kukan naka zai iya dawo maka da qafarka ne da bazaka haqura kafawwalawa ALLAH ba domin shi kad’ai yasan dalilin dayasa hakan faruwa, kuma duk yanda ALLAH yayiwa bawa to yatabbata hakan shine mafi qololuwar alkhairi agaresa.” Baffane kefad’ar haka tare da riqo hannun baffa Ali cikin sigar lallashi, dik wanda ke wajen ya matuqar tausaya masa saboda baqaramin tashin hankali bane rasa wani sashe daga cikin sassan jikin mutum, su a tsammaninsu adalilin haka yake kuka, gaba d’aya suka taru suna bashi baki da ban magana akan ya yarda da qaddarowar da ALLAH yayi akansa, Saida yayi kukansa mai isarsa sannan yayi shiru cikin jin nauyi ya d’ago kai yana kallon baba balarabe yace. “Malan balarabe kayafeni bisa maganganun dana fad’a maka cewa, yayana da d’an uwana Usman sun zauna acikin gari suna zaginku akan cewa sunyi nadamar had’a zuria’a daku saboda sanadiyar auren ‘yarku yarusa mana farincikin gida da kuma ahali, ba gaskiya nafad’a ba da nace maka sunce Nuraddeen ya tafiyarsa wajen karatunsa batare daya sanar daku ba saboda zaku iya sa akamashi arufe da sunan shiya halakar maku da ‘ya, ba gaskiya nafad’a maka ba da nace maka yayana yace bada son ransa ya bari ‘yarku ta auri d’ansa ba don dama bai yarda da tarbiyarta ba don ance ita dakanta ke bud’e baki tana iqirarin cewa aure take so kuma qiyi mata wai lallai sai tayi karatu, shine data fara bin maza kuka rufesu da d’ansu yace yana sonta kuka aura mashi ita, shine data gano cikin dake jikinta ba nasa bane tagudu tabar gari, gashi yanzu tasaka shi cikin baqin cikin da dole suka qarfafa masa ya tafiyarsa, sannan tajawo matarsa tasamu damuwa da tab’in hankali saboda qazafin da akayi mata nacewa ita ta halakar da yarinyarku, har nake fad’a maka cewa aranar suka wuce asibitin sokoto da ita sunata ALLAH ya isar had’a jini daku, wlh balarabe duk wud’annan maganganun dana fad’a maka ba gaskiya bane, qagaggiyar qaryace na shirya don cimma wani burin nawa sai gashi sanadiyar hakan najawo matsaloli da dama arayuwar mutane, don ALLAH da girmansa kayi haquri kayafemun wataqil nasamu rangwame acikin hukuncin da ALLAH ya tanadar mun, na nayi kuskuren d’aukar mata a matsayin abokanan shawarata, nayi nadamar cutar da ‘yan uwana da nayi dama ku kanku don ALLAH kuyafeni.” STORY CONTINUES BELOW  Shiru duk sukayi kowane yarasa abun cewa sai faman jinjina kawunansu sukeyi saboda giraman kalaman da sukaji nafitowa daga bakinsa, Banda kallonsa yana faman sheshshekar kuka tamkar wani qaramin yaro babu abunda sukeyi, tabbas ko ba’a fad’aba kasan rayukansu sun b’aci musamman baffa Usman, duk da kallo d’aya idan kayiwa baffa Ali zaka iya tabbatar da cewa daga kalamansa har zuwa yanayin fuskarsa yayi nadamar abunda ya aikata daga qasan zuciyarsa, jiki a sanyaye baba balarabe da tuni ya dad’e da gano qarya daya fad’a masa wanda har yasashi nadamar abunda yayiwa su baffa ya nemesu gafara, ajiyar zuciya yayi had’e da cewa. “Wannan shi ake kira da ranar nadama da kuma dana sani, haqiqa baka kyautawa ‘yan uwanka ba ka zaluncesu da yawa sannan kasa nima nacutar dasu tahanyar d’aukar hukuncin da bai kamata ba, nazamo silar raba zukatan daya kamata ace rouhinsu da gangar jikinsu nawaje d’aya awannna lokacin, saidai hakan yafaru duk bisa shiryowar ubangiji, ni tuni nayi nadamar abunda nayiwa ‘yan uwanka don nagane ba gaskiya kafad’a mani ba kuma na nemi yafuwarsu duk da ban fad’a masu dalilina na aikata hakan ba saboda gudun lalacewar zumunci tsakaninku, sannan d’an uwa da d’an uwa dama sai ALLAH idan akayi qoqarin shiga tsakani kunya akeji, nasan komai daren dad’ewa matuqar muna raye sai wannan gaskiyar tafito kuma sai ALLAH ya bayyanata, don haka tunda yanzu kafad’i komai da bakinka inma kanada laifi awajena nayafe maka, saura naka kanemi yafiyar d’an uwanka domin shine mafi qololuwar cutarwa acikin wannan al-amarin, ubangiji ALLAH karabamu da biyewa zukatanmu da kuma aikin dana sani.” Yana gama fad’ar hakan yayi saurin juyawa yafice don gaba d’aya ji yake yau komai ya dawo masa sabo, da ace bai yarda da maganar daya fad’a masa ba aranar da yanzu Rashida da yaronta basu fuskanci baqin cikin da suka shiga cikiba akwanakin baya, wataqil da tuni Nuraddeen yadawo zuwa garesu, da yanzu d’an uwansa daya rasa ta dalilin hakan yana raye duk da dai mutuwa ita batada fashi. Sallama mijin Yaya Maryam shima yayi masu sannan yabi bayansa cike da ta’ajabin hali irin na baffa Ali. Kallonsa baffa Usman yayi cikin b’acin rai yace. “Yanzu hakan da kayi daidai ne?, Kayi farinciki ka lalata sunnar annabi?, Kayi farinciki kasaka mu cikin damuwa? Kai kuma gakanan acikin farinciki madawwami ko?, tir wlh albasa batayo halin ruwa ba, iyayenmu kaf babu mai baqar zuciya irin taka, wace ribace zakaci don ka hana asanar damu dawowar Rashida alokacin daya kamata dahar tasa ka tafka mana irin wannan qaryar! Wlh Yaya duk abunda malan balarabe yayi sai yanzu nafahimci bayada laifi kuma wallahi da nine shi sai na aikata fiye da abunda yayi saboda banga yanda za’ayi wannan qaryar takasa samun gurbi azukatan da aka gama cutarwa ba tunda gabakin jininmu shaqiqinmu da muke tare waje d’aya dashi akajita, to mezaisa akasa yarda da ita tunda ba mutum yayi kanshi ba, bashi keda ikon zuciyarsa ba balle yahanata b’aci akan wannan baqar qarya wacce batada tushe balle mafari, Kai kam…” “Ya isa haka Usman, kada ka la’ancesa mana, kome zai faru yariga daya faru ALLAH ya shiryesa, yayi hakanne cike da tunanin zai d’auki fansar qarar dana kaisu ga hukuma ne aka kullesu, indai yarage wannan zafin da rad’ad’i azuciyarsa ai shikenan Bakomai, ni nayafe masa Ina roqon nima ALLAH ya yafemun daku baki d’ai, ka qyalesa kada kasaka mashi wata damuwar bayan wannan lalurar da yake ciki don ALLAH” Wani irin takaici baffa Usman yaji aransa, Wai shi wane irin mutunne daya fiye sanyin hali haka, babu ta yanda za’ayi a qure haqurinsa har ya nuna b’acin ransa sai inta b’aci sosai, fiii yayi yabar wajen don baima san abunda zaice masa ba. Baffa kuwa dake jin wani qunci aransa binsa yayi da kallo har ya fice yayi murmushi had’e da cewa. “ALLAH yakyauta yasa mufi qarfin zukatanmu.” Hannuw baffa Ali yasake had’awa waje d’aya hawaye kwance a fuskarsa zai sake roqonsa gafara yayi saurin riqewa yana fad’in. “Karka tashi hankalinka, nace nayafe maka duniya da lahira, bawai don banji zafin abunda kayi mani bane a’a, kawainayi hakanne saboda kwad’ayin nima ALLAH ya yafemun don mukam yanzu gangara kad’ai ya rage mana mu ida tare da fatan cikawa da Imani, saidai ina roqonka daka kasance mai iya sarrafa zuciyarka akoda yaushe bawai ita ta sarrafaka ba kaji ko Aliyu.?” STORY CONTINUES BELOW  “Zan kiyaye haka Yaya in Sha ALLAH.” Murmushi baffa yayi tare da riqe hannunsa ya gyara masa kwanciyarsa sannan yace. “Bari naje wajen d’an uwanka indawo kafin likita yazo muji ko zamu samu sallama cikin satin nan.” Yana gama fad’ar haka yafice aransa yana addu’ar ALLAH yasa shiriyar daya dad’e yana nemawa d’an uwan nasa ce tazo kuma yaqara had’e kawunansu waje d’aya. ••• ••• ••• A ‘bangaren mahaifin batool kuwa gaba d’aya ya hana ko sunanta yaji an ambata a gidan, gashidai yanajin kewarta atattare dashi Amma baqar zuciya tahanasa fahimtar cewa itad’in wani b’angarece arayuwarsa dake da matuqar muhimmanci atattare dashi, tun yana keb’e kansa daga mutane izuwan duk fushine yakeyi har yagaji ya bari, su uncle h kuwa girman da suke basa ada sai sake lunkashi sukayi awajensa, ko kad’an sunqi nuna masa sun damu da fushin da yakeyi dasu da kuma shashsharesu har shima yagaij ya sauko don kansa ammafa har lokacin yaqi bada damar da za’a iya tunkararsa da zancen batool ko kad’an, sau da dama takan kira lambar wayarsa yaqi d’agawa ko kuma takira tasu uncle idan suna waje d’aya ya fahimci da ita ake wayar sai yatashi yabar wajen, hakama hajiya mama itama idan tana tare dashi yaji ankirata kuma takira sunan batool zaice ta tashi tafice masa daga d’aki ko tabar wajen daon baya buqatar jin koda sautin muryar tane, ganin yanda fushin nasa ya tsananta yasa gaba d’aya duk abunda ya shafi batool ba’ayinsa idan yana kusa saboda azauna lafiya, kuma hakan yasa yafara dawowa da yanayinsa nada duk da shi kad’ai yasan irin wahalar da yakesha aqoqarinsa na ganin cewa lallai lallai sai ya manta da ita arayuwarsa. Batool kuwa kullum addu’arta ALLAH kajuyo mata da hankalin abbanta ya manta da abunda yafaru don wani zubin damuwar har hanata bacci takeyi tayita kuka sai little yata faman lallashi ko yakira hajia mama yafad’a mata tayi mata nasiha tare da kwantar mata da hankali tukuna sannan yasamu takwanta har tayi bacci. Baya ga wannan batada wata damuwa aduniya saboda tana samun kulawa sosai awajen mijinta da kuma ahalinsa, wata irin soyayya Rashida keyimata tamkar ta mayar da ita cikin ciki, duk abunda zai b’ata mata rai Rashida taja kunnen little daya nisancesa ko don halaccin data yimasa arayuwa, tana matuqar jin batool aranta da har wani lokaci take tunanin idan har ahaka akejin sarakanai ma’ana ‘ya’yan d’anka arai meyasa ita tata uwar mijin bata so taba? Meyasa tanuna mata tsanar da ko kishiyarka bai kamata ka nuna mata ba don taga ummanta bata tab’a nuna cewa tatsani hajia nafeesa ba duk da irin cin kashin kare da aibatawar da take yimata ita da jininta. Batool tazama ‘yar gata, ba awajen mijinta kad’ai ba hatta su Dr da dady suna kulawa da ita sosai ba’a batun umma data d’auketa tamkar little jikanta, duk abunda ta yayo duniya ita dai akaiwa batool, ammie ma na iya qoqarinta don duk abunda zata yiwa matar faruq to saita had’a da batool da kuma imaan matar Shakur d’and’an hajiya nafeesa. Ganin haka yasa umma tayi kwad’ayin yin haka koba komai ai dady ya kyautata masu baici ace ta wofantar da nashi ba tana nuna banbanci don itama takan sayi abubuwa wani lokacin tace akaiwa su Fatima da matar faruk wace yarinyarsu ma ta farin mai sunan ammie ana kiranta Islam tana hannun umma tun lokacin da za’a yayeta takarb’eta shikenan sai suka barta nan basu amsheta ba, gaba d’aya kulawarta tadawo tsakankanin ita da kuma ammien, hakan yasa ranar umma tasa ayo mata odar turarukkan wuta da khumra’s masu qamshi acan kano wajen wata hamshaqiyar dilan kayan qamshi masu qamshin gaske dake saidasu bisa sassauqan farashi mai suna nana hafsat (miss xoxo) wacce anfi sanin sana’ar tata da sunan da takeyi mata laqani da *YERWA INCENSE* kayanta kam akwai kyau sosai don idan kagane amfani dasu to tabbas qamshi ya aureka duk inda kaje kaida ‘ya’yanka, miji kuwa ba zancen zaman fira awaje saboda mararin yadawo gida ya shaqi wannan dadda’an qamshi dake kwantar da hankali da kuma natsuwar zuciya, ( _hajia wannan ba qanzon kurege bane, sai kin gwada zaki iya tabbatarwa, don haka idan kina son hana mijinki fira awaje saboda daddad’an qamshin da kikeyi keda ‘ya’yanki da gidanki to kinemi YERWA INCENSE akan lambarsu ta talfo kamar haka👉 +234 809 521 5215 na tabbata zaki Sha mamaki kuma ki gode mani_ ) son da umma keyiwa kayan qamshinta yasa tasa aka kawo mata bokitayyen turarukkan da kwalaben khumra’s d’in don ta rabawa sarakanan nasu, bayan ta kakkasa masu taba shahida ta d’auka taje ta kaimasu sai ta tuna da bata bada na imaan ba wato matar Shakur, da sauri tabi bayan shahida dahar takai bakin gate tana qwala mata kira riqe da bokitin turaren wutar d’aya da kuma kwalaben khumra’s guda biyu a leda, muryarta da hajia nafeesa tajiyo yasata fitowa ta zauna akan d’aya daga cikin kujerun dake gefe wajen motocin Abba da alama baqi yayi suka tafi ta zauna tana lallatsar wayarta saboda tsabar gulma. STORY CONTINUES BELOW  Batare da umma ta damu da ita ba tunda tariga tayi niya tamiqawa Shahida ledar tana fad’in. “Ungo wannan mantawa nayi idan kin shiga kin bawa maman islam nata saiki biya ki kaiwa imaan wannan, kice muna gaishesu sosai…” Ai bata rufe baki ba taji anbuge ledar da qarfi tafad’i qasa, da sauri ta d’ago kai sukayi ido biyu da hajia nafeesa sai wani faman huci takeyi sai kace wacce akayiwa laifi, bata tankata ba ta duqa zata d’auki ledar wacce ga alama kwalaben dake ciki sun mutu tasa qafa ta sake murza ledar bokin turaren ya fashe sannan tashurasu gefe tana fad’in. “Ho iyayen munafucci da asiri, wane mugun abunne za’a d’auka akaiwa matar d’ana don arabani da ita, meye alaqarki da ita ko ina ruwanki da ita da zaki d’auki abu kice akai mata ban da baqin sheri dake zuciyarki da kuma iyayi.!” Duk wannan abu dake faruwa ashe agaban idanuwan Abba ne lokacin yafito daga part d’in ammie zai shiga na ita hajia nafeesar ya d’auko wasu takardu ya hango abunda hajia nafeesar tayi, ran umma ya ‘baci sosai amma saita qyaleta saboda bata buqatar tanka mata har tazamo silar jawo wata fitina agidan tadalilinta, inda ta shura kayan umma taje tasa hannu zata d’auke sauran don wasu duk sun d’an watse musamman turaren wuta sai taga anrigata, d’ago kan da zatayi sai sukayi ido biyu da dady, lumshe idanuwansa yayi sannan yabud’e yana murmushi had’e da cewa. “Amaryata wannan wane irin turaren wutane mai qamshi da kuma sanyaya zuciya haka?” Saida ya d’an lakuto damshin ruwan khumrar dake jikin ledar ya sake sunsunawa had’e da rufe idanuwa sannan yaci gaba da cewa “kai! Masha ALLAH, wannan qamshin khumra haka sai kace an tattara qamshin turaren duniya aciki, fad’amun a Ina aka sayeshi kuma nawa nima in siya don na burgeku.” Yafad’ai hakan da gangan yana kallon gefen da hajia nafeesa ke tsaye kamar an dasa ta da gefen ijiya. Yanda yayi maganar yasa umma sakin murmushin da seda haqoranta suka bayyana suka miqe tsaye tare yana riqe da ledar sai qara shin shina yakeyi, Shahida kuwa sai faman toshe dariyar dake son fito mata takeyi aranta tana fad’in wannan tsohon akwai gwamawa mutun takaici, can tajiyo muryarsa yana kiran sunanta da sauri ta qarasa had’e da cewa. “Na gaisheka tsoho mai ran qarfe, kayi naka kayi ta raggo ka dad’e kayi shekaru adadin yawan gashin rago,” Dariya yayi had’e dasa hannu aljihu ya qirgo dubo goma ya miqawa umma yana fad’in, “Ungo wannan asake kawo wasu sai akai mata, ke kuma Shahida ungo wannan ledar kikaiwa imaan d’in kice tayi haquri sun fashe tayi amfani dasu za’a sake kawo mata wasu.” Yaqare maganar had’e da miqawa Shahida ledar ta amsa tawuce tana kallon hajia nafeesa da tayi fam tana dariya. “A’a alhaji kabarshi akwai wasu zan sake bayarwa akai mata, basai ka wahalda kanka da kashe kud’in kaba.” taqare maganar tana qoqarin saka mashi kud’in a aljihu, riqe hannunta yayi had’e da cewa “Maman Rashida kibarsu kije kiyi yanda nace kawai ai hakan shine adalci.” Kafin yarufe baki hajia nafeesa tayo kukan kura kan umma ya zura mata idanuwa yana kallo yaga mezata aikata shima ya aikata mata irinsa sai yaga taja burki ganin kallon da yake yimata tafara zuba ruwan masifa inda take shiga ba nan take fita ba harda fad’in. “Indai zalunci abunyine yaje yaci gaba dayi, akan tsohuwar mace yabi duk ya susuce ko tsufansa baya gani don kunya Bata ishesa ba agaban jikoki, to wlh in su anbasu sun canye anayin yanda akeso dasu ita ba’a isa ba, munafuccine banxa da wofi ai wannan kinimbibine za’ayi mata.” Cin mutunci kam dashi har umma tayi masu sai wanda tamance saboda zafin kishin abunda yayi mata, gaba d’aya idanuwanta sun rufe ta manta cewa yayi mata jan kunne akan karta sake takoma d’auko masa wata fitina agida baya buqatar haka sai gashi abun yauma takansa ya qare, Saida tayi mai isarta tagama sannan yacema umma tawuce part d’inta ita kuma yace daga nan karta kuru taqara taku d’aya cikin gidansa ta tafi gidansu sai yanemeta. STORY CONTINUES BELOW  Wata irin gud’a ta ski had’e da cewa. “Tafi nono fari, don ko yanzu nafita gidanka bazan rasa mai so ba, don haka takarda ta yakamata kabani ba kace intafi gidanmu ba, kana tunanin wai zaiji baqin cikine don kace intafi gidanmu?, to wlh ko d’aya don ko yanzu kasuwa tawatse d’an koli mai rabonci yaci.” Cikin yaranta ta qwalawa kira tace a d’auko mata mayafinta da takalmi dama wayarta na hannunta, ana kawo mata tasa had’e da cewa. “To Ina jiran takarda ta mijin tsohuwar…” Bata qarasa ba ya daka mata tsawa had’e da nuna mata gate yace tafita baya son ganinta… *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___95💎 Da lokacin haihuwarta yayi ta matuqar shan wahala don kusan kwana tayi tana naquda a asibiti amma ba haihuwa ba mafarinta, hakan yasa likitocin suka yanke shawarar yimata operation, koda aka fad’a mata kowa yayi tsammanin zata tada hankalinta amma saita nuna babu wata damu don yanzu batada babban burin daya wuce taga an rabata da cikin dake jikinta lafiya, damuwarta d’aya shine mahaifinta, tana kuka takira hajia mama ta sanar da ita taje itama tafad’a masa, kamar dai wancan karon haka yayi yace ALLAH yasa ayi cikin nasara kuma ya sauketa lafiya, hajia mama taso ya amshi wayar yayi magana da ita kota samu natsuwa amma sanin halinsa yasa batayi hakan ba saidai tace mata tariqe wayar kada ta tsinke har taje tafad’a masa yace hakan, wasu zafafan hawayene suka zubowa batool jin muryar mahaifinta da tayi da kuma addu’ar da yayi mata ahankali tace. “Alhamdulillah!, Ya ALLAH kaci gaba da sanyaya zuciyar mahaifina har sai yaji yayi na’am dani kafin ka amshi rayuwata.” Godiya tayiwa mahaifiyarta tare da roqonta gafara sannan tace koda ba’a fito da ita ba ALLAH ya amshi ranta taroqa mata gafarar mahaifinta kuma tafad’a masa duk tsawon shekaru shidan data d’auka ba tare dashi ba tana rayuwane da tarin d’imbin qaunarsa acikin zuciyarta, wud’annna kalaman nata sun matuqar kashewa mahaifiyarta jiki har saida suka sa tazubar da qwalla amma bata bari ta fahimci hakan ba taqarfaf mata guiwa sosai tare da yimata addu’a ALLAH yasa ashiga lafiya kuma a fito lafiya, cikin jin dad’i batool ta amsa da amin tana maijin wata irin natsuwa atattare da ita. Cikin iyawar ALLAH ana shiga da batool ko mintuna talatin ba’ayi ba aka fiddo mata da kyawawan yaranta ‘yanmata biyu masu matuqar kama da junansu wato (identical twins), both doctors da nurses d’in da suka amshi haihuwar sai ihu sukeyi cike da farinciki ganin girman da yaran ke dasu cikin qoshin lafiya, duk wanda ya kallesu da abinda zakaji yana fad’a, “Wowww…fine baby’s, wow…the baby’s are so cute, woooo..so beautiful.” Haka sukayita santin kyawon yaran har aka gama shiryasu. Da aka fito dasu hajia nafeesa ce tayi saurin amsar d’aya, imaan matar Shakur da itama lokacin ke d’auke da tsohon cikinta na farin ta amshi d’aya don wannan karon Rashida bata zoba Fatima kuma tatsaya shiryawa yara zuwa school shiyasa hajia nafeesa da imaan suka zo don yanzu familyn sun d’unke waje d’aya tsintsiya mad’aurinki guda, dama hajia nafeesa kad’aice mai matsala yanzu kuma data shiryu sai familyn yayi gwanin sha’awa, qarami na girmama babba, babba Kuma na mutunta qarami tare da kyautatawa. STORY CONTINUES BELOW  Waya hajia nafeesa taciro takira su uncle h ta sanar dasu an sauka lafiya anciro mata yara biyu ‘yan mata sak kamarsu d’aya, saboda haka sukawo toshi sun samu takwarori, nan uncle Hussain yace aduba mashi wacce duk tafi tsawon hanci koda itace hassana to itace amaryarsa mai nakakken hanci kuwa ya barwa uncle Hassan sai ya sammata nashi aqara mata dashi shidai bayayi da ita, anata dariya. Hajia mama kuwa harda sujudush shukur tayi had’e da sadaka lokacin da aka fad’a mata anfito da batool har ta farfad’o, Abbama dai ba’a barsa abaya ba lokacin da aka sanar dashi saida yayi qwallan farinciki yayi saurin sa hannu ya goge don kar agani, yace ALLAH yaraya yabata lafiya sannan yabar wajen, murmushi su uncle h sukayi tare da girgiza kai suna jinjina taurin rai da qarfin hali irin na yayan nasu. Ko sati ba’ayi ba dayi mata tiyatar tasamu sauqi aka basu sallama, amma saboda taqara samun lafiya aka d’aga sunan sai nan da sati biyu, angon qarni kam saidai ace ALLAH yaraya masa don kallo d’aya zakayi masa yafassara maka irin d’imbin farincikin dake tattare dashi, Ba’a batun Rashida da umma da ayanzu suke ganin batool tagama faranta masu a duniya tunda ta zamo jigon wanzuwar cigaban farincikinsu da suke tsammanin yankewarsa a shekarun baya da suka shud’e. Haka su baffa da baffa Usman sunyi farinciki sosai duk da basu samu damar zuwa ba saboda matsalolin da sukasha gabansu amma saida suka aikowa da little dubu talatin sukace yaqara yayi hidima ALLAH ya raya, baffa nason ganin yaran amma babu yanda zaiyi, tsufa yaci qarfinsa sosai had’e da tarin damuwowi, wanda idan yatuna cewa rashin d’ansa akusa dashi shi yahaifar masa da har hakan kefaruwa, ga jininsa aduniya amma babu damar yagansa saidai a hoto idan little yazo ya nuna masa sai yayita kuka yana addu’ar ALLAH kasa yanada rabon bada wannan labarin kafin rai yayi halinsa kuma yarayawa Rashida zuri’arta cikin aminci da kuma kariyar ALLAH. A wannan karonma a gidan Dr batool takoma saboda kula da yaran tunda acan gidanta ita kad’ai take batada wani mataimaki, Shahida ce mai hankali acikin ‘ya’yan gidan kuma tana sudan wajen karatu balle atura mata ita su zauna tare, tana matuqar jin dad’in kular da take samu awajensu umma, hakan yasa tasake sakin jikinta sosai tana renon yaranta har akayi suna akayi arba’in sannan takoma gidanta, Inka ganta bazaka tab’a cewa itace uwar yaran ba don tayi qiba tayi haske ta murmure abunta saboda gyaran da Rashida keyin tsaye tayi mata tamkar ita tahaifeta, haka suma yaran bazaka tab’a cewa ‘yan biyu bane saboda girmansu sai ka d’auka kowane daban aka haifesa, rayuwa mai kyau da inganci takeyi da mijinta da ‘ya’yanta cikin so da qauna da kuma kulawar juna, ••• ••• ••• Kuma acikin shekarunne baffa Ali ya bayyanawa su baffa Usman duk aika aikar da sukayi shida Inna ruqayya har sukayi nasarar da bokansu ya kafe Nuraddeen acan qasar malesia kuma yasa mashi tsanaar qasarsa tare da mantar dashi akan duk wani abun daya shafi rayuwarshi ta baya kafin yaje qasar. Tashin hankali wanda ba’a saka mashi rana, awannan lokaci baffa yayi abunda bai tab’a yiba saboda tsananin b’acin rai, dukkanin qarfinsa ya tattaro yana hawaye yanata kaiwa baffa Ali mari taduk inda ya samu batare da yayi la’akari da girman shekarunsa ba, ko kad’an baffa Ali baiyi yunqurin hanasa ba har saida yagaji yadena don kansa yana fitar da nishi d’aya bayan d’aya, bayan mintuna kad’an yamiqe ba tare daya d’ago kai ya kalli d’an uwan nasa ba yace. “Ali kacutar da rayuwata da dama Amma ban damu da hakan ba inata yimaka uzuri had’e da bud’e maka fika fikan tausayina ka shige aciki Ina mai yafiya ga duk wani abu da kayi mun, Amma yau Ina mai baka haquri akan cewa kayi mani cutarwa mafi muni da girma da bazan tab’a iya yafe maka itaba har sai lokacin da kaje ka walwale wannan asirin da kayiwa d’ana, idan ba haka ba zan cigaba da rayuwa a matsayin mai d’an uwa qwaya d’aya aduniya batare dana koma sanyaka a matsayin d’an uwana ba, me nayi maka haka dana cancanci irin wannan horarwa awajenka nida d’ana?, Wace irin tsanar muce kasawa zuciyarka da bazaka iya samun koda d’an qanqanen filine azuciyarka da zaka iya yafe mana idan har wani abun muka yimaka alokacin da kasan munada matuqar buqatar juna ni dashi, kasa narayu na tsawon shekaru da baqin cikin d’ana da kuma fushinsa azuciyata?, Tir da halinka Ali tunda har zaka iya duban girman soyayyar mahaifi da d’ansa karabasu, a halin yanzu bakada wani sauran amfani awajena tunda har zaka iya saka wuqa ka datsemun farinciki na tsawon lokaci kuma ka d’auka daga yau ni ba d’an uwan ka bane kuma kaima ba d’an uwana bane.” Yana gama fad’ar haka ya juya yafice, baffa Usman dake zaune gefe ya kallesa had’e da cewa. “Yanzu kayi farinciki ko Aliyu!? Ka b’atawa zuciyar data shima tana yimaka fatan shiriya da kuma kyautatawa, ka kai haqurin bawan daya jima yana yimaka yafiya da hidima qarshe har kana nema kasa kyawawan abubuwan dayayi abaya su ruguje ga banza.” Jikin baffa Ali a mace yace. “Usman ka fahimceni, wlh na shiryu na gane kuskurena shiyasa nafad’a maku gaskiya wataqil asamo mafitar da nura zai dawo garemu, kwad’ayin na faranta zuciyoyinku yasa nazab’i nayi kunyar duniya a idanuwanku ko nasamu farinciki asanadiyar naku farincikin, ko kad’an ni ban fad’a maku wannan maganar ba don cutar da zukatanku kuma ALLAH shine sheda akan haka.” Ajiyar zuciya baffa Usman yayi don ya gamsu da maganganunsa had’e cewa. “Naji, dama ni tun farko Ina zarginku akan haka amma bawan ALLAH can yaqi amincewa da zaku iyayin wani abun akan d’ansa tunda kai jinin sane, sai gashi ka watsa masa qasa a idanuwa kasa zargina yazama gaskiya akanku, maganar gaskiya baku kyauta ba kuma kun zaluncesa sosai.” “Hakane Usman Amma wlh nayi nadama da kuma dana sani, don ALLAH katayani roqonsa ya sake bud’a mani inuwar tausayinsa da kuma yafiyarsa nagane kuskurena.” “Alhamdulillah ALLAH yasa haka Ali amma gaskiya ni bazan tirsasashi akan ya yafe maka bisa hukuncin daya d’aukar maka ba, kayi qoqarin zuwa kuwarware abunda kukayi hakan zaisa ni kuma natayaka roqon yafiyarsa.” Shiru baffa Ali yayi kafin yace. “Taya Usman?, Wlh yanzu bansan inda wannan malamin da mukaje ya had’a mana maganin da akayi sammun dashi yake ba, shekarun ba kad’an ba don gidan da yayi zama yanzu haka shine akayi sababbin shagunan can masu hawa biyu a farko farkon gari, Abu d’aya zan iya tunawa shine inda mukaje muka binne abubuwan da akabamu na sammun, shi kuma malamin ya fad’a mana cewa idan har wani yayi yunqurin haqo wajen to tabbas tsakanin ni da ruqayya dole sai d’aya yamutu, d’aya kuma za’a azo mashi ciwon da bayada magani sai dai yayita jinya har lokacin da mutuwarsa zata riskesa.” Baffa Ali yaqare maganar yana hawayen dake nuna tsantsar nadamarsa, “Tirqashi wannan wane irin cacan raine kukaje kukayi da rayuwarku Aliyu don salwantar da kawai ku salwantar da rayuwar rai d’aya? Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, wannan shi ake kira da murna ta koma ciki, ga kuma qoshi ga kwanan yunwa.” Wani irin kuka baffa Ali ya fashe dashi yana hango yanda rayuwarsa zata kasance a tsakankanin wannan sirad’i mai matuqar kaifi, har ga ALLAH ba mutuwa yake tsoro ba don yanzu ashirye yake daya sadaukar da ransa matuqar Nuraddeen zai dawo ga mahaifinsa da iyalansa, ciwo da kuma jinyar da batada magani su yake tsoron kada sufad’a kansa, Saida yayi kukansa mai isarsa baffa Usman bai hanasa ba don yasan ya cancanci yayi kukan daga qarshe yamiqa komai ga ALLAH yana Mai addu’ar ALLAH yasa suzame masa kaffarar zunubbansa sannan yace da baffa Usman. “Zanje inyi abunda yakamata domin abunda na shukane zan girba da hannuna, fatana ALLAH yabani qarfin zuciya da kuma imanin da zan aikata hakan! kuma yasa Rashida da Nuraddeen su yafemun abunda na aikata ko bayan rayuwatane.” Duk zafin ran baffa Usman da haushinsa da yake ji yau saida yaji tausayinsa, tabbas SANNU bata hana zuwa…duk shaqiyancin mutum da girman kansa da kuma izgilinsa da sannu zai cimma ranar da zaiyi nadama da kuma dana sanin yinsu, dafa kafad’arsa yayi had’e da cewa. “Karka damu Ali, ALLAH gafururrahim ne kuma mai tsananin tausayin bayinsa, babu buqatar sadaukarwar rayuwarka bayan katubanma zunubbanka, muje ni zan haqo komeye kuma da yardar ALLAH babu abunda zai samemu.”…. Knocking yayi abakin qofar d’akin Rashida tagwalo idanuwa waje tana kallon umma da gaba d’aya jikinta yayi sanyi akan labarinsu Dr da take bata na rashin haihuwarsu da soyayyar da suke nunawa little Nuraddeen, yanda tayi da idanuwa yaba umma dariya don kana gani kasan tsorone kwance fal a qasan zuciyarta, jin baba na sake bubbuga masu qofar ahankali muryarsa qasa qasa yana fad’in. “Maman Rashida wace irin firace haka kukeyi har qarfe uku takusa kuna zaune, da haka kutashi kufuskanci ubangiji mana kufad’a masa buqatocinku inaga yafi wannan b’ata daren da kukeyi a banza” Yasa umma saurin cewa. “To malan dama yanzu nake tunanin haka.” “Yawwa to ai yafi, kutashi.” Baba yafad’a tare da juyawarsa yakoma masallaci yana mai fuskantar ubangijinsa yana mai godiya tare da sake miqa d’imbin buqatunsa agaresa. Haka ta b’angaren aunty marwiyya tsabar farinciki hadda sadaka tayi lokacin dasu Yaya maryam suka isa gida suka sanar da ita zancen had’uwarsa dasu umma da sukayi acan garin, rawa tadinga kwasa tanayiwa ALLAH godiya, duk da bata san taya had’uwar tasu ta kasance ba itama harda k’walla tayi. A b’angaren baba balarabe ma bacci yayi yana tunanin ko meye gaskiyar abunda yafaru ga iyalin baffa?, Kenan maganar da d’an uwansa yafad’a masa ba gaskiya bace? Idanko haka ne yatabka babban kuskure abunda yayi masu, Tsaki ya dingayi naba adadi yana ALLAH waddai da zuciyar data tunzurasa yakasa banbance qarya da gaskiya tsakanin maganganun da su baffa suka fad’a masa da kuma wud’anda d’an uwansu yafad’a masa. Matsuwa baba yayi safiya tawaye don yad’au alwashin komawa garinsu saboda sanin halin da aminin nasa keciki, a iya saninsa yasan shi da kansa yace masu susa asako yaya hawwa da d’an uwan nasa da kuma matarsa, yana tsoron kada ace garin d’aukar matakine ya jefa iyalin tasa cikin wannan halin. Tunda akayi sallar asuba baba yagama karanta azkar d’insa ya hau shirye shiryen tafiya, kasancewar dady part d’in ammie yake yasa bayan ya kammala shirinsa yace umma taje ta sanar da ammie yana son magana da dady idan yatashi bacci, yanda yace haka umma tayi sannan tadawo tana goye da little Nuraddeen tace. “Wai malan lafiya naganeka kamar cikin damuwa? Ga alama ko bacci baka samu kayi ba jiya, Kuma yau tunda sassafe kahau shiri, meke faruwa da kaine kuma Ina zakaje?” Taqare maganar damuwa kwance a fuskarta, ganin haka yasashi d’an murmusawa had’e da cewa. “Babu komai maman Rashida, zancen bacci kuwa ai bani kad’aine banyi ba….” “To naji basai ka qarasa ba, amma ina zakaje? Ko yau zamu koma.” “A’a bana tunanin haka domin idan nace zan koma banyiwa alhaji adalci ba don gaba d’aya amanar sabon shagonsa a hannuna ya damqata, zandai je kano ne Ina son in had’u da alhaji Idris akan abunda muka gani jiya dangane da iyalinsa? Kinga bai kamata ace nagani nayi shiru ba matuqar ita d’ince kamar yanda Rashida tafad’a.” “ALLAH ya kiyaye.” Umma tad’an fad’a kamar cikin jin haushi zatabar wajen. “Dakata mana, Ina Kuma zakije muna magana.?” “Ai mungama magana tunda kafad’a mani inda zakaje.” “To meya b’ata maki rai aciki maman Rashida naga zakibar wajen rai a b’ace.” “Bakya son natafi ne?” Shiru tayi batare data tanka saba tana d’an jijjiga little dake mutsu mutsu yana neman tashi, murmushi yayi don yasan dole hakan zata faru, mawuyacin abune ga uwa ta iya manta wanda ya cutar mata da d’a, musamman idan taga ana damuwa da al amarinsa alokacin da shima ya jarabtu sai taga kamar ita annuna rashin so akan nata ne da aka kasa nuna masa haka a lokacin da ake cutar dashi. STORY CONTINUES BELOW  Lumfasawa baba yayi had’e da cewa, ” kiyi haquri maman Rashida abunda zuciyarki ke tunani ba haka bane, iya sanina matuqar zamuyi koyi da mafificin halitta to bazamu rama cuta da cuta ba domin shi yakan rama cuta da alkhairi ne ga wanda yacutar dashi sannan karki manta da irin d’imbin alkhairin da d’an baiwar ALLAHn nan da mijinta suka yimani, koba komi tunda suka qaunaci ‘yarmu sunngama mana komai arayuwa.” “Amma kuma meya biyo baya malan?, Cutarwa da kuma neman salwantar mata da rayuwa, yakamata kafahimci hakan kabarsu suma da tasu jarabawar suji idan akwai dad’i, ‘yarmu aka cutar amma rad’ad’in da zafin akanmu yaqare muda muka haifeta, don haka dole suma suji irin wannan zafin alokacin da take cutuwa duk da kuwa basu ke cutuwar ba.” “Ashsha! Kada kibari ‘yarki tafiki hankali da tunani, karki manta mu da muka shiga cikin tamu jarabawar ai ba qyalemu sukayi ba, qarfinsu, lokacinsu da kuma kud’insu harma da mutuncinsu duka sunyi amfani dasu wajen nuna mana damuwa akan halin da muke ciki, shine yanzu zakice mu muwofantar dasu saboda sun zamo silar cutuwarmu data ‘yarmu?, Kiyi haquri mumanta da abunda yafaru tunda ALLAH ya maido mana da ‘yarmu duk da nasan hakan abune mai wahala amma zamu iya matuqar mukaci gama da yawan tuna alkhairansu.” Sosai jikinta yayi sanyi kuma b’acin ran da takeji akansu yad’an rage sosai, “Shikenan ALLAH yasawaqe yasa kaje lafiya kadawo lafiya.” “Amin ya rabbi, bari naje inaga kiran alhaji ne qilan yafito.” yafad’a yana ciro wayarsa dake ruri a gaban aljihu. Qarasa shiga cikin d’aki tayi shi kuma yanufi sashen ammie. Sida suka gaisa cikin girmamawa sannan yasanar dashi zancen tafiyar da yake so yayi yau, duk da ko kad’an dady baya son yayi nesa dashi haka yadaure yabashi goyon bayan yin tafiyar tare da ciro dubu goma yamiqa masa yace yayi na mota. “A’a alhaji da ka barsu wlh, akwai kud’i a hannuna sosai.” “Ai nasani, ka karb’a ni nabaka kaqara, kud’i ai basa yawa ga matafiyi.” Karb’a yayi had’e da yimasa godiya sannan yami zaifita, har yakusa kai bakin qofa alhaji ya kirasa had’e da cewa. “Am..malan bashar me zai hana kabari zuwa jibi sai mutafi tare don zanje sayo kaya, kasan duk kayan namu sunyi qasa.?” Sosa kai baba yayi had’e da cewa. “Ai da kabarshi alhaji, so nake yau ko gobe in juyo idan ALLAH ya yardar mana.” “To shikenan ALLAH yakiyaye hanya, dama nafi samun natsuwa idan kana kusa lokacin da zan tafi, don ALLAH ka gaishe mana dasu.” “In sha ALLAH zasuji mungode.” Abakin qofa sukaci karo da Dr nura yana qwalawa ammie da dady kira, kallo d’aya zakayi masa kasan cikin farinciki yake saboda wani annuri dake fita a fuskarsa, d’an sunkuyawa yayi yana sosa k’eya ya gaida baba, fad’ad’a murmushinsa yayi had’e da amsa gaisuwar daya yimasa yana fad’in. “Agaida likita bokan turai kuna lafiya?..” Bai qarasa magana ba yaga Fatima na qoqarin shigowa itama tajawo hijab d’in jikinta yarufe mata fuska, ganin yayi tarugo da gudu hango ammie nafitowa tafad’a jikinta tana kuka. “Subhanallahi.. Dr lafiya?” Baba yafad’a yana kallon Dr nura da shikam sai faman washe haqora yakeyi, gaba d’aya 34 d’insa sun kasa rufuwa, Saida ya d’an sinne kai qasa had’e da kallon Fatima ta wutsiyar ido sannan yace. “Baba lafiya klw ku qyaleta kukan dad’i ne takeyi, addu’arku da kuka dad’e kunayi ne ALLAH yakarb’a mana shine fa tunda likita yafad’a take wannan kukan.” “Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah…” Gaba d’aya falon tundaga ammie dake faman rarrashinta har baba da dady suka fad’a atare, sai alokacin Dr yaji wata irin kunya tarufesa da sauri yajuya batare daya qaraso cikin falon ba. STORY CONTINUES BELOW  Maida jiki gabas ammie tayi had’e dayin sujada hawayen farin ciki nazubo mata tace. “Lakal hamdu ala maqadait, walakash shukru ala man a dait, tabarakta ya zaljali wal ikram.” Sannan ta tofa tashafe a fuska. Dady kuwa Banda murmushi Babu abunda yakeyi, nan take yaqudurta aransa zai yiwa baba dake tsaye wata kyauta a matsayin godiyarsa ga ALLAH bisa wannan ni’imar daya yimasu duk dako ba itace ta farko ba, Hajia fareeda wato ammie itace matar dady tafarko kuma uwar gidansa tanada yara uku dashi kuma sune manyan ‘yayansa agidan, Dr nura shine babban d’ansa sai kuma qanensa faruq, saurayine Amma zaikai shekara ashirin da bakwai haka, sannan qanwarsu Khadija dake da shekaru ashirin da hud’u, tayi aure bayan shekaru uku da suka wuce bayan ta kammala karatunta a fannin lafiya wato (nursing), kuma ALLAH ya albarkaceta da samun yara biyu Shahid da Shahida idan kaganesu zaka d’auka tagwayene amma ba haka bane saboda haihuwar rurrutsa tayi, tana ilorin acan take aure saboda mijinta soja ne basu fiye zama waje d’aya ba, yau in suna wannan garin to gobe kuma suna waccan garin, wannan dalilin ne yasa dady cewa ba itace ni’ima tafarko da ALLAH yayi masu ba. Tun daga nan ammie bata sake haihuwa ba kuma hakan bai tab’a damun dady ba, acewarsa sukad’ai idan ALLAH ya raya masa sun isheshi, amma da yake ammie macece mai tsananin alkunya da kuma son mijinta ta tirsasa masa cewa dole sai yaqara aure saboda yasamu qarin zuri’a ita kanta tana sha’awar yara qanana gashi ga dukkan alamu haihuwar ta tsaya mata, don haka tayita rarrashinsa har tasamu ya amince ya auro hajia nafeesa, ‘ya ga amaninsa da suka tashi tare ya rasu yabarsu su takwas ga mahaifiyarsu, rashin wadatar da suke ciki don shi sana’ar noma yakeyi, sai gashi ALLAH yamasa rasuwa yasa dady ke tsananin tausaya masu kuma yake taimakonsu sosai, daga nan ammie tabashi shawarar ya auri nafeesar saboda hakan zai qara bashi damar taimakon ‘yan uwanta sai gashi tazamo butulu ta hanyar walaqanta duk wani dake tare dashi matuqar bayada arziqi, musamman hajia fareeda data d’auka wata maqiyiyarta aduniya. Dawowa cikin falon baba yayi fuskarsa d’auke da farinciki ya taya su hajia murna had’e da fatan ALLAH ya sauketa lafiya sannan yajuya yafita. Miqewa dady yayi shima had’e da cewa. “Dota congrat, ALLAH yakawo mana rayayyi masu albarka.” Sannn shima yajuya yafice, ammie na dariya tasa hannu ta d’ago fuskar Fatima da tayi sharkaf da hawaye tana fad’in. “Kai ‘yata wannan duk kukan farincikine ko kuma na shagwab’a ne akeyiwa ammie ankusa zama mama.” Kasa tanka mata tayi saima faman share qwallar da takeyi tana wasa da gefen hijab d’inta had’e da sissinne kai qasa, karo nafarko kenan arayuwarta data fara jin kunyar ammie irin haka, arayuwa babu abunda take b’oyewa ammie, ta d’auketa tamkar uwar data haifeta da cikinta, hatta wani abun cikin rayuwr aure idan Bata sani ba ita take tambaya tafad’a mata, haka ab’angaren kayan jiki na gyaran mata duka ammie nahad’a mata tabata kuma tayi mata bayani batare da taji kunyarta ba, sai gashi yau gaba d’aya takasa d’aga kai takalli ammie su had’a ido. Murmushi irin na manya ammie tayi had’e da cewa, “ikon ALLAH, karmuyi haka dake ‘yata, kisaki jikinki ni mahaifiyarkice don haka dena wani jin kunya akan wannan abun farinciki daya kamata muyi sharing happiness d’inmu atare, let celebrate together my dota bawani abubane, show me how much appy you feel about this, i will support you and make you enjoy it better kinji ko?.” Ahankali tad’ago kai tana kallon ammie hawaye nazubo mata afuska. “I couldn’t believe ammie, ammie ashe nima zan haihu ba juya bace ni kamar yanda ake fad’a, Ashe nima zan zama uwa am…?” Kasa qarasawa tayi sakamakon kukan farinciki da yaci qarfinta, Bata tab’a kawowa kusa cewa zata haihuba, Bata tab’a sama ranta tana da ciki ba duka da dai Bata tab’a cire tsammani da rahamar ALLAH ba, ako yaushe cikin sa rai take komai daren dad’ewa zata haihu itama in ALLAH ya yarda. STORY CONTINUES BELOW  Cike da tausayinta ammie tajawota ajiki ta rungume tana fad’in. “Ya isa haka ‘yatah, just blieve it, dama haka ALLAH yake, yakan lullub’e bayinsa da rahamarsa a lokacin da basu tab’a tsammani ba, kuma yakan dubi zukatan bayinsa da sukayi Imani dashi suka kyautata al’amurransu ya share masu hawayensu, wannan shine abunda nayita fad’a maki cewa idan lokaci yayi bazato ba tsammani zakiga abun kamar qyaftawar gira, Kuma nafad’a maki tunda dai har akece lafiyanki qalaw to kiyi haquri domin SANNU SANNU bata hana zuwa….gashi naki ALLAH yakawo ijaba har kin iso ko kuwa?” Tafad’a tana d’an turo idanuwanta kad’an tana dariya alamar tana jiran amsa. Jijjiga kai tashigayi alamar tabbatar mata da cewa hak ne ammie tace. “To mugodewa ALLAH ba kuka zakiyi ba kinji ko?, Yanzu fad’amun me kike son ci?” Rufe fuska tayi ammie nadariya tamiqe tana fad’in. “Ko zakici wainar fulawa nayi maki?” Ta girgiza kai had’e da cewa. “A’a ammie eba dai zanci.” Turo idanuwa ammaie tayi had’e da cewa. “Tofah, kice maigidan nawa d’an yarbawa ne?” Duk sukasa dariya harda Dr nura da tun d’azu ke tsaye abakin qofa yace. “Ai kuwa ammie da yaci sunan qudusu” yafad’a kamar yanda yarbawa ke kiran sunan suka sake sa dariya atare, can batare daya ankareba ammie takamo kunnensa had’e da murd’ewa tana fad’in. “Son yanzu rashin kunyarka har yakai da kanka kake fad’an ‘yata nada juna biyu kuma ka taso mani ita agaba, To Ida cikashe rashin kunyar taka ka fad’amun ko how many month ne?,” Fatima na ganin haka ta tashi tashigewarta bedroom d’in mom tana murmushi, komai na surukar tata cike yake da burgewa da kuma ban sha’awa, ko kad’an batada wata matsala komai nata tanayinsa da cikakkiyar wayewar da babu qazanta acikinta. “Awwwshhh..ammie da zafi fa.” “Nasani mana, bakai rashin kunya ba?” “Kai mom, albishir nefa nayi maku, ALLAH badon baba ba sai kun cike mani check tukuna zan fad’a, Ashe laifine nayi bansani ba, amma ita data azawa mutane kuka Ina gani sai wani lallashinta akeyi ana murmushi.” Yafad’a yana turo baki sai kace wani qaramin yaro. Murmushi tayi had’e da sakinsa tace. “Srry kaji ko son, tsantsar farincikinne har yayi mani over shiyasa nanemi regesa akanka, congrat soon zaka shiga next level arayuwa, wato mtakin zama uba bayan magidanci, ubangiji ALLAH yayi maku albarka yabamu rayayye.” “Amin ammien mu” yafad’a yana rungumeta. Baba kuwa koda yakoma sashensa acan ya tarar da Dr nura suna gaisaw da umma da Rashida yana basu labarin jiya a asibiti suka kwana saboda zazzab’in daya tasowa Fatima har saida aka qara mata ruwa, baikai ga fad’a masu zancen cikin ba baba yashigo yamiqe zai fita baba ya tsayar dashi yake sanar dashi batun tafiyar da zaiyi kano, nan take Dr yaji tafiyar bata kwanta masa ba, yayi iya qoqarinsa naganin ya hana baba tafiyar har zuwa banda gobe idan zaije wajen aiki suwuce tare amma yakafe kai da fata shidai ya barshi ya tafi ai yau zai dawo, hakan yasa babu yanda ya iya dole sukayi sallama akan idan zai tafi ya aika Rashida yakirawosa zai koma wajen ammie sai ya ajiyeshi tasha sannan yabar sashen yanajin wani irin. Baba kuwa zaunawa yayi suka sake d’an tab’a hira dasu umma yanata zolayarta wai yanzu idonta sun bud’e tadena kunyar Rashida amatsayinta na ‘yarta tafari ashe b’oyewa takeyi tana sonta sosai sunata dariya. Daga nan kuma yajuya akalar firar tasu izuwa yimasu nasiha akan rayuwar duniya sai kace wanda akace idan yatafi bazai dawo ba, bayan yagama umma tayi ajiyar zuciya had’e da cewa. STORY CONTINUES BELOW  “Malan nifa duk jikina yamutu wlh, nidai don ALLAH kabar zancen tafiyarnan har zuwa wani lokacin.” Murmushi yayi had’e da cewa “Karki manta sau da yawa bama son abu sai kiga ALLAH yasanya alkhairi sosai acikinsa, kika San alkhairan da wannan tafiyar zata jawo mana, qilama ‘yar qanwa zan samomaki shiyasa duk kikabi kika tada hankalinki akanta.” Yaqarasa maganar cikin sigar zolaya yana dariya had’e da miqewa yana d’auke da litte, “Rana nayi bari na hanzarta yau nake son nadawo in sha ALLAH, Rashida jeki kikira Dr ni kam nad’au harma.” Gaban Rashida ne taji yafad’i da sauri tace. “Baba kayi haquri kuwuce da uncle banda gobe.” “Ikon ALLAH, har dake Rashida? Bakyason sanin halin da mijinki da surukarki suke ciki halan?” “A’a baba, ni kawai…” Saurin dakatar da ita yayi tahanyar cewa “maza jeki kice Ina jiransa.” Har takusa fita yakira sunanta had’e da cewa. “Dawo nayi maku albishir ni namanta, maman Rashida matar Dr fa tasamu qaruwa.” “Da gaske baba?” Rashida tafad’a cike da farinciki tare da ficewa da kad’an ma tafad’i garin sauri, umma kuwa Alhamdulillah tace tana fad’in “ALLAHU AKBAR, ALLAH maji roqon bayinsa, kai madalla bari naje nataya hajia murna.” Kusan tare da ita suka fita yana maijin wani sanyi aransa saboda yanayin farincikin da yaga ya bayyana a fuskarsu wanda hakn baqaramin tasiri yayi ba wajen qara masa natsuwa azuciya….. _Godiya agareku masoya masu karamci da halacci bisa bibiyar lafiyata da kukayi, nagode sosai ALLAH yabar tare, maman ameera da ummu sauda ban manta daku ba, kunnuna kulawa agareni kuma jazakumullahu bikhair, fatan alkhairi aduk inda kuke👍🏻_ *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___67💎 Da gudu Rashida tashiga part d’in ammie tana kiran fatima. “Aunty, aunty..” da kad’an sunyi karo da ammie dake qoqarin shiga kitchen, d’an ja da baya tayi cike da farinciki kafin tasake matsowa kusa da ita tarungumeta tana fad’in, “Ammie kitayamu murna auntynah zata haihu.” Murmushi ammie tayi cike da mamakin irin sakewar da Rashida tayi dasu tsakanin jiya da yau sab’anin yanayin da take ganinta abaya, tabbasa iyaye wani jigone da rashinsu kan kawowa ‘ya’ya tawaya maigirma arayuwa, “Iyyeeeeee….to ina tayaku murana kice little yakusa zama big zai samu d’an qane..” Ko qarasa maganar ammie batayi ba Rashida ta saketa tanufi bedroom d’in ummie don tasan tana ciki tunda bata ganeta a falo ba, girgiza kai ammie tayi tana kallon Dr nura da yabi Rashida da kallo cike da mamakin tsantsar farincikin da yaga tashiga, juyowa yayi suka had’a ido da ammie yace. “Gaba d’aya ta canza tsakanin jiya da yau, kinga farincikin dake tattare da ita ammie sai kace wacce aa biyawa makka.” “Haba son!, ai dole tayi farinciki, iyaye fa rahamana sosai ga kuma wannan batun data tsinta alokaci d’aya, matuqar ita d’in masoyiyar kuce dole kaga fiye da wannan farincikin atattare da ita, ni yarinyar na burgeni sosai saboda sanin yakamatar ta” STORY CONTINUES BELOW  “Ehm..gaskiya hakane, Rashida kam akwai hankali.” Da gudunta taqarasa shiga cikin d’akin tafad’a jikin fatima dake zaune bakin gado ta tallafe fuskarta da tafin hannuwanta guiwowinsu na akan cinainanta. “Yeeew…auntay na congrat, agaskiya Ina cikin farinciki marar misaltuwa ayau, bayan duk wasu fad’i tashi da suruttan mutane yau ALLAH zai bamu namu d’an, Ina farinciki sosai auntynah ALLAH ya inganta yaraba lafiya.” Duk wannan surutun da Rashida keyi cikin farinciki Babu abunda Fatima keyi in banda kallonta, d’aga mata idanuwa Rashida tayi tana juya hannunta had’e da cewa. “Me akayi ne aunty?” Rungumeta tayi tajawo hannunta ta d’ora akan cikinta tana fad’in. “Maman boy I can’t believe so soon zan haifa maki baby, thank you so much for supporting me, haqiqa babu abunda yakai qarfin addu’a tasiri arayuwa, nagode bisa addu’o’in da kika d’orani akai da kuma wud’anda kikeyi mani ba dare ba rana, tabbas anasamun warakar kowace irin matsala tahanyar jajir cewa dayin addu’a, ALLAH ne yace anemi maganin kowace irin matsala amma ana samun warakane bisa qarfin addu’o’inmu agaresa, maman boy kinzamo wani haske acikin rayuwarmu da bazamu tab’a iya mantawa dake ba, yanda kika faranta mana kema ina roqon ALLAH daya faranta maki acikin dukkanin lamurrank, Ina miki albishir da cewa idan ALLAH ya saukeni lafiya zamuyi maki takwara da yardar ALLAH idan aka samu macce, wannan shine tukuicin zamowarki sila wajen tsaida hawayen da muka dad’e suna yimana kwaranya a idanuwa.” Taqarasa maganar had’e da riqo hannayen Rashida ta d’ora saman idanuwanta dake fitar da qwalla. “Kai aunty meye haka kikeyi?, Haba ya isa kidena wud’an maganganun don ALLAH, dukkaninmu ALLAH yakamata mumiqa godiyarmu agaresa, inada tabbin dama lokacin da zaki haihu yayi koda kuwa banbaki wud’an nan addu’o’inba, kawai sun zamo silane bisa wanzuwar qudurar ALLAH agareki, don haka kidena damuwa akan wannan, koda babuni acikin rayuwarku zaki haihu kamar yanda ALLAH ya tsaro, ita addu’a da kike gani ai makami ce babba da idan bawa yariqa duk nisan lokaci zai riskesa da yardar ALLAH.” “Zancen yimani takwara kuwa ALLAH ban yarda ba, sunan yazama local, ni kaina dariyarsa nakeyi wani lokaci.” “Commonnnn…” Fatima tafad’a tare dakai mata d’an duka agefen hannu tanaci gaba da cewa. “Waya fad’a maki sunanki local name ne, ai sunan Rashida da kike gani sunane mai girma, is drive from the one names of ALLAH dt’s (AL-RASHID), Ma’ana mai shiryarwa, asalin sunan ubangijine sai akayi amfani dashi ta hanyar qara harafin (a) yazama (RASHIDA) sai ma’anarsa ta tashi daga Mai shiryarwa zuwa shiryayyiya, don haka kiyi alfahari da sunnki akoda yaushe, domin sunane da bazai kusuba ga wud’anda sukasan asalin ma’anar inda aka ciro sunan, hikimace kansa iyaye nasakawa ‘ya’yayensu ire iren wud’annan sunayen saboda fatan ma’anar dake tattare dasu tad’ore akan ‘ya’yan masu.” “Laaa…kinsan ALLAH aunty! Hankalina bai tab’a kawomun wannan tunanin araina ba, atak’aice ma mantawa nakeyi da akwai sunan acikin jerin sunayen ALLAH da har zan iya tsinkayo ma’anar dake tattare da sunan nawa, kawai nidai tunda banji ana yayin sakawa jarirai sunan ba to sunan dane agurina, d’ai d’ai kune acikin yaran dake tasowa nake ji da irin wannan sunan, amma yanzu tunda kinfahimtar dani ma’anarsa da inda aka samo asalinsa Ina alfaharin kasantuwa ta da sunanan RASHIDA.” Gyaran murya ammie tayi abkin qofa tana fad’in. “Agaida qanwar aunty, dama aikoki baban naki yayi shine kikazo kikayi zaunenki?” “Laaa…. ALLAH na manta ammie, bari naje nafad’a ma uncle.” “Zauna abunki, ai ummanki data shigo tayamu murna tafad’a masa gashican har yafita.” “ALLAH shaf ni namanta sai yanzu bari naje nabashi haquri daga nan nayi masa ALLAH yakiyaye.” Tana gama fad’ar haka tamiqe tafita, ammie tace, STORY CONTINUES BELOW  “Kinga mutuniyarki tasaki jikinta sosai yanzu ko?” “Eh wlh ammie kuma naji dad’in hakan sosai, kinga kafin sutafi zata qara koyamun wasu addu’o’i sosai.” “Wlh ammie tun watan da kika aikamun da wannan ganyen guava kikace mudinga sakawa cikin ruwan tea muna tafasawa muna sha kafin muci komai da safe tun alokacin nafara jin canji da kaina ajikina, ranar muna zaune nida ita sai take cemun akwai wasu addu’o’i acikin alqaur’ani da yakamata na dingayi wud’an annabawan ALLAH sukayi da bai basu haihuwa ba kuma daga baya yabasu, hakan zai taimaka wajen sanya maganin duk da nake amfani dashi yayi tasiri ajikina sosai saboda qarfin addu’a, ammie kamar da wasa ta nunnuna manisu acikin alqur’ani nafarayi, yanzu kimanin watanni biyar inyinsu kenan sai gashi cikin yardar ALLAH ijaba tasauka, tabbas ammie ilimi nada dad’i aduniya kuma yawane dashi da bazaya tab’a qarewa ba sai randa bawa yakoma ga mahaliccinsa, Kuma duk yanda kake taqama dashi sai kaga wanda yafika shi.” “Dama hakane ‘yata, koda kuwa wanda baikai darajarka bane ko kuma yafika zakaga yasan wani abun dakai baka sani ba, duk da nasan wasu daga cikin addu’o’in ‘yata kifad’a mani sauran naji domin inada wata qawa yanzu kusan shekaru talatin kenan bta haihu ba, kuma tana matuqar son haihuwar kamar taqwato, babu gwaje gwajen da batayi ba, qasashen waje kuwa sunje ba iyaka amma har yau ba’a dace ba, kuma duk da hakan bata gaji ba har yanzu tana kan neman magani cike dasa ran wata rana zata dace, zanji matuqar dad’i idan tasamu irin wannan farincikin da ayau muke ciki kuma hakn zaisa nayi alfaharin tarayyata da ita nahar abada.” “Ai kuwa ammie bari nafad’a maki don gab d’aya nahardace su akai, ba ita kad’ai ba, ina fatar duk wanda kecikin irin wannan matsalar ya amfana dasu domin samun waraka kusa kusa matuqar zai dage dayinsu cike da yaqinin ALLAH zai amsa masa.” “To bara nad’auko biro da takarda narubuta ‘yata, kinsan qwaqwalwar taku da tamu yanzu ba d’aiba.” Takarda ammie ta d’auko Fatima tafara karanto mata addu’o’in daki daki kamar haka. ( _Rabbi laatazarni fardan wa’anta khairul warithiyn,_) ( _Rabbana hablana min azwajina, wazurriyaatina, qurrata a’ayunin, waja’alna lil muttaqina imama_) ( _Lillahi mulkussamawati wal’ardi, yakhluqu maa yasha’u, yahabu liman yashaa’u inasan, wayahabu liman yashaa’uzxukur.._) ( _Rabbi habliey minladunka zurriyatan d’ayyibatan, innaka sami’uddu’ah_) ( _Wa’inni khiftul mawaliya minw waraa’i wakanatimra’atiy aaqiran fahabliey minlladunka waliyya_.) ( _wayumdidkum bi amwalin wabanieyn.._) ( _wamaa tahmilu min unsaa wala tada’u illa bi ilmihi.._) ( _izhaa qada amraan fa’innama yaqulu lahu kun fayakuun.._) ( _qala kazalika qala rabbuka huwa alayya hayyinun waqad khalaqtuka min qablu walam taku shai’a_) ( _Yaa zakariyya Inna nubashshiruka bigulaminismuhu yahya lam naj’allahu min qablu samiyya_) ( _Rabbi habli minasswalihieyyn_). ‘Dago kai ammie tayi had’e da cewa. “‘yatah har yanzu addu’o’in basu qareba, naga har nacika takardar nan.?” Saida Fatima tayi dariya sannan tace. “Dayawa ko ammie?, Ai dama mai bid’a dole sai ya daure, balle ace d’an mutum kake so ai Dole sai an nace kuma anjajirce kafin akai ga gaci, ni ada nake ganin yawan addu’o’in amma daga baya da ALLAH yataimakeni na haddace wasu wasu kuma ina dubawa ga takardar dat rubuta mani wallahi sai nadena jin wahalarsu, kinsan ammie abun sa kaine, idan kad’auka da sauqi sai yazo maka cikin sauqi, duk yawannan nasu da kike gani idan natashi da daddare nayi raka’a biyu na sallame nakan maimaitasu fiye da sau goma wani lokacin kuma nakanyi ko sau d’ayane bayan nayi istigfari da washi zuwa ga ubangiji sannan nayiwa annabi salati tare dayiwa ALLAH godiya bisa wasu ni’imomin da yayi mana nadaban. Idan na kammala sai nakoma bacci, wani lokacin tare ma dashi mukeyi gaba d’aya idan anyi sallar asuba rana tafito sannan mukoma bacci, wani lokacin ammie ko sallarma bamayi, arwala kad’ai mukeyi muzauna muna bitar addu’o’in har bacci yana d’an fizgarmu wani lokaci.” STORY CONTINUES BELOW  “Tirqashi! Tabbas ‘yata kunkoma ga Wanda kad’ai ya isa yabaku kuma yabaku, ubangiji ALLAH ya inganta yabaki rayayyi masu albarka, albarkacin miqa wuyan da kukayi agaresa.” “Amin ammie nagode.” ‘Dan hararta ammie tayi akn godiyar data yimata, dariya tayi had’e da cewa. “Natuba ammienmu kiyi haquri.” “Shikenan, ammafa kada kiqara.” “Baran qara ba ammie..” “Shikenan addu’o’in nakirata taturo akarb’ar mata?” “Eh ammie, tun yanzu Zaki aika mata?.” “Eh mana, ai qara abugi qarfe da zafinsa.” “To ammie ALLAH yasa adace, Amma ammie kice tayi duka addu’o’in cike da yaqinin cewa ALLAH zai karb’a mata, kinsan yana d’aya daga cikin abubuwan da kesa ubangiji ya gaggauta amsar addu’ar bawa idan yayita da yaqini.” “Ai zama tayi ‘yata saboda akullum batada burin da yafi wannan, kinga kuwa dole zata dage, bari naje nadubo maki abinda kikace kina so.” Ammie tafad’a tare da linke takardar ta ajiye akan madubi sannan tabar d’akin, miqewa tayi had’e da shafa cikin nata dako motsi bai fara ba tayi murmushi, gaba d’aya ganin ranar takeyi kamar mafarkine takeyi sannan itama tabi bayan ammien. Rashida kuwa koda ta isa baba na qoqarin shiga mota har lokacin little na ahannunsa, qarasawa tayi wajen baba yamiqo matashi, har tamiqa hannu zata karb’esa cike da zolaya yaja baya dashi yana fad’in. “Bazaki bari naje dashi ba nakaishi wajen kakansa, nasan zaiji dad’in ganinsa fiye da irin dad’in da mukaji.” Murmushi Rashida tayi had’e da cewa. “Shikenan baba, kaga nida ummata dasu ammie mun huta da fitinarsa, sai yaje can yad’an tab’awasu baffa da inna Bilkisu suji yanda mukaji.” “Wai hakane mai sunan babansa?.” Baba yafad’a yana kallon little dake faman tafi da hannuwa yana kallonta, dama Dr nura naganin taqaraso wajen yad’an basu waje yana amsa waya, maida kallonsa baba yayi ga Dr da har lokacin wayar yakeyi ya basu baya sannan yace. “Rashida don ALLAH ku kula da bayin ALLAHn nan, mutanene masu karamci da halacci, duk abunda suke so kufisu sonshi wanda kuma basa so to kifisu qinsa, inaso kiriqesu tamkar mu da muka haifeki kuma ki kyautata masu iya qarfinki hakan zaisa kirage wata kunyar hidimar da suka yimana kinji ko.?” “In Sha ALLAH baba, ALLAH yasa kaje lafiya kadawo lafiya.” “Amin ya rabbi, ALLAH yayi maki albarka dake da duka zuriar da zai baki.” Yaqare maganar yana shafa kan little had’e da miqa mata shi yana murmushi. A daidai lokacin Dr yadawo fuskarsa cike da walwala ya shafa kan little had’e da cewa. “Takwara nazata dakai baba zaije?” “Yawwa uncle don ALLAH kuje dashi shima yarakashi.” Karb’arsa yayi yayi sannan yashiga cikin motar yarufe gambun yana qoqarin tada motar tace. “Laaa…uncle congrat, little yakusa samun qane, ALLAH ya inganta uncle yabamu rayayye mai albarka nima narama abunda ake yimani akan d’an wasu.” Batare daya kalleta ba yana key d’in motar yace. “Amin ya rabbi, Thank you so much maman baby, amma ko kunrama bazaku iya ramawa ba kamar yanda muka yimaku ba ko takwarana?” Da haka yatada motar had’e dayin ribas ya juya motar suka fara tafiya, binsu tayi tana d’agama baba hannu shima yana d’ago mata har suka fita, haka kurum saita tsinci kanta da fashewa da kukan da batasan dalilin yinsa ba, Saida ta tsaida kukan sannan tajuya tanufi sashen na ammie, umma tahango jikin qofa tsaye itama taqurawa gate d’in idanuwa tana mai addu’ar ALLAH ya saukeshi lafiya, STORY CONTINUES BELOW  “Umma ya nagaki a nan tsaye?” Rashida tafad’a jikinta ba qwari. “Wlh Rashida nidai tafiyannan tashi bata kwantamun ba, daya bari har sai an kwan biyu tukuna tunda muma jiyan nan muka fita alhinin rashinki.?” “Kai umma, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH zaije lafiya kuma yadawo lafiya.” Rashida tafad’i hakan saboda takwantarwa da umma hankali don ita kanta tanajin ba dad’i akan tafiyar tasa. Dr nura bai baro tasha ba har saida yaga motarsu baba nashirin tashi sannan yanufi inda motarsa take, da sauri yajuyo ya tsaida motar had’e da leqawa tagefen tagar da baba yake yace. “Baba akwai waya a hannunka nasa maka lambata idan ka isa saika sanar damu don hankalinmu ya kwanta.” “Likita kenan! ai inada lambarka tun satin can da alhaji yasaya mani wayar ya saka mani ita, in Sha ALLAH da zaran na isa zankiraku.” “To shiken baba, amma ka kirani sai inga lambar taka nayi saving tunda banida ita.” Nanfa fasinjoji suka fara suruttai suna qorafi akan suna b’ata masu lokaci amma kota kansu Dr baibi ba har saida baba yakirasa yaga lambar sannan yabar wajen, Saida yaga motar tasu tawuce sannan shima yaja tasa ya nufi gida. Ba’afi mintuna talatin da isar Dr gida ba saiga kira ya shigo ga wayarsa, lokacin duk suna zaune kan dining table suna lunch yana faman jinini wai ammie tabiyewa Fatima anyi masu eba kuma shi baya sonta, ita kuma ammie tace dole yacita don ita kad’ai tadafa kuma bazaibar gidan da yunwa ba, hakan yasashi tusa abincin yana wani b’ab’b’ata rai da kumbura fuska sunata yimasa dariya, ganin wayar tasa naruri yaqi d’agawa yasa dady tsaida dariyar tasa had’e da cewa. “Sorry son, qyale dota da ammienka, zamu rama kaji ko.” “ALLAH dady babincinnan na garin kwaki bayada dad’i ko kad’an, ci kawai nakeyi badon Ina so ba.” “Ajiye hakanan, kad’aga wayar da akeyi maka tun d’azu.” Kallon wayar tasa dake famn ruri akaro na uku yayi had’e da qoqarin d’agawa yana fad’in. “Kai, Ashe baba ne ke kira tun d’azu, Assalamu alaikum, Eh nine, eh, yanzunnan fa ta tashi” “What?” Yafad’a da qarfi yana turo idanuwansa had’e da miqewa da qarfi. Hakan yasa su dady sakin cokullan dake hannunsu suna kallonsa. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun.” Shine abunda Dr keta nanatawa kafin yakalli dady dake tambayarsa ko lafiya yace “Dady wai motarsu babace tayi had’ari acan qauyen dake kan hanya idan anfita gari kad’an.” Gaba d’aya sukasa sallami da sauri ammie tariqo hannun Fatima tayi d’aki da ita had’e da kwantar da ita kan gado tace. “‘yata kinkwantar da hankalinki, kinsn yaron ciki kejikinki in sha ALLAH Babu abunda yafaru.” Koda ammie tafito har dady da Dr sun fita. Sallallami tashigayi tana zagayar falo batare da tasan mezata aikata ba alokacin. Gaba d’aya su dady basuyi wta doguwar tafiya ba suka cimma inda akayi had’arin ashe suna fita daga cikin garinne sukayi karo da wata qaramar mota garin drivern ya kauce mata motarsu tayi cikin daji takife, kasancewar lambar Dr nura itace ta qarshe da baba yakira yasa lokacin da aka ciccirosu aka sami wayar ajikin baba da ko qwarzane baiyi ba amma rai yayi halinsa, kallo d’aya zaka yiwa gawarsa kasan mutumen kirkine saboda wani irin haske da qyalqyali da fuskarsa kefitarwa. Suna isa suka isko an jejjere gawarwakinsu agefen titi da sauri suka isa wajen, tsabar yanda hankalin dady ya tashi saida jiri yad’ebesa yayi baya baya zai fad’i Dr ya tarosa, gefe ya zaunar dashi sannan yanufi wajen ‘yan sandan dake tsaitsaye suna korar mutane yayi masu bayani tare da nuna masu gawar baba dake kwance an lullub’a masa ganyen bedi akai ya nuna masu i.d card d’insa ta asibiti, suna tsaye motar asibiti ta iso aka kwashi gawawwakin kusan mutun uku wud’anda suka rasu biyar kuma sun samu raunuka, bayan motar su dady sukabi zuwa asibiti akayi ‘yan bincike binciken da za’ayi ma gawawwakin da zai tabbatar da cewa mamatan sun rasu sukuma wud’anda suka jimu akayi masu treatment sannan akabasu dady gawar baba sukayo gida da ita, STORY CONTINUES BELOW  Baqaramin tashin hankali su baba balarabe suka shiga ba lokacin da saqon rasuwar d’an uwan nasu ya isa garesuba, yayinda Yaya Maryam tadinga sabbatu tana fad’in. “Ba gaskiya bane, jiya mungansa, munhad’u dashi, munyi magana, mun yi fira da maganganu masu tsayi dashi, wara haka duk muna tare dashi taya za’ace yamutu, inaa banyarda ba, bashar bazi mutu yanzu ba bayan jiya jiya muna tare dashi, ya ALLAH kasa wannan zancen ba gaskiya bane, bashar mutumen kirkine, baikamata ace yamutu yanzu ba..” haka tayita sabbatu tana kuka har saida aka dinga rufe mata baki. Nan take baba balarabe da mijin yaya Maryam da wasu ‘yan uwansa sukayi mota d’aya babba suka d’auki hanya cike da alhini. Duk da baba baifi shekara d’aya da watanni acikin garin borno ba babu inda mutuwarsa Bata kaiba, kuma duk wanda yab’ud’a baki fad’ar mutuncinsa da alkhairansa yakeyi, Umma kuwa da Rashida gaba d’aya sun fita hayyacinsu saboda sumar da sukayi, koda suka farfad’o itadai Rashida bata cewa komai si hawaye dake zubar mata tana kallon ammie da Fatima dake faman basu baki. Umma kuwa miqewa tayi tace akaita inda gawarsa take tana so taganesa, rirriqeta ammie da maqwabtanta da suka shigo sukayi suna fad’in don ALLAH tayi haquri kada take, ganin haka yasa Rashida tasowa tace. “Ammie don ALLAH kubarta taje.” Matsowa tayi takama hannun umma tace “Umma zaki iya ganinsa.” Kad’a mata kai tayi tariqe hannunta suka nufi wani d’aki dake gefen sashen ammie da alama d’aya daga cikin d’akunan dasu Dr sukayi zamane, suna kawowa zasu shiga faruq qanen dr yahanasu. “Don ALLAH kuyi haquri idan bazaku iya ba.” yana qara tare bakin qofar idanuwansa cike da qwalla, duk da shi bai fiye shiga shirgin mutane ba saboda haka yake kamar yanajin warin mutane shiyasa baya mu’amala da kowa, amma duk da haka yana mauqar shiri da baba sosai don acewarsa shi mutumne nadaban ko acikin mutane, tasowa Dr yayi yasa hannu yajaye faruq gefe yana fad’in “Umma kushiga matuqar hakan zai rage maku rad’ad’i arai, saidai Ina so kutuna, ba’ayiwa mamaci kuka irin na jahiliya balle ga irin baba da mukeyiwa kyakkyawan zaton cewa ya dace.” Yana gama fad’ar haka haka yad’an ja da baya yabasu hanya yana goge hawayensa, suna shiga sukaga baba kwance anlullub’esa, da sauri Rashida tarirriqe umma tana kuka tare da toshe bakinta. Duqawa umma tayi daidai fuskarsa tayaye lulub’in da aka rufa masa, ayanda taga fuskarsa tayi haske yaqara kyau tamkar yana dariya duk da tana cikin rad’ad’in mutuwarsa yasa tayi farinciki sosai. “Alhamdulillah malan, naji dad’in yanayin dana ganeka aciki, inafatar wannan qanwar dakace zaka samo mani tayimaka kyakkyawar tarba da kulawa kafin na iskoka, tsakanina dakai babu komai sai alkhairi idan ma kuma katab’a yimani wani abun nayafe maka duniya da lahira inafatar kaima baka tafi dani da komai acikin ranka ba kuma ina roqon ALLAH daya tsarowa rayuwarmu haka akan wannan bawa naka daka jiqansa da rahama, kagafarta masa ka amintar da rouhinsa.” Rashida ta amsa da amin. Tana gama fad’ar haka tagoge hawayen idanuwanta sannan tamiqe suka fito, ayanayin da tafito kad’ai idan ka kalleta zaka tabbatar da cewa tagamsu da yanda taga mijin nata kuma tana yimasa kyakkyawan zato.. _karku manta mutuwa wajibice ga duk wanda keraye, azahiri ma idan munyi tunani soyayyarmu ko kuma qiyayarmu ga wata rayuwa bazata hana idan lokacinsa yayi ba ALLAH yakarb’i abunsa balle littafi, dayawan lokuta ALLAH yafi karb’e mana mutanen kirki aduniya fiye da na banza, da son samune nafiso baffa Ali yamutu fiye da baba amma ayanayin labarin mutuwar baba kad’aice zata haifar da rabuwar da Nuraddeen yayi da mahaifinsa har ya girma kamar yanda kuka gani a farkon littafi, Amma matuqar yana raye dattakonsa bazai bari hakan tafaru ba, don haka kuyi haquri da yanda labarin yake plzzz, ALLAH YAJIQAN BABA DA RAHAMA_👏 Saida ‘yan uwan baba suka iso sannan akayimasa wanka aka sallaci gawarsa aka kaishi gidansa nagaskiya, a yanda mutane suka taru sukayi dandazo wajen sallar jana’izarsa kai ka dauka wani riqaqqen mai mulkine ko sarauta ko kuma wani hamshaqin malami, ALLAHU AKBAR, shiyasa akoda yaushe akeson mutum yazama mai sanyin hali da kyautata zamantakewa dtsakaninsa da mutane, duk da baba ba d’an asalin mazaunin cikin garin bane, kyakkyawan halayensa sun biyosa har zuwa qasarsa inda aka rufesa, bayada wani tarin arziqi kuma bai kasance wani sananne ba acikin garin da shekara d’aya kacal yayi acikinsa amma soyayyarsa ga ALLAH da kuma kyautata zaman takewarsa ga mutane yasa ubangijinsa ya soshi kuma yasa al’ummah ta soshi, babban abunda zaisa a kyautata masa zato shine yanda ruwa ke bulbulowa awajen haqar kabarinsa, har kusan sau biyu ana canza masa wani kabarin amma kowane aka haqo haka ake riskarsa, a dole aka d’aukesa akasashi hakanan acikinsu mutane namasu yabawa da ni’imarsa da ALLAH yayi masa tun akabari, duk inda kaduba cikin maqabartar cike yake da mutane ta ko ina da sukazo kawosa. Bayan andawo su baba balarabe sukaje sukaa yimasu umma nasiha akan sud’au haquri da tsarin qaddarar da ALLAH yayi masu akan d’an uwan nasu domin yanda yasamu jama’a suna kyautata masa zato had’e da yima junansu gaisuwa. Kwanan su baba balarabe uku sannan suka fara maganar komawarsu tunda anyi masa addu’ar uku, lokacin da sukaje wajen dady yimasa sallama akan zasu tafi kuma suna son suwuce da iyalan marigayin tunda dama shine jigonsu nazama garin kuma ALLAH yakarb’i abunsa sai dady yayi gyaran murya had’e da sake yimasu gaisuwar rashin d’an uwan nasu akaro na ba adadi sannan yace. “Malan balarabe Ina son in roqeki wata alfarma awajenku idan zaku iya” “Munaji alhaji ALLAH yasa batafi qarfinmu ba.” “Eh to! Banace haka ba amma Ina son ne idan har kun amince kubar iyalan marigayi anan har zuwa lokacin da zata gama takaba, nayi maku alqawarin cewa zan kula maku dasu bisa amana har zuwa lokacin idan ALLAH yabamu aron rayuwa.” Shiru baba balarabe yayi kafin yace to yabari sud’an shawarta tsakaninsa da sauran ‘yan uwansa da suka zo tare, hakan yasa dady miqewa shida dr sukabar d’akin, bayan sun fita baba balarabe ya tambayi ‘yan uwan nasa had’e da kirawo Yaya Maryam da aunty marwiyya dake can shiyar ammie da yake suma wan saheken rasuwar suka iso suda matan baba balarabe sannan yasa aka kirawo suma su umma sukayi shawara, nan take kowa ya amince da hakan don alkhairin da yayi masu bazasu iya hanasa wannan ‘yar qanqanuwar alfarmar ba, umma kuwa dama cewa tayi duk shawarar da suka yanke akai tayi daidai batada ja, don haka koda suka nuna amincewar tazauna d’in batayi musu akaiba asalima yanzu tafijin garin aranta saboda mijinta dake ciki fiye da wancan garin da suka baro, gaba d’aya yafice mata arai batada sauran sha’awar komawa cikinsa. Sosai dady yaji dad’in amincewarsu da buqatarsa yayita yimasu godiya tare da fatan ALLAH ya saukesu lafiya, har bakin motocinsu gida biyu dake wajen gate yarakasu sannan suka wuce shi kuma yadawo gida yana mai jinjinawa qoqarinsu akan amincin da suka bashi. ••• ••• ••• Baffa da baffa Usman kuwa basusan abunda kefaruwa ba har akayi zaman ukkun baba basuda labari akan rasuwar tasa sai bayan kusan sati biyu sannan suka sani, baffa yayi kuka sosai akan mutuwar aminin nasa wanda d’an uwansa yakasa sanar dashi saboda wata ‘yar rashin fahimta data shiga tsakaninsu, babu abunda yafi qona masa rai irin ace ALLAH yasa har ansan inda suka tafi amma akaqi sanar dashi har ta ALLAH ta faru akansa, yamatuqar jin zafi da Kuma rad’ad’i azuciyarsa fiye da abubuwan da suka faru abaya, hakan yasa yaqudurce aransa bazaya koma waiwayarsu baba balarabe ba akan maganar da tasa suka yanke ganawa tsakaninsa da aminin nasa idan har suna tunanin hakan tafarune da son ransa ko kuma da had’in bakinsa har sai lokacin da ubangiji yatashi bayyanar da gaskiyar al-amarin, duk da wannan matakin daya d’auka hakan bai hanashi had’a waau daga cikin ‘yan uwansa mata ba da wasu abokanansa da ‘yan uwansa maza kusan mota biyu sukaje har gida suka yowa baba balarabe gaisuwa, aranar baba balarabe yaji kunyar da bai tab’a jiba aduniya, so yake yakeb’ance da baffa suyi magana amma tsananin b’acin ran dake zuciyar baffa yasa ko bari bayayi su had’a ido dashi balle suyi wata magana, gaisuwa dai ce takawosa kuma yayi masa fatanshi d’aya ALLAH yajiqan aminin nasa kuma ya lullub’esa da rahama, haka sukabar gidan batare daya samu keb’ewa dashi ba ko kad’an, wannan abun yaqara saka baba balarabe cikin nadama da dana sanin abunda yayi don yatabbata shima baffa yayi fushi akan zancen rasuwar da ba’a sanar dasu ba, STORY CONTINUES BELOW  Su baffa nafita nan suka nufi gidan Yaya Maryam da aunty marwiyya suka yomasu gaisuwa, nanma baffa bai nuna masu komaiba banda gaisuwar da sukaje yimasu ba sannan suka koma gida. Suna isa gida baffa yanemi waje yakwanta sboda wani irin zazzab’i daya rufesa, kallonsa matarsa nusaiba tayi had’e da cewa. “Baffa don ALLAH kafidda damuwar wannan abun aranka, karka manta duka mai rai mamacine, koda kasan da maganar ganinsu bazaka iya hana mutuwarsa ba tunda lokaci yayi, haka kuma koda ansanar dakai zancen rasuwarsa dawuri bazaka iya canza komai ba akan abunda yafaru, don haka kayi haquri muma nan duk ita muke jira, babu wanda kezuwa har sai lokacinsa yayi, su day suka tafi basuyi gaggawa ba mukuma da bamu tafi ba bamuyi jinkiri ba, ubangiji ALLAH kasa muyi kyakkyawan qarshe.” “Amin.” baffa yafad’a yana kallon d’an qaramin cikin dake jikinta yataso kad’an, murmushin da yafi kuka ciwo yayi yanajin wani irin zugi aransa, anan yaqudurta azuciyarsa idan ALLAH yasauketa lafiya matuqar namiji tahaifa zaiyiwa aminin nasa takwara, ganin yanda takafesa da idanuwa kamar zatayi kuka tana fad’in. “Baffa kayi haquri kaji.” Don haka take kiransa har yanzu, yayi yayi da ita tadena amma taqi, hakan yasa yaqaqaro murmushin qarfin hali had’e da cewa. “Nusaiba to me akayi naga kina b’ata fuska, ai dole nahaqura tunda yariga ya tafiyarsa, amma inajin rad’ad’in rabuwata dashi sosai,” “To kayi masa addu’a,” “Zanyi masa nusaiba amma kema zakiyi masa takwara idan kika haifi namiji?” Cike da yarinta tasa hannuwa tarufe fuskarta, don har lokacin bata cika shekaru goma sha shida ba aduniya kuma ALLAH ya albarkaceta da samun ciki wata hud’u kenan ynzu da kwanaki, yana matuqar jin dad’in zama da ita duk da zamowarta yarinya da mafiya al-amurranta shirme sunfi yawa, amma takan nuna damuwarta aduk lokacin data ganesa cikin damuwa kuma tana bashi kulawa daidai iya qarfinta naqaramar yarinya dad’in dad’awa ma ladabi da biyayyar da take yimasa badon ‘yan matsalolin dake tattare dashiba dake hanasa samun cikakkiyara natsuwa da yace gaba d’aya bai tab’ajin dad’in rayuwar aure ba sai yanzu, qaramar yarinyace mma tanada kiyayewa sosai wajen iya zama da miji bisa turbar da yake koyar da ita, hakan yasa duk yanda damuwa tayi masa yawa idan yaga hakan zai haifar da tasirinta wajen cutar da yarinyar yake dannewa, hakan yayiko yanzu yadanne duk abunda yakeji yashiga zolayarta tana dariya. Bayan kwana biyu baffa yaje can gidansu baffa Usman ya isko ‘yan sanda sunyi cirko cirko aqofar gidan wai zasu kama muneera akan tafasama wani saurayi dutsi a ijiya har saida ta tsiyaye gaba d’aya. Inspector najida yagani a tsaye jikin motar fuskarta ba walwala tana jira ashiga akamo muneerar, wajenta yanufa tana ganinsa tasaki fuskarta had’e da qarasawa wajensa kafin ya iso, d’an russuna kai tayi tagaishesa had’e da cewa. “Baba ya gida ya kwana biyu?” “Alhamdulillah ‘yata injin dai ko lafiya?.” “Lafiya lau baba, yaron kune yafasawa wani ijiya shine aka kaimana qararsa.” “Subhanallahi wakenan.” “Muneera baba, yarinyar nan batajin magana sau biyu kenan ana kaimana case d’inta amma saboda kai sai nasa asulhunta abun, amma awannan karon dole mukai case d’in kotu.” “Haba ‘yatah, don ALLAH karkice haka ai shi taimako ba’a gajiya dayinsa.” “A’a baba! Haka ya isa batajin magana da yawa, koda zamuyi wani abun dole sai munje kotu da ita.” “Shikenan!, ‘yatah ALLAH ya kyauta, zamu biyo bayanku in Sha ALLAH muji yanda za’ayi.” Har inspector najida tajuya zata tafi sai kuma tasake juyowa ta tsaida baffa tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Baba nikam nace wai yabatun tsohuwar matarnan taka Yaya hawwa, injin tasamu sauqi?.” Saida Baffa ya sinne kai yana d’an sosa qeyarsa saboda nauyin maganar da yaji sannan yace. “Ehmm! Da sauqi zamuce, Amma har yanzu tana kware anaci gaba da bata kulawa aqarqashin jami’an lafiya.” “ALLAH sarki, ALLAH yabata lafiya, kwanakima nayita neman lambarka awayata narasa lokacin da naga ana nuno yanayin da take ciki a tv, abun yabani tausayi sosai sai natuna da zancen bokan da take zuwa wajensa dake asibiti, shaf namanta nakiraka na sanar dakai cewa bayan angama bashi treatment yafarajin sauqi da sati d’aya ashe shima yasamu matsala aqwaqwalwarsa, abun mamaki koda akayi masa gwaje gwaje sai aka samu qwaqwalwarsa lafiya take Amma yanayin abubuwa irin na miyagun mahaukata dake iya illata kowa, asibitin na shirin sallamarsa sai aka samu ya gudu, yanzu haka zaka ganesa akan tituna tsirara haihuwar uwarsa ko akan juji yanacin lalataccen abinci marasa kyau kamar yanda mahaukata keyi a wani lokacin kuma sai kagansa da sutura ajiki yana bin mutane yana bara abashi abincin da zaici, rayuwa yakeyi gatanan dai, shi ba dabba ba kuma ba cikakken mutum ba, hakan yasa nayi tunanin cewa wataqila matsalarsu d’aya da tsohuwar matarka, Ina nufin qwaqwalwarsu lafiya klw take saidai suna azabtuwane ta dalilin miyagun aljanun da suka shiga jikinsu su sukesa sunayin wud’annan abubuwan dakesa anayi masu kallon mahaukata, shine nayi tunanin kiranka nafad’a maka ko zaku koma gwada maganin musuluncine tunda yanzu kusan shekara d’aya da watanni kenan ana fama dana asibitin ba’a dace ba.” Shiru baffa yayi yana maimaita kalaman inspector najida a qwaqwalwarsa, tabbas maganarta akwai qamshin gaskiya aciki dole yayi nazari akanta sosai ko ALLAH zaisa adace. “Shikenan ‘yata in Sha ALLAH zamuyi tunani akan haka nida ‘yan uwana, dama qarfina yafara qarewa akan wannan matsalar tata, kullum cikin kashin kud’i ake, kuma duk da binciken da sukayi akanta suka yad’a aduniya ankasa samun tallafi daga ko ina.” “ALLAH yasawaqe baba, har yanzu ita matar d’an naka ba’a ganta ba ko?” Saida Baffa yayi ajiyar zuciya sannan yace. “ALLAH kad’ai yasani ‘yatah..” Ananma yake bata labarin rasuwar aminin nasa wato mahaifin matar d’ansa, tamatuqar tausayawa tare da yimasa addu’ar ALLAH yajiqansa da rahama, suna tsaye ‘yan sanda suka fito da muneera duk anbubbuge mata fuska saboda taurin kan da tasa wajen kamota, su kansu ‘yan sandan sai nishi sukeyi saboda wahalar dasu da tayi suna sake jibgarta da kulaken dake hannuwansu Inna ruqayya nabiye dasu tana d’ura masu zagi, juyowa inspector najida tayi da qarfi jin zagin da takeyi masu, Inna ruqayya naganin haka ta arta dana kare don bata manta irin azabar da tasha ahannun taba, ana qoqarin tura muneera mota tarugo da gudu ta lab’e bayan baffa da yayi tsaye yana kallon ikon ALLAH tana fad’in. “Wayyo baffa ka ceceni, wlh ba laifina bane, innace tace naje wajen salele na karb’o mata saqo ashe wai iskanci zaiyi dani ya bata kud’i, shine ni kuma na doka masa wani qarfe yafad’a akan wani abu nasamu nayi guduwata, shine akace wai nafasa masa ijiya, don Allah baffa kataimakeni bana son zuwa.” “Yi haquri munneera jeki ku tafi yanzu nida Usman zamu biyo bayanku, Ina shi baffan naki yake?” “Ya gudu baffa, kuma wlh har dashi ke karb’ewa salele kud’i wai zaya aura mani shi ni kuma bana sonsa, kuma baffa ya…” “Ashsha muneera yishiru haka jeki kinji zamuzo yanzunnan?” ‘Bare baki tayi tana kuka had’e da susar kai ‘yan sandan sukazo suka cakumeta tanata tsalle tsalle da ihu suka sakata aciki, yaran anguwa da suka taru sai faman dariya sukeyi, girgiza kai baffa yayi sannan yabar wajen don ya tabbata Usman baya cikin gidan shi Kuma mahaifin nata sakaran wofi da rashin kunyarsa akansu kad’ai ta tsaya yayi guduwarsa… Daqyar baffa Usman da baffa suka samu sukayo belin muneera batare da anje kotu ba saboda ijiyar yaron batayi komai ba amma yace sai ambiyasa kud’insa. STORY CONTINUES BELOW  Don haka sukaje suka kama d’aya daga cikin shanun baffa Ali suka sayar batare da yasani ba aka biya salele kud’insa sannan akayi masu tsakani da ita, sauran kud’in kuma baffa yakai masa, baffa Ali sai faman wasar baki yakeyi duk d’aukarsa a banza aka bashi kud’in, Saida yagama murnarsa sannan baffa Usman yafad’a masa yanda aka samu kud’in, wayyo ranar yini baffa Ali yayi yana d’ebe masu albarka tare da zunduma masu zagi, yaran gida duk Wanda ya matsosa saidai yaji ya falla masa mari yana d’ura masa ashar, daga qarshe da yaji rad’ad’in yaqi d’ebe masa yasa muneera d’aki yasata yayita jibgarta yana tsina yana fad’in sai yafidda kud’in naggensa ajikinta. Baffa Usman dake zaune yana shan fura yayi dariya had’e da cewa “Oho dai, inma kasheta zakayi ka kashe ai ‘yarka ce, ayanda kake marar hankalin nan da tunani babu abunda yakamata ace kayi illa kanunawa duniya cewa nagge tafi ‘yarka muneera awajenka, shasha kawai, mudai bazamu doku ba awajenka, ubangiji ALLAH kashiryar mana dakai kada baqincikinka yasa murasa rayukanmu *BAYAN SHEKARU ASHIRIN DA BIYAR* Abubuwa da dama sunfaru wud’anda duk wani mumuni ya ishesa d’aukar darasin duniya matuqar babu ta’bewa da ‘bata acikin rayuwarsa…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___69💎 Musamman acikin rayuwar Rashida da mahaifiyarta da idan kazauna kayi nazari zaka fahimci dalilin daya hana Rashida yin karatu tace aure take so har ta auri Nuraddeen mahaifiyarsa ta turo mata aljanu suka d’auketa suka kawota garin borno, har hakan taja iyayenta suka baro garinsu cikin qaddarawar ALLAH kuma aka sake had’asu gari d’aya da inda ‘yarsu take kuma ta ALLAH tazo ta afku akan mahaifinta da aka tsaro cewa nanne qasar da za’a rufesa, don bayan umma takammala takaba sai dady yasake bijirowa da buqatar d’ansa akan yana son Rashida ta tsaya anan taci gaba da karatu har lokacin da ALLAH zai dawo da mijinta, badon su baba balarabe naso ba suka sake amince masa akaro na biyu bisa sharad’in duk lokacin da mijin nata yadawo dole zata ajiye karatun takoma hannunsu don su mayar masa da ita, wannan dalilin yasa itama umma tace bazata komaba zata zauna da ‘yarta don itama tabata tata gudun mawa wajen cikawa baba burinsa naganin tayi karatu mai zurfi kamar yanda yaso, kasancewar tanada ‘yancin kanta yasa babu wanda ya tilasta mata akan sai takoma suka bisu da fatan alkhairi Cikin sati biyu Dr nura ya ida kammala shireshiren komawarta makarantar tare da sama mata Mai lesson na musamman da zai taimaka mata don j.s.s 3 yace akaita duk da kuwa qoqarinta bai kai can ba, nan take tafara karatu ka in da na’in cikin jajircewa da qaunar cikawa mahaifinta burinsa, Ammie kuwa tuni ta dakatar da umma batun aikin da takeyi mata tasa aka samo mata wata sai ya zamana umma bata aikin komai agidan inba kula da gyara shiyar da suke ba da kwanciya don ko girki ammie kesa ana kaimasu nasu daga sashenta idan andafa, dady kuwa akoda yaushe cikin kulawa dasu da yimasu hidima yake, kwatsam ranar yasami ammie da zancen yana son ya auri umma saboda shidai yana tsananin tausayinta aransa don tunda baba yarasu har yanzu takasa komawa daidai, kuma shi agani sa idan yayi hakan yiyi jahadi sosai tunda batawuce yin aure ba to baiga amfanin tazauna ahaka ba, asalima yana tunanin idan har tanada sha’awar yin aure Wanda zai iya damqawa amanarta kuma yariqeta hannnu biyu, hakan yasa azuciyarsa yaji ya amince d’ari bisa d’ari don tabbatar daya riqe amanarsu hannu biyu kamar yanda ya d’auka, zuciya batada qashi kuma shi kishi gaskiya ne don haka awannan lokacin ammie sai taji badad’i aranta amma saita danne zuciyarta tabashi goyon baya tare da qarfafa masa wajen aikata hakan, STORY CONTINUES BELOW  Kwana biyu tayi tunda dady yayi maganar bata barin su had’u da umma saboda abunda takeji nataso mata aqasan zuciya saboda kada tayi abunda ba daidai ba, daga qarshe kuma tasaki taroqi ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi, Hajia nafeesa kuwa da taji Babu irin maseefar da batayi ba da habaice habaice tun umma batasan abunda kefaruwa ba don bai riga ya sanar da ita ba har tasani, ta matuqar girgiza had’e da nuna qin amincewarta amma ammie tayita lurar da ita da lallashinta har saida ta amince, ba’a wata samu matsala ta b’angaren ‘yan uwanta dana baba ba sboda ganin dattako da cancantar dady suma suka amince, nan take dady yasa aka rushe sashen da take da wasu wurare cikin gidan itama aka fitar mata da part d’inta abunka ga mai arziqi cikin sati biyu aka kammala komai har d’aurin aure ta tare abinta, Duk wannan abun daya faru bisa amincewar Dr da taimakonsa dady yayis hakan kuma dashi har Fatima sunyi farinciki sosai ba tare da wata hiyana ba, Rashida ce kawai kullum take cikin jin kunya tana ganin kamar hakan da akayi ba’a kyautawa ammie ba, bayan duk taimako da halaccin da tayi masu ita da d’anta har saida ammie tazaunar da ita tanuna mata hakan ba illa bane tunda musulunci bai hana ba sannan tafara samun sakewa daidai, duk da ako yaushe idan hajia nafeesa tahad’u da ita har mahaifiyarta cikin jifarsu take da miyagun kalamai cewa wai Rashida tayi cikin shegene shiyasa tagudo suma da abun kunya ya ishesu sun kasa gano uban d’and’an dake cikinta sai suka biyo bayanta, hatta ma little da baisan komai ba kullum cikin kyararsa take tana aibantasa agaban ‘ya’yanta tana kiransa da shege wanda ba’asan ubansa ba, hakan yasa har ‘ya’yanta ma ke kiransa da haka amma da yake baisan komai ba baya damuwa. Haka rayuwa taci gaba Rashida nasamun kulawa da kuma gudun mawa sosai wajen karatunta da ita har d’anta ta b’angare biyu wato dady da kuma Dr, don tuni shima little Dr yasashi makaranta lokacin itama Fatima har tahaihu tasamu qaton d’and’anta suka rad’a masa suna basheer wato sukawa baba takwara, wannan ba qaramar kima da daraja yaqara jawo masuba a idanuwan umma da Rashida harma da ‘yan uwansa, sunyi matuqar farinciki da jin dad’i sosai aransu harma suna ganin aduniya yanzu basuda masoya da suka fimasu su dady da Dr nura ba. Rashida kuwa tun tana dakon dawowar mijinta izuwa gareta ita da d’anta har tacire rai, gaba d’aya ta tattara wata rayuwar aure data tab’ayi abaya dama auren ta ajiyesu gefe taci gaba da karatunta ita da yaronta, saidai duk da hakan daidai da rana d’aya Bata tab’a yarda tayi wani abun da zaya keta mata marta da kuma darajar auren taba har ta kammala secondary lokacin little na primary 2 amma babu wani labarinsa, a lokacin fatima har tayaye basheer da suke kira (abbaty) tasake samun ciki ta haifi ‘yan biyu duka mata saidai rurrutsa ce tayi a tsakaninsu, inda aka barsu da sunayensu na asali wato hassana da hussaina, murna kam awajen Dr da fatima bata misaltuwa, gashi dai SANNU SANNU cikin iyawar ALLAH suma sunfara tara nasu ‘ya’yan da suke matuqar qauna a cikin shekaru uku kacal ALLAH ya arzuttasu da ‘ya’ya uku, Babu wata wahalar reno da fatima kesha saboda Rashida nanan, duk wata kulawa da yaran zasu buqata tana basu tamkar ita tahaifesu. Shekarar Rashida d’aya tana jiran saka makon jarabawar tasu tafito kuma cikin taimakon ALLAH tayi nasarar lashe kowane darasin da kyakkyawan sakamako wato exelent gaba d’aya, ranar da ita har umma sunyi kuka sosai cike da son inama baba nada rai yaga yanda tafara taka mataki na biyu akaratu da kyakkyawan sakamako, godiya kuwa sunyiwa Dr da dady da ammie ba adadi har saida suka farajin kunya. Umma da ammie kuwa bazaka tab’a ganinsu kace kishiyoyi bane domin akwai tsantsar fahimta da mutunta juna atsakaninsu, hakan yaqarawa hajia nafeesa tsanar umma da rashida dama little gaba d’aya. ••• ••• ••• A b’angarensu baffama acikin shekarunne ALLAH ya sauki nusaiba matarsa lafiya saidai ba’a samu namiji ba kamar yanda yaso ALLAH ya arzuttasu dai da samun ‘ya mace kyakkyawa kamarta sak da nusaiba baffa ya rad’a mata suna Rashida, yana matuqar son yarinyar fiye da tunani saboda sunan data zauna, sau da dama yakan tuna da baba da Kuma ‘yarsa Rashida aduk sadda aka ambaci sunan ‘yar tasa da taci sunan Rashida, wannan yasa ko kad’an baya son jin kukanta balle abunda zai b’ata mata rai, hakama gaba d’aya yakasa mantawa da gudan jininsa daya kasa samun labarinsa, lokacin daya tuntubi ma’aikatar da aka turasu qasar waje don qaro karatu akan labarinsa sai suka b’oye masa ainahin halin da d’an nasa ke ciki, domin koda Nuraddeen suka isa qasae waje bayan anbasu wajen zama sai yanemi wayarsa sama da qasa yarasa, gashi gaba d’aya wud’an da aka had’asa dasu zama ‘yan jahohin kudu ne acan nageria babu wanda yasani acikinsu, asalima gaba d’ayansu babu ruwansu dashi saboda shikad’aine bahaushe sai suka nuna mashi halinsu qarara na qyamar jinsin da banasu ba musamman ma ga musulmi d’an arewa duk da kuwa qasarsu d’aya, hakan yasake jefasa acikin wata damuwar akan wacce yake ciki yana son yasan halin da ake ciki anan gida nageria amma bayada waya, kud’ad’ensa ma daya zo dasu gaba d’aya an sace balle yasamu ya sayi wata, wata irin wahalalliyar rayuwa yafarayi aqasar da kud’in ma da zai samu yayi amfani dasu babu, ana haka d’aya daga cikin qabilun da yake tare dasu yafara qoqarin jawosa jiki yana son taimaka masa da sunan tausaya masa, amma azuciyarsa bashine dalilin silar taimakon da yake yimasa ba kawai yana so ya d’orasa akan hanyar da zata hanasa karatune balle yasamu yayi abunda yakawosa har yakoma qasarsa ana alfahari dashi sai dai duk da haka Nuraddeen bai tab’a wasa da karatunsa da tuni suka fara yiba a fannin koyon likitanci na psychiatric musamman idan yatuna da halin daya baro mahaifiyarsa aciki sai yaji yaqara samun qwarin guiwar maida hankali sosai, hakan yasa yazamo kusan shine zakara kuma zaqwaqurin da yafi kowane d’alibi amakarantar, tun daga kan fararen fata har zuwa ‘yan uwansa baqaqe, wannan abun yaqara baqantawa natare dashi rai ganin shi bakowa bane acikinsu amma ace ya zartasu qoqari acikin aji, don haka suka sake d’aukar d’amara wajen ganin sun durqushesa tahanyar jansa ga jiki, sunyi amfani da yawan damuwar da yake shiga wajen ganin sun jawo ra’ayinsa tahanyar zagayawa dashi wajaje masu ban sha’awa da d’aukar hankali aqasar wanda nan take suka fara zuwa club club dashi suna nuna masa hanyoyin shaye shayen qwayoyi da barasa da sunan zasu taimaka masa wajen rage damuwar da take ciki, yau da gobe babu abunda tabari, tun Nuraddeen najin bazai iyayin hakanba har yafara sha’awar aikatawa batare daya ankara ba, akoda yaushe yakan zauna yana qoqarin tunano gida da abunda yafaru sai yaji yakasa tuna komai, sab’anin da da kullum cikin tunaninsa da abunda yafaru tsakaninsa da matarsa yake, wani abu daya sake d’aure masa kai shine yanda bayason tuna qasarsa gaba d’aya balle ahalinsa shiyasa nan take suka samu nasarar juyar dashi yanda suke so, idanma yace zai zauna yatuna wani abu akansa sai yaji kansa na matuqar sara masa da yimasa ciwo, bazaiji yasamu sauqin hakan ba har sai ya d’auki barasar da tuni ya amince da takan rage masa damuwa yasha. STORY CONTINUES BELOW  Gaba d’aya rayuwarsa tagurb’ace amma wani ikon ALLAH babu abunda ya sauya ta b’angaren karatunsa, zai iya sha yabugu sosai sannan yaje aji suyita yimasa dariya yana wartsakewa zaije yanemi topic d’in da akayi yayi reasarch akai kuma nan take yafahimta, idanma yakasa zaije yanemi malamin duk inda yake ya sake yimasa bayani, malamai da yawa na mamakin halin da yaron yajefa kansa aciki wanda shi da kansa idan an tambayesa bazai iya fad’ar daliliba, iya abunda zai iya fad’a akai shine baya son tuna komai akansa, ahalinsa da kuma qasarsa, idan kuma yayi yunqurin hakan to halin da zai tsinci kansa aciki shine zai haifar masa da shan barasa don yasamu magancesa.. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Masha ALLAH, a gaskiya zafafan comment d’inku akan yanayin da Nuraddeen keciki sun tafasa k’wak’walwata, da banyi niyar cewa komai ba but yazama dole nace wani abun wataqil hakan zaisa kud’an fahimceni, A iya sanina qarfin imanin mutum qarfin jarabawar da ALLAH zai yimasa😅alkawarin ALLAH ne cewa duk wanda yace yayi imani to dole za’a jarabcesa tako ina arayuwarsa don atabbatar da ingancin imaninsa, don haka kuyi haquri da halin da Nuraddeen ya tsinci kansa aciki, ba burina ku karanta littafin ku nishad’antu dashi kawai neba, a’a ina son kutsinci darussan dake cikine tare da fahimtarsu, karku manta alqalamin marubuci bayana ta’allaqa kawai bane akan nishad’antarwa da burgewa, dole yazamo ansamu ilmantarwa, fad’akarwa da kuma luraswa aciki, hakan shi zai bashi damar isar da saqon da ake son isarwa ya yanda yakamata, da fatar nima kun fahimceni yanda yakamata_🥰 Page___70💎 Haka rayuwar Nuraddeen taci gaba da kasancewa acan batare da mahaifinsa sun san komaiba, sukuma jami’an dake kulawa da lamurran karatunsu babu abunda basu sani ba, duk iya matakan daya kamata su d’aukar masa suna iya qoqarinsu amma hakan tafaskara, ganin yana karatunsa yanda yakamata d’abiarsa ce kawai yagagara gyarawa daga yanda take yanzu zuwa yanda take ada yasa suka qyalesa, a qa’ida tsarin karatun nasu shekara shida zasuyo acan sannan su kammala, amma bayan shekara uku zasu dawo gida hutun wata d’aya sannan sukoma su ida qarasa sauran shekaru uku. Lokacin da suka shekara uku acan aka tashi dawowa hutu Nuraddeen kafewa yayi kai da fata shi babu inda zaije, Babu irin yanda ba’ayi dashi ba yace shi gaba d’aya baya buqatar hutun balle har yakoma qasarsa, kasancewar yanada matuqar qoqarin da tun daga d’aliban makarantar har zuwa malanta Babu wanda bai sanshi ba, don haka sai ‘yan uwansa mazauna kano da sukazo tare sukaje suka sanar da wani malamin halin da ake ciki, koda yaje shima yayi masa magana irin amsar daya basu ya bashi, nan take malamin yaje ya sanar da shugabar makarantar da yake macece (Miss Florence Jackson) tasa aka kirawo matashi tayi masa magana, tayi iya juyin duniya akan yabi ‘yan uwansa amma yaqi amincewa daga qarshe ma sai yafara riqe kai irin alamun maganar na neman saka mashi damuwa, don haka sai tace subarshi zatayi magana da jagororinsu na nan qasar zai zauna awajenta saboda su awajensu kowa nada ‘yancin kansa yayi duk abunda yakeso, hakan kuwa akayi gaba d’aya d’alibban da sukaje tare dashi suka dawo gida cike da farinciki zasuga ahalinsu da iyalansu bayan tsawon shekaru uku da suka sharikke awaccan qasar. Baffa nasamun labarin dawowarsu cike da farinciki ya sanar da baffa Usman, Kwana da yini sukayi suna jiran isowarsa gida amma shiru wannan dalilin yasa baffa ya isko baffa Usman har gida cike da damuwa ya sanar dashi cewa tunda sukaga bai iso gida ba to tabbas ba lafiya yakamata suje su tuntub’i manyannasu suji meke faruwa?, STORY CONTINUES BELOW  Ba qaramin tashin hankali baffa yashiga ba lokacin da akayi masa bayanin abunda yafaru na cewa Nuraddeen yaqi amincewa yadawo wai har sai sun kammala karatun gaba d’aya nan da wasu shekaru uku masu zuwa, kusan fad’uwa zaune yayi daga tsayen da yake saida Baffa Usman yayi saurin riqosa, ba abunda kefita bakinsa inba. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, qadarallahu wama sha’a fa’ala.” Tabbas jikinsa yanzu nabashi akwai abunda kefaruwa akan d’ansa wanda aka b’oye masa, Aikuwa daya matsa lallai sai ansanar dashi dalilin da yasa hakan zata faru sai suka sanar dashi gaskiyar halin da Nuraddeen keciki don bazasu iya cigaba da b’oye masa ba a matsayinsa na uba awurinsa kuma suka sanar dashi cewa yana cikin qoshin lafiya sannan kuma yana maida hankalinsa ga karatunsa sosai don haka yakwantar da hankalinsa. Awannan ranar gaba d’aya guiwowin baffa saida suka sare had’e dayin sanyi kuma ya yadda cewa tabbas rayuwar mumini kullum cikin jarabta ta akeyi, idan yafita wannan jarabawar sai kuma wata takunno kai, yashiga kwararo addu’a ALLAH yabashi qwarin guiwar da zai rinjayi zuciyarsa har zuwa lokacin da ALLAH zai canye dukkanin jarabawowinsa. Bayan sun dawo suna tsaye a qofar gida suna tattaunawa akan yanda zasu b’ullowa matsalar, baffa Usman nata rantsuwa cewa tabbas koma meye akwai abunda badaidai ba don yayi imanin bazai tab’a aikata abubuwan da akace ba, idanko har gaskiya ne to tabbas bayin kansa bane, Ashe duk abunda suka fad’a Inna ruqayya da zata fitowa tajisu don haka sai takoma cikin zaure ta lab’e tana saurarensu. Tsabar farinciki da jin dad’in abunda kunnuwanta suka jiyo mata nassa taji wani irin sanyi azuciyarta kuma ta gamsu cewa tabbas haqarsu ta cimma ruwa kuma abunda suka dad’e suna dakon jira amatsayin fansar da suke son d’auka ya tabbata, fasa fitar tayi takoma cikin gida fuskarnan tata tamkar ambiya mata makka tashige d’aki tana tiqar rawa had’e da cewa da SANNU SANNU zakuga aikina da ciwa, kad’an kuka gani ai indai ina raye saina qumsa maku baqincikin da kuka qumsa mani nida ‘yata akan yaronku, tashi baffa Ali da bai jima da kwantawa ba yayi yana kallonta cike da mamaki, dama dawowarsa kenan daga d’aukar hatsinsu da suka girbe ta tambayesa kud’i ya hanata shine tafita tana kumburar fuska wai zataje ta aro wani wuri, sai gashi bata jima da fitar ba yaga kuma tadawo fuskarta d’auke da farinciki tana dabsar rawa, tun kafin ya tambayeta ta shiga zayyane masa abunda taji ‘yan uwan nasa nafad’a akan halin da Nuraddeen keci acan qasar. Nan shima fa yatayata har yana fad’in wai anzo wajen!, sai su baffa sunyi dana sani da nadamar turasa qasar waje yaqaro katu, don bazaya tab’a dawo masu amatsayin wanda yayo karatu ba, sai dai yadawo masu a matsayin d’an iska lalatacce da baza’a iya tab’a banbance tsakaninsa da arna ba tunda suka zab’i turasa can akan aurar masa da ‘yarsa, bayan duk walaqancin da akayi masu da wanda Yaya hawwa tayita masu alhalin ansamu damar da za’a iya aura masa ita, yazama dole yaje yabiya malan bakada imani don yanzu kam yatabbata yayi masu aikin daya dace, fatanshi kawai ALLAH yaqara duhu don girman d’ib. Ashe duk wannan abun daya samu Nuraddeen aikinsu ne, su suka kaishi wajen malamin tsibbu sukace ayi masa asarin da zai lalace kuma idan yabar qasar ya manta da kowa nasa, asamashi tsanar qasarsa gaba d’aya yadena sha’awarta balle ma yatuna da iyayensa ko matarsa, duk wata hanyar da zatasa yaci gaba a dwad’e masa ita hatta karatun da akace zaije yi ya kasa yinsa, aganinsu yin hakan shine kad’ai zaisa su d’aukar fansar abunda baffa yasa akayi masu, fansar da batada wani tushe balle asali. Ba’ayi wata da faruwar hakan ba su baffa sukaje sokoto asibiti wajen karb’owa Yaya hawwa sallama don ba laifi tafara samun sauqi, duk iya qoqarin su naganin ambasu sallama aranar hakan ta cutara daga qarshema sai ankace suje sai bayan sati biyu su dawo, ko kad’an basuso hakan ba amma babu yanda suka iya dole suka koma gida, sati biyu nacika suka sake komawa, awannan karonma saida sukayi da gaske sannan aka basu sallamar, itama d’in da sunan transfer ne akayi masu izuwa asibitin PSYCHIATRIC dake can kano sannan aka d’aukosu da motar asibitin. STORY CONTINUES BELOW  Inna Bilkisu ita tagyarawa Yaya hawwa d’akinta kafin su iso, acan asibitin aka kaisu sukayiwa wani babban likita bayani akan suna son komawa da ita gida sugwada yimata maganin hausa idan ALLAH baisa aka dace ba sai sudawo, cikin sa’a da yake bahaushene kuma musulmi ya amince masu tare dasa hannu akan file d’in nata sannan aka aai aka ajiyesa inda yakamata, kuma ya fad’a masu aduk lokacin da buqatar kawota asibiti takama ba matsala sukawota in Sha ALLAH za’a dubata, data dai takowace irin hanyace ALLAH yabata lafiya, sunyi matuqar jin dad’i bisa karamcin daya yimasu kafin suyi masa godiya suwuce da ita gida. Qwararrin malamai masu ruqya suka samo akayi mata ruqya, inda nan take mugun aljanin dake jikinta ya bayya yana wata qara da kururuwar shi bazai fita ajikinta ba tunda tasa aka azabtar dashi, aka naqasa shi tare da illata masa rayuwa don haka shima bazai gusheba yana azabtar da ita acikin jiki ba har sai lokacin da ruhinta ya rabu da gangar jikinta, babu irin magiyar da ba’ayi masa ba amma yaqi don haka malaman sukaci gaba da yimata karatu ana watsa ma aljanin ruwan magani yana wata irin muguwar qara saboda zabar qonasa da akeyi har saida yaqone tas, nan take jikinta ya saki malaman suka yima ALLAH godiya daya basu nasarar qona aljanin batare daya naqasa taba, sannan suka bada maganukkan da za’a dinga bata tare da tabbatar masu da cewa in sha ALLAH tasamu lafiya musamman idan aka dage da kulawa wajen bata maganin. Cikin iyawar ALLAH da aka dage wajen kula da bata maganin sai gashi tafara samun sauqi sosai, duk wasu kuwace kuwace da wasu caccanza halittarta da akeyi tadenayi, tadena bugu balle maqura, haka kuma tana iya gane duk wanda yazo wajenta maganace kad’ai bata iyayi, yanayin yanda idan Inna Bilkisu tashiga kaimata abinci ko bata magani take kuka hawaye nazuba a idanuwanta shike qara tabbatar da cewa tasamu lafiya, don kallo d’aya zakayi mata kasan cewa ba kukan komai ne takeyi ba illa na tarin nadama, don gaba d’aya cinta, shanta, kula da tsaftaceta duka ita keyi ita da yaranta su Aisha, musamman idan basa komai d’akinta duk suke zuwa azauna ayita fira saboda kada subarta cikin kad’aici, wani lokacin saidai taqura masu idanuwa tayita kallo batare data tanka masu ba, duk da aranta babu wanda take tunani take son tambayar Ina yake kamar d’anta ya nura amma babu bakin magana saidai tazauna tayita kuka Inna Bilkisu na faman rarrashinta da bata magana. Haka baffa ma idan yazo ganinta, Babu abunda takeyi sai kuka wanda kukan ya tabbatar masa da cewa na nadamane takeyi don haka sai yanuna mata tadena damuwa, kamar yanda yafad’a mata ashekarun baya cewa yayafe mata duniya da lahira har yanzu hakanne aransa, Kuma yasa nusaiba ta shirya ranar sukaje tare ya gabatar mata da ita a matsayin matarsa tare da ‘yarsa Rashida da har tafara tafiya, sannan yayi mata bayanin duk halin da d’anta Nuraddeen keciki saboda amatsayinta na mahaifiyarsa ta tayashi yimasa addu’a, ranar Yaya hawwa kwana tayi tana kuka azuciyarta tana roqon gafarar ALLAH da kuma yayewa d’anta halin da yake ciki, tana so ta tambayi Rashida matar d’anta amma ba halin haka domin bataga fuska ga kowa ba da zata iya tambaya, Babu mai d’auko mata zancenta ita kuma babu baki balle ta tambaya. Su baffa Ali kuwa tamkar babusu acikin gidan don sau d’aya sukaje dubata, qarama muneera takan d’anje tadubota wani lokacin shima idan basa nan. ••• ••• ••• Rashida kuwa tuni antaka matakin manyan mata don tuni an takammala karatunta na jami’a aqarqashin kulawar Dr da mahaifinsa, tasha karatu sosai fiye da tunanin mai karatu a fannin law wato shari’a, yanayin yanda tamaida hankali sosai ga karatun yasa tasamu nasara acikin kowane mataki data taka, tanada wata baiwa tamusamman da ALLAH yabata wajen jajircewa ga dukkanin abunda tasa agaba wannane yasa take nasara acikin dukkanin al’amurranta, bayan ta kammala Dr yayi sha’awar sama mata aiki Amma sai dady yahana, acewarsa hakan badacewa bane tunda tanada aure kuma dole amartaba igiyar aurenta sai kuma idan kotu za’aje araba auren tunda har yanzu mijinta bai waiwayeta ba, hakan yasa Rashida tace tahaqura duk da tanada sha’awar yin aikin, Amma har yanzu qauna da soyayyar mijinta na kwance azuciyarta da bata tunanin zata iya rayuwa da wani idan bashi ba, tasha alwashin bazata koma wani auren ba koda hakan na nufin tarabu da mijinta kenan har abada domin gaba d’aya tadena sha’awar auren, don haka sai dady yabata kud’ad’e masu tsoka sosai tafara gudanar da business, acewarsa zaifi kyau ta dogara da kanta domin ba’asan halin rayuwa ba, sosai Rashida tamurje tayi kyau tazama ‘yar gayu, idan kaganta bazaka tab’a cewa wai Rashidar nance ta qauyen yarimawa matar malan nura ba. Ana haka ranar labari ya iso mata cewa ai su Nuraddeen sun dad’e da kammala karatunsu da sukaje yi tun shekarun baya amma shi yaqi amincewa yadawo, zamowarsa qwarare a fannin daya karanta namasu fama da matsalar neorology da gaba d’aya qasar basu tab’a samun d’aliba mai hazaqa kamar saba yasa qasar tariqesa har tabashi goyon baya d’ari bisa d’ari bisa muradinsa da kuma ra’ayinsa, nan take suka bashi aiki tare da yanka masa albashi mai tsoka, ayanayin da yake aciki lokacin koda bazasu bashi komai ba yafi son ya zauna acan qasar fiye da yadawo, da gwamnatin jahar tasu tanemi tsaurara al_amarin qasar ta d’auko maqudan kud’i tabasu, kasancewar yanda qasar tamu idonta yariga ya bud’e wajen ansan rashawa da cin hanci da Kuma rashin sanin ciwon Kai ya sukayi mui basu koma tada zancenba, baffa yayi kuka da baqincikin abun sosai amma daga baya ya haqura yaci gaba da addu’a tare da yaqini akan ko yaushene zai waiwayesu, Yaya hawwa ma duk da bata um balle u’um aranta tana yimasa addu’a tare da fatar ALLAH yadawo dashi kafin ta ALLAH takasance akanta, wannan labari ya matuqar girgiza Rashida duk da aqasan zuciyarta bata gamsu cewa zaiyi hakan ba sai indai akwai wani abu aqasa da bata sani ba, amma koma meye tayi alqawarin zata zauna zaman jiransa komai daren dad’ewa, kwatsam ranar tana kallon BBC news taga ana fira da wani likita mazaunin qasar malesia amma haifaffen d’an qasar Nigeria ne, qura masa idanuwa tayi saboda ganin yanda yake matuqar kama da habibynta amma azuciyarta sai tace shi wannan yafi habibynta qiba da kuma haske sosai asalima daka kallesa kaga d’an gayu wanda hutu ya zauna masa ajiki, badon ma yanayin haskensa dana mutanen can akwai banbanci ba da bazaka tab’a cewa shi ba d’an qasar bane, tana wannan tunanin ne taji ana tambayarsa sunansa… Qara volume d’in tv tayi had’e da juyowa tana kallon yaransu Dr dake zaune suna wasa wato (walida da sultan) wud’anda aka haifa bayansu shahid da Shahida, walida ita ke bimusu twins sunan ammie ne da taci shiyasa ake kiranta waleeda sai sultan shi kuma sunan dady ne aka saka masa ana kiransa da sultan, tace masu suyi shiru, gabanta ne yafad’i jin da tayi likitan yace Sunana… 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___96💎 A’a Usman wlh maganin nan nada matuqar had’ari sosai, bazan so wani abun ya sameka ba har yayanmu ya sake shiga cikin wani hali, kaine kad’ai karage masa aduniya da zai kalla yaji sanyi bayan iyalinsa, naroqeka kabarni zanje da kaina in fuskanci hukuncin laifin Dana aikata, natabbata ALLAH baya mayar da tubar bayinsa matuqar sukayi ingantacciyar tuba kuma mai kyawo, idan ko har wani abun ya sameni to nayi imani da cewa ALLAH na nufin ya jarabta nine domin yaga qarfin imanin da nace nayi da kuma tubata idan har na gaskiya ne, saboda haka kabari inje kaji d’an uwana!” yaqare maganar had’e da d’ora hannunsa saman kafad’arsa. Kusan mintuna ashirin da wani abu sukayi suna rigima akan wanda zaije cikinsu, shidai baffa Usman ya nace shi zaije don ayanzu bai shirya rasa d’an uwan nasu ba tunda har ya tubarwa laifinsa, shi kuma baya cikin wud’anda haqo asirin zai iya cutarwa kamar yanda bokan yafad’a idan har aka haqo abun shi baffa Ali da matarsa da sukayi asirin su zai koma mawa balle wani abun ya samesa, shi kuma baffa Ali yana ganin tunda har yatuba to dole yayi qoqarin gyara laifukan daya aikata da hannunsa da kansa ko zai samu sassaucin hukuntawa daga ubangiji, ya sani ubangijinsa zai karb’i tubarsa amma haqqin wud’anda ya zalunta dolene sai yayi duk yanda yakamata wajen ganin sun yafe masa kafin ALLAH yabarshi. Dole badon baffa Usman yaso ba ya haqura ganin yanda ya dage harda kuka, amma ya tabbatar masa dacewa Dole tare zasuje koma inane bazai barshi yaje shi kad’ai ba. Da sauri sauri baffa ke tafiya ko gabanshi ma baya gani saboda tsananin b’acin rai har ya isa gida yana fitar da haki d’aid’ai ya samu gefe da tsakar gidan ya fad’i zube kwance yana kuka, gaba d’aya yau yarasa qarfin zuciya da jarumtar da zai iya hana kansa kuka, Babu abunda yake tunanin in banda lafuzzan d’an uwan nasa, ace kimanin kusan shekaru talatin yana fama da damuwar rabuwa da kuma fushi akan d’an nasa tilo duk ta adalilin kaidi da baqin sammun da d’an uwansa na jini uwa d’aya uba d’aya yayi masa, meye rauninsa a matsayinsa na babba agaresa daya cancanci wannan hukuncin?, Meyayi masa aduniya da bai cancanci yafiyarsa ba har sai ya rabasa da d’ansa na tsawon wannan lokaci?, Wace irin kulawace bai bashi ba aduniya daya zab’i jefasa cikin mummunan hali haka?, Haka yayita tambayar kansa yana tsiyayar da hawaye har ya gaji don kansa ya bari. kallon baba nusaiba da tun shigowarsa taqaraso wajen d’aya zube kwance hankalinta atashe, yanda yake kukan ya tabbatar mata daba abu qarami bane ke damunsa ba, don haka saita d’auko mafifici ta shiga yimasa fiffita batare da race masa uffan ba har sai da taga yasamu natsuwar da zai iya kallonta, murmushi ta sakar masa had’e da cewa. “Waye ya tab’a mani adilin mai gidana baban nura abban Rashida har ya karya zuciyarsa haka tasashi zubar da qwalla, kayi haquri da yanayin da rayuwa kanzo dashi na farinciki ko akasinsa, kayarda da wanzuwar qaddara mai kyau ko marar kyau agareka, ka amince babu mai yimaka sai ALLAH domin shine kad’ai ke iya sarrafa zukatan bayinsa, shiga damuwarka daidai yake da rushewar dukkanin farincikin gidannan musamman na wacce ke rayuwa bisa walwalarka da kuma farinciki, idan ni nayi maka laifi kayafeni baban nura idan kuma waje akayi maka kayafesu baban Abba amininsa?” Duk da yana jin wani nauyi a zuciyarsa da kuma wani abu da yazo ya tokare masa amaqoshi hakan bai hana jin tasirin kalamanta azuciyarsa ba da sukasa nan take yaji wani irin sanyi ya mamaye masa ita, STORY CONTINUES BELOW  Murmushin ya mayar mata kamar yanda tayi masa had’e da cewa. “Me zakiyimun aduniya maman nusaiba da zai b’atamun rai har yasani kuka inba alkhairi ba, kin zamo mani haske alokacin da nake cikin duhu, kin kauda mani kad’aita alokacin dana rasa makusantana gaba d’aya, kin zamo sanyi agareni alokacin da zafi yayi mani qawanya tare da qoqarin share mani hawaye ga dukkanin damuwar dake neman durqusar dani, taya kike tunanin duk tarin wud’annan alkhairan da kikayimun zaki iya yin wani laifi da zaisa hawayena sake kwaranya bayansu, aike ‘yar aljannah ce in sha ALLAH maman Rashida, ki kwantar da hankalinki damuwata dai irin ta yau da kullumce kamar yanda kika sani.” “Akan Nuraddeen kenan!” “Sosai kuwa, saidai awannna karon ta tarin nadamar fushin dana d’auka dashi ba bisa haqqinsa ba, wataqilma fushin nawane ya dad’a jefasa cikin halin da har aka samu yin galaba akansa, ya ALLAH ka yafemun kuma ka yaye masa wannan mummunan hali da aka kad’asa aciki.” Yaqarasa maganar wasu zafafan hawayen na sake biyo masa fuska, “Amin” baba nusaiba tafad’a tana kallon mijin nata da gaba d’aya tsufa yarufes, furfura tako ina ta cika masa fuska ga tarin jijiyoyi da suka taso masa tako Ina suka bayyana ajikinsa, wata ‘yar sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke aranta tana maijin tausayinsa, a wannan lokacin yakamata ace yana samun cikakken hutu ne bawai wahala ba, Amma tsabar neman halal d’insa da yake da kuma tarin damuwowi dake cike fal azuciyarsa da mabanbantan qalubalen da yayita fuskanta arayuwa sunsa tsufa yayi saurin bayyanar masa tayanda kallo d’aya zaka yimasa ka d’auka shekarunsa sunfi qarfin gangar jikinsa saboda manyancin da yayi, Nan baffa yashiga labarta mata abunda kefaruwa, sosai itama bataji dad’in hakan ba amma saboda ta tausasa zuciyar baffa akan d’an uwan nasa tace. “Ashsha! Gaskiya abun baiyi dad’i ba kam, Amma kayi haquri Kuma ka godewa ALLAH daya kawo qarshen lamarin alokaci d’aya, kaga dai ALLAH ya karb’a maka addu’ar shiriya da kaketa roqawa d’an uwanka sannan kuma zai dawo mana da d’anmu a hannunmu in sha ALLAH don na tabbata Ali yayi nadama kuma tubar gaskiya yayi don haka zai karya koma meye da SANNU SANNU sai kaga hankalin Nuraddeen yadawo gida, kaga kuwa banda godiya babu abunda yakamata kayiwa ALLAH, nufin alkhairansa agaremu yasa ya bayyana mana gaskiyar a fili tafito, da yaso sai yakarb’i rayuwar Ali da matarsa batare da sun sanar da abunda suka aikata ba agaresa kaga kuma shikenan babu yanda zamuyi sai dai mucigaba da haquri har zuwa lokacin da ALLAH yaso karya asirin da kansa, Amma yanzu wannan shiriyar da yayiwa Ali har yatuba ga laifinsa yafad’i abunda suka aikata ita zata haska mana al-amarin sai muga nesa ta matso mana kusa da yardar ALLAH, kayi haquri kayafi d’an uwanka ka jawosa ajiki don yanzu babu abunda yafi buqata sama da haka, shizaisa ya dad’a nadama da kuma dana sani akan abubuwan da suka aikata.” “Maman Rashida nariga da nayi rantsuwa akan babu ni babu shi har sai yaje ya tonikke abunda suka binne shida matarsa, taya zan karya wannan rantsuwar .” “Haquri zakayi kayafe masa, ai hannunka bazai rub’e ka cire kayada ba, kabari tunda akwai hatsi sai in fiddar maka da kai.” “Maman Rashida..” “Haba babn nura bansanka da haka ba, kayi afuwa da yafiya ga sabba balle d’an uwanka.” Tayi saurin katsesa tana fad’ar hakan cikin sigar rarrashi da ban magana, badon baffa yaso ba ya amince da maganarta saidai ya tabbatar mata da cewa shi bazaiyi kaffara ba kuma bazai fidda kai ba, amma ALLAH yasheda ya yafe masa abunda yayi masa, maganar sulhu tsakaninsu kuwa sai lokacin da suka warware abunda sukayi tukuna, ganin hakan yasa dole itama tahaqura taci gaba salwantar masa da hankali tahanyar dad’ad’an kalamai har saida taga ya sauka daga fushin da yayi kuma yasamu natsuwa sosai sannan tamiqe taje takawo masa ruwan tukunya masu sanyi da abinci yaci yasha ya qoshi ta kaimasa ruwa ban d’aki yayo wanka sannan yanemi waje ya kwanta, ko mintuna uku da kwantawa baiyi ba wani nannauyan bacci yayi awon gaba dashi. STORY CONTINUES BELOW  Tare su baffa Usman da baffa Ali suka nufi inda yake tunanin sun binne maganin da aka basu, yawo suka sha sosai amma basu ga wajen ba saboda gaba d’aya anguwar ta canza tunda jiya ba yau ba, kusan yini sukayi suna kaida komo a tsakankanin wajen da baffa Ali ke tunanin sun binne maganin amma ya kasa ganewa don duk anyi gine gine wajen, ko banza shi tun daga ranar da suka binne maganin bai koma zuwa wajenba saidai idan hanya tabiyo dashi ya hango wajen hakan yasa yakasa tantace wajen, wani irin kuka ya fashe dashi had’e da cewa. “Kaicona nayi asara, na rabe tsakanin d’a da uba kuma na tab’ar da kaina, wayyo ALLAH na nashiga uku bansan meye makomata ba aduniya idan har nakoma ga ALLAH batare da yaron nan yadawo mahaifarsa ba ga mahaifinsa.” Haka yayita sabbatu shikad’ai yana kuka duqe agaban baffa Usman da alokacin wata damuwa ta taso ta lullub’e masa zuciya, ya rasa yanzu ko meye mafitar wannan al_amarin, matsalar sammu kenan, koda za’ayi addu’a to samun warakarsa yana ta allaqane ga karye surqullen da akayi, gashi shida suka aikata b’arnar yakasa gano wajen. Sunfi mintuna biyar awajen kafin baffa Usman yaduqa ya d’aukowa baffa Ali iccensa(crutch) na qafa da yake dogarawa daya saki lokacin daya durqushe agabansa yana kuka ya miqa masa had’e dasa hannu ya taimaka masa yamiqe shima yana sharar qwalla. Ji baffa Usman keyi kamar yayita dukansa saboda zafin abunda sukayi amma babu hali dole ya tunda yayi nadama kuma ya tuba, haka suka dawo gida agajiya baffa Usman yawuce shiyarsa Inna Bilkisu takawo masa abinci da ruwa tana yimasa sannu da zuwa, cike da damuwa yace a’a tabari yafara watso ruwa tukana sai yaci abincin shida d’an uwansa. Shi kuwa baffa Ali zaune yayi bakin rumfa ya aza kansa saman iccen da yake tokarawa (crutch) yana kallon shiyar tasa kaca kaca ba wanda ya gyara asalima Inna ruqayyar bata nan tana wajen yawon baransa, gaba d’aya sai yaji ya muzanta awajen wasu zafafan hawaye nazubo masa afuska, tunani ya shigayi lokacin da yana Alinsa yanda Inna ruqayya ke nan nan dashi sai gashi yau ya rasa madogara, gashi da ransa Amma komai nagidansa yafi qarfinsa, abinci ma sai in Inna ruqayya tabashi shi ko yusuf idan yaje yanemo ya kawo masa, amma ita ko mutuwa zaiyi bata bashi acewarta tunda yasamu damar da zaije yayi bara ataimaka masa amma yaqi to ita kam bazata sake ci dashi ba yana zaunensa gida, haka yayita tunane tunanensa har baffa Usman yafito wanka Inna Bilkisu ta shimfid’a masu tabarma acan zaure takai abincin da ruwa ta ajiye masu had’e da ‘yar redion da baffa Usman ke sauraren labaran duniya, Kallonsa yayi had’e da cewa. “Ali taso muje muci abinci ko?” Ya d’ago kai ahankali had’e da cewa. “Naqoshi Usman, ko kad’an bana sha’awar cin komai yanzu.” “To taso muje can ko kuma nazo nakai maka ruwa kaima ka watsa ko karage gajiyar kafin ruqayya tadawo.” “A’ah bari dai in shiga ciki.” Yafad’a yana tsille da qafa yana qoqarin shiga cikin rumfar, saurin d’auko masa iccen da yake tokarawa dashi baffa yayi had’e da taimaka masa ya daidaita shi sannan yace. “Ali kacire damuwa mu zauna mu natsu musamo mafita, damuwar da kake qara cilla kanka aciki bafa zata haifama komaiba sai wahala, tunda dai har kayi nadama to kayi Imani da qaddararka mai kyau da marar kyau, in Sha ALLAH zaka samu mafita.” Nan ma kukan ya sake fashe masa dashi saida yayi daqyar yasamu suka koma zauren, Inna Bilkisu dake tsaye gefe ta shiga girgiza kai cike da tausayinsa, Wai yau alin da tasani ne fitinanne da hatsabibanci ke russunawa duniya haka, lallai rayuwar duniya ba komai bace kuma batada tabbas ko kad’an, sanin yana matuqar son fura yasa tashiga d’aki ta d’auko dawon da tasaye d’azu tunda taji yace bazai iya cin abincin ba ta dama masa takai masa acan zauren ya d’ago kai cikin sanyin murya had’e da cewa. “Sannu balkisu, nagode ALLAH yasaka maki da alkhairi.” “Amin ya rabbi, ka d’aure kasha furar ko kad’an ce, ba a biyewa damuwa azauna da yunwa domin had’uwa sukeyi waje d’aya su illata mutum.” STORY CONTINUES BELOW  Har zata fita yakira sunanta tadawo, ya sake fashewa da kuka tare da roqonta tayafe masa abubuwan daya yimata don ALLAH, da yake mace ce mai raunin zuciya nan take sai itama tafashe da kukan tana fad’in. “Ali nayafe maka duk abunda kayi mani wanda kasani da wanda baka sani ba duniya da lahira, kuma Ina roqon kaima ALLAH ya yafe maka ya dawo da hankalin iyalinka agareka ta zauna ta kula dakai kaima.” Girgiza kai kawai yayi don yasan inna ruqayya bazata tab’a hankalta ba sai ranar da duniya ta hankaltar da ita, “nagode sosai Bilkisu ALLAH ya albarkaci yaranki yakaresu da rud’in duniya.” Da ita har baffa Usman suka amsa da amin sannan tabar wajen, kallonsa baffa Usman yayi had’e da cewa. “Ali idanfa kana tuna abubuwan da suka riga suka wuce to tabbas ka dingi kuka kenan har iya qarshen rayuwarka, Ina baka shawara kayi haquri ka godewa ALLAH daya ganar dakai kafin lokaci yaqure maka.” Saida ya goge kwallan da suka zubo masa sannan ya saki wata ajiyar zuciya had’e da cewa. “Dole na zubda hawaye Usman, wallahi aduk lokacin da naga kuna hidima dani da yaran nan dake wajenku duk irin cin kashi da kuma mutunci da nayi maku sai naji waninirin nauyi da kunya sun dabai bayeni, nacutar daku amma gashi kunata kyautata mani, wlh da mutane zasu gane da sun daina cutarwa ga mutanen dake Shire da kyautata masu, don wannan abun da kike yimani shine mafi girman horon da kuke hukunta zuciyata dashi, zaifi sauqi ace cutar da mutum akayi kamar yanda ya cutar da adinga binsa da kyautatawa da kuma alkhairai domin yafi shiga kunya da nadamar da zuciyarsa zatayita d’awainiya da abubuwan daya aikata.” “Kamanta da komai, ni babu sauran zarginka ko kuma tsanarka araina, fatana ALLAH yayafe maka laifinka kuma yabamu mafita, din natabbata shi kad’aine zaisa yaya yasake baka damar jingina dashi akaro na biyu duk da dai tsananin b’acin rai yasa yakai ga yanke maka wannan hukunci amma inada yaqini akan zai sauko kuma ya yafe maka shima.” “ALLAH ya qaddara hakan, Amma girman laifina na cancanci hukuncin da yayi mani kuma koda ya gagara yafemun bayada laifi.” Yaqara fashewa da wani kukan. Haka sukaci gaba da maganganunsu baffa Usman naqara yimasa nasiha akan illar biyewa son zuciya da kuma sharrin duniya da rud’in shed’an har aka kira sallar magrib sukayi arwala suka wuce masallaci, bayan angama sallah baffa Usman yamiqe had’e da kallon baffa Ali yace. “Bari naje wajen Yaya naga halin da yake ciki ina tsoron kar shima yashiga damuwa irin yanda kake ciki!” “Shikenan bari nad’an gincira kafin akira sallar isha’i, seka dawo.” “To madallah, amma karka kwanta domin babu kyau bacci tsakanin sallar magrib da isha’i, annabinmu yayi hani ga hakan, zaifi kazauna kiyita yimasa sakati da zikiri da kuma hailala har akira sallar ko kuma ka d’auko qur’ani kayi tilawa, bari namaza naje na dawo.” Yana kaiwa nan yafice da sauri don baya son ya rasa jam’i shi kuma ya d’auko qur’aninsa yafara tilawa kamar yanda d’an uwansa ya shawartai. Koda baffa Usman yaje gidan baffa ya iskoshi tsakar gida ‘ya’yansa duka sun zagayesa anata fira ana dariya, murmushin jin dad’in ganinsa haka babu abunda yasamesa yayi had’e da qarasawa ciki yana fad’in. “Allah ya taimaki uban d’iya yaja da tsawon rai.” Yana wani d’aga hannu tare da dudduqawa kamar yanda fadawan sarki keyi gaba d’aya duk sukasa dariya hadda baffa tare da miqa masa hannu sukayi musabaha sannan yace. “Ai kaine uban d’iya malan Usmanu ko yau kabar mani d’iyan baka so.” “Inaaa.. Yaya nakai ga manyan d’iya haka tubarkallah kace in barmaka, ai Abba kawai ne banayi shida aka yimani rashin kara akansa.” Gaishesa suka shigayi d’aya bayan d’aya yana amsawa kafin akawo ga Abba yamiqa masa hannu yana fad’in. “Assalamu alaikum baffa barka da dare.” Lokacin yanada shekara goma sha biyu. STORY CONTINUES BELOW  Dariya baffa yayi had’e da kallon baffa Usman daya kama hannunsa yariqe gam yana dariya yace. “Aminina kenan, gaisuwarsa ba irin tasu bace.” Nan shima Baffa Usman yayi zaunensa akaci gaba da firar dashi har aka kira sallar isha’i yamiqe da sauri had’e da yimasa sallama sannan yabar gidan, yaso yayi masa maganar baffa Ali amma yanda yaga farinciki kwance afuskokin gidan yasa yafasa don kada yarusa masu shi izuwa damuwa aransa yana yabawa ‘yar ‘yar uwar matar tasa data iya gusar da yanayin damuwar da yayan nasa yafita dashi d’azun alokaci d’aya, tabbas Babu abunda yakai matar qwarai samun kwanciya da cikakkiyar natsuwar namiji aduniya.. Bayan anqare sallah duk suka nufi gida suna tafe suna shawara akan maganar da baffa Ali yafad’a cewa ya samu mafita akan maganarsu ta d’azu, Inna ruqayya zasu tuntub’a tunda tare sukayi komai da ita ya tabbata ita bazata manta wajen ba, damuwar d’aya ce shine daqyar in zata amince tagwada masu wajen tunda tasan sharad’in da malamin tsibbon nasu yabayar, daga karshe dai baffa Ali yace abarshi da ita zai san yanda za’ayi ta gwada masa don kai tsaye idan aka fuskanceta da maganar bazata yarda ba, da haka suka shiga shiga ya tadda ita zaune tsakar d’aki da gani bata dad’e da dawowa wajen baran ba ta bubbud’e qafafuwa ta zube kud’ad’en da tasamo tana qidaya, sallama yayi har sau biyu bata tanka shiba sai da yayi ta uku tukuna ta d’ago kai cikin tsiwa irin ta fitinannun tsofaffin matannan tace. “Kai nifa Ali ba nison tsarguwa, dolene amsa sallamar koko dai dolene, in banda gulma baka tashi dawowa ba sai yanzu da kaga ina kikkimtsa abunda ALLAH yabani, to ALLAH yasani idan ma da biyu kayi ko shishi (sisi) bazan baka ba, badai bazaka bara ba? To ni kuma bazan baka shishi (sisi) naba, in shigowa zakayi ka shigo bana son talla kawani hankad’e mani labule, dama haqoranta wasu duk sun fita shiyasa bata iya fad’an sisin da kyau take cewa shishi, batare daya tanka taba ya wucikkewarsa ya zauna gefen gado yana kallonta har tagama qidayar kud’inta sannan tajawo wata leda taciro lemu da biredi sai kuma nama atakarda tahauci abunta, qille bata raga ba har saida ta cinyesa tas batare data sammashi ko kad’an ba sannan tabuga gyatsarta tamiqe tana yimasa habaice habaice, dama shi kota bashi bazai karb’a ba don yasan haramun ne tunda roqa tayi ba bata akayi ba, kuma shi roqo baida kyau awani nassima an haramta yinsa inba da wata babbar lalura ba. So yake ya d’auko mata zancen amma ganin abubuwan da takeyi yasa yarasa ta inama zai fara, can dai yayi qarfin hali ya daure cikin yanayin da bazata kawo komai ba yace “Nikuwa ruqayya wai a inane muka binne maganin nan.”, juyowa tayi daga kan gadonta data haye had’e da cewa. “Lafiya kake tambayata?, Ina ai tare mukaje ko?” “Eh wlh, shaf namanta ko inane, kinsan anyi gine gine a wajen sai nake ganin kamar anginesa.?” “Hehehe ai nasani, tuntuni nake roqon ALLAH yasa wani ya gine wajen yanda shikenan babu yanda za’a iya tonesa amma har yanzu wajen na nan fili ba’ayi gini wajen ba, shiyasa kullum nake sa ido awajen kar wani d’an ta tsinanniya yaje yatone manashi muboni mu lalace.” Cikin wani farincikin daya kasa b’oyuwa a fuskar baffa Ali ya taso daga d’an kishin gid’awar da yayi had’e da cewa. “Da gaske ruqayya?, Kai Alhamdulillah wlh naji dad’i, a Ina ne?, Wane wajene ruqayya.” Binsa tayi da wani irin mugun kallo da zai tabbatar maka data fara zargin wani abu akansa kafin tace. “Kai Ali, kallanni nan Kar nake kallonka, wato kaje ‘yan iwan naka su lallashe maka baki don kawai sun taimaka ancire maka wannan ‘yar qafar taka data gama rub’ewa shine kakeso a tonikke maganin, ka manta da wannan karon ba qafa zaka iya rasawa ba rayuwarka ko tawa gaba d’aya ko?, to wlh saidai su mutu bazan fad’i inda wajen yake ba, ban shiryawa mutuwa yanzu ba don haka kaji dashi can dakai dasu d’in, iyyeee! Wato sun turoka tunda karasa qafa d’aya bari su ida sallama rayuwarka don baqar mugunta da mugun nufi, to aniyarsu tabisu wlh, na maji dad’i daka mance don Ina baqin cikin lalacewar rayuwarka yanzu Ali, kazama raqumi da akala sai yanda akayi da kai wato?.” STORY CONTINUES BELOW  Taqarasa maganar had’e da fashewa da kuka tanaci gaba da cewa. “Allah ya isa ga idrisu, da usmanun da baliksu, da waccan tsinanniyar ta tsallake (baba nusaiba) da waccan mokad’ad’d’iyar tsohuwar data nad’e waje d’aya ita Bata mutuba ita Bata rayuba, duk ita taja mana shiga wannan rayuwar da muke ciki yanzu data haifa tsinannen d’an daya zama silar guntule qafarka, wlh indai Ina raye su dashi har abada sai dai su haifo wani.” Shiru baffa Ali yayi yana kallonta cike da b’acin rai da wata irin tsanarta da bazai iya kwatanta adadin yawanta azuciyar saba, wato ita ba’ayi mata ALLAH ya isaba ita keyi har tana tsine masu, murmushin da yafi kuka ciwo yayi tare da cewa. “Duniya ce tafi bagaruwa iya jima ruqayya, yanzu ke ko aya bazata isheki ba ganin yanda nakoma nida Yaya hawwa kisan cewa annabi ya faku? Yakamata wannan qiyayyar da tsana da kuma d’aukar fansa ta tsaya haka, yakamata kimanta da komai kitubarwa ALLAHnki kamar yanda mukayi nida yaya, kiroqi bayin ALLAHn nan da muka zakinta suyafe maki kafin ta ALLAH takasance akanmu, ni daine abokin tarayyarki acikin wannan adawar da mukeyi, Kuma natubarwa ALLAH don haka kema ina roqon ki d’aki tuba mutaru mugyara laifin da muka aikata ko ALLAH ya dubemu da idanuwansa na rahama.” “Ali! Kanka d’aya kuwa, shin kaji me kake cewa?, to narantse maka da ALLAH indai don yaron nan yadawo kake yimun wannan wa’azin to wlh tuba ba yanzuba,” Arazane baffa Ali yace. “A’uzubillahi minashshaid’anir rajim, ruqayya idan baki tuba yanzu ba yaushe kike son tuba?, Kin manta da rayukanmu ba ahannunmu suke ba, kafin kituba ALLAH zai iya zare rayuwarki, Haba don ALLAH kiwatsar da wud’annan makaman yaqin naki idanko ba haka ba zamu farraqa tsakanin ni da ke don yanzu ni nagane gaskiya da kuma kuskuren dana tabiye maki muna aikatawa.” “Ahaf, kanka akeji ni bacci nakeji, indai kuskurene ai kai nabiyewa har nayi shi ba kace kabiye mani ba.” “Naji tunda ni kika biyewa to nagane gaskiya kema kigane gaskiyar don ALLAH kifad’a mani wajen da muka binne maganin, in Sha ALLAH Babu abunda zai samemu, idan ma yasamemu ai kinga zamu mutu muna masu baraa’a daga laifukan da muka aikata, ko banza ai dama zamu mutu ba tabbata zamuyi ba aduniyar.” Tsabar batada lokacinsa duk wannan surutan da yakeyi saidai yaji hansarinta, bubbuga kafad’arta yayi yana cigaba da roqonta amma tayi biris dashi tamkar da dutse yakeyi. Haka dai suka kwana babu wani Abu daya samu daga wajenta, da safe ma yadinga roqonta amma fir taqi tankasa ma balle yasamu amsa daga wajenta hakan yasa ransa b’aci sosai yarufeta da maseefa akan lallai lallai saita fad’a masa ko kuma yau babu inda zata fita da sunan bara yakama bakin qofar ya tare, hakan ko kad’an bai girgiza taba balle yasa tadamar da kanta saima cigaba da shirinta da tayi hankali kwance tana gamawa tanufi bakin qofar had’e da cewa. “Jaye kabani waje ko in ingijeka kasan qafa d’aya ke gareka.” “Ni zaki ture ruqayya?” “Kana wasa, to Bari kagani…” Ai kafin takawo baffa Usman dake fitowa daga cikin d’aki don tun jiya yanajin yanda suka kwashe da ita ya qaraso aguje yana fad’in. “Kul…wlh karki kuskura ki ingije Mani d’an uwa ko hukuma tashiga tsakaninmu, shashasha sakarya da batasan ciwon kanta ba.” Yaqare maganar tare da jaye baffa Ali gefe dake faman qwalla, zata fice tana suruttai yace. “Karka batta ta tafi, ita kad’aice mafitarmu kuma tunda arziqi bazaisa tafad’i komai ba akaita ga hukuma dole su zasusa tanuna wajen da kansu, don ALLAH Usman kada kubari tafita ku kira ko ‘yan sandane….” Ai kafin yaqarasa rufe baki Inna ruqayya najin yace ‘yan sanda ta arta dana kare duk da bawani gudu bane tunda tayi tsufan da batada qarfin da zatayi gudun sosai. STORY CONTINUES BELOW  Tunda tafita bata sake dawowa gidan ba har aka buge kwana hud’u saboda tsoron kada ‘yan sanda su kamata, kullum saidai taje can wajen wani shago cikin tasha takwana, baffa kuwa dama koda sukaje masa da zancen d’aukowa Inna ruqayya ‘yan sanda cewa yayi a’a su qyaleta bayason ‘yan sanda sukoma shiga sha’anin gidan saboda ya fahimci hakan naqara rura wutar tsana acikin zukatan ‘yan uwa wanda dama yanadaga cikin matsalar data haifarda sasu d’aukar fansa akan d’ansa Nuraddeen don haka aqyaleta, yana nan yana addu’a kuma yasa ayi masa sosai idan da rabon zaingana da d’ansa to ko yaushene zai dawo garesa, hakama ya sanarda little komai yace yatashi tsaye da addu’a sosai akan mahaifinsa in sha ALLAH zai dawo nan kusa bada jimawa ba, little yayi kuka sosai daga baya yakoma ga ALLAH yana fad’a masa damuwarsa, kullum cikin sadaka yake ga gajiyayyu tare da taimakon mabuqata da nufin ko meye ALLAH ka yayewa mahifinsa. Shi kuwa Yusuf dama baya nan balle yasan meke faruwa, yana can wajen karatunsa a.b.u zaria a matakin qarshe duk da baiso ma cigaba da karatun ba saboda atunaninsa yayi girman da daqyar in zai iya amma baffa yace dole sai yaje yayi saboda yarage masa ganin matsalolin dake cikin gidan da damuwa kuma yasamu ingantacciyar rayuwar da idan yayi aure bazasu samu matsaloli sosai ba tunda yanada iliminsa. Baffa Ali kuwa ko ajikinsa rashin dawowarta gida don yanzu ko ganinta baya sonyi balle yanemi sanin inda take, muneera ma batasan wainar da ake toyawa ba har aka buge wud’annan kwanakin hud’u, Ita kuwa Inna ruqayya abunda bata sani ba ashe wasu ‘yan iskan tasha na nan nayi mata kallon mahaukaciya suna dakonta ko yaushe, haka wata qatuwar mota duk marece sai tayi parking inda take zama an miqo mata kud’i kusan dubu uku, wannan dalilin yasa taqara yin zaunenta acan aganinta idan takoma gida bazata samu wud’annan kud’in da masu gidan arziqi kamar yanda take fad’a suke bata ba….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___97💎 Yau baffa Ali na bacci yadinga ganin kansa a inda suka binne maganin shida Inna ruqayya wai yanata tonon wurairai ita kuma tana masifa dashi tana rufewa, yana kaiwa bayan wani ginin wasu shaguna da akayi kusan qwara ashirin jere da juna yafara tonon wajen tana turesa sai ya tashi yaje yaci gaba da tono wajen ita kuma ta sake turesa haka sukayi tayi yana tonon wajen tana hanasa, can yaga kamar wata bulala daga sama ta sauko a laftawa Inna ruqayya ajiki tafad’i awajen some shi kuma yaji sautin muryar da bazai iya tantance kowaye ba ance yaci gaba da tono wajenne zai cimma maganin da yardar ALLAH. Firgigit sai ya farka daga baccin da yakeyi yaga ashe mafarkine yakeyi amma aransa yatabbatar da wannan wajen da akace ya tone shine inda suka binne maganin, bako shakka isharace akeyi masa kuma da yardar ALLAH kome zai faru yau sai ya tone wajen, goge zufan da yabi duk ya jiqe masa jiki ya shigayi yana karanto addu’o’i a bakinsa don mafarkin yamatuqar tayar masa da hankali, gashi lokacin qarfe uku nadare balle yaje ya sanar da d’an uwansa, dole ya haqura yakoma ya kwanta yanata istigfari da hailala da kuma tasbihi daga kwancen da yake har aka kira sallar asuba, yana jin baffa Usman ya qwanqwasa masa qofa ya amsa tare da jawo iccensa (crutch) wanda yake dogarawa yamiqe yanufi bakin qofar yabud’e yafitoa. Bayan angama sallar asuba ya zauna masallaci yayita tasbihinsa har rana tafito sannan yanufi gida, yana kaiwa bakin qofar gida ya tarar da baffa Usman shida baffa suna magana wacce akan d’an uwannasu ne baffa Usman yake roqon yayi haquri ya yafe masa, nan yafad’a masa cewa tun ranar da abun yafaru ya yafe masa amma baya buqatar alaqar komai tahad’asa dashi ko shekara nawa za’ayi har sai sun warware qullin da sukayiwa Nuraddeen. STORY CONTINUES BELOW  Baffa Ali na kawowa baffa ya miqama baffa Usman hannu sukayi sallama yabar wajen tun kafin ya ida qarasowa, binsa kawai yayi da kallo sannan ya qaraso wajen ya miqawa baffa Usman hannu suka gaisa fuskarsa cike da damuwa, ganin haka ya shiga kwantar masa da hankali har yake sheda masa cewa ai d’an uwan nasa ya yafe masa dama yafad’a masa b’acin raine yasa yayan nasu fushi dashi har ya d’au matakin daya d’auka akansa, gashi yanzu ya sauko abunda kawai yarage sukoma su rarashi Inna ruqayya tahaqura hakan shine zai ida daidaitawa tsakaninsa dashi. Baffa Ali yajima yana zubarda qwalla kafin ya d’ago kai ya sanarda baffa Usman labarin mafarkin da yayi jiya had’e da cewa. “Na tabbata wajenne Usman kuma zanje na tono wajen in Sha ALLAH, roqona d’aya agareka idan nura da Rashida sun dawo kace su yafemun, suyafemun abunda nayi masu, nayi nadama sosai, bansan abunda zai faru ba, zan dawo koko ta ALLAH zata kasance akaina.” Duk inda jikin baffa Usman yake yau saida yayi sanyi sosai, yamatuqar ji tausayin d’an uwan nasa domin gaba d’aya ya sare ma rayuwarnan ta duniya, yayi tuba taubatan nasuha tare da miqa wuyansa gaba d’aya, Qarfafa masa yayi tayi sannan yace sushiga cikin gida su, bayan sun gama karyawa sukayi arwala tare sannan suka nufi wajen tono inda maganin yake, Gaba d’aya zuciyar baffa Ali ta dake haka ya dinga shiga cikin juji har suka isa bayan shagunan, runtse idanuwansa yayi don yatuno daidai wajen kamar yanda ya gani a mafarki sannan yabud’e a hankali yanaci gaba da taku har ya isa wajen, kallon baffa Usman yayi had’e da cewa. “Kaga wajen nan in Sha ALLAH..” Bai jira amsar da zai bashi ba yafara saran wajen yana, wasu irin sautukka ya soma ji kala kala Wanda azahirin gaskiya d’aya d’ago kai ya kalli d’an uwan nasa shi bayajin komai, hakan yasa yaqara cire tsoro aransa shima yayi kamar baiji komai ba, sannu ahankali yafara cin karo da wasu abubuwa masu kama da mutane aciki suna yimasa gizo a fuska cikin ramen wani irin hayaqi ya turnik’e wajen had’e da wari Mai mugun d’oyi, jiri ne yafara d’ibarsa amma cikin qarfin hali yaci gaba da tono wajen har yakai ga qullin maganin, ji yayi kansa ya wani sarawa duniyar najuya masa yafara karanto addu’o’in faya sani ga baki, wata irin dariya yaji ansaki mai qarar gaske had’e da amsar addu’ar da yakeyi anaci gaba da karantawa. “Muma musulmi ne kamarka, muna sallah muna addu’o’i don haka baza kaci galaba akanmu ba har sai ka amshi saka makonka daidai da laifinka, bazamu barku ba kamar yanda kuka nememu to tabbas sai alqawarin ALLAH ya tabbata akanku kamar yanda mummunar makomarsa zata tabbata akanmu.” Yaji an fad’a cikin kunnuwansa tare da kecewa da wata irin muguwar dariya, kan yace wani abu yaga wata baqar mummunar halitta cikin sigar wani baqin hayaqi tana fitowa daga cikin ramen tare da nufatosa daga zaunen daya fad’i tun d’azu dafe da kansa, da sauri yasa hauyar dake hannunsa ya ida ciro maganin wanda kusan tare suka fito da wannan halittar ta lullub’esa sai dai baffa Usman dake gefe yaga iska Mai kamar guguwa tana nad’ed’e niya cikin jikin baffa Ali dako ganinsa bayayi sai dai muryarsa da yajiyo cikin wahalalliyar qara yana fad’in “Usman ka fiddo ashana ka qona wannan qullin maganin kuma kafasa tukunyar dake cikin ramin nan.” Cike da tsoro jikin baffa narawa yafiddo ashana dama sunzo da ita ya cinnawa maganin sannan yasa hauyar yaje cikin ramin ya faffasa tukunyar dake ciki bakinsa d’auke da addu’a yanayi yana kallon iskar data nad’id’iye baffa Ali, Yana gama fasa tukunyar yaga iskan yawani cure waje d’aya tare da duddun qulewa yayi can gefen daji yana gudu da qarfi shi kuma baffa Ali yashe awajen ko motsi bayayi wasu quraje duk sun feshikke masa tun daga fuska har zuwa tafin qafa, da sauri ya jefar da hauyar agefe ya qarasa wajensa jikinsa na rawa ya tallabosa yana jijjigarsa yana kiran sunansa amma ko yatsansa baya motsi, cikin qarar murya yace. “Ataimakeni…” Ko baki bai rufe ba sai ga mutane sun iso wajen, ganin yanayin da suke ciki yasama wasu shakku akan meya kawosu wajen, qilama wani abun zasuyi ALLAH ya mayar masu da abunsu don haka suka tafiyarsu, mutum biyu kad’aine suka tsaya suka riqowa baffa Usman baffa Ali aka tallabosa zuwa titi sannan suka tari napep aka sashi ciki baffa yayi masu sannan mai napep d’in yaja suka nufi asibiti dashi, tun kafin ya qarasa isa yakira baffa ya sanar dashi komai. STORY CONTINUES BELOW  Baffa na tsaye gefen gado yayi saurin zaunawa saboda wani irin jiri da yaji ya d’ebesa. Istigfari ya shigayi ALLAH yasa son kansa baisa asanadiyar rayuwa d’aya ba surasa har rayuka biyu, a wani gefe na zuciyarsa kuwa hamdala yayiwa ALLAH da akaci nasarar tono maganin yasan koba komai in Sha ALLAH d’ansa zai dawo hankalinsa kuma ya tuna dasu. Kamar antsikaresa yayi saurin miqewa yabar gidan ya nufi asibitin da baffa yafad’a masa cewa can suka nufa. Yana isa ana fitowa da baffa zuwa d’akin da zanyi jinya na ‘bangaren maza wato (male medical ward) don har angama dubashi babu abunda ke damunsa, ‘yar doguwar sumace kawai yayi sai qurajen da suka feshikke masa a jiki kuma Alhamdulillah ya farfad’o daga sumar har ansa masa drip bacci ya d’aukesa. Zuba masa idanuwa sukayi suna kallo cike da tausayinsa, tabbas duk bawan da ALLAH keso yakan nufesa da tubamawa kura kuransa kuma yaqara masa da jarrabawa don tabbatar da imaninsa, fatansu d’aya shine ALLAH ya yafi kura kuransa albarkacin tubar da yayi kuma taubatan nasu da tasashi sadaukar da rayuwarsa don jadda tubarsa ga ubangijinsa. Sudai likitoci sunyi masu bayanin babu wata matsala kuma in sha ALLAH kurajen dake jikinsa ma zasu b’ace saboda na infection ne acewarsu, amma kallo d’aya zakayi masa kasan yana jin zafin wud’annan quraje lura da yanda yake fitar da lumfashi. A b’an garen inna ruqayya kuwa safiya na wayewa aka ganeta a sheme inda take kwana jikinta duk jini, ashe daren jiya ‘yan iskan dake dakonta cikin tashar su kusan bakwai sunyo shaye shayensu suka farmata, saida suka qwace duk ‘yan kud’ad’enta sannan d’aya bayan d’aya suka dinga amfani da ita ko tsufanta da qazantarta basaji, mutum d’ayane ya ganesu a tashar yana qoqarin fitowa sai gashi ya hango wata baqar mota qatuwa tayi parking wajen wanda ganin motar yasa samarin guduwa na qarshen dake kanta ma riqe da wandonsa yabar wajen, anfi mintuna uku kafin yaga wasu qatti su biyu sun fito cikin motar suna kallon gefe da gefensu, har bakin shigowa tashar da can gefen da samarin suka arta dana kare saida suka dibo suka tabbatar ba kowa sannan suka sunkuci Inna ruqayya dake kwance a sheme wajen sukasa cikin motar kamar yanda mutumen ke bayani, tsoro da fargabar abunda ke iya faruwa dashi tasa yakasa fitowa har motar tabar wajen, can gabanin asuba sai gashi yaga motar tadawo su sake fitowa da ita da sauri sun ajiyeta inda suka d’auketa farko, shine bayan sallar asuba gari yafara wayewa mutane suka ganeta a inda tasaba kwanci yashe jikinta duk jini, babban abunda yafi d’aga masu hankali shine, ancire mata ijiya d’aya sannan anfasa gefen cikinta da alama wani Abu aka cira daga ciki anka mayar anka d’unke don har filista akwai wajen, ga qasanta sai jini kefaman fita wanda basusan dalili ba, gaba d’aya ancire yatsunta na hannun hagu dana qafar dama amma duk da haka fata mutu ba lumfashi nafita ajikinta, hakan yasa nan take shugaban tashar nazuwa yayi gaggawar kiran ‘yan sanda, ba’afi mintuna ashirin ba suka iso, yanda suka ganeta suma hankalinsu ya matuqar tashi, nan take yakira assibiti tunda da ranta bata mutu ba, tuni ‘yan sanda suka zagaye wajen da wannan d’oruwan zare da suke sawa idan wani abu yafaru da suke rubutawa (don’t across the line…) sukaci gaba da sauran bincike bincikensu kafin motar asibitin ta iso, Mintuna shabiyar suma suka d’auka kafin su iso ‘yan sandan suka basu damar isa wajen su d’auketa saboda subata taimakon gaggawa tunda da ranta bata mutu ba, amma kai kana kallonta ko ba’a fad’a maka ba kasan cikin azaba da bala’in rayuwa take, malaman asibitin na d’agota zanen dake rufe da jikinta daga qasa yafad’i, tsananin tashin hankalin abunda idanuwansu suka gane masu suda mutanen wajen yasasu sakinta, gaba d’aya abunda ya shafi al’aurarta daga qasa tsakankanin cinyoyinta anciresa wajen yayi jawur babu komai sai jan naman dake wajen, mutane kuwa ihu duk sukayi had’e daja da baya suna rufe bakinsa da qwalalo idanuwa, hatta ‘yan sandan duk saida sukayi baya saboda firgita, abunda rayuwarsu Basu tab’a gani ba azahiri ko a finafinan hausa ko littafai sai gashi yau agabansu sun gani da idanuwansu, tabbas ko ba’a fad’a ba kasan wannan aikin masu sihirce sihircene da tsafi suka yayyanke mata sassan jiki, STORY CONTINUES BELOW  Kan kace me tuni labari ya soma biye gari mutane sai rutatowa sukeyi cikin tashar don su tabbatarwa idanuwansu abunda sukaji ana fad’a, babu abunda yafi tsorata mutane irin yanda duk irin miyaku da cuwurwutar dake jikinta rad’ad’in baisa ta mutu ba, cikin qarfin hali da tausayawa d’aya daga cikin jami’an lafiyan da sukazo ta d’auki zanen ta nufi inda take da zimmar rufeta saiga wata irin guguwa daga sama tanad’o baqa qirin da ita ta turnuqe Inna ruqayya dake sheme wajen tana fidda lumfashi d’aya bayan d’aya, Banda qarar sautinta da kururuwa tana ihu babu abunda suke iya ji ko gani, wani irin ihu takeyi tana qarar da duk Mai sauraro zai tabbatar da cewa inba rahamar ALLAH ba babu abunda zaisa halittar dake fiddashi ta dace balle asa ran zata rayu, mutane kuwa duk wanda ka kalla yayi jugum yana kallon ikon ALLAH, wasu Kuma da qarfin hali suna vedioting ga wayoyinsu, Saida aka kwashe fiye da mintuna goma wannan iskan na juyi da wani qugi akanta ita kuma tana qara sannan ya b’ace. Koda likitocin suka dubata tuni rai yayi halinsa ta cika a bainar jama’a cikin wani mummunan hali tayi mummunar cikawa a idanuwan duniya bisa laifukka da zunubbai data aikata arayuwarta. _(wal iya zubillah, ALLAH kakaremu da mummunar cikawa kuma kasa sanya mu muyi kyakkyawar qarshe, dama haka rayuwa take, duk bawan dake aikata zunubi adoron qasa yaga ubangijinsa ya tona asirinsa to alamar yana qaunar sane sai ya hanzarta yin kyakkyawar tuba kafin lokaci yaqure masa, idan kuma kaga kanata sab’awa ALLAH ya qyaleka yana cigaba da baka nasara acikin alamurranka to kaiconka, wallahi talalace yayi maka, cikar wa’adi kawai yake jira yayi maka mummunar damqar da bazaka iya kuccewa ba, alokacin babu batun bud’ad’d’iyar qofar tuba agareka domin wuri ya qure maka, tabbatuwar alqawarin ALLAH akan kane kawai zai wanzu agareka, shikenan kazamo cikin tab’ab’b’u bayinsa kuma kayi asara, ya ALLAH ka aminta damu kabamu ikon tuba wa dukkanin laifukanmu da zunubbaban da muka aikata maka👏)_ Haka likitoci suka d’auki gawarta akaje akayi binciki akai, inda su baffa Usman na asibiti wannan labari yazo masu wanda dama sun san hakan zata faru kamar yanda d’an uwansu yayi masu bayani, ALLAH kenan! Wato duk abunda mutum ya aikata arayuwa da sannu zai dawo ya riskesa, batare da sun damar da kansu akan maganganun da sukaji nata yawo agari akanta da mutuwarta ba sukaje police station sukayi bayanin cewa sune ‘yan uwanta aka basu hannu sukasa sannan sukaje asibiti aka basu gawarta, bayan likitoci sun basu qwaqqwaran bayani akan binciken da sukayi suka gano cewa mutum bakwai sunyi amfani da ita har sau bakwai kafin tamutu, haka kuma cikin bincikensu sun gano ancire mata sassan jiki da dama kafin tamutu kama daga ijiyarta d’aya, dukkanin yatsun hannunta na dama da kuma qafarta ta hagu, haka kuma an yanke mata al’aura, ancir mata qoda d’aya da kuma mahaifarta wanda suna tsammanin aikin masu anfani da sassan jikine wato (secret society) amma sun miqa dukkanin bayanan daya dace ga jami’an tsaro Kuma in Sha ALLAH zasuyi qwaqqwaran bincike akai, baffa kam kuka yafashe dashi saboda tsananin tausayin irin azabar da ya kafin ALLAH ya amshi ranta, nan ma saida sukasa hannu ga wasu takardun sannan aka basu gawarta suaka tafi da ita gida don suyi mata wanka a sallaceta…. ••• ••• ••• A qasar malesia kuwa Dr nura na kwance akan gadonsa sai faman juyi yakeyi saboda tun kwanakin baya da suka shud’e ya soma jin kamar akwai wani Abu daya rasa acikin rayuwarsa amma meye? shine abunda qwaqwalwarsa takasa tuna masa, kwana biyu ma da suka wuce yaji wani d’aya daga cikin abokanan aikinsa ya ambaci zaije qasar Nigeria har yake tambayarsa wace qasa ce haka, yayi masa bayani, tun alokacin yake nanata sunan a qwaqwalwarsa kuma yake son ya tuno wani abun yakasa, kusan kullum haka yake don musamman yake shiga google ta laptop d’insa yayi searching akan qasar don kwata kwata tun lokacin da baffa yakirasa awaya yaji muryarsa har abun ya nemi zame masa tab’in hankali idan yana tunano muryar tasa ya dena amfani da waya, telephone kawaine dake ajiye d’akinsa yake amfani dashi kuma shima saboda idan za’a nemesa emergency ne a asibiti shiyasa ya ajiyesa, ayanzu kuwa ji yakeyi tabbass ya rasa wani abun awannan qasar da yakeji ana ambata, tun daren jiya yake jinsa ba daidaiba har zuwa wayewar safiyar yau hakan yasa yakasa bacci in banda aikin juye juye akan gadon nasa babu abunda yakeyi, can yaji wani irin abu ya tsirgo masa cikin kai tamkar an soka masa wani irin qarfe mai zafi aciki, addu’o’i yafara karantowa yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Wash..wash.wash!” Tun yana fad’a ahankali har ya soma sakin wata irin qarar da tasa abokinsa da suke gida guda amma kowane da part d’insa rugowa aguje, yana shigowa ya samesa kwance qasa a zube yariqe kansa, fita yayi waje ya kirawo mai gadin gidan nasu ya taimaka masa suka maidashi kan gado, saboda kusan yasan da matsalar Dr nura yasa baiyi wahalar kaishi asibiti ba ya bubbud’a wadrobe d’insa dake jikin bango ya ciro first-aid d’insa ya d’auko wasu allurai yayi masa don a tsammaninsa waccan matsalarce ta matsanancin ciwon kai da yake fama da ita idan ya matsawa kansa da tunani, kafin kace me, tuni wani irin nauyayyan bacci ya d’aukesa, bai farka ba sai kusan qarfe sha biyu da rabi, yana farkowa bakinsa d’auke da baffa cikin wata irin murya mai qarfi da zata tabbatar da cewa yadawoma tunaninsa yana bin ko ina da kallo….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___98💎 Da sauri abokin nasa dake zaune cikin d’akin gefe yana daddanna laptop d’insa ya tureta gefe yayo kansa tare da dafa kafad’arsa, cikin harshen turanci ya shiga tambayarsa lafiya?, Meke faruwa dashi ne?, meye baffa da yaji yafad’a?, dama shi d’an qasar Thailand ne babu yaren daya iya inba nasa ba sai kuma yaren turanci. Wani irin kallo Dr Nuraddeen yabishi dashi had’e da cewa. “Baffa mean dady, dt’s my father.” “oh! You mean father?, So why have you calling him?, what happened to your father!?” “Nothing..” yabashi amsa ataqaice kafin yafara qoqarin tunano abubuwan da suka faru ashekarun baya kafin zuwanshi qasar, a hankali yafara tunano fuskar mahaifinsa da mahaifiyarsa ranar da yaje police station ya iskota awani yanayi har zuwa abunda yafaru ranar da zai baro qasar da maganganun da yayi da baffansa kafin yatafi, anan tunanin matarsa Rashida data b’ata ya fad’o masa arai da sauri ya miqe kamar wanda aka tsikara yanufi inda wardrobe d’in kayansa suke, watso kayan qasa ya dingayi yana dube dube da alama wani abu yake bid’a, a hankali yake kiran sunanta yana fad’in. “Rasheedah!💔 Habibty!… habibty!!..habibty!!!.” A daidai wannan lokacin Rashida na kwance ita da ‘yan jikokin nata hassana da hussaina, gama karyawarsu kenan ta watso masu ruwa suna faman yimata rashin ji shine tasakasu agaba tace sukoma bacci itama baccin takeji, dama tuntuni aka dawo dasu wajenta saboda cikin da batool ke dashi tsufo kuma rigingimunsu na damunta sosai ko kad’an basa bari tahuta shiyasa little ya tarkatosu ya maido wajenta itama gimbiyar tasa tasamu tad’an huta kona wata d’aya ne kafin ALLAH ya sauketa lafiya, taji tsikar jikinta na tashi da wani irin fad’uwar gaba da bata tab’a jin irin saba, kwatsam taji habibinta gaba d’aya yau ya dawo mata arai, cikin wata irin rud’ewa da rashin kuzari ta tashi zaune tana fad’in, “habiby!, habiby!!..meyake faruwa da kaine?, hasbunallahu waniimal wakeel, tabbas akwai abunda ke shirin faruwa dakai, jikina nafad’amun haka innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun.” Muryar yaran da dama basu koma baccin ba tajiyo ta bayanta suna tafi da hannuwa suna zagayata had’e da cewa. “Habiby!.habiby meyeke faruwa da kaineee.” Sun maida abun tamkar waqa, abunda bata sani ba ashe maganar zucin da takeyi har tafito fili sun ji abunda take cewa, shine suka maida abun gaba d’aya tamkar wasa sai faman zagayarta sukeyi suna tafi suna maimaita maganar alokaci d’aya kuma suna dariya. STORY CONTINUES BELOW  Dariyar itama suka bata tasa hannu tajawo d’aya daga cikinsu wacce tafi rashin ji don itama bata fiye ganesu ba saboda tsantsar kamar da sukeyi da juna tana cewa. “Ja’ira zonan, wato so kukeyi ku koma yaran wofi ko? kun maidani sai kace wata abokiyar wasarku yau duk sai nayi maganinku?” ta d’aga hannu da niyar kai mata tulla a bayanta d’ayar tayi saurin riqe hannun tana fad’in. “A’a kaka, ALLAH kada ki doketa, kinsan fa ba kyau mugunta ke kike fad’a mana idan muka doki ikram” yarinyar su iman da shakur ce wacce kad’an suka girme mata, d’an harararta Rashida tayi kafin tace. “Jimun yarinya, cikamun hannu ko nahad’a dake, ai wannan ba mugunta bace, horone zanyi maku, kuda kuke tararwa ikram ku biyu kuyita cin zalinta ai shine mugunta ba nawa ba.” “To ALLAH bazaki duketa ba su abbanmu basa dukanmu, hussaina yi sauri ki gudu nariqe mata hannu.” Tafad’a tana qara qaqume hannun Rashida hannu bibbuyu har tana nishi, da sauri hussainar ta tashi daga jikin Rashida ta ruga bakin qofa tana fad’in, “cikata hassana kizo mugudu wajan kaka mama.” Sakin Rashida hassana tayi da sauri ta ruga wajen ‘yar uwar tata tana dariya suka fice daga d’akin suna yimata gwalo, murmushi Rashida tayi tanajin wata irin qaunar yaran har cikin tsakiyar ranta, idan tace zata iya banbance qaunar da takeyi masu da wadda take yiwa mahaifinsu to tabbas tayi qarya don bazata iya ba.. ••• ••• ••• Gaba d’aya duk yabi ya tone d’akin da kuma kayansa yana bincike binciken abunda idanuwansa ke matuqar mararin gani amma bai ganshi ba, abokin nasa yayi magana har ya gaji amma kota kansa baibi ba balle yasa ran tanka masa, wani irin kuka yafashe dashi had’e da duqewa wajen yanaji kamar ransa zai fita, Saida yayi abunsa mai isarsa sannan yamiqe jiki ba qwari ya kalli abokin nasa yace. “I most go back to my country, my nation, my everything…” “What!” Abokin nasa yafad’a tare da miqewa tsaye yana binsa da wani irin kallo na tuhuma, cikin yaren na turanci Nuraddeen yaci gaba da yimasa bayanin cewa tabbas yau zai koma qasarsa ta haihu, wacce ta renesa ta bashi gudun mawa arayuwa wato Nigeria, yaci gaba da fad’a masa cewa shi bai san me yafaru kanshi ba da har ya zauna wannan qasar har na tsawon wud’annan shekaru bayan yabaro mahaifansa da iyalinsa da alokacin baima san inda take ba, koma dai meye yau ba gudu baja da baya sai yabar wannan qasar yakoma qasarsa, yana so yasan awane hali iyayensa da iyalinsa ke ciki, suna raye ko sun mutu duka bai sani ba, meya faru dashi ne haka?, Yaqare maganar cikin kuka da tausayin kansa akan mezai je ya riska. Bai tsaya jiran wata shawara ba nan take ya shiga har had’a kayansa da duk abunda yake so tare da rubuta takardar ajiye aiki aqasar bisa dalilinsa nason komawa qasarsa sannan yafad’a toilet ya sakarwa kanshi ruwa, ya dad’e ruwan na dukansa kafin yayo wanka yafito yana jin wani irin yanayin da sharabon ya riski kansa aciki har ya manta, Kamar ance ya duba gefen gadon dake d’akin wajen bed side ya hango jikkarsa acan sakad’e wacce da itace ya zubo wasu kayansa da zaizo qasar, da sauri yaqarasa wajen ya cirota duk ta d’anyi qura duk da bawai sosai bane tunda shi mutumne mai tsananin tsabta akoda yaushe cikin gyaran d’akin da kakkab’esa yake ko kuma yasa ayi masa, Amma kasancewar bai fiye amfani da ita ba yasa ta d’anyi datti yasa wani d’an qaramin towel ya kakkab’e sannan ya bud’eta, abubuwan daya ta bid’a duk ya watse d’akin sune aciki wato hoton habibty d’insa da wayarta daya shiga part d’insu ya d’auko ranar da zai tafi, bin photon yayi da kallo yana murmushi saboda tsananin farincikin kallonta da yakeyi, ko yanzu ya habibtynsa takoma?, Shin anganeta ko kuwa?, Tana nan da ranta kota mutu?, Shin idanma tana raye tana tunawa dashi ko kuwa tayi aurenta da wani ta manta dashi?, Ina abunda ke cikinta?, Shin tahaifesa yana raye shima ko baya raye duka bai sani ba, Wud’annan sune tambayoyin da ya dinga yiwa kans kenan don ya tabbata tsawon wud’an nan shekaru daya kwashe baya nan dole sai d’aya daga cikin hakan sai tafaru, ji yayi zuciyarsa na wani irin bugawa da sauri da sauri wanda ya tabbata rashin fatan faruwar d’aya daga cikin abunda yake tunanine ya jawo hakan, addu’o’i yadinga karantowa abakinsa na neman tsari kafin yaci gaba da qoqarin kunna wayar Rashidar dake hannunsa amma taqi tashi. STORY CONTINUES BELOW  Murmushin qarfin hali yayi yana ganin wautarsa na tunanin cewa wayar zata tashi bayan yasan cewa jiya ba yauba, koba komai yasan cewa tuni baturin cikinta ya lalace ya dena aiki, miqewa yayi ya shirya kansa tsaf cikin qananan kaya suit royal blue sai farar riga ‘yar ciki da necktie shima kalar royal blue da d’ige d’igen fari acikinsa, kallon kansa yayi a madubi yaga yanda farin gashi yasoma d’an feso masa cikin kai yayi wani irin murmushi dake d’auke da ma’anoni kala kala. Takardar daya rubuta ta ajiye aiki ya d’auka ya saka cikin aljihu sannan ya nufi wata babbar psychiatric hospital da ake kira (Columbia Asia hospital) babbar asibitin masu tab’in hankali ce aqasar da ake matuqar alfahari da ita wacce aqarqashinta ne yake aiki, kai tsaye office d’in shugaban asibitin ya nufa wacce ta kasance macece ‘yar qasar China, cikin girmama ya shiga ya gaisheta da yaren turanci ta bashi izinin qarasowa ciki ya zauna, bayan ya zauna yayi mata bayanin abunda ke tafe dashi tare da miqa mata takardar ta karb’a, Saida tagama karantawa tsaf sannan ta linke tamayar tana kallonsa kafin tace. “Yana da kyau kafin ace kayanke wannan hukunci kayi tunanin makomarka, anan muna matuqar girmamaka tare da baka daraja kasancewarka zaqaquri kuma haziqin likita da muke dashi, bana tunanin cewa komawarka qasarka zai Haifa maka d’a mai ido saboda basusan darajar kaba, bazasu iya gane irin qwazon da kake dashi ba balle har subiyaka albashi mai tsoka da zai iya riqeka yanda kake buqata, Ina baka shawara da kayi zamanka anan, idan har salary d’in da muke biyanka ne beyi ba zamu lullunka maka shi har sau uku matuqar zakaci gaba da aiki damu.” Duk wannna surutun da takeyi da yaren turanci take yimasa shi kuma ya zuba mata ido yana kallo cike da mamakin yanda kowane d’aya daga cikin ‘yan qasashen nasu keda son Kai da son cigabar qasarsa sab’anin tashi qasar da a saninsa nada ba haka suke ba sai in ALLAH yasa yanzu sun canza, ajiyar zuciya ya sauke kafin shima cikin qwarewar yaren nasu na turanci da idan kaji zaka d’auka dashi aka renesa har ya girma yayi murmushi had’e da cewa. “Ina bada haquri mah! tare da yimaku godiya sosai bisa karramawar da nake samu daga wajenku akoda yaushe, kalmomi kawai bazasu iya tabbatar maku da hakan ba amma daga qasan zuciyata zanci gaba da alfahari da aikin da nayi a wannan asibitin taku tare da yabawa agareku aduk inda nashiga had’e da kuma addu’o’in fatan alkhairi har iya qarshen rayuwata, kuyi haquri! Bazan aje aiki bane don bana so ko kuma don qasata, zan aje aikine saboda ni Ina buqatar qasata awannan lokaci kuma Ina son nakoma cikinta a matsayin cikakken d’an qasar dake alfahari da ita, qasata uwace mai matuqar girma da daraja, qasata uwace data reneni kuma tabani ingantaccen ilimi, Bata barni ahaka ba har saida ta turoni don insamu ilimin da zan taimaketa da ‘yan uwana dake cikinta tare da bani cikakkiyar kulawar da duk yakamata, ashe kuwa wannan uwar baici na wofantar da itaba, baici namance da nauyin mutanen dake d’auke a kanta ba tana basu kulawa wud’an da sun kasance sashen jikina da kuma rouhina, ni Dr N.I ALIYU na amince zan ajiye wannan aiki koda zaku yimani salary da zalar gwalagwalai ne, kuma nazab’i na koma qasata in tayi mata bauta koda bazasu bani naira ba acikin kud’insu domin sun cancanci haka, infact ina da buqatar iyayena, iyalina, ahalina, abokanaina da kuma ‘yan qasata don haka zan koma garesu.” Shugaban makarantar data bud’e baki tana kallonsa had’e da sauraren kalaman da yakeyi bata san lokacin da wasu hawaye suka zubo mata ba tashiga tafa masa, sosai ya burgeta yanda yanuna mata yana kishin qasarsa kuma yana martabata haka, kawai dai taji ba dad’ine saboda rasa zaqaqurin likitan daya san aikinsa da zasuyi shiyasa tazubar da qwallah, miqewa tayi had’e da miqa masa hannu daidai lokacin da shima ya yamiqe daga zaunen da yake ya miqa mata hannu sukayi sallama sannan tayi masa bayanin yanzu zata gabatar da takardarsa zuwa can samanta don haka ya kasance cikin shiri ko yaushe zasu nemesa. Ko kad’an baiso hakan ba don a ranar yaso barin qasar amma hakan ta cutara saboda basu nemesa ba. Nan take yashiga sa duk wasu qaddarori daya mallaka kasuwa ya sayar dasu, hatta gidan da yake ciki da motocin hawansa guda biyu duka ya sayar don dama gidan sane yayiwa abokin nasa d’ahiri ya zauna, yanzu kuma da zai bar qasar sai yakoma wani wajen shi kuma ya saida abunshi, Saida aka kwana biyu sannan aka nemeshi wajen aikinsa ashe wata gagarumar walima suka shirya masa don karramasa da kuma appreciating d’insa akan qoqarin da yayi wajen kawowa asibitin tasu cigaba sosai. STORY CONTINUES BELOW  Cek d’in maquddan kud’in da idan aka canzasu i zuwa na qasar nageria zasu kai kimanin miliyan ashirin da wasu d’aruruwa akai suka bashi tare da kambun karramawa a matsayin qwararren likitan da yafi iya kula da marassa lafiyansa da kuma kambun likitan da yafi kowa hazaqa da kuma sanin aikinsa, yayi masu godiya sosai bisa karramawar da suka yimasa bazai tab’a mantawa dasu ba sannan aka watse bayan anci ansha anyi hotuna Wanda mafi yawa daga cikin ma aikatan asibitin na sama dana qasansa Saida sukayi qwallar rabuwa dashi kuma sun tabbatar masa da yanada alfarma a asibitin ya turo duk wanda take son a d’auka aiki matuqar ya amince da hazaqarsa da kuma jajircewa, sannan shima suna marava dashi aduk lokacin da yayi sha’awar dawowa qasar yaci gaba da aiki dasu. Murmushi kawai Nuraddeen yayi aransa yana raya cewa shi da qasar waje kuma indai ba saudiya ba to sai bayan ransa, don ko kwana biyun daya qara saboda matsalar visa ne ita ta tsaida shi da tuni ya tafiyarsa qasarsa saidai suyi walimar ba dashi ba. Duk mutanen da yake huld’a dasu saida yaje yayo bankwana dasu har wajen shugabar makarantarsu inda yayi karatu da ita tafara riqesa don awajenta ya zauna kafin yakafu da kansa, matar kama itama yanzu ta tsufa sosai yayi mata bankwana bayan yamata bayanin zai koma qasarsa, tayi kuka sosai don ta matuqar sabawa dashi tamkar d’anta na cikinta ya yimata alkhairi sannan ya wuce. Dama tuni ya gyara komai yana dawowa abokinsa d’an qasar Thailand ya d’aukesa zuwa airport, wani irin farinciki yakeji azuciyarsa marar misaltuwa awani b’angaren na zuciyarsa kuwa tsorone fal da fargabar abunda zaije ya isko qasar tasa bayan ya shafe tsawon wasu shekaru batare daya wai wayota ba. ••• ••• ••• Kimanin sati d’aya kenan kusan kullum sai hajia mama tayiwa baffa nasiha akan yayi haquri ya yafe ‘yarsa ta dawo gida, fushin ya isa haka ace shekaru kusan bakwai amma yakasa mantawa da abunda yafaru, tsananin damuwa da baqinciki yasa aduk lokacin da batool tayi yunqurin shigowa garin in ta tunada mahaifinta ya haramta mata shiga gidansu saita fasa, saboda bata san da wud’anne idanuwa duniya zata kalleta ba ace tazo mahaifarta inda iyayenta amma an hanata shiga gidan kuma matuqar tashiga garin bazata iya d’auke idanuwanta daga gidansu ba saboda qaunar da takeyiwa mahaifinta da ‘yan uwansa da kuma sauran ahalinta, hakan yasata haqura tun ranar da aka d’aukota daga garin aka kawota gidan mijinta bata sake waiwayar garinba saboda kada takasa bin umurnin mahaifin nata ta taka gidansu tsinuwarsa da yafetan da yace zaiyi sutabbata agareta, taci gaba da haquri cike dasa burin cewa zai sauko kowane lokaci ya nemeta ya dawo da ita cikin ahalinta ko don qaunar da yake yimata amma fushin zuciya yasa yakasa haqura har yanzu, hakan yasa haqurin mahaifiyarta ya qare take tunkararsa da maganar akoda yaushe kimanin sati d’aya kenan, kullum saita nuna masa illar abunda yayi na tsawon shekaru bakwai da abunda fushin nasa ke iya jefa ‘yar tasa aciki, yakanji zafi da rad’ad’in hakan da yayi shima amma yaqi fahimtar abunda take son fahimtar dashi, jiya da daddare bayan ya watso ruwa ya kwanta ita kuma tana gefen gado tagama sallarta ta shafa’i da wutri tayi addu’a tajuyo tana kallonsa yana sanye da farar riga doguwa jallabiya tayi murmushi. Murmushin shima yayi mata fuskarsa ba yabo ba fallasa yace. “Hajia mama lafiya wannan kallo haka.?” “Lafiya klw alhaji, cikakkiyar surarka da kamalarka na kalla naga irin zubin da ubangiji yayi maka na salihhan bayi dake da matuqar hangen nesa amma kai ka kasa fahimtar hakan balle har ka hango abunda nake son lusar da kai nan gaba, fisabillahi amatsayina na mahaifiya nagaji da irin hukuncin da kakeyiwa ‘yata, na d’au tsawon shekaru ina yimaka biyayya batare dana damu da akan daidai kake ba ko akasin hakan, nayita addu’a nayita jiran ranar da kai da kanka zaka fahimci kuskurenka ka gyara amma ka kasa, asalin sahabin manzon ALLAH (s.a.w) dake da sunanka tabbas yanada zuciya sosai amma ya kasance mai tsananin fahimta da saurin sauka da uzuri koda kuwa ga yarone balle babba, akwai qissarsa da aka kawo cewa wata rana yana zaune masallaci sai yaji wani bawan ALLAH na sallah a raka’ar farko ya karanta fatiha sai yakaranta qul a’uzu birabbin nas, yana jin haka ya tashi da sauri yaje gida ya d’auko takobinsa ya tsaya bayan wannan mutumen yana jiran yaji mezai karantawa a raka’a ta biyu idan ya karanta fatiha, sai yaji ya sake karanta qul a’uzu birabbinnas kamar yanda yayi d’azu.” STORY CONTINUES BELOW  “Mutumen na sallamewa sayyida umar ya kallesa yace wlh ka kuru, daka karanta wata sura bayan qul’auzu birabbinas dana sare kanka da wannan takobin nawa mai tsananin kaifi, sai mutumen ya tambayesa dalili sai yace baya halatta mutum ya karanta fatiha da wata surah a raka’ar farko idan ya tashi yin raka’a tabiyu yace yakaranto wata surar data yimasa dad’i sai kace mai karatun jarida, dolene yakaranta surar dake bima wacce yakaranta a raka’a tafarko ko kuma aya araka’a tabiyun, shiyasa nasan daga qul’a’uzu birabbinnas babu wata surah nazata zakayi wasa da alqur’anin ALLAH ne na d’auke maka kai sai naji ka maimaita surar wannan dalilin shiya qwaceka daga mutuwa a hannuna yau”. _(to sai mu kula yin hakan laifine acikin sallah, idan ka karanta surah araka’ar farko idan zakayi ta biyu to surah dake bimata zaka karanta ma’ana ta qasanta, idan kuma ayoyine to cigabansu zaka karanta, ubangiji ALLAH yasa mudace👏)_ kaga anan sayyidina umar yayi zuciya sosai da tasashi zuwa ya d’auko makami akan abunda yaji kuma yayi hasalar da tasa har yake tunanin zai iyayin kisa, amma da yayi haquri yabi abun ahankali har zuwa qarshen sallar bawan ALLAHn nan sai ya sauka daga fushinsa tunda yaji abunda yake tsammanin zai faru ba haka bane kuma abun bai faru ba, sai ya janye hukuncin da yayi niyar d’auka akan wannan bawan ALLAHn tare da yimasa bayanin da zai ilmantar dashi anan gaba, to don me kaima bazakayi koyi dashi ba?, Kayi haquri alokacin da kaji cewa abunda kake tsammani ba haka bane?, don mi bazaka janye hukuncinka ba tunda abunda kake gudun faruwarsa bai faru ba?, Don mi baza kayi uzuri ga ‘yarka ba kajawota ga jiki kafahimtar da ita dalilinka na rashin son aurenta da yaron wanda kagano hakan wataqil zaisa ta ilmantu akan girman soyayyar iyaye ga ‘ya’yansu ita kesa su yanke masu hukunci cikin b’acin rai saboda qaunar da suke yimasu don tsoron karsu fad’awa halaka.?, Maganar gaskiya ni baka kyauta mani kuma baka yimani adalci, idan kai baka buqatarta akusa dakai ni Ina son na ganeta akusa dani mu zauna tare muyi fira irinta uwa da d’iya, tafad’a mani damuwarta inbata shawara akai Amma duk saboda kai narasa wannan damar, wannan wane irin son kaine kake dashi haka, kullum kai kanka baka damuwa da damuwar kowa idan ba taka ba.” “idan ma hukunci ne kake yimata ai ya isa haka, izuwa yanzu itama tasan me ake cewa d’a da mahaifi, bana tantama duk yana cikin jarabawarta da ALLAH ya karb’e mata rayuwar ‘yarta saboda tafahimci irin girman soyayyar dake tsakanin iyaye da d’ansu ta fahimci pain d’in da iyaye ke shiga alokacin da wani abun da basa so zai sami d’ansu, b’acin haka ALLAH ya sake jarabtata tahanyar fasa jikinta aciro mata ‘ya’ya duk da kasancewar alokacin zata iya rasa rayuwarta, Ina tsammanin ta wannan fannin kad’ai izuwa yanzu tasan me ake cewa iyaye kuma tasan girmansu, to don me bazaka yafe mata ba, ko kafiso sai ranar da akazo aka cemaka tamutu ko kuma shi mijin nata daka tsana ya mutu sannan kafashe da kuka kace kayafe mata?, Alhaji umar” tafad’i ainahin sunansa wanda ya sashi d’agowa da qarfi yana kallonta, tabbas yau yakaita qul don bazai iya kawo rana d’aya ba d’aya tab’aji ta furta sunansa haka kai tsaye, Saida ta share hawayenta da tafin hannuwanta sannan taci gaba da cewa. “Ka rabu da mugun nama, ka rabu da dokin qarfe, ka yafi ‘yarka tazo garemu na roqeka da ALLAH da girmansa, idan kuma ba haka ba wlh wannan zuciyar taka bazata kaika ko Ina ba kuma zata sa kayi nadama mai yawa arayuwa don na tabbata har yanzu kana sonta kuma kana tsananin qaunarta fiye dani, yanzu haka ‘yarka nada tsohon ciki kuma shima tiyata za’a yimata akaro na biyu yarage gareka ka sauko daga fushin da kakeyi da ita ko kuma akasin haka, ita dai mutuwa rigar kowace kuma zata riskemu aduk lokacin da taga dama, ba lallaine afito maka da ita da raiba domin ba ahannunmu rayuwarta take ba don haka kana da damar canza abunda yakasa canzuwa cikin shekaru bakwai a cikin daqiqa d’aya idan kaso.” Tana gama fad’ar haka tamiqe ta lunke dardumar da tayi sallah akai sannan take ta watso ruwa ta dawo tanemi gefe ta kwanta, shi kuwa gaba d’aya yau kalamanta sun kashe masa jiki cikin sanyin murya yakira sunanta had’e da cewa. “A yanzu na fahimci cewa a cikin hukuncin da nayi nine mai laifi, a duk tsawon wannan lokacin Ina d’aukar ‘yata a matsayin ita keda laifi shiyasa na koreta daga gidannan, Amma yanzu Dana fahimci nine mai laifin yakamata nahukunta kaina tahanyar barin wannan gidan tunda shine hukuncin da nake zartarwa ga mai laifi, ALLAH shine sheda tuni nayafewa batool bana fushinda ita amma sai nakejin matuqar zanci gaba da ganinta wannan baqinciki data jefani aciki awancan lokacin zai iya cigaba da addabar zuciyata har iya qarshen rayuwata, shiyasa nakasa cewa tadawo gareni.” STORY CONTINUES BELOW  Ita dai Bata sake tankasa ba saboda ayanzu ta gama yanke hukunci akan zataje ta zauna da ‘yarta matuqar wud’annan maganganun da sukayi basusa ya haqura ba bazata sake cemasa ya haquran ba, dolene itama tagwada masa irin tata zuciyar awannan karon don tagaji, ganin taqi tankasa yasa shima ya juya ya kwanta kalamanta nayi masa yawo a qwaqwalwa, har akayi kiran sallar asuba Abba bainsamu ya runtsa ba daya rufe idanuwa batool yake gani, gaba d’aya hankalinsa yabi duk ya tashi babu wacce take so da gani idan ba itaba gashi dare yayi balle yakirata awaya yaji muryarta ko zai samu sassauci, ALLAH ALLAH ya dingayi safiya tawaye yakira ta har aka kira asuba, haka ya daure yayo sallah yadawo yayi zaune yana jiran har gari yafara haske yakira yanda hankalinta bazai tashi ba idan taga kiran amma da yake jiya bai samu wani isasshen bacci ba sai baccin yayi awon gaba dashi. A can cikin barcin nasa ya soma yin mafarkin daya matuqar tayar masa da hankali wanda bayan mintuna talatin da kwantawarsa ya farka cike da tashin hankali ya saki wata irin qarar da tasa hajia mama dake kitchen rugowa wacce saida ta karad’e gidan gaba d’aya, a yanayin data ganesa yana faman zufa duk da a.c dake kunne yasata ajiye fushin da takeyi dashi ta matso kusa garesa sosai tana fad’in, “Lafiy alhaji?..” ko rufe baki batayi ba saiga su uncle h da dawowarsu daga masallaci kenan sukajiyo sautin qararsa suka shigo sugani ko lafiya, Kasa magana yayi inbanda hawaye da zufan dake keto masa babu abunda yakeyi, a gefe gefensa su uncle h suka zauna suna goge masa zufan tare da sake tambayarsa, daqyar ya iya sake bud’e baki yace…. _Hi gusz, me yafaru ne da Abba?, Wane mafarkine yayi daya jefasa acikin wannan yanayin?, try and find it by your self🤣 the first person dana fara karanta comments d’insa naga yabada amsa daidai da mafarkin Abba to tabbas shi keda page d’in gobe sukutum in sha ALLAH, wannan alqawarinane in ALLAH yabani Aron rayuwa😅a kafta my fans🤞🏻luv you much😘_Da qyar Abba ya iya bud’e bakinsa yace hajia mama tamiqo masa ruwa, fridge taje ta bud’e ta d’auko gorar ruwa mai sanyi takawo masa ya karb’a ya bud’e marfin yafara sha da sauri da sauri tamkar wanda yakwana da yini bai sha ruwa ba har saida ya shanye ruwan tas sannan ya ajiye gorar saman bed side had’e da goge bakinsa, duqar da kansa yayi na mintota tamkar mai nazarin wani abun kafin ya d’ago kai yace. “Na shiga uku ni da kaina zan jawowa yarinyata shiga cikin wani hali da zan gwammaci mutuwata akan rayuwata, na tabka kuskuren da ayanzu ni da kaina nake tsoron qoqarin gyaransa saboda gudun kar abunda nagani yafaru.” STORY CONTINUES BELOW  Cikin rashin fahimtar wasu daga cikin maganganunsa hajia mama tace. “Kamar ya alhaji?, Taya bawa zaiyi kuskure kuma yayi nadamar aikatasa ace kuma yana tsoron gyaransa?.” Hawaya kwance a fuskarsa wanda ganinsu ya matuqar tayarwa da ‘yan uwan nasa da hankali ya sake d’agowa yana kallon ta had’e da cewa. “Sosai ina jin tsoron gyarasa kar mafarkin da nayi yanzu ya tabbata..” Kusan atare kafin ya rufe bakinsa su uncle h suka had’a baki wajen cewa. “Mafarki!” “Eh mafarki.” “Ikon ALLAH, to Yaya ai kai shi mafarki ba gaskiya bane, don haka bama tsammanin zai faru don ka gyara kuskuren daka aikata,” “A’a hussain, sau da dama mafarkin bayan sallar asuba ance yana zama gaskiya, bana son wani abu yafaru da batool domin bako shakka itace rayuwata, nasan zakuyi mamakin hakan dana fad’a lura da yanda nawofantar da ita na tsawon shekaru saidai abunda baku sani ba shine, duk tsawon shekarunnan narayune bisa d’imbin tunaninta safe, rana da kuma dare, nayi nasarar cin galabar zuciyata wajen korarta gidannan duk da irin son da nake yimata amma nakasa yaqi da qwaqwalwata da kuma ruhina wajen dena tunaninta, adaren jiya mahaifiyarta taganar dani abunda nagagara ganewa balle har na saurari gaskiyar da kuka yita qoqarin ganar dani, nayi nadamar abunda nayiwa ‘yata ta cikina kuma naquduri gyara laifina yau Amma kash nayi mafarkin daya girgizani kuma ya raunata zuciyata har nake tunanin bazan iya ba.” “Haba alhaji sai kace ba musulmi ba!, Kayi Imani da ALLAHnka kayi abunda ya kamata, kada kayi Imani da abunda kagani a mafarki, tun d’azu sai kambama al’amarin nan kakeyi kaqi ka sanar damu ko meye?” Uncle Hassan yafad’a cike da damuwa, juyawa hajia mama tayi don bata son yafad’i ko mafarkin meye don annabi yace idan anyi mafarki mai kyau babu laifi afad’a idan kuma akayi marar kyau to ayi shiru ayi sadaka sannan kada afad’awa kowa, gashi ‘yan uwan nasa na neman ya bayyana masu mafarkin da yayi Wanda ta tabbatar ba ai kyau bane tunda har ya shiga cikin irin wannan yanayin, wasu hawaye taji sun zubo mata tayi saurin sharesu don kada su karya mata zuciya ta wuce d’akinta tafad’a toilet ta d’auro arwala sannan ta shimfid’a abun sallah ta fuskanci ubangijinta tare da roqon ALLAH ya sauqaqa duk abunda yayi nufin zai jarabcesu dashi kuma kada ya d’ora masu abunda bazasu iya ba ko zai kautar masu da Imani, Shi kuwa Abba shiru yayi kafin ya d’ago kai ya kalli ‘yan uwansa had’e da cewa. _”Acikin baccina dana farka a yanzu cikin wannan yanayi nayi mafarkin batool ita da mijinta sun kamo hanya zasuzo nan kano suda yaransu ‘yan biyun data haifa sunyi accident, mijin nata ya mutu ita kuma ankaita asibiti anyi mata tiyata anfidda mata wasu jariran ‘yan biyu macce da namiji, babban tashin hankali ko data farko tasamu mental problem akanta sanadiyar buguwar da tayi, ankiramu bayan faruwar had’arin anbamu yaran nasu basuyi komai ba, Babu abunda ya samesu d’ayar kawaice ta yanke a gefen fuskarta, gaba d’aya na rud’e batool d’ina ta haukace acikin mafarkina, duk abunda nayi mata amma Bata yadda da kowa saini, hatta likitoci da mahaifiyarta dukansu takeyi, Babu wanda take ambata bakinta saini, Babu wanda take saurara saini, nikad’ai ke iya kusantarta Bata jimani ciwo ba, hakan yasa soyayyar da nake yimata naqi bari akula da ita yanda ya kamata a asibiti, da kaina na d’aukota na dawo da ita gida Ina kula da ita hatta yaran data haifa in bani na riqasuba nakais tabasu nono bata tab’a shayar dasu , ni daku munyi magani har angaji amma batool d’ina takasa dawowa hankalinta, ga mijinta ya mutu, ga qananan yaranta tabar mana da duk inda muka kallesu sai mun zubar da qwallan tausayinsu, gashi mahaifiyar mijinta ta kasa mantawa da abunda nayi mata wanda ku baku sani ba har tana kuka dani akan laifin dana aikata tare da tabbatar mani da kowaye ubansa, na matuqar girgiza daa mafarkina ya nuna mani mahaifin yaron dana tsana aduniya kuma nake shegan tasa duk da anfad’a mani shine mahaifinsa yazo a daidai lokacin da nake buqatar taimakon tawa yarinyar da zimmar taimakonmu ba tare dana san shine mahaifin mijin batool ba, inajin tsoro kar wannan mafarki ya zamo tamkar isharace akeyi mani da abunda zai faru da ‘yata da kuma mijinta….”_ STORY CONTINUES BELOW  Haka yaci gaba da basu labarin mafarkinsa da yayi wanda tun a farkon littafi ya zamo shine shimfid’ar wannan labarin har yakai qarshe yana Mai fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi, hatta su kansu saida sukaji jikinsu yayi sanyi don tabbas mafarkin nasa akwai ban tsoro da firgitarwa acikinsa, ganin yanda duk yabi ya sare yayi loosing hop d’insa yasasu qarfafa nasu zukatan ta hanyar rarrashinsa tare da maganganu masu dad’i da zasu kwantar masa da zuciya, suka nuna masa shi cewa mafarki fa ba gaskiya bane in sha ALLAH babu abunda zai faru, binsu yayi da kallo suka jinjina masa kai alamun tabbatar masa da abunda suka fad’a, don ya sake samun natsuwar zuciya uncle hassan yace uncle Hussain yakira masa shurahbil ya d’auko masa wayarsa d’aki, shiru yabiyo bayan na wasu mintuna sanadiyar wayar da uncle Hussain keyi sai ga shurahbil wanda shine d’an uncle Hassan na biyu yashigo sanye da doguwar rigarsa jalabiya riqe da wayar uncle Hassan da alama bacci ya tashi, Yana shigowa gaban Abba ya sake fad’uwa don bazai mantaba haddashi yagani cikin mafarkin don shine ma yayita kula da yaran batool kuma sanadiyar yaranne ya had’u da mutumen da shine mahaifin mijin batool har yakawo masu shi a matsayin wanda zai taimaki rayuwar ‘yarsa, har yaqaraso cikin d’akin ya gaishesu ya miqawa uncle Hassan wayarsa yafita idon Abba na akansa. Bugu d’aya uncle Hassan yayiwa wayar batool tashiga tafara ruri, cikin jin dad’i batool dake zaune tana karyawa little ya kawo mata wayar ta d’aga had’e da cewa. “Uncle h barka da safiya, antashi lafiya?” “Lafiya klw batool d’in Abba, ya kike ya nauyi?” Akunyace ta amsa da Alhamdulillah tana cigaba da cewa. “Uncle ya abbana yake, yana dai lafiya ko?” Kallon Abba yayi daya runtse idanuwa wasu zafafan hawaye na zubo masa jin shine mutum na farko da tafara tambaya kaf acikin ahalinsu wanda dama hakan yazame mata jiki aduk lokacin da tayi waya da d’aya daga cikin gidan shine take fara tambayar ya yake kafin kowa sannan yace. “Lafiya klw abbanki yake batool, ‘yan matayen namu suke?” “Suna wajen gwaggo uncle, kowa dai lafiya ko?” “Eh batool, ya maigidan naki?.” “Muna lafiya uncle, Wai yaushe Abbana zai yafemun nadawo areku uncle, Ina matuqar kewarsa da kuma ‘yan uwana sosai, kuroqamun yafiyarsa uncle kunga awannan karon ma likitoci sunce bazan iya haihuwa da kaina ba, Ina tsoron kada nakoma ga ubangijina abbana nafushi Dani don Allah kuce ya yafemun.” Taqare maganar tare dasa yatsa tagoge ‘yan qwallan da suka zubo mata tana kallon little dake faman mammatsa mata qafafuwanta, tsananin tausayin da taba uncle hassan yasa bai tsaya yin komai ba ya mannawa Abba da tun d’azu sautin muryarta da yake saurare tasashi rufe idanuwa qwalla na zuba wayar akunne. “Hello, uncle!.” Data fad’a daidai lokacin da wayar ta sauka akunnensa ya sashi saurin bud’e idanuwansa had’e da cewa. “He..he.hello Fatima!” Wata irin zabura tayi had’e da miqewa tsaye lokaci d’aya wanda seda abun cikinta ya juya tayi saurin dafe mararta tana qoqarin kiran sunan mahaifinta don gasgata abunda kunnuwanta suka jiyo mata, cikin rawar murya tace. “A.a.abbana!” “Na’am batool” yafad’a yana share hawayen idonsa, yanajin tashin sautin muryarta sadda take furta Alhamdulillah da qarfi tare da juyawa cikin qarfin hali ta kalli gabas tayi sujudush shukur sannan cikin muryar dake nuna kukan farinciki takeyi taci gaba da cewa. “Natuba Abbana ka yafemun, gaba d’aya rayuwa babu kai Abba wahalane da ita, nayi kuskure matuqa wajen kafiyawa abunda zuciyata keso duk da kuwa alkhairine sanadiyar nisan tani da kayi da kanka, bazan qaraba Abbana kayafeni.” STORY CONTINUES BELOW  “Ki kwantar da hankalinki batool nayafe maki, ni kaina tirsasa zuciyata kawai nakeyi akan saita haqura dake amma Ina matuqar shan wahala adalilin kewarki da akoda yaushe ke addabar zuciyata, idanuwana cike suke da mararin son qaninki akoda yaushe amma son zuciya da kuma sharrin iblis la’anannen Allah ya sani barinsu cikin qishirwar son ganinki, kiyafemun ‘yata bisa tsattsauran hukuncin da nayi agareki, kiyafemun haqqinki dana tauye tsakaninki da mahaifiyarki da kuma ‘yan uwanki, nayi nadama sosai kuma ina buqatar na kasance tare dake har iya qarshen rayuwata, kimanta da waccan hukuncin da nayi agareki domin mahaifiyarki ta nuna mani kuskuren yin hakan, ni mahaifinki ne kuma nan gidan kune bakida wani shamaki tsakaninki dashi har iya qarshen rayuwarki kinji ko ‘yatah!” “Eh Abbana, Ina sonka, Ina matuqar sonka Abbana don haka bazan tab’a kallonka a matsayin mai kuskure agareni ba balle har kanemi yafiyata, nice mai laifi gareka da bazan dena roqon yafiyar kaba har qarshen rayuwata, ka yafemun Abbana Ina matuqar qaunarka sosai.” “Nayafe maki ‘yatah nima ina qaunarki sosai.” Yafad’a yana dariya lokaci d’aya hawayen nasa na qara kwaranya, wanda ga dukkan alama wud’annan sun banbanta da wud’ancan don su na farinciki ne. Tun suna wayar a zaune har yamiqe sunaci gaba da wayar yana dariya, kallo d’aya zakayi masa kagano tsantsar farincikin dake tattare dashi saboda yanda wani annuri ke fita a fuskarsa, murmushi su Uncle h sukayi had’e da miqewa zasu bar d’akin yayi d’aga masu hannu alamun su tsaya wanda seda hakan yaso basu dariya, batool kuwa tuni tasamu qafafuwan little da shima farincikinsa ya kasa b’oyuwa tayi matashi dasu tanaci gaba da waya da mahaifin nata hankali kwance, Cikin sanyin murya tace. “Abbana Ina so nazo naganka, Ina matuqar kewarka sosai.” Wani irin fad’uwar gaba Abba yaji jin abunda ta fad’a da sauri yace. “A’a batool!, Don ALLAH kada kuzo kinji ko?, Ina ance tsohon cikine dake ko?, to kibari bayan kin haihu sai kizo kinji ko?” Shagwab’e fuska tayi tamkar tana gabansa had’e da cewa, “Abbana da sauran lokaci fa!, Sai 13 ga wani watan tukuna za’ayi aikin, nidai zanzo naganka abbana.” “A’a batool kada kizo kinji ko?” “A’a Abbana nidai kabarni inzo inyaso ko kwana ukune kad’ai sai nayi.” “Batool..” “A’a Abba nidai zanzo, ko baka yafemun ne ba?” Cikin rud’ewa da rashin sanin yanda zai fahimtar da ita ta gane me yake nufi, cikin wata irin qarfin murya yace. “Aaaaaa…, kada kizo nace batool kinji ko?.” Tashi tayi zaune a tsorace kamar zatayi kuka had’e da cewa. “To Abbana shikenan bazan zoba..” Tafad’i haka cikin muryar dake nuna hakan baiyi mata dad’i ba, d’an sassauta muryarsa yayi cikin sigar lallashi yace. “Sorry my dota kinji ko, kinga cikinki ya tsufa bai kamata ace kinyi doguwar tafiya ba, ki zaunawarki gidanki in sha ALLAH ni da kaina zanzo nadubaki.” “To Abbana Amma meyasa?” “Bakomai, ina shi mijin naki.” Yafad’i hakan don yabasar da maganar saboda baya son tayi masu tsawon da dole sai tasa ya amince mata da tazo d’in. Miqawa little wayar tayi tare da tashi tabar wajen tana kuka, meyasa abbanta zai hanata zuwa alokacin da take son ganinsa, halama ya manta da tsawon shekarun data kwashe tana jiran ganin wannan ranar? Kodai wani abun yafaru agidan da ba’aso tasani shiyasa abbanta saukowa daga fushin da yakeyi da ita?, gaskiya akwai boyayyen al’amarin dake faruwa da bata san dashi ba, badon haka ba yakamata ace shima zaiyi farinciki idan taje tunda yana son ganinta, wud’annan tambayoyin da wasuwasi ta dingayi azuciyarta tana kuka har zuwa lokacin da little yagama waya da Abba ya biyo bayanta, STORY CONTINUES BELOW  Sosai little yayi farinciki da zuwan wannan ranar da hawayen gimbiyarsa zasu dena zuba saboda kewar mahaifinta kuma yaji dad’in yanda mahaifinta ya nuna masa ba komai yanzu aransa akan auren ‘yar tasa da yayi ya fahimci abunda ada yakasa fahimta kuma ya roqesa yafuwa tare dasa masa albarka sosai…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _i will like to extend my gratitude in dis page to you my dear sister, *FATIMA UMAR ANKA (MOMYN J)* you’re truly among the most important people i have ever gotten in my life, you’re such a kind and very nice person dt i will never be able to forget, you did so much things to me sister!, the way you care, luv, respect, advice and so on to me is beyond the expected, all I pray, is ALLAH to protect you, guide you, luv you and take very good care of you every where you are, may he hills all your worries and put so many smile on your face, give you what ever you want in dis dunya wal akhira and make his jannatul firdaus to be your finale abode👏, thank you so much sister, FILLAH am rilly luv you more than how words can say😍_ Page___100💎 Yana shiga d’akin batool ta sake fashewa da kuka sosai ta yanda duk yanda yaso rarrashinta bazai iyaba, gaba d’aya tabi ta tayar masa da hankali, tun yana d’aukar abun zata gaji tagama har ya fahimci da hasken gaske takeyi bazata dena ba, hakan yasa ya d’auki wayarsa yakira mahaifiyar tasa ya sanar da ita halin da ake ciki, ita da kanta ta tabbatar da hakan lokacin da suke waya don tanajin sautin qarar kukanta, don haka tace masa yabata mintuna gatanan tafe. Ajiye wayar yayi gefe had’e da komawa inda take kwance idanuwanta sunyi lutulutu saboda kukan data dad’e tanayi ga fuskarta gaba d’aya tayi jajir abunka ga farin mutum, d’agota yayi tare da rungumota ajikinsa har lokacin tana kuka yace. “Gimbiya wai meyene haka!, Kina son jefa kankine keda babynmu cikin wani yanayine da bazaki haqura kidena wannan kukan hakan ba?, Ko kina so ne kiyiwa ALLAH butulci bisa baiwar da yayi maki ta juyo da hankalin mahaifinki akanki a lokacin da baki tab’a tsammaaanin hakan ba?, Ko so kikeyi ni kijefani cikin damuwa saboda kawai natsani ganin kukanki?” “Ni Ina son kawaine inga Abbana, karka manta wannan kukan bashine karo nafarko ba da nakeyi akan mahaifina, idan har zanyi kuka alokacin daya yimani kashedin zuwa inda yake make tunani idan aka hanani zuwa alokacin da da kanshi yabani damar zuwa wajensa?, don Abu sumayya ka kaini wajen Abbana Ina son ko sau d’ayane na sake ganinsa kafin ayimun wannan aikin! Ina matuqar kewar abbana sosai.” Ta sake saka mashi wani kukan had’e da tusa kanta cikin qirjinsa. A wannan karon kasa cewa komai yayi don tabbas yasan tanada gaskiya, musamman daya tuna shekarun data d’iba bata ganesa ba bayan tsananin shaquwar dake tsakaninsu, wani irin tausayinta ya rufesa tare dashi kansa da tunda yazo duniya sau d’aya yatab’a ganin mahaifinsa shima d’in ga tv ne bawai a zahiriba, bubbuga bayanta ya shigayi a hankali alamun rarrashi amma kamar yana qara cewa tayi kukan, bai tab’a sanin haka batool d’insa take da rigima ba sai yau, gaba d’aya tazame masa stubborn tayanda bama zai iya shawo kanta ba, Sallamar mahaifiyar da yaji tasa sashi saurin cire batool d’in ajikinsa da sai faman reren kukanta takeyi ko gajiya batayi. Da sauri yaje ya tarbota daga bakin qofar falo da take qoqarin shigowa tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “A’ah, a’ah Fatima har yanzu kukan kikeyi baki daina ba?, Subhanallahi meyayi zafi haka kekuwa?, Nan da lokacin da Zaki haihu ai kamar gobene ga ALLAH, don ALLAH kiyi haquri kidena wannan kukan hakan.” Rashida ta qare maganar tana qoqarin zaunawa kusa gareta. Gaisheta little yayi ta amsa tare dasa hannuwa ta d’ago batool, yanda take kukan baqaramin tayar mata da hankali yayiba musamman da taga yanda fuskar tata tayi ja had’e da kumbure sundul. “Ya Salam maman biyu, yau kece ahaka?, Kiyi haquri ni ban sanki da haka ba ko so kikeyi kitayar mana da hankali?” “To yi shiru kinji ko, ya isa haka, wannan kukan naki bana sonsa yana d’aga mani hankali” Tafad’i hakan tana share mata hawaye tare da d’ago fuskarta, “kinga yanda idanuwanki suka kumbura kuwa fatima?, Ai mugode ALLAH tunda har abban naki ya haqura ya sauko, kinga inda rabo bayan kin haihu ai zaku gana ko?” “Gwaggo idan namutu wajen haihuwar fa?, shikenan narabu da Abbana kenan na har abada?, Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun gwaggo don ALLAH kubarni inje inga Abbana tunda haihuwar nan da sauran lokaci..” Batool tafad’i hakan cikin wata irin disashshiyar muryar da ko fita batayi da kyau saboda kukan da takeyi. Shiru Rashida tayi tana nazarin maganarta kafin can taji tariqo hannuwan biyu tare da durqushewa gabanta. “Gwaggo inajin wani abu mai tsananin rad’ad’i yana kokuwa da lumfashina saboda son ganin Abbana da nakeyi, nasan irin yanda kika damu dani da d’awainiyar da kikeyi akaina a matsayinki na uwa kuma nasan bazaki gaza fahimtar irin kewa da shauqin dake tattare dani na son ganin mahaifina ba aduk tsawon shkarun nan da suka shud’e, a yau Ina roqonki daki amince mani kibada damar da zata saka nahad’u da mahaifina ko sau d’ayane kafin lokacin dazan haihe abunda ke cikina, nasan koda ta ALLAH tafaru kaina alokacin kunyimun alfarma mafi girma arayuwata.” Kallon little daya noce kai qasa hawaye na zubar masa Rashida tayi, tabbas tasan yau shima dole yatuna da nasa mahaifin wanda ko shakka babu ta tabbatar shi yasashi zubarda qwalla. Cikin sanyin muryar dake nuna itama zuciyarta tagama karyewa tace. “Shikenan batool, tashi ki goge hawayenki kije ki watso ruwa, ni zantafi nabar ‘yan biyu su kad’ai ad’aki suna bacci kada su tashi suyimun b’arnar daba daidai ba, zanyi tunani akan haka kafin anjima kinji ko.” Taqarasa maganar had’e da dafa kanta sannan tamiqe, d’ago kan da batool zatayi sai taga itama kukan takeyi da sauri tace. “Don Allah gwaggo kiyi haquri Idan na b’ata maki rai…” “Ko d’aya Fatima, kije kiyi abunda nace kuma ki tabbata kinci abinci kuma kinsha maganinki.” Tana gama fad’ar haka tajuya tafita tana sharar qwalla, yau little ya matuqar bata tausayin da tana buqatar taje tayi dogon nazari koda dangin mahaifinsa ne tahad’asa dasu, idan ma zai iya daga dubu d’ari har zuwa ko nawane zata bashi yaje koda qasar da mahaifinsa yazab’i zamane ya dubosa, tabbas tasan shi yarone mai matuqar biyayya da haquri badon haka ba da tuni shi da kansa yafara neman sanin yanda zai binciko mahaifinsa. Da yake da drivern gidan Dr tazo bata jira fitowar little ba ta shigewarta mota suka nufi gida zuciyarta namai qarfafa mata akan abunda ta quduri yi, Little kam gaba d’aya baima san fitar taba balle yabiyota baya har saida batool ta tab’asa yayi firgigit tare da fitowa daga dogon tunanin d’aya shiga yana goge hawayen idanuwansa. “Gwaggo fa ta tafi!” Da sauri yamiqe yafita amma koda yaje har motar data kawota ta jima da fita ya juyo yadawo cikin gida jikinsa sanyaye. STORY CONTINUES BELOW  ••• ••• ••• Tuni baffa da baffa Usman suka iso gida da gawar Inna ruqayya, ‘yan uwa da abokanan arziqi sai kuka sukeyi musamman idan sukaji ta hanyar data mutu, muneera kam da sauran ‘yan uwanta kam sunsha kuka har sun gaji, ba’a maganar Yusuf da alokacin yana makaranta yana zana jarabawarsa ta qarshe, saida su baffa suka yita bashi baki akan ya haqura ya zauna tunda zuwansa bazai iya canza komai ba, kuma zai iyasa ya rasa damarsa awannan shekarar sannan ya haqura amma yayi kuka kamar ransa zai fita da duk wanda yagani sai ya tausaya masa, Yaya hawwa ma kuka tayitayi tana nema mata gafarar ALLAH tare da tausayin kanta da batasan lokacin da itama tata zata risketa ba, haka gida yacika anata koke koke, Inna Bilkisu da wata maqwabciyarsu su suka yimata wanka, sunga tashin hankali matuqa wajen wankan domin wani wari gawarta ta dingayi gashi duk inda suka taba ajikinta sai fatarta tabiyosu tamkar kazar da akasa ga wuta tanine, gaba d’aya jikinta ya zimame nan take saika rantse gawarta tayi kwanakkine tasoma lalacewa, haka suka samu suka lallab’a sukayi mata wankan suka yimata sutura kowaccensu hawaye kwance da fuskarta. Haka aka d’auki gawarta akaje akayi mata sallah akaje kaita gidanta na gaskiya, ana saka gawarta akaga wani qaton maciji baqiqirin yafito daga qasanta tare da nad’id’iye gawar gaba d’aya, kan kace me kusan mutanen da sukazo wajen sun fice aguje saboda tsananin tashin hankali, baffa ne kad’ai da baffa Usman da wasu mutane qalilan suka tsaya, haka akayita qoqarin korar macijin har aka gaji amma yaqi fita daga qarshe baffa na hawaye yace. “Ya ubangiji kaine ka halicci bayinka kuma kai kake da iko akansu, ba’a shiga tsakaninka da bawanka akan duk hukuncin daka zartar akansa amma kai mai yafiyane tsakaninka dasu, rahamarka wadatacciya ce ga dukkanin wanda kaso sannan gafararka mai yawace ga bayinka, bamusan tsakaninka da wannan baiwar taka ba amma ALLAH kasheda duk abunda ke tsakaninmu muda ita musamman ni da nake da ikon kaina ALLAH nayafe mata duniya da lahira, ALLAH na yafe mata duniya da lahira ALLAH nayafe mata duniya da lahira Ina roqon kaima daka yafemata ya ubangijin sammai da qassai badon halinmu ba.” Yana gama fad’ar hakan yabada umurnin a rufeta haka dashi saboda basuda ikon hana abunda ALLAH ya tsaro, haka sunaji suna gani aka ida kakkad’a itace da ganyayyakin da za’a saka don babu Wanda zai iya shiga yajerasu yanda akeyi sannan aka ida tura qasa aka binneta sannan sauran mutanen suka watse kowa nafad’in albarkacin bakinsa akanta. Baffa da baffa Usman sunjima bakin kabarin nata suna kuka tare da yimata addu’a sosai kafin sutafi, Gari kam ko Ina ya d’auka irin yanayin mutuwar da Inna ruqayya tayi da abunda aka tarar kabarinta, wasu su tausaya mata, wasu suce haqqin baffane da suka d’auka da mijinta wasu suce haqqin jama’ane da tayita zalunta wasu kuma suce haqqin mijinta, koma dai meye musulmi bazai fidda rai ga rahamar ALLAH ba ana yimata addu’ar ALLAH ya gafarta mata. Baffa Ali ma daya farka ka sanar dashi cewa yayi hukuncin da yadace kenan da ita tunda taqi ALLAH bayan gaskiya ta bayyana agareta, bazaice komai ba sai masu irin halinta su d’auki darasi tun kafin lokaci ya qure masu kuma su tubarwa ALLAH, kana ganin yanayin da take magana kasan cike take da baqinciki da kuma takaicinta, Saida su baffa sukayi da gaske suna bashi haquri ya yafe mata kuma ya nema mata gafarar ALLAH sannan yana kuka yace. “Shikenan, nayafe mata a matsayina na mijinta Ina roqon dani da ita duka ALLAH kayafe mana, ALLAH ya sassauta mata ya lullub’eta da rahamarsa.” Kwanansa d’aya a asibitin aka sallamesa suka koma gida, alokacinne yayi kuka sosai don ya tabbata mai rabawa tariga tarabashi da ita musamman daya shiga d’akin sai yaji gaba d’aya kewarta takamasa dama mata da miji sai ALLAH, aranar kam baiyi bacci ba kwana yayi yana roqa mata gafarar ALLAH da kuma rahamarsa duk kuwa da rad’ad’in qurajen dake jikinsa dake damunsa. ••• ••• ••• Dr Nuraddeen kuwa kusan awarsu d’aya a filin jirgin kafin ya samu yaji ankira matafiya ‘yan qasar tasa wato nageria, cike da farinciki ya isa bakin matattakalar jirgin yana d’agawa abokin nasa d’an qasar Thailand hannu don tunda ya kawosa cewa yayi bazai tafi ba sai yaga tashinsa. STORY CONTINUES BELOW  Dama kai tsaye jirgin daya shiga kano zai sauka sai gashi gashi anyi sanarwa cikin jirgin cewa anaba dukkanin passinjojin ciki haquri saboda an samu matsala jirgin bazai iya qarasawa ba acan sanadiyar hazo da iska da suka yiwa sararin samaniya qawanya don haka ana bada haquri jirgin bazai iya sauka acan ba saidai a jahar borno, ko kad’an hakan beyi masa dad’i ba gashi da alama sai dare zasu sauka kuma babu wanda ya sani acan jahar balle yakwana awajensa kafin safe, tsaki yaja tare da aza kansa saman sit d’in jirgin da yake zaune yana furzar da wani iska ta bakinsa dake bayyanar da yanayin damuwar daya shiga. Haka kuwa akayi jirgin nasu bai sauka ba sai misalin qarfe goma da rabi na dare ya fito agajiye had’e da ware hannuwansa yana shaqar iskan qasarsa, a hankali yace. “Alhamdulillah, home sweet home!” Yanajin wani farinciki azuciyarsa alokaci d’aya kuma yanaji tana buga masa da sauri da sauri. ••• ••• ••• Rashida kuwa kusan yini tayi tana tunani had’e da kai da kawowa akan hukuncin da zuciyarta ke qoqarin yankewa, daga qarshe dai ta amince da little ya d’auki batool gobe yakaita taga mahaifinta saboda ba’asan halin ta rayuwa ba, kada suzo wani abun yafaru daga baya yayita damun zukatansu aqoqarinsu na ganin sun tirsasa zuciyarta akan abunda batada natsuwa dashi. ‘Dauko wayarta tayi takira little tace yazo shida batool tana son ganinsu, cikin mintunan da basu fiye ashirin ba sai gasu sun iso kowanensu cikin yanayin da Bata so ba, Murmushi tayi had’e da yimasu nasiha sosai akan yadda da dukkanin qaddarowar da ALLAH ya tsarowa bawansa sannan taroqi little daya yafemata akan hukuncin data yimasa na batason yayi mata maganar mahaifinsa da duk wani abun daya shafesa, tana hawaye ta kalli Batool tace. “‘yatah nafahimci damuwarki da kuma yanda kikeji a zuciyarki akan mahaifinki sanadiyar hakan yasa nima nafahimci irin jarumtar da d’ana yayi wajen yimani biyayya wacce natabbata idan kece bazaki iyaba saboda ke yarinya ce da bakisan ya ake b’oye zafi, rad’ad’i da kuma damuwa arai ba, sau da yawa nakanyi mamakin irin tsattsauran ra’ayin da kike dashi da kuma kafiya wanda yau sune suka lurar dani adalcin daya kamata nayiwa d’ana arayuwa, nagode maki sosai ALLAH yayi maki albarka ya kuma saukeki lafiya, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH gobe zakije kiga mahaifinki” “Kai kuma little Ina so yau kasani a matsayina na mahaifiyarka na amince maka uma na baka dama idan kukaje kacewa baba balarabe nace yakaika wajen dangin mahaifinka, kaje garesu na tabbata zaka rage damuwar da kakeji a zuciyarka kuma idan kundawo kanada zab’i kaje qasar malesia kanemo mahaifinka idan kanada ra’ayi idan kuma bakada nadai had’aka da danginsa kuma natabbata zasu rage maka kewarsa sosai. Suna can awani qauye da ake kira bebeji koda baba balarabe bazai samu damar kaika wajensu ba saboda yayarsa data hana tuntuni to kai kaje da kanka, idan kaje katambaya gidan marigayi aliyu gadanga, kakanka malan Idris Aliyu da ‘yan uwansa naciki sai kace akaika wajensa kayi masa bayani, na tabbata zai ganeka sosai don bazai tab’a mantawa da fuskata ba, kuma kayi qoqarin had’ani dashi awaya kafin kadawo.” Atare shida Batool suka rungumeta cikin jin dad’i suna godiya musamman little dake jin tamkar ya tashi sama don jin dad’i, duk dako yasan cewa yadad’e da saninsu amma amincewar da mahaifiyarsa tayi yaje da izininta ya bayyana agaresu shiya yimasa dad’in daya tabbata akwai nasara biye a bayan hakan, batool ma harda qwallan farinciki tayi amma tad’au alwashin bazata bari asan da zuwan nata ba sai sun bar garin don kar Abba yahana. Sun jima suna fira kafin suyi sallama da ita lokacin qarfe goma daidai na dare, dama tunda rana tayiwa su Dr bayanin komai wanda sud’inma suka qara qarfafa mata zuciyarta harta amince, hakama dady da umma takirasu ta sanar dasu, umma dai bata so hakan ba aranta amma jin dady ya qarfafawa Rashidar cewa taba little d’in dama yahad’u da dangin mahaifin nasa tunda dama shi yariga da yasan komai yasa tahaqura tace ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi, STORY CONTINUES BELOW  Saida suka biya wajen Dr da fatima sukayi masu sallama suka yimasu fatan alkhairi sannan suka tafi gidan dady nanma albarka sukayita saka masu hadda ammi da hajia nafeesa sannan suka kama hanyar zuwa gida zuciyoyinsu cike fal da farinciki, A daidai kan hanyarsu da zata kaisu gida idan sunyi yuton ta d’ayan titin sukaga mutum tsaye abakin titi da mita gefensa anbud’e gabanta da alama ta lalacene ana yimasu hannu, har zasu wuce sai kuma little ya tsaya mutumen ya d’an leqo ta gefensa had’e da cewa. “Don ALLAH ko zaka taimaka ka ajiye wani bawan ALLAH d’aya daga cikin hotels d’in dake kan hanyar nan? Babban mutumne na d’auko daga airport yace yau yafara shigowa garinnan sai kuma taxi d’ina ta lalace.” Kallon batool yayi sannan yace. “Ahh gaskiya da matsala, kace fa baqone agarinnan? kar fa muzo daga taimako kasaka mu a matsala.” “Haba bawan ALLAH, ALLAH dai yatsare, in Sha ALLAH babu abunda zai faru, nayarda da mutumen wlh sosai.” “Shikenan kace yazo, mudai da zuciya d’aya zamuyi.” Da gudu mutumen yaje yakira Dr Nuraddeen dake zaune cikin motar har baccin gajiya ya soma d’aukarsa, ya riqo masa jikkarsa har suka iso wajen motar su little ya bud’e masa baya ya shiga, kud’i Dr Nuraddeen yaciro aljihunsa da baisan ko nawa bane ya miqama drivern taxin cikin muryarsa mai sanyi yace. “Gashi bawan ALLAH, nagode ALLAH yasaka da alkhairi,” Baki bud’e drivern yasa hannu ya karb’a yana yimasa godiya tare da leqa inda little yake shima yayi masa godiyar yana cewa. “Don ALLAH kuyi haquri ku saukesa ko hotel d’in can tacan gaba.” “Bakomai in Sha ALLAH” Little yafad’a tare da Jan motar yabar wajen yana fad’in. “Barka da isowa yallab’ai, awace hotel kakeso mukaika, mai sauqin kud’i ko mai tsada?” “Duk wacce tasamu Alhamdulillah.” Dr Nuraddeen yafad’a yanajin wani irin fad’uwar gaba a tattare dashi haka shima little Saida gabansa yayi mugun fad’uwa da yaji muryarsa. Batool ma kasa haquri tayi Saida tajuyo da qarfi tana kallon sit d’in na baya saboda yanda taji kamanceceniyar muryar tasu duk data Dr Nuraddeen tafi kauri amma da yake duhu ya mamaye motar bata iya ganin fuskar mutumenba saidai ta juya cike da mamaki aranta…. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___101💎 A bakin wata katafariyar hotel naga little ya tsaida motarsa had’e dayin horn da sauri mai gadin dake zaune saman wata kujera a bakin gate d’in yana magana da wane dake tsaye gefensa ya ruga ya bud’e suka shiga, Saida ya daidaita tsayuwar motar tasa ya kashe sannan cikin girmamawa yace. “Alhamdulillah maigida mun iso, Ina fatan kuma zatayi maka?” Saida yayi Dr Nuraddeen yayi murmushi sannan yace. STORY CONTINUES BELOW  “To masha ALLAH, zatayi da yardar ALLAH.” Yafad’a tare da bud’e gambun qofar gefen nasa yafito had’e da jawo jikkarsa dake ajiye ya sagala a kafad’a ba tare daya damu da nauyin da take da shiba sannan ya rufe qofar yazo daidai saiti glass d’in qofar da little ke zaune had’e da miqa masa hannu, yana fad’in. “Madallah fa, nagode sosai ALLAH yasaka da alkhairi kuma yayi albarka.” Cikin rashin kulawa little dake amsa kiran da Rashida tayi masa daidai lokacin daya tsaya shima yamiqa masa hannu sukayi musabiha tare da cewa. “Ah ba komai maigida, ahuta lafiya saida safe” tare da tada motar yanaci gaba da amsa kiran mahaifiyarsa. “Little badai har yanzu baku Isa gida ba bayan kasan gobe akwai tafiya mai tsawo a gabanku?” Rashida tafad’a ranta a d’an b’ace. “Yanzun nan can muka nufa wani bawan ALLAH ne natsaya naragewa hanya, shine ma kikaji yana yimana godiya.” “To ba laifi, adai dinga kulawa ALLAH yasa ku Isa lafiya, kudaure don ALLAH ka riqamata kuyi duk shirin daya kamata kafin safe, yanda zakuji dad’in yin sakko kaji ko?” “To gwaggo in sha ALLAH.” Sannan ya kashe wayar daidai lokacin da take fitowa daga cikin hotel d’in. Dr kuwa yajima tsaye yana bin motarsu da kallo aransa yanajin kamar yasan bayin ALLAHn nan, koma dai meye yaron nada kirki sosai don ya kwanta masa arai fiye da tunani, Sam bayada rawar kai irinta samarin yanzu da rashin girmamawa, ya fahimci hakanne ganin tunda ya shigo motar baiga wani abun ya had’asa da iyalinsa koda kuwa magana ce balle sayesayen kide kiden da zakaga anayi a mota ankai volume qarshe anayi ana canza batare da andamu da wud’anda ke cikin motar ba, haka yanayin yanda yake magana dashi cikin girmamawa da martabawa shiyasa yaron yaqara burgeshi sosai aransa. Murmushi yayi sannan yasa kai yanufi cikin hotel d’in bayan yaga fitarsu don har saida motar tasu ta b’ace masa da gani sannan yabar wajen. Akan hanyarsu tazuwa gida batool ta kalli little tace. “Wai kasan wani abu Abu sumayya?.” “A’a gimbiyata sai kin fad’a.” Ya bata amsa had’e da juyowa yana sakar Mata murmushi, “Wlh muryar bawan ALLAHn nan yanda kasan taka, ni da farko ma da yayi magana saida natsorata bakaga sanda najuya baya Ina son naga fuskar saba?” Mangareta yayi ga kai had’e da cewa. “Yawwa ai kin tuna mani, wato don kinibibi mijin wata kike qoqarin kalla, to da izinin wa kikayi hakan?, Ai tun lokacin naso mangareki albarkacinsa kikaci don kar yaga rashin kunyata shiyasa na qyaleki.” Dariya ta dingayi sosai har tana kwantar da kanta saman kujerar kafin tace. “Oh ni batoolun Abbana!, Ashe kace abun yayi maka zafi haka, to i hak’uri ranka ya dad’e Abu sumayya abban hasssana da hussaina, gimbiyarka natuba ka yafeta bazata sake ba, Amma maganar gaskiya muryarku na yanayi sosai.” “Ko?” Yafad’a tare da danna hancin motarsa cikin gidansu da tuni mai gadi yana ganin isowarsu taso ya wangale masu gate d’in.” Saida ya kashe motar bayan yayi parking sannan ya juyo ya kalleta had’e da cewa. “Kinsan yanda ikon ALLAH yake, qilan qasar muce guda, hakan zata iya kasancewa amma dai ni banji hakan ba, kawai dai naji kamar na tab’a jin muryar awani wajen ne” Ya qarasa maganar yana dariya had’e da mintsilar mata kumatu. Dariyar itama tayi kafin tace. “Ahaf! Ai tara na tare da goma , wani wajen yafi muryarka da kakeji kullum.” STORY CONTINUES BELOW  “Bawani gimbiya kindai zama mayyata kamar yanda nake mayenki shiyasa kikejin muryar kowa na shige da tawa.” Yafice yana dariya don yasan yasan ya tsokalota tunda yafad’i hakan. Ita dai bata tankasa ba itama tasa qafa ta fito bayan ya zagayo ya bud’e mata gambun. Kusan kwana sukayi suna shiri tare da imagining yanda tafiyar tasu zata kasance gobe zukatansu cike da farinciki. ••• ••• ••• A can qasar malesia kuwa tuni gidan labaransu na redio da talevision suka d’auki harmar labaran komawar shahararren likitannan da akafi sani da Dr N.I Aliyu qasarsa, wanda hakan baqaramin jawo hankulan manema labaran qasar yayi ba, gashi gaba d’aya bayada lambar wayar da za’a iya samunsa hannunsa balle su tuntub’esa da kanun labaran don suji dalilinsa nayin hakan bayan yafurta cewa bayada alaqa da qasar ashekarun da suka gabata, hakan kuwa ba qaramin cece kuce yajawo ba ga mutanen qasar da kuma su kansu ‘yan jarida, Wanda daga qarshe har saida suka dangana da shugaban asibitin daya baro da kuma shugabar makarantar daya yayi wacce itace tazame masa tamkar uwa kuma uba aqasar, duk da dogon jawabai da bayanonan da suka samu hakan bai hanasu cigaba da yayata labaranba da kuma tofa albarkacin bakinsu ba akan hakan, aganinsu hakan da yayi tamkar butulcine yayi wa qasar tasu.+ Kan kace me itama qasar tasa ta nageria sun fara qoqarin mauar masu da raddi tare da son ganin lallai sai sun gana dashi ta kowace hanya kafin isowarsa, haka wani jami’in labarai yaci gaba da bin diddigi har saida yasamu sanin ko wane jirgi ya shigo daga nan yatuntub’i jami’an jirgin suka yimasa bayanin cewa, sanadiyar hazo da gajimare da suka yima sama qawanya yasa Basu samu damar sauke pasinjojin nasu a jahar kano ba suka saukesu a jahar borno, kuma sun bashi tabbacin yana cikin jahar tunda isowar dare sukayi, idan har zai bar jahar to sai zuwa wayewar safiyar gobe idan ALLAH yakai mana rai, Haka wannan d’an jaridar ya bawa abokanan aikinsa duk wani rahoton daya samu kafin safiyar gobe saboda shi d’an jahar adamawa ne. Wannan daren ya zamo wani irin dare dake cike da ban al’ajabi domin kuwa a b’angaren su batool farinciki bai barsu suka runtsa idanuwa ba haka ma Rashida kwana tayi tana salloli akan ALLAH ya qaddara wannan tafiyar tasu little ta zamo alkhairi saboda yanda ta koma jin jikinta ba daidai ba, Dr Nuraddeen ma haka, d’oki da fargabar yanda zai riski iyayensa gobe basu bari ya runtsa ba, ga b’angaren’ ‘ya jaridu da ‘yan gidan redio da talevision da sauran manema labarai suma kwana sukayi suna Shire shiren yanda zasu tarbi isowar wannan shahararren likita da labarinsa ya karad’e ko ina. Kowane b’an gare matse yake kuma qagare yake safiya tawaye don cimma cikar burin zukatansu. ••• ••• ••• A b’angaren Abba kuwa Yana gama waya da little yafad’a zaune saman katafaren gadon dake cikin d’akin tare dasa hannayensa ya dafe kai, Kallonsa su uncle h d’aya tsayar tun d’azu sukayi had’e da tambayarsa ko lafiya. Cikin raunin murya yace. “Batool ce, ta dage lallai sai tazo, Kuma bana buqatar wani abun ya sameta, don haka dole nabar garin nan gobe.” “Ka natsu da kayi hakan a ranka?” Uncle Hassan yafad’a tare da zaunawa kusa dashi, jinjina masu kai kai yayi uncle Hussain dake qoqarin zama kusa dashi a d’ayan gefen yace. “Shikenan ka kwantar da hankalinka, in Sha ALLAH gobe damu dakai duka zamu tafi, Amma Kuma kasa aranka cewa idan ALLAH yana nufin wanzuwar wani abunne akansu koda basu zoba to tabbas zai faru atawani sanadin daban saboda bawa bai isa ya kaucewa qaddararsa ba, Wanda muminin kwarai yazama dole yayi Imani da ita ya ALLAH mai kyau ko marar kyau.” Saida sukaga yad’an rage damuwa sosai sannan suka bar wajen suma suna masu addu’ar ALLAH ya kauda fitinar zamowar mafarki gaskiya. Ita kuwa hajia mama kwana tayi tana kuka tana addu’a da Abba ya sanar da ita yanda sukayi da batool, don ta tabbata yanda take da kafiya da tsattsauran ra’ayin irin nashi ALLAH kad’aine ya isa yahana zuwan nata gobe kamar yanda tafad’a don haka ta dage wajen roqon ALLAH daya sauqa masu duk wata jarabawa da zai yimasu yanda zasu iya canyeta, haka kuma tayiwa Abba tambihi sosai akan kuskuren da yayi nafad’ar mafarki marar kyau baiyi yanda annabi yace ayiba, sosai yasake shiga damu don ta fahimtar dashi cewa alqawarin ALLAH ne duk wanda ya sab’awa umurnin manzon ALLAH yabi son zuciyarsa to tabbas zaiga ba daidaiba, wanda hakan yasa tanace da addu’a tare da qasqantar da kai ga ubangiji akan idan zai jarabcesu to yayi masu wacce imaninsu ke iya d’auka don haka sai shima Abba yayi nadamar hakan daya aikata yaci gaba da roqon yafiyar ALLAH akan sab’awa karantarwar annabi da yayi cikin rashin sani da kuma neman saussauci acikin wud’annan al-amurran.••• ••• ••• Tun da asubar fari batool ta tashi ko nauyin cikin jikinta bataji tayi dukkanin abunda ya kamata, sannan ta tadashi suka hau shirin tafiya, koda qarfe takwas da rabi tayi suna qifar gidan Dr sun rakkosu bakin mota, a tsarin tafiyar bada su hassana zasuyi ba duk da taso hakan aranta saboda Abba yaga jikokinsa Amma saboda kawaici da kara da kuma alkunya ta kasa magana, suna shigewa cikin motar da zimmar tafiya suka ga ‘yan biyun sun rugo a gyare tsaf Rashida na biye dasu da akwatinsu, karb’a Dr yayi yana dariya had’e da cewa. “Lalle kinyi dubara kuma kin kyauta, yanzu nake zancen araina nace to ita wannan ‘yar tawa wayau zatayi masu ta gudu wajen abbanta bada suba bayan suma tagudar masu da nasu abban? Sai gashi Naga kin tasosu agaba, inaga maman little wannan kora da haline kike yimasu don kema kihuta da rigimarsu kwana biyu.” Saida tad’an dara sannan tace. “Aikuwa kamar kasani uncle, suje can wajen sabon angon nasu muma muhuta da qiriniyarsu kwana biyu.” Duk akasa dariya wajen tare da yimasu ALLAH ya kiyaye, suna qoqarin tashi Dr yaga tayarsu ta baya tayi faci yace. “Ashsha! Kai takwara ai tayar motar tayi faci.” Fitowa yayi yad’an dudduba had’e da shafa kansa yana fad’in. “Ahaf, sauri ya haifi nawa, to malama uwar zumud’i sai kifito, Bari naje nakirawo mai faci asa mana iska had’e da juyawa. Har ya kusa kai bakin qofa Dr yakirasa had’e da lalaba gaban aljihun rigarsa yaciro makullin mota sabo dashi ya miqa masa yana fad’in. “Karki tsaya b’ata wannan lokaci, jeka kaciro waccan sabiwar motar da shekaranjiya ka kai aka yimata service, Ina komai dai daidai ko ina andubata ko.” “Eh Abba, ammafa cewa kayi sai shahida zata dawo za’a lonceta.” “Manta da wannan, Kai da zakaje wajen surukinka babbar gaisuwa ta musamman da wajen dangin mahaifinka ai kai yakamata ka lunche mana ita muga yaya lafiyarta ko kuwa matana.” Dr yaqarasa maganar yana kallon ‘yan biyu da sukayi cirko cirko da alama sun matsu atafi yana dariya. Godiya litte yayi masa sosai cike da farinciki sannan ya amshi makullin motar yanufi inda take, bayansa Dr yabi yariqa masa suka cire ledar dake jikinta sannan yashiga cikinta bakinsa d’auke da addu’a ya fiddo tare da sake fita ya kwaso kayansu a waccan motar yazuba sannan suka sake yimasu sallama suka shiga suka tafi su Dr da ita rashidar da Fatima da sauran yaransu nayi masu addu’ar ALLAH ya saukesu lafiya bayan ya tabbatar masa dasu tafi ahankali har su isa lafiya don SANNU SANNU bazata hana tafiya ba…tunda har sun tashi dawuri. Suna kan hanya hajia nafeesa takira awaya don tun jiya sukayi sallama dasu tace mata gasu sun kama hanya a sakasu a addu’a, cike da jin dad’i tayita zuba masu addu’a tanaji tamkar tabisu taga irin farincikin da Abba zaiyi idan yaga yanda batool d’insa takoma fiye da yanda take son ta kasance akoda yaushe, tasan baqaramin dad’i zaiji ba musamman idan yaga ‘yan kyawawan jikokinsa. Suna gama waya takira hajia mama da Abba tayi masu albishir cewa Batool d’insu nakan hanya batare da tasan zullumin da suke ciki akan faruwar hakan ba. Suna gama wayar hawaye suka ratatowa hajiya mama a fuska, cikin tawakkali tare da miqa dukkanin lamurranta ga ALLAH tace. “Ubangiji ALLAH ya kawosu lafiya, dama nasan kafiyar batool bazata bari ta haqura ba, musamman yanda kullum take fata da d’okin ganin wannan ranar da abbanta zai jaye tsattsaurar katangar daya shata a tsakaninsu.” Kallon Abba tayi da fitowarsa kenan wanka yana goge jiki yaji abunda hajia nafeesa tafad’a yayi mutuwar tsaye awajen. “Kayi haquri ka amshi duk abunda ALLAH zai zo mana dashi duk da ni aqasan zuciyata banyi Imani da mafarkinka zai tabbata akansu ba, Abu d’aya nayi imani dashi shine, ALLAH yakan sassauta jarabawar bayin da suka roqesa kuma ya sauqaqa qaddarar daya tsaro zata faru akansu, don haka kawai ku haqura da wannan tafiya kuma muyi fatan ALLAH yakawosu lafiya.” STORY CONTINUES BELOW  Kasa cewa komai yayi yayi qarfin hali yagyara yaje ya sanar da ‘yan uwansa da tuni suma sun shiryo da zimmar tafiyar, nan take duk sai sukaji jikinsu yayi sanyi Amma sai sukayi qoqarin b’oye hakan don kar damuwarsa ta lunku. Arwala hajia mama tayi taje taci gaba da ganawa da ubngijinta akan ALLAH ya kawo masu su lafiya. ••• ••• ••• Dr Nuraddeen kuwa yana tashi da asuba bayan ya gama sallah tare da azkar yasamu manajan hotal din yace yana buqtar a bincika masa idan akwai jirgin da zai tashi zuwa kano yau ayi masa booking.. Nan take da yake sun gashi da maiqonsa ba’afi mintuna goma ba suka binciko masa amma jirgin sai zuwa Sha biyu da rabi na rana zai tashi, baiso hakan ba, gashi bazai iya doguwar tafiya ba saboda yanayin gajiyar dake tare dashi da wani iri da yake jin kansa saboda fargabar data addabesa kuma bazai iya bin motar kasuwa ba yasa dole ya haqura yace ayi masa booking dinsa hakanan. Tuni ma’aikatan airport d’in suka sanar da ‘yan jarida da ‘yan redio cewa shahararren likitan da ska buqaci subasu bayani akansa jirginsa zai tashi nan da awanni hud’u da rabi kamar yanda yayi booking da safennan. Kan kace me tuni manema labaran suka Isa filin jirgin bayan sun sanar da abokanan aikinsu dake kano cewa su zamo cikin shiri don wanda suke neman labaransa zai iso nan da awanni biyar da rabi masu zuwa. Lokaci na cika ya shirya cikin suit d’insa farare sai jar riga ta ciki da farin necktie yasa takalma irin cover shoe’s din nan suma farare sannan ya d’auki jikkarsa yaje ya biya charges din masu hotel d’in tare da yimasu alkhairi Mai tsoka suna ta jin dad’i had’e da yimasa godiya. Tsabar farinciki manajan da kansa ya d’aukesa cikin motarsa ya kaisa airport, Yanda yaga taron manema labarai ya tabbatar masa da cewa sun samu labarin dawowarsa kenan, cikin halin ko inkula yafito ya fara takawa zuwa bakin jirgin don tuni an soma kiran pasinjas don har sun soma makara, kasancewar tuni fuskarsa ta bayyana ga labaran qasar malesia yasa suna ganin fitowarsa sukayo ruuu kansa, sai dai yaga hasken kyamarori na bugar masa buska da wasu dogayen abun magana da aka karo masa, Fuskarsa ba yabo ba fallasa ya tsaya yana fuskantarsu daidai yana jiran tambayoyin da suka shirya yimasa, Wanda kai tsaye labaran suke tafiya ga kafafen yad’a labarai. Tunda suka fara tambayoyinsu bai amsa masu ko d’aya ba har sai da yaji sun saurara. Daidai lokacin Rashida ta shigo cikin falon su Dr da fatima na zaune suna kallon labaran da tun safe suke jin ana yayatawar dawowar wani shahararren likita, amma ko kad’an basu kawo hakan aransu ba cewa wai Dr Nuraddeen ne mijin Rashida, Saida sukaji cikin harshensa na turanci yafara amsa masu tambaya d’aya wacce ita kad’ai yaji zai amsa, lokacin Rashida na bayansu tayi mutuwar tsaye ganin fuskar da bazata tab’a iya mancewa da ita ba. _”Nadawo qasatane awannan lokacin saboda duhun da ALLAH ya yayemun dake kaina har nakasa banbance koni waye, Wanda shi kad’aine yasan dalilinsa na jarabtata da hakan, batun shekarun dana kwashe awaccan qasar batare dana waiwayo qasata ba shikuma rubutacciyar qaddarar rayuwata ce dako ina so ko bana so saita tabbata akaina, zancen iyayena, ahalina da iyalina Kuma…”_ kafin ya qarasa kawai sai akaga ya fashe da kuka tare da haye matattakalar da sauri. Ita kuwa Rashida sai jin kukanta kawai sukayi ta duqe wajen, cikin wata irin murya mai cike da ban tausayi tana fad’ar. “Ko kad’an bayada gaskiya, bazai iya wanke kansa ba, wannan kukan duka na kunya ne da nadamar abunda ya aikatawa qasarsa, iyayensa, matarsa da kuma d’ansa har taya zai iya bada wannan amsar bayan yasan tuni yabada ita ga idanuwan duniya.” _afuwan idan bakuji dad’in rashin had’uwar little da mahaifinsa ba, ko kad’an yau idan suka had’u a titi abun bazai bada ma’ana ba balle ya qayatar, SANNU SANNU dai bazata hana mu Isa wajen ba gobe in sha ALLAH, pls kuyi haquri kuma kusani cikin addu’o’in ku saboda zazzab’i na nema yayi Mani qawanya👏thanks all_ STORY CONTINUES BELOW  *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Gaisuwa tare da fatan alkhairi agareki ROUHINAH, *FATIMA TAMBARY (BATOOL)* Aminci ya tabbata agareki tare da dukkanin alkhairan Allah bisa soyayya da qaunar da kike nunamun, fatana ubangiji ALLAH ya baki miji nagari da zai kula dake har qarshen rayuwarki kuma yakare mana ke aduk in da kike, soyayyarki ga wannan littafi na matuqar faranta mani, ubangiji ALLAH yabar tare har a aljannah fiddausi👏_ Page___103💎 Tsaye sukayi had’e da qurawa motar idanuwa suna kallo, yayinda d’an jaridar naganin motar ya juya da gudu yanufi wajen riqe da makirfon d’insa hannu. Kafin kace me tuni manema labaran sun dandazo a bakin motar sai hasken kemarori kawai kake gani nafita tako ina tun kafin yafito, so yake yafito amma duk sun tare wajen babu ta yanda za’ayi ya bud’e gambun motar balle yasamu fitowa, hakan yasa yayi zaunensa aci yana kallon ikon ALLAH, wata motar jami’an tsaro ce naga ta shigo aguje wanda mataimakin gwamnan jahane ya sake turosu saboda sanin taron da ‘yan jaridu sukayiwa garin don kar wata matsala tafaru, tun kafin motar ta tsaya wasunsu suka dingi dirqowa daga samanta suna kukkutsawa cikin mutane da tutturesu gefe har suka iso bakin motar suna faman mazurai da idanuwa. Saida suka tabbatar an saki hanyar da zai iya wucewa sannan wani yasa hannu ya bud’e masa gambun motar, a hankali ya azo qafarsa waje kafin ya ida fitowa da gangar jikinsa gaba d’aya yana qarewa qofar gidansu kallo, tana nan ayanda yasanta babu wani sauyi atattare da ita balle jikin gidan, wata irin damuwa yaji tarufesa yana mai tuhumar kansa akan cewa duk laifinsa ne daya jawo wannan rashin samuwar sauyin da aka samu ako Ina cikin wannan shekarun atattare da iyayensa, ji yayi wasu zafafan hawaye sun zubo masa xubo masa a fuska ga ‘yan jarida kuwa sai famana aikinsu sukeyi na yimasa hotuna, cikin sanyin jiki ya fara takawa zuwa wajen yayin da su kuma su baffa dake kallon ikon ALLAH daya ishesu tun d’azu ganin yanda hankalin kowa yakoma akan wannan motar ana jiran fitowar ko suwaye aciki amma shiru yaqi fitowa suka fara qoqarin juyawarsu da nufin shigewa gida, suna juyawa suka sake juyowa da sauri saboda tozalin da idanuwansu suka yimasu da fuskar mai fitowa daga cikin motar da bazasu tab’a manta tab’a, cikin wani irin matsanancin mamaki baffa ya shiga nunasa da hannu, murza idanuwasa ya sakeyi yana son gasgata abunda suka gane masa, tabbas ba shakka wannan Nuraddeen d’insa ne, cikin karkarwar murya bakinsa na rawa yafara matsawa zuwa garesa yana cigaba da nunasa yana fad’in, “Sh..shi..shinefa Usman, d’a..d’ana ne nu..ra!,” “Tabbas shine ne yadawo Yaya, nuran mune bako shakkah.” baffa Usman yafad’a yana hawaye, baffa Ali kuwa cikin d’ingishin katakon da yake takawa dashi yanufi wajen Dr Nuraddeen dake nufowa wajensu idanuwansa na tsiyayar da hawaye saboda yanda idanuwansa sukayi masa tozali da iyayensa awani yanayin da ba hakan yaso ba, yanda ‘yan jaridun suka yimasa qawanya suna faman d’aukar hotonsa had’e da jefo masa tambayoyi kala kala suna Kara masa makirfon d’insu don neman amsa yasa ya shiga sa hannuwa yana tutturesu gefe don ya qarasa izuwa ga iyayensa dake tun karowa, tsabar saurin da baffa Ali keyi ya isa garesa yasa katakon da yake takawa dashi ya dinga gocewa daga hannunsa yana qoqarin fad’uwa, ganin hakan yasa Dr Nuraddeen d’aga qafa ya qarasa garesa da sauri ya riqesa yana binsa da kallo, zamewa qasan qafafuwansa yayi had’e da rirriqesu sosai yana kukan takaici da nadamar abunda ya aikata, cak Nuraddeen ya tsaya yana kuku cike da tausayin meya sami qaramin baffansa haka har ya rasa qafarsa, cak baffansa ya tsaya lokacin da sukazo dab dashi wata irin ajiyar zuciya ya sauke tare da rufe idanuwansa hawaye suka shiga zarya akan fuskarsa ya durqushe wajen had’e dayin sujada saboda tsananin farinciki, kuka baffa keyi sosai acikin sujadar yana kirari ga ubangijinsa had’e da washi da yabo daya dawo masa da d’ansa kuma gudan jininsa agaresa a lokacin da baiyi zato ba balle tsammani, yajima a hakan kafin baffa Usman da tsantsar farincikin dake kwance a fuskarsa ya kasa b’oyuwa yasa hannu ya d’ago sa, tsananin kukan da yayi yaqara karya zuciyar Dr Nuraddeen hannayensa na rawa yasa duka biyun ya riqo fuskar baffansa da gaba d’aya ya kasa magana sai binsa kawai yakeyi da kallo yana zubar da hawayen da tun d’azu suka kasa tsayawa, STORY CONTINUES BELOW  “Baf..ba.baffaa..” Dr Nuraddeen ya fad’a tare da jawosa ajikinsa, riqesa sosai baffa yayi tamkar wanda za’a kwacewa cikin muryar da tamkar yana rad’a yace. “Nurah..!” Cikin wani irin sauti dake nuna tambayarsa ce yakeyi wai shi d’in da gaske. Jinjina kai kad’ai Dr Nuraddeen ya shigayi wasu hawayen na zubowa a fuskarsa wasu bayan wasu tare da sake rungume baffa sosai ajikinsa, tun yana kukan marar sauti har yafara wanda kowa ke iyajin sautinsa da qarfi yana fad’in “Ka yafemun baffa..” Ciro sa baffa yayi a jikinsa Nuraddeen yayi saurin riqo hannayensa ya shiga marin fuskarsa dasu yana fad’in. “Ka hukuntani baffa, ka mareni sosai mana, ka dake da qarfi yanda zanji zafi kafin ubangijina ya hukuntani da kansa!, Kaico na kaicon rayuwata, mezan cewa ubangijina bisa butulci da wofantar da iyayena da nayi aduniya?, Ka hukuntani baffa na cancani hakan ko zaka rage rad’ad’in da kakeji azuciyarka, kayimun duk abunda zaisa kaji sanyi aranka baffa ko ubangijina zai yafemun zunubin haqqoqanku dana tauye dake kaina.” Kuka yakeyi yana marin kansa sosai da hannayen baffa har saida yagaji don kansa ya durqushe agabansa, gaba d’aya baisan ta Ina zai fara roqon mahaifin nasa wannan mummunan laifi mafi girma da yayi masa ba aduniya, duk ‘yan jaridun da motananen gari dake wajen suma sai hawaye sukeyi yayin da wasu suka dakata da d’auke d’auken hotunan suna kallonsu wasu kuma mutanen garin da suka san da zancen sai qus qus akeyi ana fad’in, ai shine d’ansa daya tati qasar turai yayi zaunensa, shine ai, shine yadawo…haka dai sukayi suruttansu, ji yayi baffa ya d’ora hannayensa akan fuskarsa yana goge masa hawaye had’e da cewa. “Taya zan iya hukuntaka nura bayan bakada laifin komai?, Taya zuciyata zatayi zafi da quna saboda kai bayan kai aka zalunta?, Kadena kuka baffanka baya fushi dakai balle kaico tazamo cikin tsarin rayuwarka, kai amintaccen d’ane awajena, nasan kowaye d’ana bazaka tab’a wofantar dani ba koda akan juji nake kwana kuwa, nasan ko wace irin tsadaddiyar kyautace kai da ubangijina yayi mani bazan tab’a bari zuciyata taci gaba da zargin kaba bayan gaskiya ta bayyana agareni, ina kukane awannan lokacin kawai saboda farincikina daya dawo Mani bayan wasu tsawon shekaru da shed’anin mutum dana aljanin suka tasirantu acikin rayuwarsa da son zuciyar wud’anda ke tunanin anzaluncesu har suka rabani dashi na tsawon wannan lokacin, na sani kaifin hankalinka da qarfin tunaninka bazasu bari ka iya mantawa damu ba don haka bazan yaudari kaina ba ta hanyar d’ora maka laifin da bai zamo naka ba kuma bazai tab’a zamawa naka ba,” Cikin kuka Dr Nuraddeen dake kallonsa da sauraran kalaman da gaba d’aya sukasa yaqarajin haushin kansa na nisanta da mahaifinsa na tsawon wannan lokaci batare daya san dalilinsa nayin hakan ba. “Karka fad’i hakan baffa, ni mai laifine agareka, taya d’an dake da mahaifi kamar ka dake da zuciyar zinare ace ya rabu dashi cikin matsananciyar rayuwa da kuma damuwa na tsawon lokaci kuma har ace baiyi laifi ba?, ace kaico bazata biyo baya arayuwarsa ba, ya ALLAH! Wace irin gagarumar hasarace na tabkawa rayuwata?, Wace cutarwace nayiwa kaina da zata had’ani da shiga ukuna nahar abada?” Had’a hannayensa yayi waje d’aya cikin wani irin kuka dake qiqqire lumfashinsa yanaci gaba da cewa. “Natuba baffana kayi haquri ka yafeni, bansa taya hakan tafaru ba!, bansan ko meye ya shiga kaina ba na aikata hakan!, bansan abunda ke faruwa da rayuwata ba, Na gujeka alokacin da kake tsananin buqatata, na butulcewa qasata, na zalinci kaina baffa meye makomata?” Saida baffa ya share hawayen fuskarsa da goge qasan hancinsa sannan yace. “Bakada makomar data wuce kyakkyawa aduniya nura, kuma baza kasan dalilin dayasa kayi hakan ba domin bakada niyar aikata hakan aranka, bazaka san meyasa hakan yafaru dakai ba domin ALLAH ya lullub’e mana sanin abunda ke gaibi, kayi imani da cewa wannan qaddarar kace da bazamu iya hana tafaru akanka ba, ka yarda ALLAH shiya tsaro maka hakan kuma karoqesa akan hakan yazamo yafiya da kankarar zunuban da kayi masa, ni nayarda da tsarin qaddara mai kyau da marar kyau akaina da kuma dukkanin zuri’a ta, fatana kawai ALLAH yasa daraja da d’aukaka ta biyo bayan amincin da mukayi ga qaddarar daya tsaro mana. Ka kwantar da hankalinka araina banida wani qaiqayi ko damuwa akanka” STORY CONTINUES BELOW  “Amma baffa…” Zaiqara wata maganar baffa Usman yayi saurin rufe masa baki tare da d’agosa daga durqushen da yake agabansu yana fad’in. “Ya Isa haka mana nura, kasan ko waye mahaifinka don haka kayarda dashi akan abunda ya fad’a kaji ko?.” “Kuyi haquri baffa Usman wlh bada son raina na ba hakan ta kasance..” “Nima nasani nura, ubangiji ALLAH ya tsare gaba kuma yaqara kareku aduk inda kuke, mukam Alhamdulillah mungode ALLAH tunda ya dawo mana dakai lafiya babu sauran wani Abu tsakaninmu dakai sai ALLAH yayi albarka.” Juyowa Dr Nuraddeen yayi yana kallon baffa dake murmushi hawaye kuma na kwance a fuskarsa lokaci d’aya ya jinjina masa kai alamar gaskiyane abunda baffa Usman ya fad’a. Baffa Ali kuwa da tuni kunya da nadamar abunda yayi tasa yaji Bari shi da kansa ya tona asirin kansa duniya tasan ko meye silar rashin dawowar little qasarsa masu zaginsa da zarginsa sudena, don inba hakan ba yasan ‘yan uwansa bazasu tab’a bayyana masa ko meye gaskiya abunda yafaru akan saba, don haka kai tsaye yanufi wajen ‘yan jaridar yace suzo zai basu labari akan abunda yafaru da Dr Nuraddeen har yakasa dawowa qasarsa, su baffa nacan na koke kokensu saidai suka hangosa ‘yan jarida sunsa shi agaba yafara basu labarin komai.. _”sunana Aliyu Aliyu amma amfi sanina da baffa Ali kamar yanda ake kirana, ni qanene ga mahaifin Dr Nuraddeen, nakasance mutum mai son kansa Wanda hakan yasa nayi sha’awar aurawa shi Dr ‘yatah batare da nayi la’akari da yanada wacce yake so ba ko baya da ita wanda sanadiyar hakan yasa da bai aureta ba muka azawa yarinyar daya aura tsana…..” Haka yayita basu labarin komai tun daga farko har zuwa qarshen sakamakon da suka samu daga wajen ALLAH dashi har matarsa, ya qara da cewa. “Masu zargin sonkai da abun duniya yasa Dr Nuraddeen ya guji qasarsa yaqi dawowa to ku dena ba haka bane, sahrrin shaid’an yasa batare da nayi la akari da cewa shid’in d’and’an d’an uwana bane muka aikata masa abunda yasa ba qasarsa ba hatta iyayensa da ahalinsa saida ya manta, nayi kuka sosai da nadamar hakan lokacin da shiriya tazo mani bayan ubangiji yayi masa sakayya shida mahaifinsa tun duniya akaina, wannan kuwa shine sakayyar da ALLAH keyi ga bayinsa da aka zalunta koma fiye da hakan.” Ya qare maganar had’e da nad’e qafar wandonsa da aka guntulu gundululun wajen yafito, sannan ya bud’e wasu sassansa qurajen da ke jiki suka bayyana dama tuni na fuskarsa sun bayyana. Ana hakanne su baffa suka ahamo da abunda yakeyi da sauri Dr Nuraddeen da kusan yaji duk wasu abubun yazo ya jayesa yana qare masa kallo tun daga saman fuskarsa dake cike da quraje har zuwa qafarsa da aka yanke ya rungumesa yana fad’in. “Meyasa baffa Ali?, Me yasa zakazo ka tonawa kanka asiri bayan ALLAH yarufa maka, idanma laifine aini yakamata na sani ba duniya ba, don me zaka zab’i tozarta kanka hakan?” “Kayi haquri nura, son zuciya ne, gashi yanzu ta kaini ga nadama kala kala, don ALLAH ka yafemun kuma kayafewa ruqayya.” Yafad’a cikin kuka had’e da qoqarin zamewa yaduqa agabansa yayi saurin d’agosa. “Baffa na yafe maka duniya da lahira, Kai mahaifina ne da har yanzu nake alfahari da shi, kuma zanci gaba da alfahari dakai har iya qarshen rayuwata, kowa na kuskure kuma mafi girman mutum acikin mutane shine wanda zaiyi laifi kuma ya gano cewa yayi laifi ya tuba har yayi qoqarin guarawa, haqiqa kai d’in babban mutumne mai girma baffanmu,” A yanayin yanda Nuraddeen ya karb’i zancen har yayi saurin yafewa qanen mahaifinsa shine babban abunda yafi burge wasu daga cikin ‘yan jaridar har yasa suka dingi tafawa Dr Nuraddeen. Sosai Dr Nuraddeen yake jin rad’ad’in abun aransa amma ganin irin yanda rayuwar baffa Ali takoma yasa Dole ya haqura da duk abunda yakeji ya yafe masa kamar yanda yake fatar shima ubangiji da sauran al’ummar da take tare dasu suyafe masa laifin da yayi masu tunda mai faruwa tariga da tafaru. STORY CONTINUES BELOW  Hannayensa yasa ya goge fuskarsa da idanuwansa da suka soma kumbura sukayi jawur saboda kukan da yayi sannan ya fuskanci ‘yan jaridar yana kallonsu d’aya bayan d’aya, yanda yake kallonsu yasa sai duk sukaji jikinsu yayi sanyi suka nonnoce kai qasa, babu wata tambayar daya rage suyi masa don gaba d’aya sun samu amsoshinsu abakin qanen mahaifinsa, izuwa yanzu suna ganin yakamata su dakata da wannan bibiyar da suke yimasa har zuwa wani lokaci idan buqatar hakan tasamu don ayanayin da suke kallonsa duk rashin imanin mutum dole zai tausaya masa, kusan mintuna biyar suka kwashe babu wanda yace uffan shi kuma bai ce komai ba domin ayanzu yanada qwarin guiwar da zai iya amsa dukkanin tambayoyinsu, can cikin qarfin hali wani d’an jarida yace. “Ranka ya dad’e ko me zakace ga abunda yafaru da kai ta sanadiyar qanen mahaifinka daya cutar dakai tahanyar yin asiri ya rabaka da qasarka iyayenka, da kuma iyalinka kamar yanda yafad’a.?” Cikin zafin rai Dr Nuraddeen ya d’agawa d’an jaridar yatsa had’e da cewa. “Kuskurene yin hakan agareka domin shi d’in mahaifina ne, don haka kada kaui yunqurin shigahurumin da ba nakaba, kada kayi qoqarin fad’in kalmar b’atanci akansa domin shi d’in babban mutum ne kaji nafad’a maka..” Yana rufe baki wani ya sake kad’o wata tambaya kamar hakan. “To Amma ranka ya dad’e baka ganin hakan da kayi kamar kabud’e qofar da wani na nesa ko kusa zai iya sake qoqarin cutar dakai ganin yanda ka kasa d’aukar mataki akan wanda ya cutar…” Bai qarsa ba Dr Nuraddeen yace. “Kaima ka kiyayi harshenka akansa, ko bakajin nafad’a masa cewa shid’in mutumne mai girma, ni awajena bayada sauran laifi, na yafesa ga duk abunda yayimun kuma nayarda da cewa kuskurene wanda ni da kai da Kai da kuma kai duk zamu iya aikatawa,” yaqare maganar yana nuna kansa da wanda ya tambayesa farko da kuma shi wanda yake bawa amsa yanzu. “To wane yanayi yanzu da kadawo qasarka kake jin kanka aciki yallab’ai?” “Alhamdulillah!, Yanayine da bazan iya misaltasa ba saboda farinciki, amma duk da haka inajin damuwar wani sashen atare dani, wanda nake fatan had’uwa dashi nan kusa bada jimawa ba.” “Ranka yadad’e idan na fahimceka kamar kana magana akan iyalinka ne ko?” “Qwarai kuwa amma bazance komai akansu ba domin bansan wane irin aiki qundin qaddara ya wanzu atsakanin ni dasu adaidai wannan lokacin, sai dai koma meye na tabbata cewa rouhi bazai rabu da gangar jiki ba kuma har asamu cigaban wanzuwar rayuwar.” “Wane irin qalu bale ka fuskanta ayayin da kake zaune awaccan qasar?” “Babban qalu bale shine rashin rouhi a gangar jikina da kuma rayuwar kad’aicin abokanan da zasu tayani ingantacciyar rayuwa inba kayan aiki naba.” “Yallab’ai Inna fahimta kenan bakada iyali acan?” “Taya zanyi iyalin bayan suna anan!?” “To taya akayi kadawo hayyacinka har kabuqaci dawowa qasarka.” “Wannan daga ALLAH ne da kuma qarfin addu’ar iyaye da suka dage da yimun, duk da inada yaqini akan akwai wata addu’ar ta musamman dake tare dani tana bani kariya.” “Ya batun aikinka daka baro, shin zakaci gaba dayin sane aqasarka ko ka ajiyesa kenan!” “Banida amsar wannan har sai yuyuwar hakan tasamu, Amma Ina so qasata ta sani nadawo da zimmar taimakon duk wanda ke buqatar taimakona a fannin abunda nakaranta.” “Wane sqao zaka miqa zuwa ga ‘yan qasarka?.” “Su zamo masu yadda da qaddara aduk yanda ta riskesu, su zamo masu uzuri, yafiya da kuma kyautata zato ga wanda suke tunanin ya zaluncesu, qaddara abace da batada shamaki ga dukkanin mutumen dake da rayuwa, wani tazo masa da sauqi wani kuma tazo masa a akasin hakan, to aduk yanda tazo maka ka amsheta hannu biyu kuma kayi haquri, in Sha ALLAH zakaga qarshenta domin ita mai zuwa ce da kuma wucewa, arayuwa kuwa duk nisan abu to SANNU SANNU bazata hana zuwa ba..Kuma zaka riskesa da yardar ALLAH,” STORY CONTINUES BELOW  Haka yayita sauraren tambayoyinsu daki daki yana amsawa har suka gama sannan yayi sallama dasu. Nan suka nufi wajen baffa shima suka yi masa tambayoyi shida baffa Usman suka basu amsa fuskokinsu a sake Wanda hakan ke nuna irin tsantsar farincikin da suke ciki, sunso abarsu su gana da mahaifiyar Dr amma baffa yaqi amincewa da hakan, hakan yasa suka harhad’a inasu inasu suka fara tafiya bayan sun gama d’aukar hotunan wuraren da duk suke buqata da suka shafi Dr da kuma rayuwarsa batare dasu baffa sun hanasu ba. A daidai lokacin da suke fita qauyen mashin ya ajiye little qofar gidan yana faman binsu da kallo sannan ya nufi cikin gidan, bakin zaure ya tsaya yana kwad’a sallama wanda hakan yasa Dr Nuraddeen dake zaune agaban Yaya hawwa ya rirriqeta yana kuka tana kuka saurin juyawa. Baffa bai cemasa komai ba yafita d’akin yayi wurin little ita kuma Yaya hawwa sai faman kuka takeyi tana shashshafa fuskarsa tunda ba gani takeyi ba tana fad’in. “Ina kashigene nura kabarni?, Meyasa zaka gujeni bayan kasan yanda nake tsananin sonka?, kayi haquri nura kayafeni, na tubarwa ALLAH nayi nadamar laifina, kayafe mani kada ka koma tafiya kaji nura, bazan sake ba kaga nariga da nazo gazgara don ALLAH kabari karufeni da kanka idan na mutu.”+ “Haba innarmu bazaki mutu yanzu ba kidena fad’ar hakan, ba guduwa nayi ba, ba fushi nake dake ba domin banida wannan zarrar da zanyi fushi da mahaifiyata da nake matuqar qauna, sharrain shed’anin mutum dana miyagun aljani ya nesantani daku, amma yanzu nadawo agareku nahar abada in sha ALLAH innar mu, iyaye ai ba’a fushi dasu.” “Shine katafi kabarni kullum cikin kiran sunanka amma baka amsa ba balle kazo.” Taqarasa maganar tar da fad’awa jikinsa tana cigaba da kukan, rungumeta yayi sosai yana fad’in. “Kiyi haquri innarmu, bazan sake ba.” “Ka tabbata bazaka sake tafiya ka barni ba?.” “Eh innarmu bazan tafi nabarki ba har abada.” “To Ina kabaro Rashida, itama fushi take dani ko, ka kirata naroqeta tayafemun kafin namutu da haqqinta, duk da idanuwana basa gani amma ina so nasake had’uwa da ita naroqeta ko zata yafemun abubuwan dana aikata mata.” Gabansa ne yayi wani irin mugun fad’uwa jin abunda ta ambata saboda tsoran kar ace dai ana nufin ba’aga Rashidarsa bane!, A daidai lokacin little ya shigo d’akin shikuma da gudu saboda albishir d’in dasu baffa suka yimasa cewa mahaifinsa ya dawo, wani irin burki yaja abakin qofar d’akin ganin mutum zaune tsakar d’aki rungume da Yaya hawwa, tafiya ya dingayi tamkar wanda qwai ya fashewa acikin ciki har ya iso cikin d’akin ya duqa ya tab’o Dr Nuraddeen don dama yaba qofa baya ne, juyowa Dr yayi da nufin ganin kowaye Wanda hakan yasa little ja da baya da sauri har yana shirin fad’uwa ganin mutumen da suka rabu dashi d’azu bada dad’ewa ba. Shima qoqarin cire Yaya hawwa yafarayi ajikinsa yana kallon little amma sai tafashe da kuka tan fad’in. “Karka tafi kabarni nuraaaa.” Taqarasa maganar cikin irin yanayin da kai da kaji kasan muryar tsofaffin dake cike da tsoron faruwar wani abune akansu, cike da rud’ewa gaban little ya fad’i sai kuma yaji baffa Usman dake shigowa shi dasu baffa ya dafosa yayi saurin zabura had’e da juyawa, qarasa turosa baffa Usman yayi acikin d’akin cikin rawar murya little yace “Tsa..tsaya, tsaya baffa, nakasa fahimtar wani abu anan, shin waye wannan mutumen da tun jiya a borno yake bibiyata? kuma Ina mahaifin nawa da kukace ya dawo?” “Natsu mana Abu sumayya, wannan da kake gani shine mahaifinka, shine babanka Nuraddeen yau yadawo qasar nan.” Wata irin razana little yayi tare da Isa gaban Dr Nuraddeen da tsananin kunya tasa shi duqar da kansa qasa yana hawaye. Hannu yasa ya d’ago fuskarsa had’e da furta cewa. “Mai gida kaine mahaifina?,” Dr da bayada zarra da kuzarin da zai iya kallon qwayar idanuwan little ya amsa masa cewa shi d’inne saboda yanda suka had’u har kusan so ukku Amma yakasa tabbatar masa da cewa shine mahaifinsa sai yanzu ya d’ago kai yana kallonsa yace. STORY CONTINUES BELOW  “Bazan iya amsa wannan tambayar ba domin bancika duk wasu sharud’d’a d’aya kamata mahaifi yacika ga d’ansa ba, baici in amsa wannan suna agareka ba b’acin nakasa amsar kulawa da rayuwarka tunda kazo duniya, bansan da wane ido zan kalleka ba ince nine babanka, bansan da wud’anne idanuwa zan kalleka nace Kai d’ana bane don ALLAH kayafeni.” Ya qarasa maganar yana had’a hannayensa waje d’aya, wani kuka Yaya hawwa ta fashe dashi jin hawayen Dr dake rungume da ita ajiki na zuba mata a fuska tana fad’in. “Wayyoo.. ALLAH wayene yasa d’ana kuka, don ALLAH kada kub’ata masa rai yagudu ya barni.” Dafata little yayi yana fad’in, “Kaka taya kike tunanin zan b’ata ran mahaifina Dana dad’e Ina mararin gani?, Na dad’e Ina mafarkin had’uwata dashi kafin nakoma ga mahaliccina?, Na dad’e Ina tanada soyayyar da nake yimasa araina har zuwa lokacin da zai dawo agaremu?, Ko kad’an bazanyi hakan ba kaka domin Ina matuqar qishin son ganinsa.” “Waye kai Kuma.?” Tafad’a tana qoqarin lalubo fuskarsa, riqo hannunta yayi ya d’ora akan fuskarsa yace. “Nine jikanki kaka, d’a awajen gwaggona Rashida Kuma jinin d’anki dake gabanki.” “Wayyo ALLAH na kada kuyau dareni don bana gani, jikana kuma?, Ina kabaro mahaifiyarka?, Ita bazata zoba fushi take dani?,” “Ko kad’an kaka babu yaudara ni jikanki ne, kiyarda dani ko don ta hanyar muryar mahaifina dana d’auko.” “Nayarda amma shine kaima ba ka zuwa kana dubani?, Kayi haquri kada ka tsaneni sharrin shaid’an da zuciya sukasa na aikata abunda nayiwa mahaifiyarka, don ALLAH kace tayafeni nayi nadama” “Taya na tsaneki kaka bayan ko yaushe nakanzo na dubaki, wannan kukan naki da kike yawanyi kina ambaton mahaifina shiyasa bazan iya yimaki magana ba don kada kid’auka shid’inne kukanki ya tsananta.” Cike da sha’awa da kuma burgewa Dr ke kallonsa, gaba d’aya sak d’abi’unsa basada banbanci dana mahaifiyarsa haka sautin muryarsa data dad’e tana yimasa yawo a qwaqwalwa don tunano mai irinta batada banbanci da tasa, Ashe shid’in d’ansa ne, jininsa ne shiyasa jikinsa ke bashi kamar yanada alaqa da habibtynsa ashe shid’in d’an sane, hannu little yasa ya rungumosu gaba d’aya shida Yaya hawwa da tabi ta naniqe ajikin mahaifinsa wasu hawayen farinciki nazubo masa yace. “Alhamdulillahilazi bini’imatihi tatimmusswalihaat.” Shiru yabiyo bayan wasu mintuna kafin Dr Nuraddeen yace. “Mahaifiyarka kuwa?, Anya kanaji zata iya yafemun?” Da sauri baffa yace “Mezai hana idan bakayi qasa da guiwaba wajen zuwa gareta.” Da qarfi Dr yajuyo yana kallon mahaifinsa yace. “Taya baffa!, Nasan cewa hakan zaiyi mani wuya don babu tantama ayanzu tana aqarqashin inuwar wani. Sanin cewa anganeta bayan tafiyata da nayi yanzu da kuma jin cewa tana raye cikin qoshin lafiya, da damar had’uwa da d’ana data bani kawai ya wadatar basai naje na haddasa mata damuwa ba agidan aurenta, qaddarata kenan arayuwa wataqil rasata da nayi shine hukuncin da ALLAH zai yimun akan abunda na aikata.” Ya qarasa maganar yana goge hawayen da suka zubo masa ya ajiye Yaya hawwa gefe tare da miqewa yabar d’akin, qofar part d’in da sukayi zama ya nufa yayi zaune yan kuka tamkar wani qaramin yaro, shikenan yanzu yajawa kansa rasata sanadiyar nisanta kansa da yayi da ita, wannan wace irin rayuwace da akoda yaushe jarabawa mai nauyin gaske ke biye da ita Kallon little baffa yayi shima ya kallesa sukayi murmushi sannan sukabi bayansa, daidai lokacin baba nusaiba ta shigo fuskarta cike da farinciki taci karo dasu Inna Bilkisu dake tsaitsaye suna jimamain yanayin da Dr yafito ya shiga ciki, nan fa tashiga tambayar Ina Nuraddeen d’insu da akace ya dawo, kafin tabata amsa yayi saurin d’ago kai yana goge qwalla aka shiga gaggaisawa, kan kace me tuni gidan ya cika da masoya da abokanan arziqi na gaskiya da muna fukai ana taya baffa murna, Inna Bilkisu kuwa ba’a magana yanda kikasan ta tashi sama, farincikinta biyu dawowar Dr Nuraddeen da little daya bayyanar mata ita alokacin a matsayin d’ansa, Wanda hakan ba qaramin dad’i yayi mata ba cewa tuni anga Rashida ashe harda abunda ALLAH ya arzuttasu dashi, anan ta zage tana tayasu murna tare da yiwa Dr bayanin kowace baba nusaiba awajensa da kuma ‘ya’yanta da suke matsayin qanne agaresa d’aya bayan d’aya, yaji matuqar dad’i sosai kafin yafara tambayar mutanen gidan inda nan aka sanar dashi rasuwar Inna ruqayya da auren muneera, yayi jimamin mutuwar Inna ruqayya sosai tare da nema mata gafara, ad’aya b’angaren kuwa yayiwa muneera murnar aurenta da tayi bata tsaya jiransa ba, ana hakane sai gasu baba balarabe dasu Yaya Maryam sun iso don tuni labari yakai kunnensu saboda kafafen yad’a labarai babu ta inda bai jeba, tsananin farinciki yasa suka kasa haquri suka biyo hanya don tabbatarwa kansu abunda sukaji tare da roqon baffa yafiya bisa laifin da sukayi masa na b’oye masa ganin Rashidar da akayi da kuma nura d’ansa, musaman Yaya Maryam da tafi kowa nadamar hakan don dama tuni su baba balarabe da aunty marwiyya su sun zubar da makaman yaqinsu, tayi kuka sosai tare da nadama akan yanke hukuncin da tayi bisa rashin sani don gaba d’aya taji bayanin da baffa Ali yayi a qafafen yad’a labaran da ‘yan jaridun da gidan redio da talevision sukayi. STORY CONTINUES BELOW  Murmushi kawi baffa yayi had’e da cewa “babu komai tsarin ALLAH ne duk da dai itama tayi haquri tuni an had’asa da jikansa, kawai ba’a bayyana hakan bane don kada taji har zuwa lokacin da ALLAH zaiyi ikonsa kuma gashi SANNU SANNU ALLAH yakawo lokacin.” Kallon baba balarabe tayi yayi saurin noce kai qasa yana sosa qeyarsa, murmushi tayi had’e da cewa. “Haqiqa kayi Abu mai kyau, wannan shine banbancin hankali da kuma tunanin dake tsakanin mace da namiji, badon haka ba natabbata da abubuwa marasa dad’i sun faru da yawa, kayi qoqarin riqe zumuncin d’an uwanka bashar ALLAH yajiqansa Kuma ya saka maka da alkhairi.” Sun jima ana fira cikin farinciki da kuma kewar juna da akayi, wanda anan ne Dr Nuraddeen yaji rasuwar mahaifin habibty d’insa tare da tabbacin cewa ashe batayi wani aure ba tun daya tafi, wani irin tausayinta ne ya rufesa tare da qaunarta mai tsanani, wannan wane irin halaccine da karamci tayi masa arayuwa, gaba d’aya ta qarar da quruciyarta azaman jiransa shi kam dame zai ska mata aduniya. Jan little yayi agefe bayan ya kauda idanuwan mutane ya shiga tambayarsa labarin habibty d’insa wanda sai alokacinne little ya tuna da gaba d’aya baiyi waya da itaba tunda suka iso saboda wayarsa nacan ya baro a can cikin motar da sukayi accident, da sauri yaje ya anso wayar baffa ya daddanna lambobin wayarta yakirata, Rashida dake zaune cikin d’aki lokacin tagama sauraren firar da akayi da Dr Nuraddeen da baffanninsa tasha kuka har tagaji, Saida tasa hannu ta goge hawayen da suka jiqa mata fuska sannan tamiqa hannu ta d’auko wayar had’e da d’agawa, kallon Dr Nuraddeen yayi had’e dayin murmushi sannan yace. “Assalamu alaikum, gwaggona barka da marece..” cikin muryar dake bayyana mata tsantsar farincikin da yake ciki, ‘Dan Jan majina tayi kad’an had’e da goge hancinta ta daidaita muryarta don kar yafahimci tasan wani abun don ta tabbata yasan da komai yanzu matuqar ya isa wajen sannan tace. “Wa’alaikissalam d’an gidan mamansa, sai yanzu kake kirana?, Ina kashige ne nayita kiran wayarka baka d’aga ba duk kabi ka d’agamun hankali, Saida nakira ‘yatah take fad’amun ai kin Isa lafiya amma sau biyu kuna qetare rijiya da baya da baya?” “Ina tuba gwaggo, wayar nacan acikin motar na manta da ita, wlh kam kingin qiris mukayi.” “To ALLAH ya tsare gaba, su umma ma da dady dasu uncle sunyita kiranka basu samu ba, kayi qoqari ka kirasu duk da nasan bazasu rasa yin waya da batool ba, ALLAH yahutar da gajiya kadai ci abinci ko?” “Eh gwaggo.sosai ma, ammm gwaggo nace kiriqe waya zanyi maki wani surprised.” Tanajin yafad’i hakan ta kashe wayarta, sake kira yayi ta d’aga yace. “Gwaggo nazo wajensu baffa ne, kuma na had’u da mah..” Bai qarasa ba taruntse idanuwa had’e da kashe wayar gaba d’aya ta ajiye tanaci gaba da wani irin kuka data kasa banbance shin na farinciki ne ko akasin haka.. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ _Assalamu alaikum warahmatullahi wabara katuhuun, bakina bazai gaji da gode maku ba tare da miqo gaisuwata had’e da fatan alkhairi agareku ba masoyana, tabbas shi mutum rahamane aduk inda yake, wlh namatuqar jin dad’in kiraye kirayenku ta waya kuna yimani ya jiki da addu’o’in samun sauqi kuma Alhamdulillah naji sauqi indai jikin yabi haka, Ina godiya ga dukkanin wanda yakirani da masu turo saqo through inbox na messages ko na WhatsApp, ngd ngd ngd sosai jaxakumullahu bikhair, bazan manta dakuba wud’anda sukayita turo addu’o’insu ta group musamman ‘yan group d’ina na amanata😅wato SANNU SANNU FANS GROUP 1&2 Kuma kun nunan qauna ALLAH yasaka maku da mafi qololuwar alkhairansa duniya da lahira._👏 STORY CONTINUES BELOW Jin wud’annan kalamai nata yasa Fatima dasu Dr da basuma san da tana wajen ba juyowa da qarfi, tashi yaransu dake tare dasu zaune sukayi sukabar falon cikin tausayi Fatima da alokacin da ita har Dr suka tabbatar da cewa mutumen daya gama magana yanzu a tv shi d’inne mijin na Rashida kamar yanda suke tunani tayi had’e da zuwa inda take ta d’agota daga durqushen da take qasa ta dawo saman kujerun da suke zaune ta zaunar da ita zakiyar inda take zaune da Dr sannan cikin sanyi murya yace.+ “Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah wannan shine abunda yakamata yafara fitowa daga bakinki gwaggon yara, na tabbata cewa zuwan wannan rana zai zamo wani abun farinciki azuciyar da wannan kukan da kikeyi bai isa ya gasgata hakan ba domin nasan kowa akke, a ma’auni mizani na zahiri Nuraddeen bai kyauta maki ba kuma baiyi maki adalci ba, Amma abad’ini abunda ke b’oye bazamu iya yanke hukuncin yayi daidai hakan daya yimaki ba ko baiyi ba, domin bamuda hurumin sanin gaibi sai abunda ke zahiri, ayau d’innan nayi farincikin yanda ubangiji keshirin dunqule abubuwan da suka wawwatsu waje daban daban awaje d’aya, ayau Ina cike da farincikin ganin mahaifin little yadawo qasarsa, inajin wani shauqi da farincikin cewa little zai had’u da mahaifinsa d’aya buge shekaru kusan ashirin da tara bai tab’a ganinsa ba, to idan har ni zanji irin wannan farinciki azuciyata to me ake tsammani ga wud’anda sune mafi kusanci agaresa? Musamman zuciyar data rayu tana d’awainiya da qaunarsa da kuma dakon zuwansa agareta akowane lokaci?, Nasani akwai rad’ad’i sosai kaga wanda kake tsammanin ya aikata maka kuskuren da bazai rasa hujjarsa tayin hakan ba sai kuma kaga yakasa wanke kansa akan wannan kuskuren daya aikata maka alokacin da kake tsammani, Amma akoda yaushe ana son mutum yazamo mai uzuri da kuma bincike idan wani abun yafaru, Ina so kamar yanda zuciyarki tayi masa uzurin rashin dawowarsa to tasake bashi wata damar tahanyar binciko ko meye dalilinsa na aikata hakan, wannan kukan duka bayada amfani kamata yayi mugodewa ALLAH daya nufi sake had’a fuskokinku, don ALLAH da girmansa kiyi haquri karki d’auki wannan abun da zafi haka. “Haba aunty!, Haba aunty wane irin bincike zan b’ata lokacina dayi bayan yakasa bayyana gaskiyar daya b’oye agaban duniya, ada zuciyata nafad’amun cewa duk lokacin da zai dawo agaremu zai dawone da cikakkiyar hujjar da zata tabbatar mani da abunda zuciyata ke zargi wanda harga ALLAH zan iya yimasa uzuri akai, Amma ga yanda yadawo da kuma irin amsoshin da yake bawa manema labarai gaba d’aya ban yadda dashi ba, asalima tsoro yabani kwata kwata don bayada wata hujjar data wuce masa son duniya da kuma holewa ta zaunar dashi awaccan qasar. “Subhanallahi, maman little me kike son fad’a haka?” Dr yafad’a tare da qoqarin gyara zamansa yana kallonta, cikin kukan da gaba d’aya takasa denawa tace. “Uncle kayi dubi izuwa yanayin rayuwar da yadawo tsunkensa shi kad’ai, a tsawon wud’annan shekarun da yayo ba ahaka yakamata kamilin mutum yadawo ba, atleast mata, ‘ya’ya su suka kamata suzamo abokanan rakiyarsa domin suzasu tabbatar da hujjarsa ta zama waccan qasar har na tsawon wud’an nan shekarun, Amma idan basuba bayada wani dalili ko hujja da zata gamsar dani, son kai, son zuciya rud’in duniya da holewa suka d’aine zan yarda cewa sun zaunar dashi awaccan qasar.” Shiru Dr yayi yana nazarin kalamanta kafin can yace da ita. “Eh hakane!, Amma Ina so kiyi amfani da maganganun Fatima, koma meye ki da kacesa har zuwa lokacin da zakiji ta bakinsa, hakan ne kawai zaisa iya yanke masa hukunci daidai da tunaninki, maganar mata da d’iya da kikayi kuma wannan ra’ayine, sai mutum nada cikakkiyar natsuwa da kwanciyar hankali zai buqacesu musamman a inda ba lalle bane yuyuwar samunsu agareka, nidai Ina shawartarki da kinatsu ki kwantar da hankalinki kiyi addu’ar ALLAH yasa wannan dawowar tasa tazamo alkhairi duka agaremu kuma kasa qarshen duk wani sarqaqaqqen al amarine d’aya faru wanda bamuda masaniya akansa.” Ita dai banda kukanta babu abunda takeyi wanda daga qarshe dai cikin zolaya tace da ita gwaggon yara nadai gano wannan kukan naki na dad’ine gaskiya, idan kuwa ba haka ba to kina practicing d’in irin kukan amaren da zakiyine ranar da zamu maisheki d’akinki tun yanzu.” STORY CONTINUES BELOW  Bushewa da dariya Dr yayi had’e da miqewa yabar falon yana fad’in. “To mudai koma meye ayiwa takwarana haquri har zuwa lokacin da zaizo ya wanke kansa, ni nama tafi inyowa su dady da umma albishir ALLAH maji roqon bayinsa ya dawo masu da surikinsu lafiya.” “Ah to mudai wlh munyi farinciki sosai, fatanmu d’aya ALLAH yasa hakan ya zamo alkhairi, barima na d’auko wayata nafara riganka wannan albishir d’in.” Ganin suna nema su juyar da tunaninta izuwa nasu yasa tamiqe tana kumbura fuska tabar wajen Fatima nata yimata dariya. Bayan wucewar tane Fatima tayi wata irin ajiyar zuciya had’e da cewa, “Tabbas duk abunda yayi farko zaiyi qarshe kuma duk nisan abu SANNU SANNU bazata hana akai garesa ba, yau gashi abunda basu tab’a kawowa zaizo kusaba da SANNU SANNU yazo garesu batare da zato ba balle tsammani. ••• ••• ••• Kimanin awanni hud’u su little suka kwashe akan hanya basu iso kano ba saboda yanayin yanda little ke tuqin, tafiya yakeyi ahankali wanda gudun bai gaza a 40 ba, tun ‘yan biyu na qiriniyarsu har suka gaji suka natsu waje d’aya, batool kuwa tayi bacci yafi aqirga saboda wahalar zaman motar da takeji wanda yanzu hakama yad’an ja kujerar da take zaune ta d’anyi baya yanda zata iya kwantawa saboda yanayin tsufan cikin nata dole duk d’okinta zataji gajiyar da zata sakata bacci. A b’angaren su Abba kuwa su duka sun kasa zaune sun kasa tsaya, bini bini Abba dake faman safa da marwa ya d’aga kai ya kalli qatoton agogon dake maqale ajikin bangon makeken falon da kamar ya zamo matattarar dukkanin ahalin gidan. Ganin an kwashe awanni hud’u babu labarin isowarsu yasa yasa Abba zuwa ya bud’e wani safe d’insa inda yake ajiyar kud’i ya d’ebo adadin da shi kansa baisan ko nawa bane yafita dasu, Saida yabar anguwar gaba d’aya sannan ya dinga raba kud’in ga duk wanda ya had’u dashi dake da buqata da niyar sadaka, saida kud’in suka qare kaf sannan ya koma gida lokacin ya taraddasu uncle h sun tara samari da ‘yan matan gidan manya da yara an rarraba masu irin al-qur’anin nan Mai hizib biyu biyu kowa ya d’auki inda ya iya haddasu ana karantawa, wani irin sanyi yaji aransa tare da tabbatar da cewa komai zai faru ga ‘yarsa yanzu yanada yaqinin shine yafi zama alkhairi kuma zai amshesa hannu biyu biyu. Sauran mata uwayen gidan kuwa kowace na kitchen tana ayukkanta ciki d’ure da ruwa, so sukeyi sukirata suji idan sun iso, musamman hajia mama Amma Abba yasa warning akan kada asake akirasu domin hakan na iya d’auke masu hankali, murmushi kawai hajia mama tayi aranta tace, _(ALLAH sarki! alhaji kenan! Wai shi atunaninsa hakan da yayi dubarace da zata iya hana afkuwar abun da ALLAH ya riga ya tsaro?, Baisan ita qaddara kota qaqa bane baza’a iya guje mata ba, ALLAH dai yasa mudace.)_ A b’angaren Dr Nuraddeen kuwa tuni jirginsu ya iso kano wanda tun daga lokacin da suka taso har isowarsu babu abunda yakeye sai kuka, babu abunda yake tunawa irin tambayar da akayi masa cewa _acan baya yace bayada masaniya akan zancen iyayensa, ahalinsa da kuma iyalinsa, mezai iya cewa akan haka adaidai wannan lokacin?_ duk yatuna wannan furucin sai yaji wani zafi da quna acikin ransa, yanzu da wace irin fuska zai kalli iyayensa idan har ya taraddasu?, me zai cewa masoyiyarsa data adalilinsa tashiga halin da har yau baisan a Ina take ba?, Wud’anne kalamai zai yiwa ahalinsa a matsayin ban haquri bisa wud’annna munanan lafuzza dayayi?, Yana cikin wannan tunanin ne jirginsu ya sauka a filin jirgin sama na aminu kano, nan ma dai kamar yanda ya barone acan jahar, ‘yan jarida ne birjik da ‘yan gidan redio da talevision suna jiran isowarsa, a wani b’angaren kuma mataimakin gomnan jahar da kansane shida muqarrabansa da manya manyan shuwagabannin aiki a fannin lafiya da sukazo tarbarsa wanda gwamnan jahar ne da kansa yabada wannan umurnin don karramawa garesa daga gwamnatinsa da Kuma nuna jin dad’insa bisa nasarar dawowar shahararren likitan aqasarsa lokacin mulkinsa. Yana fara tattakowa daga matattakalar jirgin manema labaran sukayo ruuuu suna sakar masa hotuna har ya qaraso, nan take jami’an tsaro suka shiga bud’a mutane ana tutturesu gefe saboda mataimakin gwamna dake qoqarin isowa wajensa, STORY CONTINUES BELOW  Yanda Dr Nuraddeen yaga ana girmama mutumen yasa ya tabbatar da babban mutumne don haka yad’an saki fuskarsa daga yanayin da take yana isowa kusan atare suka miqawa juna hannu suka gaisa sannan mataimakin gomnan ya gabatar da kansa agaresa, duk qoqarin ‘yan jarida nason ganin sun zanta da Dr hakan ya cutara saboda manya manyan mutanen da kai tsaye suka shiga gaisawa dashi suna gabatar da kansu agaresa tare da welcoming d’insa, Wata zuqeqiyar mota maikyau mataimakin gomnan yayi masa izinin su shiga domin a kaishi masaukin da gwamnati ta tanadar masa wata ‘yar qwarya qwaryar walima data shirya masa ta gaggawa don murnar dawowarsa Amma kai tsaye yace da mataimakin gomnan kai tsaye yafi buqatar wucewarsa gida, bayan ya huta zai isa wurin da ake buqatar zuwansa. Ba musu mataimakin gwamnan ya had’asa da jami’an tsaro mota d’aya bayan yakira gomnan ya sanar dashi yanda Dr N.I d’in yace yana buqata yaci ayi masa hakan. Saida suka sakeyin musabaha Dr yayi masa godiya cikin girmamawa sannan aka kawo wata motar ya shiga daga shi sai drivern daya jasa zuwa qauyen nasu na bebeji motar jami’ai d’aya na biye dasu abaya. Dama tuni wasu ‘yan jaridar kai tsaye sun nufi qauyen tun d’azu yayin da sauran yana wucewa suma sukabi bayansa. Su baffa Usman da baffa Ali da kuma baffa na zaune qofar gida suna hira kwatsam sai sukaga motocin ‘yan gidan redio da talevision na shigowa cikin qauyen wanda abun ya matuqar d’aure masu kai, tun daga kusan farkon gari suka daza motocinsu har zuwa gaba da qofar gidansu baffa, saidai sun kaga ma’aikatan na tada qarafunan setily da faya fayin motocinsu suna harhad’awa batare da suncewa kowa uffan ba don dama tun a farkon shigowarsu suka tsaya sukayi tambaya aka fad’a masu gidan, su kuwa mutanen qauyen haka suka firfito sukayi cirko cirko suna zullumin wane irin abune yasamu qauyen nasu da motoci suka cikasu haka ana faman tashe tashen abubuwan mota da sauransu, yayinda wasu kuma suka dingi tattaro ‘ya’yansu suna turawa cikin gida musamman matansu da basuda yadda akan duk abunda ya shafi mutanen birni. ••• ••• ••• Sai gab dasu little su shiga kano batool ta farka daga baccin da takeyi lokacin su hassana da hussaina sun gaji da qiriniyarsu suma sunyi bacci, bakinta d’auke da salati ta tashi zaune tana buga wata irin uwar hamma had’e da cewa. “Wayyo Abu sumayya har yanzu bamu isa ba, ni sai nake ganin kamar yau ana jawa garin nisa, don ALLAH kad’an qara taka wuta, namatsu inga Abbana.” Murmushi yayi had’e da d’an juyowa ya kalleta sannan yace. “Wai! Agaidasu gimbiya, wato kema da kika sharqi baccinki kece kika gaji bani ba ko?, Bawani kin matsu kiga abbanki, kedai kice kin matsu kici abinci wannan uwar hamma da kika buga ai tsaf kan akuya zai shiga ta bakinki.” Hannuwa tasa tad’an duddukesa ga kafad’a yana dariya yace. “Kai ko, wane kan akuya zai shiga awannan d’an mitsitsin bakin nawa?, ALLAH bana son sheri.” “Bakiga yanda kika bud’esa bane shiyasa, tsaf kan tinkiya ma zai shiga aciki.” Gano salon zolayar tasane ta motsa yasa tayi murmushi had’e da langab’ar da kanta gefe tana cewa. “Naji d’in, ba dole ba ambar mutum da yunwa fiye da awa hud’u kuma duk ansan dole ajiyarsa zata dami mutum tace itama yunwa, to meye ma idan kan tinkiyar ya shige abakina tunda yunwa nakeji sai nakama abuna na kamtse na cinye.” “Aw abun sharri ne?” “Eh man, ba yanzu kagama yimun ba nima, kaga narama mun zama 1-1” “Ai shikenan! Kiyi haquri mun kusa isa saura kilometers biyar in Sha ALLAH” “To kad’an qara gudu mana sai muyi saurin isa tunda mun kusa kace.” “Ehm.ehm..rufamun asiri, inyi maki ta bakin gwaggo tace uncle, to uncle yace kada muyi gudu, kiyi haquri muqarasa lafiya tunda munkusa isa, SANNU SANNU ai Bata hana zuwa saidai a dad’e ba’a kai ba ko kuwa?” STORY CONTINUES BELOW  “Hakane in Sha ALLAH..” Tana rufe baki sai ga wata babbar mota da alama burkinta ya katse ta nufosu aguje, da sauri little ya koma ta d’ayan hannun ALLAH yasa babu wata mota agabansu tafe ya sauka gefen titi yayi parking gabansa na fad’uwa, yafi mintuna uku aciki yana kallon yanda waccan motar ta fad’i tana qoqarin gangarawa cikin daji ta madubi kafin can ya kashe motar yafito ya nufi wajen yana kallon ikon ALLAH, nan fa sauran motocin dake tahowa wasu suma suka tsaitsaya ana jiran aga yanda sarautar ALLAH zatayi da motar, sai da babbar motar ta dad’e tana juyawa sannan aka samu ta tsaya mutane sukayi ruuu wajen ko za’a iya ceto rayukan wasu, sai gashi koda akaje mutum biyu ne kad’ai a motar daga driver sai na gefensa kuma duka ALLAH yayi masu rasuwa, Saida aka gamo jajantawa sann little yadawo ya shiga motar jikinsa asanyaye yana fad’in. “Ubangiji ALLAH ya jiqansu da rahama.” Batool da suma kad’aice batayi ba tsabar yanda ta tsorata ta samu daqyar ta amsa masa da Amin, had’e da cewa. “Duk sun mutu ko?” “Eh, dayake mutum biyune kad’ai acikin motar sun d’auko kaya da alama legas zasuje.” Yabata amsa yana kallon yanda duk yanayinta ya sauya. “Kar dai kice mun kin tsoratane?.” “Sosai wlh.” “Ki kwantar da hankalinki kinji ko, in sha ALLAH zamu Isa lafiya.” Sannan ya tada motarsu sukaci gaba da tafiya, har suka iso cikin kano batool bata sake cewa uffan ba gudun kar maganar da zatayi ta d’aukar masu hankali don ta matuqar tsorata fiye da tunani, shi kuma dayaga hakan sai bai cemata komaiba fata dai su isa lafiya. Suna kawowa daidai wata roundabout motar data d’auko Dr Nuraddeen na wucewa zasuyi yuton ta d’ayan titi ta jami’an da suka biyota baya ta shigo aguje lokacin little shi kuma ya shigo sai batool ta saki wata irin qara wacce ita tasa little rud’ewa saidai yaji sun bugi motar jami’an tsaron, Da sauri Dr Nuraddeen da har motar da yake cike ta juya ta d’ayan titin ya hango abunda yafaru ya tsaida drivernsa. Nan take go slow ya cika wurin don gaba d’aya gaban motarsu little data buga data jami’an tsaron ya molaqe Amma su babu abunda ya samesu, don little qoqarin ma bud’o gambun motar yakeyi yafito, d’an ja da baya motocin suka shigayi sannan aka taimaka masa yafito had’e da d’an dafe goshinsa daya bugu ya da sauri ya zagaya inda batool take, ita kam da alama somewa tayi da sauri wani mai keke napep ya miqo ruwan leda aka yayyafa mata ta farfad’o tana fad’in. “Innalillahi wa’inna ilaihirrajiuun, Abbana.” Murmushi little yayi sannan yariqota tafito daga cikin motar wanda daqyar ta iya takawa saboda qafafuwanta da suka kumbura, adaidai lokacin Dr Nuraddeen ya qaraso shida drivernsa yana fad’in. “Subhanallahi, injin ba abunda ya sameku?,” Juyowa little yayi da sauri don bazai manta muryar wannan mutumenba, sai da Dr Nuraddeen yakusa fad’uwa saboda wani irin jiri daya d’ebesa lokacin da idanuwansa suka sauka akan fuskar little dake fad’in. “Ko kad’an Alhamdulillah, ALLAH ya tsare.” Nan ma gabansa ne ya sake fad’uwa tuna wannan muryar wanda yarage masa hanya ne jiya da daddare a jahar borno, Abu mafi qololuwar ban mamaki dashi shine yanda sak fuskarsa irinta Rashidarsa, to wannan wane mutumne dake bibiyarsa tun jiya, yana wannan tunanin ne yaga suna qoqarin barin wajen da sauri batool tajuyo had’e da dawo wajen motar tana fad’in. “Abu sumayya su hassana fa.” Sai alokacin shima yatuno dasu da sauri ya qarasa ta gaban motar ya bud’e lock d’in daya danna tin tasowarsu don kada suyi yunqurin bud’e gambun tunda basaji, sannan ya dawo ya bud’e bayan, ga mamakinsa sai yaga gaba d’ayansu sun fad’o qasan sit d’in d’aya ta taushe d’ayar kuma baccinsu sukeyi, hamdala yayi tare da d’auko ta saman wani ya karb’eta sannanya d’auko d’ayar yana duddubata, haka batool ta qaraso wajen batare da taji nauyin cikin dake jikinta ba takarb’i ta hannun mutumen Wanda gaba d’ayansu sun tashi baccin sai faman murza idanuwa sukeyi da hannu suna kallon mutanen da sukayi cincirindo wajen, kallo Dr Nuraddeen yabi yaran dashi, ahankali ya furta subhanallah, saboda tsantsar kamarsu daya gani da wannan mutumen daya taimakesa jiya, Kai ko baka tambaya ba kasan ‘ya’yansa ne, banbancin kawai shine hasken fatar da yaran suka fishi Wanda da alamu na mahaifiyarsu ne dake d’auke da tsohon ciki. STORY CONTINUES BELOW  Gaba d’aya rud’ewa Dr Nuraddeen yayi ya rasa tawa zaiyi cikinsu, ta jami’an tsaron da wasu daga cikinsu sun fad’o sun d’anji rauni kota wud’annan ahali dake da matuqar yanayi da habibty d’insa. Baisan lokacin da yaba drivern umurni yaje yayi qoqarin fiddo motarsu little data shige cikin ta ‘yan sandan ba shi kuma yabi su little dake qoqarin komawa gefen titi yana fad’in. “Sannunku ko.?” “Yawwa” little yafad’a yana qoqarin amsar hassana a hannun batool bayan ya ajiye hussaina qasa. “Am don ALLAH nace daga jahar borno kuke ko?” “Eh, Amma kamar jiya kaine muka ragewa hanya da daddare zaka sauka hotel ko.” “Exactly! ‘yatah.” Dr Nuraddeen yafad’a cike da mamakin yanda tagano shi yana miqawa little hannu. “Bawan ALLAH baka ganeni bane, nine fa wanda kuka taimakawa daren jiya da taxxi d’in data d’aukoni ta samu matsala, Katina.!” “Eh maigida natuna..” little yafad’a yana d’an dafe goshinsa inda yabugu, da alama wajen zafi yake yimasa, “To barka da arziqi, kuzo mana ga mota can kada kutsaya abakin titi ga rana sosai, ga motar mucan kushiga kafin afiddo waccan d’in ko don yarannan.” Yaqarasa maganar jikinsa har rawa yakeyi yawuce gaba yanayi yana waigowa yana kallon su, idan ya kalli little ya kalli yaran har suka isa jikin motar ya bud’e masu suka shiga, ‘yan jarida kam ba magana ga labaran da zasu iya bugawa amma tsananin go slow da taron mutane yahana tunda motacinsu nacan baya. Anyi anyi aciro motarsu little amma taqi tashi balle asa ran za’a cirota don haka sai Dr Nuraddeen yace suciro kayansu sai su ajiyesu gida idan yaso daga baya in ancire motocin ajikin wajen sai yadawo ya d’auka, duk da little baiso hakan ba haka yayi haquri sukaje shi da drivern daya d’auko Dr Nuraddeen suka kwaso kayan aka zuba a boot, sannan yaba wani jami’i cikin jami’an tsaron da baiji ciwoba maquddan kud’i yace, a d’auki mutun ukun da sukaji rauni akaisu asibiti, sauran kuma suraba in Sha ALLAH zai biyo bayansu. Sannan suka d’auki hanyar zuwa anguwar su batool, shi dai Dr Nuraddeen baisan ko Ina ba acikin garin asalima sai kalle kallen yanda garin ya sauya gaba d’aya yakeyi don komai ya canza badon ana rubuta wasu abubuwa da wurairai ba zai iya rantsewa yace ba’a cikin kanon daya sani yake ba, drivern kawaine daya san waje ke tuqinsa cikin natsuwa da kwanciyar hankali har suka isa anguwar, ita kanta batool taga wasu canje canje da dama tunda shekara bakwai ba wasa bane, hatta gidan nasu data hango ancanza masa tsarin wajen qofar shiga da fenti sai wasu sabbin gine gine data gani acikin anguwar tasu, ana kaiwa bakin qofar gidan drivern yayi horn saboda abud’e gate a tsammaninsa zasu shiga ciki ne Dr Nuraddeen yace a’a ya tsaya waje tunda wucewa zasuyi basai an bud’e ba. Abba dake tsaye yana faman safa da marwa lokacin angama saukar alqur’anin ana addu’a suna jin horn gaba d’ayansu sukace Alhamdulillah tamkar an sanar masu da cewa su d’inne, da sauri su uncle da Abba sukayo waje jikinsa har rawa yakeyi yana qoqarin fad’uwa amma haka yaci gaba da nufatar bakin gate d’in da sauri da sauri, daidai lokacin mai gadi ya hangame gate d’in batool tafito ita da little suna rirriqe da gambunan motar, wani irin farinciki ya lullub’eta lokacin data hango mahaifinta kyakkyawan dattijo da gaba d’aya gashin kansa izuwa na fuskarsa yayi fari saboda tsufa, Amma hakan bai hana ka hango kyawonsa da hasken fatar da ALLAH yayi masa wanda adalilinsa ake kiransa da alhaji umar fari, ahankali take takawa izuwa garesa don bazata iya rugawa ba idanuwanta na zubar da qwallan farinciki, yayin da shikuma yafad’i qasa had’e dayiwa ALLAH sujudushshukur, su uncle ma tsaye sukayi suna dariya had’e dasa hannuwa suna goge qwallan da suka zubo masu yara da manya kuwa sukayo ruu wajenta suna yimata oyoyo. daqyar ta iya samu suka barta taqaraso wajen mahaifinta da alokacin ya d’ago daga sujadar da yayi, wani irin kuka ta kucce dashi had’e da durqushewa agabansa ta dafa qafafuwansa tana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Kayafeni Abbana natuba, nayi nadamar duka abubuwan b’acin ran dana saka ka aciki, nayi tir da halina da nazamo bijirarriyar ‘ya agareka bayan duka soyayyar daka nunamun, haqiqa inuwar iyaye da kuma alfarmarsu da ‘ya’ya suke samu awajensu tafi qarfin wofantarwa da kuma fifita ra’ayin zukatansu akanta, Abbana…” Bata qarasa ba da sauri Abba ya duqa ya d’agota shima yana hawayen sannan yasa yatsunsa akan fuskarta yana goge mata itama hawayen dake zubowa afuskarta. “Ya Isa haka Batool, duk da laifin nakine amma kuskuren nawane, mezai Hana iyaye sudinga fahimtar ‘ya’yansu da kuma kwatanta yimasu adalci, tabbas ni nahaifeki Amma banida ikon sarrafa rayuwarki da kuma zuciyarki tayanda zance lallai sai kinyi abunda nake so, ALLAH nagode maka, kaine maji roqon addu’ar bayinka ya ALLAH, Ina godiya agareka daka iso mani da ‘ya ‘yana lafiya.” Yaqare maganar tare da rungumota ajiki yana maijin wani irin farinciki, Kallon little dake tsaye dasu uncle h ana gaggaisawa yayi bayan yayiwa Dr Nuraddeen godiya yara sunciro masu kayansu sun wuce, a hankali ya bud’e masa d’ayan hannunsa yana fad’in. “Zo mana yarona, ko har yanzu baka haqura ba fushi kakeyi da abunda abban naku yayi maka?.” Da sauri little yaqarasa wajensa cike dajin kunya yad’an russuna yana gaishesa, cikin hawayen nadamar abunda yatab’a yimasa randa yadawo da batool gida ya saketa tayi wajensu uncle tana gaishesu shi kuma yasa duka hannuwansa biyu ya rungumo little sosai ajiki yana fad’in. “Haba Nuraddeen, nifa abbanku ne, don me zaka nesanta kanka agareni? kai da batool matsayi d’aya kuke dashi yanzu agurina, don ALLAH kayafemun duka abunda nayi maka abaya ko da sau d’ayane ka amsheni amatsayin mahaifinka kaima.” Shidai little baice komai ba don yanzu shima hankalinsa na wajensu baffa, ya matsu yaje garesu da albishirin mahaifiyarsa tabashi damar zuwa garesu tare da zuwa qasar da mahaifinsa ya tafi ya nemosa, Wanda ya tabbata hakan zai yiwa su baffa dad’i sosai, muryar Abba daya ji yana fad’in ko sai naduqa qasa zaka yafemun laifina d’ana had’e da qoqarin duqawar tasashi sairin fitowa daga tunanin da yake shima ya rungume abban yana fad’in. “Abba duk abunda zakuyi mana aduniya kunfi qarfin duqawa agabanmu domin soyayya takansa kuyi mana hakan, wancan abun daya faru Abba yariga daya wuce, ka yafemana bisa damuwar da muka saka ka aciki domin mun dad’e da fahimtar hakan kuskurene.” ‘Dan juyawa yayi tacan gefen gate ya hango su hassana sun b’uya suna leqo mutanen gidan, don kam yanda sukaga ana koke koke bazasu d’auka na farinciki bane dole suyi takansu tunda d’an banzan wayone dasu, Abba ga matanka can sun b’oye wataqil fushi suke baka tarbesu ba. Daidai lokacin ya hango shurahbil ya nufi wajensu don tun d’azu batool ke nuno masu irin ‘yar b’uyar da sukeyi suna leqowa su koma ana dariya shine yatafi wajensu shima yana dariyar. Hannu ya miqa masu har hassana zataje, hussaina tajaye hannunta tana fad’in. “Ke Hassan karkije kema asakaki kuka, bakiga wancan garin mutum mai farin gashin yasa ummanmu nildown tana kuka kuma shima wai kukan yakeyi, sai nafad’awa kaka wannan sunfimu iya muguntar ikram da take cewa munayi idan mun sakata kuka.” Bushewa da wata irin dariya shurahbil yayi har yana riqe ciki kafin daqyar ya samu ya tsaidata yace. “Kunga, uncle bazai yimaku mugunta ba, ai kinga ni bana kuka sai dariya ko?,” “Eh amma dariyarka tayi yawa kaima, bakyau inji kaka.” Hassana tafad’a tana kallonsa, d’an d’aure fuska yayi had’e da durqusowa saiti tsawonsu y miqa masu hannu. “To nadena kuzo muje ko?” “Zakije hussaina?” Ganin ta miqa masa hannu yasa itama bata tsaya wata wata ba tamiqa masa hannun yariqesu suka nufi wajen da har lokacin su uncle ake tsattsaye ana sake gaggaisawa sannan aka shiga cikin gida fuskokin kowanensu d’auke da farinciki, tana ganin mahaifiyarta hajia mama tarungumeta cike da farinciki, STORY CONTINUES BELOW  Murmushi hajia mama tayi tare da d’ora hannunta agefen fuskar batool tace. “A gaisheki d’iyar albarka sarkin kafiya, wato haka kika yimana tafiya batare da kin fad’a mana ba duk kika d’aga mana hankali ko, wannan wace irin rayuwace haka, ALLAH yasa ba haka kike bawa mijin naki da gwaggon yara ciwon kai da kafiyar nan taki.” ‘Dan cije baki Batool tayi tana dariya sannan yace. “Ayi haquri hajia mama, kewarku tasa bazan iya jira ba, kuma nasan idan nafad’a kema zaki hanani kamar yanda abbana yahanani, gashi zuciyata nafad’amun kamar cikin nan bazai barni in sake had’uwa dashi ba shiyasa, ammafa munyi arziqi har sau biyu.” Nan fa tashiga Basu labarin abunda yafaru, Abba dasu uncle suka shiga jinjina al-amarin ubangi, tabbas addu’a gaskiyace kuma duk wanda yayita ALLAH na sauqaqa al-amurransa saidai kawai qaddararce baza’a guje mata ba, haka itama sadaka tana tunkud’e kowace irin fitina ce aduniya, mafarki kuwa baya tabbata gaskiya sai abunda ALLAH yaso acikinsa, kusan atare duk ahalin gidan dake waje d’aya aka shiga yiwa Allah hamdala kafin hajia mama tace. “Wannan abun daya faru izinane ga rayuwarki data mahaifinki harma damu duka, amma alhamdulillah tunda ALLAH yakawo sauqi cikin al’amarin, duk mutumen dake tsananta addu’a arayuwarsa to haka ALLAH zai dinga sauqaqa masa al-amurransa, idan ALLAH yayi nufin silin sai fad’o maka inkana addu’a to sai kaga kana zaune qasar silin ta burbuso maka a fuska saboda addu’ar da kayi, to shi Kuma ALLAH idan ya rubutowa mutum qaddararsa to ba’a kankare masa ita, don haka sanadin addu’a sai a sauqaqa masa ita, sai kaga ta tabbata akanka amma cikin sauqi, don haka muriqe addu’a acikin kowane lamari basai munajin tsoron faruwar wata musiba akanmu ba, sai muga ALLAH na tafiyar da rayukanmu cikin sauqi, ya ALLAH ka sauqaqa mana dukkanin wani Abu daya tsananta.” Duk aka amsa da Amin, nan aka halarto da abincin kowane part kowa yaci yasha ya qoshi su hassana na laqe da shurahbil sunqi yarda da kowa saida sukaga anzage anata fira kowa yasaki jiki sannan suma suka saki nasu jikin, Little nahutawa yayi sallama dasu ya nufi bebeji wajen su baffa yanajin wani nishad’i aransa. ••• ••• ••• Dr Nuraddeen kuwa nabarin anguwar suka nufi qauyensu, tun daga kan hanyar shiga qofar qauyen yafara ganin manya manyan sauye sauyen kala kala, haka ya dinga bin ko ina da kallo cike da mamaki, tabbas ako Ina ana samun cigaba don ko aqauyen nasu yagani ba laifi, ganin motocin ‘yan jarida lokacin da suke shigowa cikin qauyen ya tabbatar masa da har yanzu suna kan dakon jiransa kenan! Adai dai lokacin su kuma su baffa sunka fara miqewa suna qoqarin shiga cikin gida saboda yanda sukaga taron ya soma yawa, kawai sai sukaga d’aya daga cikin ‘yan jaridar ya nufatosu had’e da yimasu sallama, Suna juyo motar Dr Nuraddeen da ‘yan jarida kebiye da ita tayi parking adaidai lokacin….. Duk yanda little yaso yayi mata maganar mahaifin nasa daya dawo kuma ya sadasu awaya hakan gagara yayi don koda yasake gwada kiran wayar sai yaji ance masa kashe take, d’ago kai yayi ya kalli mahaifinsa da nan take yaji wani sauyi atattare don har hakan ta bayyana a fuskar, kenan habibty d’insa fushi take dashi sosai ya tambayi kansa, wato zuciyar ce ta amsa masa da cewa to ai ta cancanci tayi fushinma da yafi wannan domin al’amarin ne da quna sosai azuciya, murmushi little ya sakar masa tare da cewa. “Baba bara nakira maka gimbiya.!” STORY CONTINUES BELOW  Saida yafad’a sannan yayi saurin toshe baki yana dariya, ya manta agaban mahaifinsa yake bai kamata yafad’i hakan ba yace cikin ransa, waskewa yayi tare da cewa. “Aww Ina nufin batool baba.” Murmushi Dr Nuraddeen yayi had’e da cewa. “Babu damuwa.” Yana rufe baki saiga aunty marwiyya ta iso wajen tana tafa hannuwa. “Ikon ALLAH, yanzu Kai little shine zaka jaye mahaifinka anan ana son ganinsa, to kazo maigidanka nason ganinka mu zamu wuce.” Hakan yasa ya fasa kiran ya kad’a wayar aljihu sannan yabi bayanta, bayan ansake tab’a wata firar little yayi masu rakkiya har inda zasu hau mota suka wuce shikuma ya dawo, Ataqaice dai ranar har kusan goma na dare suna karb’ar baqi masu zuwa yiwa Dr sannu da zuwa da masu taya baffa murnar dawowar d’ansa harma da masu zuwa tsogumi, Wanda hakan yasa little ya kasa komawa wajen batool saidai sukayi waya inda anan ya sanar da ita komai akan dawowar mahaifinsa wanda ya kasance shine mutumen daya taimakesu ayau, duk da tajima tana zargin mijin nata nada alaqa da mutumen aranta hakan bai hanata mamaki ba sosai, musamman da taji koshi waye, tayi farinciki sosai tare da jin dad’i, cikin daren ta iske mahaifinta tabashi labarin mahaifin little yadawo shima nana take yanuna farincikinsa, da kansa ya d’auki waya ya amshi lambar da tayi waya dashi yakirasa yana tayasa murna, nan little ya had’asa da mahaifinsa yayi masa barka da isowa tare da tabbatar masa da cewa gobe zasu biyo hanya suma in Sha ALLAH. Baba nusaiba kam yau gari nasu, abinci na musamman ta shiryawa babban d’a tare da babban jika, sannan ta kwashikke kayan yaranta mata tamayar a d’akinta tasa aka sharesa tass akasa qatuwar katifar nan mai tuli irinta family ta feshesa da room freshner da sababbin labulayye yayi gwanin sha’awa, koda suka shigo gidan su uku saisu baffa da suka rakkosu acan tayi masu masauki wanda hakan ba qaramin dad’i yayiwa baffa ba ta kawo masu lafiyayyen abincin data shirya masu sukaci suka sha suka qoshi sannan su baffa Usman sukayi masu sallama don lokacin dare ya miqa har qarfe d’aya tayi, Dr Nuraddeen yaso yabi su baffa ya kwana acan wajen mahaifiyarsa amma shauqin soyayyar d’ansa tasa ya shafa’a har dare ya raba suna zaune su uku suna fira cike da soyayya, duk little ya kalli mahaifinsa sai yaji wani dad’i aransa ya rufesa marar misaltuwa, yayinda shi kuma Dr ji yake ya tsani kansa sosai idan yakalli yanda mahaifinsa yakoma, Wanda ya tabbatar wahalace da kuma damuwar rashinsa akusa dashi ta jefasa aciki, nanma kasa jurewa yayi saida yayita kuka yana roqon mahaifin nasa da d’ansa yafiya don yasamu nauyin da yakeji aransa ya ragar masa. Har aka kira sallar asuba suna zaune suna fira Dr nabasu labarin halin daya tsinci kansa aciki awaccan qasar da irin rayuwar da yayi, sun matuqar tausaya masa sosai don kam ba rayuwace mai dad’i ko ingantacciya yayi ba daga qarshe duk suka taru suka yafi juna tare da addu’ar ALLAH yabawa kowanensu tsawon rayuwar da zasuji dad’in juna, shidai baffa murmushi kawai yayi tare da amsawa da Amin don yasan shikam ai tafiya tayi tafiya saidai fatan cikawa da Imani, Saida baffa yatada baba nusaiba sannan suka wuce masallaci bayan sunyi arwala, da aka gamo sallah Dr Nuraddeen ya kalli mahaifinsa bayan ya gaishesa sannan yace yayi can babban gida wajen mahaifiyarsa. Baffa ya amsa masa da “To ALLAH yatsare hanya ka gaisheta.” Ba kunya ba tsoron ALLAH little yaja qafafuwa yanda kukasan zariya yabi mahaifinsa yana yiwa baffa sai yadawo. Baffa ya amsa masa da “Adawo lafiya” yana murmushi. Baffa nakomawa gida yanemi waje ya kwanta saboda akwai bacci sosai a idanuwansa, kan kuma kace me har yayi awon gaba dashi. Su Dr kuwa Saida suka lelleqa d’akunan baffa Ali da baffa Usman suka gaishesu sannan suka wuce d’akin Yaya hawwa, tanaji anturo qofa tace. “Bilki ce?, Wai Ina yaron nan nura yaje ko yamani wayau yasake tafiyarsa.” STORY CONTINUES BELOW  Dariya sukayi atare Dr. Nuraddeen yaje kusa da ita ya zauna tare da jawo hannunta yariqe yana d’an mammatsa mata sannan yace. “Ina zanje kuma nabarki innarmu?, Barka da safiya, Ina kwana kin tashi lafiya?” Saida ta zare hannunta tad’an shafa fuskarsa sannan tace. “Lafiya klw, Ina katafi tunjiya baka dawo ba.” “Kiyi haquri innarmu, a gidan baffa na kwana kinga nan babu waje, amma yau anan zan kwana tare dake.” “A’a nura, kaje ka dawo da matarka, a wajenta yakamata ace ka kwana ba’a nan ba, Ina ance batayi wani auren ba ko?” “Eh innarmu, Amma abune mai wahala tayarda nadawo da ita koda naje.” “Kaje zanyi maka addu’a, nasan zuciyarta mai kyauce zata biyoka kudawo tare, idan ba haka ba kuwa kada ka kuskura kadawo nan har saita amince kaji ko?.” Shiru yayi yana mamakin maganganun dake fitowa daga cikin bakin mahaifiyarsa, wai yau ita da kanta take bud’e baki tace yaje ya dawo da matarsa duk irin tarin tsanar da tayi mata ada, tabbas rayuwa na koyar da mutum darasi aduniya kuma duk abunda yasaka kuka to da SANNU SANNU wata rana zai saka dariya, yana wannan tunaninne yaji muryarta kamar zatayi kuka tace. “Bakaji bane nura!, ko kana haufine da jin tsoron kada in aikata mata wani abunne makamancin waccan da nayi?” “Ko kad’an innarmu, nasani bazaki yimata komai ba, wancan ma kuskurene kikayi da Babu wani mahaluqi aduniya d’aya wuce yinsa, zanyi yanda kikace, zan kuma yi iya qoqarina, saidai idan takasa amincewa to kiyi haquri zan dawo na Ida qarasa rayuwata hakan don ko kad’an bazan iya takurata ba.” “Karka damu, zata amince in sha ALLAH kaji ko?, Ina shi wannan yaron ko yatafiyarsa shima.” Kallon little Dr yayi alamun dashi take yace. “Ganinan kakata mai kuka!, Ban tafi ko inaba nima ina nan tare da babana, wato so kike natafi na barki daga ke sai shi ko?, to Babu inda zani nazo kenan!” “Shikenan, ai ni banida ja, kayi zaunenka kayita kallon mahaifinka kanajin sanyi, nima duk da bana gani ina matuqar jin dad’i azuciyata muryoyinku danakeji.” Haka yayita tsokanarta tana basarwa har ya gaji yabari ya shiga bawa mahaifinsa labari akan iyayensa na borno da kakanninsa wato Dr nura da fatima sai dady da umma da kuma ammie, sosai Dr Nuraddeen yashiga jinjina al’amarin ALLAH yanda ALLAH ya tsaro b’atan matarsa zuwa wancan garin sai kuma zuwan iyayenta acan don ya wanzar da qulluwr alaqar dady da umma mahaifiyar rashida da kuma alaqar d’ansa little da batool, tabbas al’amarin ALLAH da girma yake, tabbas zaiso yaga wud’annan irin mutane masu tsananin karamci da kuma halacci arayuwa dako atarihin mutanen da masu tsananin karamci bai tab’ajin irinsu ba. Ana haka baffa Usman da baffa Ali suka shigo, gaida Yaya hawwa sukayi sannan suka bud’e sabon shafin fira, inda anan Dr Nuraddeen ke tambayar baffa Usman yanda akayi mahaifiyarsa tasamu lafiya wanda tun jiya yake son ya tambayi hakan. Kuka yayi sosai tare da rungume mahaifiyarsa yana maijin tausayinta akan qalubale da wahalhalun da tasha aduniya, haqiqa duk wanda ke tare dasu yakasa d’aukar darasin yanda duniya ke tafiyar da rayuwar d’an adam to tabbas yayi nisa koda kuwa zuciyar qarfene dashi, daga qarshe yayiwa ALLAH godiya tare da roqonsa yaci gaba da yafewa mahaifiyarsa har iya qarshen rayuwarta, haka itama Inna ruqayya yaji d’aci sosai aransa data jinkirta tuba har ALLAH ya amshi ranta, itama ya roqi ALLAH daya gafarta mata kuma ya haskaka kabarinta sannan yayiwa su baffa gaisuwar rashinta. ••• ••• ••• A can borno kuwa tuni labari ya Isa ga kunnuwansu dady da umma don kai tsaye Dr nura yaje yasanar dasu zancen dawowar mahaifin little, inda umma tanuna hakan ko ajikinta don ta d’auka almarane har sai bayan sallar azahar da dady yazo da sauri ya kunna tv saboda kiran da Dr Nuraddeen yayi masa yace su kunna sugani gaya nan ana fira dashi, ganin yanda abubuwan suka kasance da kiran dasu Yaya Maryam sukayi mata suka qara sanar da ita yasa ta gasgata hakan, yanda aka nuno baffa mahaifin Nuraddeen shine Abu na farko daya tab’a zuciyarta har yasata zubar da hawaye, tayi kuka sosai tare da nadamar irin tsattsauran hukuncin data d’auka akai, aranar babu wanda yafad’o mata arai, yanda ako yaushe yake tausarta idan ranta ya b’aci da irin nasihohin da take yimata akan tsaurara bincike kafin yanke hukunci da tsayuwa akan gaskiya komai d’acinta da rama alkhairi ga wanda yayi maka sharri, da haquri akan kowace irin zaman takewa amma tsananin soyayyar da takeyiwa ‘yarta da ganin yanda kamar aka cutar mata da ita yasa tawatasar da duka wud’annan nasihohin tabi son zuciyarta suka d’auki alhakin bawan ALLAHn da akoda yaushe bayada burin daya wuce ya kyautata ga dukkanin wanda ya rab’esa, shidai dady banda kallonta babu abunda yakeyi har taci kukanta mai isarta tayi shiru sannan yace. STORY CONTINUES BELOW  “To kinga irin ranar da awancan lokacin nake guje maki zuwan irinta, ba don kin d’auka da zafi sosai ba da bazaki rasa tunanin cewa taya mutum naji da ransa da hankalinsa zai guji qasarsa, iyayensa, iyalinsa da ‘yan uwansa ya zab’i zama inda babu ko d’ayansu awajen bayan sune abun tutiyarsa aduniya, azzannu zanbun walau kana haqqun, wato zato zunubine koda yazamo gaskiya amma kai da ganin hakan kasan akwai wani b’oyayyen alamari da d’aurin goro acikin wannan batu, yanzu kam koma meye anriga an gama kuma tunaninki da damuwarki nasan duk bazasu wuce b’oyewa bawan ALLAHn nan gaskiya da jininsa da kukayi har tsawon wannan lokacin, to Alhamdulillah dama hankalinku da namu ba irid’aya ba, duk da ambi turbar yanda kukaso daga baya munyi tunani kuma mun had’a yaronnan da kakansa da sauran dangin mahaifin nasa, duk wani sha’anin aurensa da qaruwar daya samu dasu akeyi, anb’oye maku hakanne don azauna lafiya daku tunda ku mata baku fiye tunani akan abunda ke daidai ba.” Wani sanyi umma taji aranta cike da kunya tamiqe tabar wajen don bata masan me zata ceba, dariya dady yayi had’e da cewa. “Ai nan kukafi gwanewa da auki, wato kunya bayan kun tafka shirme.” Ummie dake gefensu zaune tayita dariya har tana fad’in. “To dama ai mu raunine damu, basai ka goranta mana ba, Wanda kuma duk ya tsaya biye mana shima irin wannan kunyar da mukeji zaiji kaga babu kafi balle na d’ara koda kuwa namijine.” “Ah to ai ku kuka sani, daku har wanda ya tsaya biye maku, Ina ai nima haka kika izani naje na biye maki da tsufana ka dinga tata mani rashin mutunci agida, kullum sai naji kunya idan aka tafka wata tsiyar, Amma yanzu alhamdulillah ALLAH yaqara bamu haqurin zama har zuwa lokacin da mai rabawa zata rabamu.” “Amin ya ALLAH, Amma saina nafad’awa hajia nafisa yanzu kagama yimata gugar zana, bayan abunda yawuce yariga daya wuce.” Ummi tafad’a tana dariyar dady. A fannin hajiya nafeesa kuwa yau ji take tamkar tabar doron duniya akan abubuwan data aikata abaya, gaba d’aya ta gagara fidda farincikin da take ciki itama saboda jimamin aibata little data dingayi tana kira masa shege duk da kuwa tasan ta dad’e da roqonsu gafara, safa da marwa ta dingayi a tsakar falonta tana tunanin yanda yaau zata had’u da umma ta d’aga kai ta kalleta, yanda zata kalli Rashida data jefa da mummunar kalma tazina alokacin halattaccen mijinta ya bayyana agareta, yanda zata kalli Nuraddeen data kira da shega ayayin da yake agaban mahaifinsa, so take tayi hawaye amma sunqi zuwa, natsuwarta da zaune da tsaye duka sun gagareta saima wani zazzab’i da takejin na Shirin taso mata, bata san lokacin data fara sabbatu tana fad’in. “Kaicona kaico ni kaina, wannan itace ake kira da ranar nadama, ranar xubewar kima da matsayi, ranar da mutum ke tsanar harshensa, ranar da dana sani ke dabaibaye qwaqwalwa tare da raunata qarfin gangar jiki, ALLAH kasani na tubarwa laifukana, ya ALLAH kayafemun kabani qarfin halin fuskantar kunyar abunda na aikata.” Haka tayita suruttai ita kad’ai tana d’ora hannu akai tare da zagayar falon, zuciyarta sai bugawa takeyi tana fargaba tare da hasaso lokacin da zatayi arangama da wud’annan fuskoki data aibata agaban wanda yawankesu daga wannan zargin. Rashida kam bacci qaurace mata yayi adaren, babu abunda idanuwanta ke hakaito mata sai fuskar habibinta, babu zantukan da kunnuwanta ke sauraro mata idan ba nasa ba, musamman alokacin da take cewa. _Babban qalubale shine rashin rouhi a gangar jikina da kuma kad’aicin abokanan da zasu tayani ingantacciyar rayuwa idan ba kayan aikina ba_ ta tabbata cewa awannna gaba’ar saqone take isar mata domin itace wannan rouhin nasa da yake fad’ar babu a gangar jikinsa don ya jima ako yaushe yana fad’a mata cewa itace rouhin gangar jikinsa, idan babu ita atare dashi to tabbas bazai samu ingantacciyar rayuwa ba, ayau ta yarda da hakan kuma ta aminta da kalamansa, saqonsa ya iso kai tsaye azuciyarta saidai bata tunanin karb’arsa hannu biyu bayan ya shafe shekaru batare da yayi tunanin tunata koda na rana sau d’aya ne, haka ta kwana tana faman juye juye akan gado had’e da bitar duk wasu kalamai nasa har aka kira sallar asuba ta tashi tayi sallah tana mai d’oki da kuma dakon zuwansa gareta akowane lokaci. STORY CONTINUES BELOW  ••• ••• ••• Tun daga can gida baffa yasa aka d’auko abun karyawa aka kawowa su Dr nan gidansu baffa yana biye abaya don shima bai karyawar ba, nan d’akin Yaya hawwa aka kai kayan ga itama Inna Bilkisu ta shirya masu lafiyayyen abun kalaci takai can d’in duk suka taru waje d’aya suka karya ana fira cikin jin dad’i da farincikin sake had’uwarsu waje d’aya, gani sukayi baffa Ali ya miqe ya koma gefe yana goge hawaye. Tashi baffa yayi yakoma wajensa ya zauna tare da d’ora hannunsa saman nasa yayi saurin jayewa tare da matsawa gefe yanaci gaba da sharar qwalla. “Meye haka Aliyu? Me yafaru kake guduna Kuma?” “Ba gudunka nakeba Yaya, gani nakeyi kamar banyi maku adalci ba idan Ina cakud’a cikinku duk da kuwa wannan cutar da take tare dani, idan girman karamci da kawaicinku ya hana ku qyamaceni bai kamata ni kuma son zuciya yasa naciga da cakud’a daku ba, domin shine ya kaini yabaro tun abaya.” “Haba Aliyu, har sau nawa kakeso kaci gaba da muzanta kanka agaban idanuwan mutane?, Meyasa kake son tilasta kanka akan saika gamsar damu ka canza kuma kayi nadama baayan mu tuni zukatanmmu sun amince kuma sun gamsu da hakan, don ALLAH kadena qasqantar da kanka haka acikin mutane ya isa kaji ko.?” “A’a kabarni naci gaba dayin hakan don nunawa zuciyata datayita azani bisa hanyar daba gaskiya ba da nunamun cewa ni wani ne in nuna mata cewa ni ba kowa bane, banida wani girma ko d’aukakar da zataci gaba da kamba mani aduniya balle har tasake cin galaba akaina.” “Kayi hakan da dad’ewa baffa, Kuma insha ALLAH ALLAH ya yarda da tubanka, don haka kadena qasqanta kanka baya son haka domin shi da kansa yace ya karrama d’an Adam adoron duniya, kaga baici ace kuwa kana gardama hakan ba.” Baffa Usman yafad’a yana zaunawa kusa dashi yayinda shi kuma Dr Nuraddeen ya qura masa idanuwa yana karanto irin damuwar dake kwance a zuciyarsa tare da alwashin gusar masa dasu ko don yarama cutarwar da yayi masa da alkhairi. Kamar dai jiya haka yauma gidan aka wuni mutane na shigowa ciki kuwa harda Abba dasu uncle h, inda little ya gabatar dasu ga mahaifinsa amatsayin iyayen matarsa kuma ya gabatar dashi a matsayin mahaifinsa, Abba kam yaji matuqar nauyi akansa sosai bisa abubuwan da suka faru amma haka ya daure ya bayyanawa Dr Nuraddeen komai abunda yafaru wanda daga baya yayi nadamar hakan batare da sanin cewa ashe yana gab da dawowa ba, Dr yaji Babu dad’i Kuma abun ya Sosa ransa yanda akankusa hanawa d’ansa aure saboda ana zargin cewa shi shegene bayada uba, Amma komai yariga daya wuce tunda gashi ya dawo antabbatar da cewa d’ansa d’an halak ne don haka bazai iya maido da hannun agogo baya ba, cikin mutuntawa yayi masu godiya tare da fatan alkhairi akan d’orewar zumuncinsu sannan suka tafi, ganin rana na somayi Dr Nuraddeen yaba little kudd’i yaje yayi masu bkin d’in jirgi don lallae lallae yau bazai sake kwana garin ba har sai yaje wajen habibty d’insa kamar yanda mahaifiyarsa ta umurcesa, yanzu kam gaba d’aya baya fahimtar komai kuma baya gane komai inba ganinsa yayi wajen habibty d’insa ba gashi tunda little yafita bai dawo ya barshi sai faman duba agogon hannunsa yakeyi, ashe shi saida yabiya wajen batool yaga tashinta da yaransa sannan yatafi wajen booking d’in ticket d’in jirgin, cikin sa’a ya samu akwai har sauran ticket uku na jirgin da zai tashi misalin qarfe biyu narana, nan take yayi duk abunda ya kamata sannan ya kama hanyarsa ta komawa bayan ya tsaya ya saiwa mahaifin nasa waya da layoya har guda biyu mabanbanta network. Yana isa ya isko dandazon mutanen da suka kawowa mahaifin nasa ziyara ta b’angaren ma’aikatar lafiya, yana ganinsa ya taso batare daya damu da mutanen daya bari wajen ba. nan yayi masa bayanin jirgin da suka samu wanda zai tashi qarfe biyune na rana, cikin jin dad’i ya d’an bubbugi kafad’ar little yace ya maza yaje ya shirya yana zuwa shima da zaran ya sallami mutanen, Bayan yayi sallama dasu yaje ya sanarwa da Yaya hawwa zai tafi tayita sanya masa albarka da addu’ar ALLAH yakaisa lafiya yasa ya dace su dawo tare da matarsa cikin qoshin lafiya, anan bayen dake shiyar Yaya hawwa yashiga ya watso ruwa agurguje ya shirya, dama ya sanar da su baffa don haka suka d’auki hanyar zuwa airport d’in auna masu yimasu addu’ar zuwa lafiya sudawo lafiya. STORY CONTINUES BELOW  Kasancewar koda suka isa airport d’in akwai sauran lokaci yasa little ya zauna yakira battool ya sanar da ita don mantawa yayi da yaje d’azu bai fad’a mata ba, addu’a tayi masa tare da fad’a masa Abba yasa an d’auko motarsu da sukayi accident jiya har an gyara, Saida yace tayiwa Abba godiya kafin yakirasa sannan ya kashe wayar yakira dady da Dr nura ya sanar masu suna tafe shida mahaifinsa kuma jirgi zasu biyo. Wayar mahaifiyarsa ya gwada kira bai samu ba don tun safe ya kirata lambar akashe, murmushi yayi tare da kad’a wayar a aljihu sannan yaciro ta abban nasa ya dinga saka masa lambobin da yasan zai iya buqatarsu ciki kuwa harda ta mahaifiyarsa da yayi saving da my wife. Sannan ya miqa masa yana fad’in. “Baba ga wayarka, nasaka maka lambobin da zaka iya buqata.” Karb’a yayi had’e dayin murmushi yace “agaisheka ALLAH yayi maka albarka.” Sannan yafara dudduba lambobin har yakai gata Rashida da yayi masa saving da my wife, editing ya shiga ya mayar habibty sannan ya jefa wayar a aljihu little na kallonsa ta gefen ido yayi murmushin shima, aransa yace. “ALLAH dai yasa Kar habibty d’innan ta kwabsawa babansa don yalura ba kad’an yake jinta ba.” Yana wannan tunaninne yaji anfara kiraye kirayen sunaye har aka kai ga sunansu suka tashi suka shiga, bayan sun zauna cikin jirgin da yake waje d’aya suke kafin jirgin ya tashi Dr Nuraddeen ya ciro wayarsa had’e da kaikaita idanuwan little yashiga akwatin tura saqo yafara rubuta saqo kamar haka. _I am sorry for all the pain, I am sorry for the tears I am sorry for the anguish, But please fulfill my only wish, Please forgive me this time, And I won’t do this again, Nothing to pretend, Just forgive me! I am sorry!_ Ya karanta yafi aqirga kafin ya lalubo lambar habibty d’insa ya tura mata, Rashida da bata dad’e da kunna wayar ba tana zaune taji qarar shigowar message ta d’auko wayar ta karanta, ganin lambace yasa batare data damu da tabada amsa ba ta ajiye wayar, can bayan wasu mintuna tasake jin qarar shigowar wani message d’in ta d’auko wayar ta sake dubawa tana karantawa kamar hakan. _Iknow it’s very pain and It’s hard to make you understand, But, believe me I don’t pretend, Mistake has happened and I won’t deny, Blame on the situation to defy, I just want that you forgive me through, So that I don’t feel blue, Please forgive me now habibty!, b’coz it’s all part of our destiny and I don’t have any words or how! Forgive me! Habibtyyy_ Awannan karon wasu zafafan hawaye suka zubo mata domin tafahimci daga Ina saqon ke zuwa, juya wayar ta shigayi tare da rashin sanin mema zata cemasa kawai ta cillata saman gadon takife tana kukan da da’ace hawaye na qarewa to da tsakanin jiya da yau nata sun qare kaf. Tun daga umma dasu Dr Babu wanda ya sanar da Rashida zancen zuwan Dr Nuraddeen saboda yanayin da suka ganeta aciki, gashi dama tun safe bata fito d’aki ba har zuwa wannan lokacin, abun karinta dana Rana duka saidai mai aiki takai mata a d’aki hakan yabasu Fatima damar yin shire shiren tarbarsu Dr yanda ya kamata kafin su iso, Kasancewar akwai banbanci tsakanin tafiyar jirgi data mota yasa cikin mintunan da basu wuce arba’in zuwa arba’in da biyarba su little suka iso, Gaban Dr Nuraddeen ne ya shiga fad’uwa saboda rashin ganin amsar saqonsa ko d’aya daga Rashida Wanda ya tabbatar tagani kuma tasan shine, hakan yasashi fargabar kada taqi amincewa ta amshesa bayan yayi nadamar abunda ya aikata kuma bayin kansa bane. Little bai tsaya jiran azo d’aukarsuba ya tari taxi, saida suka shiga yakira dady ya sanar dashi sun iso gashi har suna cikin taxi ina zasu sauka yace su sauka gidan Dr suma gasunan kan hanya in Sha ALLAH. Motarsu little Bata dad’e da ajesu ba tasu dady ta tsaya inda a babban falo Dr yayi masu masauki bayan yayi ma Dr Nuraddeen wato takwaransa babbar tarba. STORY CONTINUES BELOW  Rashida kuwa har lokacin tana can a d’aki duk da kuwa qarar tsayawar motar da taji har sau biyu, tsananin bugawar da taji zuciyarta nayi yasata fitowa da sauri tana share qwallar idanuwanta taci Karo dasu umma, ummie, dady da hajiya nafeesa da suka shigo yanzu, da sauri ta qarasa jikin umma tare da fashewa da wani irin kuka dake tsima zuciyar duk wani mai sauraro….. *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ Page___105💎 “A’a, a’a! Rashida meyene haka kikeyi sai kace wata qaramar yarinya?, Don ALLAH ni d’agani kada ki karyani, daga shigowa kongaisuwa babu sai kifad’omun ajiki kina kuka, fisabillahi ko gajiya bakyayi abu tun jiya!” Umma ta fad’a tare da cireta daga jikinta, Riqo hannunta dady yayi suka nufi falo suka zauna itama ya zaunar da ita qasan qafafuwansa had’e da dafa kanta yace. “Yi haquri Rashida, ita rayuwar mumini haka take, matuqar kayi Imani to dole sai anjarabceka, to Alhamdulillah yau Ina cike da alfaharin cewa ‘yata tayi Imani kuma anjarabceta ta canye jarabawar da akayi mata, Abu d’aya yarage shine kimiqa godiyarki wajen ALLAH daya baki ikon canye jarabawar da yayi maki tahanyar rungumar sakamakon da yayi maki da hannu biyu kinji ko.” Cikin kuka ta d’aga masa kai yaci gaba da rarrashinta shi dasu ummi, umma kuwa batace komai ba sai kallon ‘yar tata da takeyi har suka gama bata baki, Dr ne ya shigo shida Fatima fuskokinsu d’auke da fara’a suka gaida iyayen nasu bayan suma sun nemi waje sun zauna, “Ina shi little d’in dr.” Dady yafad’a yana kallonsa. “Ai dady little ba’a magana, don yau shima yazame mana baqo yana can liqe da Dr suna cin abincin.” “Ah to Masha ALLAH, ai haka akeso, banga laifinsa ba iyaye ai rahamane, aqallah shima yanzu zaiji irin dad’in da kowane d’a kiji idan yana tare da mahifinsa, fatan dai sun iso lafiya ko?” “Lafiya klw dady.” Dr yabashi amsa yana kallon fuskar Rashida data bayyanar da mamakinta qarara jin cewa wai little na garin kuma wai harda mahaifinsa, murmushi yayi kafin yace. “Gwaggon yara kinfito?, Yau sai kika yimana yajin fitowa Saida kikaji takwarana ya iso ko.?” Batace komaiba kanta na aqasa ta sake nocesa tana maijin zuciyarta na wani irin matsanancin bugawa da sauri da sauri, ‘Dan harararsa ummi tayi had’e da cewa. “Meye haka son? So kakeyi ka tsargamun ‘ya agabana ne.” “Afuwan ummi, ‘yar takice nakasa gane kanta daga jiya zuwa yau, ita da tayi haqurin shekaru da yawa sai naga tana qoqarin b’atasa tsakanin jiya da yau.” “To ya za’ayi, mubita ahankali, wlh al_amarinne da ciwo, Amma tunda ALLAH yakawo sauqinsa sai a haqura don asamu a cike mizanin lada ko kuwa ‘yata.” Taqarashe maganar tare da d’ora hannunta saman kan Rashida, a daidai lokacin little ya shigo yana shafar ciki fuskarnan tamkar hasken farin wata saboda annurin dake kwance akanta na kasantuwarsa tare da mahaifinsa, ganinsu ya dashi sakin wani murmushi had’e da buga wata irin uwar gyatsa yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  “Alhamdulillah.” Wajen dady yaje ya zauna tare da gaishesa idanuwansa nakan mahaifiyarsa yana son yaga awane yanayi take ciki amma taqi d’agowa, “Barka da arziqi Nuraddeen, yau dai kewa ta qare, gaka ga mahaifinka, don haka sai kayi qoqarin kyautata masa tare da nuna masa nagartacciyar tarbiyar da mahaifiyarka ta jajirce wajen baka, kada ka kuskura kayi abunda zaisa ko kad’anne yaji aransa don baya tare dakai shiyasa kazama haka, Ina yimaka fatan gamawa lafiya tare dashe cikin amincin ALLAH da yardarsa.” “Nagode dady, in Sha ALLAH bazan tab’ayin wani abun daya sab’awa tarbiyar da kuka bani ba, zan zamo d’a nagari atare dashi har sai yaji cewa bababu wanda yayi sa’ar samun nagartaccin iyaye bayansu sama dani, sai na gamsar dashi cewa d’ansa ya tashi a hannun mutanen da sukafi kowa karamci da halacci aduniya, kuma na nuna masa irin irin nagartacciyar uwa da yayi sa’ar sama mani aduniya da zata iya kulawa dani had’e da bani nagartacciyar tatmrbiya ko baya nan!.” “Masha ALLAH, ubangiji ALLAH yabaka ikon yin haka, mukuwa da munci gaba da alfahari dakai har iya qarshen rayuwarmu.” Juyawa little yayi had’e da gaisheda su ummi sannan ya kalli umma ya d’aga mata gira yana fad’in. “Na gaida uwar gidana, babuki ba canzawa komai tsufanki kina nan daram a muhallinki, kujerarki ba gudu ba ja da baya.” “Ja’iri, ja da baya kam ai saidai kar aqara, tunda kasamu batoolu ka watsar dani, balle yanzu da babanka ya dawo nasan nan gaba ganinka sai nacika fayil.” Umma tafad’a tana dariya su ummi na tayata, kallonta dady yayi had’e da cewa. “Kwantar da hankalinki aini hakan yayimun dad’i, daga ni sai ke bawani da zai koma zuwa yana takuramu had’e da ‘yar muryar neman ferfesun tsufa, sai kiyita zuba mani Ina cinye abuna ko ba haka ba.” Dady yafad’a shima yana dariya. Jin sallama da motsin shigowar Dr Nuraddeen da Dr nura yaje yayowa jagora zuwa falon shi ya katse masu firar tasu, da sauri Rashida da gabanta yayi wani irin fad’uwa tamiqe har tana tuntub’e da gefen kujera ta shige d’akinta acan sahenta data nufa. Cikin girmamawa Dr Nuraddeen yashigo falon biye da Dr nura ya zauna qasa kansa na sunkuye qasa yana kallon qasa ya shiga gaishesu d’aya bayan d’aya cikin wata irin jin kunyar da yakeji tamkar qasa ta tsage ya shige. Bayan sun amsa ya d’ago kai yanda zasu iya ganin fuskarsa ya shiga yimasu gaisuwar baba da ALLAH yayiwa cikawa tare da addu’ar ALLAH yajiqansa kuma yayi masa rahama duk suka amsa da Amin. Shiru ya biyo bayan wasu mintuna kafin dady ya shiga yimasa tambayar ya hanya da ban gajiya ya amsa da duka Alhamdulillah sannan ya d’ora da fara bada haquri akan abunda yafaru don dama Dr nura ya gabatar masu dashi a matsayin mahaifin little kuma mijin Rashida wanda a daidai lokacin hajia nafeesa ta had’a ido da little ya sakar mata murmushi taji tamkar ta nitse cikin qasa saboda tsananin kunyar da taji. Yanda Dr Nuraddeen ke magana cikin natsuwa tare da qasqantar da kai da nuna baqincikinsa da nadamar abunda yafaru har kuka na neman yaci qarfinsa yasa dady ya dakatar dashi ta hanyar cewa. “Ya isa haka d’ana, mu musulmaine kuma munsan da qaddara maikyau da marar kyau kuma duka munyi Imani da hakan, wlh mudai baka yimana laifin komai ba, sannan shi musulmi aduk inda take d’an uwan musulmine, don haka ana buqatar tausayi, yarda, kyautatawa da kuma kyakkyawar fahimta a tsakani, abunda ya faru tsakaninka da iyalinka ne, mu bamuda wani zargi akanka ALLAH kuma shine sheda saboda haka ka kwantar da hankalinka, bayanan ma da muka gani a kafafen yad’a labarai wlh sun Isa suwankeka ga kowa, fatanmu ALLAH ya tsare gaba kuma yayi mana kariya da miyagun qaddarori,” “Amin” Dr Nuraddeen yafad’a cikin jin dad’in yanda duka abubuwa kezo masa da sauqi, fatansa d’aya ALLAH yasa awajen habibty d’insa ma suzo masa da sauqi. STORY CONTINUES BELOW  Nan dai yayita godiya tare da d’orawa akan wata godiyar ta kulawa da karamcin da suka nuna masa shi da iyalinsa da kuma ahalinsa daga qarshe yaroqi abashi damar ganawa da Rashida idan da yuyuwar hakan. Dariya dady yayi kafin yace. “Ikon ALLAH, kaikuwa Mai zai hana mutum da iyalinsa?, Ai har yanzu Rashida na aqarqashin inuwar aurenka don tun bayan tafiyarka daidai da Rana d’aya Bata tab’a amincewa da abunda zai shafi auren naku ba, mu daine daga baya mukayi yunqurin samun iyayen naka akai maganar a kotu taraba auren kafin dawowarka saboda gudun kada acutar da ita Amma sai tanuna batada ra’ayin hakan don haka muma dole muka haqura, yanzu tsakaninka da iyalinka ne, idan ta amince ko yaune kanada damar d’aukar abukka kutafi. Shiru Dr Nuraddeen yayi yana tunanin wannan irin Sadaukarwar kai da habibty d’insa tayi masa, koda me zai iya biyanta shi aduniya? Ya tambayi kansa yana goge hawayen da suka zubo masa saboda tsananin tausayinta. Nan dai aka shiga d’an tab’a fira amma shi gaba d’aya hankalinsa na kan ta inda zai iya hangota, ganin hakan yasa dady yayi gyran murya had’e da miqewa yana fad’in. “To malan Nuraddeen, bari mutafi marece nayi gashi anbaro yara agidan, son sai akira masa Rashida mu zamu wuce, duk abunda ake ciki saika tuntub’emu awaya.” Yaqarasa maganar yana kallon Dr nura, sallama sukayi dashi sannan suka fice umma nayi tana waiwayen yanda gaba d’aya ya canza ya zama cikakken mutum, koda yake jiya ai ba yauba tafad’a aranta tare da ficewa su Dr d Fatima nabiye dasu zaauyi masu rakiya, har sunkai qofar fita falon Dr yajuyo ya kalli lite dake zaune kusa da mahaifinsa yace. “Abu sumayya jeka ka kirawo masa gwaggonku kace injini.” Yafad’i hakan don yasan zata iyaqin fitowa sannan tajuya yafice daga falon. Saman kujera Dr Nuraddeen yakoma ya zauna yana jiran fitowar Rashida tare da qurawa qofar da yaga little yashiga idanuwa. Little ne yafara fitowa a maimakon yayo cikin falon sai yayi waje wajensu Dr da fatima da suka fita rakiyarsu dady. An d’au tsawon mintuna uku kafin tafito lullub’e da mayafinta maigirma daya lullub’e mata ko Ina na jikinta kanta na sunkuye qasa. Tunda tafito take kallonta har tasamu waje ta zauna acan d’ayar kujerar dake sakad’e a lungu, bata iya d’agowa ta kallesa ba amma saita samu kanta da iya bud’e baki tagaishesa, tunda ya amsa bata sake tankasa ba yaci magana har yagaji, Duk wasu kalamai na ban haquri da nadama yayi mata, duk wani lallashin duniya da dad’ad’an maganganu da zasu sanyaya mata rai yayi Amma taqi tankasa. Cikin karyewa muryar dake nuna gab take da yayi mata kuka yace. “Me zan yimaki kiyafemun?, Mezan ce maki ki aminta dani, duka kalamaina babu qarya acikinsu, gaskiyace qwara d’aya nake fad’a maki habibty, bansan taya hakan tafaru dani ba, bansan meyasa qaddara tazab’amun hakan tsakanina dake ba, nayi rayuwata awaccan qasar ne tamkar wani bawan da bayada ‘yanci, namanta wayeni, namanta komai nawa, abu d’ayane nakasa mantawa shine ni ruhi d’ayane mallakin gangar jiki d’aya, hakan yasa narayu tamkar maraya Kuma nakasa banbancewa tsakanin haske da duhu akan rayuwar aure balle nayi tunanin samun wani sauyi akanki, ke kad’aice tal mace d’aya da nayi alwashin rayuwa da kuma mutuwa atare da ita, ke kad’aice mace tilo dake da iko akan sarrafa zuciyar malaminta, bazan hanaki kuka ba domin ni mai girman laifine awajenki, bazan hanaki d’aukar mataki ba domin nacancanci kihukuntani iya son ranki, sai dai kuma Ina tabbatar maki da cewa ayanzu lumfashina kad’an ne, haka kuma rayuwata taqitacciyace matuqar kikace zaki ida rayuwa bada niba..” Saida yagoge guntayen hawayen da suka zubo masa sannan yataso ya fad’i agabanta durqushe yanaci gaba da cewa. “Wannan dai malamin daya kasa kauda idanuwansa akan rayuwarki abaya, wannan malamin da yayi alqawarin miqa rayuwarsa agareki nahar abada, wannan malamin daya d’au alwashin zai iya bada rayuwarsa fansa ga malamarsa yana miqo qoqon baransa bisa laifin daya aikata daki yafe masa, gangar jiki da kuma rouhi suna matuqar kewarki, idanuwa na mararin kallonki nahar abada, kunnuwa nason jin sautin muryarki, haka zuciya na neman tallafin chaji daga wajenki, kalmarki d’aya ta isa tagusar da baqin duhun data kasance acikinsa na tsawon shekaru, adadin zantukan kalaman bakinki kuma sun isa su gusar da duk wata tsatsa a kwakwalwata data toshe mani tunanina na tsawon lokaci, kiji tausayina don ALLAH kiyimun uzuri, na amshi laifina hannu bibbiyu kiyafemun.” STORY CONTINUES BELOW  Duk da tanajin dirar kowace kalma azuciyarta kuma tana son mayar masa da amsarta kasawa tayi saboda kukan da yaci qarfinta tun tanayi a hankali har tasoma yi cikin sauti, runtse idanuwa yayi da sauri saboda jin zafi da rad’ad’in sautin kukanta da yakeji a zuciyarsa. Miqewa yayi cikin d’ari d’ari yana son ya rarrasheta amma yanajin wani irin kwarjininta da bazai iya hakan ba, sai ya miqa hannunsa ya tab’ata sai kuma ya kasa, ya sake miqawa sai yaji ya kasa, ita kuwa sai tsananta kukan takeyi yanda tasan zai iyaci gaba da hurting d’insa sosai. Kasancewar little dadu Dr zaunensu sukayi waje saman kujerun dake gefen rumfar motocin dake a’aje bayansu dady sun tafi yasa bakajin tashin motsin kowa cikin falon inba sheshshekar kukan Rashida ba, a hankali ya sake runtse idanuwansa ya zauna kusa da ita tare da jawota ajikinsa yafara lallashi yana fad’a mata kalaman ban haquri a kunnuwa duk da bayada tabbacin zata iya fahimtars, cikin wani irin yanayi daya tsinci kansa aciki bayan tsawon wasu shekaru yake rad’a matasu a kunne kamar hakan. ” _I am really very sorry to start with habibty, Since the time you refuse to talk with me, I’ m completely lost. I believe that things are not the same for me and for you. My intention was not bad, the timing was wrong. You know what I feel for you is really strong. I want to talk to you in a similar way as I did before. I want to play pranks with you as before. Please forgive me now and end this for all. Because this situation…!,” Sai kuma yayi shiru ya kasa qarasawa sai ‘yar sheshshekar kuka shima yaci gaba da sakar mata a kunne, wani iri yanayi taji tasoma shiga da zai iya skata manta abunda yafaru wanda bata buqatar hakan ayanzu, zumbur tamiqe adai dai lokacin da take fad’in. ” _I am really feeling so small for what I did, I ask for you forgiveness and hope you will do it now. Always Sorry from my side!_ Hannayenta tasa ta share fuskarta tana kallonsa cikin zafi da rad’ad’in qunar da zuciyarta keyi tunawa da kalaman da taji yayi ashekarun baya a cikin tv tace. ” _There is no place for forgiveness in this relationship, we’ve being separated for along time ago b’cos of so many embarrassed you couse to me and my son, always had issues but we held for too long, I do not have any more patience to be strong now, So i choose to breaking up with you peacefully, b’coz the love lost between us since!,_” Tana gama fad’ar hakan tabar wajen batare data bari sun sake had’a idanuwa ba. Kallo Dr yabita dashi bud’e da baki jin yanda take watso masa turanci tamkar ga bakinta aka halittosa, gaba d’aya ko kad’an kalamanta basu b’ata ransa ba, asalima farinciki yaji data bud’e baki tayi masa magana da harshen da baitab’a tsammani ba, wai matarsa Rashida, d’alibar nan tasa daya sani marar son karatu itace yau tsaye agabansa tana mayar masa da magana da kalaman dake nuna baqaramin gogewa tayi wajen karatuba kafin takai wannan matsayin da zata iya hakan, ji yayi kaso arba’in cikin damuwarsa ta ragu don ya tabbata da sannu zata haqura domin akwai banbanci tsakanin fushin mai cikakken ilimi da kuma marar ilimi matuqar zaiyi aiki dashi, murmushi yayi sannan yamiqe yafito ya samu har lokacin su Dr da little nanan waje zaunensu suna fira harda abbaty daya shigo lokacin. Gaishesa yayi yana kallon fuskarsa sannan ya kalli ta little yana so yagano ko akwai kamanceceniyar tsakaninsu amma hakan ta cutara don shi little sak kamar mahaifiyarsa ce garesa d’an duhun fatar kad’aine ta mahaifinsa, maganar da abbaty yaji Dr Nuraddeen mahaifin little nayi da mahaifinsa yana yimasa sallama zai wuce ita tasa ya amince tabbas mahaifin nasa ne don batada banbanci data little d’insu. Kasancewar yace nan zai kwana Amma hotel zaije ya kama kafin gobe yasa Dr da fatima suka roqesa daya kwana nan gidan amma fir yaqi amincewa, acewarsa zaifi wali acan fiye da nan don haka dole suka haqura, bayansa little yabi da zai tafi shima yace acan wajensa zai kwana abbaty nata yimasa dariya had’e da cewa. “Yazama mayen babansa.” Yace eh yadaiji, Duk abunda akeyi Rashida na jikin window tana hangosu, sosai take kallon habibyn nata da bata samu ta kallesa da kyauba d’azun wanda little kad’aine ya hangota. STORY CONTINUES BELOW  Ciro wayarsa yayi yana dariya yakirata da take tana hannunta ta d’aga batare data duba ba yace. “Gwaggo ya kikaga habibynki?, Ki koma kadasu mama Fatima su hangoki, don babu mai rabaki dasu yau, nidai wajen baban zan kwana…” “Marar kunyar yaro aje waya…”Tafad’a tare da jayewa tasaki labulen,+ Sosai little yasha mamaki da mahaifinsa ya fad’a masa yanda sukayi da mahaifiyarsa, murmushi yayi aransa yace lallai al_amarin Mata babba me, wato duk yanda suke son mutun sai sun ja masa aji idan yazo hannunsu, Ashe abun ma baga qanan mataba har da manya, azuci take maganar amma ashe bai sani ba tafito fili sai da yaji mahaifin nasa yajawosa ajiki had’e da laqqamosa tawuya yana dariya yace. “Commoon my son, to meye laifin hakan, ai momynka ko makaranta taja ba aji ba ta cancanci tayi hakan, ko ka zata irin wannan a tsakaninkune kad’ai banda iyaye?.” Cikin jin kunya little ya shiga susar kai yana jin wata irin qunar mahaifin nasa aransa. Kusan kwana Dr yayi yana kiranta taqi d’agawa, ya tura mata messages sunfi aqirga ba amsa, da safe ma sun koma shida little taqi saurarensa hakan yasa yakoma badon yanada ra’ayin hakan ba sai don ya fahimci tana buqatar lokaci kafin tahuce. Saida akayi kusan sati ana abu guda da rarrashi Rashida taqi saukowa amma azuciyarta tuni tahaqura kawai tanayin hakan ne don tarama itama shikuwa da yariga da yasan laifin nasane sai bai damuba yaci gaba da bibiyarta, A cikin satin ya sai wani qaton fili anan cikin bebeji aka aza masa gini part uku, kan kace me da yake ya riga daya tara kud’i nan take aka gama sashen d’aya tanadar masu shida Rashida da kuma mahaifiyarsa, shi kuma sauran akaci gaba da aiki ba dare ba rana wanda kusan little ne ke kula da komai. A sati na biyune baaffa ya shirya da kansa shida baffa Usman suka fara zuwa gidan baba balarabe da Yaya Maryam suka roqi alfarmar da aba Rashida haquri tadawo mijinta tunda har yanzu aurensu nanan, sai alokacin baba balarabe da Yaya maryam suka san da shegantakar da Rashida keyi Wanda hakan ya matuqar basu mamaki, bayan kwana biyu suka sake shiryawa awannan karon kam booking little yasa aka yomasa na jirgi tafiyarsu da dawowarsu baffa da baba nusaiba sai Yaya balkisu da baffa Usman Wanda ahankali tuni rayuwarsu har tafara canzawa suka tafi borno wajen yamasa bikon Rashida, su kam su Dr abunma har dariya ya soma basu, musamman umma da ita kanta Rashidar wai biko tsofai tsofai da ita, a lokacinne ma su baffa suka samu damar had’uwa da Rashida da mahaifiyarta suka yimasu gaisuwar baffa tare da Basu haquri sosai kamar zasu yimasu sujada, umma da kunyar baffa takamata harda hawaye tayi na tausayin ganin yanda yakoma itama tabashi haquri, Basu koma ba saida dady yabasu tabbacin cewa in Sha ALLAH cikin satin ranar juma’a Rashida zata koma kenan idan ancire yau saura kwana hud’u, sunji dad’i sosai had’e dayin godiya sannan suka juya suka koma cike da farinciki azukatansu, musamman baffa da yakejin ko yanzu ALLAH yakarb’i rayuwarsa burinsa yagama cika aduniya. Haba ana sanar da Dr Shire Shire suka koma sabbi yanda kukasan wanda za’a kaiwa sabiwar amarya, dama tuni ankammala duka ginin apart d’in uku har anyi fentin, part ne guda biyu plat sai d’ayan part d’in shi kuma hawa biyu wanda shine inda Dr Nuraddeen ya tanadarwa mahaifins, d’ayan plat part d’in kuma nashine, d’aya kuma na baffa Usman da baffa Ali, Amma duka an zagayesu waje d’aya anfitar masu da gate d’aya. Hakama akwai wani qaton fili daya saya acan g.r.a dake cikin kano yasa ayi masa tsarin ginin gida biyu kowane sama da qasa, shima duka aka zagayesa amma gate d’in kowane gida aciki daban, wanda yayisu ne shi d’aya little d’aya Amma ba’a qarasa ginin ba ana kan yine. Tuni dady yasa akazo aka zubawa Rashida kaya naji na fad’a a part d’insu ko ina Saida aka cike d’akunan tsaf da kaya masu kyau da tsada wanda tuni Dr Nuraddeen yayi niyar hakan Amma dady yace kawai yayi saving d’in kud’insa ga wasu matsalolin, Rashida kuwa abunma dariya yake Bata yanda taga anata Shire Shire sai kace za’ayi bukin amare ne, d’aukar abun takeyi tamkar wata almara don gaba d’aya ta kasa gasgata hakan wai itace yau zata koma gidan mijinta bayan wasu shekaru, wannan abu da ban mamaki tafad’a aranta duk da kuwa tuni suka daidaita da habibyn nata kullum suna maqale awaya kai ka rantse irin soyayyar nan ce ta samarin yanzu da ‘yanmata, bata gasgata ba sai ana gobe zata tare, ranar kam tayi kuka sosai, haka ummanta, ba’a maganar Fatima da gaba d’aya kusan zazab’i soma kamata yayi amma babu yanda suka iya tunda dolene, roqon Dr Rashida tayi daya taimaketa yabata zainab ‘yar autarsa lokacin tanada shekara goma sha 17, ko kad’an bazai iya hanata don haka yayi Mata alqawarin zai kaimata ita da kansa har gida idan lokacin yuyuwar hakan tayi Amma bada yanzu ba, Dole tahaqura tayita yimasu godiya tare da addu’ar ALLAH yabar zumunci tsakani. STORY CONTINUES BELOW  Ticket d’in Jirgi d’aya Dr Nuraddeen yayi ooking ga duk wanda ke sha’awar zuwa rakiyar Rashida tun daga zuwa har dawowa don akwai gagarumar walima ta musamman da gwamna yasa aka shirya masa ranar asabar saboda rashin samun halartar ta ranar daya dawo da beyi ba, wanda hakan yayi masa dad’i yaroqi amaida masa da ita ta ganaral da kowa zai iya halarta don tayasa murnar reunion d’insa da iyalinsa, Kuma agidan gwamnati za’ayi, Don haka gaba d’aya dady da familynsa kwai da kwarkwata manya suka hallara wajen rakiyar Rashida, Koda suka Isa sun tarar da kayan sawa tun daga sutura mayafai takalmi man shafa, turarukka da sarqoqi masu tsada Dr Nuraddeen ya cika Mata wardrobe dasu, duk inda ka duba da akwai abunda kejere agefen. Kowa sai murna da farinciki yakeyi tare da yimata barka da arziqi. Batool kuwa tanajin zancen batun dawowar Rashida tabuga tsalle bazata koma ba sai angama. Kasancewar su baffa baffa tuni suka tare tun kwana biyu da suka wuce yasa ba’a wani sha wahalar nemawa mutanen borno wajen kwana ba, wasu suka tsaya nan wasu kuma sukayi gidansu batool, Dady da Dr da sauran maza mazan da aka zo dasu kuma suka tafiyarsu yarimawa gidan baba balarabe, umma kuma tatafi wajen ‘yar uwarta aunty marwiyya, little ma tafiyarsa yayi wajen Batool d’insa don akwai d’aki na musamman da aka tanadar masu shida ita acan gidan don ya dad’e da zama d’an gida tuntuni. Rashida kuwa aka barta ita kad’ai a part d’inta Babu Wanda ya tsaya har zuwa dare da Dr yadawo. Saida yafara zuwa wajen mahaifiyarsa dake can pay din sama ita kad’ai sai wani d’aki dake gefe wanda anan ne aka saukar dasu zainab da hussaina da Fatima wato familyn Dr, qasa kuma nan baffa da baba nusaiba suke, gaishesu yayi tare da basu abunda ya siyo masu, Yaya hawwa ma ga baki yabata har taqoshi sannan yayi masu Saida safe yawuce part d’insa inda ya tarar da Rashida kitchen tana qoqarin dafa indomie don tasoma jin yunwa gashi dare yamiqa babusa ba labarinsa. Tsaye yayi bakin qofar yana binta da kallo kafin yace. “Ikon ALLAH, ni habibyn habibty yau wace irin amarya ce aka kawomun haka da zan tsinta a tsakiyar kicin.” Saida tayi dariya sannan yace. “Amaryar da angonta ya shekara ashirin da tara batare daya sanyata a idanuwansa ba har ta tsofe, don haka metake dashi da zata tanadar masa balle har yasa ran zai iskota ad’aki Kuma a tsakiyar gado lullub’e kamar sauran amaren?.” _Gaisuwa ta musamman agareki sister *SALIHA MUSA* alkhairin ALLAH yakaimaki aduk inda kike, Ina godiya da yanda kike bibiyar littafinnan hakan yasa naga dacewar nayi maki kyautar wannan page sukutum, ngd sosai Allah yabaki aljannah da rahamarsa_👏 *ALLAH KAJIK’AN IYAYENMU*👏😭 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️ 💎 _Bata hana zuwa…_💎 _WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎* _DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER’S (AMZAHFAZ)*💋 _BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA’EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞 *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖 *FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️ 🔚 *END*🔚 Page___106💎 Daga inda yake tsaye a bakin qofar kitchen d’in yayi folding hannayensa akan qirjinsa yake kallonta yana aika mata da wasu irin saqwanni dake fitowa tun daga qasan zuciyarsa har zuwa cikin qwayar idanuwansa da itama taqurawa idanuwa tan kallo had’e da jiran amsar da zata fitowa daga bakinsa, batare daya tanka taba akan abunda tafad’a yake qoqarin ganar da ita sirrin dake kwance cikin zuciyarsa akanta, ganin haka yasa ta d’auke idanuwanta tare da juyawa taci gaba da dafa indomienta zuciyarta na qoqarin hakaito mata tarin ma’anoni da kuma fassarar saqwanninsa data hango cikin qwayar idanuwansa, wani irin murmushi mai sauti taji ya kuccikke mata batare data ankara ba wanda hakan ya tabbatar mata da gamsuwar da zuciyarta tayi na karb’ar saqwanninsa hannu biyu biyu, daidai lokacin taji motsinshi a bayanta cikin wata irin dasashshiyar murya yana fad’in. STORY CONTINUES BELOW  ” _I am extremely sorry for what i did habibty! at the same time, i also want to say thank you for being my wife, because you always show me the right path and correct my mistakes, i know It’s hard sometimes to heal a broken soul but It’s best to forget the things of the past and look forward a new life awaits you, do not think about how you were last look habibty, forward a new days dt’s waiting for you, look forward beyond all the things, life is there so be certain pain will not remain in every time, So! Hope you w’ll forgive me with all your holy heart_” Yaqarasa maganar had’e dasa hannayensa ya juyo da ita suna fuskantar juna, riqo hannayenta yayi yana murza bayansu da manyan yatsun hannuwansa had’e da kallonta, murmushi tayi ta sunkuyar da kanta qasa cikin jin kunya, ita kam abubuwannan nasa da yakeyi gaba d’aya kunya suke sata, duk daya manyanta babu wani abu daya sauya daga cikin halayensa, d’abi’unsa da kuma tsarin rayuwarsa duk sunanan kmar yanda tasansu ada, dama malan bahaushe nacewa ‘hali baran azaliya kuma mai hali baya fasa halinsa’. Hura mata iska yayi a fuska ganin yanda ta antaya duniyar tunani tare da jayeta gefe yasa hannu ya d’auke indomien da take dafawa saboda qonewar da take nema tayi, zafin da yaji ga hannunsa yasashi saurin riqe hannun tare da yarfi dashi yana fad’in. “Wash..ashe da zafi d’alibata….” Kafin ya qarasa tayi saurin riqo hannun tana hura masa. “Meyasa kasa hannunka ka d’auke batare da kasa qyalle ba gashi kaje ka qona kanka, sannu ku.” Tafad’a tanaci gaba da hura wajen da iskan bakinta, tsura mata idanuwa yayi yana kallo har ta d’ago kai tana riqe da hannun tace. “Sannu” “Nagode” Hannu tasa ta kashe gas d’in tare da ciro d’aya daga cikin filetis d’in dake here wajen ta d’auraye ta juye indomien akai sannan ta juya riqe da ita zatabar kitchen d’in yayi saurin shan gabanta. “Haba ranki shi dad’e ya bakice komai ba zaki wuce kibarni a tsaye.?” “Au! Afuwan yunwa nakeji, bana kai irin wannan lokacin banyi taking dinner ba, am sorry.” Tana gama fad’a tafice, shi kuwa kamar sakarai ya sake duqawa ya d’auko ledojin daya shigo dasu tare da plate mai d’an girma da kofuka biyu ya iskota dasu akan dining area inda take zaune tanacin abincinta hankali kwance.” Tsuramata idanuwa yayi batare daya katseta ba har saida yaga tayi rabi sannan ya ture plate d’in agefenta ya aza mata wanda yazo dashi ya fiddo rousted fish d’in dake cikin d’ayar ledar da yazo da ita ya aza akai yasha source d’in tarugu sai soyayyen arish dake gefen kifin da yankakken cocumber da cabbage da kuma albasa. “Muci wannan ko habibty!” “Gaskiya naqoshi, kaci ni kabarni in qarasa indomie na.” Marairaice mata fuska yayi had’e da cewa. “Don ALLAH idan wani hukuncin ne ki sassautamun tunda naga har yanzu baki yafemun ba.” “Ko kad’an yallab’ai komai yawuce aguna, _dama ni since the day i married you, i knew i don’t deserve someone as great as you, and with the mistakes you have committed, I know you deserve someone better too, but with all the love in my heart that i have for you, i realized i have to accept every single of my destiny over you, wether i like or not, all I hv is to work things out, fill your life with magic again, strong our relationship till d world end up and in sha ALLAH I’ll live up to my vows, to the promises i made when i said ‘I do’,_ so ka kwantar da hankalinka komai yawuce da yardar ALLAH.” “Sure.” Yafad’a yana kallon cikin idanuwanta. “Yes malamina.” “Oya show me and hug me if it’s true madam!.” STORY CONTINUES BELOW  “Lalalalaaa…karufan asiri da hug d’in nan habiby we’re a matured anough fa yanzu.” “Ki kace?” “Eh man, ai gaskiya nafad’a.” “Shikenan nayarda, Amma ayi haquri aci abincinnan.” Yaqarasa maganar tare da d’ebo kifin yakai mata abaki, murmushi tayi tasa hannu ta karb’e sannan takai abakinta tanaci shi kuma ya jawo sauran indomien duk da tafara sanyi yanaci, ahankali takecin kifin tana kallonsa har ya cinye indomien tas sannan ta tura masa plate d’in kifin shima agabansa, sai daya ciro lamukkan dake cikin d’ayar ledar ya ajiye mata d’aya agabanta sannan shi kuma yaci gaba dacin sauran kifin. Bayan sun kammala ya taimaka mata suka kwashe kayan tare ta wankesu tas tare da tukunyar da tayi amfani ta tsanesu ta goge da qyalle ta mayar da kowane inda yake, lokacin shi kuma har yafito wanka don haka itama tana shiga tawuce toilet ta watso ruwa, dama tayi sallarta ta isha’i da shafa’i da wuturi don haka alwar bacci kawai tayo tafito ta zura doguwar rigarta ta bacci tanemi waje gefen gado ta kwanta. Tana jinsa yana jero addu’o’insa bayan yagama sallolinsa wud’anda rabinsu duk kusan akanta yakeyi da kuma mahifansa da yaronsa, bayan ya kammala ya kashe fitilar d’akin shima ya haye gadon yakwanta a rigingine yana kallon rufin d’akin duk da dai duhun daya mamaye d’akin bazai bari kafahimci me yakeyi ba yadai qurawa saman idanuwa. Yafi mintuna biyar ahaka kafin can ya saki wata irin ajiyar zuciya had’e da cewa. “Habibty ni kuwa abubuwa biyu sun d’aure mani kai acikin al’amurranki.” Da yake itama batayi baccin ba tajuya kwancinta kamar yanda yayi sannan tace, “kamar name kenan?” “Kiyi haquri da abunda zan fad’a, Amma nayi mamaki sosai da nasamu labarin cewa bakiyi wani auren ba duk tsawon wud’annan shekaru da suka shud’e, na biyu yanda naji cewa kintaka wani matsayi a karatu kuma kikayi zaune ba tare da kinfara aiki ba bayan kinada damar yin hakan.” “Ikon ALLAH, ai wannan ba abun mamaki bane saboda ni nasa kaina kuma ra’ayina ne amma dai akwai lokacin dasu umma da dady sukayi qoqarin ganin annemi su baffa saboda a warware auren tunda ba’asan lokacin dawowarka ba don kada abun ya zamo akwai cutarwa aciki da ganin gaba d’aya zaman nawama ba dacewa bane amma sai na nuna masu rashin amincewata, badon komai ba sai don alokacin ni gaba d’aya aure yafice mani arai, bana sha’awarsa ko kad’an saboda ganin irin tarin matsalolin dana fuskanta aciki, da yaudara ta da nake kallon kayi, hakan yasa umma tabi ra’ayina duk da kuwa bata so zaman nawaba amma damuwowin da taga sunyi mani yawa yasa bata matsa mani ba akan dole sai ankashe auren don tasan matuqar aka kasheshi dole sai wasu sunzo neman aurena, gashi nace banida buqatar hakan, wud’annan dalilan nawa su suka iya qarfafata tare da bani qwarin guiwar iya kaiwa wannan lokaci batare da nadamu dayin aure ba, auren yariga yaficemun arai banada sha’awarsa” “Tirqashi, Amma kinyi namijin qoqari gaskiya don awannan duniyar samun matan dake da irin wannan juriyar abune mai wahala, ubangiji ALLAH yabaki dukanin ladar da kika rayu aqarqashin inuwar aurena aduk tsawon wannan lokaci.” “Amin ya rabbi, ni nasama raina zan iya kuma nayi hakan, wanda yakamata mata da yawa da ALLAH yajarabta da rashin aure su fahimci cewa rashin yinsa is not d ended of their life, komai lokacine kuma duk nisan abu matuqar anasan ran isa garesa to tabbas za’a cimmasa, juriya, haquri da kuma qarfafa zuciya shi kawai ake buqata nan za’a tabbatar da cewa SANNU SANNU bazata hana tafiya ba, kamar yanda gashi yau ALLAH yanuna mani dawowarka duk da banyi tsammanin hakan ba kuma har mun sake komawa a inuwar da nayi tsammanin banida sauran sha’awa da ra’ayi akanta, to haka duk maccen da zataga ta dad’e agida ba aure kada tayi tsammanin lokaci bazai zoba da zatayisa matuqar ALLAH ya rubuto zatayisa d’in, to ba zato ba tsammani saidai kawai tawayi gari tana agidan mijinta, sai maganar aiki, su uncle dai sun sani karatu saboda sanin koda kana nan ALLAH bai haramta mani yinsa ba asalima haqiine akanka kabarni inje innemo ilimin, Amma shi aiki abune wanda bayada dole akanka, bazai halasta inyisa ba har saida amincewarka, shiyasa sukaga duk da baka nan babu halascin yinsa agareni tunda bamu rabuba har saida amincewarka, wannan shine dalilin.” STORY CONTINUES BELOW  Nan ma wata ajiyar zuciya ya sauke kafin yace. “A gaskiya bayin ALLAHn nan sunkai qololuwa wajen sanin haqqin d’an adam tare da kyautata zamantakewa, tun lokacin da nasamu labarin irin karamcin da sukayi mana nake tunanin mezanyi na saka masu amma nakasa, wlh inada matuqar kunyarsu akaina.” “Bazaka iya biyansu ba ko kad’an habiby, abu d’aya zakayi ka kwatanta biyansu shine kadinga skasu acikin dukkanin addu’o’inka da dukkanin sallolinka na farillah, hakan shi kad’aine zaisa karage nauyin kunyarsu dake kanmu.” “In Sha ALLAH zan kiyaye hakan har iya qarshen rayuwata.” Yaqare maganar tare da jawota ajiki yana fad’a mata kalamai masu sanyi da kuma kwantar da zuciya dake tabbatar mata da irin zunzurutun qaunar da yake yimata. ••• ••• ••• Da safe bayan sun gama karyawa suka shirya tare suka nufi part d’insu baffa, kai tsaye sama Dr Nuraddeen yanufa wajen mahaifinsa ita kuma ta tsaya nan qasa wajen baba nusaiba suna gaisawa, bayan sun gama gaisawa takira mata baffa da alokacin yafito wanka shima yagama shiryawa tsaf suka gaisa, wata irin kunyarsa ce tarufe Rashida don sai ayanzu take ganin rashin kyautawarta na waiwayarsa duk da irin tarin soyayya da qaunar daya nuna mata, daya fahimci hakan yayi murmushi tare da yimata nasiha akan ta manta da komai bawa bai Isa yakaucewa duk wani tsari da ALLAH yayi masa ba arayuwa, nan ya shiga qwalawa yaransa kira duk da kuwa kowace tagirma abunta don karatu sukeyi sosai batare da baffa yadamu da girmansu ko ganin cewa su yara bane, Rashida ma tuni ta kammala jami’a yanzu haka tana wajen sarvice, wanda sosai gwaggo Rashida taji dad’in takwarar da baffa yayi mata kuma taqara tabbatar da qaunarsa agareta, haka ma mai sunan mahaifinta auta bashar (Abba) da take kira da aminina da Rashida taganesa harda qwalla tayi jin sunan mahaifinta ya saka mashi, shima dai masha ALLAH ya girma don yanzu matakin farko take na junior secondary School, sun d’an jima ana fira kafin baba nusaiba tace tazo suje can sama wajen Yaya hawwa. Gabanta ne yafad’i tayi saurin yin ta’awizi had’e da bin bayanta har suka isa d’akin Dr Nuraddeen na zaune yana bata ruwa abaki yana yimata firar Rashida. “‘yar halak, kingata nan tashigo innarmu, nazata ma jira takeyi sai nakoma qasa nad’auko maki ita,” Yaqare maganar yana matsa yatsun qafar Rashida dake kusa dashi, ita dai ko kulashi batayi ba saboda yanda taga Yaya hawwa takoma, tsananin tsufan da tayi yasa ta tamuqe waje d’aya tamkar irin qananan yarannan, wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata tana Mai qara jin tsoron ALLAH yarufeta, tabbas mutum ba komai bane arayu kuma idan ka d’au duniya da zafi akwai ranar da zata qonaka da kanka, in Kuma kana kallon kanka wata tsiya da SANNU SANNU duniya zata nuna maka kai ba kowa bane. Gaisawar da taji baba nusaiba nayi da Dr Nuraddeen yasa tadawo hayyacinta daga tashin hankalin da tashiga, cikin tausayawa ta duqa kusa da Yaya hawwa tana gaisheta, juye juye yaya hawwa ta shigayi tanabin sautin Rashida ta yanda zata iya ganinta amma inaaaa, babu ganin idanuwan balle taganeta. Cikin kuka da muryar nadama tashiga roqon Rashida gafara tana mai nuna mata irin halin da tashiga duk saboda haqqinta data d’auka, don ALLAH tayafe mata. Cikin kuka Rashida tace. “Inna nayafe maki duniya da lahira, Ina roqon kema kiyafemun abubuwan dana aikata maki da sune suka jagoranci zuciyarki wajen aikata abunda yafaru.” “A’a ni bakimun komai ba, son zuciya kad’aine yasa nayi maki haka, gashi ALLAH ya nuna mani ikonsa aqoqarina naganin cewa sai kin rabu da d’ana ni anrabani dashi na tsawon shekaru, idan ma wani abunne kamar yanda baki moresa ba haka nima ALLAH yahanani moriyarsa alokacin da nake matuqar buqatarsa, shi ubangiji ba’ayi masa dubara kuma ba’a isa a Hana wanzuwar ikonsa ba a yanda yaso, gashi ALLAH yaqara had’aku a qarqashin inuwar da nayi qoqarin tunb’ukeki a qarqashinta, ni kuma an shafe mani idanuwan da zasu iya gano mani abunda yahaifar mani da shiga cikin wannan halin awancan lokacin.” STORY CONTINUES BELOW  Sun jima suna Abu d’aya har dai kowanensu ya yafi juna, Wanda sai alokacin taji mutuwar Inna ruqayya, tayi kuka sosai kuma tayafe mata tare da roqa mata gafarar ubangiji sannan suka baro wajenta. ‘Bangaren baffa Usman tanufa ita da yarinyar baba nusaiba shi kuma ya tsaya wajen baffa su gaisa, acan ta tarar da baffa Ali aka gaggaisa shima ta tausaya masa halin da taganesa aciki sosai ya kuma roqeta gafarar abunda yayi mata tare da roqawa matarsa kuma duk ta yafe masu tana kuka, ji take aranta da gaba d’aya Bata kyauta ba da tun farko batacewa ubangiji tayafesu ba har haqqinta da na sauran mutane ya illata rayukkansu haka, koba komai tasan matuqar tayafe nata zasu samu sassaucin hukuntawa ko kad’an ne. Tana zaune dasu Inna Bilkisu saiga muneera ta shigo, dashe baki tayi cikin farincikin ganin Rashida tana fad’in. “Ahhh, kaga uwargidan kuma amaryar Yaya nura ashe rai kanga rai?” Rashida na murmushi tace. “ALLAH yanufa hajia muneera kece haka.!” Muneera tawashe baki tare da Bata hannu suka tafe, saida suka gaisa sosai sannan Rashida tashiga yimata gaisuwar rashin mahaifiyarta Inna ruqayya itama tayi mata ta baba kowanens cike alhinin rashin mahaifan nasu, daga nan kuma fira ta canza tsakaninsu kai kace wasu aminan junane har muneera taqara roqon Rashida akan ta yafewa mahaifiyarta. Ana haka Dr Nuraddeen ya shigo, muneera na ganinsa ta d’auke kai cike da kunya, saida suka gama gaggaisawa dasu baffa da Inna Bilkisu sannan ya kaikaita idanuwansu had’e da juyowa yana kallon Rashida ya kashe mata ido d’aya tayi saurin kauda kai gefe, dariya yayi sannan yakalli muneera data sunkuye kai qasa yace. “Aunty muneera badai har kin shigo ba?, Ina kika baro mijin naki kika tahowarki.” “Yana wajen sauran matansa ya nura, yau nice aunty kuma?” Tafad’a tana dariya, “Eh mana, ai yanzu kin zama babbar aunty koba haka bane habibty.” Ita dai Rashida tsabar kunya miqewa tayi hade da yimasu sallama takoma part d’insu. Kasancewar qarfe goma za’a gabatar da walimar da gwamna ya shiryawa Dr Nuraddeen yasa koda qarfe tara da rabi tayi har ancika gidan da wud’anda zasuje, tuni Dr Nuraddeen yasa aka d’auko wacce zata gyara masa Rashidarsa tafito kalar matar manya Wanda nan take kan kace me har anyi angama don dama matar qwararrace sosai, kallo daya zakayiwa Rashida ka d’auka itace matar gwamnan jahar gaba d’aya saboda yanda tayi kyau, ga sarqoqi masu kyau da matuqar d’aukar hankali da suka hau jikinta daidai tafito masha ALLAH abunta. Qarfe goma da rabi aka fara gabatar da walimar wanda koda sha biyu da rabi tayi har angama, walima kam tayi kyau abun ba’a magana komai anyisa cikin tsari da tsaro saboda manya manyan mutanen da suka samu halartar wajen, An karrama little da kambu kala biyu na farkon daga fannin sashen lafiya ne, na biyu kuma daga wajen gwamna, sannan kuma aka qaddamar dashi a matsayin kwamishinan lafiya na jahar don sun tattauna da gwamnan tun kafin yau yanuna bayada buqatarci gaba da aikin likitanci Amma zai bada gudun mawa ga dukkanin asibitotan dake buqatar taimakonsa wannan dalilinne yasa gwamna ya nad’asa matsayin kwamishinan a fannin lafiya ta jahar, Rashida itace wanda tayiwa Dr Nuraddeen jawabin godiya bisa wannan karramawar daya samu, Wanda mutane da dama taburgesu yanda sukaji tana speach agaban mutane cikin girmamawa. Bayan an watsene Abba dasu uncle h suka sake bayyana agaban Dr Nuraddeen da matarsa Rashida suka tayasu murna, nan dai Abba ya sake daurewa suka roqi yafiyar juna da Rashida akan abunda yafaru abaya sannan suka wuce. Kusan ranar yini su Dr sukayi suna karb’ar baquncin mutane masu zuwa tayasu murna da kuma barka da arziqi wanda saida Dr Nuraddeen yayi daqyar yasamu yaja iyalinsa suka bawa junansu kulawar daya kamata. STORY CONTINUES BELOW  Da marece su Rashida na zaune dasu batool da yake itama agidan tawuni baffa yashigo shida baffa Usman bayan angaisa yaciro wasu kud’ad’e masu yawa a aljihunsa yamiqawa Rashida had’e da cewa. “Wud’annan kud’ad’en da kike gani haqqinki ne halak malak gasu nan dubu d’ari hud’une da tamanin, bayan b’atanki da rashin dawowar mijinki mukaga kayan d’akinki na Shirin lalacewa nida Usman muka yanke shawarar saidasu mu jujjuya maki kafin ALLAH ya bayyanaki, a lokacin mun saida komai akan dubu d’ari biyu da saba’in, da muka juyasu ne suka zamo haka, sannan acan wancan gidan dana taso akwai gonar kaji da nake kiwo Ina saida su to gaba d’aya naki ne, sai wani d’an qaramin fili shima ga takardunsa duka haqqinkine,” Yaqare maganar yana karb’ar takardun daga hannun baffa Usman yamiqa mata. Shiru Rashida tayi tana kallon baffa, gaba d’aya Bata sanma wane irin mutunne shi da ALLAH ya halitta mai tsananin qana’a da kuma taka tsantsan, little ma sakin baki yayi yana kallon baffa, don bai tab’a fad’a masa wannan sirrinba, asalima yanada yaqinin Babu Wanda yasan da wannan sirrin idan bashi da d’an uwansa ba. Tajima shiru kafin tahad’a kud’in da takardun ta sake mayarwa da baffa tace tabar masa su gaba d’aya duniya da lahira amma yabuga kai ga qasa yace bazai karb’a ba. Dr Nuraddeen kam burgesa mahaifinsa yayi ya d’aga hannuwa sama yana roqa masa amincin ALLAH duniya da lahira tare da tsawon rai, tanaji tana gani baffa yaqi amsar komai sukayi tafiyarsu, acewarsa don ALLAH yayi don haka yafison ALLAHn yabiyasa da kansa. Kiran umma tayi ta sanar da ita dasu baba balarabe, suma sun sha mamaki sosai don maganar gaskiya su har ga ALLAH sun ma manta da wasu zancen kayan d’akinta, kiransa sukayi suka roqesa akan yakarb’a tunda ita ta bashi Amma yace a’a yadai gode, ummace tayi saurin rantsewa akan to bazasu karb’i gonar kajin ba, don haka sun barmasa idan ma bayaso to shima yayi kyauta da ita. Badon yaso hakan ba yace shikenan ya amince kuma yagode. Godiyar da yazo yayiwa Rashida tasa Dr Nuraddeen da yaji yaquduri rushe wancan gidan na baffa ya zuba masa wasu kajin masu yawa kuma ya mayar masa dashi wajen kiwon kaji ya zuba masa wud’anda zasu dinga kula masa da wajen. ••• ••• ••• Da daddare su batool na zaune suna zancen ranar komawarta da little don ya dage akan dole gobe tabisu Dr da dady su koma saiga Abba ya shigo paloun don dama su kad’aine a zaune su hassana da hussaina suna can wajen gwaggo Rashida da sukaje zasu dawowa suka tsira rigima sai an barosu wajenta Dr Nuraddeen yace su qyalesu, dole suka haqura suka barosu, Suna ganin Abba yashigo suka saki firar suka shiga d’auko wani sabon babi ana tayi haddashi yana dariya, SANNU SANNU falon yafara cika har dasu uncle da shurahbil da sauran matan gidan, Cike da tsokana uncle Hussain ya shiga Basu labarin mafarkin Abba yana dariya tuno yanda ya rud’e ranar har yana cewa batool “ya kamata tad’an sakarwa sauran ‘yan uwanta space a zuciyar abbanta don soyayyar da take yimata tayi yawa.” Sai alokacin tafahimci dalilinsa na ranar daya dinga cewa kada tazo ita kuma ta nace badon tasan da abunda ke faruwa ba, Wanda badon girman addu’ar iyayen nata ba data tabbata babu abunda zai hana mafarkinsa ya tabbata ko don bijirewar data yimasa da yace kada tazo, tabbas tayi kuskure Amma daga yau bazata koma bijirewa iyayenta ba da yardar ALLAH. Ganin yanda tad’an canza yasa Abba yayi murmushi had’e da cewa. “Ki kwantar da hankalinki dota, komai yariga daya wuce babu abunda zai faru in sha ALLAH, ni abunda ma yafi bani mamaki a mafarkin, shine wasu mutanen dana gani wanda bangansu yanzu atare daku ba cikin family d’in nasa.” Dariya su uncle h sukayi harda hajia mama tace. “Ikon ALLAH, to alhaji ai ba lallai bane ace duk abunda kagani a mafarki dole ka ganshi azahiri ba, tunda gashi kaga batool ta haukace gata da hankalinta, little ya rasu gashi kuma raye don haka badole sai kaga komai ya bayyana ba.” STORY CONTINUES BELOW  “A’a hajia mama, da gaskiyar Abbana, amma dole yayi mamaki, Abbana zainab d’in daka gani a mafarkinka autace, d’iyarsu Dr da mama Fatima tazo maka a matsayin qanwarsa, qila antabayin zancenta agabanka, shi kuma wannan abokin nasa inaga dai Dr ne har yau zancen shi barrister ne shi kuma matsayin gwaggone mafarkinka ya qwace yabawa abokinsa na mafarki daka gani” Aikuwa batool narufe baki da wannan dogon bayani nata duk aka kwashe da dariya a falon kowa na ganin wautarta ciki harda little da har yasoma hawaye, kaikaita idanuwan iyayenta tayi takai masa mintsili a gefen ciki tare da watsa masa harara, hajia mama tace, “Ahaf! In dai shirmen batool ne ai tafiye nan, bari ni naje na kwanta don bazan iya dashi ba” Bayan kwana biyu Abba yafara fita office said gashi ranar ya dawowa Rashida da takardar shedar samun aiki a federal high court dake nan cikin kano, ta matuqar mamakin yanda yayi neman mata aikin har ya gama batare daya sanar da ita ba, don ko takardunta batasan lokacin daya d’auka ba, shiru tayi tana tunanin ta ina ma zata fara yimasa godiya don har ga ALLAH tana sha’awaryin aikin kuma taji dad’in wannan kyautatawar da yayi mata sosai, Bata tab’a kawowa ranta cewa zai amince tayi aikin ba don gwargwado ALLAH yarufa masu asirin da koda da ita har shi basu nemi aiki ba zai ishesu arayuwa don babu abunda suka nema aduniya suka rasa sai gashi cikin ruwan sanyi da yake babba yake cikin gwamnatin kuma takardunta sunyi kyau sosai yasama mata aiki, kamar yasan abunda take tunani aranta yace. “Kidena matsawa kanki da tunanin mme zakiyi mani akan haka ko a ina nasamu takardunki ko kuma yanda na amince dayin aikinki duk da bamu rasa komai ba domin kin cancanci inyi maki fiye da hakan, sannan zuciyarki da tawa abu d’ayane duk abunda kike so nasani kinga kuwa dole nayi makishi matuqar zai sakaki farinciki, fatana kawai kici gaba dayi mani soyayya mai yawa tare da kula dani yanda yakamata.” Murmushi tayi sannan ta kallesa had’e da cewa. “Shi kad’ai kake buqata…?” Kafin tarufe baki yayi saurin bud’e hannayensa had’e da cewa. “Tare da wannan.” Cike da dattijantaka irin tamanta tayi murmushi sannan tashige tsakiyar hannayen nasa d’aya bud’e ya mayar ya rufe yana mai d’ora kansa saman kafad’arta, tace “Hmm! Gaba d’aya kai baka tsufar da wannan soyayyar taka habiby.” “Habibty kenan, ai soyayya bata tsufa matuqar nagartacciyar ce, mutanen da keyinta kad’ai ke tsufa ni kuma awajena tsufa baya hana soyayya. Yaqarasa maganar had’e da kissing d’inta saman kai. ” _Thank you habibty, thank you so much for your kind gesture it really made my day more special, you took time and did something magical i won’t ever forget this all my life, thanks! a word is straightly from my heart for being so considerate and kind thanks a lot! and really luv you so much._” Ta fad’a tare da qara shigewa jikinsa. Hannu yasa cikin aljihu ya ciro makullin sabuwar motar daya siyo mata don fita aiki sannan yacirota daga jikinsa ya riqo hannunta ya aza mata akai, ware idanuwa tayi zatayi magana ya aza yatsansa abakinta had’e da cewa. “Me zai hana kici gaba da qara yimun addu’a a maimakon wannan godiyar, wannan makullin motar kice anjima sai muje ki d’auko.” Yaqarasa maganar had’e da kashe mata ido d’aya yayi kissing forehead d’inta yana murmushi sannan yabar wajen. Wannan karon Rashida kam harda hawayen farinciki tayi, tare da d’aga hannye sama tayi masa addu’a Mai tsawo sannan tabi bayansa. Cikin sati d’aya Dr Nuraddeen yaje da Rashida sukayi duk abunda ya kamata wajen aikin nata sannan tasoma zuwa. STORY CONTINUES BELOW  Umma tayi farinciki sosai da tasamu labari Kuma taroqi ALLAH daya tsare mata ‘yarta sannan ya sanya alkhairi mai yawa acikin aikin nata, taso ace mahaifin Rashida naraye taga irin farincikin da zaiyi na cikar burinsa daya tabbata ga ‘yarsa amma inaaa, mai rabawa tariga taraba saidai fatan ALLAH yajiqansa mukuma yasa mucika da imani. *BAYAN SATI BIYU* Bayan sati biyu da komawarsu batool borno ALLAH ya sauketa lafiya anyi mata tiyata aka fiddo mata da kyawawan yaranta gaba d’aya maza sak ita, inda murna ba’a magana awajensu Rashida da Dr Nuraddeen tamkar su tashi sama tsabar farinciki don har sunfi iyayen jariran murna, wanda kasancewar kwananta uku aka sallameta saboda tiyatar tayanzu anci gaba sosai sati na zagayowa aka rad’awa yaran suna, Hassan yaci sunan baffa Usman wato (Usman), shi kuma Hussain yaci sunan Abba mahaifin batool wato (umar faruq), batool taso abarsu da sunayensu amma little yace a’a haka yakeso adinga kiransu, tabari idan tahaifi wasu ‘yan biyu maza sai abarsu Hassan da Hussain, Babu yanda ta iya dole tabi ra’ayinsa tare da fatar ALLAH yaraya matasu rayuwar musulunci, Amma azuciyarta taraya cewa itakam da haihuwa ba yanzu ba balle yace idan ta sake haihuwa kuma waima wasu ‘yan biyun sai kace akuya, Sosai Abba yaji dad’in samun takwara haka ma baffa yaji dad’in takwaran da aka yiwa d’an uwansa tare da saka masu albarka. Baba balarabe ma yamiqa dukkannin haqqin Rashida na gado da umma agaresu tare da dabbobin dake hannunsa daya jujjuaya masu da wasu kud’ad’e da ake karb’a na haya, wanda nan yayi masu bayanin cewa daga baya da yaga gidan na shirin mutuwa ne ya yanke shawarar zuba ‘yan haya aciki tunda yayiwa umma magana tuntuni akan gadon tace duk yanda yayi daidaine tunda gwargwado suna cikin wadata ita da Rashida yayi amfani dashi har lokacin da buqatar karb’arsa zai taso, duk da haka saida yasa aka raba aka cire masu haqqinsu shine yasayi dabbobi yana yimasu kiwonsu, acikin kud’in hayar da ake bashine yake cida dabbobin da sauran abubuwa, yanzu kuma yamiqa komai ne agaresu saboda ganin yayi rauni ta ALLAH zata iya kasancewa kansa akoda yaushe shiyasa ya hannunta masu abinsu, sukayita yimasa godiya sosai bayan sunyi masa alkhairi. Rashida kam kud’ad’enta da baba balarabe ya bata da wudanda baffa yakawo mata acan qauyensu tahad’asu tabayar tace agina masallaci sadaqatul jariya zuwa ga mahaifinta, da Basu isa ba Dr Nuraddeen ya qara mata wasu aka Ida kammala ginin. Yaya hawwa kuwa cikin taimakon ALLAH da Nuraddeen ya kaita asibiti aka aunata akace bawani magani da za’a yimata idanuwanta ba zasu iya warkewa ba balle ganinta yadawo Rashida ta nace da daddare wajen yimata addua’a tana tofa mata ga ruwa ita da baffa Ali tana basu susha kuma su shafe jiki ita kuma idanuwa tun da safe kafin suci komai sai gashi duk sun warke gaba d’aya bisa yardar ALLAH, qurajen baffa sun b’ace kamar bai tab’a yi ba, ita kuma yaya hawwa ganinta yadawo tas. _(‘yar uwa kinada buqata ko wani abu dake damunki?, to kijure kuma kijajirce dayin wannan addu’ar👇, wlh tallahi matuqar baki gajiyaba dayi kuma kikasa yaqini akan ubangijinki to zakiga biyan buqata da waraka da yardar ALLAH, itace Rashida tayi har baffa Ali da Yaya hawwa suka samu waraka ga cutukkan da ake tsammanin sai mutuwa tsakaninsu dasu)_ A kullum takan tashi da daddare misalin qarfe uku tayi arwala saita sallaci raka’a biyu ta nafila tare da ‘yan ruwa agefenta kamanin rabin kofi. _*A raka’a ta farko tana karanta suratul ikhlas, wato qul’a’uzu birabbin nas qafa goma(10) saita tofa acikin ruwan sai tayi ruku’i, idan ta d’ago daga ruku’i saita karanta wata (suratul ikhlas) qafa ashirin(20) ta tofa cikin ruwan sannan taje sujada ta farko idan ta d’ago saita karanta suratul ikhlas d’in qafa uku(3) ta tofa saita koma sujada ta biyu, idan ta d’ago ta sake karanta qafa uku(3) ta tofa duka acikin ruwan sannan saita miqe zuwa raka’a ta biyu ta sake karanto suratul ikhlas qafa goma(10) saita tofa taje ruku’i, idan ta d’ago sai ta karanta qafa ashirin(20) ta tofa sannan taje sujada, idanta d’ago saita karanta qafa uku(3) ta tofa sannan ta sake komawa sujada, to anan idan ta d’ago bazata karanta suratul ikhlas d’in ba sai tayi tahiya tagama kafin ta sallame saita karanta qafa uku(3) ta tofa sannan tayi sallama, tana sallamewa bayan tayi istigfari saita karanta ayatul kursiyu qafa d’aya(1) ta tofa duka acikin ruwan sannan tayi salatin annabi sau d’ari(100) ta tofa aciki, idan ita keda matsala bayan tagama addu’o’inta saita rufe ruwan ta ajiye, tun da sassafe kafin taci komai saita sha ta kuma shafa a inda matsalar take idan kuma ba ciwo bane to saita shanye ruwan kawai basai ta shafa ba musamman in nacan cikin jikine daba bayyananne ba, idanma tana tsoron kada shed’an ya mantar da ita da safe zata iya tana gama sallar da daddare bayan tayi addu’o’in ta saita shanye, in kuma wani akayiwa to sai arufe ruwan a ajiye kuma ayi qoqarin bashisu yasha kafin yaci komai da safe, in Sha ALLAH ko menene damuwa ko tsananin ciwo in aka nace dayin wannan sallar to tabbas za’a samu waraka da izinin ALLAH, ammafa sai an jajirce don la’anatullahi yakan bijiro da kasala sai anyi da gaske*_ (wannan addu’a sadaka ce zuwa ga mahaifina Ina bara duk wacce ALLAH yabawa ikonyi data sakashi cikin addu’o’in ta ALLAH yajiqanshi kuma yayi masa rahama da shi da dukkanin musulmi baki d’aya, ALLAH kasa adace👏) STORY CONTINUES BELOW  Hakan Rashida tayi tayi har ALLAH yasa aka cimma ijaba Yaya hawwa da baffa Ali suka warke, alokacin sun sake yin kuka sosai tare da nadamar abunda suka aikata mata gashi batare da tayi la’akari da wannan ba tayi amfani da qarfinta da ilimin da ALLAH yabata tahana kanta bacci taroqa masu samun waraka da kuma magani ga ALLAH don su samu lafiya, haka ake son zuciyar musulmi ta kasance akoda yau she mai tsananin yafiya da kuma rama alkhairi ga junansu, Haka rayuwar ahalin ta kasance cikin farinciki da kuma zaman lafiya da girmama juna, tuni anka gudanar da auren Yusuf da Rashida ‘yar baffa, manyan ‘yan boko don gaba d’ayansu sunyi karatu Mai zurfi Wanda baffa ke alfahari da hakan, acan asalin family house inda su baffa Usman sukayi zama Yusuf ya saye duka shiyoyin guda uku ya rushe ya qera gidansa mai kyau irin nasu na ‘yan boko wayayyi haka ma Dr Nuraddeen da kansa yasama masu aiki tunda gwamnatin jahar dashi take damawa tare da shahida da itama tuni takammalo karatun daga qasar waje suka daidaita da Uncle Hussain d’an baba balarabe aka d’aura masu aure, yanzu haka suna nan zaunensu kano wajen aikinsu guda da ita da Rashida matar yusuf, little kuwa yana can borno abunsa yayi zamanninsa acan saidai idan sunyi sha’awar zuwa nan kano suzo suyi satukka ko wata d’aya su koma musamman idan yara na hutu, Zainab ma autarsu Dr nura tana hannunsu Rashida kamar yanda Dr ya alqawarta komai nata gaba d’aya yadawo wajensu, tana samun kulawa sosai fiye da tsammani don ba kad’an suke jin taba har cikin qoqon ransu wanda tuni itama suka daidaita da shurahbil d’an wajen uncle Hussain baffan batool, amma saita qare karatu tukuna za’ayi auren, zainaba ma ‘yar baffa ta biyu itama tayi aure amma acan cikin kano take zaune da mijinta bayan ta kammala karatunta itama, asiya da Bilkisu kad’aine suka rage wud’anda suma gaba d’aya sun koma hannun Rashida tare da zainab sukeyin komai hatta karatu waje d’aya sukeyi, Babu wani banbanci tsakaninsu ko fifiko don su Dr Nuraddeen sun nuna masu abu d’aya suke awajensu saboda haka suso juna, haka ma auta basha (Abba) son da Rashida keyi masa yasa da wayo da wayo ta raboshi hannunsu baffa yadawo wajensu, Su baffa suka koma daga shi sai baba nusaiba babu yaro ko d’aya agabansu, ga masu aiki Nuraddeen ya zuba masu, banda suci su kwanta babu abunda sukeyi, nan take tufan da yakawowa baffa hari har yana neman durqusar dashi ya gudu gaba d’aya ya murmure yayi haske sosai tamkar ba shi ba, Yaya hawwa ma ba laifi saboda Rashida nakula da ita sosai kuma tana cikin qoshin lafiya daidai gwargwado, tafiya kad’aice har yau bata iyayi wataqil hakan nada nasaba da irin wahalhalun data fuskanta alokacin da tana gidan mahaukata, Kuma hakan be dameta ba, kullum cikin zikiri take da tilawa alqur’ani, tana neman gamawa da duniya lafiya, wani lokacin ma Rashida ke koya mata karatun tayita samata albarka. Baffa Usman ma Alhamdulillah yanzu haka sai qara habbaka yakeyi a fannin kasuwancinsa saboda gudun mawar da Dr Nuraddeen yabashi, arziqinsa sai dad’a bud’uwa yakeyi idan kaganesa zaka d’auaka wani hamshaqin d’an kasuwa ne, dama ashe talauci ne ya b’oye masa cikakkiyar sigar da ALLAH yayi masa, yanzu kuma da wadata ta sauka sai ya canza gaba d’aya tamkar ba shiba, haka Inna Bilkisu abun kam masha ALLAH sai sambarka, ga arziqin miji ga na ‘ya ‘yanta mata da akoda yaushe cikin aiko mata da saqwanni mazansu suke suna yimata godiyar tarbiyar data bawa ‘ya’yanta, Babu mai matsala ko wata damuwa acikinsu don bayan kulawar da suke samu ga mazajensu gaba d’aya Dr Nuraddeen ya sama masu sana’o’in da sukeyi su day muneera kuma ba laifi kowace tana samu daidai gwargwado. Tuni gidan gonar baffa da Dr Nuraddeen ya sake zuba wasu kaji aka rushe gidan aka mayar dashi wajen kula da kajin kad’ai sai kifaye da aka zuba suma ana kiwo shima ya bunqasa don har cdaga cikin gari motoci ke zuwa suna saye da kuma kamfanonan dake sana’arsu, ko yaushe saidai a qirgikke kud’i akawowa baffa ya soka aljihu yana gida zaune abunsa, (kaga haihuwa mai rana, ubangiji ALLAH kabamu masu albarka.) Baffa Ali ma little yasa anyo masa qafar roba yanda zaijin dad’in walwala da mu’amalar yau da kullum cikin mutane, hakan kuwa yayima kowa dad’i don babu Wanda wannan tunanin ya zoma arai, da haka su baffa sukayi qoqarin nema masa auren wata bazawara anan cikin qauyen kuma aka dace cikin sa’a ta amince ba tare data damu da yanayin saba musamman data san wajene inda zataje tahuta, qaton shago su baffa suka bud’a masa Dr Nuraddeen yazuba masa kayan drink masu sanyi da katam katam yana saidawa wanda nan take shima ALLAH ya bud’e masa hanyar samu don yana samun cinaki sosai, kan kace me wannan ahali sun had’e waje d’aya sun bunqasa qauyen na bebeji yayi suna sosai saboda yanayin mutanen zagayensu dake shiga harkokin kasu wanci na yau da kullum, musamman a fannin sana’o’in qwai kaji da lemuka, ga Kuma gone ginen zamani da sukayi ya haska cikin garin, don masallaci da makarantun da yaransu zasu nemi ilimi na boko da islamiya duka Dr yasa angina da taimakon gwamnatin jahar, asibitin dake cikin qauyen ma Dr yasa angyarata an sake fad’ad’ata da fitar da wasu fannona na marasa lafiya da basuda da kayan aikin da ba sai sun fita cikin gari ba wajen wasu gwaje gwaje, sun matuqar samun cigaba fiye da tunani don harda wata psychiatric clinic Dr yabud’e da kansa yana kula da masu lalurar qwaqwalwa dake da qaramin qarfi na qauyen da zagaye, tare da wayar masu kai akan abubun da suke jagorantar afkuwar wannan cutar, STORY CONTINUES BELOW  A b’angaren su baba balarabe ma dasu Yaya maryam da aunty marwiyya Rashida na taimaka masu sosai da taimakon mijin nata. Little ma tuni yakoma qaro karatu lokacin battol tasake haihuwa ta uku tasamu ‘yarta mace sak sumynsu tafarko data rasu aka sake mayar mata da sunanta alokaci d’aya kuma yana qara hab’b’aka sana’ar gadajensa da katifu da sauran d’aki da dady ya d’orasa akai, don har waje yake zuwa sawo kayan d’akin shida abbaty da lokacin shima yayi aure da ‘yarsa d’aya mai sunan mahaifiyarsa wato fatima ana kiranta (miemah). Batool kuwa Babu yanda Dr da little basuyi da ita ba akan takoma karatu amma takafe akan bata buqata tafiso ta zauna gidan mijinta ta kula dashi da kuma ‘ya’yanta Wanda hakan yasa Rashida tace lallae dole little yabud’e mata shagon boutique tadinga saida kayayyaki, shikuwa Dr yace Dole tahad’a da karatun kota online ne in yaso lokacin exam kawai zataje tayi tunda akwai branch d’in a a.b.u zari da sokoto duka zata iya karatu ta online batare da take ba, Dole ta amince badon tana soba sai don tayi biyayya tunda gata ce sukayi mata. Itama umma da ‘ya d’aya da ALLAH yabata tana nan tanacin ribar haihuwa don Babu abunda tanema tarasa aduniya, suci mai kyau susha mai kyau ita da mijinta dady d’an tsofo mai ran qarfe, Dr Nuraddeen ma musamman yayi gida acan lokaci lokaci su kanje can suyo kwanaki su koma, gaba d’aya mabanbanta wud’an nan ahali angame waje d’aya ba qyashi ba hasada anzama tsintsiya mad’aurinki d’aya, suna matuqar son juna tare taimakekeniyar junansu tamkar wata hatsaniya ko rigima da tsana bata tab’a shiga tsakankaninsu ba, dama ance SANNU SANNU bata hana zuwa saidai adad’e ba’a jeba, duk yanda b’acin rai yayi tsanani rabuwa takai rabuwa a zamantakewa da kuma duk girman qaddara to idan akasa haquri da SANNU SANNU za’aga zaman yayi dad’i tamkar ba’a tab’a sab’ani ba, qaddara kuma ancinyeta tamkar bata wanzu ba, ubangiji ALLAH kasanya mu cikin bayinsa masu haquri da kuma iya jurewa qaddarorin rayuwarmu. _TAMMAT BIHAMDULILLAH_ _Ina miqo godiyata ga dukkanin masoyana da suka jajirce wajen bibiyar littafinnan, Ina jinjina maku tare da alfahari daku ALLAH ya iya maku acikin dukkanin al’amurranku da dukkanin iyawarsa👏ngd ngd ngd sosai_

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *