ZUMA CHAPTER 11 BY SHATUUU

ZUMA CHAPTER 11 BY SHATUUU

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Bayan watanni hudu nayi nisa cikin service dina, duk yadda nake tunanin idan naje niger zan hadu da ko mutum daya wanda yasan mummy ban samu ba, babu wanda ya kara ce mini ina kama da wadda na sani, bayan na gama camping dina akai deploying dina zuwa jigawa anan general hospital na dutse akai posting dina. Permanent morning aka saka ni Monday to friday, kullum se mun hadu da Amina dake itama permanent morning take a Paediatric, duk wanda aiki ya sararawa zai tafi gurin dan uwan shi. A wannan kwanakin ko nace watanni na fahimci abubuwa da dama gaba daya na hakura da Aliyu na cire shi cikin zuciyata amma duk yadda nake kokarin saka Nasir a gurin abin ya faskara. Ranar wata Wednesday bayan mun tashi na fito na wuce ward din su Amina, ina zuwa na samu ta tashi se kawai na kirata a waya tace min tana male ward wajen Salem. Wucewa nayi male ward din bayan mun gaisa da attendant din sannan da staff din su na kwankwasa changing room din su dan na tabbatar suna ciki ita dashi, shi ya bude min yana murmushi yace+

“Babbar yaya! Ya dai na ganki duk kin gaji”

Hararshi nayi nace

“Kun tula mana aiki dole kace na gaji”

Se yayi dariya ya fito ni kuma na shiga na sameta a kwance kan gado tana mana dariya, zama nayi gefen ta nace

“Yau ba da wuri zaku tafi ba ne?”

Dan tsaki tayi tace

“Shi nake jira kuma wai se sunyi meeting”

Kaina na gyada daidai shigowar Lubna sanye da lab coat, ta fara IT dinta so tana lab cikin asibitin dake tana karantar MLS. Tare muka dinga hira har Salem ya gama da yan ward dinsa sannan muka fito muka tafi gida. Da yamma ina zaune sega kiran Aminatu wai zamuyi magana, nace

“Ke! Me ya hanaki fada min dazun?”

“Bana son muyi maganar muna kallon juna saboda kar kiji kunya ta.”

“Kunya kuma?”

Na fada ina dariya, itama ta danyi dariya sannan tace

“Kinaji uncle Nasir ya kirani…”

Seda gabana ya fadi na fara addua Allah yasa ba cewa zaiyi zai turo maganar bikin ba, saboda nidai har zuciyata ba son shi nake ba what i know ina ganin mutuncin shi da girman shi ne kawai!

“…shi yana ganin kamar bakya son shi kawai kina masa kara ne, yana ganin wai zai hakura kawai, nima kuma na lura da hakan yaya Nanah rayuwar ki ce fa, idan baki son shi kada ki karan ta min, ke zaki zauna dashi aure is too long for you ki zauna da abinda baki so, ba zaki iya kara for long ba”

Naji babu dadi da suka fahimci hakan amma abu ne mai dadi da hakan ta faru, in protesting nace

“Waye ya fada miki?”

Se tayi dariya kawai ta cigaba da maganar ta nima se na hakura kawai na amince cewar zargin su daidai ne. Daga wannan na closing chapter Nasir dukda muna waya sosae kuma yanzun da na san babu komai tsakanin mu se ya zamana nafi sakin jikina dashi.

Bayan yan satittika mu kaga tallar wasu abayas a gurin wata online vendor, Daddy na zaune Nawwara ta nuna mana dukkan mu seda mukai exclaiming saboda kyan abayar , Daddy yace

“Ku tambaya kudin se kowa ya dauka”

Lubna tace

“Yes! That’s lovely Daddy for us”

Yaji dadi mukai masa godiya, there and then mukai placing order kowa da color din shi da size, dama A’isha da Ummu sune kanana amma sun fimu tsayi da cika ido, 3 quarter kudin muka bayar akan zamu cika sauran bayan order yazo. Order ya dauka two weeks kafin yazo, sukai communicating da Nawwara ta fada mata ta aiko kayan dutse through Anty dinta, sannan ta tura mana number Anty din tata sede tace mana bata nan se idan ta dawo.

STORY CONTINUES BELOW

Kullum muka kira se ta bamu excuse one or two, ranar dai ta bamu address tace muje mu karba kawai amma bata gida taje biki amma zata bari a gida. Ranar Thursday ce so dukka munje gurin aiki , tunda nayi parking nasan motar bata da lafiya amma haka ban kira Daddy ba duka muka rabu, kafin naje pharmacy seda na fara wucewa ward din su Amina, ta karaso cikin blue uniform tayi kyau cikin dake jikinta ya fara bayyana, ta rungume ni tana fadin

“Fitowar da nayi gurin ki zanje fa”

Nace

“Sakon na kawo miki”

Na fada ina mika mata ledar hannuna, karba tayi da sauri ta ciro wrapped shawarma cikin wata leda se zobo daya ledar wanda ya kankare, rungume ni tayi for the second time tace

“Allah ya kawo miji na gari, ranar se an rike min zani na”

Nayi dariya na wuce department din mu, da muka tashi na lallaba motar muka je gida, wanka na fara yi sannan na canja kaya zuwa wata creme abaya da adon net red, na saka red turban cap sannan na fito mukai lunch, rufe idanuna nayi ina shakar sassanyar iskar dake kadawa daga fanka, Ummu ta shigo da assignment dinta na physics ta kawo min haka na zauna na koya mata wanda zan iya sauran na mata browsing a net tayi. Nawwara ta shigo parlon tsaf cikin gown na material tace min

“Yaya Nanah kin manta zamu fita”

Mikewa nayi dan da gaske na manta da karbo kayan, mikewa nayi naje daki na dakko karamin veil din abayar sannan nasa jan wedged sandal me kyau a gaban anyi ado da creme ribbon a jiki. Fitowa nayi bayan nasa kwalli sannan nayi damping lip balm akan lebbena masu siranta, idanuna na lumshe na kuma bude ina kallon kaina jikin babban mirror dake jikin bangon dakina, na rame har yanzun ban koma yadda nake ba, ban kuma san se yaushe zan karasa murmurewa ba, amma yar ramar da nayi se naga na kara kyau, wannan idanun nawa masu girma da haske wanda kusan su ke kara min kyau a duk lokacin da wani ya kalleni, kwalla min kiran da Lubna tayi yasa na tsayar da admiring kaina na fita, dukkan su seda suka yaba kyaun da nayi, Amal na cewa

“Wannan fitar kawai jikina na bani zaki dawo mana da in law!”

Na tada mota ina murmushi gaba daya na manta cewar motar bata da lafiya, kuma ko a zuwa bata bamu matsala ba, Nawwara na fada min kwatancen a haka muka isa wani mansion dake nan bayan government house. A kofar nayi parking muka fito na locking sannan nace

“Are we good!”

Ta gyada kai tana fadin

“Gidannan yayi kyau!”

Nace sosae muka knocking, security yace mana mu shiga cikin parlon hajiyar, a parking space motocci ne biyu anyi parking, se flowers masu kyau da aka shhushuka wasu na cikin pot, wasu a pit suke, wasu cikin pot din anyi hanging suna dangling, ba karamin burgeni gidan yayi ba, idanuna na lumshe na bude anan na hango wani daga can gefe mutum ya juya bayan shi zaune akan milk din kujera me purple din flowers, tsayawa mukai jikin giant wooden door din dake kofar parlon tareda bugawa cikin sanyi, for some unknown reason se na kurawa idanun shi, and i found myself having some unnecessary force yana jana zuwa gareshi, wannan knocking da muke yasa ya dan juyo kadan nima daidai lokacin na juya ina kallon shi se idanuna karaf cikin nashi, nidai ba zance ga duniyar da nake ciki ba amma nasan i was mesmerized into a lalaland. Nawwara ta taba ni da sauri nayi snapping daga kallon da nake
mishi tare da jan wani numfashi me karfi, tasowa yayi a hankali ya nufo inda muke tsaye, takun takalmin shi tamkar kara gudun bugun zuciyata yake, amma se na kasa dago idanuna balle na kara kallon shi, har seda ya karaso inda muke yace

“Baku kira su ba? Basa gida”

Nawaara ta zungureni lokacin data gama gaida shi, nima na dago ina hada kalmomi nace

“Ina wuni?”

Yayi min murmushi da ya bawa hakoran shi damar fitowa har na hango gap toothed space din daya saka yayi kyau. Ya amsa min sannan Nawwara ta sanar dashi abinda ya kawo mu, se ya ciro wayar shi daga aljihun gaban rigar shi ta jallabiyya yayi dialing number tareda karawa a kunne, yadda ya maida hankalin shi yasa na kura masa idanu a lokacin na fahimci wanda ke tsaye gaba na ba yaro bane dan a haife zai iya haifata amma Saboda yadda jikin shi yake na asalin fulani yasa ba zaka fahimta ba, fari ne dogo dan se na daga kaina sannan zan masa magana, ba a rame yake ba amma jikin shi ko fatar shi ka kalla kasan….

“Gimbiya…wasu sun zo karbar sako….dakin ki?…ok then se munyi magana anjima!”

Wannan conversation din yasa na dawo daga tunanin da nake, ya danyi excusing kan shi sannan ya shiga ciki within some minutes se gashi ya dawo da katuwar jaka ya mika mana yana fadin

“Shikenan?”

Na gyada kai tareda mayar mishi da murmushin da yayi min sannan muka fita daga gidan baki daya, bayan mun yiwa security da wani dake zaune hannun shi rike da key, muna zuwa na tada mota bayan mun saka kayan cikin back seat amma motar taki tashi, duk kokarina na kasa na jima ina yi amma hakan ya gagara, security ya leko yazo yace

“Ya dai?”

Nace

“Wallahi bansan me ya faru ba amma taki tashi ne.”

Ya danyi tabe tabe shi da driver amma mota taki gashi har an fara kiran maghrib, muna tsaye sega shi ya fito fuskar shi da hannun shi sun nuna alamar alwala yayi, ganin mu yasa ya tsaya yana fadin

“Motar taki tashi ne?”

Kaina na gyada raina a jagule yace

“Habu ko zaka aje su seka gano gidan, daga nan ka karbo number ta yadda zaa kai mata idan an gyara, sannan ka dakko mechanic din”

Habu jiki na rawa yace

“Tohm Alhaji yanzun zaayi!”

Mukai masa godiya ya wuce bayan ya dan min wani brief kallo dana lura ta gefen idanuna.

Muna nan tsaye driver ya fito da daya daga cikin motocin da muka tarar a parking space, ya bude Mana baya muka shiga sannan Nawwara ta Masa kwatance dake min jima a dutse gidan mu ba boyayye bane, nikam nayi shiru very deep in thought oMuna zuwa na Mika mishi key din motar tare da mishi godiya muka dauka kayan zamu shiga ciki, ya dakatar Dani yana fadin+
” Yace Zaki bani lambar wayar ki saboda….”
Purse Dita na bude na Ciro paper da pen na rubuta mishi a kasa nasa Nanah Ibrahim, sannan na Kara Masa godiya na shiga ciki, Daddy baya gari ya tafi Abuja tareda governor zaai wani inauguration. So banma Kira shi ba balle yayi fadan me yasa muka bar motar a wani wajen, na shiga ciki ina jin jikina a mace ba kamar yadda na fito ba few hours ago. Suka zo Suka tare mu Amma ba wai mu din suke yiwa ba abayar su suke yiwa oyoyo, dakina na wuce na zauna kan gado na zame turban cap din dake kaina na kwanta Ina tunanin abubuwa da dama cikin rayuwata, Ina jiyo ihun su a parlor kowa na squealing na murna. Sallah nayi sannan na fito zuwa parlor har lokacin Basu gama murnasu ba. Zama nayi nace
“Lub anti dinner ne?”
Mikewa tayi tana fadin
” Wayyo na manta wallahi”
Kai na na girgiza kawai na nufi kitchen din Ina jin Nawwara tana fadin
“Ku Kam me yasa kuke haka? Ace girki ma se ance muku, wallahi duk ranar da tayi aure muna ruwa”
Aisha ta biyoni tana ta kokarin Taya ni Amma na bata rai saboda sun bata min Rai ba kadan ba, ta Yaya se ma nace a daura abinci, ganin inata share ta se ta fice, ni kuma na karasa hada abincin da zanci, na dama custard a bowl na wuce dakina, sallah na fara Yi sannan na Sha na cigaba da sabgata a waya.
Washegari wajen Sha daya na safe patient masu siyan magani sunyi yawa, inata Kai kawo na dakko musu  naji wayata nata ringing, ban ma kula ba na cigaba da aiki na, se wajen two na gama komai har jakata na dakko sannan na tuna an Kira ni, dakkowa nayi na duba wayar see Naga new number so se kawai nayi dialing tunda daman Ina expecting Kira. Bugu daya aka katse call din se na tabe baki na cigaba da tafiyata zuwa lab gurin lubna, message ya shigo hakan yasa na duba
I’m in a meeting,will call you back after!
Maida wayar nayi cikin jakata ban masan waye ba dan haka na cigaba da sabgata, Muna komawa gida na tarar Nawwara ta gama lunch sunji abinda nayi musu jiya seda Suka no g zo cin abinci Suka tarar banyi ba so breakfast ma tun kafin na tashi Suka gama hadawa, tare muka ci masu islamiyya suka tafi, Ina kwance na Kira Daddy yace min flight dinsu se midnight kada mu rufe gida, na mishi Allah ya tsare Hanya sannan na cigaba da kallo. Se bayan maghrib sannan number nan ta kiranj, dama inata tunanin ya zaai da motar bana son ran Daddy ya baci.
“I’m sorry kin kira Ina meeting me.”
Shi ne abinda ya fara fada bayan nayi picking call din, a take na gane me magana, so se kawai na fara
” Ina wuni!”
“Lafiya Lau Nanah! Ya Rana?”
Nace
“Alhamdulillah! Motar ki , kina gida a kawo maki?”
Da sauri nace
“Eh Ina nan”
Daga haka na mishi godiya yayi min sallama, na aje wayar Ina jin sanyi a Raina, ko awa baayi ba se ga Kiran shi ya Kara shigowa, na tashi zaune nayi picking
“Kizo kofar gida!”
Fita nayi bayan na dauka katon brown hijab har kasa, tareda Aisha muka fita, duk tunani na shi dinne Amma muna zuwa na iske wani matashin saurayi da ba zai wuce shekaru ashirin da biyar ba tsaye da key a hannun shi, jingine jikin motar, da alama ya kosa mu fito Dan se kada key din yake yana karewa gidan kallo, gaishe shi mukai ya amsa yana Mana murmushi and I saw his father’s face on his, hatta gap tooth din Shima ya dakko har fatar tasu,
STORY CONTINUES BELOW
“Gashi Abbah yace a kawo Miki.”
Amsa nayi nace
“Nagode sosae, Dan Allah ka mishi godiya”
“Inshallah zaiji, sunana Yasir ke fa?”
Na danyi murmushi nace
“Nanah Fadima! Nice meeting you”
Ya lumshe idon shi hakan ya Kara fito da resemblance dinsa da baban shi yace
” You’re an epitome of beauty, nasan bani na fara fada Miki ba ko?”
Se nayi murmushi kawai, Aisha dake gefena se squealing take a hankali Dan ma Ina saka elbow Dina Ina zungurar ta, da may be ma ihu zatayi,  wayarshi ya Miki min tareda fadin
“Ko zan samu….. “
Bai karasa ba wayar ta fara ringing, sunan Pa da heart emoji yana yawo akan screen din se na Mika Masa Naga ya tattara duk nutsiwar shi ya bawa wayar, I heard him saying
” Abbah number ta zan karba”
Se Naga ya bata Rai yace
” Just Ina son mu Zama friends mee”
Ya Kara bata Rai yace
“I promise you”
Yana kashe wayar yayi min sallama ya juya ya tafi, I was very grateful da ban amsa number din ba. Na shiga na maida motar ciki an gyara ta tayi zamzam, Ina shiga naji Amal na fadin
” Yaya Nanah ina Yaya Yasir din?”
Aisha na kalla nace< /div>

” Gulma har kin fesa musu, to ya tafi gidan su”
Suka dinga murna wai shi kenan Nima zanyi aure na samu Wanda ke Sona, se ummu ta fara kuka tana fadin
” Kema seki tafi ki bar mu yadda su Yaya Rahma sukai”
Ganin yadda take kuka bilhakki da gaskiya yasa sauran ma jikin su yayi sanyi lubna me saurin kuka ta fara duk se Suka rikitani na zauna na dinga lallashin su,da kyar na samu sukai shiru hakan yasa na wuce daki bayan nace Kar suyi bacci Daddy zai dawo anjima, Ina shiga na dauka wayata ba tunanin komai na fara dialing number Abban Yasir kamar yadda na rike, katse Kiran yayi ya kirani na gaishe shi yace min
” Me Yasir yace Miki? I hope baki bashi number dinki ba”
Se abin ya bani mamaki, meye Dan na bawa Yasir contact Dina? Amma se na girgiza Kai nace
” Ban bashi ba, ya kawo min motar nagode sosae Allah ya saka da alkhairi ya Kara budi”
Cikeda nishadi, Dan daga muryar shi naji hakan yace
“Bakin ki ya iya godiya and kin iya addua, but I want you to know that you deserve it and knowing you mean the world to me”
Inada karamar kwakwalwa when it comes to stuffs dinnan se nayi murmushi Ina jin kunya tana Kama ni, to some extent words din sun danyi min nauyi a kaina kuma kamar shi ya Fadi hakan.
“Thank you!”
Na fada a hankali se yace min
“Good night Nanah”
“Night”
Nace mishi na kashe wayar, tareda aje ta Ina tuna every bit of our conversation da Yasir da kuma shi kan shi baban Yasir din, me nene hakan yake nufi a rayuwata? Na ayyana, kawai se na samu kaina da mikewa na fara zagaya dakin Ina adduar Allah ya kawo min koma menene zai so to yazo min da sauki ya kuma sa kada na Kara Shan wuya a rayuwata.
Ranar Sunday HOD dinmu ya kirani akan kada na fito morning, night zanyi saboda wadda ya kamata ta fito anyi Maya rasuwa, nace Masa to zanzo, Monday na wuni a gida misalin takwas na dare na shirya na musu sallama na tafi asibiti, inata dauki dan shi ne night dina na farko, nayi taking over na zauna akan kujera da wayata a hannu Ina chatting naji sallama da wata familiar voice, aje wayar nayi na dago Dan ganin waye da kuma tunanin ko dai har muryar ta fara min gizo ne? Ganin shi was the last thing da nake expecting, in fact nayi tunanin komai ya Kare tunda Bai Kara kira na ba balle dan shi daya Hana na bashi number ta, da mamaki yake kallona kamar yadda nake kallon shi nima sede shi mamakin ganina yake Yi at that late hour,gashi ko lab coat din ban daura ba se kayan dake jikina, gown na saka ta wani cotton material na saka hijab akai, paper hannun shi ya miko min na karba nayi going through nan na gane accident akai daga abinda akai prescribing, na dakko Masa duka na bashi, Bai Musa ba ya karba Amma ko magana bamuyi ba dan Naga he’s in a hurry, gurin cashier na biya kudin na dawo Ina tunanin waye yayi accident. Wajen 12am se gashi ya dawo, he was looking tired and exhausted, ya tsaya tareda kallona yace
” So me kikeyi anan?”
Nayi murmushi nace
” Ina service anan ne”
Se naga fuskar shi tayi haske saboda murmushin da yayi yace
” What a great news, naji dadi sosae”
Se na samu kaina da bude fridge na dakko masa ruwa me sanyi bottled da nazo dasu saboda dare, na Mika Masa yasa hannu ya karba
“Thank you darling!”
A hankali naji wasu abubuwa na bin jikina saboda wannan kalma ta karshe, ya kwankwade tas sannan yayi crushing bottle din yace
” Baki tambaye ni me nazo Yi asibiti ba”
Kaina na dafe da hannuna Dan tunda ya dawo Nike son tambayar shi Amma tsayuwar shi kusa dani yasa duka na manta me zanyi,
” I’m sorry! Waye bashi da lafiya?”
Ya Dan marairaice fuska se naga kamar Yasir ne a gabana, he looks younger and charming.
” Yusuf ya buge wani yaro yana driving yaron yayi crossing but luckily Babu karaya se lacceration da bruises”
Ajiyar zuciya na sauke nace
” Allah ya kiyaye gaba!”
Ya amsa da Amin sannan ya tambayeni zan iya bacci anan ko kuma Yaya, nayi dariya nace Zan iya se yayi min sallama ya aje min kudi ya tafi. Na Kira shi naji kudin meye yace na drugs dana biya ne, haka na hakura na dauka inata murmushi Ina jin fargaba na Kama ni, bansan gobe ba, Allah kadai yasan me zai faru,ina data tazo min da dadi.Kwanaki Suka Dan ja, an maida ni shifting gaba daya dukda ba haka naso ba amma hod yace gwara na Saba tunda yasan Dole watarana zai Kama ni. Ranar na dawo daga monthly clearance da muke Yi a Secretariat, a gajiye na dawo na cire kayan jikina na watsa ruwa sannan na kwanta bayan na kulle dukka windows, yau Yan nepa Zan Rama abinda sukai Mana daran jiya, sukai ki kawo wuta wajen 12am Mai ya Kare a gen. Kamar zanyi hauka saboda zafi se yanzun suka dawo da ita, AC na kunna Babu jimawa bacci me nauyi ya dauke ni, bani na farka ba se bayan laasar dama period nake so no need na tashi yin sallah, Shima Ina tunanin ko Yunwa ce ta tashe ni Dan kamar Zan ci Babu Dana tashi,wanka na Kara Yi na saka skirt da riga na atamfa na daura dankwalin na fito. Amal ce kawai a gidan dan dama nasan zasuje gidan Amina wai zasu taya ta sanitation,+
“Yaya kin tashi”
Ta tambaya bayan na fito da plate cike da abinci, Zama nayi nace
“Nasha bacci fa! Basu dawo ba kenan?”
Ta danyi dariya tace
“Ai se dare sannan zasu dawo”
Kaina na gyada na maida dukkan hankalina kan abincin, seda na gama sannan na janyo wayata Dan ganin missed calls din da aka bar min, hibba na fara kira tana picking nace
“Kin haihu ne?”
Tayi tsaki tace
“Thick skull, da cikin kwata kwata watan shi nawa?”
Na tabe baki nace
“Do I know?”
Se muka bar wannan maganar bayan ta fada min ai cikin is five months old, kusan daya dana Amina ta.
” Nanah ya ake ciki?”
Nasan zata tambayeni ko nayi saurayi ne, Dan ta zageni da nace mata mun rabu da Nasir, tabbas da wani yana yiwa wani aure da tuni hibba dasu Anty sumayya sun yimin, Babu dama su ganni da wani sun dinga tambayar shi kenan, Aisha seda ta fadawa Mom zancen Yasir, ta dinga min masifa akan me yasa ban bashi number ta ba nace to ni ya min yarinta da yawa, yace
“Se kije ki aura sugar daddy to, tunda ke kowanne namiji yaro ne a gurin ki.”
Nidai hakuri nake bata kawai a haka muka kashe maganar, cousins din mu na hadejia da sukai karatu musamman yayan Uncle Mahmud da suke Abuja, akwai dan shi Usman tun last week take Kirana akan yace mata yana Sona, ni kuwan se dodging nake Amma taki ganewa.
” Shiru Babu wani motsi fa, I’m still the single Nanah you know”
Na bawa hibba amsa, muryar ta naji tayi softening tace min
” Lokaci ne kin sani ko? Ina fata baki damun kanki”
Nayi dariya nace
” Kune kuke making dina nake feeling kamar rashin saurayin nan laifi na ne, idan ba haka ba me zai dameni”
Tace
” Kiyi hakuri! Amma I’m eager ne kawai na ganki a dakin ki wallahi”
” To ba se lokaci yayi ba, Nima ai Ina son nayi auran”
Muka Dan taba hira kadan, sannan mukai sallama, aje wayar nayi not minding in Kira sauran da suka Kira ni, kamar an tsikare ni na Mike tare da janyo wayar anan na ci Karo da number s
hi ya kirani Shima, ikon Allah nake ayyanawa nayi more than two months tare dashi Amma har yau bansan sunan shi ba, Bai taba fada ba Nima ban taba tambaya ba. Ina kokarin Kiran nashi sega wata number ta kirani, na dauka na Kara a kunne na
” Sunana Yusuf Idrith, Ina magana da Anty Nanah ne?”
“Eh Nanah ce! Amma ban gane waye ba”
Yace
STORY CONTINUES BELOW
” Allah ya bar Mana babbar Anty, may be baayi introducing dina properly bane, amma we will get to know each other soon!”
Kai na se ya Kara kullewa am not sure idan ni din ce gaskiya, se nace mishi
” Are you sure ni kake nema?”
Yace
” Of course kece Mana, Zan zo anjima kadan na kawo Miki sako, Ina fata Babu damuwa”
Na rasa me zance Masa se nace tohm, mukai sallama dashi nayi shiru na rasa me zance ma, to nidai Banda masaniyar waye Yusuf balle Wanda yake magana akai.
Yusuf na aje waya ya dubi Abbah dake gefen shi ya tsura mi shi idanu, alamar yana son yaji feedback, tunda Abban ya fada Masa kudurin shi yake jin tausayin shi sosae, all his life gani yake bazai taba kallon mace har ya sota ba Amma gashi seda girma ya Kama shi sannan abin yazo, kuma daga muryar da yaji yasan yarinya ce.
“Abba me yasa ba zaka fada mata ba, it’s high time ai”
Se yayi dariya yace
” Yusuf, it’s not as easy as you think it is, akwai factors da yawa da nake lura dasu. Maman ku, ku kanku, ita yarinyar da kanta kana ganin kowa zaiyi accepting cikin sauki”
Ya fahimci me uban nashi ke nufi, se yayi murmushi na karfafa gwiwa yace
” Nidai I’ve given you my blessings Abbah, mummy bana tunanin zata baka matsala sede idan an samu external forces ne, Zan baka shawara kawai kada ka fada mata se zancen ya kankama, Hanoon nasan zata amince bayan haka se muyi amfani da plan din mu, Yasir bashi da case indai zata bashi abinci ai shikenan, dama case din Adnan ne, yadda mummy tayi accepting maganar hakan Shima zaiyi.”
Abba yaja numfashi yayi shiru yana yiwa Allah kirari akan wannan jarrabawa data same shi, ya zauna da matar shi tsawon shekaru talatin, anyi mishi aure baya mantawa yana ashirin da biyu, ita kuma tana shekaru Sha biyar, ita din Yar abokin baban shi ce akai musu aure tunda yarintar su, suka ci kuruciyar su tare sukai karatu tare kowa ya Zama abinda ya Zama a wannan lokacin. Yaran su hudu Yusuf Wanda kowa yasan father’s baby ne se Adnan mummy’s boy, se Yasir dake hanging in between se auta Hanoon dake tsananin kaunar babanta, it’s obvious ba se ka tambaya ba. Tunda ya aura Barira Bai Kara ko tunanin zaiyi wani auran ba, an Sha bashi Yar aboki ko kuma boss Amma zai bada hakuri yace Barira ta ishe shi, a hakan sukai rayuwar su ta manyan Yan boko Yan gayu da yayan su, komai nashi sune , se kuma lokacin da yake ganin ta Yaya zai Kara aure kuma Nanah ta shigo rayuwar shi, se yaji Ashe dai Shima namiji ne, Ashe Shima zuciyar shi tana aiki bawai ta Zama frozen bane, yaji wani nishadi Wanda Bai masan akwai wanzuwar shi a duniya ba, yaji shi so new and Young, tuna ta kadai idan yayi ji yake kamar yafi kowa saa. Sede wannan factors din na ruda shi, yana shiga matsananciyar damuwa idan ya tuna kalubalen dake gaban shi!
A hankali ta fito daga daki bayan ta Hanoon ce sanye da wata riga da skirt na lace kanta Babu dankwali se kalba da take kan ta barbaje, a kayataccen parking sukai wa kansu masauki cikin manyan kujerun cikin parlon, idanun ta ta sauke kan Yusuf da Abba da Suma suke kallonta, tabe baki tayi tace
” Me ake discussing haka Babu ni?”
Yusuf yayi dariya yace
“Mummy ! Mummy!!”
Tabe baki ta Kara yi tace
“Abbah Hanoon na magana”
Ya dube Hanoon da ta Kara shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace
” Abbah motar fa”
Yusuf ya bude idanu yana kallonta yayin da Abbah yayi murmushi yace
” Motar me Hanoon?”
” Duka friends Dina are riding car”
”  Gimbiya kinji Yar ki ko? Shi ne abinda zai saka ma bazan siya Miki ba, friends din ki are different from you, family dinsu daban haka nan kema naki daban”
Ta kuma bata Rai kamar zatayi kuka tace
” Tohm Abbah, wayar fa”
” Wacce kike so?”
Tace
“iPhone X max”
Wayar shi ya Ciro ya Kira Mai kawo mishi wayar yace gobe ya kawo Masa X max office, mummy ta dube ta tace
” Wallahi na kuma jin maganar mota se ranki ya baci, idan driver bazai kaiki ba se ki hau machine ya kaiki!”
Yusuf ya Mike ya dubi Abbah yace
” Abbah Zan je na dawo”
Kafin Abbah yayi magana mummy tayi caraf tace
” Ina zaka je? Dinner fa?”
Ya Sosa keya, Abbah yace
“Na aike shi ne”
Yusuf ya fice yayin da mummy ta dubi Abbah tace
” Kai da Yusuf are suspicious, me kuke kullawa ne?”
Baice mata komai ba ya Mike ya nufi dining, itama hakan tayi ta bi bayan shi, suna Zama sega Adnan da Yasir sun shigo, tare sukai dinner sannan Abbah ya wuce bedroom din shi ko hirar da suka Saba Bai zauna sunyi ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *