A ZATONA COMPLETE BY Jeedderh Lawals
Www.bankinhausanovels.com.ng
*☆⋆01⋆☆*
Assalamu Alaikum wa Rahmatullah. Muna kara godiya da taruwarku a wannan zaure mai albarka, ina fata Allah Yasa mu gama lafiya kamar yadda zamu fara lafiya.
Littafin ‘A Zato Na’ mallakin wadda ta rubuta ne, ba’a yarda wani/wata su canza kowace irin suffa ta wannan littafi ba.
Muna fata zaku rike mana alkawari, ku kuma rike mana amana. Allah Yasa mu dace.
Da sunan Allah Mai Rahma Mai jin Kai’
‘Kirr! Kirrr!!’…
Karan daya ziyarci kunnena kenan lokacin da na danna lambar wayar kawata Janan. Bata dauka nan take ba, sai da yayi kara kamar sau biyar.
Kafin ta dauka hakurina ya gama karewa, saboda haka tana dagawa, ban bari ko sallama tayi ba na tare ta da; “wai dallah can malama me kika tsaya yi ne kin tsaida mutane?”.
Tace “jeez girl, bi a hankali mana. Ina jiran Anty Raheemah ne ta dawo kafin in fita”.
Na ja dan siririn tsaki, “kawai ki fito ki bar mata gidan a haka mana. Ba maigadi yana nan ba?”. Janan tayi ajiyar zuciya, “kin fa san abinda ya faru last time da nayi haka. Tace an shiga an mata satar kudi da jewelries, kuma dole sai da Yaya Bilal ya biyata sannan aka zauna lafiya, bana son abu makamancin haka ya sake faruwa”. Nace “sai kiyi ta zama ai ta mayar da ke maigadinta. Ni dai wallahi idan baki zo nan da mintuna goma ba ko? Sai dai mu hadu da ke acan kawai!”. Ban jira ta kara cewa komi ba na kashe wayar na ajiye ta a gefena.
Browsing naci gaba da yi da system dina, sai da nayi kamar minti goma sha biyar kafin na kashe na ajiyeta a mazauninta. Janan na sake dannawa kira, tana dauka tace “gani nan don Allah, sarkin gajen hakuri kawai!”. Na tabe baki ba tare da na damu da abinda tace ba, nace “better. Idan kin iso ki kira ni kawai mu hadu a main entrance” tace “toh”.
Gadona na dan gyara kafin ta iso. Zuwa lokacin da Janan ta kirani, na gama kimtsawa. Na dauki gyale na nada shi a kaina yadda ya zagaye rabin kirjina da bayana, na dauki wayar hannu, purse da flat din takalmi ruwan goro kalar veil dina da zanen flower da yake jikin doguwar rigar gown ta atamfa da na sa, na zura shi a kafata. Aylah, roommate dina na yiwa sallama na fita.
A bakin hostel din Queen Amina dake cikin campus din ABU Zaria, na tsaya ina karewa wajen kallo cikin neman Janan. Ina kokarin kiranta a waya na hango ta acan inda ake parking motoci a gefen hostel din tana dago min hannu, murmushi na saki cike da murna da dokin ganinta na taka a nutse na tsallaka zuwa inda take. A tsakiyar wajen ta tareni, muka rungume juna cike da doki. Duk duniya, ita kadai ce naki jinta kamar wata yar uwata ta jini, kamar yadda nasan itama haka take a bangarenta.
Na kalli iNext din da naga ta fito daga ciki ina daga mata gira, “Ya Almu ya sake sabuwar mota ne hala?”. Ta girgiza kai tana murmushi, “ina Almu na yayi arzikin sayen irin wannan abun? Yaya Bilal ne”. Na dan zare ido cikin mamaki, “Holy Wow!! Yaushe rabon da in ga Yaya Bilal? Har na manta wallahi. Yau dai Allah ya nufa zamu hadu kenan!”.
Tayi dariya da tasa dimples dinta suka lotsa, abinda yake burgeni da haliitar ta kenan. Tace “sosai ma. Allah ne yasa ban samu abin hawa da wuri ba, shine yace bari ya kaini tunda shima wajen FCE din yayi. Taho muje, muna kara makara”. Na bi bayanta zuwa wajen motar.
Janan ta bude gidan gaba, ni kuma na bude baya muka shiga a lokaci guda, bakina dauke da sallama. Sansanyan kamshin freshener na cytrus da mix din strawberry ya doki hancina hade da sansanyan sanyin AC daya dumame motar. Muna tsakiyar watan May ne, saboda haka ba karamin zafi muke sha ba a garin na Zaria.
A nutse na gaishe da Yaya Bilal, ya juyo a kaikaice ya amsa tare da juyawa ya tashi motar muka bar wajen. Babu abinda na iya kararwa game dashi sai cewa faded jeans ne a jikinshi da T-shirt mai zanen zebra a jiki, sai sunglass da ya saka ya sakaya idanunshi.
A hankali yake tukin, tattausar kira’ar Sheikh Malam Minshawee tana tashi cikin suratul-Kahf, na jingina kaina da kujerar motar na lumshe idanuna, a can kasan zuciyata kuma ina bin kira’ar bi da bi. Yayin da a gefe guda, shi da Janan suke hira jifa-jifa. Har muka isa makarantar Kongo, inda zamu je, a bakin gate ya nemi waje yayi parking. Sai a baki-baki ma yayi parking din, saboda yadda wajen ya cika da mutane da ababen hawa. Muka mishi godiya muka fita, ya ja motar ya tafi, mu kuma muka tunkari gate din makarantar.
Ranar babban Shehin malami, ‘ Dr. Bilal Philips’ yake zuwa yin wa’azi. Saboda haka, you can only imagine yadda wajen zai cika da mutane wai don ma na mata ne zallah. Duk da mun zo kusan mintuna arba’in kafin a fara wa’azin, da kyar muka samu wajen zama muka zauna.
Akan Matan da zasu shiga aljanna yayi wa’azin ranar. Kafin ya gama, jikin kowace diya mace dake wajen yayi sanyi saboda yadda ya dinga zano abubuwa da mu mata muke yi, muna tunanin ba wani abu bane, either ga junanmu ko ga mazaje da iyayenmu, alhalin abubuwan nan za su iya jagorantarmu zuwa wuta. Karfe sha biyu na rana aka gama wa’azin, saboda karancin abubuwan hawa da aka yi ranar, bamu samu mun koma cikin makaranta ba sai kusan karfe daya da rabi.
A dakina muka sauka, Janan tayi sallar azuhur, kafin ta gama ni da bana yin sallah na gama dafa mana jollop spaghetti. Bayan mun gama cin abincin, kan gadon muka hau, na kunna mana film din Pick the Stars, wani Korean Film, muna kallo. Bamu jima da fara kallon ba, barci ya daukeni.
“Na’ilah!”.
“Uhmn?” na amsa cikin barci.
A hankali naji an kai tattausan hannu gefen fuskana an shafa cike da wani irin tenderness da yasa naji bugun zuciyata ya canza sosai. “I Love You, baby! So much!!”.
Aka fadi a daidai saitin kunnena, cikin wata irin tattausar murya. A hankali na bude idanuna dake cike da barci, mutumin da ke zaune a gefen gadon da nake kwance, appears very blurry, bana iya ganinshi cikin rashin hasken dakin.
“Na’ilah?” naji ya sake kirana cikin tattausar muryarshi, na saki murmushi a tausashe ina amsawa, “uhmmn??”.
“Na’ilah!!”. Wannan karon naji an kirani da karfi. A gigice na tashi zaune, kaina ya bugu da bango. Da sauri na dafe wajen na maida kaina kan pillow ina hararar Janan dake zaune a gefena, tana kallona cike da alamun tambaya.
Harara na jefa mata tun karfina, cikin tsiwa nace “dallah can Malama meye haka, zaki katse min barcina mai dadi?”.
Ta daga kafada, “maganganu kike yi cikin barci. Abin naki ya dawo ne?”.
Na kara komawa kan katifar na kwanta, “Wallahi kuwa Jan. Yaushe rabon ma da inyi irin mafarkannan? Har na manta. Sai yau”.
Janan tace “to sai ki kiyaye da addu’o’i dai. Is’haq yazo yana jirana a waje, bari in tafi”.
Na duba naga yamma har tayi.
Na mike ina lalubar mayafi na, “muje in miki rakiya to!”.
Ta tashi na rufa mata baya, dakin na rufe kasancewar abokiyar zama na bata dawo ba, muka sauka kasa ni da ita.
Har parking lot na rakata inda Is’haq yake jiranta. Ta bude gidan baya ta shiga, na maida mata kofar na rufe ina daga mata hannu, a haka suka tafi. Sai da na tsaya anan kofar hostel din na sayi yoghurt babbar roba mai sanyi sannan na koma daki.
Bayan na yi yan gyare-gyare da kimtse-kimtse na, arm chair na dauka na ajiye a gefen gadona na zauna, na dora laptop dina akan gadon na bude tare da cigaba da kallon da muka fara ni da Janan.
Sai bayan magriba Aylah, roommate dina ta dawo. Har zuwa lokacin ina kan system dina, ta min sallama na amsa, a gajiye ta zauna a gefen gadonta. Sai da ta huta, sannan tayi sallah. Taci sauran spaghetti din da muka bari ni da Janan.
Ni kam karfe bakwai tana yi, na kashe laptop din na mike. Kasa na sauka inda common room yake, na kalli serieses din da nake kallo a Zee World; Twist of Fate da King of two Hearts. Karfe tara na koma daki, ina zuwa shirin kwanciya barci nayi cikin riga da wando, na bi lafiyar katifa na kwanta.
Hira muka fara da Aylah, tana bani labarin abinda ya faru a wajen bikin da taje ranar. Wai mutumin mace ta biyu ce zai aura, wadda ta kasance kawarsu ce. Shine a wajen lunch party, matarshi ta farko taje da tawagarta, aka yi rashin mutunci dai yadda ya kamata.
“Dama duka yaushe ne Yayan su Afrah kawata zai sake aure, amaryar ta hadu da uwargidan a shagon saloon. Wallahi tsiyar da aka yi a wajen sai ta baki mamaki. Kaca-kaca suka yi wa juna. Bayan anyi auren kuma da sati biyu, ya dankarawa uwargidan nashi saki. Naji ance kusan watannninta biyu a gida, sai kwanannan ta koma”.
Nayi ajiyar zuciya tare da girgiza kai. Abinda yawancin mata suke jin tsoro game da kishiya kenan, taje ta fitar dasu daga gidansu. Ko ta hana su zaman lafiya da miji. Ko ta zauna, haka zaka kare rayuwarka cikin tashin hankali, fargaba da takaici.
Aylah ta cigaba da cewa, “ni wallahi gani nake babu wani aibu game da wata kishiya. Ba abokiyar zama bace? Menene a ciki? Idan dai ka kwantar da hankalinka, tsaf zaku yi zaman lafiya da ita wallahi!’.
Na kada idanu, “baki san komi ba game da kishiya Aylah. Kiyi shiru kawai. Ina tunanin duk danginki babu wadda take zaune da kishiya ko?”.
Ta daga kafada, “Anty Hanifa ce kawai, kuma suna zaune da ita lafiya lau”.
A hankali murmushi ya subuce min, “to wannan sa’a ce tayi ba karama ba, ina gaya miki. Wallahi da tayi rashin sa’a, gabadaya sai ta girgiza family dinku saboda sanabe”.
Aylah ta girgiza kai, “naa. Bana tunanin haka. Kada dai kice min, baki son kishiya Na’ilah?!”.
Murmushi kawai nayi, na gyara kwanciyata tare da mata sai da safe.
Dare ya tsala matuka, yayin da barci ya gagari idanuwana. Zuciyata tayi wani irin nauyi, ji nake kamar an dauki wani gungumemen dutse an dora min a kai, numfashi ma sai da naji ya fara gagarata. A hankali na janyo wayata da headphone na hada, na kamo kira’ar Sheikh Malam Ahmad Suleiman na kunna. Idanuwa na lumshe a hankali, ina bin kira’ar a cikin raina.
To say that na tsani kishiya, is an understatement.
I despise her! Na tsaneta with all my being.
Tunanin zama da kishiya kadai a cikin raina, yana sa jinin jikina tafasa, zuciyata zafi kamar ana diga ruwan dafaffiyar dalma.
Allah Ya gani, bana son kishiya. Ina kuma da yakini a cikin raina, ko zan mutu tuzuruwa, sai dai hakan ta faru, amma ba zan taba zama da kishiya ba!!.
And why not, you might ask?!
A shekaru na bakwa a cikin rayuwata, na dandana zafin kaidi irin na kishiyar uwa, a wani unfortunate dare, da na kira ‘bakin dare’.
Ranar mahaifina yake sake aure, kyakkyawar bafulatanar mata, fara doguwa, tsayi wanda ta tafi gabadayanta ta mike, babu lankwasa ko duk’awa, har yau ina mamakin dalilin da yasa Baba ya aureta.
Idan kyawune, mahaifiyata tana daya daga cikin kyawawan cikin danginsu, kasancewarta ruwa biyu, shuwa-arab da barbanci, yasa ta kasance mace daya tamkar dubu. Kyawu, ladabi, biyayya, iya girki, kwalliya, kada ma ayi maganar tsafta, don gani nake duk duniya, babu na biyun mahaifiyata a tsafta.
Saboda haka, dalilin auren Babana da bafulatana Ramata, kazamiya mara kira, still remains a mystery, yet to be solved to me.
Bana taba manta ranar da aka kawota gidanmu, ina ta murna an kawo min wadda zan kira Anty na. Masu kai amarya sun shigo da habaici, suka tafi da bakaken maganganu a bakinsu, duk mahaifiyata da abokanta yan dannar cinya suna jinsu, amma suka kauda kai kamar basu ji ba. Wannan abu ya bakanta musu rai.
Wata daga cikin kawayen Mama da ta kasa kau da kai, ta tanka musu. Ba bata lokaci suka hau zage-zage, kamar dama jira suke yi, ko kuma da guzirin zagin suka shigo. Da kyar aka ba Iya Lami hakuri, su kuma suka tafi.
Bayan tafiyarsu babu jimawa, suma yan dannar cinyar suka mana sallama suka tafi, suna ta kara ba Mama na hakuri. Ni kam ina zaune muk’u a lokacin, ina jiran Mahaifina ya dawo. Bai dawo ba har barci ya daukeni.
Can zuwa cikin dare, hayaniya ta tasheni. Ba wai kuma normal hayaniya ba, kukan mahaifiyata ne ya tasheni wanda nake jiyowa yana tashi daga can dakin Babanmu.
Kasancewar gidanmu dakuna hudu ne, biyu suna kallon biyu. Dakin Mama shi yake kallon na amarya da Baba.
Daga tagar cikin dakin Mama na leka, ina hangen ta tsugune a gaban Baba. Matar da aka kai mishi a matsayin amaryarshi, a zaune a gefenshi kamar zata hau cinyarshi, tana ta wani firirita. Ban jiyo abinda suke cewa ba, daga karshe dai na ga Mama ta tashi ta fado daki da sauri.
Babu bata lokaci ta hau lalubar mayafi, ta yafa nata, nima ta miko min nawa. Ina tambayarta ‘Ina zamu je Mama?’, amma saboda tsabar kuka da take yi, ta kasa amsa min. Hannuna kawai ta kama ta ja muka fita daga dakin.
A bakin kofa, mahaifina ne a tsaye, kamar wanda yake jiran ta fito. Muna fita, ya kamo hannuna ya rike. Har yau ina tuna maganganun daya fada mata clearly,
“Kada ki kuskura kiyi tunanin zaki tafar min da diyata, yadda itama zaki je ki koya mata rashin kunya da rashin mutunci ko? To ba dani ba, yadda kika zo gidannan zikal, haka zaki tafi!”.
Wani kukan ya sake barkewa daga bakin Mama, cikin rishin kuka, magana na fita da kyar, tace “haba Malam, ta yaya zaka ce in bar maka yarinya yar shekara bakwai a hannun wannan azzalumar mata ta ka?”.
Ina tunanin hakan shi ya kara tunzira Baba, ya bude baki ya hau zazzagawa Mama masifa kamar wanda yake amayo kalmomin. Ban taba ganin tashin hankali irin na ranar ba.
Tunda aka haifeni, ban taba ganin sa’insa tsakanin iyayena ba. Tun tasowata, iyakarsu kawai: ‘Yana yi kaza, to. Yana kada kiyi kaza, to Malam’. Ganin wannan abu a ranar nan, was a first. And definitely not a good one.
Ina ji, ina gani, Mama tasa kafa ta bar gidan, Baba ya bita a baya ya rufo gidan. Bai ma kula da cewa ina kofar dakin Mahaifiyata daya gama ci wa mutunci a gabana ba, ya wuce dakinshi. Amaryarshi na tsaye a kofar daki tana jiranshi, yana shiga, aka maida kofar dakin aka rufe, ji kake garammmmm!!.
A hankali naja kafafuna da suke rawa, na koma cikin daki. Kan gadon Mamata na hau, na kwanta.
Karo na farko a rayuwata dana kwanta ba tare da na ji dumin mahaifiyata a jikina ba. Kullum sai na yi barci take tafiya dakin Baba. Sai dai kawai wani lokaci idan na tashi cikin dare, in ga bata nan.
Daren ranar barci sai barawo.
Washegari tun da safe na tashi, al’adar gidanmu ce. Na share tsakar gida tsaf, na kunna wuta a murhu na dafa ruwan zafi, kasancewar lokacin sanyi ya fara shiga. Na je nayi wanka, na koma daki na shirya.
Shiru ina zaune, ina jiran a fito a dora abincin kari, ban ga motsin kowa ba. Ganin karfe takwas tana neman shigewa, yasa na dauki jakar Islamiya ta na fita. Sai da na saka makulii na rufe dakin Mama, sannan na yi sallama a kofar dakin Babana.
Sai da aka dauki lokaci kafin aka amsa min, a hankali na tura kofar dakin na shiga. Baba yana zaune a gefen katifarshi, amaryarshi na kasa kusa dashi, tsabar kusanci har cinyarshi na gogar tata, nayi saurin yin kasa da idanuwana.
Karin safe ne a gabansu, shayi, libgegen biridi, soyayyen kwai, da indomie.
A nutse na gaidashi, ya amsa ciki-ciki. Ganin na ki gaida matarshi, yasa ya umarceni da in gaidata. Cikin tafasar zuciya na gaidata, ta amsa tana watso min wasu dogayen hakora marasa tsari, wai ita ala dole murmushi take yi. Bayan a hakikanin gaskiya, ko kare aka yiwa murmushinnan yasan cewa dole tasa aka kakaro shi.
Bayan nan zamana nayi ina kallonsu suna karyawarsu a nutse, sai daya gaji da ganina sannan ya tambayeni lafiya? Na bude baki ni kuwa nace mishi ban karya ba.
Ya yanko burodin gami da tsiyaya shayin daya sha hadi, yaje yanko kwai amarya tasa hannu ta kame, ta wani langabar da kai tana mishi magana kasa-kasa, ban san me tace mishi ba, na dai ga ya zare hannunshi ya miko min biredi da shayin, na sa hannu biyu na amsa.
Waje na koma, na zauna na shanye. Na dauraye kofin. Daya daga cikin al’adar Mama kenan da na dauka, sam bata barin kwano mai datti. Hatta da cokali idan tayi amfani dashi, a take a wurin take wankeshi.
Ban kara waiwayar Baba da Amaryarshi ba, na wuce makaranta abina.
Karfe sha daya na safe muke tashi daga Islamiya a lokacin, daga can na kan wuce gidan Kakannina, iyayen Mama. Malam Bako Kakana, babban malamin allo ne da yayi suna a ciki da wajen garin Gashua. Yana da tarin dalibai yara da manya da suka kasance a ciki da wajen garin Yobe baki daya. Kullum na tashi daga makaranta, wajenshi nake wucewa inje ya taya ni biya karatuna, ya kuma dora min nashi wanda muke yi, watarana acan nake tsayawa har lokacin komawarmu Islamiya da yamma yayi, bana komawa gida sai dai in koma makaranta daga can.
Ranar ma can na wuce. Bayan munyi karatun, anan nake jin cewa wai ya je ya samu Babana akan maganarshi da Mama. Wai Baban yayi fir yace wai shi bai kori Mama daga gidan ba, ita taga damar tafiya, anan nasan cewa lallai sake aure ya kan sa mutum ya canza halaye.
Ban taba jin Babana ya fadi abinda ba shi kenan ba, sai a lokacin.
A daren ranar da dare Mama ta koma gida. Tun daga wannan ranar, ko in ce tun daga ranar da kafar Ramata ta taka doron kasar gidanmu, bamu sake samun farinciki da kwanciyar hankalin da muka samu kafin tazo ba, har yau dake motsi…
*******
Karan alarm din dana saka ne ya tashe ni daga barcin daya daukeni. Jiya barci ya daukeni ban cire headphone din dana saka a kunne na ba, ban san ma yadda aka yi na cire shi ba, na dai hango shi a kasan gadona. Na kai hannu kasan filona na zaro wayar, dusu-dusu nake ganin komi saboda barcin daya cika min ido. Naga karfe hudu da rabi.
Na kan manta in cire alarm din da yake tashi na sallar asuba duk lokacin da nake fashin sallah.
Kashe alarm din nayi, na koma na sake kwanciya. Sai karfe shida alarm dina na biyu ya sake bugawa. Nan na samu na mike da kyar ina layi. Cikin awa daya, nayi wanka na hada abin kari. Yeah, idan zaku kira indomie da bakin shayi breakfast, to abin kari.
Lokacin Aylah itama ta tashi.
Babu wata kwalliya da na tsaya bata fuskata da ita, daga mai, hoda, da janbaki, bana kara komi. Sai a lokutan da basu cika faruwa bane nake saka jagira da kwalli.
Na janyo stool gefen gadona na zauna na karya, ina gamawa na janyo uniform dina farare tas na saka.
Dogon wando ne fari, da riga wadda ta kai har gwiwata, na daura farin dankwali a kaina bayan na cikuikuye dogon sassalkan bakin gashin kaina na daure da ribbon, sai na dauko karamar farar hijabi data tsaya a saman kirjina na saka.
Na dauki agogon hannu ruwan kasa mai haske na daura, a jikinta naga cewa bakwai da rabi ta kusa yi. Cikin sauri na dauki gyale mai yalwar fadi na yafa a jikina. Na dauki purse, wayar hannu da littafin da nake shigar da duk wasu bayanai na ilimin dana dauka a ranar da naje asibiti, cikin sauri na zura bakin toms a kafata, na yiwa abokiyar zamana sallama na fita har ina hadawa da dan gudu.
Ina zuwa, bus din da take daukanmu zuwa Kongo tana zuwa, don haka na bi jerin mutanen dake layi suna shiga ciki, bayan na biya kudin mota.
Karfe takwas da yan mintuna na sauka a inda na saba sauka. Daga nan acaba na hau, zuwa cikin unguwar Gyallesu, wani karamin public health centre nake zuwa aikin TP na. Karfe takwas muke farawa mu gama karfe daya zuwa biyu. Kowa dai yasan yadda dalibai suke da son yin latti, musamman a irin wannan lokacin da kasan cewa babu wanda zai kulle maka aji, ko ya hana ka attendance.
Duk da lattin da nayi, sai da na riga Janan isa. Ita wannan dama ba’a maganarta idan ana zancen latti, sam bata dana biyu.
Karfe sha daya da rabi muka tashi. Muka fita daga wajen ni da ita a gajiye, kuma cikin sanyin jiki. Babu ranar banza da ba zaka je asibitin nan baka ga abinda zai tayar maka da hankali ba.
Ranar an kai wata mata mai ciki asibitin. Kwanaki uku kenan da aka yi mata scanning, aka ga cewar dan cikinta ya rasu. Maimakon a yi inducing dinta, sai mijin ya ciccibeta suka koma gida. Wani abin karin haushi da ban takaici shine, mijin nata likita ne, duk da ba zan ce likitan ainihi ba tunda shago ne yake dashi babba da ake sayar da magunguna.
Tun shakaranjiya take nakuda, bai kaita asibiti ba sai ya kira unguwar-zoma. Ana ta kai da kawo dai, har jiya bata samu ta haihu ba, shine yau da safe suka tarkata ta zuwa asibitin. Ana maganar a dauketa a kaita Shika, domin a mata tiyata a cire cikin, rai yayi halinsa.
Abin gwanin ban tausayi da takaici. Ga ta da yara kanana wadanda basu gama mallakar hankulan kansu ba.
Har muka je inda muke hawa acaba, abinda muke tattaunawa kenan ni da Janan.
Ta kalleni tana canza muryarta zuwa alamun roko, “don Allah sis, kizo muje gida mana. Sai ki koma da yamma, kinji?”.
Na harareta, “tab! Allah Ya kyauta wallahi. Ni kin ma ga tafiyata!”.
Nayi saurin sa hannu ina kiran daya daga cikin yan acaban da suka yi jerin gwano, suna jiran fasinjoji.
Da sauri ta riko hannuna, “please, kinji? Don Allah!. Wallahi kwana biyun nan gidan babu dadi. Dama a wajen Yaya Bilal nake samu na dan ji sauki wasu lokutan, idan yana gida. To shima kwanannan sai a hankali. Tun jiya da yamma ya rikice, ko kallona baya yi wallahi. Yau da safe dana gaida shi, ko amsawa ma baiyi ba. Kuma ya hana ni yawo, balle inje wani wajen. Don Allah, muje ki dan debe min kewa, kinji?”.
Gabadaya tausayin ta ya lullube ni. Wani irin bahagon zama suke yi da matar yayanta. Wani lokacin sai kayi kuskure kace irin zaman kishiyoyin nan ne da suke zabga dan banzan kishi suke yi.
Ba tare dana sake tunani ba, na gyada mata kai. Tayi tsallen murna tare da rukunkume ni.
Napep muka tara, bayan na ba dan acaban da muka kira hakuri. Unguwar PZ muka nufa, wadda bata da nisa da wajen da muke zuwa TP din.
Gidan Yaya Bilal, inda Janan take zaune, babban gida ne sosai. Daga nesa idan ka hango shi zaka yi tunanin irin family house dinnan ne. Sai dai su biyu ne suke zaune, shi da kaninshi Jameel, sai kuma matansu.
Kowacce tana da part dinta, masu fadi da nisa da kowannensu, ta yadda idan daya taga dama, zata kwashe watanni bata ga yar’uwarta ba.
Sashen gidan Yaya Bilal ake fara tardawa idan aka shiga gidan. Shima can din ya kasu kusan parts uku, duk da sauran biyun duk a kulle suke, dayan ne Janan take zaune ita da Raheema matar Yaya Bilal.
Shekaru biyu da suka wuce ne suka yi auren, basu ma cika da yin shekara biyu ba. Har yau Allah bai basu haihuwa ba.
Abu ne da naji kus-kus suna tashi akan cewa wai, wai Yaya Bilal din baya haihuwa. Saboda matarshi ta farko ma, Ameerah, wadda suka kwashe shekaru kusan shida a tare, auren saurayi da budurwa, bata taba haihuwa ba itama.
A hankali muka yi sallama cikin falon gidan, bamu ji motsin kowa ba, ko na TV babu, balle na mutane. Janan ta ja ni zuwa dakinta, ta koma kicin ta dauko mana ruwa da lemu.
Ina zaune a gefen gadonta, na dinga jiyo karar sautin kida tana tashi. Na kalleta, tana tsaye a gaban wardrobe tana nema mana kaya masu saukin nauyi da zamu saka.
Nace “wannan karar fa, daga ina take fitowa haka?”.
Ta dan juyo ta kalleni, kafin ta maida kanta cikin closet din. “babu mamaki su Haleemo ne suke kallo!”.
Na dafe baki, “wai dama yaran nan suna nan har yanzu?”.
Tayi yar dariya, wadda take lullube da zallan takaici, “to dama ina zasu je? Ai suna nan a gidan nan, basu da ranar fita!”.
Ta miko min Skirt dogo na wani yadi tare da riga, na amsa na fara zare kayan jikina, nace “to Allah Ya kara rufa mana asiri!”.
Tace “ameen”.
Ni tunda nake ganin gidan aure da cakudewar rayuwar aure, ban taba ganin irin wadda ta kama kafar ta gidan Yaya Bilal ba.
An saba idan aka yi aure, akai amarya ita daya zikal dinta gidan miji. Sai dai ita wannan abun nata ya bambanta. Koda aka kai amarya, sai kannenta guda biyu suka samu waje suka share, suka mike kafafu a gidan. _Marry one, get two free kenan!._
Watanni bakwai da kai amarya, Babbar kawar amaryar ta kaso aurenta, itama taje tabi layin jerin yan’uwanta dake gidan kamar wadda bata da gidan zama. Yanzu dai su ukun duka suna zaune a karkashin kulawar Yaya Bilal ne. Amma yar kanwarsa daya tilo dake zaune dasu, sun kasa riketa balle su kula da ita.
Kullum fata da buri nasu ta bar gidan, bin malamai, asiri, kissa da kisisina, babu wadda basa yi. Allah ne kadai yake kareta a gidan nan.
Tana gama sallatar azuhur, ta ja ni muka shiga kicin domin mu nemi abinda zamu saka a cikinmu. Muna cikin girkin Yaya Bilal ya shigo kicin din, ya amsa gaisuwar da muka mishi a kaikaice.
Ya kalli Janan yana wani cin magani, “ke ina Raheema take ne?”.
A hankali kamar mai tsoron magana, tace “yanzu muma muka dawo, bamu sameta a gidan ba”.
Bai kara cewa komi ba, ya fita daga kicin din. Ko me yake faruwa kuma yanzu? Na saba ganin kallon so da kulawa daga gareshi zuwa ga yar kanwar tashi, yau kuma naga wani abu daban.
Na kalli Janan dake kokarin hadiye kwallar data cika mata ido, cike da tausayi. Haka Allah ya halicceta mai sanyin hali, da sanyin zuciya.
Danwaken fulawa muka kwaba, daidai wanda zai dauki cikin mutum biyu. Duk kokarin da tayi na mu kara yawan fulawar, ki nayi. Saboda nasan saboda wannan lalatattun yaran take so muyi da yawa. Ni kuwa da in dafa abinci da hannuna, kattin banza su cinye, su goge hannu da tissue su kara mike kafa, karshe ni ce zan kwashe kwanukan da suka ci abincin ma, na gwammace in zauna da yunwa.
Muna gamawa, muka juye shi a cikin kula tare da gyara kicin din tsaf, kamar babu abinda aka yi. Janan ta wuce mana da kular daki, ni kuma na dauki plates da vegetables din da muka yanka nima na fita dasu.
A bakin kofar kicin muka ci karo da Salama, kanwar Anty Raheemah. Duk cikin kannenta babu wadda ta fita rashin da’a da rashin mutunci, shi yasa jininmu bai hadu ba, sam.
Ta wani tsaya kerere, ta kama kugu tare da kara babakewa akan hanya. Ko tayi zaton zagayeta zanyi in wuce? Na saki wani murmushin mugunta. Lallai yarinya har yau baki gama sani na ba.
Na tunkareta gadan-gadan. Da dai taga ina shirin bangajeta, sai taja baya. Na ja dan siririn tsaki a cikin raina, ina raya ‘dama kin tsaya kin ga karshen wulakanci!’.
Ta wani daga murya, “ina namu abincin?”.
Na kuwa tsaya cak, na juya na kalleta, “ban gane naku abincin ba? Kin daukeni aikatau din yi miki girki ne dama ban sani ba?”.
Tayi gyatsine, “taya za ayi ki shigo har cikin gidan Yayata, kiyi girki sannan kuma ki k’i ajiye mana?”.
Naji wata dariya na neman subuce min, nace “to sannu hamshakiya! Sarauniya mai girma!! Allah Ya bamu hakuri mu da bamu da gidan Yaya dake aure a gidan mutane, balle muje mu shimfida mulki a inda bai dace ba!. Girki ne, bamu yi daku ba. In kinyi zuciya, ga hanyar kicin nan, ki shiga ki girka wanda yafi wanda muka girka!”.
Na juya na shige daki, tare da maida kofar dakin na rufe. Ina jin sautin maganganu da zage-zagen da take yi. Janan tace “ni dai wallahi da baki biye mata ba!”.
Harara na jefa mata, “ai a haka suke samun damar taka ki kamar wata sakara. Ke dai da kika ga zaki iya, sai kije kiyi tayi. Ni kam, ba zan iya jure rashin kunya irin nasu ba wallahi!”.
Kai kawai ta gyada, don tasan gardama dani ma bata baki ne.
Karfe biyar na mata sallama zan koma makaranta. Zuwa lokacin babu kowa a cikin gidan, muna jin lokacin da suka fita. Daidai bayan tagar dakin Yaya Bilal, na hangi wani abu daya dauke min hankali. Da sauri na kalli Janan, “kai! Kinga kuwa na manta jotter na akan gado, don Allah taimaka ki dauko min ita mana, zan jira ki anan!”.
Babu musu tace “to!”.
Tana bada baya, nayi sauri na karasa wajen. Da sauri na duka tare da yin bismillah, na fara hak’a. Kamar yadda nayi zato, wasu kullin abubuwa naci karo dasu. Da sauri na ciresu, na maida kasar na rufe kamar yadda take.
Ina komawa inda Janan ta barni, sai gata ta dawo. “Ni fa ban ganta ba, ko dai a asibiti kika barta ne?”.
Na daga mata hannun dama ta, “ashe tana hannuna, sha’afa nayi”.
Ta kada idanu, “ke dai shiriritarki tayi yawa wallahi!”.
Muka jera da ita har zuwa inda zan hau bus. Sai da taga na shiga, motar ta tashi, sannan ta juya tana daga min hannu, tare da jaddada min dana isa cikin makaranta, in kira ta.
Dariya kawai nayi na gyada mata kai, wani lokacin haka take, kamar wata overprotective Yaya, ko Uwa.
*☆⋆02⋆☆*
“Haba Sweety, ni sai ki dinga cewa wai bana sonki saboda Allah! Bayan kin san cewa duk duniya bani da kamar ki!”.
Ya fada daga can daya bangaren na wayar, whinnying kamar wani karamin yaro.
Na kada idanu sama, “To ai kai dinne sai ka dinga wasu irin maganganu da suke saka ni cikin shakku, Umar”. I mean, ta ya mutumin da yake ikirarin saboda Allah yake sonka, kuma ya dinga kokarin dilmiya ka a duniyar ‘sex chat?’. Kullum muka yi waya dashi, da kalar dirty maganganun da zai tare ni dasu, tun ina mishi alkunya, a tunanina zai fahimci zancen ya daina, har na fito baro-baro na fada mishi cewa bana son hakan, amma duk da haka bai fasa ba. Don haka nace mishi naga alamun cewa ba son gaskiya yake yi min ba, akwai abinda ya gani a jikina dai kawai. Nan ma yace ba haka bane, daga nan ya dan rage yin maganganun, note that ‘ragewa’ nace, ba dainawa ba. Ni kuma kullum ya dauko min maganar abinda nake ce mishi kenan.
Yace “to naji, shikenan. Ni dama na kula da cewa ba wani sona kike yi ba, son da nake miki yafi yawa!”.
Nayi murmushi kasa-kasa, da wata ce kam, zai iya samun damar cin galaba a kanta da irin wadannan maganganun har yayi amfani da wannan damar ya samu abinda yake bukata daga gareta, amma banda ni. A tsaye nake kyam! Akan duk wata kalma da na furta, ko abinda na kudurta a cikin raina.
Nace “duk abinda kayi tunani hakan ne, Umar”.
Ina jin dariyar daya saki mai sauti, wadda ta saka ni yin murmushi ba tare dana shirya ba. “Sweety na kenan! Shi yasa nake jin sonki kullum yana kara yaduwa a cikin sassan zuciyata wallahi. Amma yanzu Oga na ya shigo inda muke, zan kira ki anjima in shaa Allah, ok?”.
Na girgiza kai, “babu damuwa ai, sai anjiman”.
Nan muka yi sallama da juna, bayan ya manna min sumba ta jikin wayar. Kai kawai na girgiza, speechless, muka ajiye wayoyinmu.
Na sauke ajiyar zuciya tare da kurawa gadajen da patients suke kwanciya akai da suka kasance empty. Ban san lokacin dana dauka cikin tunani ba, sai da naji an dafa min kafada. Nayi firgigit! Na kalli gefen damana, Janan ce.
Murmushi na saki ina harararta cikin wasa, “wato tsabar shahara, yau sai karfe tara ma kika zo ko?”.
Tayi yar dariya, “to me yafi raina? Tunda an riga anzo anyi supervising dinmu, mun kuma yi presenting dinmu, ai babu abinda ya rage mana sai chilling. Yaya Bilal ne ma ya tsaida ni da jira, wai sai na jira shi ya karya sannan zai zo ya sauke ni. Kinsan na fada miki mun shirya dashi”.
Na gyada kai ina wasa da kan wayata, “yeah, haka kika ce. Yanzu idan muka gama ina kika nufa ne?”.
Tace “yo ni ina na sani? Watakila in tafi wajen Yaya Sa’a Funtua, ko kuma Kaduna wajen Umman mu. Ke fa?”.
Na harareta, “har wani tambayana ma kike yi? Bayan kin riga kin san komi?”.
Tace “to kizo muje wajen Umman mu mana kawai? Tunda dai ko kin je gidan ma ba wani jimawa zaki yi ba?”.
Nace “lallai ma, watanninmu kusan shida a makaranta fa, ban leka gida ko da wasa ba, kuma kinsan idan muka dawo hutu ma ba wani hutu zamu samu ba, gwara inje dai kawai”.
Ta kada kai gefe guda, “ai shikenan. In ka ki ji, ba zaka ki gani ba. Amma ai ba a goben zaki tafi ba dai ko?”.
Nace “a’ah, sai ranar assabar in Allah Ya kaimu”.
Kiran da daya daga cikin nurse din ta kwala mana, shine ya katse mana hirar da muke yi, muka tashi muka tafi wajen data kira mu.
Ranar ma karfe daya muka tashi. Janan ta sake ja na zuwa gidan Yaya Bilal, wai in taya ta hada kayan tafiya. Yau mun ci nasarar samun Anty Raheemah a gida. Tana zaune a falo sun kure kida ita da kannenta, wasu suna rawa, wasu kuma a zaune kawai suna kallonsu. Muka musu sannu da gida, suka amsa a kaikaice. Bamu kula su ba muka wuce dakin Janan abinmu.
Da yamma wajen karfe biyar, na mike ina rataya jakata. Janan ta shigo dakin hannunta rike da wasu ledoji biyu, tace “Yaya Bilal zai shiga Samaru yanzu, yace zai rage miki hanya”.
Na zaro ido, “what? No!! Kada ma ya wahalar da kanshi wallahi, zan bi bus kamar yadda na saba”.
Ta harareni, “jibe ta don Allah! To ya riga yace zai kaiki, yanzu haka yana jiranki ma a waje. Sauri yake yi, yau a gidan Anty Ameerah zai kwana, kuma dawowarshi daga Kaduna kenan, so yake yi yaje ya huta”.
Na dafe kai, “to menene na wahalar dashi akan cewa ya wani sauke ni a school? Da kin barshi yaje ya huta abinshi”.
Tace “sai kiyi kuma, tunda sabonki ne yin korafi. Yaya dai yana waje yana jiranki, idan kin tsaida shi, damuwar ki ce. Gashi Umma tace a kawo miki”.
Ta miko min daya daga cikin ledojin hannunta, na leka kaina cikin ledar. Turare ne, kayan biscuits da chocolates har da yan kunne da takalmi mai kyau. Umman su Janan tana yi min wani kallo ne kamar yadda take kallon Janan. ‘Diyarta, ‘ya kuma mafi soyuwa a gareta.
Duk wani abu da zata yiwa Janan, sai ta hada da ni. Ko ina nan, ko bana nan, ko ina sane, ko bana sane, zata bani da hannunta, ko ta bada a ajiye min.
Shi yasa nake matukar girmama matar. Ko ba don alkhairin da take yi min ba, don yadda take daukata kamar diyarta. Idan nayi wani abu da bai dace ba, zata kira ni ta zaunar dani, ta bani duk wata shawara da uwa ta gari ya dace ta bawa diyarta, ta tsaya daram, akan kafafunta, wajen dora ni akan hanya, duk da cewa bamu hada ko digon gumi ni da ita ba.
Ko a hakan kadai aka tsaya, wallahi ta gama min komi. Balle kuma ayi zancen irin alkhairanta a gareni.
Duk abinda zata yiwa Janan, ba ta taba bambanta mu, sai dai ko kala da tsayi.
Na kalleta ina murmushi, “Madallah da wannan sako, lallai Umma ta gano ni. Bari in koma sai in latsa mata kira inyi godiya. Na gode kwarai”.
Tayi dariya, “ai fa! Yanzu ke dai mu tafi, kada Yaya ya gaji da kira”.
Kamar yana ji, sai ga kiranshi ya shigo wayar. Ta daga tana ce mishi gamu nan fitowa, ban san me yake ce mata ba, na dai ji tana cewa “minti daya!”. Ta ja hannuna muka tafi.
Sai da na leka ta dakin Anty Raheemah muka mata sallama, sannan muka fita ni da Janan.
Yaya Bilal yana cikin motarshi a zaune, ya zuro kafarshi daya waje. Kyakkyawan takalmin D&G baki, budadde na fata yana ta sheki a kafar tashi. Na gaida shi kafin na zagaya ta daya gefen na shiga gefen mai zaman banza.
Janan ta leko tana min Allah ya kiyaye, yayin da Yaya ya tashi motar muka fita daga gidan.
Tafe muke a cikin motar, babu wanda yake furta uffan. Sai sautin wakar “earned it’ ta weekend dake tashi a nutse. A hankali nake bin wakar, ba lallai ka sani ba sai idan ka kalli bakina sosai, inda zaka ga yana motsawa kawai ba tare da sauti ya fita ba.
Idanuna suna ta tagar gefena suna kallon cikin garin Zaria. Na dinga jin alamun idanu a kaina, nasan cewa zargin hakan ne kawai nake yi a cikin raina. Da abin ya girmama, sai na juya a hankali cikin dabara, na kalli inda Yaya Bilal yake, idanunshi straight suna kallon gabanshi. Na girgiza kai, dama sai da nace zargine nake yi.
A kofar Bitmas Bakery naga yayi parking motar. Ya kashe tare da fita daga motar yana muttering “excuse me!”. Wanda ba don na juya a daidai lokacin idanuna sun sauka akan fuskarshi, na ga bakinshi ya motsa ba, ba zan ji mai yace ba.
Na zaro wayata a cikin jaka ina dubawa don in rage kadaicin zama.
Bayan kimanin mintuna biyar da fitarshi, naji an kwankwasa gilashin tagar motar, gefen inda nake zaune.
Na daga kai, naga Umar a gefen a tsaye.
Nayi murmushi tare da sauke gilashin kasa, “hey handsome, me kake yi anan?”.
Shima yayi murmushin, “wai mun tsaya ne zamu sayi fruits fa, ina jiyowa kuma sai na ganki. Daga ina?”.
Nace “daga gidansu Jan. Tare muke da Yaya Bilal, zai sauke ni a makaranta”.
Ya gyada kai, “uhmmn… Ya shirye-shiryen tafiya gida? Jibi zaki tafi ko?”. Nace “ehh!”.
Yana nan a tsaye muna hira, Yaya Bilal ya dawo. Kwata-kwata ban ga wucewar shi ba, sai da ya bude motar ya shigo. Na kalli Umar ina murmushi, “handsome, bari mu wuce ko?”.
Ya gyada kai, “Ok Sweety, zamu yi waya ko?”.
Na jinjina kai, “in shaa Allah. See you!”.
Har ya juya ya tafi, sai kuma ya juyo da sauri, “hey, bari in miko miki fruits”.
Na daga baki da niyar cewa na gode, Yaya Bilal ya katse ni ta hanyar yiwa motar key. Ya kalli Umar, “ta gode, sauri muke”. Da wannan yaja motar. Ina hango Umar ta cikin gilashi yana daga kafada.
A main gate na kalleshi nace “Yaya ko zaka ajiye ni anan kawai, sai in karasa ciki?”.
Yadda kasan bango, haka ya maida ni. Bai ma nuna alamun yaji abinda nace ba, sai ma ya karawa motar wuta ya shige ta cikin makarantar.
A bakin hostel ya samu waje yayi parking din motar, na fara yunkurin bude kofar ina jera mishi godiya,
“na gode Yaya, a gaida Anty Ameerah”.
Sai da na fita, ina kokarin maida kofar in rufe, naga yana miko min leda mai dauke da tambarin Bitmas, na kalleshi fuskata dauke da alamun tambaya, kafin inyi magana ya riga ni, “karbi mana, kina bata min lokaci!”.
Nasa hannu biyu na karba, nace “nagode, Allah Ya amfana”. Yace “Ameen” a kaikaice, yawa motarshi wuta ya kara gaba. Ni kuma na shige cikin hostel.
Sai bayan sallar magriba dana gama komi, na bude ledar. Bread ne da roll cake da suke yi a wajen guda biyu, da ice cream biyu shima. Na dauki daidaya na mikawa Ayla, tana ta min tsiya, wai “lallai yau Umar ya tuna damu!”. Dariya kawai na mata na koma gefe ina cin nawa. Sai da na gama ci sannan na tashi na hau hada kayan tafiya gida.
Bayan na gama, na turawa Baba sako akan cewa zan taho ranar Asabar, ya turo min kudin motar tafiya gida.
Washegari muka je asibiti muka yi bankwana dasu. Daga nan muka yi bankwana da Janan, itama ranar Lahdi zata tafi Kaduna wajen Umma. Ni da ita kuma sai idan mun dawo hutu.
Na dawo hostel na karasa shirya kayana, wadanda zan bari anan kuma na hade su waje daya tsaf na rufe da mayafai saboda kura. Na share waje na zauna ina jiran kudin mota.
NA’ILAH!
Mahaifana su duka biyun, asalin yan garin Gashua ne. Mahaifina, Alhaji Al-Hassan Hannafi, cikakken haifaffen garin Gashua ne. Iyayenshi hausa/fulanin dake cikin garin ne, duk da cewa sun rasu tun ma kafin a haifeni, sai sauran dangi na nesa-nesa kawai. Yayin da mahaifiyata, Yana, ta kasance ruwa biyu. Mahaifinta Barebari ne, mahaifiyarta kuma Shuwa Arab.
Kakana Bako Audu, shahararren malami ne, Kakata Fatima da muke kira da Fatsu, ta kasance mai sana’ar sake-saken kaya, a cewarta tun tana budurwa.
Mahaifiyata ta kasance kyakkyawar mata, fara, doguwa, mai dogon hanci da dogon gashi da dara-daran idanu masu tsari. Babu abinda ta bari na Fatsu. Allah Ya hore mata hakuri, Kawaici da kawar da kai. Aurenta da mahaifina ya kawo yar matsala a tsakanin danginsu ta fannin mahaifiyarta, su a sonsu ta auri dan uwanta ta fannin uwa, ko Barebari, amma ta kafe. Sai kuma matsalar rashin aiki, don a lokacin da suka yi aure, ya gama kammala degree dinshi akan banking and finance, amma bai samu aiki ba. Jajircewar Bako ce kawai tasa aka yi auren, suma kuma dangin nata suka hakura.
Bayan auren nasu da kadan, ya samu aiki da bankin GT, anan cikin Gashua din, ya fara zuwa aikinshi.
Yaya Mudatthir shine ‘Da na farko a wajen iyayenmu. Shekaru biyar cur ya bani.
Yawancin rayuwar yarintata a gaban su Fatsu da Bako nayi ta. Ba kamar Ya Mudatthir daya dauko kamanni da suffofi da halayen Mama kamar tayi kaki ta tofar, ni babu abinda na dauko nata sai yanayin idanuwanta da kuma dogon sassalkan bakin gashinta. Bayan haka, gabadayana Bako Audu ce. Ina da tsayi na daidai-wa-daida, da zubin halitta mai daukar hankali. Shi yasa bana shiga mai fitar da surar jiki. Kalar fatata baka ce, wasu kuma su kan ce wankan tarwada. Ko ma dai wace iri ce, ina jin dadi da alfahari da kalar fatata. Kalata mai sheki ce, sannan fatata mai taushi ce.
A halayen Mama kam, zan iya cewa tsafta da wasu halayen na dauko nata. Hakuri na kadan ne, sannan bana daukar wulakanci ko kadan, ko daga wajen waye kuwa. Bako ya kan ce shi duk cikin danginsu bai ga mai hali na ba, zafin kai, kafiya da taurin kai. Ina da rikakken ra’ayi, idan nace zan yi abu, to zanyi. Idan kuwa nace ba zan yi ba, mai canza min wannan magana kam sai ikon Allah.
Munyi zama mai dadi da iyayenmu, a dan abinda zan iya tunawa na rayuwarmu da wanda Mama ko Ya Mudatthir suke bani labari, Babanmu ya so mu, mutum ne mai son iyalanshi da kuma kyautata musu. Duk da cewa bashi da wani hali na azo a gani, amma rayuwarmu Alhamdulillah, babu abinda muka nema muka rasa.
Wannan kafin ya auro bakar ashana Ramata kenan. Lokacin da aka yi auren, Ya Mudatthir yana makarantar maza ta kwana a cikin Yobe. Ni kadai ce a cikin gidan, sai su Mama.
Tunda aka yi auren wannan, muka nemi walwala da kwanciyar hankalinmu muka rasa. Muka nemi Babanmu, Mama ta nemi mijinta, duk muka rasa. Rayuwar gidan ta koma kadaran-kadahan, yau daci gobe b’auri. Babu wani armashi. Ance wai ba’a kure mai hakuri, amma ni na gani akan idanu na, ranar da aka kure hakurin Mama a gidan nan, ranar da ta daga baki tace hakurinta ya kare.
Ranar ce Baba yasa belt ya zane mu ni da ita a tsakiyar gidanshi, akan naman kaji.
Ya kai mata nama ta soya, aka nemi naman a dakinta aka rasa. A cewarshi, satar nama take mishi idan ya kawo, dama kullum idan ya kai nama a soya sai ya ga babu wani bangare.
Mama tace “haba Malam, in rasa abinda zan daukar maka a gida sai nama? Tunda muke zaune da kai, na taba daukar maka abu ba tare da saninka ba?”.
Budar bakin amaryar Baba sai cewa tayi, “kenan kina nufin ni na dauki naman ko kuwa me?”.
Mama tace “ni ban ce ba, amma haka bai taba faruwa tsakanina da mijina ba, sai da kika zo!”.
Kawai ba sai mata ta dora hannu aka ba? Ta hau ihu, tana kururuwa, ita wallahi ba zata yarda ba, ance mata barauniya, zata bar wa Babanmu gida, sai yaci gaba da zama damu tunda yana zaune a gabanshi aka zageta bai ce komi ba.
Daga nan sai saukar duka kawai Mama taji, nayi tsalle na rungumota. Bai damu ba, ya hada mu mu duka ya mana lilis, kuka ranar haka muka shiga daki muka sha, babu mai lallashi.
Daga ranar dai bamu kara ganin nama a idanunmu ba, an haramta mana shi, duk wannan bai dameni ba, sai ganin an fiddo kwanon da Mama ta zuba naman da aka nema aka rasa daga dakin matar Baba, da tsakiyar ranar Allah Ta’ala. Babu kunya balle tsoron Allah. Wani karin abin haushi ma, da naje na yiwa Baba maganar, saboda Mama taki zuwa ta fada mishi, wai bata son wata rigimar ta sake tasowa, sai ya hau fadace-fadace, abinda na kira borin kunya.
Daga ranar muka kullata da ita. Ban kara ganin idanunta da kwalli ba, ban sake kallon kanta da gashi ba, ban kara mata magana cike da ladabi ko girmamawa ba.
Shekaru shida da karin auren da Baba yayi, shekaru uku da muka rasa walwalarmu. Muka yi rashin da har yau bamu samu mun cike wannan gurbi ba. Mama ta rasu wajen haihuwa. Nakuda ta kamata, cikin dake jikinta yana wata takwas da yan satika a lokacin, haka ta rasu, bata kai ga haihuwar abinda yake cikin nata ba, Allah ya karbi ranta. Munyi kuka, kuka ba kadan ba, Allah kadai yasan tashin hankalin da muka shiga ciki a lokacin.
Muna tsakiyar karbar ta’aziyar Mama, muna cikin wannan yanayi na jimami, tashin hankali da kunar zuciya, kwana biyu kenan da rasuwar mahaifiyata, har zuwa lokacin ina jin zafin rashinta kamar a lokacin ne hannunta ya silale daga cikin nawa, babu rai. Sai ga Ramata ta fito daga dakinta, taci kwalliya ta sha gyale sai zuba kamshi take yi, tana rike da hannun Aliyu dan data haifa dan kimanin shekaru biyu, Yayarshi Maryam mai kimanin shekaru biyar tana binta a baya. Babu wanda ta kalla a cikin yan karbar gaisuwa, ta tafi wajen bikin kanwarta. Da yake duk dai anan cikin unguwarmu suke dama, layi daya ne a tsakaninmu, muna iya jiyo sautin karar kidan da suka saka na biki kamar a tsakiyar gidanmu aka sa kayan.
Har yau dake motsi, matar nan bata yi min gaisuwar rasuwar Mama ba.
Har yau kuma, ina jin zafin hakan, sai dai idan ban kalleta ba.
Ita ta gwada min cewa kishiya ba karamar masifa bace, kuma kishiya, ba mutuniyar arziki bace, shi kanshi kishin, ba abu bane mai dadi. Na fara neman tsari da kishi irin nata, a ganina bashi da amfani. Da wannan tunanin, na girma na tashi.
Rayuwar dai gata nan sai godiyar Allah. Bayan yan gaisuwa sun watse, gida ya koma sai ni sai ita don Yaya ma ya koma makaranta saboda jarabawa, sai na kasa zama a gidan. Saboda haka na kwashi kayayyakina na koma wajen Fatsu. Na dauki lokaci mai tsayi a wajensu, kafin in koma gida.
Kafin in saba da sabuwar rayuwar wannan na jima.
Da rayuwa nayi mai dadi, ruwan wanka sai an kai min bandaki, abinci sai an zo ance min in ci, makaranta sai an zo an ce min in tafi, kayan makaranta sai an wanke an goge min. Amma yanzu wadannan duk sun zama tsohon tarihi. Abinci sai na je na nema, an wulakanta ni kamar ba gidan uba na ba. Kai sai da ta kai ta kawo, sai kannenta sun je gidan sun ci abinci, sannan za’a bani sauran inci.
Kullum ina hanyar gidan su Bako, cin abinci, kullum. Na fadawa Baba ya fi sau shurin masaki, ko maganar bai taba mata ba. Ni kuma na gaji.
Idan nace ta bani abinci ta ki, sai in shiga har kuryar dakinta in zubo abina. Idan Baba ya dawo ta fada mishi, inyi kyar da idanu ince hana ni tayi, baya da yadda zai yi dani.
Cikin haka Yaya ya dawo gida. Gabadaya taso ta maida mu yan aiki a tsakiyar gidannan. Kayan fitsari da kashin Aliyu da nata har ma dana Maryam haka zata libgo mana su tace mu wanke, Yaya ne yake zama yayi aikin wankin nan, watarana yana gamawa ma zata ce sai ya sake wai bai yi ba. Idan nace ya daina mata, sai yace wai ai bamu da yadda zamu yi, matsayin mahaifiyarmu take. Sai inyi tsaki in ce Allah ya kiyaye. Kuma fa kada ku ce hakan shi yake hana ta zage mu, ko kadan. Haka kawai zata hau zaginmu, watarana ma haka har sunan Mama zata kira ta kare mata zagi, a gabanmu kuma.
Da naga ya matsa kuma ya ki saurarena, sai na kyale shi yake ta mata aikace-aikacen. Ni dai na ki. Koda ya koma makaranta, idan ma ta kawo kayan wankin sai in tsere abina, watarana ma fakat zan ce ba zan yi ba. Idan an gayawa Baba naki yin aiki, ince yankewa nayi, ko yatsa ta take ciwo, ko kuma wani abu dai. Na dai zame mata karfen kafa kiri-kiri kamar yadda nima ta zame min. Koda wasa ban bari ta juya ni ba.
Wannan yana daya daga cikin manyan dalilan da yasa kullum nayi sallah sai na daga hannuna sama na roki Allah Ya kareni daga sharrin kishiya. Allah ya kiyaye ni da haduwa da ita a gidan aure.
A cikin haka aka wa Baba kari da kuma canjin wajen aiki. Dama lokaci zuwa lokaci ana mishi canjin wajen ayyuka, amma kuma ba mai nisa bane. Wannan karon Katsina aka kaishi. Saboda haka muka fara shirin kaura zuwa Katsina. Yaya yana ajinshi na karshe lokacin a sakandire, don haka aka barshi a can. Ni kuwa da nake aji daya, aka min canjin makaranta zuwa Ulul-Albab.
Babu yadda banyi ba akan a barni a gaban su Bako, fir Baba ya ki. Ranar da za’a tafi din kam da kuka muka rabu. Da kyar aka tura ni cikin motar da Baba yayi shata ta kwashe mu zuwa Katsina.
Mun dauki lokuta kafin mu saba da yanayin sabon garin da muka je. Musamman gari inda babu dangin Uwa balle na Uba kuma ko abokai, yana da wahalar sabo, amma a hakan dai muka zauna muka fara sabawa dasu din. Anan kusa da inda muka koma, wata Ummu-Kulsum, itama kimanin shekaru na ce, mun fara sabawa da ita da mutanen gidansu nake jin labarin itama a Ulul-Albab din take, nan na makale mata sosai. Nan da nan abota ta kullu a tsakaninmu. Ya zamana na gwammace in yini cur a gidansu maimakon inyi gidanmu, saboda idan ma na zauna a gidan me zanyi? Habaici ne nake sha da bakar magana, sai kace ni ce kishiyar ta ba diyar kishiyarta ba.
Da na samu ma baba ya sai min form din islamiyar da Kulsum take zuwa shikenan, sai muka kara gamewa da ita.
Suna kare hutunsu na bita muka tafi. Duk da ba wasu kayan azo a gani aka hada min ba, naji dadin dan abinda yayi din, ban raina ba. Allah Ya taimakeni term daya kadai nayi missing, dana maida hankalina kan karatuna sosai, tuni na wuce aji biyu.
Mun koma gida hutu, na tarda amarya Alawiyya a gida. Abin ya bani mamaki, ko kadan ban ji labarin auren ba, wanda a yadda ake fada min, kusan watanta uku kenan a gidan.
Kodayake, daga bakin wa ma zan ji labarin? Tunda aka kaini aka ajiye a makarantar, ban kara ganin kowa ba. Ni da visiting dama sai in su Inna – mahaifiyar Kulsum sun je, sannan nake ganin na gida. Ni da Baba dama sai dai in ina bukatar wani abu, in ari wayar wani malami in kira shi in fada mishi. A hakan ma sai ya dauki lokacin shi kafin ya turo abinda zai turo din, kudi ne ko kuma abin bukata. Watarana kuma sai dai ya ba su Inna su kawo min kam.
Na sha shigewa bandaki in shaki kukana, ko kuma in haye can kan gadona in yi kukan. Abin yana da matukar cin rai da ban takaici, na rasa dalilin da yasa ni hakan take faruwa dani. A kaika makarantar kwana na wata da watanni amma ka rasa naka wanda zai leko ka ko da wasa? Rashin uwa ne ya janyo haka ko kuma rashin dangi? Saboda na tabbata cewa da a gaban su Bako nake, da lallai sai na ma gaji da ganin dangina. A hakan nake ta cijewa ina danne komi a cikin raina, har muka koma gida hutu.
Amarya ko in ce bazawara Alawiyya ta shiga da rawar kai da jiji da kai, sai dai bai je ko’ina ba ya sauka. Saboda Ramata ba kanwar lasa bace ba. Zama a gabansu sai ya zama kamar zama da wasu kishiyoyi ne, suka sako ni a gaba. Ni abin yana bani mamaki, ban tsarewa kowa komi ba, amma ni kuma ace na tsare? Shima din taso taga tayi dani, taga dai daga ita har Ramata din na jefa su a kwandon shara, sai ta saddakar, ta koma kan Ramata din.
Matsala ta farko a cikin wannan gida, ita ce rashin adalci. It was obvious Baba yafi son Ramata akan Alawiyya, zata iya yiwuwa so ne na tsakani da Allah, ko kuma wanda ta nemo a wajen malamai da yan tsibbu, koma dai wannene, amma kuma bai san ta yadda zai daidaita ko ya boye son nata ba domin samun adalci a cikin iyalansa, hakan yasa a kowane abu ne sai ya fifitata akan Alawiyya da ‘ya’yansu. Ita da ‘ya’yanta sun fi kowa kima da mutunci a idanun Baba.
A hakan ma kuma bata bar Alawiyya din ta zauna ba, ta hana ta zama lafiya da mijinta, ta hana ta sana’a. Kudi duk yawansu idan ta tarki sana’a dasu, zasu kare ne kafin a je ko’ina. Wani abu ne da naji suna kira wai ‘mai rariya’, duk yawan kudin da zasu shiga hannun mutum to zasu koma kamar an cinna musu wuta, nan da nan zasu kare ka rasa ta inda suka shiga. Abubuwa ne da ni na sha gani da idanuna. Wani lokaci na tashi cikin dare zan yi sallah inji ana kurumtu ko a bayan dakin Baba ko na Alawiyya, watarana shara zan shiga yi a dakin Baba in ga kulli-kulli na magani ko dami na layu da dai tarkace a lungu da sako na dakin, sai dai in daukesu in shiga wajen su Inna in kona su.
Bazamar da Alawiyya tayi wajen malaman Allah da Annabi domin neman kariya da kuma karyewar abubuwan dake kanta, itama ta fada cikin taskun bin malamai da yan tsibbun har ma da yan bori. Wannan masifa dana gani da idanu na, ta tsorata ni fiye da tunani na.
Duk sallar duniya idan nayi, sai na roki Allah ya raba ni da zama da kishiya. Ya zamana tunanin zama da kishiya kadai kan sa inji kamar zuciyata zata rabe biyu. A zamanin budurcina, saurayi yana zuwa daya, tambaya daya ce: kana da ra’ayin zama da mata biyu nan gaba? Idan yace eh, to sai in ce Allah ya kiyaye hanya tun ma kafin tafiya tayi nisa. To da yake ma ba kula samarin nake yi ba, saboda a lokacin hankalina yana kan in gama sakandire da sakamako mai kyau, in samu in shiga jami’a.
Allah Ya taimakeni sosai, gabadaya jarabobina na waec da neco suka yi matukar kyawu, sai dai kasancewar banyi jamb ba, -a cewar Baba in bari sai sakamakon jarabawar ya fita sannan-, yasa da Baban su Kulsum ya tashi sai mata form din makarantar SBRS, kasancewar ita bata ci jamb ba, yasa na roke shi akan ya nusar da Baba nima ya sai min. Allah Ya taimaka ya siya min, muka samu admission muka tafi.
*☆⋆03⋆☆*
A SBRS muka hadu da Janan. Haduwa irin ta wajen registration, daga tambayar zuwa wajen signing, sai kuma muka ji cewa ai duk dakinmu daya, nan muka hade. Ita Janan wanda yake auren Yayarta shine ya mata hanyar zuwa can, a lokacin shine DG din makarantar ma. Amma da yake irin mutane ko in ce iyayen nan ne na da, bai barta ta zauna a gida ta huta ba, da kanta tayi komi na registration.
Kasancewarmu a daki daya yasa zumuntarmu gaba daya tayi karfi. Yayarta, Anty Sa’a anan cikin makarantar suke zaune ita da maigidanta da ‘ya’yansu, duk da cewa suna da gida a Zaria, amma bata taba zuwa can ta kwana ba, wani abu da Anty Sa’a din da maigidanta suka ce wai zai sa ta dinga slacking akan karatunta.
Abotarmu tasa muka saba da danginsu sosai, har ma watarana Yayansu Bilal yazo ya daukar mana excuse, ya daukemu zuwa can gida Kaduna lokacin da aka yi bikinshi da Anty Ameerah. Yan’uwansu mutane ne masu mutunci kwarai, karimci da kyautatawa, jininmu ya hadu dasu sosai. Wannan shine ganina da Yaya Bilal na farko.
Mun gama makarantar da sakamako mai kyau, amma ba wanda zai shigar damu jami’ar Ahmadu Bello ba. Da yake Remedial Studies ne muka yi, idan Allah ya taimakeka ka fitar da sakamakon da ake so, za’a baka gurbin karatu a jami’ar Ahmadu Bello, matakin karatu na aji biyu, to mu Allah bai kaddara zamu samu ba. Amma mun sake rubuta jamb, mun kuma samu sakamako mai kyau both a jamb da kuma post-utme. Cikin ikon Allah duk suka bamu course din da muke so, nursing.
Nan muka koma gida muka fara shirin tafiya. Sai da muka tsaya aka yi bikin Kulsum. Kasancewar wanda zata aura ya dage akan yana bukatar ayi aurensu, yasa aka daura musu auren, da sharadin zata nemi gurbin karatu anan Umyuk, kuma zai barta tayi, yace ya amince.
Bayan bikin, muka je muka yi registration. Na koma gida na kara kimtsawa na sati daya, na tafi makaranta.
Mun shiga aji na uku muka hadu da Umar, ya raka kanwarshi registration lokacin. Shi NDA ta Kaduna yayi, ya samu ya gama, ya fara posting dinshi kenan muka hadu. Allah Ya taimake shi yana da hanya, shi yasa suka barshi a nan Zaria basu jefa shi waje mai nisa ba.
Babu bata lokaci muka fara soyayya ni da shi. A duk tsayin rayuwata, wannan shine karo na farko da na tsaya nayi wata soyayya da wani da namiji, ban taba ba kaina wannan damar ba.
Lokacin da ina gida da, na fara tsayawa da wasu. Sai dai, ban san dalili ba, duk wasu kalamai na so da zan ji sun fita daga bakinsu, sai inji ina karyata hakan. Wannan dalili yasa zancen ma baya yin nisa, ake watsewa. Daga karshe dai na fahimci cewa ban yarda da soyayyar bane. Duk lokacin da zan ji wani ya ambaci true love, to zan ce maka bata existing sai cikin littafan novels da fina-finai. Janan ta kan ce saboda ban samu wanda raina ya kwanta dashi bane, ko kuma ina jin tsoron commitment ne. Koma dai wannene, ban damu ba.
Shi kanshi Umar din, lokacin dana fara amincewa dashi, ba so bane, it was more like burgewa ko kuma abokantaka. A lokacin I was in a desperate situation, you know irin lokutan nan da zaka ji kana bukatar wani a kusa da kai, bayan abokai da yan uwa of course, sai kuma ya kasance na samu duk wani abu da ake bukata a wajen namiji a tattare dashi Tattali,kulawa da saukin kai. Irin free-spirited mutanen nan ne, duk inda zaku zauna dashi, in shaa Allah zaka ji ya shiga ranka. Sai dai rawar kai da ba’a rasa samarin yanzu da ita, wanda shima sai da muka yi nisa da haduwa dashi sannan na fara karantar hakan, amma nasan cewa lokaci ne, zai daina, tunda ina matukar yin kokari wajen ganin cewa duk lokacin da yayi kokarin yi min maganar banza na dakatar dashi. Hakan yasa lokuta da dama zamu yi fada burum-burum dashi, daga baya dai zai sake dawowa mu shirya.
Bayan wannan sai kuma daga baya da naji na zama very comfortable a tare dashi, ba kamar sauran samarin da nayi a baya ba. Ina jin shi kamar Janan, yadda zan zauna inyi hira da ita babu wani boye-boye, shima haka zan zauna inyi hira dashi. To ko bana son shi, a ganina wannan kadai ai zai ishi rayuwar aurenmu ko? Tunda mun fahimci juna sosai. Balle ma ina son shi. Duk da cewa maganar aurena dashi tana sa inji wani unsettling abu a cikina. Kodayake, har yau bai ma fara zancen auren namu ba, nafi tsammanin kila sai bayan mun gama karatu sannan, and I’m totally fine with that.
Shekararmu ta farko a makaranta babu sauki, yanayin karatunsu mai zafi ne, duk da cewa mun yi wanda yaci uban wannan a SBRS, still, yana mana wahala. Ni a cikin hostel din makaranta na zauna. Yayin da Janan take zaune tare da matar Yaya Bilal anan cikin samaru.
Yaya Bilal yana aiki da kamfanin jaridar daily trust ne. Kasancewar kamfanin yana Abuja ne, yasa yake tafiya can duk ranar lahdi da yamma ko litinin da safe, ya dawo ranar Juma’ah da yamma. Ban san dalilin da yasa bai tafi da amaryar shi ba, tunda naji Janan tace yana da gida acan Abujar. Ban kuma taba tambayarta ba koda wasa. Daga bakinta dai naji tace ashe ma gidan da suke zaune, mahaifin Ameerah ne ya sai musu gidan. Duk da abin ya daure min kai, ban tambayeta dalili ba shima.
Na sha jin korafin bata jin dadin zama da matar Yaya, ban taba fahimtar dalili ba sai da watarana daya da muka je gidan.
Muna cikin shirye-shiryen exams ne, Janan ta saba shigowa makarantar a ranakun weekends, muje library mu yi karatu. Ranar tana zuwa, Yaya Bilal ya kirata yana tambayar tana ina, ta fada mishi. Ba’a jima ba sai gashi yazo, ashe Anty Ameerah ce bata jin dadi, yace zai je ya dauko family doctor din su Ameerah din, muje mu tayata zama kafin ya dawo, a karo na barkatai, naji lamarin nasu ya daure min kai. Nan dai muka tarkata muka tafi.
A kofar gidan ya ajiye mu ko ciki bai shiga ba, ya juya, mu kuma muka shiga ciki. Gidan nasu dan madaidaici, mai kyau. A kalla mun dauki fiye da mintuna goma sha biyar muna doka kararrawar sanar da zuwan bako gidan. Ina tunanin ba wanda yake cikin gidan ba, hatta da wanda yake makotaka dasu, yaji wannan bugu da muka dinga yi. Yadda Janan tayi, very calm and collected, babu alamun wata damuwa a tattare da ita, yasa na gane cewa wannan ba shine karo na farko da irin haka ta faru ba.
Sai da aka kara kusan mintuna biyar sannan naji motsin taba kofa, aka bude kofar falau, cikin sanyin jiki duk muka shiga cikin falon. Ance wai shimfidar fuska tafi ta tabarma, duk da irin kayan alatun da suke cikin falon, hakan bai sa naji ni very welcomed ba a gidan. Ba’a bamu wajen zama ba, babu sannu da zuwa balle ga ruwan sha, haka aka barmu tsaye a tsakiyar falon dakin. Sai Janan ce ta min nuni da kujera, tace in zauna bari taje ta dauko min ruwa. Jiki a sanyaye na lalubi kujera na zauna, cikin nuna girmamawa na gaidata. Sai data gama shan kamshi sannan ta amsa, ya saukin jikin dana mata ma Allah bai bata ikon amsawa ba. Dama na gama shaka da ita, daga nan nima na maida kaina cikin wayata na cigaba da karatuna. A zuciyata kuma cike da mamakin wannan mata. Ita ba wata babba ba, saboda daga ganinta shekarun data bamu kadan ne, ita ba wata dangin sarauta ba balle ince ko jinin sarauta ne a jikinta, amma kice dole sai kin shimfida mulki? Duk da cewa yes, tana da kyawu Masha Allah, kuma daga yadda naji, mahaifinta mashahurin mai kudi ne, kila hakan ne yasa take dagawa. Na girgiza kai kawai.
Ko kallon ruwan da Janan ta kawo min ban yi ba, Allah-Allah nake Yaya Bilal ya dawo, in narko wani excuse din in karawa bujena iska don ba zan iya zama a haka ba Allah ya sani.
Muna zaune mu duka ukun, babu wanda yake cewa wani ci kanka, har rana ta daga sosai babu alamun Yaya. Gashi ko TV ba’a kunna ba a falon balle mu ce zata dauke mana hankali. Gabadaya naji na takura, ban iya dogon zama irin haka babu hira ko wani abu to discuss ba. Rawar kai na da tsokanata basa barina zama waje daya.
Janan ce ta katse dogon shirun daya mamaye dakin ta hanyar tambayar ta, ‘Anty ko za’a dora abinci yanzu ne?’.
Budar bakinta sai cewa tayi, ‘daga gida za’a kawo mata abinci yau, bata son jin kamshin gas ko risho’, da dai na samu na hana kaina daga kama baki in ce to?!, sai na bame bakina na kara tura kaina cikin wayata.
Allah ya taimakemu Yaya ya zabi daidai wannan lokacin ya fado falon kamar an jefo shi daga sama.
Tayi tsalle ta afka jikinshi, mu da muka dago da niyar yi mishi sannu da zuwa sai kasa muka yi da kanmu a rikice saboda ta’asar dake gudana. To ta’asa mana! Ba kullum bane kake ganin irin wannan ‘intimate moment’ a gabanka ba. Sai daya gama tsotse mata baki da fuska, sannan muka jiyo alamun tashin muryarsu kasa-kasa, hakuri ya dinga bata kan cewa bai samu ganin likitan nasu ba, kuma har gidanshi yaje, amma ko zata daure su tafi asibiti yanzu? Ta wani lankwashe murya kamar wata yarinya karama, tana cewa ai ita so tayi ya zauna kusa da ita kawai, bata wani bukatar likita.
Nayi kokari na danne dariyar data kusa kamo ni, irin wadannan ‘cheesy lines’ din ai nayi zaton a films kadai suke amfani da novels, ba a ainihin rayuwarmu ba.
Yaya ko kallon mu bai kara yi ba, ya dai jefo mana “ku zauna ku jira ni, ina zuwa!”, bai jira jin ta bakinmu ba, ya ciccibi amaryarshi suka shige daki. Na kama baki na bi bayansu da kallo, a zuciyata ina kara tausayawa Janan. Idan har haka ake treating dinta a gidan Yayanta, Allah kadai yasan halin da take ciki gaskiya.
Ta ja ni zuwa dakinta inda yake can cikin falon, can karshe kusa da wani karamin daki da suka mayar dashi kamar store. A gefen katifa duk muka zauna, na titsiyeta sai data bani labarin abinda yake faruwa a gidan, tun daga farko har karshe.
Matar Yayanta irin matannan ne da idan Allah ya hada ka kishi dasu, taka ta kare. Babu boka babu malam, zasu dafa ka cikin ruwan sanyi ka kankare. Irin matannan ne masu dan banzan kissa.
Tace a bayan idon Yaya Bilal, ita, Janan din da sauran dangin shi har ma da Ummansu, basu maraba da kayan wanki a wajenta, amma idan a gabanshi ne sai tayi ta tattalinsu tana ririta su.
Ameerah irin sangartattun yaran masu kudin nan ne. A wannan shekarar ta gama karatunta. Bata aikin komi a gidan wannan sai zama, kallo da nanikewa miji. Tana da yan aiki kala-kala, don ma dai ba kwana suke yi a gidan ba. Da masu girki, masu sharar waje, masu wanki, har da masu gyaran daki, kuma duk mahaifinta yake biyansu. Tace yanzu haka garar da aka kawota da ita tana cike da store, ko alamun tabata ba ayi ba, saboda bata yin girki. Watarana ma daga gidansu takanas ake dafo abincin a kawo mata. Kai hatta da wutar amfani wannan ta gidan, mahaifinta ne yake biya. Yayan yayi magana game da hakan, amma mahaifanta suka nuna duk cikin son da suke yiwa diyarsu ne.
Tunda Janan taje gidan, take gasa mata aya a tafin hannu cikin ruwan sanyi. Bata da bakin korafi saboda koda wasa bata bar hanyar da Yaya zai yi suspecting dinta ba. Spare makullin gidan da Yaya ya bata, ta amshe, kullum sai ta buga mata gida idan ta dawo daga makaranta, kuma sai ta wulakantata kafin ta bude mata gidan, store din abinci a kulle yake, wani lokacin sai dai ta saka kudinta ta sayi abinci. Idan Yaya baya gidan to ita da babu duk daya suke, duk kokarin Janan akan su daidaita abin yaci tura. Ita cewa ma tayi gwanda ace fada suke yi akan wannan zaman doya da manja din.
Ita kuma tayi-tayi dashi akan ya bari ta koma wajen Anty Sa’a tunda suna Zaria yanzu, ko basa nan akwai kanwar mijinta da suke zaune tare a gidan sai ta zauna dasu, ko kuma ya kama mata gida a samaru, ko ma dai a ina ne, amma yayi fir ya ki. Ita kuma bata so ta takura mishi da maganar kada yace ko bata son zama da matar shi ne ko wani abu.
Sai a ranar naji cewa ashe ba mahaifinsu daya da Yaya Bilal ba. Mahaifinsu Yayan ya jima da rasuwa, bayan nan ne ta auri wani mutum a Kaduna, shine mahaifin Janan din. Sai lokacin na fahimci komi, ina ta mamakin dalilin da yasa Ummarsu take zaune a Kaduna bayan duk danginsu suna Zaria, nayi zaton ko aikine ya kai baban su Janan din Kaduna. Amma nayi mamaki, koda wasa basu taba nuna mata banbanci ba, ita ko su Harira diyar kishiyar Umma, basu taba nuna mata wani ki ko kyama ba.
Janan kuka take yi sosai lokacin da take bani labarin wannan, na rungumeta ina bata hakuri, don shine kadai abinda zan iya yi a lokacin, har ta gama kukan. Daga nan muka fito da littafanmu muka cigaba da karatu har aka kira sallah muka tashi muka yi, muka koma muka cigaba da karatunmu. Muna nan sai ga Anty Ameerah ta leko, tace muje mu debi abinci, Janan ta fita zata zubo mana abincin, sai gata ta dawo wai Yayan yace muje muci tare dasu. Tace haka yake, in dai yana gidan tare suke cin abinci. Na dauki hijabita na saka muka fita.
A falon sai na daga baki ina kallon ikon Allah, gabadaya mata ta rikide, ta koma kamar wata salihar kirki, kamar ba wannan matar da take amsa mana magana da dai-daya ba.
Sai nan-nan take yi damu, abinci kamar zata zuba mana a baki yadda take ta turo mana plates na varieties din abinci gaban mu. Tsabar mamaki ma ni kasa yin magana nayi. Lallai an saka Janan a cikin tsaka mai wuya. Idan har haka take mata, to lallai kuwa babu wanda zai yarda da cewa idan an saka mata yatsa a baki zata ciza, sai dai idan har tayi hakan a gabanka.
Muna gama cin abincin muka koma daki. Muna shiga na fara zuba magana, tsananin mamakin matar ya hana ni hada maganganu masu ma’ana ma, Janan sai gefe ta koma tana min dariya. Sai dana nutsu sannan na iya zama muka yi magana akan haka da ita.
Sai bayan sallar la’asar can, sannan na mike ganin cewa Yaya bashi da niyar barin gidan. Janan tayi-tayi dani akan in tsaya Yaya ya fito, nace mata ina da abubuwan yi ne a hostel, dole ta kyaleni na tafi.
Daga wannan rana ban kara taka kafata zuwa gidan Yaya Bilal ba har yau.
Karatunmu yaci gaba da tafiya cikin nasara. Ni da Janan duk bamu dauki karatunmu da wasa ba, duk da bamu yin topping, amma dai Alhamdulillah, babu abinda ya taba dawo mana.
Muna shekarar mu ta uku, Yaya ya sake yin wani auren, ya auro Anty Raheemah. Yadda ya rikice akan wannan auren, yasa na kara tsurewa da lamarin maza. Lokacin bikinsu da Anty Ameerah yadda yake ta rawar kai da zakewa, kai sai kayi zaton babu wata ‘ya mace da zata sake yin daraja ko kuma a idonshi bayan ita, sai gashi tun ba aje ko’ina ba ya karo wani auren.
Janan tace ba karamin rikici suka yi da matar Yayan ba, har ta kai ga cewa ya fita ya bar mata gida, inda abin ya yiwa Yaya ciwo matuka. Ya karasa gyara gidan gadonsu, dama can ya fara gyarawa zai kai Ameerah din, iyayenta suka hana.
An dai yi biki lafiya, despite tashe-tashen hankulan da aka sha, amarya ta tare a gidan mijinta, Janan ma tayi kaura can.
Muna ta murna, a tunaninmu wannan zamu tafi da ita, tunda sa’ar mu ce ita, ashe yaudarar kanmu muke yi.
Raheemah da kannenta irin ‘ya’yan mace dinnan ne. Zaku yi mamaki idan kuka ji cewa suna da uba da yake raye, kuma auren iyayensu yana nan, amma suna zaune separately. Duniya da son abin duniya ya rufe musu ido daga su har uwarsu, mahaifinsu kuwa mutum ne mai wadatar zuciya da tsoron Allah.
Tun yarintarsu, bin bokaye da malamai shine amsar tambayarsu da komi nasu. Kodayake, wanene a garin Zaria bai san da zaman Hajja Ladidi ba? Shi yasa tashin farko da naji wai Yaya zai auri daya daga cikin diyanta, abin ya bani mamaki kwarai. Sam ire-iren su ba irin wadanda yaya yake hulda dasu bane.
Kannen Raheemah biyu da suka tare a gidan su suke kara rura wutar dake cikin gidan Yaya Bilal. Su duka biyun suna karatu a jami’ar Kongo. Saboda haka suka baro gidansu dake Hanwa, suka koma can saboda ya fi kusa da makaranta. Duk da a zahirin gaskiya ba hakan bane. Haleemo da Salama sune yan kanzagin ta, sune masu zuwa garuruwa da kauyuka amso mata magunguna wajen malamai da yan tsubbu yayin da take gida ta mike kafa.
Sai da na yiwa Janan fatan dama a wajen Anty Ameerah ta zauna, tace mugun fata nake mata. A cewarta zama dasu Haleemo, duk da gallazawar da suke mata, yafi mata sau dubu akan zama da Ameerah. Don haka na kawo idanu na zuba mata. Don haka ban taba ganin laifinta ba don tana zuwa wajen Umma weekend ba duk karshen sati, watarana ma nima ina binta.
To da yake ita rayuwa babu abinda hakuri baya maka, gashi yanzu har zamu shiga shekararmu ta karshe, ko ma in ce mun shiga. Duk da har yanzu dai babu abinda ya canza, sai ma karuwa da yake yi. Tun basa cin karfin Yaya akan Janan, har suka zo suka ci galaba a kanshi. Wasu lokutan haka zai birkice mata kamar ba Yayan nan nata mai son ta ba, sau tari sai dai ta kira ni tayi ta kuka, ni kam sai dai inyi ta bata hakuri. Rabin abubuwan da ake mata a gidan nan, ko Ummarsu bata sani ba, tunda duk cikin danginsu babu mai zuwa gidan balle yaga halin da take ciki.
Shi kanshi Yaya din, yau da gobe ce tasa ya gane tana zaman gallazawa a gidanshi. Sai ma watarana da yazo ya tadda Sa’adiya wadda suke cewa Adi, kawar Raheemah din da take zaune a gidan, tana ta zagin Janan akan wai bata yi mopping din falo ba, ran Yaya ya baci matuka, ya tara su su duka ya ja musu kunne, kuma yace daga ranar duk wadda ta sake taba mishi kanwa a gidannan, sai ta bar mishi gida. Aikin gidan ma kuma daga ranar ya hana ta yi, ita ce dai taga dama taci gaba da yi, tunda kunnen kashi gareta. Duk yadda nayi da ita akan ta bari tunda yace ta bari din, kiyawa tayi. Don haka na zuba mata ido, ni dai nasan da ni ce, da zuwa yanzu su duka sun bar gidan.
To rayuwar dai haka ake yinta, yau dadi, gobe madaci, gashi yanzu wasu abubuwan sun zama sai dai a tarihi. Nan da lokaci kadan ma, zata bar musu gidan.
*
*☆⋆04⋆☆*
* ☆ *
Har washegari Lahdi ina jiran Baba ya turo min kudin mota, amma shiru kake ji, kamar an shuka dusa.
Na duba agogon dake daure a tsintsiyar hannuna, naga cewa karfe goma sha daya na safe ta wuce. Nayi kwafa. Wani text din na sake tura mishi. Sai can wajen karfe sha biyu da rabi naji karan shigowar text, na duba naga shine ya turo min kudin motar, nayi kokarin resisting takaicin daya tuko ni, zuciyata na tunatar dani gida za ni ba wani waje ba.
Sai da nayi sallah sannan muka yi sallama da Aylah cike da kewa. Ina shirin fita kiran Umar ya shigo wayata, ya sanar dani yana waje yana jira na, don haka na ciccibi akwatuna na fita.
Ya saka akwatin a bayan booth, ni kuma na bude gidan gaba na shiga. Ya shigo motar ya tashe ta. Sai daya tsaya a banki na ciri kudi, sannan muka tafi. Har tashar mota ya kaini. Sai daya biya min kudin mota, sannan ya min sallama. Na mishi godiya sosai. Allah ya taimakeni motar ta kusa cika, ba’a jima ba muka dauki hanyar Katsina.
*
Karfe biyar na yamma a cikin garin Katsina ta mana. Motar tayi karan karshe a cikin tasha, a gajiye na fito daga motar ina mika. Na rataya jakata a kafada tare da daukar dan madaidaicin trolley din dana sako kayan da zan bukata na fita daga tasha din. Shatar adaidata nayi har unguwar Magama inda gidanmu yake.
Madaidaicin gidane daidai masu rufin asiri. Na fita daga cikin adaidaita din bayan na biya shi kudin shi. Wasu daga cikin yaran gidan dake kofar gida suna wasa suka bazamo da gudu suna ihun min oyoyo, nayi dariya ina dukawa kasa yadda zasu ji dadin rungumeni sosai. Abbakar ya dauki trolley na, yayin da Auwal ya rike jakar hannuna, na kama hannun Mufeedah muka shiga gidan.
Matan gidan suna zaune a tsakar gida, Anty Alawiyya na dura kunun aya da take yi na sayarwa a cikin gororin ruwa, Anty Ramata kuma tana kofar kicin a zaune, ina zaton ita take da girki yau.
Duk suka saurara da abinda suke yi jin hayaniyar yara har muka shiga cikin gidan. Anty Alawiyya ce ta mike tana dan murmushi, “mutanen Zaria ne yau a garin? Ai bamu ji labarin zaki zo ba koda wasa!”.
Nayi murmushin yake, dama a ina zasu ji? Na san koda wasa Baba ba zai fada musu ba. Ni kuwa dama ba waya muke yi dasu sosai ba, tunda na fara makaranta, babu wadda ta taba daga waya ta kira ni da sunan mu gaisa, sai nice idan naga an kwashi kwanaki nake kiransu haka nan dai, musamman ma don mu gaisa da yara. Kullum idan na dawo daga makaranta zancen daya, ne babu wani canji.
Na sauke Mufeedah kasa tare da gaidasu daya bayan daya, suka amsa fuska babu yabo babu fallasa, na tabe baki tare da ciccibar akwatuna na tunkari dakin daya kasance nawa tunda muka dawo Katsina.
Na ja nayi turus, sakamakon ganin kofar dakin a bude, abin ya bani mamaki. Na tabbata da zan tafi makaranta sai da na saka kwado na rufe kofar dakin, kuma ban bar dan makullin a gida ba. Babu wanda yayi tunanin yi min karin bayanin abinda yake faruwa, don haka na tura kofar dakin.
Abu na farko daya fara min sallama shine tarin kayana da aka hade waje guda acan karshen lungu, akwatuna daya kan daya, kwalaye bisa kwalaye, yayin da ilahirin tsakiyar dakin yake shake da tarkacen kayan Maryam. Na juya na kalli Saudah yar autar Anty Ramata dake zaune a kofar dakin mamanta dake kusa da dakin da nake, nace mata “waye yake kwana a dakina?”.
Tace “Anty Maryam ce, Mama tace ta koma dakinki tunda kullum a kulle yake kuma tayi girma da zama a dakinta”.
Nayi kwafa ina kallon Uwarta ta, nace “shine saboda tsabar bani da muhimmanci babu wanda yayi tunanin sanar dani?”. Duk suka yi tsuru su biyun. Na sake yin kwafa tare da shiga cikin dakin. Ko karewa dakin kallo ban yi ba naje na dauro alwala na dawo dakin nayi sallah. Sai dana gama sannan na kira Umar na sanar dashi sauka ta, yayi min sannu da zuwa. Bayan nan na kira Janan itama muka gaisa, tana dariya tace “bana miki wayo, ni tun safe ina gaban Ummana!”.
Nayi yar dariya, “ya miki kyau ai, Allah ne ma yasa motar tayi gudu sosai, kila da sai magriba zan iso ni kam”.
Mun dan yi hira kadan da ita, har ta bani Umma muka gaisa, sannan muka yi sallama da ita.
Tashi nayi na fara gyara kayana da aka wulakanta a dakin, ina maida su ainihin wajen da suke da. Kafin a kira sallar magriba na kammala gyarasu tas. Nayi sallah, na zauna akan abin sallar nayi karatu kamar yadda na saba har aka kira isha’i nayi, sannan naci gaba da gyara dakin. Na share shi nayi mopping, na dauko room freshener dana saba yin guzurinta na fesa a dakin. Nan da nan dakin ya fito tas dashi, ba kamar yadda na same shi dazu ba kamar bana mahaukata.
Tun ina karatu naji alamun karan motar Baba alamun ya dawo gida. Kasancewar yau babu aiki nasan cewa daga shago yake. Zuwa yanzu nasan cewa ya ci abinci kuma ya huta, na dauki hijabina na fita zuwa dakinshi. Babu kowa a dakin na shi sai shi kadai. Na durkusa acan gefenshi na gaida shi, ya amsa. Da alamun yana cikin yanayi mai dadi, tunda har na zauna muka danyi hira dashi. Abinda sai lokaci zuwa lokaci yake faruwa.
Ban san me yasa ba, ni da Baba sam bamu cika shiri ba. Amma nafi kyautata zaton rawar kaina ce ta janyo hakan, tunda ya sha fada ba sau daya ba, ba sau biyu ba.
Sai da Ramata ta shigo dakin sannan na mishi sai da safe, na koma dakina, ko ince dakinmu.
Ina komawa shirin barci na fara yi. Bayan nayi Sallar shafa’i da wutiri, na samu gefen katifa na zauna tare da dauko wayata dana ajiye a kasan filona. Ina cikin chatting Maryam ta shigo cikin dakin.
Duk yan dakin Ramata, ita, Aliyu da Hareerah, da ita kadai muka fi dasawa. Sauran suna kan hudubar uwarsu na cewa ‘yan uba, ba ‘yan uwa bane! saboda haka bamu cika shiri dasu ba. Amma ita babu ruwanta ko kadan.
Tayi murmushi tana kallona, “yanzu Hareerah take fada min cewa kin zo, ina ta mamaki”.
Nayi yar dariya ina kallonta tana zame after dress din dake jikinta, riga top mai karamin hannu da wnadon bakin jeans suka bayyana a jikinta, dariyata ta koma daga gida mai nuna alamun tambaya, nace “daga ina kike, kuma wannan shigar fa?”.
Ta kalli jikinta kafin ta kalleni, “kawata take bikin birthday, shine na leka wallahi”.
Na girgiza kai, “birthday party kuma sai da irin wannan shiga Maryam? Me yasa?”.
Tayi dariya, “Yaya Na’ilah ke da kike makarantar jami’a kin fa fini sanin irin wadannan abubuwan. Yanzu ‘yanmata ai sai da swagger! Idan mutum ba so yake a dinga mishi kallon taro-uku-sisi ba!”.
Cikin mamaki nake kallonta, “ban san daga ina kika dauko wannan kalar abu ba Maryam, amma hakan bai kama ce ki ba gaskiya. Ta ya kike zaton Mamanki zata dauki wannan maganar idan taji irin shigar da kike boyewa a cikin hijabi? Don daga ji nasan cewa wannan ba shine karonki na farko ba”.
Tayi dariya tana watso min wani kallo irin ‘are you kidding me’ dinnan Tace “me Mama zata ce kuwa? In fada miki gaskiya ita ta bani shawarar in dinga sanya after dress idan zan fita, in naje can inda zan je sai in cire saboda kada wani idon sani ya ganni a haka… Amma meye na wani boyo? Zamaninmu ne fa!”.
Tunda ta fara maganar bakina a hangame yake a bude, Subhanallah! Yaushe yaran gidanmu suka fara bin wannan hanyar ne? Nasan cewa tsakanin iyalan dama babu hadin kai da kaunar juna, saboda tun farko basu ga hakan daga wajen iyayensu ba, amma wannan wani babban al’amari ne, wanda nake ganin idan har aka bari ya girmama, akwai matsala. To amma, abinda uwa take supporting da dukkan karfinta, waye yake da karfin hana ta?
Ta tunkari kofa zata fita tana furta, “bari in zo inyi sallah!”.
Ina nan zaune ina ta saka da warwara ta dawo, ta shimfida abin sallah ta kalli gabas. Yadda take yin Sallar ma kadai abin zai baka mamaki. Kamar wadda bata taba taka ajin islamiya ba Raka’o’in data jero masu yawa yasa na fahimci cewa ba sallar isha’i kadai tayi ba.
Sai dana bari ta gama duk abinda zata yi, har ta kwanta sannan na dubi inda take, nace “ni kuwa a wani matakin karatu kike yanzu a islamiya?”, na dai san cewa yanzu tana ss2.
Tayi dariya, “na kusa wata ma ni rabona da makarantar nan yanzu, yan ajinmu aka wa karin aji zuwa na yan sauka, ni kuma aka barni a ajin baya shi yasa na daina zuwa ma kwata-kwata”.
Na tashi zaune sosai ina kallonta, sanin halin Maryam na saurin fahimta da ganewa yasa nafi jin dadin zama yi mata magana ko gyara akan wani abu, ba kamar Aliyu ba. Sau tari dan karamin gyara sai ya kaimu ga ya kalli tsakiyar idanuna ya zage tas kamar wanda yake jira dama.
Nace “kin san fa yanzu kece babba a gidannan Maryam. Kuma duk abinda kika yi, kannenki da suke tasowa shi zasu dinga yi. Yanzu idan basu ga yayarsu na zuwa makaranta ba, ta ya kike tunanin zasu samu kwarin gwiwar zuwa makaranta? Kinga ke dai baki da bakin cewa su zo su tafi, tunda kema ba zuwa kike yi ba. Sannan dubi dai irin shigar da kika yi yanzu, ya Baba zai ji, kuma me kike zaton zai ce duk ranar da yaci karo da irin wannan abu da kike yi? Maryam, kinga ke diya macece, sannan yarinya, kada ki bari rudin duniya da abokai ya rude ki, ki saka kanki cikin rayuwar da tafi karfinki. Shiga irin wannan da kike yi ta nuna jiki, ki shiga cikin kawaye ana ta cakuda da maza, akan wane dalili? Ina kika baro tarbiyar gidanmu da kuma al’adarmu ta hausa/fulani?”.
Tayi kasa da kanta a kunyace, “wallahi Yaya, Mama ce take cewa in dai ba za’a hada mu da yan ajinmu ba, sai dai in daina zuwa makarantar. Kuma ita take sawa inyi shigar. Ranar ma ana bikin Na’imah dana sanya hijabi sai ta hau fada, tana cewa wai ni ban waye ba!”.
Na girgiza kai cike da jimami, iyayen yanzu yawanci su suke bada gudummawa wajen lalacewar tarbiyar yaranmu. Uwa ce wai zata dorawa diya akidar yafa gyale da saka suturun banza, ita zata sanya mata akidar bin kawaye da samarin banza, daga karshe kuma idan lamari yazo ya bace bakinta ne zai fi na kowa wajen ihun cewa an lalata mata tarbiyar yara, bayan kuma itace tayi contributing wajen lalacewar tata.
Tsam na tashi na koma kusa da ita na zauna tare da dafa kafadarta, nace “idan tayi hakan ba laifi bane, tana so ne ki zama abar kallo, kamar tauraruwa. Sai dai, zaki iya zama fiye da hakan ma, ba kuma sai kin sabawa Ubangiji ba, kin gane?”. Ta daga kai.
Nace “good. Saboda haka gobe zamu je islamiyar taku, zan samu malaman naku muyi magana dasu. Sannan don Allah, shiga ta banza mai nuna jiki, ki daina yin ta. Ko ba don ke ba, ki duba kimar da Baba yake da ita a idanun mutane, balle ke kanki idan baki kame kanki a matsayinki na ya mace ba, Maryam zaki ga kin rasa girmamawar mutane, kin fahimce ni?”. Nan ma ta gyada kai.
Nayi murmushi cike da jindadi. Yanayin yadda jikinta yayi sanyi ya nuna min cewa taji, kuma ta dauki abinda nace. Na rungumota gefen kafadata ina kara yi mata bayanai da nasiha akan rayuwa. Daga karshe dai na janyo laptop dita na kunna mana kallo a ciki, babu TV a dakinmu sai na Baba dana matanshi, yawanci can muke zuwa muyi kallo. Ranar akan katifarta na kwana.
Tunda Baba ya tashemu sallar asuba ban koma barci ba. Ina gama azkar din dana saba yi lokacin gari ya fara yin haske, na fita na share tsakar gida tas. Na hada kayan wanke-wanke nayi, na shiga kicin na kunna wuta tare da dora ruwa wanda yara zasu yi wanka dashi na kuma dora musu abincin da zasu tafi makaranta dashi.
Har wajen karfe bakwai na safe ban ga motsin kowa a tsakiyar gidan ba. Matan sun riga da sun san dama ni nike ayyukan gidan, shi yasa daga ranar da nazo, har in bar gidan babu wadda take ayyukan gida. Duk da har yanzu Ramata bata sakar min ragamar ayyukanta ba, ranar girkinta ita take yin girkinta gabadaya, wanke-wanke da shara ne dai take bari na dasu. Hakan bai dameni ba.
Yanzun ma ina kan zuzzubawa yara taliyar dana dafa musu a cikin kulolim makaranta, sai gata ta fito daga dakin Baba. Kicin din ta shigo, na gaidata ta amsa. Tukunyar ruwan zafi ta bude, ta zuba daidai wanda zata hadawa Baba shayi ta fita daga kicin din.
Daya bayan daya yaran suka fara fitowa, na dauki kofi ina zuba zuzzuba musu. kowannensu yazo, sai ya duka ya gaida ni, ni kuma sai in mika mishi kofin shayi da biredi ya amsa ya tafi.
Maryam da take tsaye a gefena tun dazu, tayi murmushi lokacin dana mikawa Auwal nashi kofin shayin bayan na shafa kanshi.
Tace “shi yasa nake son ki zo gida wallahi, yaran nan sun fi behaving. Yanzu da ni ce da har yanzu ina nan ina ta faman su zo su amshi abincin, amma su ki”.
Nayi dariya, “kin san yara sai da lallashi da lalama. Yadda nasan halinki na zafin kai dama, ta ina yara zasu dinga binki sau da kafa?”.
Duk muka yi dariya ni da ita. Itama na zuba mata nata ta tafi ta karya.
Ban fita daga kicin din ba sai da duk suka tafi, sannan nima na zuba nawa nan tafi daki na karya.
Bayan na gama gyara kicin, wanda nasan idan ban gyara ba haka zan dawo in same shi. Musamman ma tunda yau da safe Ramata ta fita daga girki. Haka kuma Anty Alawiyya zata shiga tayi nata girkin ta barshi kaca-kaca. Na girgiza kai cike da takaicin halayen wannan matan.
Dana gama da kicin daki na koma shima na gyara shi. Kai tsaye wanka na fada, na sanya riga da zani na atamfa, dinkin single da fitted riga. Sallama na wa mutanen gidan na shiga cikin unguwa. Daya baya daya na bi gidajen makota muna gaisawa, daga karshe na dire a gidan su Kulsum, a raina ina ayyana sai da yamma sannan zan je nata gidan, in yaso bayan magriba sai in dawo.
Ina yin sallama a tsakar gida, na ja nayi turus ganin yar halas din a tsakiyar gida tana wa yarinyarta yar shekara uku, Muneerah wanka.
Tana ganina tayi murmushi, “saukar yaushe?”.
Nayi dariya ina zama a gefenta, “jiya da yamma wallahi. Me kike yiwa mutane a gida haka tunda safiyar Allah Ta’ala? Inna ina kwana?”. Na gaida Inna data fito daga cikin madafi. Inna ta amsa tana min sannu da zuwa.
Na kalli Kulsum, “ko dai awon ciki kika zo ne?”.
Ta dan harareni, “wani irin awon ciki kuma ana zaman lafiya? Mu a gidannan ma muka kwana in fada miki!”.
Jikina yayi sanyi da jin abinda tace, nace “kamar ya? Ban gane ba, wani abu ya faru ne?”.
Inna tace “menene ma bai faru ba yar nan? Ai tafi wata daya a gida yanzu”.
Naji zancen kamar wani saukar guduma a kaina, nace “Innalillahi wa Inna ilaihi raji’un!”.
Inna ta girgiza kai kawai, “ai ke dai abin ba’a cewa komi Na’ilah. Sai dai abinda Allah ya kaddara dama babu makawa sai ya faru, sai hakuri kawai”.
Na fara cira idanu tsakanin Inna da Kulsum, Babu wanda ya sake yin magana a cikinmu har ta gama yiwa Muneerah wankan, ta tsaneta cikin zani. Muna zaune ta shiryata cikin kayanta, ta tura ta zuwa wajen Inna. Kallo kawai nake binta dashi.
Tun can nasan cewa dama suna ta faman samun sabani da mijinta Mukhtar. Ko waccan zuwan da nayi dama, sai da suka sha dabi har sai da Iyaye suka shiga cikin maganar. Sai dai wannan karon, jikina yana bani cewa wannan yafi karfin fadan da suka saba yi.
Tana gama hada kan kayan, na ja ta zuwa dakin da yake nata da. Tarin akwatunan dana gani da kuma kayan kwalliyar daki yasa naji jikina ya kara yin sanyi. Na zaunar da ita a gefen gado nima na zauna, tun kafin in daga baki ma in tambayeta ta riga ni, tace “rabuwa muka yi da Abban Muneerah!”.
Na zare ido kamar zasu fado kasa, na kara yin wani salatin dai na sanar da Ubangiji. Ta girgiza kai, “Abban Muneerah ya rikice. Zama yaki ci yaki cinyewa. Ki duba lokacin da aka yi aurenmu, yazo ya hana ni karatu kiri-kiri, haka muka hakura ni dasu Baba. Yazo ya dinga gallaza min a zamanmu, wasu abubuwan ma kawai shiru nake yi. Tun ina kawo kara gida ana mishi fada, har aka daina. Abinci wannan haka ya dinga gagarata a gidanshi, ke kin san yawancin abubuwan dake faruwa. Sana’a na fara yi da kudina, amma haka zai zo ya cinye kudin kuma ya hana ni. Kwanan nan aka ba Inna kudin adashi, ta hada kan kudinnan ta sai min keken dinki, wallahi ko sati uku keken bai rufa ba ya dauke shi yaje ya sayar. Wai kudin toshi ya kai da kudin…”. Kuka ya kwace mata anan.
Na dafata ina lallashinta har tayi shiru.
“Ashe wata ce ya hango a wajen aikinsu. Bai ma gaya min yana nemanta ba, sai a gari naji labari. Wata makociyata ta jiyo labarin take gaya min. Dana tuhume shi, kai tsaye ya amsa babu musu. Na tambayeshi dalili, sai cewa yayi saboda tana da ilimi, kuma ta fi ni hankali da natsuwa. Nace laifin waye to da bani da ilimin? Sai ya hau cewa ni ce sakara ai. Daga wannan rana gabadaya sai ya kara rikicewa, wallahi bamu kara samun zaman lafiya ba. A gabana zai kira ta a waya, su raba dare suna hira, tun ina kuka har na hakura na daina. Iyayenmu duk sun shiga cikin maganar, Kawu Bala da yaje akan maganar baki ji zagin kare dangin daya mishi ba, yace ina ruwanshi tunda ni matar shi ce? Bashi da ikon da zai hana shi yin abinda yaga dama. Ke magana taki ci taki cinyewa fa. Ranar nan kawai ina zaune da dare, sai gashi ya shigo gidan. Yace min an sanya aurenshi watanni biyu masu zuwa, nace mishi to Allah ya sanya alkhairi, yace ameen. Washegari wai sai ya sameni yace shi tafa bashi da wajen da zai saka amarya idan tazo, nace ‘to Abban Mufeedah, ya kake so ayi kenan?’, bai ce komi ba dai ya tafi. Haka muke ta zama dai, hatta yan uwanshi sai da suka fara shigowa suna zagina. Wai ni matsiyaciya ce, ban iya komi ba sai ci. Ita kuma wadda yake neman auren tana ta musu hidima. Abubuwa fa duk suka rikice. Yanzu kawai ranar nan ina zaune, sai gashi yazo da takarda ya miko min, wai ya sake ni saki biyu. Nace ‘me na maka?’, sai ya hau zage-zage da daga jijiyar wuya, wai shi dama can ya gaji da zama dani, yana ta hakuri da nine dama, kuma hakurinshi ya kai makura, in fita in bar mishi gidanshi kawai. Nace to shikenan, shine na tattara kayana na dawo gida abina!”.
Cike da jimami nace “to Allah yasa hakan shine mafi alkhairi. Kuma babu wanda ya same shi game da maganar akan haka?”.
Tace “ace mishi me Na’ilah? Last week aka daura mishi aure, har cikin gidannan yayi sallama ya kawowa Malam katin gayyata”.
Na zare idanu, “ikon Allah! Wannan ai cin fuska ne!”.
Tayi dan murmushi cike da takaici, “cin fuska kuma wani iri ne ban gani ba a wajen Mukhtar? Ai sai dai in karas kawai. Kuma yaje na barshi da Allah!”.
Nayi saurin girgiza kai, “a’ah, kada ki ce haka mana. Ko babu komi mahaifin diyar ki ne, kuma akwai sauran igiyar aure a tsakaninku, idan Allah ya nufa sai ki ga kun komawa aurenku!”.
Tace “da wa? Allah ya tsareni wallahi. Kinsan cewa sauran Kayankayan dakina da ba’a dauka ba, ya sayar dasu?”.
Nace “me yake damun wannan mutumin ne haka?”.
Tayi kwafa, “tijara mana! Su Malam zasu yi magana, nace su barshi. Wallahi na yafe mishi duniya da lahira, Tunda dai na samu aka rabu lafiya, to ni na godewa Allah”.
Na janyo ta jikina na rungume cike da nuna lallashi, nace “to Allah yasa hakan shine mafi alkhairi a gareku ku duka”.
Tace “Ameen. Ni yanzu haka so nake in gama iddata, makaranta zan koma in cigaba da karatu na”.
Nace “haka ne, Allah ya sanya albarka to. Allah kuma yasa hakan shine daidai”.
Tace “Ameen. Ina Janan?”.
Daga nan muka canza akalar hirar zuwa ta Janan. Sai ma dana kirata muka sha hira da ita. Ita kanta taji haushin abinda Mukhtar din yayi, ta ma so ta fi ni jin zafin abin. Sai data gama kumfar baki sannan kuma muka hau hira.
A gidan na yini, muna daki muna ta maida bayanai, irin zaman da suka yi da tsohon mijinta, da yadda danginshi suka juya mata baya lokaci daya. Wasu abubuwan ma dai gwanin ban takaici. Tunda kwata-kwata wasu abubuwan kawai sai dai fa yayi su ya kawo wani excuse da bai hau ba ya dora. Kawai abin dai dama kamar yana neman hanyar fita ne, shi yasa.
Da lokacin yin abinci yayi na shiga gida na dafa, na koma muka dora daga inda muka tsaya.
Da yamma na raka Maryam islamiyarsu, na samu malamanta muka yi magana dasu. Korafinsu daya, rashin maida hankali da take yi. A sati bai fi taje makaranta sau biyu ba, idan tayi da yawa sau uku. Na musu alkawarin idan Allah ya yarda za’a mata magana, nan suka ce idan ma ta maida hankali zata iya bin yan ajin nasu, dama as a warning ne yasa aka yi mata hakan, ko zata hankalta. Nan dai na musu godiya tare da biyan kudin watanta da bata biya ba, tace Baba ya bata amma cinyewa nayi. Anan na barta ni kuma na koma gida.
Kwana na shida a gida, komi yana tafiya yadda yakamata. Yawanci a gidan su Kulsum nake yini. Da safe idan na gama yin komi nawa zan shiga can. In taya ta aikin awara da dankali da take yi na saidawa da rana. In muka gama kuma mu hau aikin zobo shima da take yi ana kaiwa shaguna suna sai da mata. Haka dai nake juya rayuwar tawa.
Na shigo gidan kenan da yamma, daidai kofar dakin Aliyu dake kusa da kofar gida naji motsi da hayaniya. Sautin kida yana ta tashi daga dakin nashi. Na girgiza kai, ban san me yake damun yaron ba, haka zai tara yaran unguwa sa’anninshi su yi ta hayaniya a daki. Basa komi sai jin kida da wake-wake. Bana tunanin yaje makaranta ma yau.
Har na wuce ta kofar dakin, sai kuma na koma sakamakom hayaki da naga yana fita daga jikin labule da aka sakaye dakin dashi. Daga farko nayi tunanin ko girki ne yake yi a dakin, tunda wasu lokutan yana shiga cikin gidan ya kwashi garwashi yace zai dafa ruwan shayi.
Sai dai abinda na gani ne yasa na yaye labulen dakin sosai.
Shisha ce a tsakiyar dakin, sun sakata a tsakiya shi da abokanshi su uku suna zuka.
Nace “Aliyu!! Meye haka kuke yi?”.
Duk suka dago a tsorace suna kallona, sai dai idanun Aliyun kyar suke a kaina, babu ko dar a cikinsu.
Na harari abokan nashi da suka yi cirko-cirko a zaune, nace “ku tashi ku fita”. Babu musu suka mike sumi-sumi suka fita daga dakin.
Na maida kallona ga Aliyun, nace “kai yanzu abinda kake yi dama a cikin dakin kenan kai da abokanka? Shi yasa kullum kuke shiga ku rufo daki a rasa abinda kuke yi?”.
Ya mike tsaye yana wani muzurai, “to meye hadin mutum dani? Naga cewa dai rayuwata ce bata uban wani ba! Meye hadinki dani?”.
Nace “ko banza naci darajar kasancewa yayarka Aliyu. Wannan sam ba dabi’ar data dace bace, ka rasa a inda ma zaka sha shisha sai a gidan mahaifinka?”.
Caraf! Sai Ramata ta cafe maganar, “kinga kada ki sake cewa d’a na yana shaye-shaye. Gwanda ma shi an san abinda yake yi, kuma a gabanmu yake. Ke waya san wace tsiyar kike yi a can?”.
Na kalleta idanuna har juyawa suke yi saboda yadda maganganunta suka dake ni, nace “ke kan ki kinsan cewa nafi karfin yin wannan rayuwar da kike ambatowa, kuma karya kike yi kice saboda bana gaban iyayena zanyi rayuwar da bata dace ba!”.
Ai sai shima Aliyun ya hayyako min, “kada ki kuskura ki zagar min uwa fa!. Ba gaskiya ta fada ba? Ke har kina da bakin kirana dan shaye-shaye??”.
Nace “Aliyu ka kiyaye ni, kada bakinka ya sake kuskuren ci min mutunci!”.
Sai ya kara matsowa daf dani, “idan naki fa? Nace idan naki fa? Kashi zaki bani? Ke din banza! Ke har kin isa ki zauna kina gaya min kabli da ba’adi? Wallahi idan baki kiyaye ni ba sai in kwantar dake anan wajen!!”.
Ramata tace “yayi daidai da na. Yanzu na tabbatar da cewa nice na haife ka! Ka cika da!!”.
Inna data jiyo hayaniya da wata Assibi makociyar mu suka shigo, itace ta tari bakin Ramata din, tace “haba ke kuwa! Da girmanki zaki biyewa yara har ki goya mishi baya. Yanzu ko Na’ilah bata girmi Aliyu ba, ai tana da damar idan yayi abinda bai yi daidai ba ta kwabar mishi!”.
Sai ta harari Innar, tace “yo meye a cikin shishar? Uban wa yace miki kayan shaye-shaye ne ita?”.
Inna ta kama baki cike da mamakin zagin data yi. Assibi tace “amma kuma ai daga nan yara suke ganin hanyar shaye-shayen ko?”.
Sai Ramata ta kara kumbura, ta karkace daurin dankwali ta kawo shi goshi ta kafe. “ni fa dama ina sane da duk munafurcin da kuke min a cikin unguwar wannan musamman ma ke!”, ta nuna Inna. “Na’ilah tana zuwa gidanku kuna zagina da gulmata. To wallahi ta Allah ba taku ba! Kuma ni da ‘ya’yana nan gani nan bari. Idan ma wani kulli ake musu don su lalace to wallahi sai dai dan wani ya lalace don ni naci dubu sai ceto! Kuma bari uban Na’ilar ya dawo, sai ya gaya min in uban wani ne ya haifar min diyana ko ni!!”. Ta kama hannun Aliyu suka shige dakinta ta barmu anan a tsaye.
Assibi tace “to kuwa Allah ya kyauta miki gaskiya lamarinki sai du’a’i!”.
Tuni mutane har sun fara shigowa gidan jin hayaniya. Inna da Assibi ne suka kore su, bayan sun tafi suka lullube ni suna bani hakuri. Ban iya magana ba, na zame na shige daki.
Ina shiga daki jikina ya shiga rawa, na zame gefe katifa na zauna. Ban iya rigima ba ko kadan. Sam bani son rigima. Barni da tsiwa dai da mita, da kuma rashin barin ko ta kwana. Abin ya min ciwo kwarai da gaske, kanina wanda na bashi shekarun da suka fi yatsun hannu, zai tsaga tsakiyar idanuna yaci mutuncina a gaban uwarshi. Kuma nasan cewa ya zage ni a bulis, nasan cewa ko na gayawa Baba babu abinda zai yi akai.
Abubuwa irin wadannan ba yau ne suka fara faruwa ba, kuma kowane lokaci haka abin yake, ya zageni, kuma bani da bakin ramawa ko na kai korafi, sai dai in shige daki in shaki kuka. To na gama kukan. Nayi alkawarin in dai akan Aliyu da uwarshi ne, to na daina kuka.
Wayata na janyo, banyi tunanin komi ba na dannawa Ya Mudatthir kira. Ina jin sautin muryarshi, naji na fashe da kuka. Take naji ya rikice, ya fara tambayata lafiya? Me ya faru? Duk yadda naso in daina kukan kasawa nayi, sai da nayi mai isa ta, sannan na fara zayyane mishi dukkan abinda ya faru tun daga farko har karshe. Nasan wasu abubuwan kawai yaji su ne ba don ya fahimta ba, saboda yadda muryata dama jikina suke rawa.
Bai katse ni ba har na gama mishi bayanin, sai dana gama sannan ya fara jefo min tambayoyi. “ita babar tashi me tace ne?”.
Nace “itama fada ta hau yi, tana cewa wai nace mishi dan shaye-shaye, kuma ni wallahi ban ce mishi haka ba. Kawai magana ce na mishi!”.
Yace “na sani Na’ilah, nasan ba zaki ce mishi haka ba. Zan kira Baban anjima, yana nan aka yi?”
Nace “a’ah, baya gida”.
Yace “to shikenan. Kina son zuwa nan ne?”.
Da sauri na hau daga kai kamar yana ganina, nace “ehh!”. Yayi yar dariya, “to shikenan, zan turo miki kudin mota. Idan zaki iya tahowa gobe, sai ki taho. Idan kuma baki samu dama ba, sai ki bari sai jibi”.
Nace “to Yaya, nagode. Allah ya kara girma”.
Muka yi bankwana dashi na kashe wayar.
Sau tari ina fata dama ace ni ce na samu damar da Yaya ya samu. Yana gaban danginmu lullube dasu hankalinshi kwance. Tun lokacin daya gama sakandire, Yobe ya koma yayi degree dinshi acan. Da Allah ya taimake shi ya samu aiki yana gama makaranta, sai ya zaune acan abinshi. Ni kam tsakanina dasu sai dai zuwa hutu, ko kuma idan wani daga cikinsu yazo, ko kuma wata sabga ta biki wanda Baba bai cika bari na naje ba.
Duk da hakan akwai shakuwa da kusanci a tsakaninmu dashi sosai. Yana so na kuma yana tattalina.
Ina gama sallar isha’i na hau hada kan kayana waje guda. Maryam da take kwance tana kallo ta kalleni, “wai garin zaki bari ne kike hada kaya?”.
Nayi dan murmushi, “wallahi kuwa”.
Ta tashi zaune, “ba dai akan rikicin dazu bane ba ko?”. Tunda aka yi abin ma ni babu wanda ya tuntube ni da zancen, sai naji abin ya dawo min sabo.
Na girgiza kai, “ko kadan. Dama ina son zuwa”.
Tace “to shikenan. Ki dai kara hakuri don Allah. Mama ta daure mishi gindi da yawa wallahi, ni kaina rashin kunya yake min, bani da yadda zanyi dashi kuma”.
Kai kawai na iya daga mata don bana ma son maganar tayi tsawo.
Washegari tunda safe nayi wanka na shirya tsaf, na fito da akwatuna na ajiye a kofar daki nayi sallama a kofar dakin Baba. Sai da aka amsa min sannan na shiga.
Yana zaune a kan kujera yana duba jarida, na durkusa a gefenshi na gaida shi ya amsa. Nace “Baba zan tafi Gashua!”.
Nayi zaton ma zai yi magana akan zancenmu da Aliyu, ga mamakina bai ce komi ba, sai tambayata da yayi, “shi wanda yace kije din, ya baki kudin mota ko? Don bani da kudin da zan baki”.
Na gyada kai, nace “ehh”.
Yace “to madallah. Allah kiyaye”. Daga haka ya maida kanshi ya cigaba da karatun shi. Na tashi na fita daga dakin.
Sai dana bi su daki na musu bankwana, Maryam ta taya ni daukar akwatina muka fita. Na shiga gidan su Inna su ma na musu sallama. Kulsum da Maryam suka raka ni har bakin titi kasancewar babu ababen hawa tunda safiya ce sosai, na tari adaidaita sahu na hau muka tafi tasha. Motar Kano na hau, tana cika muka dauki hanya.
*☆⋆05⋆☆*
Tunda muka isa Kano da misalin karfe goma na safe, muka hau motar Gashua. Sai a tasha na samu yogurt mai sanyi da cake na ci. zuwa karfe sha daya muka dauki hanya. A Hadejia muka tsaya aka yi sallah tare da cin abinci, muka sake daukar hanya. Karfe biyar da yan mintuna muka shiga garin Gashua.
Yaya Mudatthir da kanshi yaje ya dauko ni. Ya kalli yadda nayi wuki-wuki saboda gajiya yayi dariya, “Subhanallah!! Illo! (nick name din da yake kira na dashi), you look like a total mess!”.
Nima nayi dariya, “Yaya tafiyar awanni fiye da bakwai a mota ai ba ta wasa bace ba!”.
Ya gyada kai, “kwarai kuwa. Sannu da zuwa. Ya hanya?”.
Nace “Alhamdulillah”. Ya taya ni daukar akwatina ya dora akan mashin dinshi, nima na hau muka tafi.
A gidan Bako ya ajiye ni, ko shiga bai yi ba yace min zai dawo bayan magriba, na mishi godiya. Ya juya ni kuma na shiga gidan wani almajiri ya biyo ni da akwatina.
Inna Fatsu na gaban wuta tana tuka tuwo nayi sallama na shiga cikin gidan. Ta tashi tsaye tare da dago kanta sakamakon jin muryata a kanta. Kafin ta tantance ko ni ce ko ba ni bace ba, na saki jakar hannuna kasa na falla da gudu na fada jikinta. Allah ya taimaka ta dafe bango da sai na kaimu kasa gabadayanmu.
Ta fara kokarin yakice ni tana mitar, “ban san ko sai yaushe bane zaki daina wannan shirmen naki ba Na’ilah. Ina ga dai sai ranar da Allah ya baki sa’a kika buga mu da kasa mu duka kika karya min kugu sannan zaki daina!”.
Nayi dariya tare da daga kaina na kalleta, “Fatsu na, kin sake yin kyau wallahi. Me Malam yake baki kina ci ne?”.
Ta girgiza kai, amma murmushine akan fuskarta, “tuwon dawa ne da miyar. Idan so kike yanzu in bada nikanta”.
Nayi dariya, “Inna kin san wannan ba cima ta bace. Abu zaki bane mai sanyi da mai romo don na kwaso gajiya da yunwa”.
Tace “ki fara shiga kiyi wanka, sai ki zo kici abinci”.
Nace “haka za ayi”. Na fada daki.
Ita ta biyo ni da jakar hannuna dana yasar da akwatina tana mita. Dariya kawai na dinga mata.
Idan ina gabansu ji na nake yi kamar wata karamar yarinya yar shekara goma.
Da nayi wankan sai na dauro alwala kawai. Na shiga dakin Fatsu da aka mamaye da carpet mai laushi. Dakin irin tsarin nan ne na mutanen da, gadon karfe babba da kuma karami na katako, sai wardrobe babba, da kuma tarkace da ba’a raba tsofi dasu. Na zauna na shafa mai tare da lalubo kaya masu karancin nauyi na saka. Ina sakawa sai gata ta shigo dakin da plate da kula.
Na mike kafa akan carpet din tare da amsar plate din, maltina ce mai sanyi har raba yake da ruwan sanyi, kular kuma soyayyar indomie ce a ciki.
Tace “Yayanki yace kada ayi abinci dake, za’a dafo daga gidanshi a kawo miki”.
Nayi murmushi cike da jindadi, “sai ni yar gatar Yaya da Anty Sailu”.
Tayi dariya, “kwarai kuwa, dazu zuwanta biyu nan wai taga ko kin zo”.
Nima nayi dariyar. Sailuba itace wadda Yaya Mudatthir ya aura. Wannan shekarar su ta biyo ne kenan. Auren dangi ne suka yi, diyar Iya Lami kanwar Mama ce. Da yake duk tare muka taso da ita da sauran diyan dangi sa’anninmu, kusan duk abokan juna ne mu.
Na sa fork na fara cin indomie, taji maggi da dan taruhu, dama in dai Inna Fatsu ce bana jinta wajen girki. Ta iya hada abinci kala-kala, tun daga na da har na zamani.
Sai dana kusa yin rabi sannan na daga kai na kalleta, “wai ni ina Malam yayi ne? Nayi zaton ma yana dakin soro ne”.
Tace “ai Malam wajen jana’izah yaje, nasan kuma daga can zai wuce masallaci. Shi da gida sai bayan isha’i”.
Nace “Allah sarki, waye ya rasu?”.
Tace “wani abokinshi Malam Mati idan baki manta shi ba”.
Nace “ina zan manta Malam Mati? Shi da nake kaiwa rubutuna idan nayi a allo ya wanke min kafin in iya?”.
Inna tayi dariya, “Aikuwa shi ne. Rashin lafiya ce yayi wallahi, ya kusa share watanni biyu a aaibiti”.
Nace “Allah ya jikanshi, Allah kuma yasa mutuwar hutu ce a gare shi. In shaa Allah idan na fita gobe kuwa zan je inyi gaisuwa”.
Tace “yakamata dai”.
Ina gama cin abincin aka fara kiran sallah. Na daukesu na fidda waje na koma daki nayi sallah.
Ina gamawa naji wayata tana kara, na tashi a nutse na dauketa daga inda na ajiyeta, lokacin kiran har ya katse. Na duba naga Maryam ce. Murmushi nayi kafin na sake kiranta. Yana fara ringing ta dauka, “Yaya Na’ilah tun dazu nake kiranki baki dauka ba, hankalina har ya fara tashi wallahi!”.
Nayi dariya, “ban jima da isowar bane, ina zuwa kuma wanka nayi. Ina ga lokacin kika kira. Na sauka lafiya, ina dakin Fatsu na ma idan abinda kika kira ki tambaya kenan”.
Tace “shine dama. Ya hanya? Kin same su lafiya dai?”.
Nace “lafiya lau kowa. Ya gidan?”.
Mun danyi hira da ita ta fada min yadda su Muneerah da Auwal suka dinga cigiyata a gidan, ina ta dariya. Daga karshe dai muka yi sallama da ita akan cewa zan kira washegari ta hada ni da yaran. Bayan mun kashe wayar Baba na turawa text na sanar dashi na sauka lafiya duk da cewa nasan Yaya zai fada mishi.
Kan abin sallah na koma na zauna gefen Fatsu da take lazumi nima na fara nawa har aka kira sallah.
Sai bayan sallar isha’i sannan Malam ya shigo gidan. Na dauki kwanukan da aka zuba mishi abinci na tafi dakinshi. A bakin kofar dakin nayi sallama, daga can ciki na jiyo ya amsa cikin muryarshi mai cike da kamala da haiba.
Na yaye labulen dakin na shiga, yana ganina ya hau sakin murmushi “Masha Allah, amaryar tawa ta karaso kenan?”.
Nayi yar dariya tare da zama a gefen shi, “ni ai nayi fushi, tunda kaki zuwa tarya na!”.
Yayi yar dariya, “to, ki ce wannan karon da yan rigimun kika zo kenan?”.
Inna data shigo dakin hannunta dauke da kofin ruwa tace “kamar kuwa ka sani!”.
Na zauna a gefenshi tare da ajiye kwanukan a gabanshi. A nutse na gaida shi ya amsa tare da tambayata mutanen gida, na amsa tare da mishi ta’aziya.
Inna ta gama zuba mishi tuwon. Ya wanke hannunshi tare da yin bismillah ya fara cin tuwon. Ya kalleni, “yau ba za’a taya ni cin abincin bane?”.
Inna tace “yau dai kai kadai zaka ci abincinka. Girkin matar Yayanta take jira”.
Tana rufe baki sai ga sallamar Yayan a tsakar gida. Na tashi da sauri na fita tsakar gidan. Wani dan ihu nayi na dafe Sailuba dake gefen Yayan. Ya girgiza kai kawai ya shige dakin Malam ko tunanin yi mana magana bai yi ba, don yasan in muka hadu sai a hankali.
Sai da muka gama murnar ganin juna sannan muka shiga ta gaida su Malam.
Na dauki kwandon da suka shigo dashi na ja ta muka koma dakin Inna. Da yake da wuta kar a garin, na kara mana gudun fanka.
Farfesun busasshen kifi ne ta kawo min da chips din doya. Na zuba iya wanda zai ishe mu na ciccibi sauran na kaiwa su Inna.
Dakin na koma muka dasa dandalin hira ni da ita, bamu san dare yayi ba sai da Yaya ya leko yace mata ta tashi su tafi. Na raka su har kofar gidan muka yi sallama dasu.
Dakin Fatsu na koma nayi shirin kwanciya barci na. Ina zaune Fatsu itama tayi nata shirin ta tafi dakin Malam. Wutar dakin na kashe tare da sakaya dakin, na kara ware iskan fanka na fada kan karamin gado na kwanta.
Sai dana kira Janan muka gaisa na fada mata ina Gashua sannan na dannawa Umar kira.
Yana dauka ya tare ni da, “haba Sweety na, ina kika shiga ne tun safe nake nemanki?”.
Nayi murmushi, “hello to you too, and yes, lafiya lau na wuni!”.
Ina jin sautim dariyar daya saki, “Lols.. Da gaske nake fa. Har na fara shirya kayan tahowa Kt gobe idan baki amsa kira na dama”.
Nayi murmushi, “lallai ma, yanzu kawai sai ka taho Katsina?”.
Yace “ai ba kawai bane, ina lafiya bugun zuciyata bata daga kira na?”.
Nace “ba kin daga wayarka nayi ba, ina tunanin matsalar netwok ne. Kasan ina Gashua fa!”.
Yace “hope komi lafiya?”.
Dadina da Umar kenan, kulawarshi a gareni na matukar tafiya dani. Nace “lafiya lau fa, kawai nazo ganinsu ne!”.
Yace “good. Shine kuma sai yanzu kike fada min ko?”.
Nayi dariya sosai, rigimar Umar watarana tafi karfin mai rai.
Mun dauki kusan mintuna goma muna sa’insa akan ban fada mishi ba, daga baya dai ya saki zancen muka shiga wani kan yanayin aikinshi.
Sai dana fara jero hamma sannan muka yi sallama dashi, “goodnight dear, dream of me fa! Zan kira ki gobe ki bani labarin kalar mafarkin da kika yi”. Abinda yace kenan kafin ya kashe wayar.
Nayi murmushi kawai tare da ajiye wayar a gefen gado. Nayi addu’ar kwanciya barci tare da jan abin rufa zuwa jikina tare da rufe idanuna.
*
Funkasu muka ci a matsayin abincin kari. Ina gamawa nayi wanka na shirya na tafi gidan Yaya. Naci sa’a yana gida bai kai ga fita ba. Yana aiki ne da wani research institute. Na gaida shi ya amsa. Sailuba ta fito daga daki tana murmushi, “yanzu nake cewa ya kira ki kizo ki ci abinci”.
Na kalli inda take nuna min, kuloli ne a shirye akan ledar cin abinci. Na shafa cikina, “abincin nan sai dai ko anjima don yanzu dai kam cikina a cike yake”.
Tace “to ai shikenan”.
Yaya ya mike zai wuce, na mishi Allah kiyaye, ita kuma ta bishi zata mishi rakiya. Yace “kada dai a yi nisa Na’ilah, na san ki da yawo. Duk ranar da kika zo haka zaki ja matata ku shiga gari sai na nemo ku”.
Nace “Yaya sau daya ne fa ka taba nemo mu”.
Yace “oho dai. Idan dai kuka dade, babu fita gobe!”.
Nayi dariya “matar ka zaka ja wa kunne kuma wannan, ita ce mai son yawo bani ba”.
Yace “ni dai na fada muku!”. Daga haka ya fita.
Ina zaune a inda suka barni ina wasa da kan wayata ta dawo, tace “bari in shirya sai mu fita ko? Abincin sai mu tafi dashi gidan Yaseerah mu ci”.
Na gyada kai, “haka za ayi”.
Ta shige can kuryar daki ni kuma na cigaba da danne-danne na har ta fito sanye da riga da zani na atamfa, hannunta rike da jaka da hijabi. Na bita da kallo kafin inyi sequeling na fara tsalle akan kujera, “ke matar Yaya sai kice kin kusa sauke mana baby!”.
Tayi sauri ta ja rigarta kasa tana hararata kasa-kasa, “ni kada ki min ihu anan. Don mayuntaka har kin hango abinda ko wata uku bai rufa ba!”.
Na daga mata gira ina dariya, “haba mata, kada kiyi underestimating dina ta wannan fannin!”.
Ta shafa cikin tana dan murmushi, “ku dai taya mu da addu’a dai kawai, Allah yasa mai tsayawa ne”.
Murmushin tsokanar kan fuskata ya dusashe, sau biyu tana yin barin ciki, likitoci sun ce mahaifarta bata da karfin da zata dauki ciki ne, saboda haka aka mata daurin mahaifa.
Na dafa kafadarta ina murmushi reassuringly, nace “da yardar Allah babu abinda zai faru, zaki haifo mana babynmu lafiya lau, in samu takwara!”.
Hakan yasa ta saki dariya a tausashe, ni kuma nayi murmushi, tace “muje, Yaseerah har ta fara danno min flashing”.
Nayi dariya tare da ciccibar kwandon da ta saka abincin data ajiye mana, muka fita.
Yaseerah diyar Baba Adama kanwar Mama ce. Su hudu ne a wajen su Bako duka mata, Inna Talatu ita ce ta farko, tana aure a Damaturu, sai Mama na, Iya Lami da Adama, su duka suna nan Gashua ne. Yaseerah, ni, Sailuba, Ma’u kanwar Sailuba da Lawisa kanwar Yaseerah duk tare muka taso dasu, kusan duk sa’annin juna ne mu. Yaseerah a shekara daya aka aurar dasu ita da Sailuba. Yanzu har tana da yar diyarta Hafsat.
Gidan Yaseerah muka fara zuwa, a shirye muka sameta tsaf tana jiranmu. Bayan mun gaisa da yin yar hirar yaushe gamo, muka ci abinci, daga nan muka fita.
Gidan Iya Lami dake nan unguwar su Yaseerah muka fara shiga muka gaidata. Daga can muka biya gidan Marigayi Malam Mati muka yi gaisuwa.
Yinin ranar dai a haka muka gama shi. Shiga nan fita can, sai wajen karfe biyar muka koma gidan Sailuba.
Yaseerah da Ma’u suka koma gidanta, ni na tsaya wajen Sailuba. Sai da na taya ta tayi girkin abincin dare, sannan na mata sallama na tafi, lokacin har an gama sallar magriba.
Nayi sallama na shiga dakin Fatsu. Tana zaune akan abin sallah tana lazumi a tsakiyar daki, ta bini da kallo lokacin da nake ajiye hijabin dana cire akan gado.
Tace “wato Na’ilah kina nan da yawon nan naki ko? Yanzu saboda Allah ace kin fita tunda sanyin safiya amma sai yanzu zamu ganki? Saboda kin raina mu ne ko me? Idan a gaban mahaifinki kike kina wannan yawace-yawacen ne na babu gaira babu dalili?”.
Nace “haba Fatsu, ya zaki ce wai ina yawo? Ziyarar yan’uwa ce fa nayi, zumunci. Kuma a gida yawon me zanyi? Bani da kowa acan sai nan din dai, kin san haka”.
Tace “ai sai kiyi tayi, tunda bakinki bai iya bada hakuri ba balle ya iya amsa laifin da yayi!”.
Na koma gefenta na zauna ina yar dariya, “to naji Fatsu na, Allah ya baki hakuri, na tuba na bi Allah na bi ki. In Allah ya yarda gobe babu inda zan je, a kugunki zan wuni. Kinji dadi?”.
Ta dan harareni cikin wasa, gefe daya kuma tana kokarin danne murmushin da take yi, tace “Allah yasa, kullum ke dama maganar ki daya, amma baki cikawa!”.
Nace “in Allah ya yarda wannan karon da gaske nake, I’ll be all yours gobe!”.
Kamar yadda nayi alkawari, washegari a gidan na yini, ko nan da kofar gida ban leka ba. Da yake ba wasu ayyuka muka yi a gidan ba, na shiga dakin Malam na fiddo kayan ciki gabadaya na sharo dakin tas, na maida na sake mishi wani sabon shirin.
Da yamma bayan nayi wanka, na dauko littafaina da textbooks dana taho dasu ina bita. Nasan cewa nan da sati daya ne zasu fara zancen mu koma makaranta. Bana bari koda wasa in shantake a gida idan naje hutu, ina da lokuta na musamman da nake warewa, lokaci zuwa lokaci na kan dauko littafaina inyi bita musamman akan courses din da zamu yi a semester ta gaba ko kuma wadda muke cikin yi.
Da dare bayan isha’i muna zaune akan tabarma a tsakar gida. Bura-busko muka ci, (tuwon biski/tuwon tsakin masara ko na gero), wannan karon na masara ne muka yi, da miyar kuka da man shanu. Kamshin tuwon ma kadai ya isa yasa yawun mutum tsinkewa balle dadin da yayi. Malam yayi baki, tare suka ci abincin shi da bakin a dakin soro inda ya saba ajiye baki na nesa.
Bayan mun gama cin abincin, na koma na zauna ina taya Fatsu hade kayan sakar da tayi da zare, kasancewar babu wutar lantarki, hasken farin wata ne tar ya mamaye kafatanin tsakiyar gidan, sai kuma hasken wutar candle dana kunna daya kara taimakawa wajen kara haskake wajen.
Ita tana gaban murhu tana zubawa almajirai abinci. Malam ya dauki nauyin ciyar da kananan almajirai wadanda karfinsu bai gama kaiwa ba. Yanzu ya daina karbar almajirai na nesa ma, sai wadanda suke cikin Yobe kawai, kuma garinsu bai yi nisa ba.
Manyan tsofin almajiranshi kuwa tuni ya yaye su, wasu sun koma garuruwansu. Yayin da wasu suna nan cikin Gashua, wasu sunyi aure, wasu suna sana’o’insu, su da garuruwansu sai dai ziyara.
Da ta gama zuba musu, ta dawo gefena ta zauna muka cigaba da yin aikin tare.
Wani almajiri yayi sallama ya shigo, duk muka amsa mishi. Ya durkusa a gefen Fatsu, yace “wai ance ana sallama da Na’ilah a waje!”.
Nayi kasake da zare a hannu ina kallon yaron baki a dage, wa na sani da zai yi sallama dani a garin Gashua ne? Inna ce ta tambayeshi inji wa? Yace “yace wai ace Magaji ne”.
Sai lokacin naji na sauke ajiyar zuciyar da ban san dalilinta ba, nace “kace mishi ina zuwa”.
Bayan fitarshi Fatsu ta kalleni cikin yin kasa da idanu, murya cike da gargadi tace “kinsan dai Yayanki ba zai ji dadin wannan magana ba ko?”.
Na kada idanu, “gaisawa ce fa kawai ba wani abu ba. Beside, babu wata magana a tsakanina da Magaji sai zumunci kawai da girmama juna”.
Tace “ai shikenan!”. Hijabina na saka na fita.
Magaji kusan zan iya cewa abokin Yaya ne, duk da dai ba aboki bane na kut-da-kut, they were more like classmates. Shekaru kusan uku da suka wuce ya nuna yana da sha’awar aurena, tun ma kafin mu hadu da Umar. Na sanar dashi ban shirya yin wani relationship ba a lokacin, yace ya yarda zai jira ni. Ni dai na fito fili na sanar dashi cewa bani da ra’ayin yin wata alaka data wuce ta mutunci dashi, yace babu laifi, ya amince. Amma lokaci zuwa lokaci ya kan yi min tuni, ko kuma nuna alamun har yanzu fa yana so na, ni kam sai dai in banzatar da maganar kawai.
Yanzu ma gaisawa kawai muka yi, ya sanar dani dama wucewa yazo yi, da yake jiya ya ga wucewar mu ta kofar shagon dinkinshi, shine yace bari yazo ya min barka da zuwa.
Muna tsaye anan Yaya yazo wucewa, na dan duka ina gaida shi, hararar daya daka min kadai tasa naji diyan cikina suna kadawa. Ya ba Magaji hannu suka gaisa yana ta wani basarwa, ya shige cikin gida.
Yana bada baya Magaji ya dube ni yana dan yin murmushi, “to ranki ya dade, bari in koma shago, sai wani lokaci kuma”.
Na gyada kai, “to Magaji, na gode”. Na shige ciki, shi kuma ya wuce.
Ina yin sallama a gidan, Yaya ya taro ni da fada, “wato Na’ilah kunnen kashi ne dake ko? Sau nawa ina fada miki na hana ki tsayawa da Magajin wannan?”.
Nace “ni fa Yaya babu abinda yake tsakaninmu dashi sai mutunci kawai, zuwa ne yayi mu gaisa fa ba wani abu ba!”.
Murya cikin fada yace “koma menene, na fada miki na hana. Kuma wannan shine gargadi na karshe da zan miki akan wannan maganar, idan na kara ganinki dashi a tsaye, kinsan hakan ba zai miki dadi ba. Kina ji na?!”. Ya shura kafa ya bar gidan tun kafin in ce mishi wani abu.
Na turo baki ina satar kallon Fatsu da take sakar ta kamar bata san abinda yake faruwa ba. Na kara turo baki na wuce daki ina dira kafa.
Washegari a Damaturu na wuni gidan Inna Talatu. Da yamma Hafiz, babban danta namiji ya biyo ni muka dawo gida. Sana’o’in shi yake yi a garin Gashua da sauran kananun garuruwa da kauyuka dake makwaftaka da Gashua.
*
Kwanaki bakwai nayi a Gashua ina shan hutu na. Da za’a tambayeni menene ainihin ma’anar hutu? To ni zan ce hutu a gaban Fatsu da Yaya ne hutu.
Nan kadai ne zan yi rayuwata yadda naga dama ba tare da an juya ni ba. Babu abinda yake burgeni da zama a Gashua sai gani na tare, kuma lullube da dangi, duk inda na juya sune. Babu ranar banza da wani nawa ba zai yi sallama ya shigo gidan Bako ba, ko kuma ni ban je naga wani nawa ba. Wannan kadai, ni abin dadi ne a gareni. Ina son dangina, musamman fannin Mama.
Dangin Babana da yake suna da rufin asirinsu daidai misali, kuma da yake babu wasu na kusa, daga diyan kawunnai sai kannen kakanni. Idan kaje gidajensu sai su yi ta wani daga hanci suna shan mur, ko suna zaton rokonsu kaje yi ne? Shi yasa wasu lokutan idan naje Gashua bai fi in leka su sau daya ba, sai dai ko idan biki ake yi ko wata hidimar.
Yau kauyen Alkali muka je ni da Sailuba. akwai wata kanwar Babana, from another father da take aure acan, sunanta Fatima amma Juma ake ce mata. Duk cikin dangin Baba ita kadai ce mai kirki da kuma zumunci. Yawanci idan harka a gidanmu ta tashi, musamman idan su Anty suka haihu, ita kam tana zuwa. Haka idan nazo Gashua, watarana har takanas take yi tazo nan mu gaisa. Shi yasa nima bana zuwa ba tare dana leka ta ba.
Kayan dana kai wa diyanta, yawancinsu wadanda suka min kadan ne na kai musu, sai mazan dana shiga kasuwa na samo musu, tayi ta godiya yadda kasan harshenta zai fadi kasa.
Yini guda muka musu, musamman da yake yau kasuwar garin take ci, muka shiga mu da Hanne babbar diyarta da take kai tallar nono. Rana ta dan fara alamun faduwa lokacin da muka yi sallama dasu zamu tafi, suka ciko mu da tsarabar kayan kauye cike taf da buhu.
Kasancewar Fatsu ta min fadan jimawa a unguwa yasa ko gidan Sailu ban shiga ba na wuce gida.
Bako yana kofar gida yana alwalar sallar magriba, na durkusa na gaida shi, kai kawai ya gyada min, na mike na shige gida. A gidan ma itama Fatsu alwalar na tarar tana yi, na shiga daki na ajiye kayan hannuna na fito nima na daura alwalar.
Tun wajen karfe tara na kwanta saboda gajiya da nayi saboda mun sha yawo a garin Alkali yau. Har barci ya fara dauka ta na jiyo muryar Yaya a kofar dakin Fatsu suna magana shi da ita, Fatsu take cewa “aikuwa ta dade da kwanciya, idan ba sa’a ba ta riga tayi barci zuwa yanzu”.
Yace “to gashi ki ajiye mata, nima a hanya na sayo shi, kin santa da son kifi soyayye”.
Ai jin an ambaci kifi sai nayi wukit, na hantsalo daga kan gado. Kawai sai gani na suka yi a gabansu. Fatsu ta dafe baki, “kai wannan ‘ya, Allah ya kyauta miki ke kam. Nayi zaton kinyi barci?”.
Na ja ledar dana gani a gabanta ina murmushi, nace “na dai fara, amma bai yi nauyi ba. Yaya ya hanya?”.
Yayi dariya, “lafiya lau Na’ilah.. Bari in karasa gida ni”. Muka mishi sai da safe ni da Fatsu, ya tafi ni kuma na tashi na shiga daki na dauko yaji na koma na zauna. Kifin na bare, ina cire mana kayar ina dangwala shi da yaji ina ci, Fatsu kam haka nan taci shi. Ganin Malam bai shigo ba yasa na kai mishi nashi daki.
Ruwa na kora mai sanyi na koma daki na kwanta.
Wayata ta fara haske wanda yake nuna min ajiyayyen sako da ban daga ba, nayi unlocking wayar ina dubawa. Umar ne da Janan. Shi yana tambayar yadda na wuni, ita kuma tana tambayar ko naji komawa makaranta nan da kwanaki hudu? Na maida mata amsar na sani, shi ma Umar din na maida mishi reply din.
Na koma kan gadon na kwanta, zuciyata cike da tunanin Umar din. Kwana biyu bamu yi waya dashi ba, ko musayar sako, to da yake ma sau tari haka muke kasancewa yasa ban cika damuwa ba.
A hankali tunanin nawa ya gangaro kaina, jibi nake so in koma gida saboda in fara shirye-shiryen komawa makaranta. Kasancewar shekarar karshe zamu shiga, nasan projects da sauransu ba zasu bari in kara samun hutu mai tsayi kamar wannan ba.
Tuni kewar su Fatsu ta fara lullubeni. Nayi fatan ace na hado duk wasu kaya da zan bukata daga gida, da bari zanyi kawai in wuce daga nan tunda dama na saba yin hakan. Amma yanzu babu damar yin hakan, su ma nasan kila tsakanina dasu sai dai ko in Yaya yaje Kano ko Kaduna, ya biya ta wajena. Amma na kudirta idan muka samu hutun sallah wannan karon anan zan yi shi. Da wadannan tunanikan barci ya daukeni.
Washegari na shiga yin sallama da mutanen garin Gashua, wasu dangin ma sai a ranar na leka su kasancewar Mama na Allah ya albarkace su da dangi Masha Allah.
Ranar da zan tafi kam ban ma fara shirin tafiya ba sai dana karya. Sai wajen karfe tara sannan na mike, tuni kayana sun nabba’a a bayan mashin din Yaya. Bayan akwatina, akwai jakar Ghana madaidaiciya shake da tarkacen tsaraba da aka hada min wadanda zan koma makaranta dasu, dangin busasshen kifi, cukwi. Akwai wani abu da Iya Lami take yi wai shi ‘mitimis’, da nikakkiyar danyar gyada ake yi da sugar, sai a yanka in cubes kamar dai tuwon madara. Shima sai data cika min katuwar leda dashi. Haka dai abin yake kasancewa a duk lokacin da naje Gashua.
Kaunar da mutanen nan suke nuna min is so overwhelming da take saka ni zubar da hawaye a lokuta da dama. Ko yanzu da Yaya ya raka ni tasha, ya biya min kudin mota tare da damka min wasu a hannu in case zan bukace su, ga kuma hannuna rike da plastic rubber da Sailu ta soya chips din dankali da sauce din kwai ta bashi ya kawo min, hawayen nake sharewa, ya dafa kaina yana murmushi fondly, cike kuma da tsokana, yace “daina hawayen mana. Bansan wanda ya shagwaba ki da yawa ba Illo, har sai yaushe ne zaki girma ke kam?”.
Nayi murmushi ina share hawayen, yana tsaye na shige mota, da yake karama ce ba bus ba, tuni ta cika. Yaya yana tsaye yana daga min hannu muka fita daga cikin tasha din. A mota na rubuta text na turawa Janan da Umar don su san da tahowata, na maida kaina jikin kujera na kwantar.
*
Wasu masallatai har sun gama sallame sallar isha’i lokacin dana yi sallama tsakar gidanmu. Motar Baba tana fake a nan bayan dakin su Aliyu inda ya saba ajiye ta, hakan ya sanar dani yana gida. Babu kowa a tsakar gidan, don haka na ja akwatina na shiga daki.
Maryam dake kan abin sallah, tayi tsalle daga jin muryata ta dafe jikina tana ihun oyoyo, ina tunanin jin ihunta ne ya janyo hankalin su Auwal, sai gasu sun fado dakin da gudu su ma suna nasu ihun murnar. Nayi dariya tare da zama daram a kasa sakamakon jin suna neman kayar dani a kasa. Sai da suka gama ihun murnar, na bude jakata na ciro cakuletin eclairs na damkawa kowannensu a hannu, sannan duk suka watse.
Na tashi na shiga bandaki na dauro alwala. Kasancewar an fara yin ruwa, iska mai sanyi yake kadawa sakamakon ruwa da aka yi da rana.
Sai da nayi sallah sannan na dauki wayata na sanar da su Yaya da Fatsu karasowa ta gida lafiya.
Na fita na leka dakin su Anty duk na musu sannu da gida. Nasan cewa in ba lekawa nayi ba, babu wadda zata damu da ko furta min kalmar sannu da hanya ne. Zamu iya haduwa dasu a tsakar gida ma gobe su nuna kamar dama can ina gidan.
Ina gamawa dasu ban bata lokaci ba na nemi makwancin barci, ina yada kai akan katifa kuwa, barci yayi awon gaba dani.
*☆⋆06⋆☆*
“Ni dai yanzu haka maganar da ake yi babu kudi a hannuna Na’ilah, duka-duka shekaranjiya na biyawa yara kudin school fees su ma, ga kuma sauran hidimar gida dake kaina, ta ina kike zaton zan lalubo naira kusan dubu arba’in cikin kwana biyu?”.
Na kifta idanuna kamar wanda abu ya fada cikin idanun, tunda ya fara maganar kallonshi kawai nake yi babu ko kiftawa saboda jin maganganun da suka fita daga bakinshi, sai dana hadiyi yawu na jika makoshina da naji ya bushe, nace “amma Baba tun da nazo dama na fada maka, kuma yanzu idan ban biya kudin akan lokaci ba, ba zan taba samun accomodation ba!”.
Ya kalleni a kaikaice, “to yanzu ya kike so inyi ne? Tunda nace miki bani da kudi a hannuna, ta ina kike tunanin zan je in lalubo su?”.
Ramata dake gefenshi ta kalleshi tana wata kwarkwasa, “kasan akwai kudin anko na dake kanka ko? Kuma bikin satin sama ne”.
Ban san lokacin dana jefa mata harara ba, aka yi sa’a ta kalloni muka hada ido, da sauri ta janye kanta daga kallona, nayi kwafa, can kasan zuciyata ina raya ‘kin kyautawa kanki!’.
Baba yace “to bari mu jira zuwa ranar laraba mu ga yadda hali zai yi”. Daga wannan magana sai ya dauke kanshi gabadaya daga inda nake, clearly dismissing me, na mike gwiwa a salube na fita daga dakin.
Gefen katifa na laluba na zauna, Allah ya so ni Maryam bata gidan, wai ta tafi suna gidan kawarta, shigar banzar dai dana mata magana akai, ita tayi. Binta da kallo kawai nayi lokacin da naga ta fito sanye da riga da siket na atamfa, an musu wani irin dinki na cin mutunci. Siket din ya matseta tsam, kamar in tayi nishi mai karfi zai yage, rigar ma haka, ga wani dan iskan ‘show me your back’ shima da aka yi, tayi daurin dankwali mai nadin doughnut a goshi, ga gyalen nan kamar matacin koko saboda shara-shara da yayi ta dora a wuya. Ban ma yi tunanin yi mata magana ba, har yanzu fushin abinda Aliyu yayi min kamar sabo yake a cikin raina, ban shirya shiga wani bacin rai makamancin haka ba so soon kuma. Koma dai menene tayi, Allah ya gani, nayi iyaka bakin kokari na. Magana akan shigar banza irin haka ba tun yau nake yiwa Maryam ita ba, tun kafin ta fara kirgan dangi muke haka. Sai kuma ta nuna ta fahimta, taji maganata, daga baya sai uwar ta kara zuga ta dai, sai ta koma cikin ruwa tsamo-tsamo.
Allah yasa for now dai, ita kadai ce budurwa mai tasawa a gidan, sauran duk suna kan hanya, ina kuma fata kafin su gama yin hankalin kansu, su dauki irin dabi’arta, zata daina.
Rashin Maryam a dakin shi ya bani damar jingina da bango, na tsunduma cikin tunani mai zurfi. Yakamata ace na saba da abinda Baba yake yi min, sai dai, kamar yadda ba’a taba sabo da wahala, haka ma ba’a sabo da bacin rai. Musamman idan wanda yake haddasa maka hakan ya kasance majibanci, kuma majingini a gareka, wanda kake ganin zaka iya rab’a a duk lokacin da komi ya yaye maka baya, kuma ya tallafa maka. Sai dai no, ko kadan ba hakan take ba.
Lokacin da zamu tafi registration dinmu na farko, haka Baba yayi min wannan delaying din. Sanadiyar haka na rasa accomodation a cikin hostel, wata kawarmu da muka yi sbrs da ita, ita tayi squatting dina. Believe me when I say, it wasn’t fun at all. Ban taba raina kaina ba sai a wannan lokacin, ban taba jin dadin rayuwar gidanmu ba, in fact, ni zan iya dukan kirji in ce rayuwar makaranta ta fiye min rayuwar gidanmu, amma a wancan lokacin sai dana fara rethinking wannan tunani. Sai dana gwammace rayuwar gidanmu sau dari akan wannan rayuwar. At least a can, ina da wajen da zan kira dakina, sannan duk lokacin da dare yayi, a gida nasan cewa ina da wajen da zan kwantar da hakarkarina, amma ban da nan.
Haka taci gaba da faruwa, for once, ban taba biyan makaranta akan kari ba, kullum, kuma kodayaushe, sai na kara kwanaki ko satika, duk da cewa kowani lokaci nakan fadawa Baba da wuri yadda zai tanadi kudin, but no, kodayaushe akwai uzirin da zai ratso ya shiga ta cikin kudinnan. Ban sani ba, daga gareshi ne ko daga matanshi, ko kuwa in ce matar shi? Allah ne masani.
Yaya Mudatthir, Allah ya albarkaci rayuwar shi. Da ba don shi ba kam, ban san yadda karatuna zai kasance ba. Idan Allah ya taimaka yana da kudi, shi yake daukar jigilar registration dina, daga baya in Baba ya turo, in tura mishi, duk da a yawancin lokuta ya kan dawo min dasu ko kuma yace in barsu, sai dai in maida mishi rabi ko ya dawo min da rabi.
Ko last year, Allah ne yasa Yaya Jameel, yayan Janan, da yake lecturer ne a cikin makarantar, ya bata daki, Yaya ya hanata zama, ni kuma ta bar min shi.
Da tunanika iri-iri na kwanta. Sau tari sai inji gabadaya karatun ya fita a cikin raina, inji kawai gwanda in hakura dashi, in huta da bakinciki da takaicin da nake kwasa daga wajen Baba. Sai dai wasu lokutan, sai in ga daurewar tafi. Musamman idan naga cewa shine kadai gatana a yanzu. Karatun shi zai tallafa min, in tsaya akan kafafuna ba tare dana jingina da wani ba. Idan nayi hakuri, na dan lokaci ne. Komi wucewa zai yi, ya zama tarihi, kamar bai taba faruwa ba. At least, abinda nake fata kenan.
*
Washegari da dare, mun zagaya nan bayan gidanmu ni da Kulsum dubo wata Hassana wadda muka yi aji daya da ita a makarantar Islamiya. A hanyarmu ta dawowa, muna tattaunawa game da matsalolin da ita Kulsum din take fuskanta daga tsohon mijinta.
Ya fara mata zarya akan cewa yana so ya amshi Muneerah daga wajenta, ita kuma tace gaskiya bata son bashi ita.
Ni kaina shawarar dana bata kenan. Nace idan da yadda zasu yi akan haka, gaskiya suyi, ya bar mata diyarta ta tarbiyantar da ita a gabanta. Tunda ma ba maganar aurenta bace ta taso, ko iddah bata gama ba, balle yace ta wannan dalili yake son karbar ta.
Wahalhalun dana sha a hannun kishiyar uwa, shi nake guje mata. Duk da cewa ni rashin mahaifiya ne ya jawo min, ita tata mahaifiyar tana raye. Kuma tana ji tana gani, haka za’a fi karfinta akan diyarta. Bana fata ko makiyina ya dandani kwatankwacin abinda na dandana. Abinda na dinga tunani a cikin raina kenan, ban furta mata hakan ba amma.
Koda kasancewarta kawata, ko ma ince aminiya, tarihin gidanmu, da irin zaman da nayi da mutanen gidan, dama wanda nake yi, ba duka ta sani ba. Ta dai san wanda kunnenta ya jiye mata, kuma idanunta suka gane mata, shikenan. A tunanina, tado abinda ya wuce, yake kuma sosa ran mutum, duk ba solution bane. Hakan babu abinda zai haifar sai ma wani karin bacin rai, hakan zai sa ka kullaci mutane a cikin ranka, kila dan mutuncinta da kake gani nasu ya zube. Babu abinda zai sa, kuma babu abinda zai hana.
Daidai bayan gidanmu, na hangi wata yarinya Lubah, yar dakin Ramata ce. Anan cikin unguwar take, duk wata gulma da tsegumi daya taba gidanmu, daga gidansu yarinyar yake fara fita.
A durkushe na ganta, kamar tana tona kasa ko kuma wasa take yi? Sai waiwaye take yi da kalle-kalle, kamar dai wadda take tsoron wani ya ganta. Na dan yamutsa fuska in suspicion, kamar zan karasa in ga abinda take yi, sai kuma naga hakan ba hurumina bane, tunda ba shiga harkarta ko ta mutanen gidansu nake yi ba. Muka wuce ta.
A tsakar gidan su Kulsum muka zube ni da ita akan tabarma, muka cigaba da tattaunawa. Mun yanke shawarar zata je ta samu Kawunta tayi mishi bayani, zai je ya samu iyayen Mukhtar din sai suyi mishi magana. A cewar Inna, hakan zai fi kawai, in yaso idan ta tashi yin aure, ko kuma Muneerah din ta fara mallakar hankalin kanta, sai ta koma din. Tunda dai duk inda za aje a dawo, gidan mahaifin nata dai nan ne mutuncinta. Da wannan na musu sai da safe na wuce gida.
☆
Washegari Laraba, nayi sa’ar samun Baba kafin ya tafi wajen aiki. Na gaida shi, ya amsa yana kora shayin da Alawiyya ta hada mishi, yayin da Ramata take gefenshi zaune a hakimce. Yadda nayi zaune a gabanshi, nasan cewa yasan dalilin yin hakan, amma ya basar dani.
Ban yi fushi ba, na kaskantar da murya, nace “Baba zancen registration dina?”.
Daga farko shiru yayi kamar ba zai yi magana ba, can kuma yayi gyaran murya, yace “kudin nan naki fa sai dai kiyi hakuri sai zuwa satin da zai kama. Ranar litinin zan biyawa kaninki kudin waec da neco, abubuwan zasu yi min yawa!”.
Wani abu daya kusa bani dariya shine, jarabawar waec da neco zata iya jira har nan da watanni biyar zuwa shida masu zuwa, tunda dai ba’a fara zancen yin ta ba balle akai ga saka deadline din wadanda basu biya ba zasu rubuta jarabawar ba da sauransu. Naso in tunatar dashi hakan idan ma mantawa yayi, yadda naga ya zubo min ido ne yana jira yaji ta bakina, Ramata ma da Alawiyya sun zubo min nasu suna jira inyi magana, kila dalilin haka Baban ma yayi fushi, satin samar ma yazo yace bashi da kudi, yasa na hadiye duk takaicina da kududun daya makale min a makoshi, nace “to babu laifi, Allah ya hore!”. Na tashi na kara gaba. Banyi kuskuren ganin yadda suka bini da kallo baki a dage ba.
Magana ta gaskiya ita ce, na gaji da takaicin da suke guma min. Daga Baban har su. A kullum, kuma a kodayaushe, hidimar kansu data ‘ya’yansu ita ce ta farko a idanunsu, koda tawa matsalar tafi bukatar agajin gaggawa, haka za ayi shagulatin bangaro da ni da lamarina, har sai an biya musu nasu bukatun. Idan kuma nayi magana, sai cibi ya zama kari. All tables will turn, and bets will be off. Sai laifi ya dawo kaina, ace na cika bakin ciki, su ce bana son cigaban su ko na ‘ya’yansu, su ce bani da godiyar Allah, daga karshe kuma su zo suyi sanadin wannan abin ba za’a yi shi ba kenan. Idan ma anyi, to a kurarren lokaci ne.
Saboda haka naga, meye amfanin yin maganar? Babu abinda hakan zai karas dani sai bacin rai. Meye kuma amfanin sanya maganar a cikin raina, again, sakamakon hakan dai bacin rai ne. Don haka nayi wurgi da maganar cikin kwandon shara, naci gaba da harkokina cikin kwanciyar hankali.
Sai dai Baban yana fita, sai ga Ramata ta fiddo dankareren Swiss lace daga daki, ta fito tsakar gida tana ba danta Aliyu da bai je makaranta ba, labarin jiya Baba ya bata kudin, dubu ashirin da biyu ta sayo, ya kara mata da dubu uku kudin dinki. Tace yayi maza-maza yazo ya kai mata shi wajen telanta ya watsa mata dinki na rashin mutunci, na shiga taron manya.
Nasan duk don inji haushi take yin hakan, sakonta kuma ya shigeni yadda yakamata, naji haushin. Sai dai wannan karon ma maimakon magana, sai na kada kaina na shige daki. Ai sai ina wajen sannan zata yi tunanin tsokano ni ko? Sai dai ga yadda na ga fuskar Alawiyya, to ta shaka da yawa. Nasan a cike take dam, kiris take jira ta fashe. Nasan kuma da Baba ya dawo zata tare shi da maganar, idan Allah ya taimaketa, ya dorata a kanshi itama ya siyo mata lace din ko ya bata kudin yace ta dinka. Wanda kuma da kyar ne, hakan sau daya yake faruwa a gidanmu a shekara.
A tunanina, idan mutum ya sai wa matarshi wani abu, itama dayar tana da hakkin ya sai mata irinshi, ko kuma ya bata adadin kudin daya batar wajen sayen abin? But no, banda gidanmu. Ban taba ganin haka ba, koda wasa.
Yawanci idan abu makamancin haka ya faru, sai dai hakan ya kare ga fada kawai. Ita Alawiyya bata hakura, kullum aka yi haka sai ta bukaci itama a bata nata kason, lokuta daidaiku ne Baban yake bata, basu fi a daga hannu a kirga su ba.
Wani lokacin tausayinta dana ‘ya’yanta yana cika raina, amma nafi tausayawa Ramata dana ‘ya’yanta.
Wunin ranar haka nayi shi smoothly. Da yamma ina kicin ina tuka tuwom dare, Maryam ta fado kicin din da sauri, wayata dana bata tayi kallo tana ringing a hannunta, ta miko min. Na duba naga mai kiran Janan ce, da sauri na daga ina murmushi.
“Hi…”, na furta a hankali, da niyar gaisuwa.
Tace “hii yourself, yaushe kike da niyar dawowa makaranta ne? Ni fa har na dawo Zaria”.
Na zaro ido cike da mamaki, “wow, lallai kina kaunar Zaria da yawa. Ni yanzu haka ban san ranar dawowata ba”.
Tayi dariya, “bana son shakiyanci wallahi, meye abin so a Zariar ne? Kinsan da maganar council exams dinmu ana tunanin kamar upper week fa za’a yi. Kinsan wasu lecturers har sun fara shiga aji kuwa?”.
Na dafe kai, “damn! Subhanallah! Daga dawowa?”.
Ta sake yin dariya, “exactly abinda na fada Saboda haka ki fara tattara naki-ya-naki, ki ciccibo kanki ki taho wallahi. Gobe in shaa Allah zan shiga in ga yadda ake ciki”.
Nayi shiru ina kallon wutar da take ci bal-bal a cikin murhu, da kyar na samu muryata, “ina tunanin kuwa sai dai inyi karatuna a gida. Ni da Zaria maybe sai upper week din”.
Tuni naji ta rikice, “ban gane ba, mai ya faru ne? Baki da lafiya ne? Ko wani ne a gida bashi da lafiya?”.
Nace “sam ba haka bane, ke da kika san banyi registration ba?”.
Tace “sai aka yi yaya?”
Banyi mamaki ba, nasan hakan zata fada, nace “sai bani da wajen zama. A kanki zan zauna in na dawo ba’a riga an bani daki ba?”.
Tace “ko baki zauna a kaina ba, kin zauna a dakina. Ki zo sai ki zauna dani kafin ki biya!”.
God!, wai komai ma sai nayi guessing dinshi daidai? Shima nasan abinda zata fada kenan, nace “nop… Nagode, amma zan jira a gida har sai na kammala komi sannan”.
Shiru ya biyo baya, again, nasan fada ne zai biyo baya, illa kuwa,
“wai Na’ilah, ni ce baki son zama dani ko kuwa me? Kada ki manta, last time ma abinda kika min kenan, hutun kirsemeti wannan na kwana hudu da aka bamu kin zuwa kika yi muyi a gidan Yaya, kika zauna ke kadai a daki kamar mayya. Yanzu ma kuma kina fada min wai zaki zauna a gida, baki son zama dani ne?”
Na kai hannu ina sosa bayan wuyana, ni dama nasan za’a rina. Nace “kamar ya bani son zama dake, ya ma zaki ce haka?”.
Wannan karon muryarta ta fara dagawa cikin alamun fada, tace “haka ne mana! Kada ki manta, duk lokacin dana miki tayin kizo mu zauna, ko wani abu makamancin haka, sai ki hau kame-kame kina wani kawo excuses. Me kike so in zata, idan ba haka ba?”.
Na girgiza kaina kamar ina gabanta, “wallahi ba haka bane Janan, ba haka bane. Kin san yadda muke sarai da matar Yaya da kuma kannenta, bana son harkar da zan je gidan mutane in zauna, wata magana da bata dace ba tazo ta fara fita. Ko kuma rashin hakurina yasa in zo inyi abinda zai janyo mana matsala, shine kawai”.
Da alama maimakon maganar ta sanyayar mata da rai, sai ma ta kara tunzurata, tace “to akansu zaki zauna ne da zasu yi korafi? Idan kinzo din duka kwana nawa ne zaki yi ki wuce hostel abinki? Ba lallai kullum sai kun hadu dasu ba!”.
Nace “duk da haka Janan, gaskiya kiyi hakuri kawai. Zan kara turzawa dai in gani, tunda jarabawa ce kawai, zanyi karatuna a gida, sauran lectures idan na dawo I’ll catch up with you”.
Dan siririn tsaki taja, “ai sai kije kiyi tayi, sarkin kafiyar kai. Ba’a tana nuna miki gabas ki bi, sai dai kiyi yamma!”. Ta katse wayar tana gunguni. Murmushi na saki a hankali ina girhiza kai, Janan kenan!.
Sai dai ba’a yi mintuna talatin ba, sai gashi ta sake kirana. Na daga da sauri, sai dai tun kafin inyi magana ta riga ni, “to Yaya dai yace ki hado kan kayanki ki taho gobe!”. Kafin ince komi ta sake kashe wayar, na bi wayar da kallo baki a dage.
Dawowar Maryam yasa na mika mata wayar, na cigaba da tukin tuwona cike da sake-sake. Wani bangaren na zuciyata yana fada min inje, wani kuma yana ce min a’ah. Na farko ni dai ban taba zuwa gidansu na kwana ba, na biyu ga yar tsamar da muke yi da kanwar matarshi nasan da kyar ne idan watarana, duk kawar da kaina, na biye mata mun raba hali ba, sannan ni fa bana son zuwa gidan mutane haka kawai in zaune musu. Ni duk wani abu da zai sa in zama uncomfortable bana son shi ko kadan.
Na gama tuwon na gyara kicin din tsaf, wanke-wanke na barshi sai gobe don dare ya riga yayi. Kulolin dana zubawa Baba nashi, na cicciba na tafi zan kai dakin Alawiyya da take yin girki. A gefen gado na sameta a zaune dafe da gefen cikinta, na ajiye kayan a kasa, na kalleta cikin kulawa nace “Anty baki jin dadi ne?”.
Ta dago ta kalleni, fuskarta na yamutsewa cikin nuna jin ciwo, tace “babu komi, cikina ne yake dan juyawa, amma zan sha magani”.
Sai dai jikina ya bani ba wannan bane, zata iya yiwuwa ciwon cikin ne, amma ba na shan magani bane. Jikina yana bani wani abu ne daban. Kai kawai na gyada mata, na mata fatan Allah ya bata lafiya na fita daga dakin.
Ina yarinya kimanin shekaru takwas, na fara ganin haka. It was weird. Wani lokacin kalar idanun mutum ce zata canza, wani lokacin hayakine zan ga yana fita daga waje ko jikin mutum, wani lokaci kuma jikina ne kawai zan ji ya bani. Wanda aka yiwa sammu, ko wanda yayi sammun, da wajen da aka binne ko aka kona abinda aka yin, cikin ikon Allah duk ina iya gani.
Mama Allah jikan rai, farkon abin tace iska ne, Malam Bako yace ba lallai sai shafar aljanu bane yake kawo hakan, Iko ne kawai da wata hikima ta Ubangiji ba wani abu ba.
Koma dai menene, ina godewa Allah. Zaman Mama da Ramata na sha ganin ire-iren abubuwan nan. Wasu lokutan a bandaki, daidai wajen tsuguno, sai dai in ciro layoyi, wasu lokutan kofar dakin Mama, watarana na Baba, sai dai in daukesu kawai in kaiwa Malam. Ko Mama watarana bana fadawa balle ta sani. A yanzu haka, bayan su Malam da Yaya, babu wanda yasan da hakan.
Ina shirin kwanciya, Janan ta sake kirana, a sanyaye na daga. Tace “har kin gama shirin ko?”.
Ni sai ma ta bani dariya, nace “wani irin shiri kuma kike magana a kai?”.
Tace “dawowa mana”.
Sai dana dan yi shiru kafin na fara magana, “look Janan….”
Tayi saurin katseni, “a ganina ko yankar namanki za’a dinga yi, hakan ba zai hana ki k’i zuwa ki zauna dani ba. Haba Na’ilah, ba fa cewa aka yi zaman har abada ba zaki yi, duka satika nawa ne, zasu kai biyu? Ki zo mu zauna muyi shirin exams dinmu, mu fara fuskantar projects da suke tunkaro mu. Kin san idan kika zauna a gida babu abinda zaki iya yi, na riga na yiwa Yaya magana, ya kuma ce babu matsala zaki iya zama, to me kike jira kuma? Matar Yaya da kannenta duk ba matsala bace, ba fa a gidan zaki dinga wuni ba!”.
Na kada kai gefe guda, ta wani bangaren haka ne, it’s for my own good. Don haka na daga baki nace “to zan sanar da Baba, amma sai ranar Lahdi zan taho”.
Ihun murnar data saki shi ya sake bani dariya, na girgiza kaina kawai. Tace “ko ke fa? Sai ki fara shirin tahowa”.
Nace “in Allah ya yarda”, muka yi sallama da ita, na kashe wayar.
Koda na fadawa Baba, haka yace “Allah ya kaimu kawai”. Babu tambayar yadda mutanen gidan suke, ko yadda ita yarinyar take, kawai to yace. Na koma daki na fara hada kan kayana. Wanki na fara yi.
Rana ta fara yi lokacin da naji wani irin gurnani mai kama da kuka yana fitowa daga dakin Anty Alawiyya. Da sauri na saki kayan da nake wankewa na fada dakin, kwance rub da ciki a tsakiyar dakin, itace dafe da cikinta tana ihun kuka. Na tallabota jikina ina tambayar lafiya? Amma ta kasa magana. Yadda take yi har numfashinta yana alamun daukewa, yasa naji wani irin tausayinta ya lullubeni. Na tashi na dauki kofi na debo ruwa, nazo na dinga mata tofi a ciki. Ayoyin tsari da kariya na karanto na tofe mata a ciki, na tallabo kanta na dura mata ruwan, wani yana zubewa a kasa haka nan na dura mata, sauran ruwan da tayi kuma na shafe mata cikinta dashi.
Mintunanmu kusan arba’in a haka, sannan ciwon ya fara lafawa. Ta fara zufa kamar wadda ake kwarawa ruwa. Na tashi na kara mata iskan fanka. Data dan dawo cikin hankalinta na taimaka mata ta koma kan gado ta kwanta, ni kuma na fita. Duk wannan abin da ake yi, Ramata tana tsakar gida a zaune tana jin rediyo abinta. Nayi kwafa kawai lokacin da muka hada ido da ita.
Duhu yana fara yi, na salube jiki na fita daga gidan. Inda naga Lubah jiya naje na duka ina haskawa da fitila har na hangi inda nake nema, hannu kawai nasa ina tona wajen kasancewar kasa ce a wajen. Hannuna ya fara cin karo da wasu irin duwatsu da ban taba gani ba, wasu irin kala su ba bakake ba, kuma ba jajaye ba. Sai dana ciro kusan guda biyar, sai kuma naga wata tsohuwar wuka, gashin dabba kamar na Tunkiya dankare da wukar gaba da baya. Nayi bismillah na daukesu na nade su gabadaya na maida kasar wajen na rufe kamar babu abinda ya faru, na shige gidansu Inna.
A gaban Inna na zubesu ina mata bayani, ta hau tafa hannuwa tana salati. Tace “ai wannan sai dai a kona, kai Allah ya kiyashe mu da rashin tsoron Allah irin na mutane. Allah kadai yasan mugun abin da yake kunshe da wannan abu!”.
Nace “duwatsun fa? Ya za muyi dasu? Tunda ba lallai su kone ba?”.
Tace “to sai dai a nunawa Malam ya gani, sai muji abinda zai ce!”. Anan take muka kona wutar, wata irin kalar wuta data dinga fita daga jiki, ga wani irin wari kamar na bunsuru da take fitarwa, haka dai muna tsaye suka gama konewa kurmus. Wukar Inna ta dauka ta hada da duwatsun nan. Sai dana yi sallah sannan na koma cikin gida.
A haka dai na lallaba zuwa ranar Lahdi. Karfe goma na safe ina cikin tasha, bayan nayi sallama da mutanen gida.
*☆⋆07⋆☆*
Muna shigowa Zaria, kiran Umar ya shigo cikin wayata kamar ya sani. Kamar ma babu network a inda muke, saboda bana jin shi ta bangaren da yake, na gaya mishi bana jin shi amma idan na karasa gida zan kira shi, na kashe wayar.
Muna shiga tasha mota ta samu waje tayi parking. Na biyo jerin wadanda suke fitowa, na dauki akwatina da jakata. Fita nayi daga tashar ina wurga idanuna ta tsallaken titin domin hango abin hawan da zan kira. Kamar wanda yake jira, ina fita, Umar yana tsayawa a gabana. Yayi murmushi lokacin da yake fitowa daga motarshi, nima na maida mishi martanin murmushin. Ya tsaya a gabana yana kallona, “welcome sweetie!”.
Na saki dariya a hankali ina kallonshi cikin girgiza kai, “is this suppose to be a surprise welcome?”.
Yayi murmushi, yace “ko kadan, na kira ki in fada miki na fito daukar ki sai baki ji na… Maza ki shigo mu wuce kada ki zube min anan saboda gajiya!”. Ya karasa fadar haka yana bude min kofar gidan gaba.
Na silala jikina cikin motar ina murmushi, “tafiyar merely awa hudu ba zata gajiyar dani haka ba, Umar”.
Ya maida murfin motar ya rufe tare da ciccibar akwatina da jakata yasa a bayan booth, ya zagayo ya shiga yayi wa motar key, sai a lokacin ya juyo ya kalleni, “sai ina?”.
Nace “gidan su Janan”. Yayi jim, kafin ya juyo ya kalleni, fuskarshi na nuna alamun tambaya, cike kuma da mamaki. Na ajiye ajiyar zuciya, cikin alamun bayani nace “a can zan zauna zuwa lokacin da zan samu wajen zama”.
Yace “shine baki fada min da wuri ba? Da baki je wajen Mommy kin zauna ba?!”.
Na daga baki ina kallonshi kamar wani wanda ya fitar da sabon kai, ya kyalkyale da dariya yana dukan sitiyari, “just kidding!”.
Kai kawai na iya girgizawa. Abin ma sai ya bani dariya. Kawai sai aga budurwa taje gidan su saurayi zama, babu aure kuma babu komi. A can kasan zuciyata ina tunanin ai ko da ace Mommynsu da sauran kannenshi suna so na, ba zan iya wannan danyen aikin ba. Har yau bamu gama clicking waje daya da yan’uwanshi ba, ban san dalili ba. Amma na fi danganta hakan a rashin sanin juna sosai da muka yi.
Ya juya baya yana lalube cikin wata leda har ya ciro gwangwanin maltina ya miko min, na amsa, sanyinta na ratsa hannuna. Na fasa na kafa a kai na daddaka, na ajiye numfashi in bliss, “God! Kamar kasan abinda nake bukata kenan!”.
Yayi murmushi kawai tare da jan motar muka tafi.
A kofar gate din gidan Yaya Bilal yayi parking din motar tare da kashewa. A kofar gidan, Halima da Salama kannen Anty Raheemah ne zaune a karkashin inuwar babbar bishiyar mangwaro kofar gidan, da alamu hira ce suke yi ko kuma shan iska kawai.
Na bude murfin motar na zura kafata waje na fita daga ciki, shima Umar din ya fito, duk suka bi mu da kallo. Na gyara zaman gyalena a kafadata ina kallonshi nace, “na gode Umar, bari in karasa ciki”.
Yayi murmushi, “it’s my pleasure!”
Zagayawa yayi ta baya ya bude booth ya ciro min kayana dake ciki, ya sake bude bayan motar ya fito da shopping bag ya miko min, na daga baki zan yi magana yayi saurin katseni, “snacks ne kawai da drinks ba wani abu”.
Nasa hannu biyu na karba ina mishi godiya, ya girgiza kai, “kila zuwa anjima idan na gama abubuwan da nake yi da wuri, zan biyo”.
Nace “Allah ya kaimu anjiman”.
Daga haka ya sake zagayawa ya shige cikin motarshi ya ja ya bar wajen. Na dauki akwatina a hannu daya, dayan kuma na dauki daya jakar da ledar da Umar ya kawo min na tunkari gidan. Strangely, naji bugun zuciyata ya canza, na danganta hakan da nervousness.
Haleemo ta kalleni tana murmushi, “ashe yau kike tafe? Sannu da zuwa, ya hanya?”.
Na dan saki tight murmushi, gajiyar dana kwaso tana kara lullubeni, nace “lafiya kalau, sannunku”. Na gaishe su gabadaya, a lokaci daya. Duk suka amsa min, na wuce cikin gidan.
Duk cikin kannen Anty Raheemah, har ma ita Rahimar, Haleemo ta fi su sanyin hali, shiru-shiru, da kuma rashin rawar kai. Shi yasa tamu tafi zuwa daya da ita. Har wani lokacin idan naje gidan mu kan dan hiranta da ita. Salama kam, tsabar tsiwarta da rashin mutunci yasa ranar farko da muka fara haduwa da ita muka kusa yin baram-baram. Bata da kirki ko kadan, zata iya tsaga tsakiyar idanun mutum, ko ma wanene shi ta yanka mishi rashin mutunci ta kara gaba. To kada kuma Adi taji labari, ita ta damesu ta shanye.
Ni dai fatana daya, in samu in gama dan zaman da zanyi dasu lafiya ba tare da wani rikici ba. Shi yasa na taho da kudiri, kuma da burin kai zuciyata nesa, kauda kai daga lamarinsu koda zasu taka ni ne, da kuma maida komi ba komi ba. A takaice dai, naci damarar ba banza ajiyarsu.
Ina bi ta kofar gidan, maigadin gidan, Ahmad. Dan matashine, kuma buzu, ya fito daga dan dakinshi da sauri yana min oyoyo. Murmushi nayi a gajiye na amsa, ya karbi akwatin hannuna da jakar ya biyo ni a baya har sashen Yaya Bilal din.
Na buga kofar falon gidan, jin alamun kofar a bude take yasa na tura kofar na shiga bayan na cire takalmina anan dan corridor din da suka tanada musamman saboda ajiye takalma.
Ahmad ya ajiye min kayana na sake dauka na shiga babban falon nasu bakina dauke da sallama. Raheemah da kawarta Adi na zaune suna kallo, gefensu gwangwanayen lemuka ne da plates wanda nake tunanin suka gama cin abinci daga ciki.
Babu wadda Allah ya bata ikon amsa min sallamar da nayi, sai kallo da dukansu suka fara bi na dashi, dani da kayan hannuna. Duk kokarin da nayi, sai da naji zuciyata ta fara rawa. Wani bangare mai rauni na zuciyata ya fara raya min over and over, zuwana nan gidan was a bad idea. Yana kara gaya min dalilai da dama, masu nuni da cewa gaskiya yake fada min.
Bisa wadannan dalilai dama wasu, yasa naji na fara tantamar anya ba zan juya inda na fito ba kuwa? Musamman tunda Janan bata riga ta san da zuwa na ba, zan iya ce mata wani uziri ne ya taso na gaggawa da yasa na koma gida, ko rashin lafiya, ko…!
Daidai lokacin da kofar dakin Janan din ya bude, ta fito daga ciki. Muna hada ido da ita, ta saki murmushin daya haskake mata fuska baki daya. Ban san dalili ba, naji wani kwarin gwiwa ya shige ni, wani over confidence dana rasa daga inda yake. Da sassarfarta ta karaso wajena, bata yi wata-wata ba, ta janyo ni ta rungume.
Sai data gama murnar ganina sannan ta sake ni, ta ja baya tana kare min kallo tun daga sama har kasa. “ke hutun nan dadi ya miki sosai fa da alama… Taho muje daga ciki dai, kiyi sallah ki huta!”.
Ta kama akwatin hannuna ta fara ja. A hankali na maida kallona ga su Rahima da har lokacin, idanunsu na kanmu kurr. Yadda suka yi yasa na fara tunanin anya sun san da zuwan bakuwar da zata zaune musu a gida na yan kwanaki kuwa? Nayi kokari na danne uneasiness din da naji a jikina, ko ma dai menene, tsakanina da Allah bana son wani abu yaje ya zo, a dinga cewa ta dalilina hakan ya faru.
Don haka na dage tun karfina na kakalo murmushin da ni kaina nasan cewa sun san na yake ne, gajiyar da nayi ta kara worsening abin. Nace “Anty Rahima, Adi, sannunku da gida!”.
Adi ta amsa da ‘lafiya lau’, yayin da Rahimar ta dauke kanta daga gareni ta maida kan Janan.
Cewa tayi wai, “wannan fa?”.
Nayi kwafa a boye, wani ‘wannan fa!’ sai kace wata shara ko kayan wanki, yadda kasan bata taba ganina ba.
Janan da bata kula da rainin wayon da tambayar tazo dashi ba, ko kuwa ta fahimta fuskewa kawai tayi? Cikin murmushi tace “Anty kawata ce fa, Na’ilah. Yaya ya fada miki zata zauna damu kafin ta samu wajen zama a cikin hostel”.
Antyn ta sake waiwayowa ta kalleni, fuska a murtuke, bakinta a tsuke, wanda ba karamin kokari nayi wajen danne dariyar data kamo ni ba sanadiyar ganin expression dinnan ba. Tace “zama damu ko ke?”.
Janan din ta danyi turus! Kafin ta sake yin murmushi ta cigaba da jan akwatin zuwa dakinta tana furta “muje”. Ban kara waiwayarsu ba na bi bayanta.
Sai dai ko daga inda nake, ina iya jiyo sautin muryarta da maganganun da take yi da dan karfi, obviously yadda zamu jiyota sosai, “shima ‘Baby’ da dan banzan kwashe-kwashe. Kawai babu dangin iya balle na Baba ka wani kwaso mana yarinyar da baka sani ba, ka ajiye mana a gida. Ko da wanne yake so mutane su ji? Da wannan yar rainin wayon kanwar tashi ko kuwa da wata bare kuma?”, tayi shiru tare da yin kwafa, “wai wani kafin ta samu daki! Ko kuma kwadayi ba!!. A dai zo a zauna din, aga idan wata tsiya za’a b’anb’ara daga jikinmu….”.
Sauran maganar ta mutu lokacin da muka shige dakin Janan muka maida kofar muka rufe.
Janan ta dubeni fuskarta cike da damuwa, “don Allah kiyi hakuri da abinda tace!”.
Na daga kafada cikin nuna alamun rashin damuwa, duk da cewa kawai don kada ta damu ne na fadi hakan, amma fa maganar kwadayin nan ta taba raina sosai, nace “menene abin jin haushi a maganganunta? Babu komi wallahi. Bari inyi sallah”.
Tace “to”, a lokaci daya kuma tana fita daga dakin. Ni kuma na fada bandakinta.
Ina gama sallah, ta hau turo min plates da bowls na abubuwa. Na kallesu ina kwashewa da dariya, nace “baiwar Allah ina kike so in kai wadannan abubuwan? Ba dai cikina ba ko?”.
Itama tayi dariyar, “na san ki da rashin son cin abinci idan zaki yi tafiya, na tabbata rabonki da abinci tun karin safe”.
Nayi shiru ban amsa ba saboda haka ne, shima karin safen da nayi shayi ne kawai, babu abinda na hada dashi. Daga shi sai maltina din wajen Umar. Hakan ya tuna min da ledar daya hado ni da ita.
Na tashi na nade abin sallar, na koma gefenta na zauna bayan na dauko ledar. Lemuka ne kala-kala was ciki, wasu juices wasu kuma fruit juices sai su tarkacen doughnuts da cupcakes. Tare muka ci abincin da ita muka gama, bayan mun gama ta fita da kwanukan abincin, yayin da na ciro wayata daga cikin jaka na hau kiran yan gida ina sanar dasu na sauka lafiya.
Wajen karfe takwas saura bayan mun gama yin sallah, Umar ya kira ni ya sanar dani yana kofar gida. Na dauki gyalena dana rataye a jikin hanger ina kokarin yafawa, ko hoda ban kara ba balle janbaki. Ni kwata-kwata bana ganin amfanin yin wannan kwalliyar ta dare idan za’a fita hira, koda yake dama ta yaya za ayi in gani tunda dama can kwalliyar ba damuna tayi ba?.
Janan dake kwance ruf-da-ciki akan katifarta tana chatting ta kalleni lokacin da nake shirin fita, tace “kada dai ki wuce karfe tara da rabi, idan kuma ya shigo daga ciki, ku koma daga waje duk da nasan cewa ba lallai Ahmad ya bude mishi gate ba, sai dai idan baya nan”.
Nayi yar dariya ina kallonta, “kada dai kice min kuna da curfew a gidannan?!”.
Tace “Yaya ne yasa wallahi. Samarin su Salama suke shiga da fita babu kakkautawa a gidannan, ko ina kuma shigo dasu suke yi har cikin falon nan, shine ya kafa wannan doka”.
Na gyada kai, “yayi kokari gaskiya, da haka ake yi a wasu wajajen ai da an samu zaman lafiya kuwa”. Tayi yar dariya, “kin ci sa’a ma Yayan baya nan, da sai kin amsa tambayoyi daga wajenshi kamar kina rubuta jarabawar jamb kafin ki fita yanzu”.
Na kama baki cike da mamaki, gefe daya kuma ina jinjina kokarin Yayan, a ganina hakan da yayi hanya ce mafi sauki ta sanin halin da kannenshi da samarinsu suke ciki. Na dai mata sallama na fita.
A kofar gate muka yi clashing da Haleemo ita kuma zata shigo, ta ja da baya tana daga waje alamun ta bani waje in fara fita, na danyi murmushi appreciatingly na raba ta gefenta na fita. Ta kalli gefen gidan inda Umar yayi parking din motarshi, tace “saurayinki ne ya dawo?”.
Mamakin tambayar ta kama ni, amma sai na fuske nayi yar dariya kawai ina gyada mata kai, tace “kinyi sa’a abinki ke kam!”. Ta shige gida, na bita da kallo baki a bude slightly, ko meye hadinta da zancen soyayyata, sa’a ko rashinta? Na daga kafada tare da tsallakawa daya gefen.
Da kanshi ya bude min murfin motar, na shiga ciki bakina dauke da sallama. Barin murfin motar nayi a bude, ban maida shi na rufe ba. Ya amsa min sallamar, scowling, na kula baya son hakan ko kadan, ya sha fadin hakan ma ba sau daya ba sau biyu ba. Kunnen uwar shegu kawai nake yi dashi.
Mun fara hira dashi game da makarantarmu da wajen aikinshi. Ya fada min anyi posting dinshi zuwa Kaduna, satin sama zai shirya ya tafi. Na mishi addu’ar Allah ya taimaka. Daga nan hirar ta koma ta masoya, ya fara amayo kalmomin soyayya. Jinsu kawai nake yi suna shiga suna fita cikin kunnena. Ban sani ba, ko akwai ranar da zanji wani yace yana so na, in yarda da hakan? Inji zuciyata ta mamaye da haske da farinciki sanadiyar jin haka? Nayi nisa cikin tunanina, totally zoned out. Wani abu daya zame min jiki da zarar naji mutum ya fara amayo kalmomin nan, ban san lokacin da hakan take faruwa ba, kawai sai dai in tsince ni nayi nisa a duniyar tunani, I couldn’t help it.
Umar ya murza yatsunshi biyu a fuskata, sautin da suka yi ne yasa na dawo daga tunanin dana shiga. Na kalleshi sosai, kallona yake yi, nace “me kace?”.
Fuskarshi ta nuna alamun damuwa da kulawa, yace “Sweetie, ban san sau nawa kike so in fada miki cewa bana jin dadin abinnan da kike yi ba. Sau tari sai in ganki kinyi nisa cikin tunani, hakan yana kona min rai. Don Allah ki fada min, idan wata damuwa ce take damunki, ki fada min inyi miki maganinta!”.
Na girgiza kai, ina mishi murmushi a sanyaye, “babu abinda yake damuna Umar, kaima kasan cewa da da akwai zan fada maka ne”.
Ya juya kai, “abinda kike cewa kenan kullum, babu canji. Har zuwa yaushe ne don Allah? Sai inga kamar baki jin dadin kasancewa da nine”.
Na kalleshi cike da mamaki, “meya sa ka yin wannan tunanin? Ni fa na fada maka babu abinda yake damuna, idan akwai zan fada maka wallahi, kaima ka sani”.
Ya rausayar da kai, “to ai shikenan sweetie, yadda kika ce”. Shiru ya ratsa wajen, kafin naga ya bude dashboard ya ciro wani kwali. Yanayin tsayin kwalin yasa nayi zargin waya ce a ciki.
Ya miko min, bakinshi dauke da murmushi kamar zai tsaga bakin. Yace “dazu na ganta a shago, sabuwar shigowa ce, ban yi tunanin kowa ba sai ke lokacin dana ganta”.
Na sanya hannu na karba tare da budewa, sabuwar wayar Samsung ce sai sheki take yi. Duk da bai fada min kudin wayar ba, nasan ba karamin kudi zata yi ba.
Cikin alamun tambaya nace “amma me yasa? Ina da waya, ka tuna?”.
Murmushin fuskarshi ya bace, “na sani mana, shi yasa ma na sai miki. Na kula da taki ta ma fara fading fa, kai gabadaya ma ta tsufa”.
Na kai yatsa daya na shafo saman hancina, wani abu da nake yi unconsciously idan magana bata karbu a wajena ba, ko kuma idan maganganun mutum were so bored. Niyyata in tambayeshi sai me don wayata ta fara tsufa? Naga dai ina amfani da ita lafiya lau, kamar dai yadda sauran masu latest wayoyi suke yi. Sannan wayata lafiyayyiya ce, bata bani wata matsala balle yace saboda matsalar ta ne.
Sai dai nayi shiru kawai, nasan cewa idan na daga baki nayi magana hakan zai kaimu ga yin sa’in’sa, hakan kuma ba dadi zai mana ba. Don haka nace mishi “to nagode kwarai, Allah ya amfana. Amma zaka amshi tsohuwar tawa wayar ne ko?”.
Yayi wani irin murmushi, idanunshi na karade fuskata da kallo, “ko kadan sweetie na, amma zaki iya bani dan kiss, a matsayin tukuici na”.
Na daga kai na kalli tsakiyar idanunshi, babu alamun wasa ko kadan, alamunshi sun nuna da gaske yake. Duk da haka, sai na maida abin wasa, nayi yar dariya kawai, “dadina da kai ka cika ban dariya wallahi Umar… Bari in koma daga cikin gida don lokacin da aka dibar min ya kusa cika!”..
Ban jira ya bani amsa ba, na yunkura da niyar fita daga motar. Kawai ji nayi murfin motar ya koma ya rufe, tare da wani karamin kara alamun an sa motar a lock. Na kai hannu da niyar bude motar, sai dai naji gam, kamar yadda nayi zato ya rufe ni.
Na juya ina kallonshi, fuskata a dinke tsam babu alamun wasa balle yayi tunanin kawo min maganar shirme, nace “meye haka? Bude min kofa in fita don Allah”.
Ya gyara zamanshi sosai, “a’ah, magana zamu yi dake sosai. Na kula duk lokacin dana fara furta miki abinda yake cikin raina, sai ki banzatar da maganar ki maidata wasa, an fada miki ni dan wasan kwaikwayon ban dariya ne? Ni fa in fada miki gaskiya na gaji haka nan Na’ilah! Na gaji! You are officially my girlfriend!! Yakamata ace zuwa yanzu mun wuce kan wannan maganar, ba tun yau ba yakamata ace wannan maganar a tsakaninmu ta wuce, ace mun wuce wannan matakin. Nima fa mutum ne. Nima ina so ace ina taba ki, ace zuwa yanzu jikinki ya riga ya saba da nawa, amma kullum sai ma kara janye jikinki da kike yi daga nawa, to na gaji, yau sai dai ayi ta ta kare tsakanina dake!!”.
Tsananin mamakinshi ya dankarar dani a zaune, na kasa motsi. Bakina nake motsawa ina so inyi magana, in maida mishi martani ko yaya ne, amma kamar ansa zare da allura an dinke min shi, na kasa buda shi.
Ganin haka yasa ya cigaba da magana babu kakkautawa, “meye bana miki? Meye bana baki?? Idan ma abinda nake miki ne bai isarki, kema kinsan ai ba sai kin zauna kina wani shan kwana ba, ki fito ki fada min mana ki ga idan ban baki ba yanzu take! Meye na roki ki min? It’s just a kiss fa! Meye a cikinshi?”.
Sai lokacin naji bakina ya motsa, saboda tsananin bacin ran da maganganunshi suka haifar min yasa naji jikina yana wani irin rawa, nace “sau nawa kake so mu yi wannan maganar da kai? Jikina ba jikim banza bane da zan sakar maka shi kawai saboda kana yi min hidima. Na fada maka ina bukatar abubuwan da kake yi min ne? Na taba daga baki na tambayi wani abu a wajenka? Ko kuma na taba furta maka ina bukatar irin rayuwar da kake son yi? Kawai saboda kai kana ganin irin wannan rayuwar itace wayewa, ni a ganina ba hakan bane. Ba zan taba yin rayuwar zubda mutunci ba, ba zan taba zubar da mutunci da kimata ta ya mace ba akan mata’ul hayat, abubuwan da zasu kare cikin dan kankanin lokaci, saboda haka ka bude min kofa in fita!”.
Cikin saurin magana da bacin rai nake maganganun, nasan da kyar ne idan ya fahimci duk abinda na fada.
Ya sauke ajiyar zuciya, “come on Na’ilah! Ni fa ban ce ki bani kanki ko wani abu ba, kawai kananun abubuwa nan da can ne fa, what’s the harm in it? At least ki dan dinga appreciating dina mana!”.
Na galla mishi harara, “kai a wajenka ba komi bane, saboda shaidan ya riga ya rufe maka idanu, amma ni a wajena it’s a big deal. Kada ka manta, mun taba yin wannan maganar da kai, na fada maka idan kasan wani abu kake bukata daga wajena yafi mana sauki mu yanke alakarmu, don babu abinda zan iya maka. Ba zaka taba taking advantage dina ba Umar, ba zaka taba yin amfani da kayan banza ka yaudare ni ba wallahi, in Allah ya yarda nafi karfin haka. Don haka ka bude min kofa in fita tun muna shaidar juna ni da kai wallahi. Kuma ga wayar ka nan, bana so, kai bana so in kara ganinka ma!!”.
Na hau kici-kicin bude kofa da sauri kamar wadda ta fita daga cikin hayyacinta. Ina ji yana kiran sunana amma nayi banza dashi. Ban tantance ba naji saukar hannunshi yana dafe min hannu, banyi wata-wata ba na wancakalar da hannun nashi can gefe. Bai daddara ba dai ya sake dafa kafadata, wannan karon dana kama hannunshi, twisting nayi da karfina duk da nasan ba lallai yaji zafin hakan ba, duba da yanayin aikinshi.
Cikin tsananin bacin rai da tunda muke dashi bai taba ganin kwatankwacinsa ba, daga murya da tsawa nace “kada ka sake taba ni!! Kada ka sake kuskuren taba ni!! Kuma wallahi ka cuce ni da kayi tunanin zaka iya saya na da kyale-kyalin banza, in shaa Allahu sai Allah ya saka min. Ka bude min kofa nace!!”.
Tsananin ihun da nayi ni kaina ya bani mamaki balle shi. Ina jin hakan ne yasa bai ma san lokacin da hannunshi ya danna madannar ba, ina jin na taba murfin ya bude, na fita daga motar da sauri. Ko sakan biyu ba ayi ba naji shima ya fito, ya hau auna min kira. Babu ko waiwaye, na shige gida da sauri.
Jikina rawa yake, hannu, kafa, baki, kai, komi nawa rawa yake yi. A daidai parking space dinsu na tsaya, na dafa wani pole ina haki kamar wadda tasha tseren rai da rayuwa. Kodayake kusan hakan ne.
Tunanina daya a lokacin, da ace yaki bude kofar fa? Me zai faru da yaki bude kofar? Me zai faru idan bai daina taba ni ba? Me zai faru idan wajen da muke babu mutanen da zasu ji ihuna idan ina ihun neman taimako? Tambayoyin suka yiwa zuciyata yawa. Ban san lokacin da gwiwoyina suka saki ba, na zube akan gwiwata a wajen. Allah kadai yasan iya lokacin dana dauka a wajen, ban ma san a wani hali nake ciki ba. Kai ban ma san ina hawaye ba sai da naji lema da alamun gishirin hawaye akan lebena sannan na ankara. Sai kuma vibrating din da wayata take tayi babu kakkautawa. Na daga na ga sunan Umar yana rawa a jiki, tsaki na ja nayi declining, yana katsewa wani kiran ya sake shigowa. Wayar na dauka gabadayanta na kashe.
Na mike na kakkabe jikina tare da share hawayena. Sai dana tabbatar da na dawo cikin nutsuwata sannan na wuce cikin gida. Su duka suna falon suna kallo banda Janan, na musu sannu na wuce ba tare dana jira naji sun amsa min ko basu amsa ba.
Janan tana tsaye a tsakiyar daki da waya a kunnenta, ina shiga ta sauke wayar, “yanzu fa nake kiran wayarki, sai kuma naji ta kashe”.
Na kalli wayar kafin na kalleta, “kashe ta nayi”.
Ina tunanin bata kula da yanayin da nake ciki ba sai a lokacin, da sauri ta matso wajena, fuskarta dauke da alamun damuwa, “lafiyarki lau? Me ya faru??”.
Na girgiza mata kai, “babu komi fa!”.
Ban jira amsarta ba na yaye gyalena na rataye na shige bandaki. Alwala na dauro na fito.
Janan ta bini da kallo har na shimfida abin sallah, bata ce komi ba. Har na gama shafa’i da wutiri, na fara shirin saka kayan barci. Tasan ko ta dameni ma babu abinda zan iya gaya mata, sai ma karin bacin rai da hakan zai haifar min, don haka taja bakinta tayi shiru, tasan duk lokacin dana sauka don kaina, zan fada mata. Babu boye-boye a tsakanina da ita.
Instead sai tace “idan kin gama kafin mu kwanta, ki zo in danyi briefing dinki akan abubuwan da muka yi wannan satin”.
Kai kawai na iya gyada mata. Dana gama shiryawan, naje gefenta na zauna, ta dauko littafinta ta bude ta fara min bayani.
Zuwa lokacin da muka gama, na dan fara saukowa daga fushin, haka ma zafin zuciyata ya dan lafa, amma duk da haka abin yana makale a cikin raina.
Kai har lokacin dana kai ga kwantar da jikina akan katifar Janan da niyar inyi barci, abin yana makale a cikin raina. Nasan cewa shi da fita har abada.
*☆⋆08⋆☆*
Da azumi muka tashi washegari, bayan munyi sahur, wanda ni ruwa kawai na iya sha, muka yi nafiloli har aka kira sallah, muka yi.
Janan ta tashi zata fita bayan gari ya fara yin haske kadan, lokacin na gama azkar dina kenan. Na dubeta cike da alamun tambaya, tace “breakfast zan je in hada, kiyi wanka kafin in fito”.
A zato na ko haka dokar gidan take, don haka naga bai kamata in barsu suyi aikin su kadai ba. Na tashi na saka karamar hijabi akan kayan barcina, duk da ba masu fitar da jiki bane, kuma Janan tace Yaya a gidan Anty Ameerah ya kwana, still ba zan dauki chances ba. Sai dai ina zuwa kitchen din nayi turus, ganin Janan ita kadai a tsakiyar madaidaicin kicin dinsu tana kokarin dora tukunya akan gas. Na shiga ina karewa kicin din kallo, “ina sauran?”.
Da sauri ta juyo ta kalli inda nake, ina tunanin bata tsammaneni a wajen ba shi yasa taji abin unexpected, “su wa fa?”. Ta tambaya lokacin da take kokarin zuba mai a cikin tukunyar.
Na kada idanuwa, “ina nufin sauran wadanda kuke zaune a gidan dasu, ba zasu fito kuyi aikin tare bane?”.
Ta danyi murmushi cikin girgiza kai, “ni kadai nake aikin dama can!”.
Na zaro ido, “say what??!”. Ta kwashe da dariya, na harareta, “wannan ba abin dariya bane Jan, this is serious! Ta ya za ace gardawan banza suna kwance sun saki baki da hanci suna barci, ke kuma zaki dage ki girka musu abinci? Wow! Ko da kike cewa suna sakar miki aikin gida, ban yi zaton har da wannan ba ai”.
Tayi yar dariyarta a sanyaye, “ni ban ga abin daga jijiyar wuya a cikin wannan lamari ba. Na riga na saba ne, har ya zame min jiki wallahi. Sannan yawanci kafin Yaya ya wuce Abuja yana biyowa ta nan yayi karin safe, shi yasa nake tashi in hada, sai kuma abin ya zame min jiki.”
Duk bayanan da take yi sai lokacin ta dago ta kalleni, ganin yadda nake kallonta kamar wata tababbiya yasa ta sake sakin wata dariyar, “da gaske ba wani abu bane, ni wallahi ban damu ba. Besides, su suke yin abincinsu da rana, wanda sai na ga dama nake ci”.
Nace “ai shikenan, me zan taya ki dashi ne?”.
Ta jefo min peeler, na cafe, tace “fara da dankalin can mu gani”.
Na fara fereye dankalin yayin da taci gaba da soya kayan miya da tayi grating.
Cikin dan lokaci kankani na gama firar, muna yi muna hira jifa-jifa, duk da dai shiru yafi yawa. Na kunna stove tare da dora frying pan da mai a ciki, yana yin zafi na fara zuba dankalin da na yanka a tsaitsaye, bayan na zuba maggi da dan gishiri, wata dabarar soya chips da Fatsu ta koya min.
Muna gamawa ta dauko kula da flask, ta zubawa Yaya nashi da kunun gyada, fari tas dashi yana ta kamshi, ta kai falo ta ajiye.
Muna cikin maida kayayyakin da muka yi amfani dashi bayan mun wanke, muka jiyo karan bude gate. Janan ta leka ta tagar kicin din da take fuskantar gate, ta jiyo ta kalleni “Yaya ne!”.
Na ajiye frying pan a inda yake na juya ina kallonta, “bari in shiga wanka kawai, bakwai ta kusa yi”, kai kawai ta gyada min saboda hankalinta yana kan sauran kunun gyadar da take juyewa a cikin wani babban silver flask. Na fita daga kicin din.
Ina shiga daki na hada kayan da zan bukata na fada toilet. Bandakinta babba ne, yana da fadin shi daidai misali da kuma kayan amfani na zamani. Nayi amfani da sabulunta na ‘Vix’ mai kamshin sandalwood nayi wanka. Ban tsaya bata lokaci ba don nasan bamu da cikakken lokaci.
Ina gama wankan nayi amfani da karamin towel na kafe jikina. A cikin bandakin na zura doguwar rigar material ruwan kasa mai laushi, kafin na fita.
Janan tana gefen katifarta daure da towel, waya a hannu, da alamun jirana take yi. Ta daga kai ta kalleni lokacin da taji na maida kofar bandakin na rufe.
“wai fada kuka yi ne ke da Umar?”.
Naji wata irin faduwar gaba lokacin da naji ta ambaci sunanshi. Tunda na tashi da safe nake ta gujewa tunaninshi a cikin raina. Na hana kaina sakat, da naji sunanshi ko fuskarshi na shirin fado min a cikin raina sai inyi saurin sako wani abun daban.
Na daka fuska ina zama akan kujerar dake gaban dressing mirror dinta, “me kika gani?”.
Cike da tuhuma tace, “ban sanar dake bane kawai, amma tun jiya da dare yake kiran wayata da turo texts, sai daina dagawa nayi. Yanzu ma tun dazu yake kira, yace in baki hakuri”.
Nayi kwafa kawai ban amsa mata ba, ta tashi tsaye tazo ta dafa kafadata, “ki daure ki daga kiranshi don Allah, baki san abinda yake son ya fada miki ba. Nayi zaton kun wuce matakin irin wannan fadan ke dashi?”.
Na harareta ta cikin madubin, “bamu wuce ba, kuma ma in Allah ya yarda wannan shine karo na karshe da zamu yi fada dashi, we are done Jan!”.
Fuskarta bata nuna komi ba, babu mamaki, farinciki ko akasinsa, sai kai kawai data gyada, tace “bari inyi wankan nima, amma ki dai daure ki bude wayarki, ko ba don shi ba saboda mutane masu nemanki. Yaya Mudan ma ya kirani lokacin da kina wanka, shima dai ya nemi wayarki a kashe”.
Sai lokacin naji nayi murmushi, nace “wato har yanzu dai Mudan dinnan yana nan ko? Kinsan Yaya ya tsani sunan nan”.
Tayi dariya, “ramawa kura aniyarta kenan!”. Daga haka ta shige bandaki. Nayi dariya kawai naci gaba da shirina.
Zuwa lokacin dana gama hada komi da zan bukata, Janan ta fito daga wanka itama ta fara shiri. Da wayarta nayi amfani na kira Yaya, yana jin ni ce ya fara zuba min korafin ina na shiga? Excuse din dana bashi shine ‘wayar ce babu caji tun jiya’.
Yace “su Malam ne nima suka dameni da kira tun safiyar yau, wai suna ta kiran wayarki su ji in kin sauka lafiya kuma a kashe, shine hankalinsu ya tashi!”.
Ni gabadaya na ma manta ban kira su ba a jiyan. Na manta yadda suke ne, musamman idan zanyi tafiya, hankalinsu baya kwanciya sai sunji muryata na tabbatar musu da saukata lafiya sannan.
Nace “afuwan, ka basu hakuri don Allah. Wallahi mantawa nayi ban kira su ba, idan nayi caji zuwa anjima zan kira su”.
Yace “to shikenan, Antynki tana gaishe ki”, daga nan inda yake ina jiyo sautin muryarta tana kiran sunana, nayi murmushi nace “a gaishe ta itama, sai anjima”. Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefena.
Ina zaune har Janan ta gama shirinta, ta dauki jaka tana zuba jotters da handouts dake tsakiyar dakin a yashe inda muka barsu jiya da muka gama karatu. Na mike nima ina kara gyara kayan jikina. Muna gamawa muka fita daga dakin, ina kallo tasa key ta rufe dakin ta maida key din cikin jakarta.
Har yanzu falon babu kowa, gabadaya gidan ma shiru kake ji kamar babu masu rai.
Sai da muka fita daga gidan muka dauki hanyar da zata sada mu da babban titi inda zamu hau bus, tace “Yaya sauri yake yi, shi yasa bai tsaya kun gaisa ba, ya bar sakon gaisuwa dai”.
Nayi murmushi, “babu damuwa, idan ya dawo zamu gaisa ai in da rabo”.
Ta zage zip din bayan jakarta ta ciro dubu biyar, sababbi kar ta miko min, na amsa ina kallonta fuskata cike da alamun tambaya, nace “me zanyi dasu?”.
Ta daga kafada, “Yaya yace a baki!”.
Na zaro ido, “what?…,” a lokaci daya kuma ina mika mata kudin, “A’ah, gaskiya ba zan amsa ba, this is way too much!”.
Ta harareni, “sai ki bari in yazo ki maida mishi da hannunki. Kafin kuma ki fara wani tunani, wannan ba wani abu bane. Kamar kudin albashi ne daya saba bamu gabadayanmu har su Haleemo, saboda hidimar makaranta da sauransu, kin gane?”.
Na karkata hankalina gabadaya na maida kanta, “duk sati yake baku 5k, kawai saboda hidimar makaranta?”.
Ta gyada kai tana kallona, irin ba wani big deal bane a wajenta.
Nayi yar dariya, “Woah, dole a makale a gida aki tafiya, kuma dole ace kwadayi nazo yi ba wani abu ba. Maganar gaskiya though, ba zan iya amsar kudin nan ba gaskiya, kiyi hakuri ki amsa”.
Ta fara huro hanci alamun na fara bata haushi, “sai kiyi kuma tunda kin saba, ni na gaya miki sako aka bani na baki, in kinga dama kada kiyi amfani dasu, ki jira har sai Yaya ya dawo sai ki maida mishi ki gani idan amsa zai yi!”.
Na dan dakata da tafiyar da nake yi, “meye abin fushi kuma anan Jan?”.
Tace “ke din ce ai idan ba gani kika yi ana miki wuta ba, baki cika fahimtar abu ba”.
Nace “to naji, na karba, kuma na gode, Allah ya saka da alkahiri”.
Ta harareni cikin wasa, “abinda yakamata ki ce tun dazu kenan, ba ki tsaya neman magana ba!”.
Nayi dariya kawai jin abinda tace. Muka cigaba da takawa har muka fita bakin titi. Shatar keke-napep kawai muka yi saboda lokaci daya fara kurewa.
Allah ya taimaka muka isa akan lokaci. Kasancewar duk practicals ne muka yi, kuma abubuwa basu fara yin nisa ba, yasa bamu jima ba muka taho gida. Karfe biyu ma bata karasa ba muka dawo.
Wannan karon ma napep muka hau. Muna sauka, wata hadaddiyar Range Rover tana shiga gidan. Muka bita a baya muma muka shiga gidan. Ganin ta gangara can bangaren Yaya Jameel, yasa na kalli Janan, “Anty Sarah ta sake mota kenan?”.
Tace “da alama, ko kuma ta gidansu ce. Tunda ko yau da safe motar bata nan”.
Wadda muke maganar a kanta ta bude gidan gaba ta fito. Matar Yaya Jameel ce. Saratu da muke kira, ko ince ake kira da Sarah, cikakkiyar yar gayu ce, wadda tasan fashion, kodayake kamar akan abinda naji ance tayi karatu kenan, ko kuma dai wani abu mai kama da hakan. Daga yanayin yadda take shigarta, takunta da gudanar da al’amuran rayuwarta, zaka tabbatar da cewa wayayyiyar mace ce, wadda ilimin boko ya ratsa ta. Gidansu gabadayansu yan boko ne. Kai ita kanta a kasar Germany naji ance taje ta hado degree dinta. Matsalarta daya, rashin shiga mutane. Zaku iya kwashe sati cikakke baku hadu da junanku ba, ni da yake dama ba zuwa gidan nake yi sosai ba, zan iya cewa na kwashe watanni fiye da biyar ban ganta ba.
Muka karasa wajen da take, daidai lokacin da diyarsu mai kimanin shekaru biyar, Ruqayyah wadda suke kira Mimah, ta fito daga daya gefen mai zaman banza dauke da jakarta da lunch box.
A lokaci daya muka gaidata ni da Janan, ta amsa tana kama hannun Mimah da take kokarin isowa gareme, jininmu ya hadu da ita sosai. Halin mahaifiyarta na shiga part dinta ta rufe ta kuma hanata fitowa yasa bamu haduwa da ita sosai, sai lokaci zuwa lokaci.
Tana gamawa amsawa ta latsa key tasa motarta a lock, taja hannun diyarta suka tafi.
Duk da haka sai da Mimah ta juyo tana daga mana hannu, mu duka muka daga mata hannun muna murmushi har suka shige part dinsu, ta rufo. Ni da Janan muka kalli juna muka sake yin murmushi, kafin muma muka shige nasu part din.
Adi, da Haleemo suna kicin lokacin da muka shiga, Raheemah kuma tana zaune tana sana’ar kallo, ban san ina Salama ta shiga ba tunda bamu ganta ba. Mu dai muka musu sannu, muka shige daki ba tare da mun damu da kallon banza da aka bimu dashi ba.
Bayan la’asar muka fita waje ni da Janan muka sayo fruits a bakin titi. Muka zo muka hada fruits salad da kayan shan ruwa. Muna cikin soya yam balls, Salama ta shigo kicin din. Babu wanda ta yiwa ko sannu a cikinmu, ta dauki plate kawai sai ganin tana zuba yam balls din a plate din muka yi. Ta debi iya wanda zata dauka, ta fita daga kicin din. Duk kallo muka bita dashi har ta fita. Maimakon abin ya bani haushi, sai ya ma bani dariya. Na girgiza kai kawai, a zuciyata ina furta ‘Allah ya kyauta!’.
Sai bayan mun sha ruwa sannan na kunna wayata. Messages, missed calls, voice mails, messages din whatsapp da voice notes babu iyaka daga Umar, duk abu daya yake tambaya, ‘don Allah in daga wayata’, na harari wayar tawa kamar shine a gabana, in daga wayata in ce mishi me?!
*☆⋆09⋆☆*
Har washegari Umar bai daina kiran wayata ba, nima kuma ban daga ba. Zuwa lokacin missed calls dinshi sun fi a kirga.
Da safe ina browsing din wasu procedures a wayata lokacin da nake jiran Jan ta fito daga wanka, don na rigata shiryawa. Wata bakuwar lamba ta min sallama ta whatsapp. Daga farko nayi zaton ko Umar ne, sai dana bi ta cikin description dinshi sannan naga kwata-kwata komi nashi bai yi shige da na Umar ba. Na farko dai Umar daya zauna ya zubo miki layi biyu a rubuce, ya gwammace kuyi awa biyu akan waya kuna hira. Shi yasa yanzun haka voice notes dinshi ne suka cika min waya.
Kamar wanda yake jira, ina amsawa ana maido da amsar ya nake? Fatan na tashi lafiya?.
Nace lafiya lau, ko wanene yake magana?
Sai aka turo, ‘ba lallai ki sanni ba gaskiya, amma ni na sanki farin sani. Ba tun yau ba nake ta so in miki magana, sai yau Allah ya yarda. Sunana Muhammad’.
Na rubuta, ‘to Malam Muhammad ko zaka iya sanar dani inda ka sanni? Don bana tunanin nasan wani Muhammad anan inda nake’.
Yace ‘in shaa Allah zaki sanni nan ba da jimawa ba, na miki wannan alkawarin. Magana ta gaskiya yanzu bana gari shi yasa, amma da zarar na shigo zan zo in same ki, nasan lokacin kuna shika’.
Na daga gira cikin mamaki, ta alama mutumin nan ya sanni fiye da yadda nayi tsammani. Nace ‘ta yaya aka yi kasan haka?’, ina tura mishi amsar Jan tana fitowa daga bandaki, na kashe datar na sauka daga kan WhatsApp din ina kallonta. Zama tayi ta gama shirinta a nutse. Tana gamawa muka ci pancake da muka yi da ruwan shayi, da muka gama muka dauki sauran da muka yi muka kai kicin muka wuce.
*
Yau sai yamma likis muka dawo daga asibitin. Da yake yau a bakin titi muka sauka, akan kafafunmu muka gangaro zuwa gidan Yaya.
A kofar gidan, Umar ne tsaye ya jingina da motar shi. Na danyi turus da ganinshi, gabana yana faduwa, kafin na dake muka cigaba da tafiya.
Da sauri ya tari gabanmu, “Na’ilah, sweetie, don Allah ki dakata, don Allah ki saurareni, wallahi na tuba, don Allah….”.
Jan ta kalleni, yadda na hade fuska kamar naga wani dan aiken mutuwata, yasa ta fara raba idanu tsakanina da Umar. Yaci gaba da zuba magiya yayin da na zagaya ta gefenshi na tunkari kofar gidan gadan-gadan. Janan ta riko hannuna, na juya ina kallonta, tace “meye haka Na’ilah? Ban san ki da wulakanta mutane ba sam”.
Nace “kiyi shiru Janan, baki san abinda ya faru ba, don haka kada kiyi kokarin shiga cikin wannan fadan”.
Umar yayi tsulum da bakinshi, “don Allah ki saurareni Sweetie, please…”.
Na kare mishi kallo, duk da kokarin dannewa da nake yi, da nuna kamar ban damu ba, amma nayi kewar shi. Kwana daya da yini daya kacal, amma nayi kewarshi.
Na kalli Jan data tsaya tana kallonmu, nace “ki wuce abinki kawai, zan shigo in same ki”. Babu musu ta shige cikin gidan ta barmu a tsaye.
Na harde hannu a kirji ina kallonshi, “me? Yanzu kuma mai kake bukata ne? Kana so mu kebe wani waje ne ko kuma ka kama mana daki ne a hotel?”.
Ya dafe kai, “Subhanallah, haba Na’ilah me ya kawo wannan maganar kuma? Kuskure ne nasan dana riga na tafka shi, amma ina neman afuwarki don Allah. Wallahi ban san abinda ya hau kaina ba, ok, na sani. Gajen hakuri ne irin nawa, amma wallahi na gane kuskurena, ba zan kara ba, don Allah ki bani dama Na’ilah, na miki alkawarin hakan ba zata sake faruwa ba”.
Naji zuciyata ta fara yin sanyi da jin hakan, nace “how sure are you? Ta yaya zaka tabbatar da cewa nan gaba ba zaka sake tare ni a cikin mota, trying to touch me inappropriate ba?”.
Ya hau girgiza kai da sauri, “I assure you hakan ba zata sake faruwa ba, na miki alkawarin ba zan kara taba ki ba tare da izinin ki ba har auren mu!”.
Nace “idan kuma hakan ya sake faruwa fa?”.
Yayi shiru yana kallona, nace “magana daya ce Umar, idan abu makamancin haka ya sake faruwa, we are over! Dama kasan hakan ta taba faruwa, yazo ya sake faruwa yanzu, to babu na uku. Idan kuma muka rabu, mun rabu kenan, ka yarda?”.
Ya gyada kai, “it’s not as if zan sake maimaitawa, but yeah, na yarda. Fushin ki ba abu bane da zan yi marmarin sake gani ba koda wasa. Yanzu dai kin yafe min?”.
Nayi jim ina tunani, na yafe mishi? Ya riga yayi convincing dina, kuma yayi alkawarin hakan ba zata kara faruwa ba, saboda haka meye aibun yafe mishi a ciki? Don haka na gyada kaina, ya saki murmushi a tausashe wanda ya sanya ni sakin murmushin nima, “oh thank God! Wallahi baki ji yadda na damu ba, God, I miss you wallahi”.
Nayi murmushi kawai, yayin da naji wani sanyi yana kwaranya a cikin raina. Ban sani ba, na yafe mishi din da nayi ne, ko kuma na dawowa gareni da yayi bane. Kafin in sake daga baki inyi magana, muka ji kiran sallah, ya kalleni yana murmushi, “bari in wuce masallaci to, zan kira ki zuwa anjima”.
Na gyada mishi kai tare da shigewa gida.
Bayan mun ci abincin dare a dakin Janan, ta zauna a gefen katifa suna waya da Al-Mustapha saurayinta, ni kuma na shiga whatsapp chatting. Sakon mutumin nan na dazu shine abinda na fara gani, ni na ma manta dashi.
Amsar tambayar dazu dana mishi da safe ce ya turo min, “kamar yadda na fada miki, na san ki farin sani. Kuma ina matukar kula da lamuran wadanda suke very special a gareni, don haka ba wani abin mamaki bane”.
Na maida mishi da amsar ‘haba? Ta yaya aka yi na zama very special a gare ka?’.
Babu jimawa sai ga reply ya shigo, ‘oh, you are very very special in fact! Idan nace zan miki bayani zamu jima a haka, to cut it short, ina jin ki a cikin raina fiye da yadda kike tsammani’.
Haka kawai na tsinci kaina da darawa. Wani abu game da mutumin is very fascinating, yet so familiar. A karo na kusan biyar tunda muka fara chatting dashi yanzu, da naji a jikina duk yadda za ayi mutumin nan ya sanni fiye da sani na, kuma nima ko yaya ne na san shi. Sai dai duk hakan bai dameni ba, yadda naji hira dashi ta dauke min hankali, shine abinda ya bani mamaki ya kuma daure min kai a lokaci guda. It’s a first.
Mintunanmu talatin kacal muna hira ta hanyar musayar rubutattun kalmomi, sai gani kwance rigingine a tsakiyar daki, ina kallon fankar dakin dake juyawa, waya a hannu ina ta faman rubutu, yayin da lokaci zuwa lokaci sautin dariya zai fito daga baki na, walau na sani ko ban sani ba. Hakan ya kan sa Jan, da har lokacin tana kan waya, zata juyo ta kalleni cikin alamun tambaya, amma bata tambayeni ba.
Zuwa lokacin da yayi min sallama akan wani aiki da zai tafi yayi, ba ni kaina ba, hatta zuciyata da gangar jikina naji sun aminta da mutumin. Wanda hakan a karan kanshi ma abin tambaya ne, na farko ban san mutumin ba, babu abinda na sani dangane dashi sai sunanshi, yana aiki da wani kamfani da yake sarrafa takardu, shikenan. Dana tambayeshi yana da mata? Sai yace ba ga ki nan ba? Hakan yasa naji sautin bugun zuciyata kamar zai tsaga tsakiyar kirjina zuciyar ta fito.
Tsakanina da Allah ban so muka yi sallama dashi ba, na tabbata idan zamu kwana muna chatting dashi ba zan taba damuwa ba a cikin raina, kai a takaice ma zan so hakan ba kadan ba. Muka yi musayar sai da safe, ya tafi bayan ya turo min ‘sleep tight!’, ya Allah, ban taba jin dadin ganin kalmomin nan daga kowa ba a rayuwata sai a yau din nan.
Yana sauka naji gabadaya chatting din ya fita daga raina, don haka nima na sauka.
Na lalubo jakata na ciro littafai daga ciki na fara karatu da bibiyar practicals din da muka yi yau.
Sai wajen karfe goma Jan ta gama tata hirar da Almunta, (yadda take kiranshi). Ta juyo ta kalleni tana murmushin tsokana, “fadan masoya hutu, wato saboda kun shirya shine kike wannan glowing?”.
Nayi murmushi kafin na jefa mata harara, “ni kada ki min sharri wallahi”.
Tace “wani sharri? Ga abu nan a fuskarki, kin kuwa ga yadda kike ta zuba murmushi sanda kuke chatting dinnan? Har wani dariya kike yi, irin soyayya tayi dadi dinnan!”.
Na danyi frowning ina kallonta, a hankali nace “ba da Umar nayi chatting ba dazu”.
Ta hangame baki cikin mamaki, “wasa kike yi ko? I mean, idan ba Umar ba, waye to? Yanzu da kika fadi haka sai na tuna Umar baya dogon chatting, wanene muka samu??”. Ta karasa fada tana daga min gira cikin alamun tsokana.
Na jefeta da littafin hannuna, ta cafe tana dariya, “fada min mana!”.
Na mike ina tattara kayan dana baza a wajen na maida su cikin jaka. Bandaki na fada kai tsaye na barta tana ihun, “ko shekara zaki yi a ciki sai kin fito kin fada min wanene yarinya!”. Dariya kawai na saki mai sauti. Nasan kafin in fito ta manta da zancen.
Har mun kashe wutar daki bayan mun kwanta, Janan ta kira sunana, na amsa a dan gajiye da kuma barci daya fara cin idanuwana, tace “wai me ya hada ki da Umar ne da?”.
Nayi sighing a hankali, “abinda ya faru ya riga ya faru Jan, mun riga mun shirya dashi, that’s all that matters. Tone-tonen abinda ya riga ya faru, babu abinda zai mana, don haka ki manta da maganar”.
Tace “of course sugar, baki da matsala dani”.
Kaunarta naji tana kara ratsa zuciyata, fahimtarta da goyon bayanta a kullum suna kara sa inji ta can cikin zuciya da ruhina. A hankali nace “nagode Jan”.
Ina jin sautin murmushin data saki cikin duhun dakin, “sai da safe Na’ilah!”.
Nima na maida mata martanin murmushin duk da nasan ba lallai ta gani ba, nace “sai da safe Jan!”. Na juya barin damana, tare da rufe idanuna.
Daren ranar mafarkai nayi masu yawa, da yawa daga cikinsu sun kunshi wani mutum da yake ta nanata kalmar, “ke ce Matata!,” kamar waka.
-Afuwan, in shaa Allah gobe zan turo mai yawa, wannan dinma aradun Allah da kyar hannuna da idanuna suka bada hadin kai nayi typing dinsa. Thank you all.
#F.W.A
.
.
*☆⋆10⋆☆*
A gabadayan tarihin rayuwata, ban taba, ko a cikin mafarki kuwa, tunanin akwai wata rana da zata zo da zan kwanta in kuma tashi da tunanin abu daya a cikin raina ba, musamman idan abinnan ya kasance d’a namiji. Amma yau sai gani na tashi cike da tunanin wannan bawan Allah da ko sunan shi ban sani ba. Har nayi wanka, na shirya, muka karya, muka dauki hanyar asibiti, tunaninshi ne a cikin raina. Daidai da sakan daya bai bar cikin raina ba.
Muna kan hanya, text message dinshi ya shigo cikin wayata. Na zaro wayar daga cikin jaka na daga, kawai cewa yayi,
*’salam, just wanted to say hi… Ban sani ba ko kinyi tunanina tunda kika tashi, ni dai nayi. Anyway, have a nice day!.’*
Ji na nayi kamar wadda aka wa kyautar kujerar makkah. Garin bai ma gama wayewa ba, amma wannnan text din kadai made my day already.
Na shiga cikin contacts dina nayi saving number da, ‘Mysterious’. Wannnan a karan kanshi abin tambaya ne ga wadanda suka sanni farin sani, domin haka kawai bana saving lambar mutane a cikin wayata, musamman wanda na sani na rana daya kacal, abu ne mai matukar wahalar yarda a wajensu.
Yau ma da wuri muka dawo gida. Yau gidan babu kowa, muka dauki makullin gidan a wajen da suka saba ajiyewa muka bude muka shiga. Bayan sallar la’asar muka shiga kicin ni da Jan, muna cikin girki sai ga Haleemo ta fado kicin din, bamu ma ji lokacin data shigo gidan ba. Ta mana sannu muka amsa, tace “don Allah wayar wa take da sauran canji a cikinku ta taimaka min inyi kira?”.
Jan tace ta baro wayarta a daki, ni kuma da wayata take saman cupboard muna sauraren kida da ita, na dauka na bata. Tayi godiya ta amsa ta fita.
Janan ta kalleni bayan fitarta, “da alama kuna shiri da Haleemon nan”.
Nace “tafi sauran yan uwanta kirki da rashin rawar kai shi yasa”.
“uhmmm, don dai kawai ba a gabanki take yin abubuwa bane, amma kada ki bari shiru-shirunta ya kwashe ki wallahi, duk ta fisu rashin mutunci”.
Na kalli kofar da tabi ta fita cike da mamaki, “amma kuma yanayinta sam bai yi kama da irin nasu ba”.
Tace “dama idan mutum bashi da mutunci, rubuta shi yake yi a goshi ne? Ai ba tambari gare su ba, lokacin da suka buga miki shi ne zaki ji kamar kiyi kuka”. Na kyalkyale da dariya.
Ta girgiza kai, “wato dariya ma na baki? Zaki yi bayani ne yarinya!”.
Haleemo ta dawo kicin din, ta miko min wayar tana murmushi, “yauwa, nagode Na’ilah”. Na jinjina mata kai ina dan murmushi kawai, na karbi wayar na maida na ajiye.
Ta leka kanta cikin tukunyar da muke girki da ita, “sai kamshi mai dadi yake tashi, me kuke dafawa ne?”.
Nace “shinkafa ce da miya”. Tayi murmushi, “ki ce yau dadi zamu ci? Amma nasan sai zuwa dare don yanzu kaya zan dauka, wajen kamun bikin wata cousin dinmu zamu je”.
Ni da Jan dai “humm!” kawai muka ce mata, ta fita daga kicin din. Bayan ta dauko kayan ma, sai data biya ta mana sallama sannan ta wuce. Mu dai muka samu muka gama girkin. Muka zuba musu a cikin manyan kuloli, mu kuma muka dauki namu muka wuce daki.
Da dare Umar yazo, mun jima dashi a gefen gidan muna hira dashi, fir naki shiga motarshi. Ko yanzu ma hirar da muka yi dashi cikin dari-dari muka yi ta. Tun yana korafi har ya koma magiya, ya dawo ban hakuri. Nace mishi yayi hakuri, amma na kasa sakin jiki dashi, a haka dai muka yi sallama.
*
Ranar assabar yini muka yi a daki. Yaya ya dawo daga Abuja, amma da yake a gidan Anty Ameerah ya sauka, kawai dai ya biyo ne muka gaisa. Ina bandaki lokacin daya dawo a jiyan da yamma, har ya tafi bamu gaisa ba. Naji Jan tana cewa sai yau da yamma zai dawo nan.
Tunda muka tashi wajen karfe goma na safe, brush kawai muka yi muka fita falo. Da alama mutanen gidan suna daki don babu kowa, muka shiga kicin da niyar dora abinda zamu karya dashi. Ga kaya nan baje a kicin din, da alamu anyi amfani da kayan ne amma ba’a wanke ba. Abinda suke mana kenan tunda nazo gidan, kodayake nafi kyautata zaton sun riga sun saba yin hakan ne tun ma kafin in zo gidan. Idan suka yi amfani da abu, anan zasu watsar dashi sai dai mu mu gyara. Hatta da su plates din da suka ci abinci, yawanci anan tsakiyar falo suke barinsu sai idan mun je gyara sannan zamu dauke shi.
Yanzu ma tattara su kawai muka yi, bayan mun dama kunun tsamiya, Janan ta soya mana kosai muka shiga daki muka ci.
Muna cikin ci muka ji anyi knocking a kofar dakin, muka kalli juna ni da Jan, kafin ta tashi ta bude kofar. Ina ji ta fara cewa “Yaya ina wuni?”, nayi sauri na lalubi hijabi na dora a saman kaina, nima na tashi lallaba na raba ta gefenta na durkusa nima na gaishe shi. Ya amsa hankalinshi akanta.
Dadina da halin Yaya kenan, yana da kulawa, sai dai yana da kame kai matuka. Bai cika sakarwa Janan fuska ba, amma kuma ta acts dinshi kadai zaka san da cewa yana matukar son ta, kuma yana kulawa da ita matuka.
Ya kara zuro kanshi cikin dakin yana shinshinawa, “meye haka kuka ci yake neman tado min yunwata?”.
Janan tayi dariya, ni kuma na sunke kai a cikin hijabi ina dan murmushi. Tace “kosai ne muka yi, ko zubo maka zanyi?”.
Idanunshi suka dan bude sosai, kamar alamun hope ko dai wani abu mai kama da haka, “kun girka da ni ne dama?”.
Tace “mun dai yi da dan yawa ne saboda munyi tunanin zamu iya cinyewa saboda yunwa sai kuma muka yi saura.”
Yayi yar dariya, “watarana zarinki zai janyo miki yin kibar da baki so. Ni dai tunda Allah ya taimakeni ya tsaga da rabona, ki zubo ki kawo min ina falo. Dama ban karya ba wallahi…. Mutanen gidan basu tashi bane?,” ya tambaya yana juyawa yana kallon falon kamar mai duba wani abu.
Janan tace “bari in kawo maka kunun”, ba tare data amsa mishi tambayarshi ta karshe ba. Ya juya ya fita yayin da ta bi bayanshi ta dawo da plate da kofi a hannunta, ta zuba mishi ta cicciba ta fita. Ina jiyo sautin tashin muryarsu, suna hira, don haka na janyo wayata na jingina da bango na tsokano My mysterious Man, kamar yadda sunan nashi ya koma yanzu cikin wayata.
Cikin yan kwanakin nan, mun kulla wata irin abota mai karfi dashi. Bai taba kirana a waya ba, kullum daga text sai ta chats kawai muke hira dashi, duk da cewa Allah kadai yasan yadda nake iya cijewa rashin jin muryarshi da ban taba yi ba, ban taba kokarin gwada kiranshi ba. Amma ina kwadaituwa da hakan. Ina yawan tunano yadda muryarshi zata kasance, yadda shi a karan kanshi zai kasance in person. I really want to see him. Amma dai na daure, ina jira in ga iya gudun ruwanshi.
Har Janan ta dawo, ina kan waya ina chatting dina. Ina jinta tana korafin watarana sai ta dauke wayata, ko kuma ta goge whatsapp da duk chats dina, sai dai kasancewar hankalina yayi nisa ko jin abinda take cewa bana yi sosai. Sai da aka kira sallah muka hakura.
Bayan azuhur, zaune muke a tsakiyar dakin, nayi matashin kai da cinyar Jan din tana warware min kalbar da tayi min. Saboda tsananin santsin kaina da tsayi, ban cika yin kitso ba. Idan ma nayi, baya daukar kwana uku yake warwarewa da kanshi. Jan take zaunawa ta min kalba, watarana sai ta sanya rubber bands kanana a karshen kowane kitso sannan yake dan yin kwanaki biyar zuwa sati. Shi yasa ban cika yin kitson bama sam.
Littafin ‘Always a Fighter’ nake karanta mana a fili, lokaci zuwa lokaci zan saurara mu dan dara idan na karanta abin dariya, ko kuma mu dan tattauna akan wani abu daya ratso.
Muna cikin haka sai b’ammm!! Karan turo kofa kamar za’a balleta, gabadayanmu sai da muka zabura muka tashi zaune a firgice.
Mimah ta afko dakin a sukwane, kai tsaye bayan labule ta shige ta kame kamar wadda mutuwarta ta biyota. Cikin mamaki nace “Mimah lafiya? Ke da wa?”.
Kafin ta amsa, an sake turo kofar dakin dai an shigo, muka maida hankalinmu ga kofar gabadayanmu. Anty Sarah ta fado dakin, tana karewa dakin kallo, da alamu Mimah ta biyo.
Sai data karewa dakin kallo tsaf, sannan ta jiyo tana amsa mana gaisuwar da muke mata, ta kara da, “Mimah bata shigo nan bane?”.
Muka kalli juna ni da Janan, ni ce na fara cewa “a’ah, bamu ganta ba”. Daga haka ta juya ta bar dakin. Tana bada baya muka hade kawuna ni da Janan muka kwashe da dariya, tace “baki da kirki wallahi, mutum da diyarshi?”.
Nayi dariya nace “kika san ko laifi tayi zata bata kashi? Sannan yarinyar nan tana bukatar fresh air da hasken rana, na tabbata rabonta da waje tunda aka dawo da ita daga makaranta jiya”, na maida hankalina wajen inda Mimah ta boye, “Mimah fito, ta tafi”.
Ba musu ta fito daga bayan labulen, da gudunta tazo ta haye kan cinyata, na shafa kanta ina murmushi, “meye na gudowa daga gida, laifi kika wa Mommy hala?”.
Ta girgiza kai tana dariya, “naa, naki zuwa ta min wanka ne wai zamu raka daddy unguwa, ni kuma Uncle nake so, yace zai kaini wajen granny”.
Muka yi dariyar yadda take maganar ni da Jan, na kamo kumatunta ina ja cikin wasa, “uhhhh Mimah, soooo adorable. Amma yi hakuri ki tafi kafin Mommy tayi fushi, ki bari idan kun dawo daga unguwar, sai Uncle din yazo ya kai ki”.
Yadda ta dago da sauri, idanuwanta manya, farare tas cike da murna yasa naji zuciyata tayi rashin dadi akan turbar da zan dorata tunda nasan ba lallai hakan ta faru ba, tace “da gaske?”.
Na daga mata kai da sauri, “hmm, ni da Janan ma zamu biyo ku muje tare”. Tayi tsalle daga jikina ta dire cike da murna, “yay!!”.
Gabadaya ni da Janan muka saki dariya, nace “to maza ki tafi kafin ta sake dawowa nan, ki kawo mana tsaraba fa”. Ta fita daga dakin da gudu, ni da Janan muka bita da kallo muna murmushi har ta fita, sannan muka cigaba da tsifar da muke yi.
*
Washegari tun da safe, ina jin ko karfe tara bata yi ba, muna kwance muna barcinmu, muka jiyo ana ihun murna daga falo, hakan ya tashe mu babu shiri duk muka tashi zaune muna sosa idanu.
Su Haleemo ne suke ihun ‘oyoyo, Mommynmu!’, a raina na girgiza kai cike da mamaki. Zuwan suruka gidan surukai tun da safiyar Allah Ta’ala? Ban taba jin haka ba.
Janan ta fara shiga ta wanke baki da fuskarta ta fito, nima na bi bayanta. Bayan mun dan fito more presentable, muka fita falon. Babu kowa, amma muna jin tashin hayaniyarsu daga can dakin Raheemah da yake kusa dana Yaya.
Janan ta ja ni muka leka muka gaidata. Daga ganinta kasan kaga mahaifiyarsu, saboda kama da suke yi da ita gabadayansu, kamar tayi kaki ta tofar. Kallo daya zaka mata kasan cewa ka ga wayayyiyar mace, wadda duniya ta bude mata ido, wayewar kan har tayi yawa. Tun daga kan daurin dankwalin da tayi na yan duniya, da shigar da tayi, hakan yasa na daina mamakin irin shigar dasu Salama suke yi idan zasu fita, daga gani babu tambaya kasan gani suka yi ana yi. Duk da kasancewarta fara, har ma da ‘ya’yan nata, amma daga ganin farinta kasan cewa an kara dana kanti.
Ta amsa mana gaisuwarmu tana yatsina kamar taga kashi, tuni naji matar ta fita daga raina. Tun ma kafin a sallamemu, muka sallami kanmu don bamu ga fuskar zama ba a wajen. Muka dafa abinda zamu dafa muka koma daki abinmu.
Yinin ranar nan cur, haka suka wuni a gidannan suna hayaniya da iface-iface kamar kananun yara. Da rana suka zage suka shiga kicin, kada ku sha mamaki idan kuka ji nace muku har uwar, suka dafa abinci, aka soya nama, su kaji, drinks. Muna daki aka kira mu aka ce muje mu ci abinci, muka fita. Ganinsu gabadaya a zaune suna cin abincin yasa muma muka dosana muka zauna, muka zuba namu muna ci, hankalinmu yana kan talabijin da take ta faman aiki.
Mu muka tattara kan kayan muka je muka wanke, suna rarrashe a tsakiyar carpet din dakin suna hira. Ba wai kuma normal hira ba, a’ah, hira ta gulma da abubuwan da basu dace ba. Su ambaci wannan matar, su kwashe mata albarka ita da iyalanta, su kira waccan, itama dai su mata nasu kalar yankar kaunar.
Bayan la’asar aka sayo musu tsire suka baje a tsakiyar falo suna ci, bayan nan suka kure gidan da kidan Ladi mai Kidan Kwarya, suka sha casun su kamar su kadai ne a duniyar.
Tunda garin ya waye bamu ga giccin Yaya a gidan ba, amma naji dadin haka. I mean, ta yaya zai kalli surukar shi tana irin wadannan abubuwan? Bana tunanin zai kara kallonta da mutunci. Sai dai again, ban sani ko hakan ta saba faruwa dama can ba.
Sai yamma likis sannan ta fito da shirin tafiya, dan siririn gyalenta a kafada kamar wata budurwa. Lokacin muna kicin muna dafa abincin dare, suka shigo kicin din. Da yake kicin dinsu hade yake da store, suka shige ciki. Babu kunya babu tsoron Allah suka dinga jidar mata kaya, kifin gwangwani, naman gwangwani, madarar gwangwani, kai tulin kaya kamar wani provision store ne suka shiga. Sai da suka cika mata leda shake da kaya, sannan ta bar gidan.
Kai kawai nake girgizawa, ina gyadawa cike da tsananin mamaki daya daure min jijiyoyin da suke sarrafa magana a jikina. Nayi tur da wannan rayuwa, ko wa ya fada musu rayuwar auren hauka ce, kuma abin wasa ce? Da har uwa zata dinga zuwa gidan diyarta, tayi bushashar da taga dama, ta kwashi kaya ba tare da izinin mai shi ba ta kara gaba kamar wani abin wasa? Ita daya kamata ta musu gyara, idan taga sun dauko hanya irin wannan ta tsawatar musu, amma ita ce take dora su akan wannan hanyar? Lallai suna bukatar gyara kwarai a cikin lamarinsu.
#F.W.A
*☆⋆11⋆☆*
Kafin yinin ranar Lahdin nan ya kare, gabadaya naji na gama takura da zama a gidan. Na riga na saba da hayaniyar hostel, can hayaniya ce mai cike da nishadi, ko ta tsakanin roommates, classmates, ko abokai. Na riga na saba da rashin shirun can, duk lokacin da naga damar fita, zan dauki hijabi ne in fita kawai, ba kamar gidan Yaya ba. Nan da kofar gida sai ka nemi izini kamar wata matar aure, hayaniya kuma daga ta zage-zage sai ta gulmace-gulmace, don haka ji na nake yi kamar wata fursuna.
Zuwa ranar laraba da Baba ya turo min kudin registration dina, ji na dinga yi kamar wadda take yawo a sararin samaniya don murna. Dungurungum na ki shiga aji na tafi banki na biya kudin makaranta. Aka bani rasiti na tafi ofishin hall admin dake cikin hostel din yanmata na asibitin koyarwa na Shika na kai mata. Bayan ta dudduba files da sauransu dai, tayi assuring dina zuwa ranar Juma’ah zasu bani dakin saboda sai sun bincika wanda bai cika ba. Nayi mata godiya tare da mata sallama, aji daya na samu ranar, daga haka muka wuce gida.
Washegari ranar Alhamis data kasance ranar public holiday, bamu tashi daga barci da wuri ba, muna ta warware gajiyar da muka kwasa cikin wannan satin don lectures dinmu sun fara yin zafi yanzu.
Can da rana, Janan ta fita zata raka wata kawarta da take can cikin unguwar bakin titi. Ina zaune a falo, su Haleemo, Raheemah da Adi na zaune suma suna kallo, aikin da suka saba yi kenan. Yayin da nake wasa da wayata. Babu wanda yake magana a cikinmu sai su da suke hirarsu jifa-jifa. Abinda yake takura ni kenan. Na tsani zama kusa da mutanen da ba zamu yi hira dasu ba, meye amfanin zama a waje dayan to idan ba za ayi hira ba?.
Aka fara kwada sallama daga can waje, duk muka kalli kofar muna jiran a shigo, duk cikinsu babu wanda yayi kokarin tashi. Na mike na fita wajen, ina bude kofar na ci karo da Ummah tsaye. Nayi tsalle na fada jikinta, tayi yar dariyarta mai cike da haiba ta dora hannunta a bayana tana shafawa.
Cikin tsananin murnar ganinta nake gaidata, ta amsa fuskarta na bayyana murmushi sosai. Tace “Na’ilah, idonki kenan ko?”.
Na sadda kaina kasa a kunyace, rabon da inje Kaduna har na manta, sai dai a waya kawai muke gaisawa, to yanzun ma a wayar mun kwana biyu, nace “Ummah kiyi hakuri don Allah, kin san al’amuran makaranta ne suka yi yawa wallahi”.
Tace “ba wani nan, ke dai kawai kice zumuncinki yayi karanci ne!”.
Na fara girgiza mata kai da sauri, “Allah da gaske fa Umma…”, sai lokacin na tuna a kofar falo fa muke tsaye. Da sauri na matsa gefe daga cikin falon ina cewa, “Ummah shigo don Allah”.
Ta shigo ciki tare da cire takalminta, fararen kafafunta da suka sha lalle jawur gwanin sha’awa suka bayyana. Muna shirin wucewa, Janan ta fado falon. Tana ganin wadda take gabanta ta tsaya cak, “Ummah na?”. Sai kuma tayi tsalle ta dafe ta, na matsa gefe ina kallonsu cikin burgewa.
Hannunta ta kama ta fara ja kamar wata karamar yarinya, ni kuma na bi bayansu. A falo babu kowa haka muka tarar dashi kamar ba yanzu-yanzu na bar mutane suna kallo ba. Ga kuma talabijin din tana aikin yi. Gabadayanmu sai da muka dan dakata, sannan Janan ta wa Ummah jagora zuwa dakinta. Ummah tace “ni fa ba zama zanyi ba, yanzun nan zan koma Kaduna direba yana jirana a waje”.
Ta turo baki cikin shagwaba, “amma dai kin tsaya ko ruwa ne ki sha ko? Sannan ku gaisa da mutanen gidan”.
Ummah tace “suna nan ne? Naji gidan shiru”.
Tace “ina zasu je? Yanzun nan da suke kallo anan falo fa, kila sun gaji da zaman ne suka koma daki”. Ummah ta lalubi kujerar roba daya da take dakin ta zauna akai, Janan ta fita da sauri zata dauko mata ruwa. Gefen katifa na zauna, Ummah tana tambayata karatu da kuma yanayin damina daya fara shigowa, nace lafiya lau.
Babu jimawa Janan ta dawo dakin hannunta dauke da gorar ruwa mai sanyi, Ummah tana sha ko rabi bata yi ba ta mike tsaye, muma duk muka mike.
Janan tana turo baki ta kamo hannunta ta rike, “yanzu Ummah na maimakon ki jira sai yamma tayi sannan ki tafi?”.
Umma tayi dariya tana rungumota jikinta, “Janan kenan, nasan idan kika ji na shigo Zaria ban leko nan ba ba zaki taba bari in samu lafiya bane shi yasa yanzun ma nazo”.
Ta kara turo baki, “ni ai dama nasan kin daina so na yanzu shi yasa!”.
Ni da Ummah duk muka dara, tace “yanzu idan na daina sonki wa zan so Janan??”. Bata amsa ba sai baki data kara turowa.
A kofar dakin Raheemah muka tsaya, Janan ta tura kofar, amma gam, a kulle. Tasa hannu ta dan kwankwasa, nan ma shiru, babu ko alamun motsin mutane. Da ace ba kofar fita daya bace a gidan, duk inda zaka je dole sai kabi ta babbar kofar falo, da sai ince ko ta wata hanyar suka bi suka fita daga gidan. Amma suna zaune fa a falon tazo, daga zuwa bude mata kofa ta shigo har sun bace kamar masu tafiya akan iska? Shin hakan yana nufin da gangan suka buya kenan??.
Ummah ta kallemu tana dan murmushinta na manya, duk da haka zaka karanci damuwa da rashin jin dadi a cikin idanunta. Tace “da alamu ko barci suke yi, kada ku tashe su. Bari kawai in tafi, watarana idan na dawo in Allah ya yarda sai mu gaisa din”.
Janan ta daga baki zata yi magana, nayi saurin girgiza mata kai alamun kada tace komi, nasan ce mata zata yi bai ci ace sunyi barci ba yanzu, hakan kuma shi zai ba Ummah damar sanin da gangan suka shige daki suka rufe mata kofa duk da dai ina zargin da kyar idan bata harbo jirgin ba. Janan ta kama bakinta ta datse, muka saka Ummah a tsakiya muka fita.
Sashen Yaya Jameel ta tsaya, nan kuma sai da muka kwashe kwararan mintuna uku muna buga kofa, har mun fara tunanin kila basa gidan ko kuma barcin rana suke yi, mun fara tunanin mu juya kawai, sannan muka ji alamun ana taba kofar alamun za’a bude. Anty Sarah ta bude kofar tare da dan fitowa waje, alamun bata da niyar barin wanda yake buga mata kofar ya shiga ciki.
Sai dai tana ganin Ummah, ta fara fara’a da nan-nan da ita, “su Ummah ne? Ku shigo daga ciki mana! Sannu da zuwa Ummah, sannu, ya hanya?…”, ta fara jera mata sannu har ta zauna akan kujera. Ko zama bata yi ba ta fada kicin dinsu da sauri.
Ni da Janan kam falon kawai muke bi da kallo, da alama ta canza kayan daki akan wadanda muka sani da. Wannan wasu irin saitin royal kujeru ne purple da gold, gaskiya sunyi kyau ba karya. Ga kamshi da sanyi mai ni’ima da yake tashi, irin mai warware gajiyar nan. Dama can Anty Sarah ba daga nan ba indai ta fannin tsabta ne, babu na biyunta.
Ta fito daga kicin din hannu niki-niki da tarin kayan motsa baki akan wani katon tray, ta ajiye a gaban Ummah ta hau zuzzuba mata. Sai bayan data zuba mata komi sannan ta zauna a kasa a gefenta tana gaidata cike da girmamawa, Ummahn ta amsa.
Tace “ai kuwa yanzu suka fita shi da Mimah”.
Ummah tace “ehh, na hadu dasu a babban gida (main house dinsu), Hajiya babba ce bata ji dadi ba kwana biyu dama shine nazo na dubata kuma sai nace bari in biyo a gaisa, kwana biyu”.
Anty Sarah ta sadda kanta kasa tana dan murmushi, “wallahi kuwa Ummah, muna ta cewa zamu leka ku, bamu samu dama bane”. Daga ji kasan ta fada ne kawai, amma duk da haka dai tafi wadda ta rufe kofar dakinta ma gabadaya.
Ummah tace “dama haka ne, bari mu wuce mu”. Tace “Ummahn tun yanzu? Ba zaki bari mu sauke abinci ba, yanzu aka dora”.
Ummah tace “Allah ya amfana, amma nagode”. Ta mike, da sauri Anty Sarah ta koma kicin din, sai gata ta dawo da leda a hannunta, ta juye duk snacks din data kai a ciki, ta mikawa Janan. Daga nan muka mata sallama, ta biyo bayanmu har bakin kofa, ta wa Ummah Allah ya tsare hanya, ta maida kofarta ta gamtse. Ni da Janan duk kai muka jinjina kawai, muka takewa Ummah sawu har inda direban daya kawota yake jiranta.
Janan ta bude mata gidan baya ta shiga, ta dora mata ledar wajen Anty Sarah akan cinyarta.
Kafin direba ya ja motar su tafi ta kalleni, “yata Na’ilah, yakamata ki daure watarana ki zo mana weekend mana?”.
Na yi murmushi a dan kunyace, “in Allah ya yarda Ummah, zamu zo”.
Ta gyada kai, “to madallah, a maida hankali kan karatu dai. Allah yayi muku albarka”. Duk muka amsa da ‘ameen’. Direban yaja suka tafi. Sai da Ahmad maigadi ya maida kofar ya rufe bayan sun fita daga gidan sannan muka juya. Har muka shiga cikin falon babu wanda ya furta uffan a cikinmu.
Muna shiga falon muka ci karo da Adi da Raheemah a zaune abinsu, suna kallo. Wato da gaske dai suna sane suka gudu daki? Haushin abin ya cika ni, naji kamar in rufe su da duka su duka. Duk da ba ni suka wa abin ba, amma zafin da naji sai naji kamar ni ce naje gidan Yaya, matarshi ta rufe kofar dakinta don kada mu gaisa.
Duk da yadda naso danne zuciyata, hakan bai hana tsakin da nake ta dannewa ya fito ba. Daidai lokacin da zamu wuce su.
Adi ta wani tashi a fusace ta rike kugu, “ke malama waye kike ja wa tsaki a cikin dakin nan? Kin ga sa’an ki anan?”.
Na tafi zan zagayeta ni da Janan, tayi saurin kamo wuyan hijabina ta janyo ni, na dawo muna fuskantar juna ni da ita ido da ido, tayi kasa-kasa da nata idanun cikin masifa, “wato yarinyar nan naga alamun wuyanki yayi kauri da yawa irin zama a gidan mutane yayi miki dadin nan. Ke har kin isa in dinga miki magana ki maida ni yar iska?”.
Na kalli tsakiyar idanunta, ina kara nuna mata nima ba kirkin nan gare ni ba fa, nace “ai banyi zaton dani kike ba ganin cewa ni din ba yar iska bace. Maganar kiba kuwa da kike cewa nayi, gwanda ni ina girmama wadanda nayi kibar ta dalilinsu, ke kuma me kike yi?”.
Ta fara hura hanci, dama gasu tubarkallah kamar kofofin wando, tana daga murya, “kan abu ta kazar abun nan!! (ta kawo zagi ta narka). Lallai yarinya kin daukowa kanki ruwan dafa kanki!. Ni zaki daga wannan tsantsaman bakin naki ki zaga kamar wata sa’ar wasanki? To wallahi na rantse da Allah yau ko ni ko ke a gidannan, sai naga wanda ya daure miki gindi!!”.
Wani abin ban dariya shine, gabadayanta bata wuce sa’ar mu ba, abinda nafi tunani kenan tunda ko a tsayi ma na fita. Na kyalkyale da dariya, ina watsa mata wani kallon kaskanci tun daga sama har kasa, duk iskancinta sai data rusuna. Ina shirin maida mata amsa daidai da ita, Janan tayi saurin kama hannuna taja ni.
Adi ta fara ihu, “idan ba tsoro ba ki tsaya mana ki gani?! Wallahi da sai na nada miki na jaki, yadda ko uwar data kawo ki duniya ba zata gane ki ba!!”.
Janan dai ta samu ta ja ni daki, ta maida kofar dakin ta rufe, amma duk da haka bamu fasa jiyo zage-zagen da Adi take yi ba, har Salama data fito itama ta sanya baki itama tana nata kalar zagin da gori. Wai anzo musu gida an zaune, an ki tafiya saboda sanyin AC da naman kaza, ni abin ya ma so ya bani dariya.
Na tsaya a tsakiyar dakin ina ajiye ajiyar zuciya daya bayan daya da sauri-sauri. Ta kalleni, “haba Na’ilah! Sau nawa nake fada miki ki daina biyewa wadannan mutanen? Kin san cewa ba ajinki bane ki zauna kuna sa’insa dasu ba ko?”.
Na harareta cike da fushi, “wai sai ki dinga magana kamar baki wajen lokacin da take sauke min kwandon zagi da dibar albarka!”.
Tace “ko ma menene dai, rashin tankawar yafi tankawar dai. Meye alfanun musayar kalamai, meye a cikin hakan?”.
Na watsa hannuwa sama frustrated, “koma dai menene. Allah ne ya rufa mata asiri bata kai ga daga hannunta a kaina ba, da wallahi sai na baje shegiya yau a gidannan!!”.
Janan ta girgiza kai kawai, ta fada bandaki tana furta “Allah ya shiryeki ke kam!”. Nace “ameen”, cike da izgilanci.
Sai dana huce sannan na zauna a gefen katifa. Sakon text din mysterious daya shigo wayata a lokacin ne ya kara sauko da zuciyata kasa sosai. Na hau karanta sakon ina kara maimaitawa kamar mai harda, daga karshen sakon nashi ya rubuta *’talk to you soon babe!’,*
Shin hakan yana nufin mun kusa yin waya dashi? Nayi tsalle na sake dira akan katifa ina dan ihun murna, Janan da fitowarta daga bandaki kenan ta kalleni baki a dage, “ke kuma lafiyarki lau kuwa? Yanzu-yanzu kina fushi, yanzu kuma kina ihun murna again?”.
Na harareta cike da wasa, fuskata na dauke da murmushi.
Washegari Juma’ah, muka shiga asibiti. Muna fita ajin karfe goma na yiwa ofishin hall admin tsinke. Nan ta bani lambar daki da teller, sai dana fara zuwa bank na biya kudin sannan na sake dawowa wajenta nayi clearance. Dakin mu uku ne, ka’ida mutane biyu ne a kowane daki, amma kasancewar wannan karon muna da yawa shi yasa suka maida shi uku per room. Ni duk bayanan da take yi ba jinta nake yi ba, ban damu ko mu hudu ko biyar zamu zauna ba, bukatata kawai in samu dakin.
Tana miko min makullin dakin, na karba na mata godiya na bar ofis din.
Dakin na fara zuwa na gani, wadanda suke zaune a dakin basa nan lokacin. Na sanya key na bude dakin, na kare mishi kallo sannan na maida dakin na rufe na koma class.
Lokacin period ta biyu ya ma kusa cika, don haka na samu wasu seats da aka tanada a gaban classes na zauna ina jiran su fito. Kafin su fito na ciro wayata na turawa Yaya text din abinda ya faru. Babu jimawa ya turo min da sakon taya murna da tambayar yaushe zan koma cikin hostel din gabadaya? Nace mishi sai ranar Lahdi, nasan duk abinda zanyi Janan ba zata bari in koma gobe asabar ba.
Ina nan har suka fito, na tari Janan a hanya muka dauki hanyar barin asibitin kasancewar mun gama da ranar. A hanyar nake fada mata yadda muka yi da hall admin da kuma ranar da zan koma hostel din. Daga ganin yadda ta turo baki nasan bata yi na’am da maganar ba, don haka na canza maganar kawai zuwa wata.
Yau ma kamar yawancin ranaku, gidan babu kowa muka same shi. Muka tura kofar dakin Janan muka shiga, kayan jikinmu muka fara ragewa muka dauro alwala muka zo muka tada sallah.
Da yamma wajen karfe hudu da rabi muna tsakiyar falo a kwance muna kallon ‘Baaghi’ a tashar Zee World. Meat pie din da Anty Sarah ta miko mana ne daga dawowarmu muke ci da lemun fanta na pineapple a kusa damu.
Gardama muke akan tsakanin jarumi Tiger Shroff da Hrithik Roshan wa yafi wani iya rawa?.
“ina fada miki Hrithik shine oga, ni gani nake duk duniya babu kamar shi ma. Kin san dai idan fannin rawa ne, babu wanda zai iya gwada mishi ko wanene kuwa, kada ma ayi zancen physique, halitta, kyawu, and his eyes! Ya Allah, how I love his eyes!!”. Na fada dreamily ina kara zooming hoton shi dake cikin wayata ina kara nuna mata idanunshi da suka fito sosai a daukar da aka mishi.
Janan ta kada idanu sama, “nasan da haka, amma ki duba, Hrithik ya fara tsufa yanzu, Tiger shine jarumi mai tasowa yanzu, sannan idan halitta ce, shima fa Tiger ba baya bane, ga iya lankwasa jiki da acting”.
Na mike zaune sosai, sautin muryata ya fara yin sama, “ni fa komi zaki ce, babu abinda zai canza min tunanina, Hrithik ne nawa. Sannan wa yace miki Hrithik ya tsufa? As in kin kuwa ga yadda yarintar shi take kara fitowa yanzu?”.
Ta daga baki kenan zata musa, sai ga sautin, “idan kun gama musun naku, zaku iya taimaka min da wadannan kayan?”.
Da sauri muka daga kai zuwa inda muka ji sautin maganar. Yaya Bilal ne tsaye a tsakiyar falon ya nade hannu a kirji. Sanye yake da suits ash color, ya sanya tie baki mai ratsin ash color akan white linen shirt din daya sa a kasan suit din. Cikin yan sakannin dana yi ina kare mishi kallo, naji ina raya ‘wannan shine ainihin misalin wanda yarintar shi take kara fita kullum’, a cikin zuciyata.
Da sauri duk muka tashi muna mishi sannu da zuwa. Ya amsa mana yana dan murmushi, “wato maimakon ku zauna kuna debate ko quiz akan karatu, sai ku zauna kuna gardama akan mazajen mutane ko? In anyi magana kuma sai ku ce duk duniya kun fi kowa yin karatu ko?”.
Janan tace “wallahi Yaya ba haka bane, yanzun ma hira ce kawai, arashi ne aka yi kai kuma kazo a daidai lokacin”.
Yace “whatever, kuzo ku taya ni dauko kaya a waje”. Ya juya ya fita, muma muka bi bayanshi. Doguwar riga baka kirar kasar Saudiya ce a jikina, dama gyalenta yana kan kujera don haka na dauke shi na dora shi a saman kaina.
Kayane zube a kofar falon, kayan miya ne, vegetables, su doya da irish potato. Ahmad yake ta daukosu daga cikin mota yana ajiyewa a kofar falo, bakin kofar falon nan ne iyakar da Yaya ya musu. Ba’a barinsu su wuce nan.
Muka fara daukar kayan zuwa kicin sai da muka gama gabadaya. Yaya ya zauna akan kujera a falo yana cire takalmin kafarshi, Na dauko ruwa mai dan sanyi a cikin firjin na dora akan karamin tray na roba da cup, na kai gabanshi na ajiye.
Janan ce ta tsiyaya ruwan ta mika mishi ya karba yana furta “thank you”.
Sai daya kusa shanye ruwan gorar gabadaya, ya ajiye kofin ya koma jikin kujerar ya jingina. Ya cewa Janan “gabadaya kayan can ku raba su uku, kashi daya ku mika gidan Jameel, dayan ku zuba su a cikin wani abun za’a kaiwa Ameerah, sauran ku ajiye su na nan ne”. Muka ce “to”.
Yace “ina Raheemah ne?”, muka kalli juna ni da Janan, itace tace “bata nan!”.
Ya karkata kanshi gefe daya kamar cikin mamaki, yace “ina taje?”. A lokaci daya muka ce “bamu sani ba!”.
Yayi shiru kamar cikin tunani kafin ya girgiza kanshi a hankali, ya tashi tsaye, “shikenan, kuje”. Muka wuce kicin abinmu.
Muna gama aikin daya sanya mu, muka dora girkin dare. Sai gab da magriba sannan suka dawo gidan. Raheemah ce ta leko kicin din, muka mata sannu da zuwa, ko amsawa bata yi ba ta fara jero mana tambayar “yaushe baby ya dawo? Ya tambayi inda nake?”.
Janan ce ta amsa mata, ni kam juyawa nayi ina juya miyar da muke yi, tace “tun dazu dai, kuma ya tambayeki muka ce kin fita”.
Taja wani dan siririn tsaki ta juya ta fita, muna jiyota ita da Adi a falo tana tambayarta me zata ce mishi idan ya tambayeta inda taje? Adin tana cewa “meye na wani rikicewa don ya dawo baki nan? Kawai ki fuske ki ce mishi wajen Momcy kika je mana!”.
Raheemah din tayi ajiyar zuciya, “baki san abinda muke ciki bane kwanannan, a saman ruwa muke dashi wallahi!”.
Adin taja tsaki tana cewa “sai kiyi kuma, na tabbata ko tambayarki ma ba zai yi ba”. Daga haka suka shige daki.
*
Washegari na hade kan kayana tsaf waje guda, nayi wanki da guga da sauransu. Ranar Lahdi Yaya ya bada mota da yamma, Is’haq direban gidan wanda yake musu aikace-aikace ya kaimu hostel ni da Janan. Sai ranar muka hadu da roommates dina, daya musulma ce yaren Ibira, sunanta Murjanatu, dayar kuma Esther Christian ce. Janan ta taya ni hade kan kayana waje guda muka shirya su, daga nan ta min sallama ta tafi. Na rakata har waje ta hau bus ta tafi, sannan nima na juya na koma hostel.
#F.W.A
*☆⋆12⋆☆*
“Ok, spill the beans, me yake faruwa dake ne?”.
Janan ta tambayeni. Fitowarmu daga labour ward kenan da yammacin ranar Laraba, mun tsaya a wani karamin gidan cin abinci dake nan mini market din asibitin. Na fasa lemun Dudu na jefa abin zuka a ciki ina kallonta cike da alamun tambaya, “ban gane ba, me yake faruwa dani?”.
Tace “na fahimci tun shekaranjiya kamar jikinki a sanyaye yake, wani lokacin ana miki magana amma ba kya ji, ko kinji sai in ga kamar ba kya wajen saboda kinyi nisa a cikin tunani. Wani abu yana damunki ne? Ko kuma baki da lafiya ne? Kin gaji da zaman hostel dinne?”.
Nayi murmushi jin tambayarta ta karshe, na girgiza mata kai, “ko daya, kawai dai…”, ta dago kanta da sauri tana kallona cikin sauraren jin mai zan ce.
Na kawo ajiyar zuciya na sauke tare da girgiza kai, “na kasa fahimta ne ni kaina wallahi, kwana biyun nan sai in ga kamar Umar yana min kauce-kauce, amma ban tabbatar ba”.
Ta kalleni a nutse bayan ta taune egg roll din data kai baki ta hadiye, ta kora da lemun la Casera. Tace “me yasa kika ce haka? Ko kuma ince me kika gani?”.
Nace “na farko kusan sati daya kenan rabon da in kira Umar ya daga, daga farko ya fara biyo baya, ya cikani da maganganu marasa kan gado akan wai aiki ne yayi yawa, to yanzu yau kwana uku kenan rabon daya daga kirana ko kuma ya kirani ma. Sannan baya maido min da replying din message idan na mishi. Ke duk chats dinshi babu inda ban bishi na mishi magana ba, amma a banza, na fara damuwa”.
Tace “haba, kada ki wahalar da kanki a banza mana, kamar yadda yace, zata iya yiwuwa aiki ne ya sako shi a gaba!”.
Nace “shine kuma zai kasa daga wayata balle messages dina? Gaskiya sai dai wani abu daban, amma ba wannan ba. Ko lokacin da suka yi posting dinsu, abubuwa ai sun fi haka tsanani, amma a hakan yake samun lokaci ya amsa kirana har ma yazo ya ganni, balle yanzu”.
Ta gyada kai, “haka ne kuma. Amma ki kara bashi lokaci dai, baki san abinda yake faruwa dashi ba, zata iya yiwuwa wani abun ne daban”.
“to shikenan!”. Na fada ina karasa juye sauran lemun daya rage a bakina, na jefa robar cikin kwandon ajiye shara na kalli Jan data gama jefa nata itama, nace “muje muyi sallah a hostel ko? Karfe hudu yanzu zata yi, kuma kinsan hudu da rabi ya kamata mu koma”.
Duk muka mike muna daukar jikkunanmu, muka dauki hanyar hostel. Hostel dinsu yana da nisa da ainihin cikin asibitin, tafiyar kusan mintuna goma sha biyar ce. Muna isa alwala kawai muka yi, muka yi sallah, muka koma ward din da aka kaimu wannan satin.
Muna zaune a reception, Janan tana rubuce-rubuce, ni kuma ina gyara wasu files. Karan shigowar kira a wayata ya katse mu, abu na farko daya fara fado min rai kawai shine Umar. Na rarumo wayar da sauri, a raina ina raya kalar dibar albarkar da zan mishi. Sai dai duk wasu alwasai na sai suka koma can bayan zuciyata, sakamakon ganin mai kiran ba Umar bane, Maryam ce.
Na dan matsa can gefe kadan saboda hayaniyar mutane na daga kiran, maimakon muryar Maryam sai naji ta Aliyu. Babu kunya wai gaisheni yake yi, “Yaya Na’ilah ina yini?”.
Mamaki ya kama ni, tunda na dawo babu wanda ya neme ni a gidan, daga iyayen har ‘ya’yan. Kiran Aliyu a yanzu yana nufin abu daya ne,
Na daure na amsa da “lafiya lau Aliyu, ya kuke?”. Ya amsa da lafiya lau, tare da fara kame-kamen tambayar ya karatu na da sauransu dai. Daga karshe dai ya dire a ainihin dalilin da yasa yayi kiran daga farko.
“Kati zaki turo min, subscription dina ya kusa yayi expire!”. Wani lokaci sai in dinga mamakin ko ajiye ni yayi a matsayin personal bank account dinshi, da zai dinga cirar kudi a duk lokacin da yaga dama?
Sai dai Allah bai halicceni da riko ba, sannan bana rikon mutum inyi amfani da hakan idan yana bukatar abu a wajena in wulakanta shi. Bugu da kari ina son ‘yan’uwana, ina kuma iyaka bakin kokarina wajen ganin na kyautata musu, na hidimta musu, matukar ina dashi ina musu iyaka bakin kokarina. Ba yabon kai ba, ina hana kaina ko cikina in ciyar da nasu cikin ko wata bukata tasu.
Su sun san da haka, ina zaton shi yasa suke amfani da wannan damar suna taka ni yadda suke so.
Nace mishi “har katin nawa kake so kuma?”.
Yace “na dubu daya da dari biyar ma ya isa”.
Na girgiza kai, ni kaina wannan watan ban yi subscribtion ba, kodayake Allah ne yasa Janan ta mana ni da ita. Nace “zan turo maka zuwa anjima, yanzu muna cikin ward sai mun fita”.
Yace “babu damuwa, Maryam ma na bidar katin dari biyar”. Babu ko godiya ko karin bayani, ya maidawa Maryam wayarta sai itace ta min godiya sosai. Daga nan muka kashe wayar.
Saboda haka muna fita daga ward din da misalin karfe shida na yamma, na tsaya a kasan ginin na sayi kati na tura musu. Zan yiwa Janan rakiya kamar yadda na saba yi mata, tace “yau dai an hutar dake, ga Almu na can yazo daukata”.
Na kalleta ina daga mata gira cikin tsokana, “shi yasa tun dazu baki yaki rufuwa, masoyin usul yazo gida!”.
Janan ta kai min duka a hannu tana yar dariya, “ni bana son sharri irin naki fa!”.
A haka muka karasa jikin motar Almun Jan, silver Matrix 56 ce, daga ganinta ko dai sabuwar yayi ce ko kuma sabuwa ce dal, yadda take ta sheki da walwali. Yana ganinmu yayi kasa da gilashin motar yana murmushin shi da kullum baya barin kan fuskarshi.
Al-Mustafa kyakkyawan namiji ne, fari, dogo, mai dan jiki. Yana da kirki, haka gabadayan yan’uwanshi suke, wadanda muka sani kenan. Mazauna garin Kaduna, a takaice ma a unguwar NDC unguwar kaji, unguwar su Ummah ainihin gidansu yake. Yayi degree dinshi anan Jami’ar Kongo, yanzu haka lauya ne mai zaman kanshi anan Kaduna din. Soyayyarsu da Janan ta samo asaline tun daga zamanin da take sakandire, suka kulla soyayyarsu mai tsafta, gashi har yanzu suna tare, kuma ana son juna. Ba shi kadai ba, hatta da yawancin yan gidansu sun sanni, na sansu saboda yawan zuwa Kaduna da nake yi, kuma muna yawan zuwa can gidan ko kuma su kannenshi su zo mana. Daga ganinsu kuma Janan ba zata samu matsalar zama dasu ba, saboda suna da kirki da sanin yakamata.
Na gaishe shi a nutse, har ya hada da yar tsokanar daya saba min idan muka hadu, muna ta dariya. Daga karshe dai Janan ta shiga gaban motarshi ya tasheta yana kallona, “to Na’ilar Janan di ta, in shaa Allah a yau dinnan zan wuce Kaduna, sai dai in ce sai Allah yayi mana dawowa kuma”.
Na gyada kai ina dan murmushi, “haka ne, to Allah ya tsare hanya. A gaida mutanen gida”.
Yayi murmushi, “in ce musu me? Wadda ta guje su shekara da shekaru babu waiwaye tana gaida su?”. Ya fada cike da tsokana.
Nayi dariya sosai, “ni wannan korafe-korafe naku dai, in Allah ya yarda hutunmu na gaba zan samu inje Kadunar nan dai, ko kwana biyu ne in muku hakanan”.
Yace “inaa, ai rike ki zamu yi sai kin karas da hutunki sannan zamu sake ki”.
Na girgiza kai ina murmushi, nace “to ai shikenan, yadda kuka ce haka za ayi. Ku gaida gida”. Na musu sallama na wuce don nasan idan na tsaya zamu iya kaiwa har magariba anan muna hira, abin kamar a jinin shi yake, idan kuna hira dashi sam baka sanin lokaci yayi, kafin ka ankara sai dai kaji ka kwashe awanni dashi kuna hira. Ko kuwa yanayin aikinsa ne?.
Har na karasa hostel ban ji daga Maryam ko Aliyu ba, hakan yana nufin katinan sun shiga kenan. Idan naji kiran waya ko please call me bayan na tura kati, hakan yana nufin nayi kuskuren lamba kenan, dana tura kuma zan ji su dif, sai kuma bukatar hakan ta sake tasowa. Maryam ce ma ke kokarin kira lokaci zuwa lokaci haka nan a gaisa.
Akan katifa dana nade ta da zanin gado yellow mai dauke da kwalliyar Malam buda min littafi da wasu kyawawan furanni na zube, da uniform dina da komi har takalmin toms baki da yake kafata. Dakin babu kowa, da alamu basu dawo ba ko kuma sun shiga makotan dakunanmu. Yau ba karamar gajiya muka nada ba, yadda majinyata suka dinga karakaina a ward din da aka tura mu yasa bamu samu mun zauna ba ko da wasa. Na lumshe idanuna a hankali, ina jin gajiyar jikina na neman rinjayata barci ya daukeni. Da sauri na tashi zaune.
Kayan jikina na hau cirewa, na rataye su a jikin kusa dake jikin bango, na daura zanin atamfa tare da dora wata T-shirt baka akai, hula na dora akaina na fita tare da kulle dakin. Can kasa na sauka, da yake a sama muke. Sai dana tsaya a tap na debi ruwa, na daura alwala sannan na ciccibi bokitin ruwana na koma sama.
Murjanatu na tarar a dakin, na mata sannu kawai. Ita kadai take hadamu da ita tunda nazo dakin, wani irin girman kai ne da ita, tunda ta ganta da wata akwalar 406 data fara cin duniya, gani take yi kamar ita din wata shegiya ce. Ni kuma naga meye abin dagawa akan haka? Akwai masu motoci da suka ninka nata a kyau da tsada da ake zaman lafiya dasu a cikin hostel din, wadanda iyayensu suka fita kudi ma. Ni fa ganina nake daidai da uban kowa, yadda kake sanya sutura mai tsada kayi kyau, haka nake saka mara tsada inyi kyau, har ma a kasa banbance mu. Abinda zaka fini kawai in damu, shine yawan maki, a test, assignment, exam ko result, wannan shine kawai. Itama don ta ita ne da bamu gaisa ba, sai dai ni ba’a zaman gaba dani. Ko sannu sai ta hada mu da kai, in yaso zabi ya rage naka, ko ka amsa, ko kar ka amsa, matsalarka ce, ni dai na fita hakkinka. Esther ce muka fi mutunci da ita dama.
Kafin a kira sallah na dora jollop din macaroni, ana kiran sallah na rage wutar karamin gas din dana saya na tada sallah ta. Murjanatu tana zaune a gefen wayarta tana hira da saurayinta har na gama sallah ta na zuba abinci, tunda nazo dakin na kula sallah bata dameta ba ko kadan. Yau da asubahi dana tasheta sallah, cewa tayi period take yi. Sai da rana ta fito gade-gade, tana kallonta suna kallon juna, wai ta kalli gabas ta tada sallah. Na girgiza kai kawai dana tuno abin.
Tayin abincin na mata ta girgiza kai kawai taci gaba da wayarta, nima na girgiza nawa kan na saka cokali na fara ci. Ko loma uku banyi ba Esther ta shigo dakin, nan ta dauko nata cokalin muka zauna muka ci muka yi nak, har da kari. Na sauka kasa na wanke plate din, na sake dauro alwala na dawo sama.
Kan sallaya na koma na zauna ina lazumi har aka kira sallar isha’i nayi. Karfe takwas saura na dauki dan karamin littafin da nake daukar bayanai idan mun shiga ward, textbook akan matsalar da mata ke fuskanta yayin da suke dauke da juna biyu, sai kuma biro da pencil na sauka kasa. Common room naje na zauna, ba jimawa aka fara hasko diramar da nake zuwa kallo kullum. Ko bayan an gama anan na zauna can wani lungu inda babu hayaniya sosai, na cigaba da bita da karatuna har karfe goma tayi. Na mike na koma daki.
Yanzu kuma Murjanatu ce bata dakin, babu mamaki daya daga cikin samarinta ne yazo.
A rayuwar makaranta, musamman wadanda suke zaune a cikin hostel, babu abinda idanunka ba zasu jiye maka ba. Babu tabara, rashin kunya da banzatar da kai da ba zaka gani ba.
Kai ne iyayenka suka taso ka tun daga wani gari, suka kawo ka wani, domin me? Domin fa kayi karatu ne, idan kuma kayi kai zai yiwa amfani ba wani ba. Amma sai kazo, ka biyewa kawaye da samarin banza ayi ta bushasha da dibar albarka, har ma ka manta da abinda ya kawo ka. Ka ci amanar kanka, ka ci ta iyayenka, ka kuma yaudari kanka. Tunda daga karshe dai, su wadanda ka rike din, zasu zo su maka tawaye, kawaye da suka zuga ka su yaye maka baya su koma gefenka suna maka dariya, samarin banza da suka daure maka gindi su samu wasu da suka fi ka, su kyaleka. A lokacin ne kuma idanu zasu raina fata, an barka da carry overs in ma kayi rashin sa’a da spilling, daga nan idan shaidan ya maka huduba, ka koma bin lecturers domin gyara takardu. Idan kuma hakan bata samu ba, a barka da hamma, kayi babun badinihu, baka ga tsuntsu baka ga tarko, sai zare idanu. Lokacin ne kuma zaka yi dana sani.
Yanzu ita Murjanatu da muke magana a kanta, yar spilling ce. Kamata yayi ace yanzu ta gama nata aikin tana internship kamar yadda sauran yan ajinsu da suka gabata suke yi yanzu haka anan Shika din, amma gata nan.
Yanzu haka har nayi shirin kwanciya barci na kwanta, bata dawo dakin ba. Sai wajen karfe goma sha biyu da rabi na dare sannan ta turo kofar dakin ta shigo. Ina kallonta ta cikin dusu-dusun hasken dakin ta kwanta akan katifarta. A raina na nema mata shiriya da ita da sauran masu hali irin nata, Allah ya nuna musu hanya madaidaiciya.
#F.W.A
*☆⋆13⋆☆*
“Assalamu Alaikum wa Rahmatullah wa Barakatuhu, ina fata kin wayi gari cikin koshin lafiya ya ke ma’abociyar haske dake haskaka fadin zuciyata bakidayanta!”.
Kamilalliya, kuma tattausar muryar ta fada, cikin wani irin huskinesa da sexiness da… da… abubuwa da dama.
Jin muryar kadai ya haifar min jin wasu abubuwa, wadanda nafi fahimta a cikinsu shine faduwar babu gaira babu dalili da gabana yake yi, sai kuma wata irin kasala, sauran na kasa fahimtar ko meye kuma.
Karfe tara na safiyar ranar asabar, sai dana kusa tuntsirawa kasa lokacin da vibrating din da wayata tayi ya tashe ni daga daddadan barci da nake yi. Sai dai ba wannan bane yasa nayi suman zaune ba, ko kuwa kwance zan ce? Sunan wanda yake kiran ne da yake tsalle yana rawa akan screen din wayata ya kusa sumar dani. Mamakin ya wuce misali, haka fargabar ta wuce misali, nayi zaton mafarki nake yi, hakan ne yasa na kurawa wayar idanu tana ta ringing, wakar Chainsmokers da cold play ta ‘something just like this’ tayi-tayi har ta katse. Ba’a dauki wani lokaci ba aka sake kira, nan ma dai naci gaba da kallon wayar. Sai a karo na uku ne na samu kuzarin kifta idanuna, sannan na daga wayar na kara a kunne.
Muryar data fara dakar kunnena rendered me speechless, na kasa magana. Na tabbata a lokacin da za’a dauki abin gwajin bugun zuciya, za aji zuciyata tana gudun fanfalaki.
Na sha ayyana yadda muryar wannan bawan Allah zata kasance, har mafarki na sha yi. Amma muryarshi da naji yanzu, ban taba tunanota ba, ban taba mafarkinta ba, ban taba jin mai kama da ita ba.
Na hadiye yawu mukut! Da kyar na iya warto murya da natsuwata da suka fara shawagi a saman kaina suna kokarin dagula min lissafi.
Cikin rawar murya dana rasa dalilinta, na amsa. Zata iya yiwuwa saboda yadda muryarshi ta sanya zuciyata tsalle ne, ko kuma saboda yadda muryar tashi ta sanyayar min da jiki ne, zata kuma iya yiwuwa saboda yadda abin yazo min a bazata ne, za kuma ta iya yiwuwa duka abubuwan ne.
Yace “wow, Masha Allah, ban taba tunanin muryarki zata kasance haka ba, lallai tsarki ya tabbata ga Ubangijin daya tsara ki, ya baki murya wadda zata iya shagaltar da mutum ga yin abu, shin ko ya zaki kasance a fili?”.
Sai naji kunyar maganganunshi sun kama ni, don haka na buge da gaida shi. Ya amsa, ya kara dorawa da, “To daga farko dai sunana Muhammad M.B, ni bahaushe ne sannan ina aiki a Abuja, ban sani ba ko malamar ta ganeni?”.
Nayi yar dariya, “na gane ka mana, Mr. Mysterious!”.
Ya saki wata irin tattausar dariya data sa na kara narkewa akan katifata, jin muryarshi nake kamar ana min busar sarewa a kunne, yace “da gaske nayi zaton sai na zauna dogon bayani, shi yasa tunda gari ya waye nake ta hardar abinda zan fada miki, ki ce da ban wahalar da kaina ba?”.
Na gyada kai ina dariya kamar wata sakara, “gaskiya kam, da ka kira tun da wuri”.
Yace “yadda zan katse miki barci? Yanzu ma naji kamar daga barci kika tashi, sorry, na katse miki barci. Na kasa daurewa ne wallahi. Ina fata banyi laifin komi ba?”.
Na girgiza kai kamar yana kallona, “ko kadan baka yi laifi ba, zan ma iya cewa kayi daidai!”.
Ina jin ajiyar zuciyar daya sauke, “good. Don ba zan so ace daga wayar farko ba na fara yin laifi ba gaskiya”. Duk muka yi dariya.
Daga nan duk muka yi shiru, baka jin sautin komi sai karar dake fita daga cikin wayar kawai. Zuwa can yayi gyaran murya, yace “to Malama Na’ilah, kamar yadda nasan cewa kin san dalilin da yasa na tunkareki tun farko har ya kawo ga wayar da muke yi yanzu, magana ce ta so. Wadda nake so, kuma nake fatan idan Allah ya yarda ya amince, zata kaimu ga aure na sunnah. Magana ta gaskiya ban fito da wasa ba, kuma nayi niyar dana bayyana a gareki, muka samu fahimtar juna ni da ke, ba zanyi sanya ba zan fara zancen aurenmu, in samu in killace ki a dakina kafin kwado ya min kafa, me kika ce?”.
Daga jin sautin muryarshi da yadda yake fitar da haruffa daya bayan daya, kasan cewa kaji mutum wanda yasan ciwon kanshi, wanda yasan me yake yi, ya kuma san yadda duniya take ci. Naji ya kara shiga raina. Nan nayi mishi bayanin cewa yanzu dai karatu nake yi, sannan kuma akwai wanda muke tare dashi a halin yanzu dai, ban boye mishi komi ba, na fada mishi komi da komi. Shi kuma ya burgeni daya saurareni tunda na fara magana har na gama bai katse ni ba. Hakan ya kara min wata martabar shi a cikin idanuna.
Sai dana gama, ya nisa yace “naji dadi kwarai da baki boye min komi ba game dake, sannan maganar karatu a wajena ba matsala bace, koda ace baki fara ba, zan iya daukar nauyinki har ki gama, balle kuma duka-duka Allah na tuba menene ya rage a cikin karatun naku yanzu? Sauran kadan ne. Zancen wanda kuke tare kuma, wannan ai lokaci ne zai nuna mana ko ke din ta wacece. Illa iyaka, mutum ya zage damtse, ya shiga filin dagar neman ki sai aga wanda yake da nasara!”.
Nayi dariya sosai da maganganunshi, da alamu Allah ya hore mishi iya sarrafa maganganu matuka. Shima ya biye min muka yi ta kyakyatawa kamar wasu kananun yara. Sai dana nutsa sannan nace mishi, “to Allah dai yayi mana zabin mafi alkhairi”.
Ina dire aya ya cafe da; “in shaa Allahu ma kece alkhairin”, ko yawu bai bari na gama hadiyawa ba.
Nace “to Allah ya yarda”.
Yace “ameen… Tunda yanzu mun yi wannan magana, ina fata mun fahimci juna ni dake? Kina da wata tambaya da kike son yi game dani?”.
Nace “na fahimci komi, tambaya kuma bana tunanin a yanzu akwai ta, amma idan ina da ita nan gaba, zan yi maka”.
Yace “zaki iya yi a koda yaushe, tunda yanzu na ji muryarki, ina tabbatar miki da cewa sai kin gaji da ganin kira na a wayarki, don zan so ace kullum cikin sauararen muryarki nake!”.
A zuci so nayi in ce, “ai nima hakan take”, amma a fili sai nayi dan murmushi kawai.
Yace “yanzu dai bari in barki ki karya, nasan baki karya ba kika fara waya da ni. Bayan kin gama cin abincin zan kira ki mu dora daga inda muka tsaya, ki huta lafiya Baby na!”. Daga haka ya tafi.
Na bi wayar da kallo kamar shine a gabana, ina nanata kalmar ‘baby na!’ a cikin kaina kamar wata bakuwar kalma da ban taba jin kamarta ba sai yanzu. Gabadaya sai naji cikina ya cika, bana marmarin komi. Don haka na koma kan katifa na kwanta ina kara maimaita hirarmu da Malam Muhammad M.B a cikin zuciyata kamar wani shirin film da yake matukar kayatar dani, ina zabga murmushi kamar wadda ta fara zarewa.
Amma dan saurara, wani hanzari ba gudu ba., me yasa muryarshi take min kama da wani wanda na sani? Ban tabbatar ko waye ba, amma naji kamar na taba jin muryar nan, inda na taba ji dinne na kasa tunawa.
Ban san iya lokacin dana dauka a cikin wannan hali ba na tsananin bege, sai dana ji an daka min duka a cinya. Nayi firgigit! Na mike zaune ina sosa wajen. Esther dake gefen katifata a zaune dangargar ta kalleni tana murmushi, “Babe, tunanin meye kike yi ne haka? Hala oganki ne?. Ta fada cikin harshen turanci kamar yadda ta saba magana dashi.
Nace mata “nothing o…”.
Tace “na lie… Kada kiyi tunanin ban ga yadda kike ta murmushi ba kina dariya lokacin dana zo fita”. Na zaro ido ina kallonta, da gaske har fita tayi ta dawo ban sani ba?.
Ta kyalkyale da dariya ta dauki wata bakar leda da ban kula da ita ba, ta miko min, “dama kina ta soyewa ta ina zaki ji motsin mutane bayan kinyi nisa a duniyar da daga ke sai shi? Na tabbata za’a iya ciccibarki a lokacin baki ma sani ba!”.
Harara kawai na jefa mata cikin murmushi. Na daga ledar, kamshin masa ne ya fara bugo ni tun ma kafin in ga masar. Sai a lokacin na tuna da cewa jiya da dare kafin mu kwanta na fada mata idan zata je siyan masar yau da safe ta tashe ni koda ina barci ne, don marmarin cin ta nake yi sosai.
Nayi murmushi ina kallonta, “nagode kwarai Esther, ta nawa ce kika sayo?”.
Tace “ban san ko ta nawa kike bukata ba, sai na sayo ta dari biyu”.
Nace “tayi, nagode fa”.
Tace “babu damuwa!”.
Tashi nayi na dauki purse dita na bude na bata kudinta, na kara mata godiya, sannan na sauka kasa naje nayi brush na koma dakin. Bowl na dauka karama ta plastic na juye miyar da aka daure a cikin leda, na fara cin masar.
Ina cikin ci ne na dauki waya na kira Janan, finally, abinda muke ta jira, mysterious dina dai ya kira waya. Nan muka sha ihun murnarmu da maida yadda aka yi. Wani labarin ma ai sai ta shigo ranar Monday sannan za ayi shi baki da baki.
Yinin ranar wannan gabadayanshi, Allah ne kadai yasan farincikin dana yini dashi, wata irin far’ah dana rasa dalilinta, nishadi dana rasa dalilinshi. God, I’m so whipped, totally!!.
Yini aka yi ana ruwa duk da ba mai karfi bane, amma yanzu da nake kudundune cikin bargo a dakina da dare, sanyin da ruwan saman ya haddasa da kuma kamshin ruwa da jikakkiyar kasa da yake tashi, da kuma tsananin taushin muryar Mysterious dake ratsawa ta cikin dodon kunnena a daidai wannan lokacin, sai naji babu wata damuwa a raina. Babu kowa, kuma babu komi a wannan lokacin sai ni sai shi kawai. And nothing matters!.
Tuni mun riga mun sabarwa junanmu jin muryar junanmu a kowace rana. Muryar dayanmu zamu tashi da ita, texts zasu mana rakiya duk inda zamu je a yinin ranar, haka kuma zamu ji muryar juna kafin mu kwanta da dare.
Da asuba tun ma kafin alarm dina ya buga, Muhammad zai kira ni ta waya, nan kira kawai zai yi in tashi, to idan na gama ne zamu yi wayar minti biyar zuwa goma, sai muyi sallama. In shiga wanka in shirya, in karya, in fita. Kafin in karasa ward ya turo min text mai cike da kalamai dadada da zasu sa in yini ina kallon wayata cikin murmushi, ina kara karanta shi over and over, sai in tura mishi amsa. Kafin yamma ta fadi at least zamu yi musayar messages sau uku ko fi, sannan da dare dole ne sai ya kira ni kafin in kwanta barci, watarana ma muna cikin hirar barci zai daukeni sai dai ya kashe wayar in yaji shiru.
Ni kaina nasan cewa na canza, kamar wani abu yayi snapping a jikina ne. Duk wasu makamai da katangu dana sa a jikina, daya bayan daya Muhammad ya bisu ya sassare, kamar basu taba wanzuwa ba.
Wani abu ne da bai taba faruwa dani a tarihin rayuwata, da shekaruna dai-daya har ashirin da hudu a duniya ba. Ban kuma taba zaton zai farun ba. Amma yanzu daya faru, sai nake jin ina zargi da tuhumar kaina, me yasa tun farko ban bar kaina nima naji dadin wannan abu ba? Na dinga takura kaina, ina matsawa kaina? Kodayake, komi yana da lokaci, kuma kamar yadda Janan take yawan cewa, _’idan lokacin ki kamu da so yayi, baki da yadda zaki yi, kina so ko ba kya so, zaki fada tarkon ko, kin sani ko baki sani ba!’._
To yanzun ma ina tunanin abinda ya faru kenan, lokaci na ne yayi. Na kamu da soyayya, soyayyar Muhammad mai zurfi. Zurfin da ya kai naji ina so inyi kugi da karaji, wanda duk duniya da mutanen cikinta zasu ji cewa ina cikin zazzafar kaunar mutumin da ban taba sakawa a cikin idanuna ba!.
* * *
“Kyawunta ace wannan azumi da zai zo, wani mutumin kirkin zai zo ya dauki dubu ko hamsin ce ya baka, ya hada ka da buhun masara, gero, sukari ko rabin buhu ne! Kai ai da kakar ka ta yanke sa’a!! Sai ka nemi inuwa mai ni’ima kawai ka fuske, ka yini tun safe har dare a kwance Malam, babu ruwanka!!”.
Wani kwandastan mota da muka hayo daga asibitin Shika zuwa kasuwar Samaru yake cewa. Duk cikin motar aka saka dariya.
Wani mutum daga baya yace “wannan duk mafarki ne kake yi, wanda baya zama gaskiya. Abu mai yawa da zaka samu daga hannun manyan nan shine kwanon masara ko gero, ba’a hada maka guda biyu ma. Sai ka samu wani mai tsoron Allah shine zai kawo wata lalatacciyar dari biyu ya dora maka yace kayi nika. Ai yanzu wannan alherin a tsakanin masu kudi kawai ake yi, ka dauka ka kai gidan mai kudi, shima idan ya tashi yin nashi sai ya maido maka. Su kuma talakawa sai suje su nemo da karfinsu”.
Wani ya cafe zancen, “ai sai dai kawai Allah ya kara rufa mana asiri. Wata irin rayuwa ake yi ta danniya da rashin tsoron Allah, mai shi ya dannewa mara shi, masu kudin namu kuma basa taimakon talakawanmu. Kowa kanshi ya sani ba wani abu ba, Allah dai yasa mu dace!”. Duk muka amsa da ameen.
Har motar ta tsaya a bakin kasuwar, da yawanmu muka fita daga ciki, wasu suna ta tururuwar shiga, da alamu ranar da ake zabgawa yau ta gama dakar su.
Ni da Janan muka tsallaka titi muka shiga kasuwar. Kasancewar Azumi yana ta gabatowa, ana tunanin nan da kwanaki biyar masu zuwa ma za’a tashi dashi. Shi yasa nace bari in shiga kasuwa in dan yi sayayya da sauran kudin da nake dasu kafin in cinye su.
Mun shiga mun danyi saye-sayen mu, muka fito hannu riki-riki da kaya. A bakin titi muka tsaya, Jan zata tsallaka ta hau bus zuwa PZ ni kuma in matsa gaba in hau wadda zata maida ni asibiti. Kallon motoci, masu mashina, kekuna da ma masu tafiya akan kafafu da keken guragu nake yi suna ta karakaina, kowa harkar dake gabanshi ce ta dame shi.
Janan ta fara daddabata da sauri, nayi saurin juyawa na kalleta, wata mota da take wucewa ta gabanmu wadda dan banzan go-slow din da ake yi ya saketa, nace “lafiya?”.
Tace “waccan motar bata miki kama data Umar ba?”.
Na kara bin motar da kallo wadda zuwa yanzu ta bace min, yanzu da tayi maganar sai naga irin tashi ce, amma kuma garin Zaria mai fadi, ba lallai ace shi kadai yake da irin wannan motar ba. Ko yanzu da zamu baro asibiti naga wata nurse ta fita a cikin irin motar tashi, wadda har kala bata banbanta su ba. Balle kuma wannan motar dana hango kamar mata da miji ne a ciki? Sannan bugu da kari, Umar yana Kaduna ba Zaria ba.
Dana juyewa Janan wannan bayanai, sai ta gyada kai, tace “haka ne, mantawa nayi”. Muka samu ababen hawan suka ragu a lokacin, ta tsallaka da sauri tana min bye-bye, sannan ne nima na juya na shiga bus.
⋆
⋆
Ranar Juma’ah da wuri na fita zuwa cikin asibiti, kasancewar da wuri na tashi. Ranar tun daga cikin hostel muka fara waya da Muhammad har na shiga cikin ward, sannan muka yi sallama dashi akan cewa zai kira ni kafin ya tafi masallaci.
Har karfe goma na safe babu Janan babu alamunta, hankalina yana bakin kofa, da naji alamun za’a shigo sai inyi sauri in kalli kofar cikin tsammanin itace, sai in ga wani daban. Ganin karfe goma tana shirin wucewa yasa na lalubo wayata daga cikin aljihun wandon uniform dina na kirata cikin faduwar gaba. Hakan bai taba faruwa da Janan ba. Duk son makararta, Janan bata yin fashi, don haka ne naji na damu.
Wayarta tayi ta kara tana katsewa, a karo na kusan uku ne ta daga. Da sauri na fara jero mata tambayoyi, “wai ya ne har yanzu baki zo bane? Baki tashi da wuri bane ko kuma yau kinyi shawarar kin zuwa ne?!”..
Daga farko shiru aka yi, kafin daga baya inji muryar da ba ta Janan ba tace “uhmm, Janan din bata ji dadi bane”.
Naji gabana ya fadi, nayi salati na sanar da Ubangiji, nace “lafiya, me ya sameta? Waye kuma?”.
Mai maganar yace “Asthma dinta ne ta tashi, sannan Bilal ne”. Na kalli wayar cike da mamaki, kwata-kwata muryar bata yi kama da tashi ba, a takaice ma dai muryar bata yi kama data mace ba balle namiji. Amma sai nafi kyautata hakan a matsayin sharrin network kawai.
Nace “Subhanallah! Kuna gida ne?”.
Yace “a’ah, muna asibitin Delicate dake bayan gidanmu, kin san shi?”.
Nace “ehh, gani nan zuwa”. Na kashe wayar da sauri na maida ta aljihu.
Kayana na dauka a gaggauce, na tunkari office din matron din ward din. Na kwankwasa ta min izinin shiga. A gaggauce na mata bayanin abinda ake ciki, nan tace in tafi kawai babu komi, har ma ta kara da ‘ki dubata. Sai ranar Monday idan jikin nata ya warware’, na mata godiya na fita a sukwane kamar wadda zata tashi sama.
Wata irin wahalalliyar asthma gareta, bata cika tashi ba, amma duk ranar data tashi sai ta jikatar da ita. Shi yasa naji hankalina ya kasa kwanciya, ko tunanin komawa hostel in canza kayan jikina banyi ba. Allah ya taimaka na samu abin hawa da sauri kasancewar ranar Juma’ah ce, kowa yana kokarin ya je inda zai je kafin lokacin masallaci yayi.
~Phewwwwww!!!!!
#F.W.A
*☆⋆14⋆☆*
Halin dana sameta a ciki ya sanyayar min da jiki, gabadayanta ta fita daga hayyacinta don ma sun ce wai a hakan ma tayi dama. Yayan da Anty Sarah kadai na tarar a asibitin, a cewarsu wai Raheemah bata jima da barin asibitin ba. Na zauna a gefen gadon tare da shafa gefen fuskarta cike da tausayi, har ta dan fada, gashi yanayin numfashinta bai gama daidaituwa ba har yanzu.
Muna zaune a hakan har rana tayi, Yaya yake ta shiga da fita daga ofishin likita zuwa inda aka kwantar da ita din. An samu tayi barci, bayan anyi mata allura har aka samu numfashinta ya daidaita.
Da lokacin tafiya masallaci yayi, Yaya ya tafi akan cewa zai turo Raheemah tazo ta zauna damu, sai dai har aka fito daga masallacin, har muma muka yi tamu sallar bamu ga alamunta.
Lokacin daya dawo ina kan sallaya a zaune, Anty Sarah kuma tana zaune akan farar kujera tana jan carbi, ya ajiye ledar take away a gefen gadon, yace “ga abinci kuci, likitan yace zamu iya tafiya gida da ita idan ta tashi”.
Anty Sarah tace ta koshi, nima nace na koshi da yake cikina a cike yake.
Karan text daya shigo wayata ne yasa na maida hankalina ga wayar, na duba naga daga Muhammad ne. “Hey baby!”, abinda ya turo kenan. Na kara maimaita text din cikin mamakin kalmomin, motsin da Jan ta fara yi ne yasa na wancakalar da wayar gefe na nufeta da sauri. Yaya ya taimaka mata ta zauna akan gadon, gabadayanmu sannu muke jera mata tana amsawa a hankali.
Yaya ya dauko madarar ruwa ya fasa tare da mika mata, ta amsa ta sha kamar rabi ta maida mishi sauran, yace “har kin koshi?”, ta gyada mishi kai.
Anty Sarah tace “dama ba lallai ta iya cin abinci yanzu ba”.
Yaya ya umarcemu da mu hada kan kayanmu, ya miko gyalen Janan na yafa mata. Da taimakona ta sauko daga kan gadon, ina tallabe da ita a jikina muka fita daga asibitin zuwa wajen da Yaya yayi parking din motarshi. Ya bude mana gidan baya duk muka shige ciki. Bayan ya gama clearing din komi a asibitin, yazo ya shiga motar ya tayar muka tafi.
Yaya Bilal ya kashe motar a ainihin inda suke ajiye motocinsu, farko-farkon shiga gidan, daga nan tafiya ce zaka yi kadan daga bangaren damar ka da zata sadaka da wani zagayayyen karamin garden, grass carpet ne shimfide a wajen, wajen yana da fadi sai kuma bishiyoyin mangwaro, gwaiba, gwanda, ayaba, da sauran kayan marmari dai. Daga gefen garden dinne aka shimfida doguwar hanya da interlocks, kanana masu kyau, itace zata sadaka zuwa bangaren Yaya Bilal. Wadda kuma tayi barin hagu itace zata sada ka da bangaren su Anty Sarah.
Kan Janan yana kan kafadata, wani barcin ne yake kokarin daukarta. A hankali na tasheta, muka fito daga motar. Anty Sarah ta mana fatan Allah sauwake, ta wuce sashenta muna mata godiya. Rabin jikin Janan yana jikina, na tallabota muka wuce saboda har yanzu jikinta babu karfi sosai. Yaya Bilal yana binmu a baya hannu rike da makullin motarshi da kuma ledar take away din da yayi.
Gabadaya mutanen gidan suna falo, wannan karon a zaune suke kawai suna hira sabanin kallo da suka saba yi a yawancin lokuta. Raheemah ce ta fara ankara da shigarmu falon, ta mike tana zuba sannu da zuwa cikin alamun borin kunya, kannenta suma suka mike, “ah.., har kun dawo ashe? Yanzu muke cewa mu tashi mu koma fa! Sannunku, ya jikin?”.
Muka amsa musu ciki-ciki, Yaya ya umarce ni da in taimaka mata Janan zuwa dakinta, don haka na gewaye su muka wuce zuwa dakinta. Bansan Yayan yana bayanmu ba sai dana ji karan sake bude kofa bayan na maida na rufe.
Na kwantar da ita akan katifarta, na ja abin rufa na rufa mata daga kafafunta zuwa rabin jikinta, tuni barci yayi awon gaba da ita. Yaya ya miko min ledar hannunshi, yace “ki samu ki zauna kici abinci haka nan, ki zauna ki huta kema”.
Na karbi ledar, kaina a kasa, wata irin kunyarshi naji ta lullube ni wanda na rasa dalilin hakan. Nace “to, nagode, Allah ya amfana”.
Ya girgiza kai a hankali, wani irin kallo a cikin kwayar idanuwanshi da suka sanya naji jikina ya dauki wata irin kyarma, ikon Allah! Ko dai bani da lafiya ne nima?! Yace “ni ne da godiya Na’ilah! You’ve no idea how grateful I am right now!”.
Subhanallah!! Me ke shirin faruwa da ni ne? Jin fitar sunana daga bakinshi ya haifar min da jin wani irin abu a cikin raina, shin ko mai yasa hakan? Hakan bai taba faruwa dani ba! Sannan muryar Yaya Bilal, yau naji tana min kama da wata murya hallau, matsalar na kasa tunawa ko a ina ne na ji muryar.
Ban san lokacin daya juya ya bar dakin ba, sai karar rufe kofa naji.
Na bude ledar na fito da take away din ciki, guda biyu ne da lemukan fanta suma guda biyu, don haka na dauki daya na ajiye, dayan kuma na barsu a cikin ledar na fita domin in mikawa Anty Sarah nata.
A falo Yaya Bilal ne a tsaye kikam, kamar wani tsohon soja. Su kuma suna lafe akan kujeru kamar wadanda aka kama sun nannagawa sarki garinsu karya. Daga yanayin fuskar shi da take a cune da yadda bakinshi yake kumfa, zaka san cewa fada yake musu, fada kuma bana wasa ba. Tunda nake dashi ban taba ganin fadan shi ba sai yau. Janan tana yawan cewa Yaya Bilal yana da fada, duk da cewa baka sanin fadanshi sai ka mugun tabo shi sannan, to da alamun yau dai an tabo shi.
Ni dai na kada kai na fita. Yau kofar gidan na Anty Sarah a bude take, abin mamaki, na tura kofar na shiga. Tana kicin. Yanayin gidanta da ka shiga kicin zaka fara tararwa, sai falo da kuma bedrooms. Ta dago ta kalleni lokacin dana shiga, nace “kofar a bude take, shi yasa na shigo kai tsaye”.
Tace “babu komi, ina tsammanin Mimah ne yanzu shi yasa, ya aka yi?”.
Na mika mata ledar hannuna, “dama abincin da Yaya ya kai ne na kawo miki”.
Murmushi naga tayi wanda ya bani mamaki, tace “da kin barshi wallahi kun ci, kin ga abinci ma nake shirin dorawa yanzu”.
Nace “a’ah wallahi, ai guda biyu ne ya kawo”.
Tace “to shikenan, na gode. Ya Janan din?”. Nace “ta koma barci”, daga haka na juya na fita daga gidan.
Har na koma can, Yaya fada yake yi, “… In fada muku gaskiya ba zan dauki wannan cin mutuncin ba! An fada muku ita yar aiki ce? Ko kuma bata san ciwon kanta ba? Waye bai san tana da asthma ba, da zaku barta tayi aikin da zai tado mata shi?!”. Ya dire maganar yana sauke numfashi cikin bacin rai.
Raheemah ce ta samu ta iya magana duk cikinsu, “kayi hakuri, hakan ba zata kara faruwa ba. Ita ce tace zata yi ai…”.
Tun ma kafin ta karasa ya katseta, “ke kuma saboda rashin hankali sai kuka barta ko? Na fa san abinnan ba tun yau yake faruwa ba, ina sane, iyaka gudun ruwanku ne kawai nake so in gani. Wallahi Tallahi, kunji rantsuwar da nayi, ba zan yi kaffara ba! Idan makamancin haka ya sake faruwa, gabadayanku sai kun bar min gidana. Kuma daga yau, duk wadda take son yin girki, ta shiga ta girka abinda zata ci ban yi mata iyaka da komi na gidannan ba, amma kun gama cin abincin Janan. Ba zata kara muku girki ba, haka ko tsinke ta tsince a gidannan da sunan shara ko gyara Allah zamanku a gidan nan ya kare! Kun dai ji na fada muku!!”. Ya wuce dakinshi fuuuu! Kamar kububuwa tare da maida kofar dakin ya gamtso kamar tashin duniya. Mu kuwa duk muka bi bayanshi da kallo baki a dage.
Maimakon hakan ya dan zame musu darasi, su dan saduda koda na dan lokaci ne, inaa. Tunzura su ma yayi.
Adi ce ta fara jan tsaki, “mtswww, aikin banza! Yo mun taba matseta muka ce dole sai ta mana girki ko aiki? Kashi zamu bata idan bata mana aikin bane? Har da za’a zauna ana zagin mutane akan wata banzar bazara, gidan banza dana wofi! An fada musu mu bamu da gidan iyaye ne da za’a zo ana zaginmu ana mana gori?”.
Salama ta cafe maganar, “ke ma dai kya fada. Aikin banza dana wofi, da dai ace bamu da gidan uba ne da sai muji haushi, to mun gode Allah muna da gidan uba, kuma ba a inda ba’a son zamanmu muke zaune ba! An fada mishi mu mabaratan abinci ne??”.
Raheemah kuma tana ta kokarin sanya su suyi shiru a dan tsorace, “don Allah kuyi shiru mana!”, ko kuma tace “don Allah kuyi a hankali kada ya jiyo ku ya sake fitowa!”. Na girgiza kai kawai, wato shi dai mai rai ba’a taba iya mishi. Allah ya kyauta.
Na barsu anan na koma daki. Har yanzu Janan barci take yi. Na duba cikin kayanta na ciro doguwar rigar leshi mara nauyi, na dauki kayan na shiga bandaki na sanya na fito, na sake zama a gabanta.
Har bayan sallar la’asar bata tashi ba, bayan nayi sallah na zauna naci abincin da Yaya ya kawo mana, na maida sauran na rufe dana koshi. Ina nan a zaune naji karan buga kofa, na tashi na bude. Ga mamakina Anty Sarah ce a tsaye da kwando a hannunta, na mata sannu tare da bata hanya ta shiga cikin dakin. Tace “har yanzu bata tashi ba?”.
Nace “wallahi har yanzu, kila an hada mata da allurar barci ne”. Ta gyada kai idanunta akan Janan din, “Allah ya bata lafiya”. Nace “ameen”.
Ta min nuni da kwandon data ajiye, tace “ga wannan idan ta tashi sai taci, ba yawa”.
Nace “Allah ya saka da alkhairi”. Ta amsa tare da tashi ta fita, na bi bayanta na maida kofar dakin zan rufe. Su Raheemah suna falon a zaune har yanzu, ta wuce ta gabansu. Ina tunanin basu cika shiri dasu ba, kila ma hakan ce ta goge mu, ko kuwa wani abu daban? Naga kwana biyu kamar ta dan sassauto.
Sai wajen karfe biyar sannan ta farka, jikinta ya dan yi karfi ba kamar dazu ba. Na taimaka mata zuwa bandaki tayi wanka da ruwa mai dumi. Bayan ta fito na zuba mata abinda Anty Sarah ta kawo, wani irin abu ne tayi da kifi ban ma san sunanshi ba, kamar ta soya kifin, kamar kuma dahuwar ruwa ce, ga veggies da abin yasha sai tashin kamshi yake yi kuwa. Na zuba mata ta samu ta dan ci, tayi sallar azuhur da la’asar da aka yi tana barci. Na ballo magungunanta da aka rubuto mata ta sha, ta zauna a gefen katifa ta dauki wayarta da tun dazu sai gajiya nayi na sakata a silent saboda yadda ake kira.
Ummah ta fara kira, taje umara kamar shekaranjiya naji Janan tace ta tafi. Bayan sun gaisa ta tabbatar mata da lafiyarta lau yanzu, ta miko min wayar muka gaisa da ita. Bayan munyi sallama ne ta amshi wayar ta kira Ya Almu. Ni kuma na dauki wayata ina game.
Bayan sallar magriba Yaya Bilal ya sake shigo mana da abinci, chips ne da sauce da gasasshiyar kaza, nan ma sake zama yayi ya zuba mata dogon sharhi akan aikin gida, ya fada ya kara maimaitawa, daga wannan rana kada ta kuskura ta sake cewa zata yi kowani irin aiki ne in dai na gidan ne.
Ashe wai gyaran gida ne suke yi saboda matsowar azumi, wanda ake tsammanin ranar litinin ko talata za’a tashi dashi. Ita ta fara dauko maganar ayi aikin tun daga farko ranar Alhamis bayan ta koma gida, shine sun shiga can cikin gidan, wani daki da suka maida dakin tarkace kawai, zasu gyara shi da niyar da azumi za’a dinga taruwa acan ana sallar tarawihi, suna fara aikin suka fara zamewa daya bayan daya har suka barta, wannan kura data shaka ita ce fa ta tado mata asthma. Allah ne ya taimaka da asubahin washegarin yau, Yaya Bilal daya dawo jiya da dare, ya leka dakin kasancewar bai samu ya ganta ba daya dawo, shine fa ya sameta a cikin mawuyacin hali. Da Allah kadai yasan abinda zai faru.
Bayan mun ci kaza da chips munyi nak, kwanciya muka yi tun wajen karfe taran dare don ba karamar gajiya muka yi ba daga ni har ita.
Ta kalleni lokacin da nake ta faman buga keyboard din wayata ina turawa Muhammad sako, tun wayar da muka yi da safe bamu yi wata ba har yanzu, haka tun text din daya tura min lokacin da muna asibiti bai sake tura wani ba, nima ban sake tura mishi ba saboda ban samu kaina ba sai yanzu. Bayan na tura mishi ne, idanuna suka sauka akan conversation dina da muka sha yi da Umar, rabon da in ga text dinshi a wayata kusan sati biyu kenan, haka ma kira. Tun ni ina yi da tura text, har na gaji na hakura kawai na koma gefe ina jiran ya sake waiwayata.
Janan ta dafa goshina, tace “ke ma fa kamar baki da lafiya, jikinki zafi sosai”.
Na kai bayan hannu na ina dafa wuyana, “lafiya ta lau Jan, ina tunanin yanayin nan ne, ko kuma mura. Kin san yadda murata take”.
Muna hira kadan-kadan da ita dai har barci ya kwashe mu.
*
Washegari ma haka Anty Sarah ta kawo wa Janan abin kari, bayan fitarta muka koma gefe ni da Janan muna gulmar kirkin da tayi kwanannan.
“Allah da gaske dama can tana da kirkinta, kafin zuwan Anty Raheemah kenan. Tana zuwa kwata-kwata sai ta hau kulle kanta a gidanta, ina tunanin jinin su ne bai zo daya ba”. Cewar Janan tana shan romon naman kan sa data kai mana.
Ni kam na kasa cin komi, sai sandwich daya na samu naci wanda tayi filling da sauce din kwai da sardines na gwangwani, ga cucumber a ciki, shima rabi, sai shayin dana hado mana da nake ta kurba. Tashi nayi bakina salam babu dadi, ga wani shafal da nake jina kamar babu laka a jikina ko kuma idan aka hure ni zan fadi, gefen kaina bugawa yake yi tun karfinshi idan nayi dan motsi, jiya da zazzabi na kwana a jikina, ga wani jiri da nake ji idan na tashi, daurewa kawai nake yi muna hira da Janan, amma Allah kadai yasan yadda kaina yake sarawa. Ita kam jikinta da kwari tubarkallah, kamar ba ita bace tasha jinyar nan jiya ba. Da safe su Raheemah sun leko sun mata sannu da jiki suka kara gaba. Kamar ma unguwa muka fita, don mu kadai muka yini a gidan, sai bayan isha’i suka dawo.
Janan ce ta takura akan sai mun fita bakin titi mun sayo tangerine da mango.
Nace “wai ke ma ga Ahmad nan, ki tura shi mana?”.
Tace “ke zaki fita kiyi gadin gidan ko? Yadda Yaya zai dawo ya tadda baya nan ya tsige ni da raina ko?”.
Nace “to yanzu kina tunanin idan ya dawo yaga bamu nan, ba zai tsige ki da ran naki ba dai?”.
Tayi dariya, “sis, ki taso kawai mu fita, babu abinda zai faru. Ni fa bana jin dadin jikina wallahi, ai nayi kokari, kusan awanni na arba’in da takwas fa ba tare dana taka waje ba!”.
Na jefa mata harara, “da can kuma da kike fin sati ma ba tare da kin fita ba fa?”.
Tace “wannan ai ya banbanta, don Allah taso mu tafi kada mu bata lokaci har Yaya ya dawo”.
Duk da ban so ba, haka nan na tashi na bi bayanta muka fita. Har yanzu ina jin jikina ba daidai ba, duk da dai tunda nasha paracetamol da yammar nan, zazzabin ya sauka, amma har yanzu ina jin jirin kadan-kadan da kuma ciwon kai.
Can bakin titi muka fita, muka yi siyo duk abubuwan da idanunmu suka dora ido a kansu. Niki-niki haka muka juya gida hannuwa cike da ledoji. A hankali muke tafe akan titin, yanayin unguwarsu kamar G.R.A haka take, da rana ma baka cika ganin mutane suna shawagi ba balle da dare. Yanzu ma sai jifa-jifa muke ganin mutane, sai kuwa ababen hawa da suke ta wucewa. Wasu na fita wasu na shiga.
Gab da zamu shiga gidan naji nayi turus, sakamakon wata mota dana hango can gaba kadan da gidan. Idan da ba don wata sticker dake bayan motar ba, an rubuta ‘born to fight’, da cewa zanyi ba ita bace. Sai dai wannan babu tantama motar Umar ce, amma me zai kawo shi nan yanzu? Janan tana tambayata lafiya? Amma hankalina baya wajenta, wayata nake kokarin cirowa. A tunanina kila ya kira ni ban ji kiran ba, yanzu haka ma kila ni yake jira ko wani abu. Amma babu kiran Umar a wayata babu alamunshi.
Na kalli Janan ina nuna mata motar, da yake akwai hasken da kwayayen dake kofar gidajen unguwar suke badawa, take ta gane motar, tace “kai! Kamar motar Umar dinki fa!”.
Babu ko tantama nace “motar shi ce, amma me yake yi anan? Ko kirana fa bai yi ba!”.
Tace “ko dai bashi bane?”. Da sauri na hau girgiza mata kai, gabadaya na rasa akan abinda ya kamata inyi tunani a lokacin. Haka kawai naji jikina ya dauki wata irin rawa, ba kuma zazzabin da nake ji bane ya haddasa ta ba.
Ba tare da tunanin komi ba, naji na fara daga kafa ta zuwa wajen motar. Duk taku daya, rawar jikina karuwa take yi, haka bugun zuciyata yake ninkuwa.
Ban san tunanin me nake yi ba dana tunkari motar gadan gadan ba, amma ban shiryawa ganin abinda idanu na suka gane min ba. Ban shirya ba!.
Umar ne kamar yadda nayi zato, zaune a gaban motar, sai dai ba shi kadai bane kamar yadda nayi zato. Tare suke da ba wata ba illa Haleemo. A zaunen ma zama na rashin da’a, saboda kusancinsu kamar a kan cinyarshi take zaune saboda irin zaman da suka yi. Ba wannan kadai ba, daidai lokacin da wata mota ta danno cikin layin a sukwane, haskenta ya dallare gaban motar, daidai lokacin da bakinsu ya hade da kiss. Hannuwanshi na yawo a wuyanta da bayanta.
Naji kamar an katse duk wata magudanar jini a jikina, ban san lokacin da kayan hannuna suka zube ba. Innalillahi, me idanuna suke gani ne haka??! Da sauri na kauda kaina don bazan iya kallon irin wannan badala dake afkuwa a gabana ba.
Tunanin farko daya dirar min, shine in kwashe kayana da suka zube a kasa in wuce gida, tunda dai sam basu san da kalar wainar da muke soyawa ba, sai kuma naga inaa! Don haka kafin ma in sake tunanin yin wani abu, naji kafafuna sun daukeni zuwa wajen motar. Na tsaya a daidai wajen da direba yake zama na bubbuga.
Sai da aka dauki lokaci kafin aka yi kasa da tinted glass din da aka saka aka rufe motar, Umar ya zuro kanshi waje. Yadda idanunshi suka waro cikin gigita yasa naji wata irin tsanar shi ta cika min rai, me yasa zai yi min haka??
Da sauri ya fito daga cikin motar yana wani kame-kame, “hh-hheyyy… Sweetie. M-me kike yi… anan?!”, ya tambaya cikin rawar murya.
Na daure, na cije, na tattaro duk wani kwarin gwiwa daya rage min, nace “oh, wai zamu wuce ne sai naga kamar motarka, nace bari in tabbatar. Ashe kai dinne. Mai kake yi anan? Nayi tunanin kana Kaduna??”.
Ya fara shafa bayan wuyanshi yana wuri-wuri da ido, “wannan? Ai dazu na dawo, tunda na tafi ban dawo ba sai yau! Ai ayyuka ne suka yi yawa! Kusan satina daya ban daga wayata ba saboda aiki!! Yanzu…. Yanzu ma wani abokina ne anan unguwar nazo gani, ai ban ma gane layin gidan su kawarki bane saboda duhu. Me ma kike yi anan unguwar? Nayi zaton kina Shika??!”.
Ji nayi na gama sauraren kame-kamen da yake yi, rainin wayon yayi yawa. Banyi wata-wata ba na daga hannu na watsa mishi tafi…
#F.W.A
*☆⋆15⋆☆*
Ba shi kadai ba, ni kaina nayi mamakin marin dana mishi, amma banyi nadamar hakan ba.
Ya dafe kuncinshi yana kallona cikin zare ido, “sweetie….!”.
Cikin tsananin tsiwa da balbalin masifa nace “idan ka sake kirana da wannan sunan, Allah ya isa ban yafe maka ba Umar!!”.
Yayi sararo a tsaye da baki a bude, ya rasa abin cewa. Nace “dama abinda kake yi kenan? Nayi tunanin cewa abubuwan da kake nuna min kawai kana yi ne saboda desperation, ashe halinka ne?”. Munafikin sai yayi shiru kai a kasa yana muzurai. Daidai lokacin Haleemo ta fito daga cikin motar, kai a kasa babu kunya babu tsoron Allah tana nukutu.
Na kalleta, wani tsabar takaici yana cina, ji nike kamar in kamata in hadata da bango ko motar, amma na cije don nasan shaidan ne yake so ya zuga ni. Na nunata da yatsa, “akan wannan abin ne ka yaudare ni? Akan wannan abin ka share ni tsawon watanni, ina bibiyarka kana yazga ni kamar wata mara aikin yi? Ba ni kuka cuta ba wallahi, kan ku kuka zalunta. Kuma ni babu abinda zan ce muku, babu kuma mummunar addu’ar da zanyi muku. Sai dai ku sani, za ku gani da idanunku, Allah ya kara muku dankon kauna!”. Daga haka na juya da sauri na wuce, babu wanda ya iya cewa uffan a cikinsu. Janan data tsaya ta tsince kayan da suka zube, ta biyo bayana da sauri, jerawa muka yi muna tafiya ba tare da dayanmu ya cewa daya ci kanki ba.
Muna shiga daki naji jikina ya dauki wata irin rawa, ba shiri na lalubi kujera na zauna. Na kai hannuwana duka biyu na dafe kaina ina girgizawa, dama abinda yake faruwa kenan, ni ina gefe guda na hangame baki ban san abinda ke wakana ba? Lallai, idan kana raye zaka sha kallo. Kallo ba na wasa ba kuwa.
Janan ta zauna a kasa tana fuskantata, babu wanda ya iya magana a cikinmu, har muka dauki lokaci mai tsayi a hakan. Can na daga baki, a hankali nace “me yasa? Saboda bana son shi ne ko me?”.
Janan ta dafa kafafuna da nake ta jijjigawa, cikin tausasshiyar murya tace “ko kadan, kawai son zuciya ne da rashin godiyar Allah. Kiyi hakuri, ban san hakan zata faru ba”.
Na kura mata rikitattun idanuna da nasan sun rine da jan bacin rai, nace “me kike nufi?”.
Tace “kamar sati biyu da suka wuce, na taba ganin hoton Umar din a wayar Haleemo, sai nake tambayarta a ina ta san shi, sai tace min abokin saurayinta ne. Ni kuma sai na share maganar. Ranar nan da nace miki kamar Umar, ni na tabbata na gan su su biyun, nasan banyi kuskure ba. Dana nuna miki kika musa sai naga babu amfanin fitowa gar da gar in fada miki, tunda ban tabbatar da alakar dake tsakaninsu ba… Don Allah kiyi hakuri!”.
Na girgiza mata kai, “ki daina bada hakuri akan laifin da ba ke kika aikata shi ba Jan. Haushina daya, daya bari son zuciya ya rinjaye shi har ya iya juya min baya, amma kanshi ya yiwa ba wani ba. Na kuma gode Allah da yasa na ga hakan da idanuna, basu dinke ni a baibai ba. Da muka zo muka yi aure a haka, inyi yaya?”.
Janan snorted, na bita da kallo cikin mamaki, tace “wai ke don Allah kina tunanin Umar yana da sha’awar kuyi aure?”.
Na bita da kallo mai dauke da alamar tambaya, amma dai duk da haka na amsa mata, nace “ehh mana, me kike tunani ne, daukar lokacin da muka yi a tare a banza zata tashi ba tare da munyi aure ba?”.
Tace “abinda nafi zargi kenan!”, zanyi magana tayi gaggawar katseni, “ki duba fa, ba fa yau kuke tare dashi ba, amma bai taba tado miki maganar aure ba. Idan ma kin tado sai ya hau miki kame-kame, baki taba zargin ko baya son auren bane?”.
Nayi shiru cikin tunani, ban taba yin wannan tunanin ba. Nafi kyautata zaton ko rashin maganar aure da baya min, baya so ne in hada karatuna da aure, yafi so sai na gama sannan ya fara maganar, don haka ban taba kawo zargin wani abu ba. Don haka na girgiza kaina kawai.
Tace “ko ma menene, ki godewa Allah daya nuna miki hakan tun kafin zance yayi nisa. Samari irin su Umar su kan yi iyaka bakin kokarinsu wajen ganin sun cimma burinsu akan macen data burge su. Ina tunanin dalilin daya tsayar dashi kenan, ko kuma sun yi tsubbace-tsubbacen da suka saba sun shawo kanshi”.
Na girgiza kai, “babu boka babu malam a cikin wannan lamari, ina tabbatar miki Umar a cikin hankalinshi yake”.
A nutse na warware mata dalilin daya haddasa fadan da muka yi dashi last time, har ma wasu fadan da muka yi akan matsala irin wannan, wanda bata taba jin hakan ba sai yanzu.
Ta kama baki cike da tu’ajjibi, tace “kin gani ko? wato da yaga cewa ta bangarenki babu sa’a, shine ita kuma data kai kanta yace bari ya biye mata. Kila a dabararshi idan ya gama da ita sai ya dawo kanki? Ko kuma wani shiri gare shi na daban?”.
Nayi shiru kawai ina kara juya lamarin a cikin raina. Har yanzu kaina bai gama yayewa ba, mamakin abin bai sakeni ba. Dama ana haka a duniyarmu? Kina sane, kana sane, ku take sanin, ku yaudari kanku ku yaudari wasu? Ina jin labarin snatching da dama, mafi yawa a labarai ko a gidajen radio ko a fina-finai, ban taba zaton yana faruwa da gaske ba, sai gashi yau ya faru a gaban idona, a kaina kuma.
Duk yadda naso in jurewa abin, kasawa nayi. Ji na nayi kawai hawaye na bin fuskata. Janan take ta bubbuga bayana tana bani kalamai masu kwantar da hankali, har naji zuciyata ta dan yi sanyi, amma nasan cewa na dan lokaci ne.
A hankali na mike, jiri yana kwasata, na shiga bayi. Tsaye nayi a gaban babbar mirror dake manne a bangon bandakin ina karewa kaina kallo. Idanuwa sunyi luhu-luhu, sun kuma yi jawur, daga ganina babu tambaya kasan kuka na gama shaka. Ko yanzun ma wasu hawayen ne suka ciko min idanu. Me na yiwa Umar a duniya dana cancanki wannan yaudarar daga gareshi? Ko kuwa Haleemo zan ce? Shin wai, ta yaya ma har suka hadu suka kulla wannan cin amana? Tun yaushe kuma??
Wato dai kaji tsoron dan Adam. Kuma kaji tsoron mutane masu halin shiru-shiru, sai yanzu nake gane gaskiyar Jan da tace halinta yafi na sauran muni. Lallai na ga misali akan kaina.
Na ciza lebena na kasa ina danne kwallar data ciko min ido. Ba zan kara zubda hawaye akan su ba, they are not worth it!. Na wanke fuskata kawai na daura alwala na fita. Katifa kawai na hau na kwanta, na ji wayata tana kara da vibrating, ina dagawa naga Umar ne yake kiran. Na jinjina kai kawai cikin rashin abin cewa, lallai rashin ta ido irin ta dan mutum tayi yawa. Wayar na dauka kawai na kashe nayi jifa da ita can bayan katifar, na sake komawa na kwanta.
Janan duk yadda taso ta ja ni da hira, kasawa nayi. Haka nan ta hakura tayi shiru. Har barci ya dauketa idanuna biyu, ina ta saka da warwara har barcin ya daukeni nima.
Washegari haka na tashi da matsanancin zazzabi da ciwon kai a jikina. Da kyar na iya yin sallar asuba, na koma na kara kwanciya na kawo bargo mai nauyi na rufawa jikina, amma hakan bai hana ni rawar sanyi ba. Har wajen karfe takwas na safe ina cikin wannan hali.
Janan tana zaune a gefena tana kallona cike da alamun damuwa rubuce a fuskarta, tun da asubahin take bin kaina akan in shirya mu tafi asibiti, amma na ki tashi. Yanzun ma abinda take ta fama dani kenan, “don Allah ki tashi Na’ilah, jikin ki kara rikicewa yake yi”. Ta fada cikin alamun lallashi da kuma roko, kai kawai na girgiza mata alamun a’ah, na kara jan bargo na rufa.
Ta kura min idanu, akwai alamun takaici da kurar da ita da nake yi rubuce baro-baro akan fuskarta. Tace “shikenan, kiyi duk abinda kika ga dama, an fada miki na damu ne?”.
Ta ga dai bani da alamun motsawa, sai ta kara matsowa kusa dani, cikin sanyin murya, cike kuma da nuna tausayi tace “haba Na’ilah! Ke da nake ganinki da hankalinki da komi, amma ki kasa yarda da abinda Allah ya tsaro miki? Akan namiji! Haba Na’ilah!! Akan namiji zaki zauna ki kashe kanki? In fada miki gaskiya? A banza zaki kashe kanki idan ma haka ne, mantawa zai yi dake, dama can bai daukeki a bakin komi ba. Yanzu haka ma kila ya riga da ya manta dake, kila yanzu haka suna can suna kwasar soyayyarsu babu abinda ya dame su yayin da ke kina nan kin saka bakin cikinsu a cikin ranki, kina nema ki kashe kanki a banza!”.
Na samu na girgiza kaina da kyar, murya na fita da kyar, ina ganinta dishi-dishi, nace “ba akan Umar bane!”.
Ta fusata, “to akan waye idan ba shi ba? Ke karamar yarinya ce da za a dinga bin kanki akan rashin lafiyarki wai? Idan kina so in yarda ki taso mu tafi asibiti yanzun nan!”.
Nace “mura ce kawai ba wani abu ba, zuwa anjima zai sauka, ki daina damuwa”.
Ta hau girgiza kai, “wannan kafar kai taki ban san irinta ba wallahi, Allah ya kyauta miki!”.
Na lumshe idanuna kawai saboda yadda nake jin sunyi min nauyi. Janan kuma ta saka ni a gaba tana kallo. Wani wahalallen barci ya daukeni kenan, naji alamun taba kofa alamun an fita. Ba’a jima ba aka sake bude kofar aka dawo.
Jin tashin murya ba daya a dakin ba yasa na bude idanuna da kyar.
Yaya Bilal ya kalleni fuska babu yabo ba fallasa, sai dai can cikin kwayar idanunshi, akwai wata kwantacciyar damuwa dana tabbatar ba rashin lafiya ta bace ta haifar da ita ba. Wannan, ko kuma dai idanuna ne suke min gizo kawai.
Ya dauke kallonshi daga kaina ya maida kan Janan dake tsaye a gefenshi, “me ya sameta?”.
Tace “zazzabi ne da ciwon kai, tun jiya da dare, amma bata son mu je asibiti. Kuma zazzabin karuwa ma yake yi maimakon ya ragu”.
Ya sake maida kallonshi kaina, duk da halin da nake ciki kasa daukar kallon shi nayi. Wasu irin sakonni ne suke fita daga cikin idanun nashi, bana tunanin shi kanshi ya san suna fita. Ga… Dan saurara! Wasu irin sakonni nake nufi? Anya kaina bai fara motsi ba kuwa? Ni wacece din shi da zan ce yana turo min sakonni ta idanunshi? Wow! Dama naji ance zafin zazzabi yana sa mutum ya dinga sambatu kila ma har da ganin hallucinations. Babu mamaki abinda nake gani kenan nima yanzu.
Maganar da Yaya yake yi ce ta dawo dani daga rants din da nake zabgawa a cikin kaina, yace “bari in kira Dr. Zubair in gani, Allah yasa yana kusa”. Ya juya ya fita daga dakin wayarshi a hannu yana dannawa. Janan kuma ta dawo gefena ta zauna, hannu ta kai tana daga goshina zuwa wuyana, ni kaina nasan ba karamin zafi jikina ya dauka ba, har wani tiririn zafi nake ji a jikina.
Ba ayi cikakkun mintuna goma da fitar Yaya ba sai gashi ya dawo. Yace “bismillah dakta, shigo”.
Janan ta tashi da sauri ta dauki gyale ta dora akan kayan barcinta. Ni kuwa dama kayan barcin dana saka doguwar rigar cotton ce mai dan gajeren hannu wanda ya tsaya min a damtsen hannu.
Yaya ya fara shigowa dakin, wanda nake zaton shine likitan daya kira ya biyo bayanshi. Ya ajiye dan karamin akwatin daya shigo dashi, ya bude ya fara ciro abubuwan gwaji da sauransu. Yana fiddo komi ya fara aikinshi.
Cikin awa daya sai gani manne da drip a hannu, da tulin magungunan malaria, har ma da typhoid.
#F.W.A
*☆⋆16⋆☆*
Ana sa min ruwan barci mai nauyi ya daukeni. Lokacin dana motsa har an cire ruwan, da alamun rana tayi sosai ko kuma ma lokacin azzuhur yayi saboda Janan dana hango akan abin sallah.
Jikina yayi karfi sosai fiye da lokacin dana tashi dazu da safe, na lallaba na tashi zaune. Cikin ikon Allah babu jirin da nake ji da kuma ciwon kan. Janan da taji motsina ta juyo, murmushi ta saki a hankali, “har kin tashi?”. Na gyada mata kai.
Ta tashi ta matso inda nake, “sannu, zaki iya tashi tsaye ko sai na kama ki?”.
Nace “zan iya, jikina yayi karfi yanzu”.
Tayi dan murmushi, “well, ai dole. Ruwa da kika sha!”. Na murmusa kawai ina girgiza kai. A hankali na mike tsaye, karfin jikin nawa ba sosai bane, haka nan na lallaba na shiga bandaki. Sai da nayi wankan ne ma naji jikina ya danyi karfi ma, nayi brush tare da dauro alwala na fito. Janan bata dakin, na zauna na shafa mai tare da bude wardrobe dinta na ciro wata buba ta wani jan yadi mai taushi na saka. Da yake haka na taho shekaranjiya zikal dina, kayanta nake amfani dasu. Don ma yanayin jikinta da nawa kusan daya ne, abinda zan nuna mata kawai cikar kirji, amma bayan haka babu wani bambanci mai yawa a tsakaninmu.
Na shimfida abin sallah na tayar da sallah, bayan nayi na jero nafilfili, na zauna ina jan casbaha. Janan ta shigo dakin, na bita da kallo tana ajiye wani babban flask, fita ta sake yi ta dawo da gorar ruwa da faranti da cokali. Sai data ajiye sannan ta kalleni, “taso ki ci abinci, ki sha magani”.
Sai da tayi maganar abinci sannan naji cikina yana juyawa, ba musu na tashi na cire hijabin jikina na ninke ta da abin sallar. Tun kafin in zauna kamshin kifi ya cika min hanci, naji yawun bakina ya guda. A kasa na zauna muna fuskantar juna, ta turo min plate cike da faten doya. Anyi garnishing dinshi da green beans, peas, alayyahu, hanta da aka yanka kanana, ga kifi da dafaffen kwai a gefe. Ina yin loma daya na lumshe idanuna, kai na hau girgizawa, “ramgwadi! Gaskiya yau ba karamin baje basira kika yi wajen girkin nan ba, meye sirrin?”.
Ta kalleni, “ke yanzu nace miki ni na dafa wannan abincin yarda zaki yi? Yanzu na amsa shi wajen Anty Sarah”.
Na bude baki cikin mamaki, watakila lokacin da yan kirki suke kan Anty Sarah bamu taba sa’ar cin karo dasu ba sai a wannan lokacin. Iyaka sanina da ita, wannan baya daga cikin halayen dana santa dashi. Amma zata iya yiwuwa dama can hakan take, kila sanin hakan ne bamu taba yi ba.
Nace “ta kyauta sosai, nagode”.
Ta kai cokali daya bakinta, “ta shigo ne taga yanayin jikina fa sai ta ganki da drip a hannu. Dazu kuma sai ta turo Mimah tace in je in amsar mana abinci”. Na gyada mata kai. Har muka gama cin abincin babu wanda ya sake yin magana. Bayan mun gama, Janan ta kauda kayan can gefe, ta dauko magungunan ta fara balla tana miko min. Da kyar na iya watsa su a baki na hadiye. Wannan yana daga cikin dalilan da suka sa naki tashi dazu da safe zuwa asibiti yana nufin allura da magunguna, ni kuma bana son allura da magunguna.
Janan ta harareni lokacin dana hadiye kwayar maganin karshe da kyar, na fara kakari. Tace “dazu ai da ana tsira miki allura a jiki ko a jikinki”.
Nace “kema kin san saboda bana cikin hankalin kaina ne, amma ina ji ina gani in zauna a tsira min allura? hauka nake?”.
Ta kwashe da dariya, na harareta, “muguwa kawai!”. Gwalo ta min kamar wata karamar yarinya.
Tashi tayi ta dauki kwanukan ta fita. Na lallaba na lalubo wayata daga bayan katifa inda na jefata jiya. Nasan anyi ta nemana babu kakkautawa, musamman ma Muhammad. Na kunna wayar na tsaya tayi loading kafin na bude ta, nayi gaskiya kuwa. Sakonni daga Muhammad sun fi cikin kwando, tambayarshi daya, lafiya? Na hade fuska lokacin dana kula daga cikin sakonnin akwai na Umar, ko kara kallonsu ban yi ba na goge su gabadaya. Na tafi dungurungum nayi blocking dinshi daga wayata.
Komawa nayi daya bayan daya ina karanta sakonnin shi. Duk karantawar da zan yi, zuciyata kara narkewa take yi cike da begen shi, Allah ya sani, a kullum kaunar bawan Allahn nan kara yado take yi a sassan zuciyata. Ban sani hakan ko abu mai kyau bane ko kuma akasinsa. Kafin in gama karantawa jikina yayi wani irin sanyi, daga cikin kalaman shi kawai, babu tantama zaka karanci tsananin kulawa, tsantsar so, da kauna mara iyaka a cikinsu. Jikina yayi sanyi saboda babu mahalukin daya taba nuna min kwatankwacin irin wannan so, kauna da kulawar da wannan bawan Allahn yake nuna min. A duniya yanzu waye yake damuwa kawai don ya kira wayar wani daga dare zuwa safe ya ji a kashe? Sai Muhammad. Sai daya kai ga tambayar ko dai wani laifi yayi min ne, a cikin sakon. Ina gama karanta shi na lalubo lambar shi na danna kira, ban ma san me zan ce mishi ba. Sai dai cewa aka yi line busy, alamun yana waya. Don haka naci gaba da karanta sauran sakonninshi, nasan idan yaga missed call dina zai kira.
Janan ta dawo dakin da waya a kunnenta, daga yanayin yadda take maganar da Yaya Bilal take wayar. Hankalina yana kan sakonnin M.B da nake ta nanatawa, kamar wani karatu. Don haka sama-sama nake jin muryarta a kaina. Bayan ta gama ta zauna a gefena, tace “Yaya ne ya kira yana tambayar ko kin tashi nace eh. Yana Funtua shi da Anty Ameerah, wai ya kaita wajen sunan kawarta,” ta fada tana tabe baki, ni kuma na dan murmusa saboda yadda ta bani dariya, “yace a duba ki da jiki dai kafin ya dawo”.
Nace “babu komi wallahi, ai na warware”.
Tace “yauwa, na ma tuna! Ummah tace tana so ta duba ki itama”. Ta ciro wayarta ta kirata, bayan sun gaisa sun yi yar hira, Janan ta miko min wayar na amsa, na gaisheta cike da girmamawa kamar tana gabana. Tace “Janan dai ta goga miki, daga zuwa jinya sai kema ki buge da jinya?”, ni da Janan muka yi dariya sosai. Mun jima muna hira da ita, Ummahn su Janan ta iya bi da mutum cikin sanyin kalami kaji ka saki da ita, akwai lokuta da dama da zamu fara hira da ita cikin dari-dari ko rashin sakin jiki, amma cikin dan kankanin lokaci zan ji na saki da ita sosai, inji na hau hira da ita sosai. Wasu lokutan sai daga baya zan zauna ina mamakin hakan. Munyi sallama da ita tana ta zuba mana addu’o’i kamar yadda ta saba, na kashe wayar na mikawa Janan.
Kwanciya tayi rigingine tana kallon ceiling din dakin, ni kuma na lalubo game din candy crush a wayata ina bugawa. Shiru ya ratsa dakin na dan wani lokaci, can naji tace “Nan da sati biyu Yaya zai tafi umarah shima”.
Na kalleta cikin mamakin dalilin da yasa ta fada min, nace “and?”.
Ta kalleni tana wani yin kasa-kasa da idanu, “don Allah kizo ki taya ni zama kafin ya dawo!”.
Na zaro ido, “wa? Ni?? Ki rufa min asiri in mutu maza su kaini ba mata ba! Ana zaman lafiya, da hankalin kaina, anya kina ma so na kuwa?”.
Ta harareni, “yo meye na wani zaro ido? Wuta nace ki zo ki taya ni zama?”.
Na koma na kwanta ina dariya, “lallai ma, zama a gidan nan naku ai sai wanda ya shirya, ni kuma ban shirya ba. Jira nake goben nan tayi, idan na cira kafa na bar nan gidan sai kuma baba ya gani. Idan da son rai na ne ma, har in bar Zaria ba zan kara zuwa nan ba!”.
Tace “inaa, kema kin san wasa kike yi coz you are stuck with me babe, babu yadda zaki yi dani. Sannan gobe babu inda zamu je sai jikinki ya kara yin kwari sannan, maybe zuwa talata?”.
Na kalleta ina dan murmushi cike da jindadi, “babu wani hutu da nake bukata don ni nan garas nake ji na, amma kuma wa zai ki hutu koda na kwana daya ne musamman daga wannan asibitin?”. Itama tayi murmushi.
Karan da wayata tayi ne yasa na kalli hannuna duk da kida na musamman ne, na riga nasan mai kiran. Na turo baki cikin shagwaba, ban san dalili ba, duk lokacin da nake tare da Muhammad, na kan ji ni kamar wata yarinya karama, kamar wata sabuwar halitta.
Cikin shagwabar na daga, yana ta magana nayi shiru, yace “haba baby na, come on, talk to me mana. Nayi laifi ko? Am sorry!”. Nayi shiru ina jinshi ya cigaba da cewa “haba baby na, baki so in ji daddadar muryar nan taki ne? Come on…”.
Na turo baki kamar yana gabana, “ba kai bane ka ki daga wayata dazu ba?”.
Ya saki murmushi mai sauti, “tuba nake gimbiyata, ina amsa wata waya mai muhimmanci ne. And you are the one to talk, idan maganar gaskiya ake yi ai nine ma yakamata ace nayi fushi. Na ga tun jiya nake kiran wayarki a kashe. Baki ji warin kunar da zuciyata ta dinga yi bane?!”.
Ban san lokacin dana kwashe da dariya ba, nace “oohh, da gaske?”.
Yace “sosai ma, da yadda nayi ta kiran sunanki. Duk baki ji ba?”.
Na sake yin wata dariyar ina girgiza kai cikin wani irin matsanancin farinciki, nace “ban ji ba gaskiya!”.
Yace “nayi tunanin gabadaya mutanen Zaria sun ji!”. Na cigaba da kyalkyala mishi dariya.
Mun jima sosai muna kwasar hirar soyayyarmu, har na rasa tracing din lokaci. Lokacin da muka yi sallama dashi, bakinshi yana furta I miss you’s da I love you’s. Zuciyata fara kal, kamar farar takarda.
Janan da tunda na fara wayar take kallona baki a dage, ta kalleni tana murmushi, “anyi nisa a lambun soyayya!!”.
Nayi dariya ina birgima a tsakiyar dakin, “baki san komi ba Jan… You’ve no idea. Ya Allah, I love that man!!”.
Dariya ta saki, ta taso ta rungume ni, ban san dalili ba, amma nima rungumeta din nayi. Tace “na taya ki murna, dear. Congratulations!”. Nayi murmushi.
#F.W.A
*☆⋆17⋆☆*
Yinin ranar a daki muka yi shi. Bayan munyi sallar la’asar, Janan ta kunna mana film din X-Men a wayarta muka fara shi tun daga farko. Babu abinda ya dinga tada mu sai sallah da cin abinci.
Bayan isha’i, Janan ta tado ni muka fita waje, a cewarta kafa zamu dan wasa musamman ni da babu inda na fita tun yau. Ban damu ba, na dauki hijabi ta na saka muka tafi. Garin tun da yamma tayi yayi alamun hadari, ga wani irin zafi da aka yi kamar zai kona mutane. Sai dai zuwa yanzu ya dan yi sanyi, iska mai sanyi yake bugawa a hankali.
Muka taka ni da ita har bayan layin su, can wajen irin masu suyar wara da doya da fulawa dinnan don Janan tace abinda take son ci kenan yanzu.
Matar inyamura ce, sana’ar hannu take yi tun karfinta, safe, rana, dare, babu hutu balle kakkautawa. Shi yasa wajenta kullum cike yake da kwastomomi da kuma ma’aikatan da suke kama mata aiki.
Saboda yawan mutane yasa bamu samu mun siya da wuri ba, lokacin da muka tsaya a gabanta, ta kallemu cikin murmushi. Ba laifi mun dan saba da ita, saboda a yawancin lokuta a wajenta muke sayen buns da eggroll da rana. Ta kalli Janan tace “kwana biyu kun dauke mana kafa!”.
Ni da Janan murmushi kawai muka yi muka gaisa da ita. Ta kulla mana wanda muka saya a cikin leda, muka amsa muka mata sallama muka juya.
Cikin rashin sa’a kafin mu karasa gida ruwan sama ya sauka mai karfi, muka daga kafa cikin sassarfa muka kara sauri. Duk da haka kafin mu karasa gida, jikinmu ya jike sharkaf! Har digar ruwa muke yi. Da sauri muka karasa cikin falo, a dan corridor dinsu kafin a shiga falo muka tsaya domin mu dan kafe kada mu bata musu carpet din falo da lema.
Muna tsaye anan sai karan turo kofa muka ji, muka juya muna kallon Yaya daya shigo shima yana linke umbrella din daya shigo da ita. Muka zaro idanu mu duka a tsorace muna kallonshi, nayi zaton a gidan Anty Ameerah yake yau, ko kuwa ba acan yake ba? Aka fara kallon-kallo tsakaninmu dashi.
Ba Janan kadai ba, ni kaina sai da naji zuciyata tana tseren tashin hankali.
Ya hade fuska kamar yaga wasu mala’ikun daukar rai, “daga ina kuke?!”. Ya tambaya murya a cune.
Janan ta fara kokarin ja da baya a tsorace, cikin in’ina ta fara cewa “um… nan.. ne baya!”.
Ya daga murya, “ina ne nan bayan exactly?! Ba na hana ki fita waje da dare ba? Ban da rashin hankali kawai sai ku kama kafa ku fita daga gida da dare babu tunanin komi, kuna ganin hadari kuma! Ku duba yanda ruwa yazo ya muku duka, musamman ke da kike rashin lafiya! Karatun da kuke yi kenan dama? Idan fa jikin ki ya kara rikicewa?”. Ya maido tambayar kaina. Na dan yi tsalle a tsorace, na koma bayan Janan na lafe kamar ita zata kare ni daga fadan shi.
Allah ne ya bata kwarin gwiwar iya daga baki don ni gabadaya jikina rawa yake yi, tace “kayi hakuri Yaya, abinci muka fita muka sayo”.
Yace “abincin waje a gidana? An hana ku dafa abincin ne? Waye ya hana ku?!”.
Janan tayi saurin girgiza kai, “babu ko daya wallahi, kawai mun ji marmarin awara ne, shine muka fita muka sayo. Bamu yi zaton ruwan zai same mu a hanya bane amma kayi hakuri…”.
Ya dan sauke ajiyar zuciya alamun ya dan sauko, yace “to shikenan, amma kada ku kara”. Muka hau gyada kawuna kamar wasu kadangaru.
Yace “to ku wuce kuje ku canza kaya kafin wani abin ya kama ku”. Bamu jira ya sake cewa komi ba, muka bar wajen a sukwane.
Sai da muka shiga daki muka maida kofar muka rufe, sannan muka sauke wata nannauyiyar ajiyar zuciya, kafin muka kalli juna muka kwashe da dariya.
Bayan mun canza kayan jikinmu, mun shanya wadanda muka cire, muka cigaba da kallonmu muna cin awarar.
*
Washegari bamu tashi da wuri ba saboda mun san cewa ba asibiti zamu je ba. Da muka yi sallar asuba, Janan ta wa wata sister Mairo matron dinmu text akan cewa ba zamu samu damar shigowa ba saboda rashin lafiya, bayan ta turo mata da amsa akan babu damuwa Allah ya bamu lafiya, muka koma gefe muna dariya kafin muka koma barci. Sai wajen karfe tara na safe muka tashi. Janan ta fita kicin zata dora mana abinda zamu ci, ni kuma nayi amfani da wannan damar na shiga bandaki na watsa ruwa.
Kafin in fito ta dafo mana indomie, muka zauna muka ci ta sake daukar kayan ta fita dasu. Ta dawo ta zauna a kusa dani ina duba wasu textbooks dinta, zuwa yanzu naji na warware sosai, kamar ban taba yin wata rashin lafiya ba, amma duk da haka sai da Janan ta takura min ba sha magani.
Tace “ki zo muje ki taya ni in yiwa Yaya doughnut da cin-cin don Allah”.
Nace “nayi zaton ya tafi?”.
Ta girgiza kai, “sai gobe. Abin azumin da za’a fara gobe, yana can babban gida, jiya da yau yayi rabon azumi”.
Na ajiye textbook din ina kallonta, “amma banda abinki Jan, saboda Allah me zai yi da doughnut da cin-cin da azumi?”.
Tace “ya dinga sahur ko shan ruwa mana!”.
Na fashe da dariya ina girgiza kai, “gaskiya Ummah tana da sauran aiki a gabanta wallahi, haka zaki yi aure kije ki dinga soyawa miji cin-cin da azumi?”.
Ta mintsileni a gefen cinya tana dariya, “bana son iskanci wallahi, zaki taya ni ne ko yaya?”.
Na mike ina laluben abinda zan sakaya jikina dashi, “kin san ni bana wuce tayin kayan zaki dangin fulawa”. Muka fita daga dakin muna dariya bayan na dauki karamar hijabi data tsaya a ruwan cikina na sa.
Gidan shiru, haka falon babu kowa hatta da TV a kashe take. Na san kila sun tafi makaranta, wannan ko kuma suna daki suna barci. Muka fada kicin muka fara aikin daya kaimu.
Bamu yi minti talatin cikakke ba, muka ji an bude daki an fito. Ba’a jima ba Salama da Haleemo suka shigo kicin din cikin kayan barci, na kallesu na kauda kai cikin girgiza kai. Haka suke yawo wani lokacin a gidan cikin kaya masu bayyana jiki, a ganina duk da a gidan Yayarsu suke ai hakan bai kamata ba. Ba fa kowane mutum bane na Allah.
Haleemo ta dan dakata data ganmu a kicin din, sai kuma ta maze ta kallemu, wai “sannunku!”. Muka yi banza ni da Janan muka kyaleta kamar ba damu take ba. Salama tayi dariyar mugunta tana bude firjin, tace “Allah ya kara, uwar sanabe da neman gindin zama!”. Ta dauki abinda zata dauka ta fita daga kicin din ta bar Haleemo a tsaye.
Kame-kame ta fara, “uhmn, Na’ilah nace., ni fa ban san wannan gayen saurayinki bane! Shi ya fara zuwa wajena, kuma sai daya ne, na rantse da Allah…”.
Na katseta ta hanyar juyawa ina watsa mata harara, nace “ni fa kinga Haleemo, idan na raina kasuwa ko sako bana badawa cikinta. Ban tambayeki alakar ki da tsohon saurayi ba ba, ko kallon banza ban miki ba, saboda baki kai matsayin da zan zauna ina cacar baki dake akan wani saurayi ba wallahi. Alfarma kika min babba da kika lallaba kika hillace shi, godiya ma yakamata in miki, don haka ki kwashi jikinki ki bar nan wajen wallahi, duk abinda mutum yayi dai ai kansa ya yiwa, walau mai kyau ko marar kyau!”.
Ta saki baki tana kallona, sai kuma ta juya ta bar kicin din da sauri. Naja dan siririn tsaki.
Da yake kwabin doughnut din da muka yi babu yawa, nan da nan muka gama soya shi. Muka fara na cin-cin din, zuwa lokacin rana ta fara yi.
Ni kadai ce a kicin din lokacin da Raheemah ta fado kicin din kamar wata kububuwa, Janan ta leka waje zata samu wani yaro ta suka can bakin titi.
Na gaidata a kaikaice, hankalina yana kan fulawar da nake murzawa.
Maimakon ta amsa, sai naji ta ja dan tsaki, “uhumm, ihunka a banza kenan! Ina amfanin wadda za’a kwace saurayi a hannunta tana zaune? Hakan yana nuna aikin banza ne, kuma abu mai wahala ace za’a iya kwace miji! Don ma dai mutum yaji ya sani, idan ma saboda mijina ne ake min zarya ana min shige da fice a gida, to wallahi mijina yafi karfin haka. Nima kuma nafi karfinshi!”.
Allah sarki, naji maganganunta sun bani takaici sun kuma bani dariya, na girgiza kai a hankali ina dan murmushi. Banda tsabar hauka da rashin tunani, har ta wani kalleni tace wai zanyi kwacen miji? Tsakanin ni da ita ko wa yayi kama da wanda zai yi kwace? Na sake girgiza kai.
Ta kama kugu tana wani jijjiga jika ganin ban tanka ta ba, tace “ke Baiwar Allah dake nake, aha! Ni dai na fada na sake fada miki, mijina yafi karfinki!”.
Na juya na kalleta ina murmushi, “ai na fiki sanin haka, saboda haka ki kwantar da hankalinki, mijinki naki ne ke kadai, ban iya snatching ba wallahi!”.
Sai ta hau wasu tsalle-tsalle cikin masifa, “dariya ma kike min kenan? Ke wallahi na ga alamun iskancin ki yawa yake yi fa! Ke har kin isa ki zauna kina min ba’a? Wacece ke, yaushe aka haifeki? Aikin banza dana wofi!! An ga mijina mai kudi an makale mishi kamar maganadisu, ana ta wani shige da fice a gida har da rashin lafiyar karya. To ta Allah ba ta mutum ba wallahi, kuma duk dan iskan da yace zai kara dani wallahi shi zai ji jiki. Haka nan za’a koma gida aci gaba da cin tuwon datsa miyar kuka tsanwa, mu dai mun fi karfin mutum!!”.
Na janye robar hannuna gefe ina kallonta, raina ba karamin baci yayi da maganganunta ba, amma na danne, nasan so take take raina ya baci in biye mata. Na fuskanceta sosai, ina watsa mata wani wulakantaccen kallo, babu shiri ta shiga taitayinta. Nace “na farko, ban san abinda na miki ba da zaki zo haka kawai ki hau zagina, sai dai bari in tabbatar miki da wani abu daya, I’m not into your husband! Hakan da kike yi ya tabbatar min da cewa ko dai kema kwacen mijin kika yi, ko kuma dama can kwacen samari da mazaje a jininku yake. Kowanne ne dai wannan matsalar ku ce, don ni ban saba ba, ban iya ba, kuma ba zan yi ba. Ke gida da dukiyar miji suka dama, dama don su kika aure shi. Mijinki baya cikin yan kayana, ki godewa Allah, da ba don haka ba wallahi da sai na sa kin zubda hawaye, don haka baiwar Allah, ki shiga taitayinki. Gida ne, daga gobe idan kika kara ganina a cikinshi ki min duk abinda kika ga dama!”.
Ta daga baki zata yi magana, amma ta kasa. Tayi haka yafi sau uku, kafin tayi kwafa a fusace ta juya ta bar kicin din da sauri, na ja tsaki ina furta “sakarkaru” a kasan raina. Raheemah sakara ce, daukar zugar kanne da kawaye yana nema ya jefa rayuwar aurenta cikin garari da matsala. Wani abun ban dariya da takaici shine, zasu zuga ta ta wa miji ko danginsa rashin mutunci, ta hau kai ta zauna, su kuma su koma gefe suna mata dariya da ba’a, me amfanin hakan kenan?
Muna gamawa na koma daki na bar Janan zata gyara kicin din ta kuma hade kan kayan. Na wuce mutanen gidan a zaune su duka, muna kallon-kallo dasu daya bayan daya. Ni har mamaki nake, anya kuwa karatu suke yi? Ita dai Raheemah dama tun daga karatun diploma tace ta yanke karatu, su kuma su Salama da suka zo suka zaune a gidan da cewar karatu suke yi, ba makarantar suke zuwa ba. A sati idan suka je sau uku, to wannan shine highest. Babu aikin da suka iya sai kinibibi da gulma. Ban san daga ina Raheemah take samun idea din wai saboda Yaya nake zuwa gidanta ba, abin is so absurd. Tunanin hakan a karan kaina idan nayi sai inji kaina yana juyawa. Na dauki kudurin daga wannan lokaci, ni da gidan Yaya sai dai ziyara amma banda kwana. Ziyarar ma da ace har in gama karatuna in bar Zaria ban kara yin ta ba, da naji dadi.
Karan wayata ya katse min tunanin da nake yi nayi nisa a tunani ko karan ban ji ba sai daya kusa katsewa. Yana katsewa aka sake kira, na dauka naga Yaya Mudatthir ne, don haka na daga. Bayan mun gaisa da tambayar mutanen gida, yace ya ba wani abokinshi da zai je Kaduna gobe sako zai kawo min, zai tsaya ya kwana a Kano sai ya taho da safe, ina ganin zan iya fitowa bakin hanya in karba? Nace mishi ehh, yace to ya bashi lambar wayata zai kira ni. Nace to, tare da mishi godiya, muka yi sallama.
Komawa nayi kan katifa na kwanta zuciyata cunkushe da tunanika, har Janan ta dawo dakin hannu dauke da plate shake da abubuwan da muka yi. Ranar su muka yi ta ci ko abinci bamu nema ba.
Washegari talata aka tashi da azumi. Bayan mun shirya, mun saka uniform dinmu, muka wuce asibiti. Allah ya taimaka wanda zai kawo sakon muna fita ya mana waya, don haka muka tsaya muka amsa muka wuce asibiti. Hostel kawai na wuce na ajiye su ko dagawa ban yi ba, muka wuce ward dinmu.
#F.W.A
☆18☆
Azumi bai taba bani wahala irin na ranar Alhamis ba. Muna dawowa daga hutun sallah zamu zana wata irin exams da suke kira ‘council exam’, wannan exam ita zata yi deciding din kasancewar ka nas a cikin wannan shekarar ko kuma akasin hakan. Don haka hankulan kowa a tashe yake, karatu kowa yake yi babu sassautawa balle takaitawa. Ga projects da suka sako mu a gaba. Kafin mu gama projects uku zamu yi, bayan mun gama TP dinmu munyi daya, yanzu haka preparation din proposal muke yi cikin wannan azumin. Ga kuma wani da muka fara cikin wannan satin. Yanzu haka dawowata daga cikin makaranta kenan ganin supervisor dina, wani inyamuri mai dan banzan rashin mutunci. Allah kadai yasan wahalar daya bani yau. Nayi zarya zuwa department dinmu ta kai sau goma yau, yana cewa inje in dawo, hawa bene ma kadai ya isheni. Cinyoyina masifar ciwo kawai suke yi, ga rana, ga azumi. Tun ruwan ranar Lahdi da aka yi ruwa ya mana duka, ba’a sake yin ruwa ba har yanzu, dama daminar ba karfi tayi ba.
Komawata ofishin Mr. Akafyi a karo na kusan goma, na riga na rantse na kuma maya, wannan karon idan naje ya sake cewa inje in dawo, to warewa ta kawai zanyi, in yaso na dawo washegari. Don na gaji.
Na sameshi da daya dalibar da aka hado mu wajenshi da ita a zaune akan lumtsumemiyar kujerar ofishin suna kwasar hirar abinsu. Dama ina jin kishi-kishin cewa mutumin irin yan adawa da musulmai ne, duk mai saka hijabi da nikabi, apparently shi a wajenshi makiyi ne. Nayi kwafa a kaikaice, wato ita wannan da yake tasha izgar doki aka ta fiddo cinyoyi da hannuwa waje, zai iya bata lokacinshi kacokam a kanta, tunda zai iya taba ta yadda yake so, duba da irin zaman da suka yi. Duk da akan teburi ne, sai da yayi yadda yayi yake taba hannunta.
Na gaida shi ya amsa yana wani cijewa, Allah kadai yasan iya dauriyar da nayi ban sakar mishi tsaki ba. Da ace ina da hanyar da zan bi a canza min supervisor, wallahi da da gudu zan bita, a canza min shi in huta. Sai dai a babbar makaranta kamar wannan, babu wani abu da yake zuwa ta sauki ba tare da hanya ba. Wadanda suke samun wannan garabasar it’s either iyayensu suna da kudi, ko sun san wasu da suka san wasu manyan a cikin makarantar, ko kuma ke kinsan wasu manya a cikin makarantar, ta nan ne kawai zaki samu yanda kike so. Ire-iren mu mu ya-ku-bayi, da bamu san kowa ba kuma kowa bai san mu ba, haka nan muke cije duk wani wulakanci ko kaskanci da za’a nuna mana, muyi ladab, domin mu samu mu gama karatunmu cikin sauki ba tare da an janyo mana wata matsala da zata fi karfinmu ba.
Kusan mintuna na talatin a ofishin shi, yana min bayani amma rabin hankalinshi yana kan yarinyar dake gabanshi, abin ban takaici shine daga gani yayi diya da ita in ma ba jika ba. Nayi Ala-wadai a cikin zuciyata, na samu ya sallameni ni dai na bar musu ofishin, in yaso ma su cinye kansu kowa ma ya huta.
Bayan na fita daga makaranta na tsaya a banki da niyar cire wata naira dubu daya da nayi tanadinta a cikin akawun dina. Abin ban haushi da takaici sai da layi yazo kaina bayan na sha uwar rana da jira, wai kuma suke ce min ‘insufficient balance’, haushi yazo min iya wuya. Na gwada ciro naira dari biyar, shima a lokacin suka ce babu. A matukar fusace na karasa hostel. Na san ko hauka nayi ba zan cewa Baba ya turo min kudi ba. Ni yanzu haka taraddadin yadda zan ce ya turo min kudin jarabawar da zamu yi nake yi. Kudi ne kusan naira dubu hamsin da doriya.
Na haye kan katifa na kwanta kawai na lumshe idanuna, gajiya, tunani, yunwa, zafi kai komai ma, suka taru suka min rubdugu sai dana rasa ina zan jefa kaina inji sauki a ciki. Sai da yamma tayi likis, ban ma sani ba sai da Esther ta fara tambayata wai yau ba zan yi dafe-dafen karya azumi ba? Sannan na mike ina dingishin wahala. Sauran kayan miyar da suka rage min basu da yawa, dama nufina idan na ciro kudin in tsaya a kasuwa in siyo kayan miyar in kuma karo wasu abubuwan, to kuma ga abinda ya faru. Sauce nayi, na dafa farar spaghetti da zan ci da ita. Nasan zasu isheni in sha ruwa in kuma yi sahur.
Na sauka kasa dakin wata student da take saida ruwan sanyi da kankara, na sayo. Zobon dana yi saura jiya na kara gyarawa na juye a cikin jug. Naje na dauro alwala na dawo na zauna akan abin sallah ina lazumi har aka kira sallah. Na dauko dabino kwara uku da Yaya Bilal ya bani ranar talata, irin yan makkah dinnan gida hudu, nasan har azumi ya kare ina ci, na ci. Sai da nayi sallah sannan na ci abinci.
Ina gama sallar isha’i naji wata irin gajiya da kasala ta saukar min, haka nan na daure nayi tarawihi. Zuciyata na rada min in kwanta kawai in huta, it has been a long day, yayin da wata take kara karfafa min jiki akan in dai daure in tafi karatu. Bayan dogon nazari da saka da warwara dai na daure na warci wayata da littafai na tafi aji. Kwana biyu ko zaman kallon ma bana yi. Yawancin fina-finan da nake kallo kafin, ko lokacin sallar tarawihi ake yinsu, don haka na ajiye su gefe. Idan na samu lokaci ina hawa YouTube in kalla dai. Yanzu ma nasan idan na shiga common room ba karatun zanyi ba, shi yasa na fara zuwa class.
Karfe sha daya tana yi, na fara haramar hada kan kayana. Na rungumi littafan dana dauko na fito daga cikin theatre hall din. Yanayin wajajen musamman da dare, zaka ji shi shiru, babu zirga-zirgar komi sai ta ababen hawa da basu cika yin wajen hostel din ba sai da can babban titi sai kuwa dalibai da suke zuwa aji ko kuma masu dawowa. Na kan ji yawancin mutane suna korafin tsoron wucewa ta wajen da dare, sai dai ni ban taba ganin dalilin da zai sa naji tsoron ba. Naga a cikin waje mai tsaro muke, idan ba wani Iko na Allah ba, babu abinda zai faru da mutum.
Idan nayi addu’ata na shafa ni kam shikenan, sai in jona earpiece in done kunnena, in rufe komi kwata-kwata sai karatun da nasa, ko kida ko kuma wa’azi. Babu irin yanayin da nake matukar so irin wannan. Na kan ji ni free, without worries.
Yanzun ma abinda nayi kudirin yi kenan, musamman yadda ranar yau ta kasance min. Ji nake kamar inyi tsuntsuwa in ganni akan katifata. Sai dai banyi nisa da fara tafiya ba, kiran Muhammadu na ya shigo wayata. Ina jin wannna muryar tashi yana ambatar “baby na!”, I was a goner. Mantawa nayi da komi dake cikin duniyar nan, har ni kaina kuwa, sai shi kadai. Rakiya ya min har cikin dakin da nake, muna ta hirarmu cikin raha, kafin muka yi sallama dashi. Na cire kayana na sa na barci na dauro alwala nazo na kwanta.
Karfe uku alarm din dana sa ya buga na tashi, na fita na dauro alwala na zo na fara nafilfili har lokacin sahur yayi, nayi na sake tado wata sallar har dai aka kira sallah nayi na zauna ina karatun Al-Qur’ani kafin lokacin fara shirin shiga cikin asibiti yayi.
Kamar yadda nayi tunani, maganar kudin jarabawa bata zo min da dadi ba. Yadda Baba ya rufe ido yana masifar shi bashi da kudi, ina nema in tatuke shi, abin ya bani mamaki. Tun bayan kudin school fees daya turo min, naira dubu goma ta sake hada ni dashi. Yanzu kusan wata na biyu kenan a Zaria, amma ba halin in daga baki inyi maganar kudi sai ya hau zagina. Ko provision yawanci Yaya ne yake turo min su, sai kuwa kudin da yake turo min jifa-jifa, dasu nake amfani in sayi kayan bukata. Bayan doguwar wayar da muka yi dashi a ranar Assabar kenan, daki na koma na kwanta. Esther ta tafi weekend gidan kawunta, Maimunah kuma bata ma dakin tun jiya, babu wanda yasan inda ta tafi. Don haka ni kadai na kwana a daki.
Nayi lamo akan katifa cikin tunani iri-iri, kala-kala, ban taba jin karatun nan ya fita a raina ba sai yau. A raina na raya wai da wanne ake so inji ne? Abu ne da bai taka kara ya karya ba, wanda na tabbata yafi karfin Baba, amma kullum cikin ja wa kanshi babu yake, kullum babu, kuma babun a kaina kadai take.
Yawancin matsaloli irin haka idan suka taso dama sai dai in tuntubi Yaya da maganar, idan bata fi karfinshi ba ya maganceta, in kuma tafi sai ya kai ga dangana da su Malam. To ita kuma rayuwa ba zai yiwu taci gaba a haka ba, ba zai yiwu ace kai kullum cikin bani-bani da a maka-a maka kake ba, kowa ma dama zai ji ya gaji.
Sai dai idan nayi duba ta wani bangaren, sai inga yaushe na cika bani-bani kamar yadda Baba yace? Tsakanina dashi kawai kudin handout ne, sai abinda yaga dama ya dan lafo min ciki kawai. Dama can yawancin hidima da dawainiya Yaya ne yake yi, idan aka samu ya biya school fees da kyar, ya hado min provision, to sauran fa sai dai yadda hali yayi, sai na sha matukar wahala ya kuma yazga ni yadda yaga dama sannan zai turo min na bukatun yau da gobe. To maganar gaskiya na gaji yanzu, yanzu haka kwanciyar da nayi ina tunani, tunanin hada kan kayana nake in koma gida kawai, azabar ta isa.
Sai kuma naga idan ma na koma, ni zan kwari kaina, babu wanda zai ji a jikinsa dai sai ni. Don haka naci gaba da tunani ina laluben mafita. Nasan mafita daya itace in fadawa Yaya, amma gani nake kamar abin yayi yawa. Shi shikenan kullum cikin ji da matsalata, kullum babu hutu?.
Ban tashi daga kwanciyar ba sai da aka kira Sallar azuhur, ashe wani wahalallen barci ne ya daukeni. Wani irin barci mai dauke da wasu irin sarkakkun mafarkai. Na tashi ina mika da hamma, maimakon inji gajiyata ta tafi, sai naji kamar an dauko gajiyar duniya ne an dora min aka. Haka nan na lallaba na watsa ruwa a jikin nawa ya dan min karfi, sannan nazo nayi sallah.
Ina cikin karatu Janan ta kirani. Roko na ta dinga yi akan inje in mata weekend, kai tsaye nace mata a’ah, ta dawo tana magiyar to inje in tayata shan ruwa, nan ma nace a’ah. Ni dai tunda na samu nayi sa’a, Allah ya taimakeni na baro gidan, ai an wuce wurin. Ta gaji tayi fushi ta ajiye wayar. Da yake ba a cikin yanayi mai dadi nake ba, kyaleta nayi kawai.
Yinin ranar haka na yi shi sukuku, can da yamma wai sai ga Maryam, mun gaisa da ita gari-gari, wai in na shiga kasuwa in sayo mata sarka da yan kunne idan ma naga da halin takalmi in karo, naji kamar in hau rusa mata ihu na dai cije nace mata to kawai, na ajiye wayar.
*
Dole kanwar naki haka na dage na kira Yaya zuwa ranar talata, domin duk ta inda na buga abubuwan babu sauki, babu wata mafita. Na zayyane mishi matsalar da muke ciki da Baba, Yayan yayi shiru yana tunani, kafin daga baya yace zai kira shi sai yayi mishi bayani. Na mishi godiya nace to, na kashe wayar.
Allah ya taimakeni cikin satin aka turo mana kudin scholarship da aka saba bamu. Kuka ne kadai banyi ba ranar saboda murna, dama nayi karaf, bani da ko sisi. Haka kayayyakin da suka rage min duk sun tasamma karewa. Yawanci idan aka turo min ina fadawa Baba, amma wannan karon da yake a wuya nake da kowa, babu wanda yaji labari. Kasuwa kawai na fada.
*
Abu wasa-wasa, tun ana yau azumi, har gashi mun zo mun ci tsakiyar shi. Yaya ya samu ya shawo kan Baba da kyar ya turo min kudin, naje na biya. Allah ya taimakeni basu kai ga rufewa ba. Abubuwa zuwa yanzu sun yi min sauki nesa ba kusa ba, ba kamar satin daya gabata ba. Ban bar wannan abin ya dameni ba ko kuma ya hana ni aikata abubuwana na yau da gobe. Allah ya kan jarabci bawanshi ta kowace irin hanya. Zata iya yiwuwa ta kankanin abu, ko babba, ko iyaye, ko ‘ya’ya, ko cuta, ko kuma sauran abubuwa. Na yarda hakan yana daga cikin jarabawata, don haka ban damu ba sosai. Fatana Allah ya bani ikon cinyeta. Nasan watarana idan da rai, hakan zai zamo tamkar ba ayi ba. Don haka nake godewa Allah a kullum, kuma a koyaushe.
Jiya Yaya Bilal ya tafi Umarah shi da Anty Ameerah. Ba’a tafi da Raheemah ba saboda last year da ita aka je a cewar Janan. Bata ji dadin hakan ba, saboda haka sai da suka dan yi rikici da Yayan akan wai yana gwada mata rashin adalci kafin ya tafi. Bayan tafiyar tashi kuma sai abin ya koma kan Janan, tsangawamar yau daban, ta jibi daban. Wai kicin ma suke rufe mata yanzu, bayan da Yayan zai tafi sai daya cika kicin din ya batse shi da duk kayan amfani. Nace ta kira shi a waya ta gaya mishi mana, tace wai bata son ta dinga tada musu zaune tsaye, nace “ai sai kiyi tayi!”.
Kawai sai ganinta nayi da dubu dai-daya har guda goma, wai inji Yaya inyi sayayyar azumi. Abin ya bani mamaki matuka, na karba nayi godiya. Da yake ma hannuna da kudi, cikin wannan satin wata karamar kwangila da Yaya yayi ta fito, cikin kudin da aka samu ne nima ya dan tsakuro min. Na hada su waje guda na ajiye ban tasar musu haikan ba, nasan a hankali a hankali idan na tattala zasu dade min.
Tunda Yaya Bilal yayi tafiyar nan, kusan kullum anan wajena Janan take shan ruwa. Wasu lokutan ma sai mun gama sallar tarawihi sannan take tafiya gida, idan kuma Allah ya taimaketa Is’haq ya shigo ta nan wajajen, sai ya dauketa su tafi.
Kasancewar ba wani dogon hutu zamu yi ba, yasa na yanke shawarar bin Janan Kaduna kawai inyi sallata acan. Don haka na lallaba Maryam ta karban min kayan sallar da aka bani, atamfa da leshi da takalmi kala daya, ta bayar ta motar haya aka kawo min na kai wajen dinki. Tun dai ana saura kwana biyar muyi tafiyar na kira Baba na fada mishi, yace babu laifi.
Shi dama Yaya da yake ya riga yasan Janan, itama wasu lokutan idan muka samu hutu gajere muna zuwa Gashua da ita. Sannan idan Allah yasa yayo ta wajen Zaria ya biyo mu gaisa, suna haduwa da ita. Ya santa sosai har su Ummahn, saboda haka koda na fada mishi acan zanyi sallah cewa yayi hakan ma yafi, tunda yafi kusa. Shima dubu biyar ya turo min wai in samu karamar atamfa in saya in dinka, na mishi godiya sosai kuwa.
Ranar da muka dauki azumi na ashirin da takwas, ranar muka wuce Kaduna. Sallah ta rage kwana biyu ko daya kenan. Itama Ummah a daren ranar zata dawo, yayin da Yaya Bilal kuma sai washegari.
#F.W.A
*☆⋆19⋆☆*
Ranar sallah muka sha kwalliyarmu, da safe muka bi yaran gidan muka je idi. Jiya da dare bamu kwanta da wuri ba saboda hidimar abincin sallah. Mun yi miyar taushe, aka soya nama, kaji, har da su snacks. Da safe da zamu tafi idi muka bar yan aiki suna soya masa ta farar shinkafa. Don haka muna dawowa aka fara rabon abinci, gida-gida.
Ummah mace ce mai mutane sosai, saboda haka yinin ranar mutane ne yara da manya, yan gida ko yan unguwa, suna ta shigi da fici kamar wata hidimar biki ko suna.
Gidansu Janan babban gidane, Alhaji Salisu Makarfi mahaifinsu Janan babban mutum ne kuma dan dangi, tsohon soja ne amma yanzu yayi ritaya. Kafin ya auri Ummah yana da mata wadda ta mutu ta bar manyan ‘ya’ya maza har su hudu, bayan sunyi aure da Ummah kuma ta haifi Janan, daga baya ne ya sake aurar Usaina babar su Harira da suke kira Yaya. Mutum ne shi na mutane, ya kuma rike zumunci sosai, shi yasa iyalanshi suka taso cike da zumunci da kauna ta yan uwantaka, idan kaje gidan baka banbance dan gida dana waje, baka banbance dan daki da dan daki. Yawancin diyan yan uwanshi a gidan suka girma har suka riski lokacin aure wasu kuma tare da nashi diyan suka yi makaranta wanda shi yake biya musu kudin makarantar. Shi yasa kullum baka raba gidan da mutane.
Samarin gidan da suka taso a gidan, ko bayan da suka yi aure, wasu lokutan idan kaje gidan zaka gansu ko a kofar gida, ko kuma a cikin gidan karkashin daya daga cikin bishiyoyin gidan suna hutawa ko suna hira. Da yake babban gidane, akwai part daban da aka ware wanda mazan gidan suke amfani dashi.
Yau ma haka gidan ya wuni, jama’a ta ko’ina musamman yara jikoki.
Muna dakin Ummah da yammacin ranar, yawanci duk kowa ma a dakinta yake. Ummar yara ma suke ce mata, yayin da suke kiran mahaifinsu Baban yara.
Nayi kwalliya cikin leshin da Baba ya bani, Janan kuma atamfa ta saka. Mu kusan biyar ne a dakin, Ni, Janan, Harira da Firdausi diyan Yaya sai wata Umaimah matar Yayansu Haneef. Danta Shamsu yana kan cinyata yana wasa da motar roba ina taya shi, hirarsu suke yi cikin raha, ni kam rabin hankalina yana ga hirar da suke yi, rabi kuma yana kan tunani akan Muhammad. Yace min zasu shiga can cikin wani kauye a Benin field work tun cikin azumi, yace ba lallai mu dinga samun damar yin waya dashi ba, amma fa yana min text kullum. Nayi tunanin zasu samu su fito daga kauyen tunda yau sallah, amma shiru kake ji. Yau ko albarkacin text din nashi ma ban gani ba. Tun safe nake zuba ido akan wayata, da naji tayi kara sai in zabura in wawureta a tunanina shine, sai inga wani ne daban. Wani lokacin har tsaki nake saki a kule.
Na tura mishi text amma shiru ba reply, idan kuma na kira wayarshi sai inji a kashe. Jikina ya fara sanyi. Nayi kewar mutumin nan, ina kan kewarshi. Sati biyu da muka yi bamu waya dashi, ji nake kamar shekaru biyu ne. Ban san cewa nayi mugun sabo dashi ba sai a wannan lokacin.
Janan ta tabo ni, nayi sauri na kalleta, ban san lokacin da Shamsu ya sauka daga jikina ba, sai yanzu na kula da cewa yana hannun mahaifiyarshi yanzu. Ta kalleni cikin nuna damuwa, da baki ta min alamar tambayar “lafiyarki lau kuwa?”.
Nayi saurin girgiza mata kai, alamun babu komi. Nayi kokarin saka bakina cikin hirar da suke yi akan samarin su Harira muna ta kwasar dariya, amma fa lokaci zuwa lokaci idanuna su kan sauka akan wayata cikin fata.
Ummah ta shigo dakin da sauri, su Yaya Hafiz sune manyan mazan gidan. Shine na farko, suna ce mishi Babba saboda sunan mahaifin Baban Yara gareshi, sai Yaya Auwal, Yaya Haneef da Yaya Kabeer. Janan itace take bi musu, sai Harira, Firdausi da kuma auta Faisal, kanin Janan ne. Shekarunshi sha daya yanzu. Yaje gidan Yaya Hafiz hutunshi na sallah Abuja shi yasa bamu hadu dashi ba.
Karamar walima ce suke hadawa, a lokaci irin wannan, duk suna taruwa a gidan duk da kasancewar suna garuruwa mabanbanta wajen aikinsu duk cikinsu Yaya Haneef ne kadai yake zaune a Kaduna. Ina ga saboda kara karfafa zumuncinsu ne. Ummah ce akan hidimar hada musu abincin da zasu ci, shi yasa tun dazu ta kasa zaune tsaye ita da Yaya, mu kanmu tare damu aka yi aikin abincin da rana, sai bayan mun gama ne sannan muka yi wanka muka shirya.
Tace “wai dama kuna nan a zaune kuka barmu da aiki? Ku taso maza-maza aje a shirya wajen can, har sun fara zuwa”.
Firdausi tace “Ummah ai kece da kin daukar shawara wallahi, sai da Yaya Babba yace za’a dauko wadanda zasu kula da hidimar nan, kika ce a’ah, sai anjima kuma kizo kina ta jajen ciwon kafa da baya!”. Su Janan suka kwashe da dariya, nayi dan murmushi ina girgiza kai.
Ummah ma dariyar tayi, ta wa Firdausi dakuwa, “karbi nan ja’irar yarinya kawai. Da karfina da lafiyata sai in ki hidimtawa diyana? Idan suka dauko yan aiki ni ina zaune, to meye amfanina kenan?”.
Harira tace “ki huta mana Ummah, muma kinga da yanzu ai bamu tashi daga zaman nan ba!”.
Ummah tace “wai zaku taso ko kuma sai na zo na tada ku?”. Babu shiri muka tashi gabadayanmu, muka bar Umaimah a falon.
Can bayan gidan inda aka ware musu kicin dinsu na gargajiya muka wuce tunda acan ake aikin. Akwai makeken kicin daya sha kayan zamani na yayi, amma ya zama na kwalliya kawai. Saboda basu cika amfani dashi ba, idan kaga matan gidan a ciki sai dai idan karamin abu ya kaisu, dafa ruwan zafi ko kuma wani abu dai. Yaran gidan ne ma suke amfani dashi.
Tuni an riga an zuzzuba komi a cikin abinda ya dace, saboda haka muka fara daukar kayan tare da wasu daga cikin yan aikin zuwa sashen maza. Babban falo ne sosai daya saitin manyan kujeru, dinning room shima babba, sai kuma dakuna. A dinning room din muka shirya komi, wasu daga cikinsu suna falo suna hira, wasu kuma suna waje yayin da wasu suke can kofar gida.
Muka shirya komi da zasu bukata, hatta da cokali, drinks da ruwan sha sai da muka ajiye komi sannan muka bar wajen.
A cikin yan hirar falon muka hango Yaya Bilal da Yaya Jameel a zaune, suna ta hirar sports da Yaya Auwal. Yawan zuwa yasa suka saba da yan gidan musamman mazan kasan zumunci irin na maza, shi yasa in ka gansu kamar yan uwa.
Zamu wuce Yaya Jameel ya kira Janan, mu kuma muka yi gaba. Can ta biyo bayanmu da kudin barka da sallah wai inji shi. Yau kam barka da sallah da muka samu daga yan gidan, da baki masu zuwa gidan Allah kadai yasan iyakarta. Ban taba zuwa sallah gidan ba sai wannan karon, shi yasa abubuwan duk suke zuwa min a mamakance.
Daga nan makotan su Ummah muka wuce, kannen Al-Mustafa suka zo muka hadu dasu ana ta cafta da kashe flashes din hotuna, kamar kada yinin ranar ya kare. Bamu samu kanmu ba sai da dare.
Muna falon Yaya da dare, hayaniyar gidan ta ragu kowa ya tafi gida, wasu kuma sun nemi makwanci. An gyara ko’ina ya fito fes, yana ta kamshi.
Janan ta ritsa ni da tambaya akan abinda yake damuna, nace mata babu komi.
Tace “wai karamar yarinya kike son maida ni ne? Tun da safe fa a haka kike, kina da wanda zaki gayawa matsalar ki ne bayan ni?”. Ina shirin bata amsa da wata babu komi din, Firdausi ta shigo falo hannu dauke da babban tray da aka hada fruit salad a ciki. Dama shi muke jira, don haka duk muka sauka kasan carpet din dakin muka zauna.
Shiru babu wanda yayi magana tunda muka fara ci, sai talabijin da take ta faman aiki kawai duk da ba kallon ba muke yi. Firdausi ce ta fara sako hirar, cikin alamun gulma tace “ni fa nayi zaton Anty Ameerah zata tsaya ne anan, ko kuma tazo yau”.
Da yake ta Kaduna suka sauka, sai da suka fara biyowa ta nan a jiyan. Gabadayanmu munyi zaton anan zasu zauna, har Ummah ta fara maganar azo a gyara musu daki, sai kuma suka ce wucewa zasu yi, amma shi Yayan zai dawo yau. Babu wanda ya tambayesu dalili.
Janan tace “lallai ma, wasa kuke yi da Anty Ameerah wallahi. Jiyan ma ganin idon Yaya ne yasa tazo, da ita kadai ce wallahi ko yace tazo ba zata zo ba”.
Firdausi tace “amma dai kinsan tafi Anty Raheemah ko? Na tabbata ko tare suke da Yaya ba lallai tazo nan ba”.
Harira tace “kinsan ai tunda Ummah ta hana aurensu da Yaya Bilal daga farko, take kulle da ita. Amma ni nafi son ta akan Anty Ameerah wallahi, bata da kirki ko kadan!”.
Janan ta gyada kai cikin amincewa, yayin da Firdausi ta jefa mata harara, da yake shekara daya ce a tsakaninsu, kusan kansu tsaya, zasu iya yin sa’a da Maryam. Tace “Lallai ma baki san kirki ba, ke ni fa da mutum ya dinga gwada min mutunci saboda ganin ido, gwanda muyi ta zuba rashin mutunci dashi nasan dama can ba so na yake yi ba!”. Kafin kace me! Muhawarar ta koma kan wanda aka fi so tsakanin matan Yayan. Nan da nan falon ya rikice da hayaniya. Ni kam ina gefe, ina zuba musu dariya idan wata ta fadi abin ban dariya.
Yaya ta shigo falon, muka yi tsit muna kallonta. Tace “idan kuka kuskura daya daga cikin Yayanku yaji wannan magana sai ya bata muku rai. Ina ruwanku da rayuwarsu? Ba tasu bace ba? Kuma kuji da taku mana!”. Ta shige dakin barcinta.
Muka bita da kallo har ta shige, hirar dai ba’a daina ba, dorawa aka yi daga inda aka tsaya sai dai wannan karon cikin yin kasa-kasa da murya.
Firdausi ce mai cewa “ni wallahi wani lokacin har tausayi yake bani, kamata yayi ace zuwa yanzu ya samu yayi settling a waje daya, da matanshi da ‘ya’yanshi. Amma ace kullum yana hanyar Abuja, Kaduna da Zaria? Baya gajiya ne wai?”. Duk maganar da suke yi sai lokacin na gyada kai cikin nuna amincewa, ni kaina ina mishi wannan tunani. Sai dai a ganina, hakan duk shi yaso. Kasan cewa matan nan a karkashinka suke, to meye na zama kana rara-gefe akan tituna kamar wani mara galihu? A ganina idan ya nuna musu karfin ikonshi na mijin da yake aurensu, a sukwane zasu bishi.
Harira tace “ni kaina wallahi ina tausaya mishi, ko meye mafita a rayuwar aurenshi?”.
Janan tace “aure kawai ya kamata yayi. Ya samu wata rikakkiya da tasan sirrin rayuwa ya aura”. Suka fara gyada kai da sauri.
Kofar da aka turo aka shigo yasa muka maida kanmu can. Yaya Bilal da Yaya Jameel suka fado falon, jin mu kake yi munyi kus, kamar ruwa yaci mu. Har suka zauna akan kujerun falon. Yaya Jameel ya kallemu cikin murmushi, “gulmar me ake yi ne?”.
Da sauri muka hau girgiza kai, Firdausi tace “laa, babu komi Yaya. Kawai hira ce muke yi!”. Yaya Jameel ya kwashe da dariya.
Cikin yayun biyu, shine mai fara’a da faram-faram, yafi Yaya Bilal sakin fuska nesa ba kusa ba. A sauran halayya ma suna da banbancinsu, duk da ko a kamanni ma suna da banbanci. Shi Yaya Jameel yafi kama da Ummah da Janan, daka gansu shi da Janan kasan kaga yan’uwa. Shi kuwa Yaya Bilal ina tunanin ko mahaifinsu ya dauko, saboda kamanninsu da Ummah ba wai wani can bane. Sai dai kawai abubuwan da ba’a rasa ba, wanda haduwar jini yake haddasawa.
Duk muka gaida su cikin girmamawa suka amsa. Yaya Bilal ne yace “ina Yaya?”.
Firdausi ta tashi taje ta kirata, tare suka fito da ita, ta samu kujera dan nesa dasu kadan ta zauna. Suka dan zame daga kujerar suka gaida ta, ta amsa cikin fara’a, bayan sun gaisa suka ce mata wucewa Zaria zasu yi yanzu, tace “ba zaku hakura ku kwana ba ku kuwa? Dare ya fara yi, karfe tara fa!”.
Yaya Jameel yace “ai babu komi Yaya, in shaa Allah zamu isa lafiya, nan ne da Zaria fa”.
Tace “to shikenan ai, Allah ya tsare ya kuma kiyaye hanya. Ubangiji Allah ya albarkaci rayuwa data iyali”. Duk suka amsa cike da jin dadi, suka mata sallama suka bar falon muma muna musu Allah kiyaye.
Suna tafiya muma duk muka tashi. Dakin mata muka wuce muka yi shirin kwanciya. Kananan kadajen kwatako guda uku ne a dakin, sai spare din katifa, ita nake shimfidawa ina kwanciya akai. Ni kam ina kwanciya na rufa da bargo har ka a kaina, ina jinsu har lokacin suna tafka mahawararsu naki motsi. Damuwar cikina na ma ta ishe ni. Shirun Muhammad ya tsorata ni, ko dai shima irin na Umar zai min??!.
*
Kwana biyu hidindimun sallah sun riga sun wuce, amma banda gidan su Janan. Har yau wannan gida a cike da iyali yake yini. Yau Assabar, kwana biyar da gama sallah kenan, gobe kuma muke shirin komawa Zaria. Har yau shiru babu labarin Muhammad, nayi text har na rasa abinda zan rubuta tunda wayar bata shiga, ina cikin damuwa. Wani laifi na mishi dana cancanci wannan hukunci haka?
Yau tare muka wuni da iyalan Yaya Hafiz, sai yau suka zo tasu barka da sallah din. Matarshi mace ce mai mutunci da sanin yakamata, haka ma ‘ya’yansu masu shiga rai.
Da yamma da kanta ta saka mu a mota dasu Harira muka shiga kasuwa tayi musu sayayyar komawa makaranta. A makarantar yanmata ta kwana ta FGGC Munjibir suke. Muma sai gamu mun shigo cikin sayayyar. Muna dawowa suka mana sallama suka tafi.
Washegari muma muka yi sallama da su Ummah, suma su Firdausi da safe aka tafi aka kaisu tasu makarantar. Mun fito daga dakin Baban Yara, mutum mai tsananin mutunci da kirki, yana ta mana addu’o’i da fatan alkhairi, muka samu su Ummah a falo. Tuni an fitar mana da kayanmu waje, nan muka musu sallama, har waje suka raka mu suma. Direban da zai kaimu yana tsaye a jikin motar gidan, yana ganin fitowarmu ya shiga ya tayar. Muka sake sallama dasu Ummah muka shige motar, direba ya ja muka fita daga gidan muka dau hanyar Zaria.
*☆⋆20⋆☆*
Tun da asubahi naji wayata tana kara babu kakkautawa, washegarin ranar da muka dawo kenan wadda ta kama litinin. Ko a cikin nisan duniyar mafarki, nasan kalar ringtone din, na kuma san ko waye mai kiran tun ma kafin in duba. Saboda haka duk da a cikin magagin barci nake, ban kasa rarumar wayata ba na latsa tare da kaita saitin kunnena na fara watsowa Muhammad tambayoyin da suka jima suna susar bangon zuciyata:
“Muhammad! Lafiya dai ko? Kayi rashin lafiya ne? Accident kuka yi a hanyarku ta dawowa daga Benin? Ko kuma wayarka aka sace maka ko ta lalace? Kayi welcome back ne? Ko kuma ka fara mantawa da ni ne?… Muhammad?!”. Na saurara da tambayoyin da nake jera mishi sakamakon jin shiru da nayi ta daya bangaren da yake.
Sai daya ji na saurara sannan naji ya saki murmushi mai sauti, yace “naji dadi da kika damu dani har haka baby na… Sannan na farko babu abinda ya sameni, waya ta bata lalace ba, sannan lafiyata kalau kamar dai yadda kike ji na!”.
Na hade fuska tamkar ina gabanshi, “shine kuma sati biyu cur ka dauke min wuta babu wani bayani. Kana ganin jerin texts din dana dinga turo maka a cikin wadannan kwanakin kuwa?”.
Yayi shiru kamar ba zai yi magana ba, can kuma yace “kiyi hakuri, ina da dalili!”.
Duk wani haushi da takaicin dana dinga tarawa ina makalewa a cikin raina na kwanaki masu dama sai suka zo suka tarar min a lokaci guda. Cikin tafasar zuciya nace “kana da dalili? Wane dalili?”. Yayi shiru. Nan na sake zuwa wuya, nace “kada ka ma damu da yi min wani bayani, na gane. Wato ka gaji kana neman hanyar da zaka bullo ka rabu dani ko? To menene na wani boye-boye da kashe waya? Ka fito kayi rayuwarka yadda kake so, ka fada min cewa ka gama dani, ba damuwa zanyi ba, ba kuma binka zan dinga yi ba, bai kamata ka wahalar min da zuciya ba. Kasan iyaka damuwar dana shiga a cikin yan satikan nan kuwa? Kodayaushe tunanina ya ta’allaka a kanka, gani nake kamar wani mummunan abu ne ya faru da kai, gani nake kamar zan rasa ka har abada! Shine yanzu har kake da bakin dagawa ka fada min wai lafiyarka lau?!”. Na karasa fada cikin dan karajin bacin rai, ban damu da cewa duku-dukun safiya bane, zan iya tashin sauran yan dakinmu. Bacin da raina yayi a lokacin ba karami bane.
Yace “baby…!”, muryarshi na nuna tsantsar nadama da damuwa, har sai dana kusa bude baki a take a lokacin ince mishi koma menene na yafe, amma na cije bakina. Nayi shiru ina jira inji abinda zai ce, amma shiru, daga wannan kalma bai sake maimaita wata ba. Kusan sakanni talatin tsakanin ni da shi babu wanda yake furta uffan, don haka nayi kwafa, nace “tunda haka ne sai anjima idan ka samu bakin magana sai ka kira ni!”. Na kashe wayar nayi jifa da ita can karshen katifata na mike zaune. Tashi nayi na fita naje na dauro alwala, na dawo daki na samu wayata na kara, na duba naga shine kawai na kashe karan wayar na tada sallah ta.
Koda na gama ina ganin yadda take ta haske tana mutuwa alamun ba’a hakura da kiran ba, don haka na tashi na dauki wayar tare da fita waje na amsa saboda kada in damu yan dakin. Na dauka nayi shiru kawai ina sauraron abinda zai ce.
Yace “baby please ki saurareni. Na rantse ba da gangan nayi hakan ba, ba kuma da son raina bane, please!”.
Duk da yadda magiyar ta shige ni, amma sai na dake nace “ina jinka ai”, cikin basarwa.
Yace “ina son ki Na’ilah, fiye da tunaninki wallahi!”.
Maganar tazo min a bazata, don haka na rasa abinda zan ce mishi, jin nayi shiru yasa ya cigaba da maganar shi.
“Tsorata nayi. Ina so in zo in ganki, ina so in bayyana miki ko ni wanene. Sanin cewa muna soyayya dake kuma har mun aminta da juna, amma kuma baki san ko ni din ainihin wanene ba, yana damuna sosai fiye da tunaninki. Saboda haka na fara tunanin sanar dake ko ni wanene, sai dai tsoron in fada mikin nake yi. Baby, ba zan juri kiyi rejecting dina ba don ba zan iya daukar hakan ba. Wadannan tunanika su ne dalilan da yasa na kashe wayata, saboda ina so in lalubar mana mafita daga ni har ke, wadda zata zaunar damu karkashin inuwar aure, ta kuma zaunar mana da soyayyarmu ni da ke”.
Na ajiye wani dogon numfashi, tuni naji zuciyata tayi sanyi, ta kuma yi haske kamar ya sanya soso da sabulu ya wanketa tas! Nace “haba dai, akan wannan ne dama ka tashi hankalinka nima ka tada min nawa?”.
Yace “ba zaki gane bane Baby”.
Nace “kaine dai ka kasa ganewa, kana da wata nakasa ne? Ko kuma kana tunanin baka da kyau ne, don nima ai ba kyawun gareni ba. Rashin aikin yi ne?”. Duk ya amsa min da a’ah, ya kara da cewa, “matsalar ta wuce inda kike tunani, ni dai fatana a duk yanayin dana bayyana a gareki, ki karbeni don Allah!”.
Nace “ni ai na riga dana gama karbarka, wace irin karba kuma kake so inyi maka ne?”.
Yace “dari bisa dari nake so ki karbeni!”.
Nace “tuni ka samu wannan karbuwar, believe me!”.
Yace “zamu gani ne dai, amma yanzu naga lokacin fita zai kure miki kada ki makara. Zan kira ki anjima. I love you!”.
Nayi murmushi a dan kunyace nace mishi “you too!”, na kashe wayar da sauri ina dan murmushi. Sai lokacin na kula da yadda garin yayi haske alamun gari ya waye sosai. Allah yasa ina azumi, don haka ban tsaya wani kokarin hada abin kari ba kawai nayi abinda ya kamata na fita da sauri.
*
Wannan karon muna bangaren yara ne. Tunda muka je wani likita, Dr. Habib Na Abba ya sanya min ido kamar yaga wata danyar nama, bibiyata yake tun karfinshi tun cikin azumi. Yanzu ma muna tsaye ni da Janan muna rubutu a register, Janan din ta tabo ni. Na dan daga kai distractedly na kalleta, tace “likitan can fa tunda ya shigo idanuwanshi suna kanki”.
Na daga idanuna a hankali na dubi inda take yi min nuni, aikuwa muka hada ido dashi, na janye nawa da sauri na maida kan littafin gabana ina jan dan siririn tsaki, “na tsani yawan kallo wallahi, haka kawai ka wani saka ni a gaba kana kallo kamar ka samu wata talabijin? mtsww!”, na sake jan wani tsakin.
Tayi yar dariya, “hala har yanzu baku shirya da Muhammadun naki bane? Na jiki yau gabadayanki a wuya kike, kamar wadda take jira a tabota, sai ki hau fada”. Na jefa mata harara ina shirin maida mata amsa daidai da ita, sai naga Dr. Na Abba yana tunkararmu, don haka muka kama baki muka bame kar yaji muna magana a kanshi, har yazo ya tsaya a inda muke muka gaida shi.
Ya ja tunga ya tsaya yana watsawa Janan tambayoyi game da aiki da kuma ward din, duk wannan abin da ake yi idanunshi suna kaina amma. Ji nayi gabadaya na takura, na tsani kallo. Gashi shi kuma yazo ya mana wani kememe bashi da alamun motsawa ma. Don haka na ajiye littafi da biron da nake rubutu dasu, na kalli Janan nace mata “bari in dan fita”, na juya zan bar wajen.
Maganar da yayi ce ta dakatar dani, “haba sister, daga zuwana kuma sai ki tafi sai kace ina korarki? Idan dai saboda nine, yi hakuri ki dawo ki zauna, sai in tafi”.
Na juya ina kallonshi cikin dan murmushin da bai wuce fatar baki ba, nace “ba don kai bane likita, kawai naji ina son fita in dan shaki iska ne”.
Yace “to idan haka ne, muje in raka ki shan iskan mana? Nima wajen na nufa yanzu ai”.
Nace mishi “babu komi likita!”.
Na zagaya kusa dashi muka jera muka fara tafiya. Muna ba Janan baya ya juyo ya kalleni, “to ya sunan malamar?”.
Nace “Na’ilah!”.
Ya maimaita sunan, “Na’ilah! So unique, I like it!”. Nace mishi “nagode”.
Muka cigaba da tafiya yana min kananun hirarraki har muka fita wajen, muka cinye karshen ginin. Ko dai ya fita, ko kuma ya hau sama ko kuma ya koma inda muka fito. Ya tsaya ya ja tunga tare da juyowa ya kalleni hannuwa cikin aljihun fara kal din rigar labcoat daya saka tana ta sheki a cikin ranar da muka tsaya a ciki, ya juyo muna fuskantar juna dashi.
Yace “ni fa son malamar nake, ya za ayi ne?”.
Banyi mamaki ba, don dama nasan ko ba dade ko ba jima sai ya fadi hakan, nace “ni kuma?”.
Ya langwabar da kai gefe, “yanzu duk alamomin da nayi ta jefo miki, kina so kice min baki taba kula ba?”.
Na girgiza kai ina kallonshi, “ko kadan, ta yaya kake so in kula da hakan? I mean, ba tambari bane a goshinka da idan na ganka zan ga hakan kai tsaye ba”.
Ya kyalkyale da dariya, “I like you, kina da ban dariya gaskiya. Ga murmushinki mai kyau”. Na dan saki murmushi kawai.
Yace “nasan ke ba karamar yarinya bace, kin fahimceni tunda ba tun yau kike a cikin ward dinnan ba, amma tunda haka kika ce, zan bi ta hanyoyin daya kamata tuntuni, ko zan iya samun lambar malamar?”.
Na dan girgiza kai ina murmushi, mutumin nan is very charming, da dai ace wani Muhammad bai sace min zuciya ba. Nace “ni fa kayi hakuri likita, an riga anyi mun miji a gida”.
Ya kalleni tun daga sama har kasa yana wani murmushi, “ke din?”. Na gyada mishi kai.
Yace “well then, na makara kenan. Amma shi mutum ai baya cire rai daga rahamar Allah, don haka ba zan saddakar ba tun yanzu…”, ya ciro dan katinshi daga cikin aljihunshi ya miko min, nasa hannu na karba, ya cigaba da magana, “ina fata zamu cigaba da gaisawa haka nan, don maganar gaskiya kina burgeni sosai. Ina fata zaki taimaka min da lambar wayarki?”. Wannan babu musu na karbi wayarshi na zuba mishi lambobina, ya karba yayi saving. Ya dago ya kalleni da dan siririn murmushi akan siraran fatar lebenshi, “sai kin ji daga gareni dear, thank you”, ya kanne ido daya tare da juyawa abinshi ya tafi. Na bishi da kallo, yar karamar dariya na subuce min, na girgiza kai kawai.
Ban yi cikakken minti biyar ba na juya na koma, Janan ta kalleni tana wani murmushi tunda na shiga har na je kusa da ita, na ja kujera na zauna ina kallonta a daddage. Tace “meye kike wani hade fuska? Tambaya ce sai na miki ita, you and the doc?”.
Na kwantar da kaina akan benci, “ni fa babu abinda yake tsakaninmu, ke da kika san komi, ina zan kai Muhammadu na kuma?”.
Tayi murmushi, “ke da Muhammadun nan naki, Allah dai ya mana zabi nagari. Zaki shiga makaranta gobe, ko kuma zaki raka ni ne?”.
Nace “zan raka ki dai kawai, ka samu dan hutu daga wannan wahalar”. Ta kwashe da dariya, “daga dawowa har kin gaji?”.
Na maida kaina na kwantar kawai.
*
Wajen karfe goma muka shiga cikin makaranta washegari bayan mun dauko excuse, da yake akwai sauran abokanmu dake cikin hostels din makarantar, Janan ta wuce department wajen supervisor dinta, ni kuma na shiga cikin makaranta da niyar idan ta gama dashi zata kira ni sai mu hadu da ita a gate mu koma asibitin. Ni sai gobe zan ga nawa supervisor din.
Dakin wata kawata Fatima da muka yi mutunci da ita naje sai aka ce min ai tana sick bay ma bata da lafiya, don haka na karkata na tafi wajenta. Na dan jima a wajenta muna hira da yake jikin nata da sauki, har ma ana za’a sallameta anjima. Janan ta kira ni tace min ta gama yanzu zata fito daga department, don haka na yiwa Fatima sallama da fatan karin sauki, na fita.
A daidai bakin gate naga Yaya Jameel sun shigo shi da Anty Sarah, abin ya bani mamaki da naga ciki a jikinta, dama ciki gareta? Suka wuce ni a mota ni kuma na wuce na fita. Sai dana ganta ne ma sannan na tuno cikin Sailuba itama, nasan cikinta ya tsufa yanzu, haihuwa ko yau ko gobe.
Akan hanya na kirata nake tambayarta, tace ai tana ma cikin asibiti, suna expecting din baby nan da sati daya. Nan muka yi sallama da ita muka kashe wayar.
A bakin gate muka hadu da Janan, muka jera muka fita daga cikin makarantar. Cikin asibiti zamu koma gabadayanmu. Nace mata “baki fada min Anty Sarah tana da ciki ba”.
Tace “a ina kika gansu ne? Ashe baki kula da cikinta ba, kodayake last zuwan da kika yi baki ganta ba sosai, amma naji suna cewa ya jima ai”.
Nace “a sick bay na gansu, naga ma kamar irin dadadden nan”.
Tace “kinsan dogayen mutane dama, yanzu haka idan ba ido kika sanya mata ba, ba lallai ki gane tana dauke da ciki ba”.
Na gyada kai, nace “haka ne, Allah ya raba lafiya”. Tace “ameen”.
Muka samu bus muka hau, tunda muka hau babu wanda yayi magana a cikinmu, da alamu kowa da tunanin da yake damunshi. Ni yawanci akan yadda zan karke rayuwata a gida ne idan na koma kafin inga yadda Allah zai yi dani, ko mai zai faru? Ita kuma Janan ban sani ba, har muka sauka daga bus din dai muka shiga cikin asibitin. Sai da muka fara tunkarar ginin asibitin sannan ta kalleni, murya cike da damuwa tace “ko yaushe matan Yaya Bilal zasu haihu ne?”.
Nace mata “ita haihuwa ai ta Allah ce, idan ya nufa sai kiga an sameta ba zato babu tsammani”.
Tace “haka ne, amma ina tausaya mishi wallahi. Shekaru suna ja suna kara wucewa, yakamata ace kamar yanzu dai ya fara ajiye nashi iyalin, kowa a cikin dangi ma abinda yake fada kenan”.
Nayi shiru ina jinta, ni kaina wasu lokutan ina wannan tunanika, sai dai mafiya yawanci ban san akan wani tunani zan tsaya ba. Tsakanin Yaya da matanshi ban san waye bai haihuwa ba zata kuma iya yiwuwa wata kaddara ce daga Allah. Don haka na dafa kafadarta, nace “kada ki damu, in Allah ya yarda Allah zai kawo masu albarka”.
Tace “Allah ya yarda”. Muka cigaba da tafiya ba tare da mun sake yin magana ba har muka shige cikin ward din.
Ko bayan da muka tashi dakina muka wuce da ita, na mana danwake da yake Janan tana matukar son shi, ina cikin yin danwaken ita kuma tana gefe tana yanka mana cocumber, tumatiri da dafaffen kwai Esther kuma tana gefenmu tana taya mu hira, har na gama muka zauna muka fara ci bayan mun zambada yaji kamar na kamun mayu. Bayan mun gama ci muka sauka kasa ni da ita muka wanke kayan muka dauro alwala daga can muka dawo daki muka yi sallah. Tana sallame sallah wayarta ta dauki ruri kamar dama jiranta ake yi, ta daga wayar tayi murmushi tare da nuno min, sunan Yaya Bilal ne yake ta tsalle akan screen din wayar, na taya ta murmushi cike da mugunta.
Ta daga wayar a ladabce tana wani yin kasa-kasa da kai da kuma murya, hakuri kawai naji tana badawa, daga karshe dai ta kashe wayar tare da mikewa tsaye, ko babu tambaya nasan tafiya zata yi don haka nima na dauki hijabina na saka na bita a baya. Kamar kullum, sai dana rakata ta hau bus sannan na juyo na dawo hostel.
Ina dawowa sallah nayi na, dana gama na koma kan katifa na zauna tare da dauko littafaina ina kara reviewing takardun da zan kaiwa supervisor dina gobe, dana gama kuma na dauko textbooks ina kara karatun exams din da zamu yi sati mai zuwa. Har wajen karfe goma tayi Muhammad ya kira ni, na hada kan littafan na ajiye na amshi wayar.
*
Washegari sai da rana Mr. Akafyi ya min waya akan inje in sameshi, don haka na tafi makaranta. Bayan ya dudduba takarduna da sauran gyare-gyaren da zai min, yace inje inyi printing din wata chapter, na sauka kasa da sauri nayi, ina tsaye mutumin yayi da yake babu yawa kuma babu layin mutane, ya gama na biyashi na koma na kai mishi. Abin haushi da takaici, ina kai mishi yace ai ba wannan chapter din yace ba, wata ce daban, meaning na bata lokacina da kudina a banza. Tun farko kuma shi yace ba sai na dinga printing ba, kawai in dinga rubutawa ina kai mishi, gashi yanzu yana kokarin janyo min ciwon kai ta dalilin haka.
Nan na sake sauka kasa na bashi takardun, kusan zaman awa daya nayi a wajen yana aikin typing, ya gama ya miko min. Ina komawa ofishin mutumin aka ce ai har ya tashi, wani dan banzan makoko da kududu ya tsaye min a makoshi, naji kamar in kurma ihu. Takardun kawai na tura mishi ta karkashin kofar ofishin na tura mishi text akan na ajiye su, na tafi. Na kula mutumin da alamu sai na biyo mishi ta bayan gida sannan zamu rabu lafiya dashi.
Ina fita daga cikin department din naji ana kiran sallar la’asar, don haka na tsaya a masallaci nayi sallah sannan na wuce. A bakin gate na tsaya na sayi yoghurt mai sanyi, da niyar dana koma asibiti kafin in shiga ciki zan tsaya in sha saboda tun dazu cikina yake kiran ciroma, dama ban wani ci abin kirki ba yau da safe. Bayan na biya kudin an saka min a leda, na karbi canjin da suka rage min na maida cikin purse dita. Typing din da Mr. Akafyi ya saka ni sun cinye min kudi, nasan sai na sake zama na tsara yadda zan tafiyar dasu kafin in kashe su ban tantance ba.
Na daga kafa da niyar tafiya kenan, naji karan horn a bayana. Banyi tunanin da ni ake ba daga farko, don haka na daga kafa na fara tafiya. Sai naji an sake a karo na biyu, an kuma kara, na dan juya gefen inda naji karan a kaikaice, gabana naji yayi wata irin faduwa lokacin da muka hada ido da Yaya Bilal. Na kalli gefena domin in tabbatar da cewa ni yake yiwa horn, da dai naga alamun da ni yake, don gashi nan har yanzu ni yake kallo, sai na daga kafa a hankali na tsallaka ta inda ya tsayar da motarshi a bakin titi.
Kofar gidan gaba ya bude min, don haka na silala na shiga a hankali kamar wata mai takatsan-tsan. Nace “Yaya ina yini?”.
Yana kokarin tayar da motar ya amsa da, “lafiya lau, daga ina haka?”.
Nace “naje ganin supervisor dina ne, amma cikin asibiti zan koma yanzu”.
Ya gyada kai tana humming, amma bai sake cewa komi ba, kawai motar naga ya ja ya abinshi.
Kamar yadda na kula da motar shi baka rabata da tattausan kida ko karatu, yau ma tattausar kidan wakar mawaki ‘Zayn Malik_Let Me’ ce take tashi. Ina son wakokin mutumin sosai. Na kwantar da kaina akan gilashin murfin motar, kamshin turaren Polo na RL da kamshin fresh strawberries na turara mota da kuma sanyin ac dake tashi a cikin motar, yasa na lumshe idanuna. Wata irin natsuwa dana rasa daga ina take naji tana shigata, naji kamar ana zare min duk wata gajiyar dake jikina. Ban san lokacin da barci ya fara daukata ba.
Sai da wani irin awkard feeling ya dameni a bayan kaina sannan, irin wannan feeling din da zaka ji idanu a kanka, kallo kuma na kurilla. Na tuna wata rana lokacin daya daukoni daga gidanshi, irin wadannan abubuwan na dinga ji har na dinga tunanin ko kuma kawai ina imagining hakan ne.
A hankali na saci kallon inda yake, karaf sai muka hada ido. Yayi saurin janye idanunshi daga kaina ya maida kan titi, sai dai ba’a jima ba muka sake hada wani idon dai.
Wannan karon ni na janye nawa idanun da sauri, na maida su na rufe, ban sake dagowa ba.
Tafiya da Yaya Bilal a rufi daya na mota ba yau muka fara yinshi ba, tun muna SBRS ya sha zuwa ya daukemu muje muyi hutun karshen mako a Kaduna, haka ma bayan mun dawo Zaria. Duk da cewa yawanci tare da Janan muke yin tafiyar, amma akwai daidaikun lokuta da yake rago min hanya daga gidanshi. Amma hakan bata taba faruwa ba, idan ma ta taba ko kuma tana faruwan, ni ban taba kula ba sai a dan wadannan lokuta. Shirun cikin motar yayi yawa, kidan ma ya tsaya cak kamar da can babu shi, it was unsettling.
Cikin sa’a muka karasa asibiti cikin dan kankanin lokaci, da kwatance na kwatanta mishi inda muke, yana gyara parking din motar na fita a sukwane kamar wadda ake mintsila, sai dana maida murfin motar na rufe sannan na leka ta saitin motar ina zuba mishi godiya. Ko jira inji ko ya amsa ko bai amsa banyi ba, na kara gaba kamar zan tashi akan iska saboda sauri.
Na rasa dalilin da yasa Yaya ya kirkiro da wasu irin halaye da bai saba ba sam cikin wadannan kwanakin. Koma dai menene, ni dai ina fata Allah Yasa lafiya.
*
Ranar Juma’ah, har na kwanta da dare kiran wayar Muhammad ya tashe ni, donhaka na daga wayar cikin barcin daya fara daukata, mun kwaso gajiya a asibiti yau.
Maganar daya fara min bayan mun gaisa ne tasa na bude idanuwana sosai, yace “are you ready baby?”.
Nace “ready for what?”.
Yace “ganina mana baby!! Kin shirya gani na gobe?”.
Na tashi zaune sosai akan katifata, nace “da gaske?! Don Allah kada kace min wasa kake yi!”.
Yace “kin san babu irin wannan wasan a tsakaninmu baby, da gaske nake. Kin shiryawa gani na gobe?”.
Na hau gyada kaina da sauri kamar ina gabanshi, “oh God yes, I’m hella ready!!”.
Ya saki yar dariya mai sauti, “yayi kyau. One thing though, ina neman alfarmar kiyi min fahimta mai kyau, ki kuma fahimci kyakkyawar manufata a gareki. Don Allah idan na bayyana miki kaina Na’ilah, kada ki guje ni!”.
Tunda muke dashi yau ne karo na farko da naji ainihin sunana ya fita daga fatar bakinshi, naji jikina yayi sanyi, nasan he’s serious. Nace “in shaa Allah Muhammad, zan yi iyaka kokarina”.
Yace “good, and no matter what kada ki manta cewa ina son ki Baby”.
Sai kuma naji gabana yana duka sosai, maganganunshi suke nema su tayar min da hankali, nace “wani abu yana faruwa ne Muhammad? Kana tsorata ni!”.
Yace “babu abinda ya faru baby, ki kuma kwantar da hankalinki. Am sorry idan yanayin halayena suna tsorata ki, I couldn’t help myself”.
Sai muka yi shiru, kamar wasu wadanda aka wa rasuwa, can kuma sai yayi gyaran murya, yace “don’t mind me fa, insecurities ne irin nawa, amma babu komi we are safe. Saboda haka ki koma barcinki yadda zaki tashi da wuri kin shirya delicacies na tara na, tuwo za’a dafa min ne ko kuma shinkafa?!”.
Nan da nan na warware, muka fara magana akan abinda ya dace in tanadar mishi. Sai daya tabbatar da cewa na ware, sannan ya min sallama, bakinshi yana kara nanata min kalamomin so da kauna.
Muna gama wayar na koma na kwanta tare da janyo filo na rungume a kirjina, zuciyata cike da farinciki mara misaltuwa. Gobe zan ga Muhammadu na!!.
*☆⋆21⋆☆*
Daren ranar nayi barcin da ban taba yin irinsa ba koda wasa, cike da mafarkai masu dadi wasu kuma very weird.
Abu na farko daya fara fado min a cikin raina lokacin dana farka daga barcin daya daukeni bayan nayi sallar asubahi shine, ‘what a ridiculous dream!’, wani irin mafarki dana rasa gane kanshi balle gindinshi. A ganina meye hadin biri da kaska?! Na yakitar da wannan mafarki domin kwata-kwata bai ma yi kama da abinda zan kasa a cikin raina ya dameni a banza a wofi ba.
Tunda na tashi da safe na rasa inda zanyi da raina saboda murna da jindadi. I practically glowed all day. Tun da safe na gama duk wasu abubuwa daya kamata inyi, nayi wankin kayan uniform dina, bayan sun bushe na goge su na ajiye, sannan na kara gyara kayana.
Munyi dashi akan sai yammaci likis sannan zai zo, ban san abinda yakamata in mishi ba wanda zai ci ba, don haka bayan na gama wanki na hada meat pie wanda nayi filling da minced meat har da su carrots da dankalin turawa. Na hada mishi zobo hadadde saboda in dai harkar hada drinks ne musamman na gargajiya, ni kaina nasan cewa na iya sosai. Mawuyaci ne wanda ya sha ya kushe. Bayan nan na sayo lemun exotic na abarba da kwakwa da ruwan cikin gora, na kaishi dakin wata yar ajinmu da take da firjin na roketa ta ajiye min zuwa anjima da yamma yadda zai yi sanyi, tace babu damuwa.
Gabadaya na kasa zaune na kasa tsaye, motsi kadan na lalubo waya, ko in duba lokaci ko kuma in turawa Muhammad text. Ji nake kamar in janyo yinin ranar saboda nisan da naga yayi min.
Karfe hudu na yammacin ranar, ina zaune a gefen kujerata ina nade gashin kaina. Jiya na warware kalbar kalbar sallah da Janan ta min, na je saloon na wanke shi. Yanzu dana taje shi sai ya zubo har gadon bayana, yana ta sheki da tashin kamshin shampoo. Da yake ban cika son nuna gashi a waje ba, sai nake nade kayana in saka cikin dakwali ko hula.
Wata bugaggiyar doguwar rigar atamfa ce na saka, irin dinkin yan Senegale dinnan ne. Atamfar kanta yar can ce, wata tafiya da Yaya Mudatthir yayi zuwa can gudanar da wani aiki, ya kawo min ita a dinkenta. Sau daya kacal na taba sakata. Dinkin zanen single ne, rigar kuma kamar half buba dinnan ce, data tsaya min a gwiwa, dankwalin mai fadi ne sosai, na kashe daurin Zara Buhari a kan nawa. Dana tsayawa karewa kaina kallo a madubi, ni kaina sai dana burge kaina. Allah ya azurtani da baiwar wani irin tattausan kyawu, irin kyawun nan da ba’a gani kai tsaye, sai a hankali a hankali yake fita. Wai a hakan ma don ba wata kwalliyar kirki nayi ba, hoda kawai na shafa tare da murza kwalli a idanuna, nayi amfani da brush na taje gashin girata, daga shi ban kara komi ba.
Abinda Esther ta dinga yiwa korafi kenan, tace in zo ta min kwalliya ko da simple one ce, “bai kamata ki je wa saurayin da zaku hadu dashi yau a karo na farko haka ba, ba kya tsoron yaji baya yi dake?”.
Na rolling idanu sama tare da jefa mata baki, nace “a haka nake so ya ganni ya kuma so ni, ni fa ba rokon ya so ni nake yi ba. Sannan ke kina ganin nayi miki kama da wadanda maza zasu kalla suji basa so ne?”.
Ta girgiza kai tana murmushi, “ba karya abokiyar, kinyi fa! Ai karya ne wani da namiji ya kalleki yace baki yi ba, ko matan ma tankawa suke yi balle kuma maza. Abinda kawai nake so ki sani shine, ku hausawa da kanku ne kuka ce idan kana kyau ka kara da wanka. Kinga duk da kina da kyanki tubarkallah son kowa kin wanda ya rasa, ina ga da kin dan kara koda mascara ne da eyeshadow yadda zaki kara fitowa sosai, ki kara rikita shi, kin gane ai”.
Ni duk bayanan da take watsawa sauraronta kawai nake yi ba wai don ina fahimtarta ba, duk wucewar dakika daya, fargabar dake cikin zuciyata karuwa take yi. Nerves sun cika min ciki.
Nace mata “ni duk ban damu da irin wadannan abubuwan ba, fatana kawai ya karbeni a yadda nake. Zan fi son ya ganni a ainihin wacece ni, ba wai kyale-kyalin banza ba”.
Tace “kinyi yar gaskiya kuma”. Ni dai na kauda kaina gefe kawai don bana jin zan iya tsayawa yin doguwar hira a halin da nake ciki yanzu.
Karfe biyar da rabi daidai, sai ga kiran wayarshi. Hannuwana har rawa suke yi lokacin dana dauki wayar na karata a saitin kunnena. Nace “hello?”, da kyar kamar wadda take koyon magana.
Yace “yanzu na karaso kofar hostel din, ina daga waje ina jiranki”, cikin wani irin husky voice, deep and soothing a lokaci guda. Sai naji kamar yau na taba jin muryar. Naji wata irin rawar cikin jiki ta ziyarceni, kamar na fito waje cikin muku-mukun sanyinnan, na kakaro sautin “to”, daga can kasan makoshi na kamar an shake ni. Na kashe wayar na ajiye a gefena ina maida numfashi da sauri da sauri kamar wadda tayi gudun ceton rai.
Sai dana tabbatar da natsuwata ta dawo cikin jikina, sannan na tashi tsaye, duk da haka sai da naji kamar zan kifa saboda yadda kafafuna suke rawa. Wani tray dana amsa wajen Esther, mai fadi ne ba laifi, da zanen manyan jajayen furanni a jiki. A cikin jug dinshi na zuba zobon da nayi, na yanka cucumber da kankana kanana a ciki bayan na cire ‘ya’yan, su kuma kananun cups din jug din na kifa guda biyu akan tray din.
Na shirya meat pie din akan wani karamin plate, na kawo foil paper na rufe shi. Na dora lemun dana amso da ruwan akan tray din, aka yi sa’a ya kwashe duka.
Na kara duba fuskata a cikin madubi naga lafiya lau, na dauki gyale mai dan fadi nayi yafawar zamani, na kawo turaren fantasy na kara badawa a jikina. Duk wadannan abubuwa da nake yi, cikin takatsan-tsan da rawar jiki nake yinsu. Na dauki takalmi mai dan tudu baki na saka, sannan na dauki tray din wannan da wayata na fita.
Akwai wani karamin waje daga can gefen hostel din, yawanci dalibai kanyi karatu a ciki musamman irin group assignment da aka hada maza da mata a ciki, nan suke zuwa suyi karatun. Ko kuma idan wata daliba tayi baki nan take zuwa dasu idan maza ne. Nima can na fito da rana na samu wata yar kwana, inda babu yawan giccin mutane sosai na share na kuma goge kujerun da aka kera na sumunti a wajen da niyar nan zan jagoranci Muhammad din idan yazo.
Lokacin dana fito waje ban ga kowa ba, da alamu a can wajen gate ya tsaya, don haka na fara kai kayan hannuna wajen da zamu zauna na ajiye su, sannan na taka a hankali zuwa wajen gate din. Idan wani ya kalleni a lokacin, nasan babu bata lokaci zai ce tafiyar yanga ce nake yi, sai dai a zahirin gaskiya, tsananin fargaba da tsoro ne suka sa nake tafiya kamar wadda take jan kafarta. Ban san dalilin wannan sudden tsoro da naji ya dirar min ba, amma nafi danganta hakan da cewa kila saboda kawai haduwarmu ta farko kenan yau.
Na fita daga gate din, idanuwana suka fara karade ilahirin wajen da kallo, ina duba gefena na dama, na hango shi. Jingine da motar rav4 baka kirin, sanye yake da wata jikakkiyyar danyar shaddar getzner ruwan kasa mai haske, ta sha dinkin surfani na zare shima ruwan kasa amma mai duhu sosai, takalmin kafarshi shima ruwan kasar ne irin flats dinnan na maza, ko ba’a fada maka ba kasan ba karamin kudi da daraja zasu yi ba. Daga inda nake, babu abinda zan iya karaswa game da features dinshi, kawai dai nasan dogo ne, ya danyi min nisa, ban hangi komi a fuskarshi ba, musamman da yake a daidai wannan lokacin ya nutsa wayar tashi cikin wayar hannunshi. Sai hular kanshi kawai.
Na samu kaina da takawa a hankali zuwa inda yake, kaina a kasa ban iya dagowa na kalleshi ba saboda wani irin nauyinshi da naji ya dirar min, amma duk da kan nawa a kasa yake, ina jin zafin kallonshi a cikin jikina. Sai dana fara ganin kyawawan jerin dogaye kuma zara-zaran yatsun kafarshi da suka yi matukar kyawu cikin kyakkyawan takalmin kafarshi, sannan na iya daga kaina a hankali.
‘Assalamu Alaik…”, sallamar da nayi niyar yi mishi, ta makale a makoshina lokacin da na dago kai a lokacin, muka hada idanu hur-hudu dashi.
Fuskarshi bata nuna mamaki, al’ajabi ko rikicewar tunani kamar yadda na tabbatar suna zane akan fuskata ba baro-baro. A tsaye take kyam, maimakon hakan ma, sai wani tattausan murmushi daya bayyana akan fatar bakinshi.
Yace “wa alaikumussalam wa rahmatullah… Har kin fito?”.
Na tsinci kaina da karkata kaina gefe guda cikin tsananin mamaki, can kasan zuciyata kuma ina maimaita kalmar ‘har kin fito?’, ko me yake nufi da hakan?.
Na dan duka cike da girmamawa nace “Yaya Bilal ina yini?”. Gabadayan idanunshi fuskata suke karewa kaina kallo kamar yau ya taba ganina, yace “lafiya lau Na’ilah! Ya kike?”.
Na gyada kai kawai, zuciyata cike da tambayoyi, yayin da a gefe guda kuma naci gaba da dube-dube ko zan hango Muhammad. Ya nake ganin kamar mu kadai ne a gaban hostel din? Ko kuma bai zo ba yace min yazo?.
Na furta tambayar da take ta ci min rai tunda naci karo da Yaya ne, nace “ko kazo wajen wata ne anan ko wani?”, a raina nace ko dai wani auren yake nema ne? Na danyi shivering lokacin da tunanin abinda hakan yake nufi ya darsu a cikin raina.
Ya cigaba da jefa min irin wannan kallo da tunda muka hadu dashi yake jefa min, yana kuma gyada kai a hankali, “wata”.
Na dan zare ido cikin mamaki, kafin nayi kokarin maida mamakina na kulle, sai anjima Janan zata sha labari, nace “uhmm, to. Dama nima akwai wanda na fito gani ne dama, tunda bai zo ba kuma bari in koma, ka samu wadda kazo ganinta ne ko kuma kana bukatar in dubo maka ita ne?”.
Idanuwanshi na fitar da wasu alamu, awe and mischief, yace “a’ah, no need. Nagode. Na ganta ai, gata nan a gabana!”.
Na dan juya bayana cikin tunanin in hadu da wadda take nufi din, sai naga wayam. Na girgiza kai kamar wadda take kokarin shaking din wani feeling, gabadaya abinda yake faruwa yanzu yana da matukar daure kai, na kasa banbance tsakanin karya da gaskiya. Ina bukatar in ganni a cikin dakina, in kwanta akan katifa inyi tunanin abinda yake faruwa.
Na gyada kai a hankali, a hankalin dai nace “to shikenan, zan koma ciki ni, a gaida gida”. Kafin ma ya samu damar daga baki ya maido min amsa, maybe juya da sauri na daga kafata na fara tafiya.
Yace “Na’ilah, Muhammad ne fa!”.
Naji na tsaya cak, kamar wadda aka kafe. A hankali na juya, zuciyata tana bugu da karfin masifa, cikin idanunshi nake kallo directly, ina laluben wani alamu da zai nuna wasa yake yi a cikin idanun nashi. Tunani nake, ta yaya aka yi yasan zance na da Muhammad? Ko dai yana daga cikin abokanshi ne? Haba, babu mamaki. Kila ma Muhammad din abokinshi ne, kila shi yasa zai biyo shi su zo tare ko. Na dauke idanuna daga kanshi zuwa cikin motarshi, so nake inga ko akwai alamun mutum a ciki, amma duhun gilasan motar ya hana in hango komi.
Kallon-kallo muka fara yi dashi, ganin bashi da niyar yi mun karin bayani akan wannan katoton al’amari, yasa ni na bude baki kamar wadda take tsoron magana, nace mishi “a ina kasan Muhammad? Ka san shi ne?”.
Akwai wani nag feeling da yake damuna, daga can kasan zuciyata, wani bangarene yake jefo min tambayar, anya? Amma nake danne shi tun karfina, babu wata anya ko tantama, babu abinda yake faruwa. Yaya Bilal ba wani bane face aboki, ko kuma wani daya san zancena da Muhammad, and nothing more!.
Maimakon ya bani amsar tambayar daya min, sai ya daga kafa ya fara takowa a hankali har ya iso daf dani, ni kuma saboda tsabar rikici, na rasa ta yaya zan iya daga kafata inyi baya duk da cewa mun danyi kusanci dashi. A hakan ina iya shakar kamshin turaren daya fesa, kamar tufafin na nutsa a fuskata.
Ya daga yatsarshi manuniya yana nuna saitin kirjinshi, yace “ni nan, Na’ilah, nine dai Muhammad din da kike jira, Muhammad naki, wanda zai so ya ganki!”.
Na kura mishi idanu kawai, idan banda bugun zuciyata babu abinda ya canza daga yanayin motsin jikina. Kila ma sandarewa nayi a tsaye ban sani ba. Ban san me yasa Yaya Bilal zai ji bukatar yayi min irin wannan wasan ba, halayenshi na kamewa da rashin son wasa yasa kwata-kwata na kasa yarda da cewa tsokana ce kawai kamar yadda nake nanatawa kaina domin karyata abinda zuciyata take fada min tunda na bayyana a gaban Yaya Bilal yanzu.
Allah kadai yasan iya lokacin dana dauka a haka, kawai ina kallonshi kamar wata bakuwar halitta. Na rasa gane a duniyar da nake, shin duniyar mafarki ce ko kuma ta gaske?.
Na samu kuzarin daga baki da kyar, bayan dogon lokacin nan, nace “wane Muhammad kake magana akai, Yaya?”.
Ya saka hannu cikin aljihun rigarshi, ni kuma kamar sakara na bi hannun nashi da kallo har ya ciro wata kirar iPhone, fara kal da ita. Ina kallo yayi unlocking dinta ya fara danne-danne, ba’a dauki lokaci ba wayata ta hau kara da vibrating a hannuna. Sunan Muhammad ya fito baro-baro a jiki, yayin da a gefe guda kuma Yaya yake nuno min wayar hannunshi fuskata. Lambar wayata ce itama gata nan, da sunan ‘baby na’ a jiki, ga kuma hotona akai.
Yace “ko baki yarda da cewa nine Muhammad ba? Kina bukatar wata shaida ne daban?”.
Na rikice, na rasa abinda zan tunana a cikin raina, me ke faruwa ne wai?!. Mafarki nake yi ne? Ko kuma kwalwata ta fara samun matsala ne? Ko kuma kwalwar Yaya Bilal din ce ta samu matsala?”.
Kamar wata mahaukaciya sabon kamu, haka na fara ja da baya ina girgiza kaina, komi juya min yake yi, shi kanshi Yayan dake gabana bana ganinshi sosai. Da alamun hawaye ne suka ciko min idanu, naga lokacin da Yaya ya fara biyo ni shima, tun yana tafiya a hankali har ya daga kafa sosai ya tadda ni, ya kai hannu da niyar kamo ni yana mai ambatar sunana, “baby na!!”.
Ko rufe baki bai kai ga yi ba, na juya na daga kafa a sukwane na fada hostel. Wani daga cikin security yana tambayata lafiya lau? Me ya faru?? Amma na kasa amsa mishi.
Tunani daya ne zuwa biyu a cikin raina a wannan lokacin, lallai na cika sakara mara tunani. Ta yaya aka yi duk tsayin wannan lokaci da muka dauka muna waya dashi ban taba daukar muryarshi ba, ta yaya idanuna suka rufe ne? Ta yaya nayi sake irin haka? Kuskure ne ko kuma rashin sani??.
_’Na sanki farin sani!…’_
_’Sunana M.B!…’_
_’Ina aikine da wani kamfanin buga takardu…’._
Of course ya sanni farin sani, Yaya Bilal ne shi fa after all. M.B yana nufin Muhammad Bilal. Yana aiki da kamfanin buga takarda, dama mutumin da yake aiki da daily trust ai dole ma ya sarrafa takardu.
Mai yasa ban taba yin irin wannan tunanin ba, sai yanzu da ta faru ta kare? Babu zancen komawa baya??!.
*☆⋆22⋆☆*
A kofar daki muka ci karo da Esther ita kuma zata fito. Ta biyo bayana da sauri ganin yadda na wuceta a rikice tana jefa min tambayar lafiya? Amma na kasa daga baki in bata takamaimaimiyar amsa.
Na hade da gyalena da wayata nayi jifa dasu kan katifa, ni kuma na silale na zauna a tsakiyar dakin. Gabadaya na rasa abinda yake min dadi, shin wai ko dai mafarki ne nake yi?.
Esther ta dafa ni tana dan shafa bayana in a comforting manner, tace “Na’ilah, me yake faruwa ne? Wani abu ya faru da Muhammad dinne?”, na bita da kallo kawai, ban ma san me zan ce mata ba. Kai ko na daga baki ma bana tunanin magana zata iya fita. Don haka na cigaba da binta da kallo kawai.
Wayarta tayi kara, ta duba mai kiran, da sauri ta juyo tana kallona, “sorry Na’ilah, ana jirana a waje. Don Allah kiyi hakuri kinji? Bari inje in dawo yanzu”. Ta fita da sauri.
Bayan fitarta na tallafo kumatuna da duka hannuwana biyu, na kurawa wayata dake yashe a kan katifata kamar ita zata bani amsar tambayoyina. Abin gwanin ban dariya gwanin ban haushi, yanzu ashe duk wannan waya da muke sha da shi, duk tsayin wannan lokacin, dama da Yaya Bilal muke waya? Haba, biri yayi kama da mutum! All those stolen glances idan muka hadu a karkashin rufi daya dashi wadanda daga farko na dauka ko ni ce nake wassafa hakan a cikin raina, kallon daya dinga jefa min ranar nan da nayi rashin lafiyar nan, har na dinga tunanin zafin zazzabi ne yasa nake ganin hakan, dama da gaske ne? Dama duk wannan lokacin, kallona kawai yake yi a dage, yana min kallon wata sakara wadda bata san abinda take yi ba? Da kuma maganganun daya dinga min a jiya, ba karamin godewa Allah nayi ba da bai sa giyar soyayya ta kwasheni na dauki alkawarin da ba zan taba cikawa ba. Yanzu da na amince mishi fa aka sa mana aure ko aka daura ba tare dana taba ganinshi ba? Nasan mutuwata ce tazo kawai.
Hankalina ya kasa kwanciya, duk inda na juya idanun Yaya Bilal kawai nake gani a cikin dakin, haunting me. Naji na fara damben warto numfashina da naji ya fara guduwa, ina warto shi da kyar.
Ban san lokacin dana rarumi wayata ba na dannawa Janan kira.
Ta dauka cheerily, murya cike da tsokana, “hey.., har Muhammadun naki ya tafi ne?!”.
A rikice na hau kiran sunanta ina maimaitawa kamar karatu, “Janan… Janan…!!”.
Nan da nan ta rikice, tace “subhanallahi, Na’ilah me ya faru ne?”.
Nace “Yaya ne! Yaya Bilal ne… Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Yau ya zanyi da rayuwata? Hasbunallahu wa ni’imal wakil!!”.
Ai sai na kara rikitata, naji alamun motsa kaya daga can inda take, “me ya samu Yayan? Kun hadu dashi ne? Wai meke faruwa ne? Kiyi min bayani please!”.
Na daga baki da niyar yin magana, amma sautin komi ya kasa fita.
“gani nan” kawai tace, kafin inji ta kashe wayar. Na koma na jingina da bango ina lumshe idanuna.
Abin kamar a almara haka nake jin shi. Yau da safe dana tashi, mafarki na farko dana fara tunawa wanda nayi ne akan Yaya Bilal. Maimakon abin ya bani mamaki, sai ma ya bani dariya. A tunanina meye hadin kifi da kaska? Tunanin Yaya Bilal da ni a waje daya, abu ne da bai taba, ina nufin koda wasa bai taba gittawa ta cikin raina ba, ko a mafarki ban taba ganin hakan ba sai a yau din. Shi yasa ko a dazun abin ya matukar bani dariya, saboda babu wani abu daya kamata inyi a wannan lokacin da yafi inyi dariyar.
Amma yanzu da naga abin yana shirin ya zama gaskiya, sai kuma abin yake shirin ya sanya ni kuka.
A yadda nake dinnan, a haka Janan tazo ta sameni. Ta tattagoni jikinta cikin tsananin nuna damuwa, ko bata furta ba fuskarta da idanuwanta sun nuna min hakan baro-baro. Hakan yasa naji jikina yana relaxing, na kwantar da kaina akan kafadarta, totally vulnerable.
Kusan mintunanmu biyar a hakan, kafin ta dago kaina daga jikinta, murya a tausashe, kamar wadda take tsoron idan ta dan kara daga muryarta zata saka ni kuka. Kodayake, hakan ne, ni nasan a yadda nake jina dinnan, zuciyata a wuya, to abu kadan da bai gamshe ni ba a yansu zai iya sa ni fashewa da kuka.
Tace “me ya faru ne? Wani abu ya faru da Muhammad dinne? Me kuma ya jefo Yaya Bilal cikin wannan magana?”.
Na daga baki nace “Janan, Muhammad… Shi.. Yaya Bilal…”. Nan da nan na fara hargitsewa. Tayi saurin taba kafadata, tace “kinga, nutsu kin gane? Yauwa, just calm down. Everything’s good, ok?”.
Na gyada mata kai a hankali, na fara jan numfashi ina saukewa a hankali har naji bugun zuciyata ya daidaita. A hankali na bude baki nace “Muhammad, Yaya Bilal ne! Yaya Bilal ne Muhammad Janan!!”.
Naji wata zazzafar kwalla ta ciko min idanu, nayi saurin kokarin maida ta. Sai da na fadi maganar da karfi ta shiga kunnuwana, sannan naji gaskiyar lamarin yana shigata.
Janan ta zuba min idanu tana kallo, kamar wadda take jira in ce mata tsokanarta nake. To ai ni kaina jin abin nake kamar a mafarki ko a almara. Ni kaina na kasa yarda wai hakan ta faru.
Zuwa can tace “ta yaya?”.
Nan na gyara zama na fede mata biri har wutsiya, ban rage mata komi ba. Tun daga fitata daga hostel, maganar da muka yi dashi har gudowar da nayi. Ban san cewa hawaye nake ba, sai dana sauke aya. Naja numfashi na ajiye, sannan naji lema tana bin kumatuna. Na sa hannu na share, amma ina dauketa wata ta sake gangarowa.
Na dora da, “Me yasa ni? Me yasa Yaya zai yi min haka? Me yasa hakan zata faru dani? Janan ya zanyi?”.
Tace “mafita daya ce, kiyi hakuri ki danne zuciyarki, ki saurareshi kiji abinda zai ce”.
Na tabe baki ina jinjina kai, “tab, lallai ma! In saurareshi ince mishi me? In gaya miki gaskiya ni da Yaya yanzu sai dai hange daga nesa, kai ko daga nesar na hango shi, zan canza hanya ne a sukwane ba tare da bata lokaci ba!”.
Tace “amma kuma hakan ba mafita bace Na’ilah. Kika san ko yana da wani kwakkwaran dalili da yasa yayi hakan ne? Kada fa ki yanke hukunci cikin fushi Na’ilah, daga baya kuma ki zo kiyi dana sani!”.
Nayi wata yar dariya da daga jinta babu digo ko alama ta farinciki a cikinta, sai akasin sa. Nace “wane dalili ne daya wuce ya muzanta ni, ya maida ni sakara? Da ba don nasan Yaya ba sosai, da sai ince baki ya hada da Umar ko wani akan suyi wasa da hankalina. Kodayake, ban san shi ba yanzu anymore!”.
Janan ta kalleni, frowning. Tace “Ni nasan Yaya Bilal sosai, ba zai taba stooping that low to do something like this ba. Kamar yadda nace, da ace baya da kwakkwaran dalili, to ina mai tabbatar miki da cewa da ba zai taba ma bata lokacin shi tsawon lokutan nan ba!”.
Na turo baki, “yanzu kuma kina bin bayan Yayanki ne, zaki yace min baya?”.
Ta matso kusa dani da sauri, “koda wasa wallahi, haba, akan me zan miki haka? Ni fa shawarar da nake gani zata fissheki ce naki baki ba wani abu ba”.
Na tashi tsaye, “whatever dai, ni dai an gama min wasa da hankalina, bana kuma tunanin zan iya tsayawa in sake sauraron shi”.
Janan bata ce komi ba, ta zuba min idanu. Ni kuma na fara cire kayan jikina.
Idan da ace wani zai gaya min cewa a haka yinin na yau assabar zai kare min, da tuni zan karyata shi. Idan ma raina ya baci sosai, in kara da fada mishi bakar magana. Yau dana tashi da safe, ba haka na hango ni ba, ban taba tunanin akwai wani abu da zai zo yayi ruining yinin nawa na yau ba, sai gashi tun ba’a je ko’ina ba, yinin yayi bacin da ban taba tunani ba.
Na kalli kayan jikina dana cire, naji wani makokon takaici ya kawo ni wuya, ko linke su banyi ba na cukuikuyesu na jefa cikin kayana. Na dauki towel babba na daura a jikina. Ban cewa Janan komi ba, na dauki bokiti na sauka kasa na tari ruwa naje na watsa ruwa a jikina haka nan.
Ina cikin yin wankan naji an kira sallar magriba, don haka na daura alwala na koma sama.
Ina shiga dakin naci karo da Esther a zaune, da kayan dana baro a inda na ajiye. Ni na ma manta dasu. Daga ita har Janan suka bini da kallo.
Esther ce ta fara magana, ban san me Janan tace mata ba, amma naji bata tado min zancen dazu ba. Na dai ji ta tana mitar, “Ni wallahi nayi zaton ko accident ne suka yi ko wani abu a dazun, har na tsorata. Daga yace wani abu na gaggawa ya taso, sai ki wani rikice har haka? Lallai kina da babban aiki kuwa yarinya!”. Ni dai na shareta ban ce komi ba.
Kayan dana ke sanyawa na shan iska na sa, na tada sallah nayi. Ina gamawa itama Janan ta shigo dakin, don haka na koma gefe na bata waje itama tayi. Tana gamawa Esther ta kallemu, tace “ni fa yunwa nake ji, kuma na rantse ba zanyi wani girki ba alhalin ga abinci nan ina gani a gabana. Idan ba zaki ci wannan abun ba, ki bani inci don ba zan so ayi asarar su ba gaskiya”.
Nace “gashi nan kiyi ta ci”.
Tayi tsalle ta rarumo kayan, Ina ji Janan tana itama a ajiye mata bari tayi sallah ta zo taci, nayi banza dasu su duka.
Ana kiran sallah na tashi nayi. Janan ma tana gama nata, ta zauna ta tada meat pie din da Esther ta rage mata da sauran drinks din. Dama guda biyar ne nayi babu yawa. Janan tana gamawa ta kalli agogo, tace “bari in tashi in tafi kafin Yaya ya dawo, yayi fada”.
Ai jin an ambaci sunan Yaya, sai naji raina ya kara dagulewa. Na koma kan katifa na zauna, na harde hannuwa a kirji ina turo baki ina kallon Janan tana gyara zaman hijabin jikinta a wuyanta, ta gama ta juyo tana kallona, “mai kike jira ne, ba zaki raka ni ba?”.
Na kara turo baki, “a’ah, ki gaida mutan gida!”.
Ta daga hannuwa sama in mocking surrender, cam cikin idanunta alamun dariyar da take ta kokarin boyewa ne. Na harareta, ta kara yin murmushi, tace “yi hakuri ki maida wukar, ba ni na kar zomon ba kin gane? Bari in karasa gida ni kam. Don Allah kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki, kada ki bari wannan abin ya taba zuciyarki kinji?”.
Na kalleta kawai, sanya abu a cikin rai na nawa kuma?
A haka dai ta mana sallama ta tafi.
Ina zaune ina kallon Esther data tashi tana hada kayan, tana cewa ita dai ba zata yi wanke-wanke ba fa, “Sai dai idan kin tashi gobe ki wanke kayanki amma ba zan iya ba”.
Ta dai gaji da mitar ta tayi shiru ganin ban tanka mata ba. Tana gama abinda zata yi, tace min ta tafi class. Exam dinmu ranar monday ne, amma nasan ko giyar wake na sha ba zan iya yin karatu ba yanzu. Don haka na kwanta kawai ina ta faman saka da warwara a cikin raina.
Har wajen karfe goma sha daya na dare idanuna biyu kyar, babu alamun barci a cikinsu. Juyi kawai nake yi, ba tare da takamaiman wani abu da nake tunani a kai ba. Wayata ta fara kara, daga farko cak nayi a zaune, hatta da numfashina sai daya tsaya sakamakon jin kalar karan. A hankali na juya na kalli wayar, babu shakka sunan Muhammad ne, ko kuwa Yaya Bilal zan ce? Yake yawo akan wayata.
Ban iya motsawa ba har ta katse, tana katsewar aka sake kira. Na hau gyada kai ina kara girgizawa cikin tsananin mamaki, yanzu har Yaya yana da sauran kunyar da zai iya kirana a waya dama? Oh duniya ina zaki damu?!.
Na dauko wayar da niyar kasheta, hannuna ya silale ya taba answer and speaker button ba tare dana kula ba, sai dana ji muryar shi radam kamar a cikin dakin yake yana magana, “hello? Oh thank God! Baby kina ji na? Baby…?!”.
Da sauri na danne wayar har ta mutu, na dafe saitin zuciyata data hau bugawa da sauri kuma da karfi. Jin muryar shi a yanzu, sai naji kamar an tado min wani tsumi. Ko ba’a fada ba, nasan yau munyi baram-baram ni da barci.
Kuyi hakuri da wannan zuwa gobe don Allah. Jiya sai dana yi typing, nayi zaton na turo na goge, sai daga baya naga ashe ban turo ba.
*☆⋆23⋆☆*
Washegari na tashi da wani azababben ciwon kai wanda ban taba zaton wani mahaluki zai taba yin kamar sa ba sai a ranar. Ni dama nasan za’a rina, yadda jiya na kwana ina sake-sake, barci ma sai gab da sallar asubahi sannan ya daukeni. Dalili kenan da yasa na so in makara sallah yau. Ina yin sallar kuma dana koma barci ma, kasa komawa nayi, sai can rana har ta ma fara fitowa sannan nayi barcin.
Yanzu kam zaune nake akan katifata da misalin karfe goma da rabi, kaina da yake bugawa kamar ana kwankwasa guduma tallabe cikin hannuwana guda biyu. Dakin babu kowa, Esther ta tafi church, Maimuna kuwa dama rabona da ita tun ranar juma’ah da safe da zan bar daki, ban kara ganinta ba.
Na samu na lallaba da dafa bango na tashi na fita. Ruwan wanka na jona a jikin heater, kasancewar ruwan da aka yi yau da asuba, yasa har yanzu garin sanyi garai. Yana dan yin zafi na je nayi wanka, nayi brush hadi da dauro alwala. Sai dana fara yin sallar walaha sannan na sake dafa wani ruwan a cikin kofi karami, na hada hot chocolate shi kadai na sha. Bayan na sha na balli paracetamol guda biyu na afa a baki na kora da ruwa.
Bayan na gama kin komawa in kwanta nayi, na kuma ki zama in saka tunanin Yaya Bilal da al’amuranshi a cikin raina. Sai kawai na dauki wayata na jona ta a jikin caji ba tare dana kunnata ba, na hada kan kayan wanke-wanke na kulle dakin na sauka kasa nayi.
Bayan na gama na koma dakin, ciwon kan ya dan sauka kadan, amma jifa-jifa na kan ji ya sara min har yanzu. Na bude dakin na shiga tare da maida kofar dakin na rufe. Kasancewar yau students suna ta hutawa kuma safiya ce, wasu kuma sun tafi gida, yasa hostel din yayi shiru babu hayaniya, yadda kasan ma babu kowa.
Na fara da kunna wayata. nasan dai ba zan dawwama a haka ba, komi daren dadewa nasan dole in fuskanci wannan chakwakiya. Ban shirya ba, amma nasan dole ne. Don haka naga gara in fara tun yanzu, the earlier, the better.
Ko minti goma cikakke banyi da kunna wayar ba, ta hau kara. Na saurara da goge-gogen da nake yi tare da tsayar da kira’ar Sheik Minshawi da dan yaro a cikin suratul-Mulk dake tashi daga cikin laptop dina, na dauki wayar. Ganin sunan Yaya Mudatthir na daga da sauri, cike da tunanin ko Anty Sailu ce ta sauka. Sai dai ina dagawa, tun ma kafin inyi magana ya riga ni, yace “wai ni Illo don Allah menene amfanin wayarki ne? Ke kullum aka kira wayarki a kashe? Me yasa ba zaki ajiye wayar kawai ki cire komi nata ba kowa yasan baki amfani da waya?”.
Nayi dan murmushi, “Yaya, nasan amfanin wayata ni fa, wasu lokutan rashin caji ne yake sawa idan kun kira kuke ji a kashe”.
Yace “kwarai kuwa, ai da yake duk Nigeria baby garin da ake wa kwauron wutar lantarki kamar nan ko?”.
Nayi yar dariya, “ni ban ce haka ba. Anty Sailu ta sauka ne?”.
Yace “tukuna dai, yanzu haka muna asibiti ma”.
Nan da nan naji gabana ya fadi, nace “lafiya? Jikin ne ya motsa?”.
Yace “a’ah, amma likitocin sun ce tana bukatar zama a asibitin zuwa lokacin da zata haihu domin su dinga monitoring dinsu ita da babyn. Amma so far dai komi lafiya lau”.
Na dan sauke ajiyar zuciya, “Masha Allah, Allah ya sauketa lafiya. Amma nayi fatan ace ina nan yanzu tare daku wallahi”.
Yaya yace “to ya zaki yi? Haka karatun ya gada ai. Ina fata dai idan ta haihu zaki zo ko?”.
Nace “sosai ma! Ai ko muna exams sai na kansileta nazo!”.
Yaya ya saki yar dariya, “ba wani nan. Ke dai kawai kiyi fatan kina free lokacin”.
Nace “to shikenan. Ya su Inna? Kwana biyu ma bamu gaisa dasu ba”.
Yace “a asibiti na baro ta, ni na dan fito yanzu. Amma idan na koma zan kira ki sai ku gaisa dasu”.
Nace “to shikenan, sai ka dawo din”.
Yace “babu dai wata matsala ko?”.
Nayi dan murmushi a hankali, nace “babu Yaya. Sai anjima”. Muka yi bankwana na ajiye wayar.
Aikin da nake yi na komawa, ina yi ina bin kira’ar har na gama. Ina gamawa na fara gyaran wajen da nake. A takaice sai wajen karfe daya na gama komi.
Bayan nayi sallah na fita waje can wajen yar kasuwar su na siyo kayan miya na dawo daki na hada miya na dafa farar shinkafa na ci.
Na dauki system dina na fara aiki akan project din da nake to har zuwa lokacin da Janan ta kira ni, sannan na dakatar da aikin na dauki wayar. Bayan mun gaisa ta watso min tambayar lafiya ta lau dai ko? Na kada idanu kamar ina ganinta, “ehh, ga wanda ya kwana ya wuni cikin tashin hankali da damuwa da rashin barci har da karin ciwon kai, lafiyata lau Jan. Ina fata kinyi kin tashi kin kuwa wuni cikin koshin lafiyata?”.
Janan tayi yar dariya, “ai daga ji ma babu tambaya lafiyarki lau, ba sai kin janyo min wani dogon bayani ba. Ya karatu, ina fata dai kinyi ko?”.
Na dan saci kallon tulin jotters da textbooks dana fiddo dazu wadanda suke jiran in daga su, tare da sauke ajiyar zuciya lokacin dana tuna akwai fa sauran gingimemen aiki a gabana. Nace “ban fara ba wallahi, amma anjima da yardar Allah zan fara tunda dama revising ne kawai zan yi”.
Tace “hummm, nima hakan take. Allah dai ya bamu sa’a”. Nace “ameen”.
Tayi shiru, hesitating, banyi kokarin katseta ba ko tambayar lafiya, nasan tunda naji haka akwai magana da take son muyi, wadda kuma bata wuce ta mutum daya. Sai da tayi radin kanta tace “me zai hana ba zaki saurari Yaya ba don Allah? Ko sau daya ne Janan, ya cancanci wannan damar daga gareki”.
Nayi shiru ina sauraronta, sai data dire aya sannan nace a hankali, “dalilin kenan da yasa kika kira ni dama? Saboda Yaya?”.
Itama ta danyi shiru kafin tace “wai me yasa kike cewa haka ne Na’ilah? Ke kinsan cewa tsakanina dake ai babu wannan abin, wallahi jin ki nake kamar yar uwata ta jini, sai dai shima Yayan ina jin shi a cikin jinin jikina. I just want what’s best for you Na’ilah, shine kawai!”.
Na san duk abinda ta fada hakan take, idan kuma da kunya da kara, bai kamata in watsawa dan uwanta kasa a ido ba, sai dai bana tunanin zan taba iya wannan abu da Janan take kokarin sanyowa, ba zan iya yin wannan karar ba.
Nayi kasa da murya, cikin tsananin son yi bayanin da zata fahimta, wanda kuma ba zata kullace ni ba, nace “Janan… Ke kinsan abinda yake damuna, kin kuma fi kowa sanin yadda nake kin wannan akidar, don haka don Allah don Annabi Jan, ki taimake mu ki daina sako wannan maganar. Kince you just want what is best for me, barin wannan maganar shine mafi a’ala a gareni, don haka don Allah mu daina yin ta kawai. Don Allah kice min kin fahimce ni?”.
Tace “na fahimce ki, sai dai Na’ilah, wannan fa ba karamar magana bace ko kuma maganar wasa da zaki ce a barta kamar bata taba faruwa ba. Yaya ma ba zai taba kyaleki ba in gaya miki gaskiya, shirun da kika ga yayi kawai ya baki iska ne ki hada tunaninki waje daya. Ina ga da kin hakura kun yi magana, kiji abinda zai ce mikin”.
Na fara gajiya da maganar wannan, tun jiya muke nanatata kamar cin kwan makauniya, cikin nuna alamun gajiya da maganar nace “kamar yadda nace miki, kawai mu bar maganar nan. Babu wani abu da zamu tattauna tsakanina da Yaya Bilal, ke kin sani. Ba zan taba mika wuyana a sare shi ba alhalin ina cikin hankalin kaina, haba Janan, idan har kin tabbatar kina so na kuma kina kaunata, bai ma kamata ace kina nema kiyi convincing dina ba koda wasa”.
Itama cikin nuna alamun gajiyawa tace “whatever Na’ilah, ni dai iyaka shawarar da naga zan iya baki kenan. A gani na idan kuka yi maganar, kika yi mishi bayani, zai iya ba zuciyarshi hakuri ya nemi daidai dashi wadda zata iya zama dashi da matan shi tunda ke kin ce baki iyawa. A ganina kenan. Sauran kuma, Yana gareki. Dabara ta rage ga mai shiga rijiya, sai mun hadu a asibiti gobe!”. Ta katse wayar.
Na bi wayar da kallo. Daga jin yadda muryarta ta dan daga, ranta ne ya fara baci. Ban yi kokarin sake kiranta ba, na maida wayar na ajiye. Bana tunanin wani abu zai iya canza min kudirina, ciki kuwa har da fushin Janan.
Na fahimci kaunar da take yiwa dan uwanta ce ta haddasa hakan, sai dai me yasa ni ba zasu fahimceni ba? Me yasa ba zata yi kokarin fahimtar dalilina ba??!.
Nayi kokari na kauda tunanina daga kan wannan magana na ci gaba da abinda nake yi.
Sai bayan la’asar sannan na fita karatu. Har aka kira magriba ina can, sai masallaci naje nayi salla. Akan hanya na tsaya na sayi doughnut da yoghurt, na koma class. Sai wajen karfe goma na koma daki. Ina komawa ko kayan jikina ban iya cirewa ba na zube akan katifa saboda barcin daya cika min ido.
*
Washegari kuwa garas na tashi, bayan nayi sallah na fara duk wasu al’adu dana saba kafin in fita zuwa asibiti. Jikina a dan sanyaye yake saboda nerves din jarabawa, kodayake nasan kusan kowa ma haka yake ji, an riga an saba. Na shirya a nutse, ban dora abin karyawa ba saboda azumin sitta shawwal da nake yi, zuwa gobe zan gama gabadaya in Allah ya yarda.
Akan hanyata ta zuwa venue din da zamu yi jarabawar, wayata ta fara pinging alamun shigowar message. Ina dubawa naji gabana yana dukan uku-uku, Yaya ne. Kin dagawa nayi, ina tsoron in daga in karanta abinda zai hana ni sukuni bayan ina da muhimmmiyar jarabawa a gabana.
A kalla kafin in karasa venue din, ya kara turo wasu sakonnin kamar guda uku haka. Na tsaya na bada ajiyar wayar wajen securities bayan na kasheta, sannan na shiga ciki.
Seat dina yana kusa dana Janan ne, yadda muka rabu da ita jiya nayi tunanin ko kallon arziki ba zan samu daga gareta ba, sai ta bani mamaki data haskeni da murmushin man nata, ta dan matsa kadan yadda zata bani waje sosai tana cewa “sai yanzu? Wato kema kin koyi makara ko?”.
Na dan saki murmushi a tausashe, duk da yanayin da nake ciki, sai naji raina ya dan yi sanyi, na zauna kusa da ita, “ai kin san zama da madaukin kanwa…”.
Tayi yar dariya, “idan ma dani kike, bani na goga miki ba, can zaki je ki nemo wanda ya goga miki yarinya!”. Muka yi musayar murmushi.
Ba abin mamaki bane ga halayyar Janan, sanyin zuciya irin nata da kawar da kai har kullum shine abinda ya tsananta tsayin abotarmu da ita. Ina girmamata saboda hakan.
Muka fara revising ya junanmu gami da tambayoyi game da abubuwan da muka karanta, har zuwa lokacin da masu tsaron jarabawar suka shigo. Da misalin karfe tara kenan.
Jarabawar ta daukemu awanni biyu da rabi cur, kusan tare muka gama ni da Janan amma ta riga ni fita. Na mika takardar bakina dauke da addu’o’i iri-iri, idan nayi rashin sa’a jarabawar nan ta dawo min ban san ya zamu karge da Baba ba.
A bakin kofar wajen na sameta tana jirana, na amshi wayar hannuna, muka jera ni da ita hannu da hannu har zuwa cikin hostel. Allah ya taimaka yau sun daga mana shiga cikin asibiti har sai zuwa gobe. Muna ta tattaunawa game da jarabawar har muka shiga hostel din.
Muna shiga ta cire uniform din jikinta, nima na cire nawa. Na ciro mata rigar shan iska, doguwa mai wadataccen fadi, nima na saka shigenta, muka kwanta akan katifata, sai a lokacin na bata labarin Anty Sailu fa tana asibiti, ta jinjina lamarin tare da cewa zata kira ta mata sannu.
Ba karamin dadi naji ba da bata kara tado min zancen Yaya Bilal ba. Again, nan ma ta bani mamaki. Janan ba irin mutanen nan bane masu saurin sakin abu ba, idan ta sako abu a gaba ko kuma wata magana, bata saki don wasa har sai ta cimma nasara. Shi yasa yanzun nake ta kaffa-kaffa da ita, ban san ko me take tunani ba a cikin ranta.
Sai da muka yi sallar azuhur bayan mun koma mun kwanta, sannan na bi bayan sakonnin da Yaya ya turo min dazu, hannuna har rawa yake yi.
Na farkon cewa yayi; _’Hey, you okay?’_
Na biyun kuma: _’Nasan cewa ba ta haka ya kamata in tunkare ki ba, nayi kuskure. Should’ve thought about it more kafin in tunkare ki ta wannan hanyar, saboda haka ne nake baki hakuri!’._
Sai kuma, _’Baby, na san cewa kina ji a cikin ranki kamar ban kyauta miki ba, ko kuma wasa nake miki da hankali. Ina tabbatar miki da cewa ba haka bane, please let me explain myself!.’_
Akwai kuma wanda na kula ya sake turowa nan da mintuna sha biyar da suka wuce: _’Please baby, da gaske ba zan iya cigaba da zama a haka ba. Nayi kokarin ganin cewa na baki cikakken lokaci domin ki samu kiyi tunani akanmu, I know it’s sudden. But that’s it! I can’t do this anymore.. Let me see you again, please? I promise zan miki bayanin duk abinda kike son ji, kinji baby na?!’_
Ina gama karanta wannan naji wani abu mai zafi ya daki zuciyata, idanuna suka fara min zafi alamun kwalla ta fara taruwa. Na lumshe idanuna tare da kwantar da kaina akan pillow. Yaya Bilal ya riga ya bata rawar shi da tsalle, koda yake tun daga farko dama bashi da wani chance a wajena, amma me yasa raina yake kuna idan na tuna cewa zamu rabu dashi har abada?! Me yasa nake jin kamar ina gab da rasa wani muhimmin bigire na jikina ba? Ko dai zan bi shawarar Janan ne, inyi rethinking wannan bakon al’amari?.
Nayi gaggawar girgiza kaina, inaa! Ba zai yiwu ba!.
A hankali na sake bude idanuna, har yanzu hasken kan wayata bai mutu ba. Na dinga scrolling sama ina kara karanta sakonnin da muka dinga canzawa a tsakaninmu, kafin in san ko shi din wanene. A da, da ban san ko shi din wanene ba, kawai ina jinshi acan kasan raina ne, yeah, ina son shi, kuma ina kaunar shi, amma yanzu dana san ko shi din wanene finally, sai nake ganin komi daban, at least yanzu idan ina tunaninshi zan ga fuska kuma zan ji murya sosai. Sai dai nasan koma menene nake ji game dashi, dole ne in manta dashi. Ko za’a yi me, nasan cewa ba zan taba amincewa da Yaya Bilal ba.
Saboda haka na kashe hasken wayar, na ajiyeta a kusa dani na rufe idanuna cike da fatan barci ya dauke ni a lokacin.
***
“… Na’ilah?!”.
Da sauri na bude idanuna, Janan na zaune kusa dani tana kallona cike da yar damuwa a fuskarta. Na sauke idanuna akan agogo, naga har karfe hudu da rabi tayi. Na tashi zaune ina salati. Tace “har an kira sallah, ki tashi muyi mu leka waje mu ga abinda zamu lalubo na shan ruwa, yau anan zan sha ruwa”.
Na mike tsaye, ko don barcin da nayi ne? Jikina naji yayi min wani nauyi. Na tashi na dauki hulata na fita, idanun Janan a kaina. Nasan dalili, mafarkin da nayi ne wanda ta tashe ni a daidai lokacin da bana son tashi, daidai lokacin da nake kwadayi, kuma nake marmarin ganin wannan mutumi da duk duniya babu wani mahaluki da yake kada min sassan jiki kamar shi ba. Amma kullum anan nake tsayawa, ban taba ganin fuskarshi, muryarshi ma haka nan nake jinta sama-sama kamar ba a kusa dani yake ba. Wani lokacin ni nake tashi a karan kaina, watarana kuma sai ayi arashi wani ne a kusa dani zai tashe ni. Koma dai menene, na zubawa sarautar Allah ido ne kawai domin ni kam na kasa gane wannan abu.
Bayan munyi sallah, muka fita zuwa kasuwa muka sayo abubuwan da zamu bukata, muka dawo muka yi yam balls da kunun aya. Har muka gama shan ruwa da ita bata yi alamun sake tado maganar jiya ba, don haka naji na fara relaxing. Cikin annashuwa kamar yadda muka saba muka sha ruwanmu, na tashi na rakata ta hau mota na dawo, na tattare kayan da muka bata na ajiye a inda nake tara kayan wanke-wanke, nayi sallar isha’i.
Daga nan common naje nayi kallo. Karfe goma na dawo daki. Na samu Maimuna da Esther a daki, na musu sannu suka amsa nayi shirin kwanciya barci na kwanta.
Wani irin sad feeling da naji ya rufe ni a lokacin, da ace da ne, da yanzu muna nan muna zuba soyayyarmu ni da Muhammadu na. Me yasa Yaya Bilal ne zai zama Muhammad? Mai yasa ba wani mutum ne daban ba, wanda bashi da mata daya balle mata har biyu? Me yasa? Wai me yasa abubuwa suke zo min ne a hagunce?
Daren ranar yau dai da kuka shabe-shabe nayi barci.
*☆⋆24⋆☆*
Ni a karan kaina nasan cewa idan nace bana yin kewar Yaya Bilal to karya nake yi, ina kewar shi fiye da tunanina. Sai dai wani sashe na zuciyata yasan cewa yaudarar kaina kawai nake yi. Ko zan mutu, ko zuciyata zata tsattsage saboda damuwa, zama da Yaya Bilal ba zai taba zama maganin hakan ba. Don haka nake iyaka bakin kokarina wajen ganin na danne duk ma wata kewa, so da bege da nake ji game dashi. Nasan cewa na dan lokaci ne, nan da lokaci kadan zan daina.
Sai dai duk wanda ya ganni, yasan cewa ina cikin damuwa. Idanuna kadai sun isa shaida, saboda bana samun barci mai yawa. Ko nayi, saboda tsananin sanya maganar Yaya Bilal da matanshi a cikin raina, haka zanyi ta mafarkinshi. Watarana ma har da matanshi, wani lokacin kuma barcin ne ma gabadaya baya zuwa.
Yanzu ma muna zaune a cikin ward ni da Janan da wata Aisha, a ranar alhamis kenan. Janan da Aisha ne suke ta hirar su, ni kuwa hankalina yana kan wata calender dake rataye a wajen. A zahiri idan ka kalleni, zaka yi tunanin jerin magungunan dake cikin takardar nake karantawa ko kirgawa, amma a hakikanin gaskiya hankalina ma kwata-kwata baya tare dasu. Tunani nake, tun wannan text din da Yaya Bilal yayi min ranar litinin, har yau bai sake kirana ba, kuma bai sake turo min wani sakon ba. Ta wani bangaren naji dadin hakan, so nake ya barni, ya kyaleni, idan ma da hali ya manta dani. Duk da cewa nasan har abada zan dinga kallonshi da wannan maganar, ba zan taba mantawa ba, sai dai in binne abin acan karshen bangon zuciyata.
Ta wani bangaren kuma tunani nake, dama kirarin da yake akan cewa yana sona duk kuri ne da cika baki? Har ya manta dani kenan? A yadda yake nunawa dinnan, nayi zaton zai zage damtsensa ne har sai inda karfinsa ya kare. Amma dana fara irin wannan tunanin, sai inyi gaggawar katse kaina, idan ma ya ci gaba da bibiyata babu abinda hakan zai sa sai ma kara min ciwon kai da damuwa da hakan zai yi. Don haka gara ma yaje can ya karata da matanshi ya fiye min alkhairi. Shima wannan kuri ne kawai da zuciyata take yi, can can kasanta, tana fatan ace ba haka bane.
Kai wasu lokutan sai inji da ace ana cire zuciyata a sake sabuwa, da na garzaya zuwa ko’ina ne na canza tawa. Komi nisan wajen kuwa.
Nayi nisa cikin tunani, ban ankara ba sai ganin Dr. Na Abba nayi a kaina yana snapping hannuwanshi a fuskata. Nayi firgigit! Kamar wadda ta tashi daga barci na kalleshi.
Yayi dan murmushi, “haba Nas, wannan dogon tunani haka har ina? Idan dai don nine kada ki damu, gani a gabanki. Ba zan matsa ko nan da can ba har sai kinyi min iznin hakan!”.
Ban san sanda na saki dan murmushi ba, Allah ya zubawa mutumin baiwar iya ba mutane dariya koda mutum bai shirya ba kuwa, ko kuwa ni ce kadai?.
Yace “haba! Ko ke fa? Ba gashi har kyakkyawan murmushin nan naki ya fito ba? Wallahi ba karamin kyau kike yi ba idan kika yi murmushi!”.
Nan ma ban iya daurewa ba sai dana kara yin wani murmushin.
Yace “so what’s up? Kwana biyu na daina ganinki anan, nayi zaton ko kin bar ward dinne. Jiya sister Mairo take ce min ba canza ku aka yi. Kin san yanzu evening duty nake yi, ina ga shi yasa bamu cika haduwa ba”.
Na dan gyada kai tare da cewa “haka ne kam, ya aiki?”.
Yace “Alhamdulillah. Ko kina da yan mintunan da zaki taka min zuwa nan waje Na’ilah? Ba don kowa na shigo da wuri ba sai don ke”.
Sai lokacin na kula da cewa yau ba sanye yake da labcoat dinshi ba. Na juya na kalli su Janan da suke yan rubuce-rubuce da danne-dannen waya, amma ni nasan hankalinsu gabadaya a kanmu yake. Na gyada mishi kai a hankali tare da sauka daga kan kujerar da nake, ni dashi muka jera muka fita.
Bai furta min komi ba, nima kuma banyi yunkurin cewa komi ba har muka fita waje. Kaina a kasa yake, ina dai bin sawun kafarshi ne dake sanye cikin takalmi sau ciki, don haka ban san sanda muka isa wajen ajiye motocin likitocin asibitin dake ta wannan bangaren ba, sai dana ji ya ja birki sannan. Ya jingina da jar motar shi 406, ni kuma na tsaya ina fuskantar shi.
Yace “Wato Na’ilah dalilin da yasa na so mu kebance muyi magana dake shine, ina so ne inji inda maganar mu ta kwana ne. Shin, har yanzu kina ganin bani da chance ne a wajenki?”.
Na dan yi wuri-wuri da ido, kafin in tsaida su waje daya, murya a shake nace “to ni me zance maka kuma, ina tunanin tun ranar nan na fada maka anyi min miji a gida?”.
Yayi dan murmushi, yace “Hmm, Na’ilah kenan! Aka yi miki miji ko kuma kika yiwa kanki miji, kika fada min?”.
Nace “kamar yaya? ban gane ba!”.
Yace “come on mana, daga jin yadda kike cewa ‘ai anyi min miji a gida!’, ko dan jariri yaji yasan cewa kin fadi ne kawai don kiji dadin bakinki!”.
Ban san lokacin dana kyalkyale da dariya ba, musamman lokacin daya make murya wai shi ala dole kwaikwayo na yake yi. Shima yayi murmushin ya kara jingina da motarshi yana dan murmushi, nayi shiru ina girgiza kai, amma murmushin fuskata bai bace ba.
Yace “da gaske ba. So I’ll like it idan kika manta da zancen mijin da ba’a riga an san ko wanene ba, let’s talk about us for now. Kamar yadda na fada miki ranar nan, gaskiya kina burgeni. Kuma ina fatan ace zaki bani dama, mu samu fahimtar juna a tsakaninmu. Me kike tunani?”.
Nace “magana ta gaskiya ni a halin da ake ciki yanzu likita, babu wannan maganar a cikin raina yanzu. Ina fata hakan bai bata maka rai ba?”.
Ya girgiza kai, “ko kadan. Kin san ku mata da jan aji, hakan ba matsala bace a wurina. Zan baki iyaka lokacin da kike bukata, amma ina neman alfarmar dinga yin waya dake zuwa lokacin da zaki sauko?”.
Nasan wannan rana ba zata taba zuwa ba, don dai mu rabu lafiya dashi sai kawai na gyada mishi kai. Yayi dan murmushi, “yauwa, nagode. Muje in dan taka miki ko?”.
Nayi yar dariya, nace “nayi zaton ni na rako ka?”.
Yayi yar dariya, “a’ah, ni na isa? Kawai dai ina so ne mu dan tattauna dake ne a waje dama dai kawai”.
Muka sake kwasa muka sake komawa dai, anan ne yake dan fada min tarihin rayuwarshi. Gidansu yana palladan, har kwatance yayi min amma da yake ba sanin unguwar sosai nayi ba ban gane ba. Ya fara min bayani akan irin rayuwar da yayi, da kalar makarantun da yayi, muka koma wajensu Janan.
Muka yi sallama dashi ya juya ya tafi, ni kuma na zauna akan kujerar da nake. Ina zama naci karo da idanun Janan tana hararata. Nace “malama lafiyarki kuwa?”.
Tace “ban sani ba. Ni zo ki raka ni waje inje in sayo wani abu in ci”.
Ba musu na tashi na bi bayanta, da yake karfe sha biyu da rabi ta kusa, lokacin tafiya sallah yayi. Muka yiwa Aisha sallama muka fita, nace mata “ai nayi zaton kina azumi ne yau”.
Tace “a’ah”. Ganin tana amsa min magana dai-daya yasa nayi shiru nima.
Tace “wannan likitan da kike biyewa, son shi kike yi ne?”.
Na dan yamutsa fuska, “wace irin magana ce kike yi haka? Wani irin so kuma?”.
Tace “to sai wani yage mishi baki kike yi kina dariya, me hakan yake nufi?”.
Na girgiza kai, “don Allah kada mu ja maganar nan tayi tsayi. Ni babu wani son shi da nake yi”.
Tace “to sai ki daina bashi fuska, a haka kina leading dinshi ne kawai ba wani abu ba!”.
Na daga baki hangamgam, nace “to wai ke meye matsalarki ne? Idan na kula shi ko naki kula shi, meye damuwarki?”.
Har ta daga baki zata yi magana, sai kuma ta fasa, tace “oho dai, ke kika sani!”.
Muka yi shiru muka cigaba da tafiya, can kuma tace “ya labarin su Sailu?”.
Muka karkata hirar zuwa can, wanda hakan ba karamin dadi yayi min ba.
Mun je ta sayi abinda zata ci, muka biya ta masallaci nayi sallah sannan muka koma ward. Acan taci abincin, muka cigaba da ayyukanmu har lokacin tashin mu yayi.
Janan ta riga ni tafiya saboda lokacin da aka tashi, wani yaro nake yiwa dressing. Faduwa yayi garin wasa da keke. Don haka ta wuce saboda a cewarta, zata biya kasuwa ta sayi wasu kayan bukatu kafin ta wuce gida.
Sai wajen karfe biyar da kwata na gama, na yiwa mutanen wajen sai da safe, na fita.
Sai dai cak! Naja na tsaya lokacin da nayi arba da abinda ban taba tunanin zan gani a daidai wannan lokacin ba. Yaya Bilal ne a tsaye kyam, tsayuwar sojoji, ya zube hannuwanshi duka biyu a cikin aljihun wandon kaftani dake jikinshi.
Kamar wanda aka ce mishi ya dago kanshi, karaf muka hada idanu dashi.
Abu na farko daya fara zo min a cikin raina, shine in fyalla da gudu. Sai dai da nayi tunani, sai naga meye na gudunshi to? Hakan ba wata mas’ala bace. Shawara ta biyu ita ce in tafi in raba ta gefenshi kawai in wuce, in nuna kamar ban san shi ba. Sai dai matsalar itace, kafafuna sun kasa motsawa balle har suyi tafiya. Don haka naci gaba da tsayuwa anan inda nake, ina kallon Yaya Bilal.
Ganin bani da niyar yunkurin yin wani abu, yasa ya tako cikin wani nutsattsen taku ya tunkaroni. Sai lokacin naji kafata ta motsa, na fara ja da baya, amma bai daina tunkarata ba. Da dai naga ya kusa cimma ni, sai na juya na sake fecewa a karo na biyu.
Can A&E na tafi, na shige can wani lungu da mutane basu cika bi ba na labe kamar wata munafuka. Na kwashe fiye da mintuna ashirin a wajen, zuwa lokacin nasan idan ma nema ne Yaya ya gaji ya kara gaba, don haka na fito daga maboyata.
Sai dana karewa wajen dana ganshi dazu kallo na tabbatar da cewa baya nan, sannan na daga kafa da sauri kamar wadda aka cilla daga jikin mashi, na dauki hanyar komawa hostel.
Sai dai da yake kwata-kwata yau sa’a ba a sashe na take ba, sai dana fara hango gate din hostel, har ina kara daga kafa, kawai sai ganin mutum nayi a gabana kamar wanda ya diro daga sama. Nayi tsalle nayi gefe daya a tsorace ina rafka salati, kafin in daga kaina in sauke su akan dodon nawa. Shi din dai da nake ta gudu.
Na sake juyawa da nufin ranta ana kare, ya sake shiga gabana, juyawar da nayi da sauri, da niyar bi ta wata hanyar, sai naji ni shame-shame a jikin bango. Shi kuwa yayi babakere a gabana, ya tsare gaba da baya, ta yadda babu yadda za ayi in tsere, sai dai idan bangaje shi zanyi. Ko kuma in ratsa ta jikin bangon dana jingina.
*☆⋆25⋆☆*
Ga duk wata diya mace da take jin ta cika ‘ya, mai cikar halitta da kamala, wadda zata shiga ko’ina ne a fadin duniyar nan kanta a tsaye, ta kuma amsa cikakken suna na ‘ya mace, to ta cancanci gwarzon namiji kamar Yaya Bilal.
Irin mazajen nan ne da ake kira mazajen duniya. Wadanda Allah yayi wa ilhama da kuma rufin asiri ta kowane fanni.
Tun bayan rasuwar mahaifinsu, a lokacin yana ajinshi na shida a makarantar firamare, yayin da babbar yayarsu Yaya Sa’a take aji na biyar a sakandire, Jameel kuma yana primary three, duk da kankantarshi, Bilal bai yi kasa a gwiwa ba wajen zagewa tun karfinshi wajen ganin cewa ya tallafa musu. Wannan duniya da muke ciki ta riga ta zama abinda ta zama. Mutane basu san kowa ba daga kansu sai iyalansu, wasu ma iyalan nasu sai na kurkusa kawai. Mahaifinsu mutum ne mai rufin asiri daidai gwargwado, bayan rasuwarshi kuma sai rayuwa take nema ta zamar musu wata aba mai tsananin wahala.
Ummansu ta fara sana’o’i na hannu iri-iri domin ta samu ta tallafi ci da shan ‘ya’yanta da karatunsu. To shima Bilal bai zauna ba, kananun sana’o’i na hannu babu wanda bai kama ya taba ba, kanikanci, dinki ne, bude karamar tired, da dai duk wata hanya daya san zata sada shi da samun halaliyarshi.
Duk da cewa yan uwa na iyaka bakin kokarinsu, sai dai kamar yadda nace, wannan zamani da muke ciki yanzu ya zama naka sai na naka. Koda suka fara abin daga farko kamar abin arziki, sai suka zo suka watsar. Shi kuwa yau a duniya, babu wani abu da yafi saurin zubar da mutunci da kima irin yawan bani. Ko iyaye gajiya suke yi balle kuma wadanda alaka ce kawai da bata kai ta kawo ba ta hada. Don haka suka kama kansu, idan an kawo musu abin amfani ko na tallafi, su karba suyi godiya, idan basu dashi, suyi kama-kama su rufawa kansu asiri.
Wannan gida da suke zaune, shi kadai mahaifinsu ya bar musu a matsayin gado, su ukun da kawunsu daya kasance kanin mahaifin nasu. Sai kuwa wata karamar gona da aka sayar da ita lokacin da Yaya Sa’a zata zana jarabawar fita daga babbar makarantar sakandire.
A cikin wannan lokacin ne mahaifinsu Janan ya fara neman Ummansu, lokacin matarshi bata jima da rasuwa ba. Kuma abokin mahaifinsu ne kafin ya rasu. Aka daura aure ta tare a Kaduna abinta.
Nan ya hade Bilal da Jameel din ya saka su a makaranta tare da sauran ‘ya’yanshi suka cigaba, ita kuma Yaya Sa’a ya shige gaba, aka daura mata aure da wanda yake nemanta a lokacin bayan ta gama sakandire, taci gaba da karatunta a gidanta.
Bayan ya gama secondary, ya taho nan ABU Zaria yayi degree dinshi akan mass comm. Allah ya taimakeshi da taimakon Baban yara, ya gama degree dinshi da offer dinshi ta aikin jarida a hannu. Ya fara aikin a gidan jaridar Daily Trust da kafar dama, cikin dan kankanin lokaci ya samu karin matsayi, nan da nan yayi kaurin suna. Ya saye gidansu da suka gada a wajen kawunsu, itama Yaya Sa’a ya sayi nata ya bata kudinta. Yaje aka warewa Jameel nashi, ya tada gini abinshi. A cikin dan lokacin aka yi aurensu da Ameerah. Sun jima suna soyayya da ita, tun yana karatu a abu.
Har gashi a matsayin da yake tsaye a yau. Magidanci ne dan kimanin shekaru talatin da hudu, wanda ilimi na musulunci da zamani ya gogar dashi. Yana fara aikinshi da Daily Trust, ya cigaba da neman kwalin masters dinshi ta online, bayan wannan bai dakata anan ba, yayi kwasa-kwasai da dama da suka kara mishi experience akan aikinshi, da kuma taimakonsu ne da taimakon Allah yake akan matsayin da yake yanzu a wajen aikinshi, Deputy Manager din Daily Trust.
Yana da wani irin hali na son yan uwanshi, zumunci da kyautatawa iyayenshi. Shi yasa har a kullum, Allah yake ta kara mishi budi da haske a cikin al’amuranshi. Allah ya wadata shi da haliita, zubi da kira irin na maza. Idan ka kalleshi sau daya, ba zaka so ka kauda kai ba. Irin halittar jikinshi halitta ce irin one in a million dinnan, kafin ka samu mai irinta sai ka dade. Sai kuwa alamun hutu da kasancewa cikin ni’ima ta rayuwa da suke kokarin boye yawan shekarunshi a duniya, wanda idan ba fada maka aka yi ba, mawuyaci ne ka iya cankar shekarun nashi kai tsaye.
Ta kowane fanni dai, Yaya Bilal irin mazan nan ne da idan mace ta samu irinsu, zata ce Allah ya karbi addu’arta, ya bata miji na kerewa sa’a. Idan kyawun ne, yana dashi, dukiya da rufin asirin ma dai Allah ya bashi, kyawun hali, kamala da nagarta, duk yana dasu. Duk dai wani abu da ake bukata a da namiji, miji na gari, kuma uban ‘ya’ya na kwarai, idan aka zo kan Yaya Bilal dole a diga aya. Sai dai me yasa ni nake kokarin guje mishi tun karfina?!.
A yanzu daya zagaye ni ta ko’ina, duk inda na waiga babu abinda nake gani sai faffadan kirjinshi sai kuwa fuskarshi da sai na daga kai sannan zan iya ganin zagayayyun lebunan bakinshi, ni kuwa banyi wannan gigin ba. Kaina a kasa yake, ina kallon yatsun kafata kamar duk duniya babu wani abu daya kaisu kyawu.
Tattausan kamshin turaren da yake yi a karan kanshi, seems very inviting. Ji nake kamar wani maganadisu ne yake kokarin janyo ni zuwa jikinshi, domin inyi ta shakar kamshin kamar ba zan daina ba, kada ma kuma ayi maganar wannan managarcin kirjin nashi. Da na fara dago da kaina naga zan sauke idanuna akan shi, sai inyi saurin kara dunkufar da kan nawa kasa sosai.
Gashi a bakin hanya muke, mutane suna ta wucewa wanda duk da cewa kaina a kasa yake, amma na tabbatar kallonmu suke yi. Nan da nan nayi narai-narai, idanuna suka kawo kwalla.
Ina tunanin ya kula da hakan ne, ko kuwa wani abu ne na daban? Saboda da sauri naga ya ja da baya kamar wanda wutar lantarki ta ja, hannu daya soke cikin aljihun riga dayan kuma yana shafa bayan wuyanshi sheepishly.
Yace “God, don Allah kiyi hakuri. Amma meye na guduna Na’ilah kamar wani makiyinki?”. Nayi shiru kaina a kasa.
Naji ya ja dogon numfashi ya ajiye, yace “ok…, na ji na kuma yarda ban kyauta miki boye kaina da nayi ba, sai dai bani da zabi ne Na’ilah, nayi tunanin wannan ita ce hanya mafi sauki da zata sa in saba dake. I was wrong ashe!”. Yayi shiru yana kallona, ni kuma dana kasa iya hada ido dashi saboda tsabar kwarjinin da yayi min, nayi kasa da kaina.
Ya sake cewa, “kiyi min alfarma daya mana, ki zo muyi magana a nutse. Kinga nan a bakin hanya muke, sannan mutane suna wucewa ba zamu samu muyi magana a nutse ba!”.
Gabadaya naji jijiyoyin jikina kamar an dauresu. Sai lokacin na dago muka hada idanu dashi, sanyin jikina ya karu, babu ma ta yadda za ayi in iya musawa wannan halittar da take gabana. Saboda haka na gyada kaina kawai, saboda a lokacin babu wata kalma da zata iya fitowa daga bakina.
Ya saki dan murmushi daya sa naji bugun zuciyata ya canza, na kara yin kasa da kaina. Yace “Masha Allah, bismillah!”. Yana yi min nuni da tsallaken titi inda ya ajiye motarshi, ni sam ban ma kula da ita ba sai a lokacin. A hankali na daga kafafuna da nake jinsu kamar babu laka a jikinsu, na bi bayanshi har zuwa inda motar take. Muka jingina da motar, kaina a kasa ina wasa da yatsun hannuna, shi kuma yana ta aikin kallona. Bai yi magana ba, har sai da naji kamar inyi fiffike in bar wajen saboda yadda idanuwanshi dake kaina suka addabeni. Nan da nan naji babu abinda nake so a lokacin kamar kasa ta tsage in shige ciki ta rufe ni.
Sai da ya gama kare min kallo son ran shi, sannan yayi gyaran murya, ya kuma ambaci sunana cikin wata irin murya data girgiza gabadaya sassan jikina. Ban iya amsawa ba, sai daga kai kawai da nayi briefly na kalleshi wanda ko rabin sakan banyi ba na sake sadda kaina kasa.
Yace “Na’ilah kamar yadda na fada miki, ko kuma nake fada miki, takowa nayi musamman domin in baki hakuri. Na yarda cewa abinda nayi was not wise, kuma ba haka yakamata ace na biyowa abin ba. Na fahimci kina fushi, kina ganin kamar kawai ina yi miki wasa da hankaline wanda sam ba hakan bane. Saboda haka ne nake so ki bani izini, in bi ta hanyar data dace. Ina so ki yarje min, in gana da mahaifinki!”.
Nayi gaggawar daga kaina na kalleshi sosai, kamar wadda aka bugawa guduma a ka. Wanda na tabbatar da cewa gurguwar shawara ce, saboda muna hada idanu dashi, I was a goner. Kamar maganadisu, haka na kasa janye idanuwana daga kanshi, ban san me kuma ya hana ni yin hakan ba. Gabadaya sai ma na manta da dalilin da yasa na daga kai na kalleshi har muka hada idanu dashi.
Shi ne ya fara janye idanunshi, sai a lokacin na hau kyafta idanu kamar wadda abu ya fada mata cikin idanu. Dole na saddakar, na ajiye duk wani abu da nake son fada a lokacin na tsaya ina saurarenshi.
Ya cigaba da cewa, “wannan yana daga cikin manyan dalilan da yasa na baro wajen aikina yau, domin ina so ne ace gobe in shaa Allah na hadu dashi munyi magana, mun tattauna an san da maganar mu. Tunda nan da watannin da ba zasu gaza shida ba zaku gama karatu, ina so kafin nan mu samu fahimtar juna a tsakaninmu, ta yadda kina gamawa ba za’a bata lokaci ba, sai kawai a daura mana aure. Ya kika ce?”.
A raina naji wani banbarakwai. Abin dariya wai yaro ya tsinci hakori! Wato shi ana maganar son a san juna, shi ta maganar aure ma yake yi. Kodayake, yayi zancen fahimtar junan ai. Ganin na dauki lokuta ban tanka mishi ba, yasa ya sake cewa “ina saurarenki”, cikin nuna kagara da son jin amsa daga bakina.
Ina so in daga baki ince mishi ni bana son shi, bana son aurenshi kuma bana son zama dashi, amma sam bakina ya kasa motsawa. Don haka na girgiza mishi kai kawai.
Yace “baki son aurena?”. Na gyada mishi kai.
Ya dade yana kallona, har sai da naji na tsargu kafin ya nisa, yace “saboda menene? Na miki tsufa?”.
Naji kamar into kwashe da dariya, wa yake ta wani maganar tsufa a halin da ake ciki yanzu? Balle ma Allah na tuba, wa zai dubi Yaya Bilal a yanzu ya kira shi da tsoho? Ai sai dai mara tsoron Allah.
Don haka na girgiza mishi kai alamun a’ah.
Yace “to idan ba wannan ba, menene? Baki so na?”. Wannan karon ban ce mishi komi ba, a tsaka tsakiya nake. Kowace amsa na bashi yanzu, a tsakiya nake. Idan nace mishi bana son shi, na yiwa kaina karya. Idan na amsa ina son shi kuma, na karyata wani bangare na zuciyata kenan da yake so tun karfinshi ya nuna min bana bukatar shi a cikin rayuwata.
Nan ma ya jima yana kallona kamar wanda yake karanta ta, kafin ya sake cewa “saboda ina da mata ne har biyu?”.
Nan fa ya sosa min inda yake min kaikayi, ba ko sake tunani na gyada mishi kai. Yace “me yasa? Matana zasu hana mu zaman aure dake ne, ko kuma kina tunanin ba zaki samu kulawar da kike bukata daga gareni bane saboda mata na?”.
Ta wani bangaren har da wannan, sai dai wadannan duk sharar fage ne akan babbar matsalar. Wani abin mamaki kuma, sai a lokacin ne naji na samu muryata.
Nace “Babu ko daya, kayi hakuri don Allah. Ba zan iya abinda kake so ba!”.
Yace “amma me yasa? Ina zamu kai son da muke yiwa juna?”.
Nace “ai ana barin halas don kunya!”.
Yace “wace kunya ce za’a bar halas saboda ita? Kada ki ce min wai saboda Ummah ne ko Janan, domin na tabbata su a garesu dauri ne zai tsinkewa mai kaya a gindin kaba. Bayan su kuma ban ga wanda zaki ce zaki zauna jin kunya ba. Idan ke zaki iya kauda kai, ki tuge son da kike min daga cikin zuciyarki, in gaya miki gaskiya ni ba zan iya ba! Don haka tun ma da wuri ki sake tunani”.
Ni kuwa na sake baki kaina a kasa, kunya kamar kasa ta dare gida biyu in afka ciki. Tun da muke da Yaya, da duk sanin dana mishi, bamu taba doguwar magana mai tsayin gaske ba, balle har maganar so da aure ta shigo ciki.
A hankali na fara girgiza mishi kai, nace “ni fa duk ba wannan ba, kayi hakuri don Allah ka rufa min asiri, ka janye wannan maganar a tsakaninmu. Idan kai zaka iya, ni ba zan iya ba!”.
Yace “babu abinda bawa ba zai iya ba Na’ilah, sai wanda kawai yaga damar ba zai iya din ba, sannan wannan magana da muke yi yanzu, babu wani abu da ba zaki iya ba. Zama da nine ba zaki iya ba, ko kuwa zama da kishiyoyin?”.
Na girgiza kai kawai, Yaya Bilal ba zai taba ganewa ba. Ba zai fahimta ba, saboda haka nasan zama yi mishi wani bayani ma bata lokaci ne, don haka nayi shiru kawai.
Ya fara wasu dogayen maganganu akan yadda zai kama min gidana in zauna ni kadai ba tare da takura ba, da yadda zai kula dani. Har dai ya fahimci cewa ba fa saurarenshi nake yi ba, daga karshe dai yace in shiga cikin hostel, zamu sake yin magana.
Ni dama jira nake, na daga kafa da sauri na fada ciki, dama a kagauce nake. Bana so in mishi tsaurin ido ne, in tafi yana cikin yin magana kawai. Har yanzu da sauran mutuncinshi a cikin raina, ina kuma ganin girmanshi.
*☆⋆26⋆☆*
“Wai ni wasu maganganu ne nake ji suna tashi a cikin ward dinmu game dake da Dr. Na Abba. Da gaske ne?”.
Aisha, kawata take tambayata lokacin da muke kan hanyarmu ta dawowa daga cikin asibiti zuwa hostel a ranar juma’ah. Janan ta wuce gida abinta.
Na girgiza mata kai distractedly, “kin san mutane da son yayata abinda ba shi kenan ba, babu wata maganar azo a gani a tsakaninmu, har yanzu tangarda take yi”.
Aisha ta gyada kai cikin nuna fahimta, tace “seriously, I shall warn you though, ana yawan fadin rashin kyawun halayen mutumin nan fa, duk da nima ba gani nayi da idanu na ba, ji nayi ana fada”.
Na gyada mata kai kawai ina dan murmushi na yake, ba ita bace ta farko ba, ba kuma ba yau aka fara tarana da magana makamanciyar wannan ba, duk dai akan Dr. Na Abba. Cikin sati biyun da suka wuce, a kalla mutane fiye da shida, ciki har da Doctors da matrons, sunyi min magana ko ince sun buga min gargadi game da tarayya ta da Dr. Na Abba. Sai dai wani abu da basu sani ba shine, ni dai ba son shi nake yi ba. Ban kuma taba considering din maganar shi ba a cikin raina koda wasa. Saboda haka ni a ganina bata yawun bakinsu ne kawai suke yi, da kuma bata lokaci. Sai dai ban taba fada musu hakan ba, illa iyaka kawai duk abinda suka ce in tsaya in saurara, idan suka gama in musu godiya a wuce wurin.
Yanzu ma abinda na yiwa Aisha kenan, na mata godiya tare da tabbatar mata da cewa zan kiyaye kamar yadda ta bukata. Tace tayi farinciki da fahimtarta da nayi muka yi sallama da ita lokacin da muka shiga hostel, na haye sama ita kuma ta wuce sama dakinta.
Na saka key na bude dakin, kasancewar yau juma’ah, Esther ta tafi weekend, nasan cewa ni kadai zan dinga kwana a dakin daga yau har zuwa ranar sunday.
Na cire kayan jikina na rataye a jikin kusar da muke rataye kayanmu, na saka riga da wando cotton, na barci. Ba sallah nake yi ba, saboda haka lafiyar katifa kawai na bi na kwanta. Na janyo wayata na kunna, na hau chatting, bugs games, kallo, jin wakoki, har kokarin yin reviewing din project work dina dana kammala nayi, amma babu abinda ya dauke hankalina daga kan abu dayan nan da nake ta gujewa; Bilal Al-Qaseem.
Na rasa abinda zan yi akan mutumin nan, Allah ya gani, nayi iyakar kokarina, amma a banza. Gabadaya duk wata idea da tunanin yadda zan yakice duk wasu feelings da nake ji game dashi, na rasa. Duk wata hanya da zan bi, na bi. Amma a banza.
Kullum ta Allah ji nake kamar kara min so, bege, da kaunarshi a cikin raina ake yi. Na rasa kalar wannan masifar.
Wadannan yan lokutan, lokuta ne masu tsananin wahala da ban taba fuskantar irinsu a cikin rayuwata ba. Saboda haka ne na rasa yadda zan tunkari wannan al’amari.
Yaya Bilal ya zamo wata gagarumar wuta da take ci ganga-ganga a cikin raina, amma na rasa kalar ruwan da zai kashe min wannan wuta. Na kuma rasa yadda zanyi, saboda a kullum wannan wuta kara ruruwa take yi a cikin raina, tana kuma kona ni fiye da tunanina. Tana azabtar dani.
Yau dai kwanaki kusan goma sha uku rabon da inyi waya da Yaya Bilal. Tun washegarin ranar da yazo ya turke ni, ya kira ni. Lokacin muna cikin yin wayar, I snapped. Ban san lokacin dana mishi tsawa ba. Yana magana ne akan da gaske yana son aurena tsakaninshi da Allah, ya dage akan ba zai hada mu waje daya dasu ba, zai min nawa gidan daban. Ban san abinda ya shiga kaina ba a lokacin, su kansu kalmomin dana furta ban san na fade su ba sai bayan da suka fita daga bakina, nace “Wai ana dole ne? Ko kuwa ance maka ban san ciwon kaina ba? Dole ne? Ka kyaleni don Allah, nace maka bana son ka!!”.
Nayi shiru ina sauke ajiyar numfashi kamar wata kumurcin macijiya.
Yaya Bilal shiru yayi a lokacin, kusan mintuna biyu tsakanin ni da shi babu wanda yayi magana. Sai sautin saukar numfashinmu dake tashi kawai. Daga baya ma sai ya kashe wayar shi, bai ce komi ba.
Daga wannan rana bai sake kirana ba, ban sake ganinshi ba.
Daga farko cewa nayi tafi nono fari tas. Sai dai me! Ba’a cinye kwararan kwanaki biyu ba, jikina yayi sanyi da jin yanayin shirun da yayi. Ban san me yasa na damu ba. Haka zan saka wayata a gaba ina kallo sau tari, ina contemplating din in kira shi ko kuma in kyale shi. Komi da yake faruwa a lokacin sabo ne a gareni, wanda ban taba experiencing dinshi ba a tsawon rayuwata. Ko rabuwar mu da Umar, ban ji kwatankwacin abinda nake ji a halin yanzu ba. Duba kuma da tsawon lokutan da muka dauka tare da shi, da kuma wanda muka dauka da Yaya Bilal, abin mamaki ne.
A kwanaki na hudu sai gani kunshe akan katifata cikin dare ina shakar kuka na fitar hankali. Kamar wadda aka sanarwa da wani babban jigo nata ya bar duniya. A lokacin kukan shine kadai abinda nake gani mafita ce mai kyau. Bayan nan barci ya kwasheni, wanda washegari na tashi da ciwon kai mai zafi da kumburarriyar fuska. Tun daga wannan ranar har yau ban daina yin wannan ciwon kan ba.
Janan, dama duk wani wanda ya sanni, ya san irin natural cheery behavior dina, yasan cewa wadannan yan kwanakin ba lafiya ta lau ba. Duk wanda muka hadu dashi sai ya tambayeni, lafiya?. Tun ina murmushi ina basar da maganar, har na gaji, idan ma an tambayeni sai dai kawai in kalli mutum blankly ko kuma kawai in basar in ki amsa tambayar, yaudarar kaina kawai nake yi, ba lafiyata lau ba. Ta yaya ma zan zauna lafiya bayan na ki ba zuciyata abinda take muradi?.
Yau Janan ta gayyaceni zuwa Kaduna mu yi weekend a can, sai dai kai tsaye nace mata ba zan je ba. Tunanina daya, idan fa naje muka hadu da Yaya Bilal acan? Me zan yi, ko kuma me zan ce mishi? Ita kanta Ummah ban san da wani ido zan kalleta ba idan naje, don haka duk da ina son zuwa, haka nan nace mata taje ni ina da abubuwan yi. To itama bata matsa ba, tace to, muka yi sallama ta tafi.
Itama na kula tun maganar nan da muka yi da ita ranar da Yaya Bilal zai zo, bata kara tado min zancen ba. Amma kuma gabadaya sai nake ganinta kamar ba Janan dita ba, kamar ta canza. Duk da bata fito kai tsaye ta nuna min wata canjin fuska ba ko wani abu, amma she just seems very distant.
Shi yasa nake jin kamar an dauko duk wani nauyi da damuwa ta duniya an dora min. Duk duniya, Janan ita kadai ce abokiyar shawarata. Kafin in nemi Kulsum ko Yaya Mudatthir ko Fatsu da suke manyan abokan shawarata, da wata shawara, Janan nake fara nema. Mu zamu kashe mu binne a tsakaninmu babu wanda ya sani balle yaji labari, sai idan tayi wari ne a mafiya lokuta suke ji.
Yanzu kuwa da babu ita, sai naji kamar komi ya hargitse min.
Nasan babu ta yadda za ayi in nemeta da shawara game da dan uwanta, bayan duk wasu abubuwa da maganganun da nayi game dashi. Nasan ranar na bata haushi ba karami ba, amma kuma ai gaskiyata na fada mata ba wani abu ba. A tunanina zata fahimceni, nayi zaton zata fahimci inda na saka gaba. Sai dai abinda na manta shine, dan uwa, dan uwa ne. Yaya Bilal dan uwan Janan ne, hakan yana nufin cewa ko a halin runtsi da wuya, zata iya zabar Yaya Bilal da gudu ta barni. Balle wa zai juri yaji kalmar rashin so zuwa ga Yayanshi da yake matukar so da girmamawa na fita daga bakin abokinshi? Babu.
Shi yasa na fahimceta, ban kuma ji haushinta ba. Shi yasa nima ban kara tada mata maganar ba, kunya ma ba zata barni ba. To wai ma ince mata me? ‘Ni fa tunanin Yayanki ya ki barin zuciyata, kuma lokaci na karshe da muka yi waya dashi na zabga mishi rashin mutuncin da bai cancanta ba, shi yasa bai sake bibiyar rayuwata ba har yanzu, me kike tunanin yakamata inyi yanzu!’, yeah, da alamu na fara rasa alkiblata ma ni yanzu.
Tun wannan kwanciyar da nayi, ban motsa ba. Sai da Janan ta kira ni, lokacin har duhun dare ya fara shigowa sannan na motsa. Wuyana ya amsa da ciwo saboda kwanciyar da nayi a gefe daya na tsawon lokaci ba tare da na motsa ba, haka nan ina yamutsa fuska na dauki wayar muka gaisa. Ta sanar dani isarta gida kenan, na mata sannu da zuwa tare da sakon ta gaida su Ummah.
Muna cikin maganar na jiyo sautin muryar Yaya a can background din wayar, kamar ma dariya yake yi lokacin. Naji kamar anyi freezing din komi da kowa a lokacin banda ni dashi, muryar Janan ta dauke kamar bata wajen, babu abinda nake ji a cikin kunnena a lokacin sai sautin tattausar dariyar Yaya Bilal da take tashi a lokacin ina jinta kamar busar sarewa saboda yadda take tashi very deep, very soothing.
Ban san dalilin da yasa naji kwalla mai zafi ta ciko min idanu ba, amma zata iya yiwuwa saboda tsananin dadi da salamar da naji sun sauka a cikin zuciayata ne a lokacin, ban taba tunanin zan ji dadin jin muryar wata halitta a doron kasa bayan dogon lokaci da muka dauka ba tare da mun hadu ko mun ji muryar juna kamar yadda naji dadin jin muryar Yaya Bilal yanzu ba, ban taba ba.
Allah ne ya bani ikon dawowa cikin hayyacina kafin Janan ta fahimci wani abu, ko kuwa ta fahimtar kyaleni kawai tayi? Koma dai menene ban damu ba a lokacin, damuwata daya a lokacin inyi gaggawar katse kiran wannan kafin jin muryar Yaya ta sanya ni yin abinda ban shirya yi ba, ni da nake gudunshi tun karfina, in kare da making fool out of myself.
Don haka nayi gaggawar yin sallama da Janan, tana tambayar lafiya? Ina lalubo dalilin da nasan ko dan jariri haihuwar yau ba zai yi convincing ba na jefa mata, na kuma kashe wayar ba tare dana jira abinda zata ce ba.
Lokacin dana koma kan katifa na kwanta, idanu a lumshe, hannu daya dafe da gefen kaina da yake bugawa, zuciyata da wani irin nauyi kamar an dauki wani gungumemen dutse an aza mata, babu abinda yake cikin raina sai tunanin azabar bata isa ba haka ba? Anya, ba zan nemawa zuciyata sanyi ba??!.
~Am really, very, very sorry. Please ku yi maneji da wannan, in shaa Allah gobe zaku samu dogon feji.
*☆⋆27⋆☆*
Ranar Lahdi a cikin makaranta na yini. Tun wajen karfe goma sha daya na safe na tafi wajen Aylah, tsohuwar room mate dina wadda muka zauna da ita last year. A wajenta na yini, muka sha hirar yaushe gamo da ita. Da yammaci kuma na tafi wanke kaina saloon din cikin makaranta.
Tashin hankalin dana shiga cikin yan kwanakin nan, ba muhimman al’amura kadai na banzatar ba, har ma da kananan irin wanke kai da yanke farce na manta. Ban ankara ba sai da naji kaina yana masifar tashi, sannan.
Da yake akwai wata mata dana saba zuwa wajenta tun ma muna cikin makaranta, nasan duk da cewa yau Lahdi ce tana nan saboda musulma ce ita. Don haka kai tsaye na wuce shagonta. Abinda naci karo dashi ne a gabana daga shiga cikin shagon, ban shiryawa ba.
Adi, Raheemah da Salamah a zaune akan kujerun jira da aka tanada a shagon, yayin da ake wa Adi karin gashin kanti a kanta. Muka tsaya muka danyi kallon-kallo dasu, kafin muka kauda kanmu mu duka, babu wanda ya nuna alamun yasan wani. Na dai musu sannu, nima kuma na samu waje can gefensu na zauna.
Rabon da in gansu su dukansu, tun azumin farko da naje gidansu, gashi yanzu har muna tunkarar watan Zhul-Hijja nan da yan kwanaki.
Ina nan zaune ina wasa da wayata kawai, ina sauraren hirar da suke tayi da yake mu kadai ne a cikin shagon. Tsantsar gulma ce suke yi, wadda nafi kyautata zaton akan Haleemo ce, babu kunya balle tsoron Allah. Wani karin abin haushin shine, Raheemah tana fita domin ta dauki kiran da aka yi mata a waya, suka ajiye hirar Haleemo gefe suka dasa tata. Na girgiza kaina cike da takaicin halayya irin tasu, ku a tsakaninku kuna a matsayin yan uwa babu aminci da amana, ina ga wadanda ba yan uwansu ba kuma?.
Kafin kace me, naji na kosa da zama wajen, da ba don na riga na shigo wajen ba da wallahi baya zanyi.
Allah ya taimaka ba’a jima ba wata daga cikin yan aikin wajen tazo ta kama kaina. Ta tambayeni retouching zanyi ko kuma wankewa kawai? Nace mata wankewa, don ni koda wasa ban taba sanyawa kaina relaxer ba. Yanayin natural santsi da laushin shi yafi yi min.
Na cire gyalena na ajiye a gefe, muka koma can gefe inda ta wanke min shi tas, muka koma tayi drying. Tana gama gyarawa, na sallameta na kara gaba na barsu acan.
Ina fita na sake cin karo da Haleemo, wani mutum daga ganinshi babba ne ya sauketa a mota, itama dai kallon-kallon muka yi, na tabe mata baki na wucewa ta.
Sai da nayi sallar magriba anan sannan na koma cikin asibiti.
*
Washegari da safe bayan duk mum gama ayyukan da suka kamata muyi a cikin ward, su dressing, bada magungunan yara majinyata da sauransu dai, duk muna zaune a nurses station. A yanzu wani yaro da ake yiwa blood transfusion muke monitoring dinshi duk bayan mintuna sha biyar, don haka muke zaune kusa da wajen.
Wasu matrons ne su biyu daga can gefenmu, suna ta zuba hirarsu. Da alama daya daga cikinsu ce aka yiwa aure, yanzu haka tana kan yin hutun amarcinta ne.
Sister Mairo ce take cewa “… Ai ina gaya miki, daga zuwanta sai ga mata a kicin washegari tana girka abinci, ba fa nata ita kadai ba, wai har uwargidan da ‘ya’yanta saboda uwargidan ta tashi da ciwon ciki. Nace to a haka za’a ci amarcin ne? Me zata ji, me zata karas? Allah na tuba duk wanda bai ji dadin kwanakin nan bakwai na aure ba, ai bai ji dadin amarci ba!”.
Daya sister din da ban san sunanta ba ta kwashe da dariya, tace “maganinta kenan ai. Nan muka zo, wace irin nasiha ce ba’a mata ba akan Alhaji Mati? Amma ita ta nace ta kekashe kasa, wai mutum mai mata ko wanda ya taba yin aure is more responsible, waye da waye, gashi nan ai tun ba’a je ko’ina ba, zata zama yar bauta. Ai ni wallahi inaa, Allah ya tsare ni wallahi. Ko a lokacin da Abban su Humairah yake ihun mata biyu zai aura ban ko daga ido na kalleshi ba balle in wani daga jijiyar wuyana, abu daya na sani koma mata nawa dai zai aura, anan zasu zo su sameni dai. Sai na gama tsintar abinda zan tsinta, na gama morewa mijina yadda naso sannan in bar mata sauran. No biggie!”. Suka sake sakin dariya.
Ina kallon yadda Janan take watso min wani irin kallo daga can kasan idanuna. Ban san abinda take sakawa ba a cikin ranta, bana kuma fatan in sani. Don haka nayi shiru, kunnuwana duka biyun akan hirarrakin da su sister Mairo suke yi, wanda yawancin hirar akan ire-iren abubuwan da suke yawo ne a cikin raina.
Har dai lokacin da zamu sake duba yaron nan yayi, muka dauki abubuwan da zamu bukata ni da Janan muka je muka duba shi tare da rubuta cigaban da aka samu game dashi, muka fito.
Muna fitowa, muka ci karo da Dr. Na Abba, ya ja ya dakata yana kallonmu cikin murmushi, “hey, ‘yanmata!”.
Ni da Janan muka maida mishi martanin murmushin tare da gaida shi ya amsa. Janan ta dan yi gaba kadan, ni kuma na dan dakata haka nan muka gaisa. Bamu ja hirar da tsayi ba, saboda yace yana da patients amma yayi min alkawarin sake zagayowa zuwa anjima, nace mishi babu damuwa. Ya wuce, ni kuma na daga kafa na karasa wajen Janan muka cigaba da tafiya zuwa wajen da muke zaune.
Zuwa lokacin da muka koma, su Sister Mairo sun canza hirar da suke yi zuwa ta sana’o’in hannu.
Muna sake komawa wajen yaron a karo na hudu, muka tarar an gama mishi transfusion din. Saboda haka bayan munyi handling din bayanan yaron wajen likitan daya duba shi, ni da Janan muka wuce masallaci domin raka Janan tayi sallar azuhur.
Bayan tayi sallar, muna kan hanyar dawowa, Janan ta kalleni, tace “na yi zaton zaki sayi wani abu ki ci tunda ba azumi kike yi ba yau?”.
Tunda muka fito waje sai lokacin tayi min magana. Na girgiza mata kai a sanyaye, nace “bana jin yunwa!”.
Daidai lokacin mun je wani dogon corridor, Janan taja ta tsaya tana fuskanta ta. Tace “kada ki ce min rashin son auren Yaya da kike yi, yana da nasaba da maganganun da su sister Mairo suka dinga yi dazu?”. Na zuba mata idanu kawai ina kallonta.
Tace “Na’ilah, haba don Allah! Wa yace miki rayuwa zata tafi a haka ne? Da dai nayi shiru in ga iyaka gudun ruwanki ne, amma da alamun baki da niyar tsayawa a matsaya daya, don haka na gaji da kallonki haka nan. Duk kin bi kin kwarzabi kanki Na’ilah, kin hana kan ki sukuni, kin hana kanki kwanciyar hankali, haka ake yi dama? Wai a kanki ne mai mata ya fara neman auren budurwa ne? Shi Yaya Bilal din ba mutum bane? Mutum ne shi, guda dayan shi sukutum. Amma ke kin hana kanki kwanciyar hankali, kin hana na kusa dake samun nasu kwanciyar hankalin saboda wani dalili naki mara fa’ida!”. Tayi shiru tana ajiye numfashi. Har yanzu ban ce mata komi ba, ban ma yi yunkurin tanka mata ba.
Tayi kwafa, “to naji. Ina ce kin ce baki son Yayan? Kin ce ya kyale ki? Ba ya kyale ki din ba? To kuma menene na sanya kanki cikin damuwa? So kike yi ya dinga bin ki duk inda zaki je, kina wulakanta shi Na’ilah? Meye haka kike yi wai?”.
Nan ma na sake yin shiru, haka kawai naji kwalla ta ciko min idanu, na sadda kaina kasa ina sauraronta tana zuba bayanai. Ni kaina a halin da ake ciki yanzu, ban san me nake tunani ba, ban kuma san me nake so ba. Ina son Yaya Bilal ya cigaba da kirana, ya cigaba da kulawa da ni, ina son in kasance dashi. Sai dai a duk lokacin da tunanin zama da kishiyoyi musamman irin su Ameerah da Raheemah ya fado min cikin raina, sai inji duk wani abu da nake ji game dashi ya bi iska.
Darare da dama da na sha zama, ina kokarin lallashin kaina, sai dai I just can’t bring myself to do that! Na kasa! A duk lokacin dana tuna da irin ukuba, tashin hankali, damuwa da rikicin da muka shiga ciki, ko kuma wanda muke ciki har yanzu a gidanmu, wanda kishiyoyi ne suka yi sanadin haka sai inji zuciyata ta dugunzuma, inji hankalina ya tashi.
Jin shirun da nayi, yasa ta dafa kafadata, tare da tallabo kaina da hannunta daya. Bani da zabi sai na daga idanuna da suka cika da kwalla na sauke a kanta.
Ta girgiza kanta, tace “wallahi mamaki kike bani Na’ilah. You are just beating yourself akan abu mai sauki. Sai me don Yaya Bilal yana da mata? Ke yanzu ba abin alfahari bane a gareki, mutum kamar Yaya Bilal ya so ki, ya sadaukar da muhimman bigire nashi a kanki? Ba yabon kai ba, Yaya Bilal kyakkyawan mutum ne, mafarkin kowace diya mace. Amma ke ga damar samunshi a ruwan sanyi kin samu, kin zauna kina jan aji da kawo wasu dalilai naki da basu da makama ko kadan. Gaya min, matan shi ne, rashin haihuwar da baya yi ne, ko kuma shi a karan kanshi ne?? Idan mata ne, yace miki ba a waje daya zai hada ki dasu ba. Idan kuma haihuwa ce, ina mai tabbatar miki da cewa Yaya Bilal lafiyarsa lau, Allah ne bai kawo mishi haihuwa ba har yanzu. Idan kuma shi dinne, menene aibun Yaya Bilal saboda Allah? Ni dai nasan Yayana mutum ne mai nagarta, sai dai idan anki Allah ne za’a ce bai yi ba!”.
Tunda ta fara maganar nake girgiza mata kai, amma banyi yunkurin katseta ba sai data dire aya. Nace “ban taba tunanin kin Yaya saboda rashin haihuwa ba, ita haihuwa nasan ta Allah ce, duk kuma kokarin mutum, idan Allah bai mishi baiwar haihuwar ba, babu abinda zai iya yi game da hakan sai dai hakuri kawai. Don haka ban taba yin wannan tunanin ba. Sai dai kamar yadda kika ce, yes matan Yaya, sannan shi a karan kanshi ba tsaran aurena bane. Meye hadin biri da gada idan ba rigima ba? Daidai ruwa daidai tsaki, sai kiga an zauna lafiya. In gaya miki gaskiya Yaya Bilal ya fi karfina.
Ba son kai ba, aure nake so inyi mai cike da kwanciyar hankali Janan, ba zan baro masifar kishiya ba, sannan kuma in fada cikin wata wadda ma tafi waccan, kuma ina sane. Idan nayi haka ban yiwa kaina adalci ba. Na fa san komi Janan, ba yau aka auren soyayya ba a gaban idanunmu ba, amma tun kafin aje ko’ina kiga labari ya sha banban. Wannan wadanda ba zaune suke da kishiya bama fa kenan, ina ga wadanda zasu zauna da kishiya? Allah ya gani, so nake in shimfida rayuwar aure mai ma’ana, daga ni sai mijina sai ‘ya’yan da zamu haifa. Wannan itace rayuwar dana dinga hangowa kaina Janan, bana kuma tunanin zan iya kauda kai, ina ji ina gani, in kai kaina cikin kabari na!”.
Ina dire maganar ta tare ni, “to wa yace miki ba zaki iya irin rayuwar da kike hangowa ba da Yaya Bilal? Kin gwada ne kin gani?”.
Nayi dan murmushi cike da kunar zuciya, nace “Janan kenan! Ke baki san kaidi irin na kishiya ba, baki san komi game da sharri da kissa da kisisina irin ta kishiya ba, bana kuma tunanin zaki taba sani. Don haka ki kama bakinki kawai ki ja, ni naga abinda na gani da idanun nan nawa, abinda na gani kuma ba abu bane mai kyau, don haka tarihi fa ba zai maimaita kansa a kaina ba Janan! To dame ma zan ji ne? Da miji zan ji, ko kuwa tashin hankalin kishiya? Barni dai inji da abu daya, hankalina zai fi kwanciya!”.
Janan kallona take yi kamar wata sabuwar halitta, nasan yadda na hakikance ne abin yake bata mamaki. Bazan damu ba though, ance wai riga-kafi yafi magani, kuma hanyar lafiya a bita da shekara. Gwanda dai in tsaya kyam akan ra’ayina, idan zuciyata ta fara rawa akan wannan maganar, me zai faru kenan? Na san it’s only a matter of time, da zan manta da wani Yaya Bilal. Balle duka mai ya rage mana a Zaria? Yan watanni ne kawai. Idan na samu na lallabi zuciyata, na lallaba na bar Zaria, nasan ikon Allah ne kawai zai sake dawo da ni cikinta. Kenan idan na tafi, ta ina zan ga Yaya balle har wani tunanin zama dashi da masifaffun matanshi ya darsu a cikin raina? Abinda nake bukatar inyi kawai shine in daure, in kuma yi kokarin mantawa dashi.
Sai dai fadar, tafi aikatawar dadin fada.
Janan ta girgiza kanta cikin rashin sanin abin cewa, tace “gaskiya kinyi nisa da yawa, Allah ya ganar dake”.
Nima na girgiza mata kaina, nace “ba zaki taba ganewa ba Janan, ba zaki gane ba!”.
Bata ce komi ba, ta cigaba da tafiya. Nima na bi bayanta.
Tun daga wannan yar sa’insa da muka yi, babu wanda ya sake tado maganar har lokacin tashinmu yayi. Kai babu ma wata doguwar magana data sake hada mu da ita, naga kamar ma wani haushi na take ji. Ni ma da yake raina a dagule yake, ban wani damu ba. Lokacin tashi yana yi, na bar ward din. Ranar ko sallama bamu yi ba.
Ina komawa daki na dora indomie, ba wata yunwa nake ji ba, amma tunda ranar garin yau ta waye babu komi a cikin cikina sai biskit din pure bliss da hot chocolate. Ina gama dafawa na dora ruwan shayi, na dauki lemun tsami na matse a cikin shayin na juye a cikin mug. Dana gama na daukesu zuwa gefen katifata na ajiye, ni kuma na zauna. Laptop dina na dauka na kunna kallon wani American film, ‘Another Cinderella Story’ na fara kallo ina kuma cin indomin. Kallo kawai nake yi, amma bana wani fahimtar kallon. Har na gama na kauda kayan, na dawo na cigaba da kallon. Ina nan zaune Esther ta dawo, na mata sannu da zuwa, na maida hankalina kacokam ga film din da nake kallo don bani da kuzarin zama yin hira da ita. To da yake ma ba zama ya kawo ta ba, kayan jikinta kawai ta canza ta sake fita.
Ina cikin yin kallon barci ya kwashe ni.
*☆⋆28⋆☆*
Ban jima da fara barcin ba amma, kiran daya shigo cikin wayata ya katse min shi.
Na zabura na tashi zaune tare da lalubar wayata, duk da kalar ringtone din, hakan bai hana ni kara duba sunan mai kiran ba domin in tabbatar da cewa da gaske ne ba mafarki ba.
Ban san dalilin da yasa na kasa goge lambar Yaya Bilal daga cikin wayata ba, kai ko suna har yanzu ban iya canza mishi ba. Har yau ‘Muhammadu na’ ne a jiki, shine kuma yake tsalle yana karawa akan screen din wayata.
Duk da tsananin rawar da hannuna yake yi, da yadda zuciyata take bugawa, da yadda nasan bani da abinda zan ce mishi, hakan bai hana ni dagawa ba.
Hatta da muryata rawa take yi lokacin da naji muryarshi tana ratsawa ta cikin dodon kunnena, na amsa cikin sanyin jiki da murya. Yaushe rabon da inji wannan muryar? Ji nake kamar na shekara da shekaru.
Yaya Bilal yace “hmmm, Na’ilah kenan, manyan kasa. Kin gama fushin ne?”.
Nace “fushi kuma, fushin me zan yi?”.
Yace “nima ban sani ba Na’ilah, kawai dai nasan kina yin fushi. Amma duk ba wannan ba, kina ganin zamu iya magana yanzu? Are you ready for that?”. Nayi shiru ina sauraronshi, ina tunanin ya dauki shirun da nayi a matsayin go ahead, don haka ya fara magana.
Yace “ba kya ganin it’s high time, mu ajiye duk wasu abubuwan da suka faru a baya a bayanmu mu fuskanci gaba? Bai kamata ace muna ta tsalle-tsalle a waje daya ba kamar kananan yara, please let’s do this like the matured people we are!”.
Tabdijam! Naji wani kululu ya makale min a makoshi, cikin nuna alamun bacin rai nace “kana nufin kace min ni yarinya ce ko kuma ina dabi’a irin ta yara?”.
Yace “ban ce ko daya daga ciki ba, illa iyaka ina so in nuna miki cewa wannan kauce-kauce da kike yi babu abinda zai haddasa mana sai bata lokacinmu da yake yi kawai. Na’ilah, mu fa ba kananan yara bane, bai kamata ace mun dauki magana daya muna ta nanata ba, bayan muna da yadda zamu fuskanci matsalar mu kuma magance ta. Saboda haka yanzu ki fada min, meye matsalar ki game dani? Kin san ina son ki ko?”.
Amsar dana bashi ta fito daga cikin bakina tun ma kafin in tauna ta, kai ban ma san na fade ta ba sai dana ji tana ringing a cikin kunnuwana, da kuma shirun daya biyo bayan na furta ta, da alamun shi kanshi bai yi tsammaninta ba; “nima ina sonka!”.
Kusan sakanni biyar da fadin hakan, kafin naji yayi gyaran murya, ni kam sai aka barni da kyafta idanu, yace “good. To menene matsalar? Na riga na fada miki idan ta matana ne baki da matsala da su, gidan ki daban zan ware miki, ba lallai sai kun hadu dasu ba. Wannan ganin damar ki ne, idan kin so haduwa dasu sai ki hadu dasu, idan baki so ba, sai kiyi yadda kike so. Bayan wannan kuma sai me? Ban takura ki ba Na’ilah, zan jira ki gama karatunki kafin a tado maganar auren, bayan nan zan bar ki kiyi aikinki, ba zan hana ki ba. Sai me kike bukata kuma?”.
Shi a tunaninshi rashin hada mu gida daya kamar wani solution ne, sai dai a nawa tunanin, wannan ba komi bane. Ya hada mu gida daya ko bai hana ba, duk dai yana da mata ne dai, kuma zamu yi sharing dinshi dasu. Na daga baki nace “bani da wata matsala Yaya, kayi hakuri. Nima ba wai ina jindadin wasa da hankalinka da nake yi bane, amma the fact that zan zauna da kishiya daya ma bana so balle kuma har biyu, kayi hakuri don Allah”.
Yace “shi kuma son da muke yiwa juna fa? Kin kasa daukar matsaya daya Na’ilah ki zauna a kanta, daga yau kice wannan, sai gobe ki ce wannan. Kina ganin ina da lokacin zama bin kanki ne? I can’t leave my work da duk wasu harkokina, ina chasing dinki Na’ilah! I just can’t. Don haka idan zaki zauna ki yanke shawarar da zata fisshemu, gwanda ma tun wuri ki yanke. Haba! Na gaji! Na gaji wallahi!! Wai baki da zuciyar tausayi ne? Ko ke baki san kaddara ba ne? Kada ki manta da cewa Annabinmu ma da muke yin koyi da koyarwa shi bai zauna da mata daya ba. Ke a ganinki rashin zama da kishiya zai hana ki rayuwar farinciki a gidan aurenki bane ko me? Kina ina mata da dama suke baro gidan auren nasu babu kishiya ba kome, gasu nan birjik suna yawo akan titi muna ganinsu, amma kuma masu kishiyar suna zaune a nasu gidan salin-alin suna zaman lafiya? Kin kishiya da kike yi kamar izgilanci ne kike yiwa Allah, tunda kin karanta, kin kuma san cewa ba haramun bane a musulunci. Ita kishiyar hauka ce?!”.
Yadda ya hakikance yana fada yasa naji nima raina ya dauko baci, a tunanina idan ba’a lallasheni ba, bai kamata ace za ayi min ihu ba. Nace “da kake maganar kaddara da kuma izgilanci, shi Allah ai baya dorawa rai abinda ba zai iya dauka ba sai dai bawa ya dorawa kanshi. Saboda haka ina ji ina gani ba zan kai kaina wajen wahala ba. Tunda nace ka kyaleni, bana so, ba sai ka kyale ni din ba? Ana dole ne?!!”.
Yace “haka kika ce ko? To ba laifi. Dama ina bin kanki ne kawai saboda kada kice anyi miki rashin adalci ko wani abu, amma tunda ke kunnenki na kashi ne, kuma idanuwanki a rufe suke, ba kya fahimtar komi, to zan biyo miki ta hanyar da baki so. Idan ke kin iya yiwa zuciyarki rashin adalci ne, ni ba zan cuci kaina ba akan wani dalili can naki! Ina ce ba mahaifinki ne da bakinshi yace ba zaki aureni saboda ina da mata ba ko? Kuma ba Allahn daya halicce ki bane? To ki kashe kunnenki da kyau, ki saurareni kiji, maganar neman aurenki yanzu na fara ta, ba kuma zan tsaya ba sai inda karfina ya kare. Zan kuma yi duk abinda zan yi in ga cewa kin shiga gidan da kike matukar ki, don Allah ki kashe kanki ranar da aka kaiki gidana a matsayin matar aure, sai in ga karshen tsana!”.
Nace “Wallahi ba zai yiwu ba, ba kuma zan yarda ba. Ni dama nasan ba sona kake yi ba kamar yadda kake ikirari, in Allah ya yarda sai Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu. Mugun kudirinka ba zai cika a kaina ba!”.
Yace “zamu gani Na’ilah!”. Daga haka ya kashe wayar.
Naji kamar in fasa ihu, jikina har rawa yake yi tsabar bacin rai. Lallai Yaya Bilal has got some nerves! Har yana da bakin da zai daga yace wai zai aureni ba da izinina ba? Har yana da wannan ikon a kaina?! To ai idan yasan wata bai san wata ba. Zan ga da abinda yake takama dashi kuwa!.
Na share hawayen da suka zubo min, na kara daukar wayata da nayi jifa da ita, na shiga cikin contacts dina. Ina ganin sunan wanda nake bukatar gani, na danna kiran ba tare da bata lokaci ba. Tayi kara daya, biyu, ana uku aka dauka.
.Cike da cheeriness da alamun tsokana da baka taba raba muryarshi da ita, yace “hello, Nas. Ya kike?”.
Na dauki ajiyar numfashi na sauke a hankali, na dan kakaro murmushi duk da nasan cewa ba ganina yake yi ba, nace “hello Doctor, maganar ganin iyayena da kayi ranar nan, ka shirya yi yanzu?”.
Yace “of course Na’ilah! Dama ni ai jiranki kawai nake yi. Yaushe ake bukatar gani na ne?”.
Nace “idan ma a gobe ka shirya, zaka iya zuwa ka gansu”.
Yace “Masha Allah, that’s good. How about in zo anjima sai mu sake tattaunawa akan yadda za ayi?”.
Na dan jinjina kai sama, “yeah, hakan ma yayi. Sai ka zo kenan?”. Yace “in shaa Allah. Gani nan zuwa”.
Nace “sai kazo!”. Na ajiye kan wayar.
*
Kwana uku bayan haka, Janan ta shigo asibiti tun da safe ranar alhamis. Abin ya bani mamaki. A bakin hostel muka ci karo da ita, ni zan fita ita kuma zata shiga. Na kalleta cike da mamaki, nace “lafiya kuwa? Mai ya shigo dake nan da wuri ne?”.
Bata tsaya amsawa ko yi min bayani ba, taja hannuna muka koma daga ciki, can gefe, tace “abinda kika yi kina ganin shine daidai a wajenki?”.
Nace “me nayi?”.
Tace “Yaya Mudatthir ya kira ni dazu tun da sassafe”.
Sai lokacin na fahimci dalilin shigowarta din da kuma tambayoyinta. Nima bamu jima da yin wayar dashi ba.
A yadda muka yi da Dr. Na Abba lokacin da yazo ranar litinin, mun tsaya akan cewa zai je Gashua ya samu su Malam su akan maganar mu. A washegari talata na kira su Fatsu na sanar dasu bakin da zasu yi, zai je ne kawai suyi magana, a san dashi, sannan a tsaida ranar da yakamata magabatanshi su je. Su Malam suka yi farinciki matuka, har Fatsu tana cewa har ta cire rai da zaton zata ga wannan rana, ni dai kawai uhmm nace mata.
A daren ranar jiya bayan Dr. ya kira ni ya sanar dani cewa sun dauki hanyar Kano daga Gashua, Yaya ya kira ni. Tambayata kawai ya hau yi akan wai na tabbatar da cewa wanda na turo mishi na amince dashi? Nace ta yaya zan tura wanda naji ban aminta dashi ba wajen iyayena?. Yaya yayi shiru kamar ba zai yi magana ba, kafin yace “amma kuma Baba yace wani yaje wajenshi a jiya din, shima duk akan maganar ki ne!”.
Naji an fara min wani luguden daka a kirji, ashe dai Yaya Bilal da gaske yake ba da wasa ba. Amma a zahiri sai na dake, nace “ni fa bansan ko wanene ba, don ni babu wani wanda muka yi magana dashi akan zai zo bayan Dr. Na Abba”.
Yaya yace “to ai shikenan”.
Daga nan muka dan yi hira, na tambayeshi jikin Sailu da har yanzu tana asibiti. Yace dukansu lafiya lau. Sannan muka yi sallama.
To yau kuma da safe sai ya sake kirana, yana tambayar wai dama wanda yaje wajen Baba Yayan Janan ne? Nace “ni fa Yaya na fada maka ban san kowanene ba”.
Yace “kada ki raina min wayo mana Na’ilah. Ni nasan yadda kika sako karatun nan naki a gaba, maganar aure yanzu bata cikin kanki. Tunda naji dama wai kin turo wani gida kai tsaye, nasan da wata a kasa. Don haka ki fada min abinda yake faruwa”.
Nace “to ni Yaya sai dai kuma in karya kake so in maka, amma babu abinda yake faruwa. Kawai na samu wanda hankalina ya kwanta dashi ne, dama can don dai ban samu wanda ya shiryawa auren bane”.
Yace “ina wannan yaron da kuke tare dashi kuma fa, sojan nan?”. Nace “ni tun yaushe da muka rabu dashi?”.
Yaya Mudatthir yace “shikenan Na’ilah, ni dai ina shawartarki da ki bi koma menene a hankali!”. Bai jira abinda zan ce mishi ba ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo cikin yamutsa fuska, me yasa ne yake wani magana yana bani a linke? Sai ban saka maganar a kaina ba, naci gaba da shiryawa ta.
To kuma gashi ina fita naci karo da Janan, itama tana bani tata linkakkiyar maganar.
Nace mata “eh, ina ganin shine mafi a’ala a wajena Janan. Ina ganin kuma hankalina zai fi kwanciya a hakan”.
Tace “ki dai bi a hankali, kada kije ganin neman gira ki rasa idanu. Ki gujewa garwashi ki fada cikin wuta!”.
Na dan jefa mata harara, “ni fa saboda wutar da Yayanki ya hada min yan kwanakin nan, kwalwata bata gane maganganu masu baki biyu. Don haka ki daina bani a dunkule kawai ki fito ki min magana kai tsaye don bana fahimtarki”.
Itama ta harareni, tace “shi wanda kike likewa din, kina da tabbacin zai rike ki kamar yadda kike hange ne? Kin kuwa san waye Dr. Na Abba? Shekarunshi talatin da biyar, aurenshi bakwai Na’ilah! Aure bakwai! Amma yanzu bashi tare da mata ko guda daya sai ‘ya’ya kashi-kashi dake gaban mahaifiyarshi wadanda matanshi suke ajiyewa idan suka rabu. Kin san me yake hada shi da matan har su rabu? Kika sani ko yana da wasu halaye da basu dace bane shi yasa? Kina da tabbacin ke idan kika aure shi a hakan, zaki zauna a gidanshi ne? Wallahi ina jiye miki yin dana sani Na’ilah”.
Nace “na farko ba ni na like mishi ba, idan da wanda ya likewa wani a cikinmu to shine. Sannan nasan da labarin hakan ai, kawai mutane ne da basu rabuwa da tashin zaune-tsaye. Kika sani ko matan nashi ne masu halaye marasa kyau? Idan ma ba hakan bane, wai meye ruwan mutane ne da rayuwarshi iye?”.
Janan ta daga baki cike da mamakina, tace “wai lafiyarki lau kuwa? Kin ma san abinda kike fada ne? Auren mutumin wannan da zaki yi sunan shi gudun gara, kin guji auren mai mata kin fada gidan mai ‘ya’ya. Yo ba gwara auren mai matar da kika sani ba sau dubu akan wanda baki sani ba? Kodayake, rayuwarki ce ai. Kiyi duk yadda kike so da ita. Daga yau na daina yi miki magana game da Yaya Bilal in Allah ya yarda. Kiyi duk abinda kike ganin shine daidai a wajenki, jiki magayi!”.
Ta juya ta wuce abinta, ni kuma na bita da kallo na wasu lokuta, kafin na bi bayanta da sauri ina kwala mata kira.
Da yamma Yaya Mudatthir ya kirani, Anty Sailu ta haifo yaranta maza biyu.
🙏🙏🙏🙏
*☆⋆29⋆☆*
“Yanzu yaushe kike tunanin zamu tafi wajen sunan ne? Ina ganin kamar mu tafi Talata ko? Ya kike gani?”.
Janan take tambayata a washegarin ranar da aka yi haka, bayan mun dawo daga masallaci.
Nace “zaki je ne?”.
Ta dan yamutsa fuska cikin nuna alamun rashin jin dadi, “ban gane ba? Kina tunanin ba zan je bane ko me?”.
Nace “kinga, ni fa ba cewa nayi ki hayayyako min bane. Nasan Yayanki da protectiveness dinshi, ban sani ko zai barki kije bane, shi yasa”.
“Wannan kuma matsalar mu ce ni dashi, don’t you think? Kawai ki fada min lokacin da kike ganin yakamata mu tafi!”. Ta fada a dan zafafe, har sai dana kara kallonta cikin mamaki.
Naja tunga na juya ina kallonta tare da kama kugu, nace “ni fa na kasa gane miki ne, tun da kika zo yau kike hade min girar sama data kasa. Na miki wani abu ne?”. Duk yadda naso inyi masking damuwar data lullubeni, na kasa. Janan ita ce mutum daya kacal da duk duniya nake ganinta kamar jinina, kai wasu lokutan ma fiye da jinina. Ita ce kuma kadai nake ganin duk duniya, babu abinda ba zan iya sadaukar mata ba. Sai dai banyi tunanin sadaukarwa zata zo da consequences kamar wannan ba, wannan shine abu dayan da ba zan taba iya sadaukarwa ba. Don haka nake iyaka bakin kokarina wajen ganin cewa ban biye mata mun raba kai a tsakiyar titi ba, nasan cewa zuciyarta cike take da haushina dankar. Amma na fara kaiwa bango.
Tayi ajiyar zuciya, kanta yayi kasa cike da nuna nadama, “am sorry… Kawai na kasa wrapping kaina akan abubuwan da kike yi ne. Kin san cewa na damu dake, bana so ki aikata abinda zai zo ya zame miki dana sani daga baya wallahi. Why not Yaya Bilal kam? Kinga bayan mun bar nan, babu ruwanmu da tunanin rabuwa, zamu sake zama tif da taya, mu zama yan uwa na hakika”.
Na dan sosa saman hancina cikin nuna alamun gajiya da zancen wannan, kamar ba ita bace take ihun maganar wannan ba zata sake hada mu ba jiya-jiyan nan.
Nace “Janan kenan! Wai ke a tunaninki zan iya jera kafada ne da matan Yaya Bilal muyi kishi dasu? Ki dube su fa ki dube ni, me zan nuna musu bayan bakar fata da tsaurin ido? Yadda yake da mata fararen nan tubarkallah, kamar ka taba jini ya fito, ban san me yake nema a wajena ba”.
Janan ta kwashe da dariya, tace “babe! Wani lokacin shirmen ki dariya yake bani wallahi. You are very shallow, God! To an fada miki farin fata shine auren? Shi kanshi Yayan idan zan iya tunawa, ai ba fari bane. Allah wallahi ina shawartarki ni dai, ki sake zama kiyi tunani. Har ga Allah ba wai don Yaya yana Yayana bane, amma da ace shi wanda kika kafewa din kina son shi, kuma zai iya rike ki cikin mutunci, wallahi da baki kara jin bakina cikin maganar nan ba. Saboda ba karamin bata min rai kika yi jiyan nan ba”.
Nace “kiyi hakuri”, cikin sanyin murya. Jiyan yini nayi cike da damuwar bacin ran dana haddasa mata. Sai dai hakan fa bai yi kusa daya sanyayar min da gwiwa ba. “Amma wa yace miki bana son Dr. ne? Kina tunanin zan iya amincewa da auren wani bayan bana son shi? Kawai zama da kishiya ne baya cikin abubuwan da zan iya yarda Jan”.
“Ke dai kawai ki ce, tsoron matan Yaya kike yi. Kina tsoron kiyi hadaka dasu, ki dinga challenging dinsu, suna challenging dinki, kina tsoron may be, you’ll lose…”. Ta fada cike da confidence, kamar tana da tabbacin abinda yasa nake gudun auren Yaya Bilal din kenan.
Nayi dariya da daga jin ta kasan bata kai zuci ba, nace “Jan kenan. Kin sanni sarai da tarar aradu da ka, sai dai wannan aradun tafi karfina, idan na dauketa tarwatsa ni zata yi. Maganin kada ayi, kada a fara. Gwanda in zauna a inda Allah Ya ajiye ni, kada in kai kaina inda zan hallaka!”.
Da alamun ta fara gajiya da kokarin sanya ni fahimta da take ta kokarin yi tunda zancen wannan ya taso, tayi kwafa, “shi yasa zaki gwammace ki cuci kanki kenan akan ki bi zuciyarki? ‘Cause let’s face it, kina son Yaya Hilal, ni nasan wannan. Yanzu kin gwammace akan wani dalili naki na daban, wanda ba na Allah da Annabi ba, ki tauye zuciyarki da rayuwarki?”.
Na daga kai na kalleta sosai, cikin girgiza kai, “baki san abinda na gani ba Jan, baki kuma dandana abinda na dandana ba, ba zaki taba fahimta ba… Ina kallo kiri-kiri ba zan jefa kaina inda nasan takaicin miji ko kuma na matansa ne zai kashe ni ba, ko kuma duka. Ba zan iya ba!!”. Na kara maimaita mata, don tasan cewa da gaske nake, kuma ba zan canza maganata ba.
“To amma idan fa shi wanda kika kafe zaki aura din, shima yazo zai kara aure daga baya?”.
Nayi shiru cikin tunani, lokaci zuwa lokaci ina irin wannan tunanin, sai dai har yau akan mafita daya nake sauka, “sai ya zaba ko ni, ko ita!”.
Maganar ta fito tun daga kasan zuciyata har cikin bakina, babu wata tantama ko fargaba.
Ta zare ido cikin mamaki, ta daga baki zata yi magana, nayi gaggawar katseta, “na san abinda kike kokarin yi Jan, maganar gaskiya zan fada miki, itace ki daina bata yawun bakinki. So kike yi kiyi provoking dina, ko kiyi convincing dina, koma dai wannene daga ciki ba zai yi aiki a kaina ba. Kin san hali na sarai. Zama da kishiya daya ma bai cikin tsarina, Allah ya gani, balle kuma mai mata har biyu? Not a chance! Ba wai ba zan yi bane, ba zan iya ba! Don haka gwanda ma kiyi hakuri kawai, mu canza magana, kafin rayukanmu su zo su baci a banza!”.
Maganar da nayi ta sosa mata rai, sai dai tasan kamar yadda nace, idan ta kafe akan wannan maganar, lallai rayukanmu zasu baci. Don haka ta girgiza kai kawai, “Allah ya ganar dake” kadai ta iya furtawa.
Nayi murmushi ina kai gorar yoghurt din dake hannuna baki, “Ameen”.
Ban nuna mata na kula da kallon da take min ba na takaici da ban haushi, abu daya na sani, ba zan taba canza magana, ra’ayi, ko tsari na ba. Ba zan taba zama da kishiya ba!!.
Janan ta juya taci gaba da tunkarar pediatric ward bayan wannan, na bi bayanta da sauri tare da sankala hannuna bayan wuyanta, ina kallonta cikin kokarin ganin na dan yi lifting din mood dinta.
“Come now Jan, kada ki bari wannan maganar ta shiga tsakaninmu mana, shi yasa seriously maganar nan does not appeal to me that much. Haka kike so inje in auri yayan naki, idan muka yi fada ki dinga goyon bayanshi?”.
Na fada cike da tsokana.
Janan tayi dan murmushi kawai, “Na’ilah kenan. Ni nasan ko hakan ta faru babu ta yadda za ayi in juya miki baya, ko mai zai faru kuwa… Yanzu mu bar wannan maganar, yaushe kike ganin yakamata mu tafi?”.
Na dan sauke ajiyar zuciya cike da jindadin ta bar maganar, nace “kin san fa da kyar ne su bari mu tafi har na kwana hudu Janan”.
Tayi yar dariya, daidai lokacin da muka shiga cikin ward dinmu muka wuce nursing station kai tsaye, tace “mu masu uwa a gindin murhu? Ango guda fa garemu a cikin wajennan, Allah na tuba ko wata ne ai ba zamu samu wata matsala ba”.
Na jefa mata harara cikin wasa, nace “amma kinsan bana using mutane to my advantage ko?”.
Tana shirin bani amsa, muka ji gyaran murya a gefenmu, muka daga kai. Dan halas dinne a tsaye a gefenmu, ni da Janan muka gaida shi ya amsa da murmushi akan fuskarshi from ear to ear, idanunshi a kaina yace “amaryata!”.
Yadda kasan saukar aradu haka naji kalmar, wani irin vile feeling dana ji ya taso min daga can cikin cikina ya makale min a makoshi, yadda kasan zanyi amai. Na daure na hadiye shi, na kakaro murmushi duk da ni a karan kaina ban ji alamun murmushin ba. Nace “Dakta!”.
Ya dan girgiza kai, “gaskiya zamu zauna muyi magana akan wannan sunan Na’ilah dear. Amma wannan zama zamu yi na musamman, ya kike?”.
Na amsa a tausashe, duk da cewa can kasan zuciyata ji nake kamar ana tafasa min ita. Lallai idan aka cigaba da tafiya a haka, akwai matsala.
Ya jima anan muna yar hira dashi, Janan tashi tayi ta bamu waje. Rabin hirar sama-sama muka yi ta saboda hankalina baya tare da ni. Har sai daya kai ga tambayata lafiya? Na mishi karyar kaina ne yake ciwo. Nan da nan ya rikice, ya fara watso min tambayar ina bukatar ganin likita ne? Nace mishi a’ah, nagode.
Ranar da wuri muka tashi saboda ciwon kan da nace mishi ina yi, hasalima a motar shi ya kaini har gaban hostel dinmu, ya hado ni da tulin magunguna da yoghurts. Sai dai duk abinnan da rawar jikin nan da yake yi, ban ji wannan so da kaunar da nake ji ba a duk lokacin da Yaya ya nuna min kulawarshi ba.
Da kyar muka samu suka barmu zamu tafi ranar Laraba, shima sai da Dr. Na Abba ya sanya baki sannan.
Ranar larabar, da kanshi ya kaini har tasha inda zamu hau mota, muna zuwa muka hadu da Janan itama zuwanta kenan.
Muka yi sallama da Dakta, ya hada ni da dubu ashirin, goma muyi kudin mota, goma kuma in ba maijego ta sai wa yara kwalli. Da kyar ma dai na amshi kudin sai daya fara nuna alamun bacin ranshi sannan na amsa na mishi godiya. Muka hau mota muka tafi.
Motarmu ta samu matsala can wajejen Hadejia, gyaran da aka tsaya akan yi yasa bamu isa cikin garin Gashua ba sai karfe tara na dare. Yaya Mudatthir ne da kanshi yaje ya dauko mu daga tasha kamar yadda ya saba a yawancin lokuta. A gidan Malam muka sauka.
A gurguje muka yi wanka muka dan ci abinda aka ajiye mana, daga haka muka bi lafiyar katifa.
Washegari muka yiwa gidan suna tsinke. Yara sun ci sunan Malam da sunan Mahaifin Sailuba din.
Yinin nan cur haka muka yi shi cikin kujiba-kujiba, da kai da kawowa. Mutane ne mu na dangi, wadanda suke da son zumunci da karah. Taron da sunan Sailuba yayi, da irin alkhairan da suka samu ita da ‘ya’yanta kadai ya isa ya tabbatar maka da hakan. A gidanta muka kwana ranar, saboda bayan watsewar yan taron suna, mun zauna gyara mata gidan har zuwa tsakiyar dare. Sai hakura ma muka yi muka bar wasu ayyukan zuwa washegari.
*☆⋆30⋆☆*
Dogon salatin da Fatsu ta ja ne ya tashe ni daga dan barcin daya fara daukata. Sai da daren nan muka dawo daga gidan sunan, bayan mun ci abinci mun dan kimtsa, muka yi sallah. Muna gamawa Janan ta fita waje inda Fatsu take zaune tana sak’arta, ni kuwa na kwanta akan abin sallar muna waya da ango na to be, wanda bamu jima akan wayar ba muka yi sallama saboda ciwon kai, gajiya, da barci da suka lullube ni (don dai kawai ya kyale ni). Ban san ma barci ya daukeni ba sai da naji wannan salati.
Na zabura nayi waje a sukwane, dankwali a hannu. A tsakar gida na samesu zaune akan tabarma, hasken wuta da aka kawo da yammacin nan ya haskake wajen. Na kallesu a rikice, nace “lafiya, me yake faruwa ne?!”.
Fatsu da take tafa hannuwa, cikin salati har yanzu ta kalleni kamar na bullo wasu kawuna daga jikina. Na bisu da kallo ita da Janan cike da mamaki.
Sai data gama salatinta da sallallami sannan ta dakata, ta kama haba tana girgiza kai, tace “oh ni jikar su! Na’ilah wace irin shiririta ce nake ji haka? Kanki daya kuwa?”.
Na fara raba kallo tsakaninta da Janan, fuska na bayyana tsananin mamaki da nake ciki. Nace “wai me yake faruwa ne? Kin sanya ni a duhu!”.
Ta min dakuwa da hannuwanta biyu, “amshi nan ja’irar kawai! Ke dai wallahi baki ji dadin halinki ba. Dama wannan dan banzan ra’ayin rikau din naki yana nan? Nayi zaton duk yarinta ce ta janyo haka. To wallahi bari kiji, ba dani za ayi wannan haukan ba. Ina Yayan naki yake ne? Bari yanzu a kira min shi yazo!”.
Ta fara neman wayarta tana cigaba da mitar dana kasa fahimtar abinda take cewa.
Na daura dankwalina tare da zama a gefen Janan da tayi tsumu-tsumu.
Nace “wai ni akan menene kike ta wannan fada ne kam, Fatsu na?”.
Ta hararoni da duka idanuwanta, dama gasu tubarkallah, manya ne. Tace “gidanku nace! Wato ma baki san akan menene nake miki magana bane? To akan wannan yaro Yayan wannan yarinya da yake nemanki ne, kika badawa idanunki toka wai ke baki auren mai mata. Ba’a auren aka auri uwaki? Ko a gidanku don iyayenki mata nawa ne a ciki? To bari kiji in gaya miki, tun ma kafin tafiya tayi nisa, ki sallami wannan dan dukurkushin yaron da yazo nan. Ni dama tunda na ganshi naji raina bai kwanta dashi ba”.
Duk da haushin Janan da naji ya ciko ni, hakan bai hana ni kwashewa da dariya ba, itama Janan ina ji ta saki dariyar. Nace “ji Fatsu don Allah, wai dan dukurkushi. Idan baki son mutum bai kamata ki bata mishi suna ba wallahi”.
Ta dauki zaren da take saka dashi ta jefe ni dashi, “gidanku! Wato ke abin dariya ma ya baki kenan? Bari dai ki ga…”, ta komawa neman wayarta, tana ganinta ta mikawa Janan ita, “yauwa yar nan lalubo min Mudan ki kira shi, ce mishi yazo yanzu-yanzu”.
Dan halas din, kafin Janan ta ma lalubo lambar shi, sai gashi ya kwaro sallama ya shigo. Fatsu ta ware hannuwa kamar wadda zata rungume shi, na hau danne dariyar data taso min despite haushi da tsoron abinda zai je ya dawo daya cika min ciki. Fatsu ta harareni, ni kuma na harari Janan. A raina ina saka kalar rashin kirkin da zan mata idan muka samu muka kebe. Wato da biyu tazo Gashua kenan? Zata yi bayani ne.
Yaya ya samu waje ya zauna, shima dai cike da murmushi da kuma mamakin dabiar Fatsu a daidai wannan lokacin.
Yace “me yake faruwa ne anan?”.
Fatsu ta gyara zama, “dama kiran ka nake kokarin yi yanzu. Kaji-kaji abinda yake faruwa”.
Ta zauna ta zayyane mishi magana da halin da muke ciki da Yaya Bilal yanzu, babu ragi babu kari. Yaya bai ce komi ba tunda ta fara maganar, har ta direta.
Sannan yace, “ni dama nasan da walakin wai goro a miya, nasan tunda ta turo wani akan yazo ya ganmu kamar daga sama, nasan da wata a kasa. Ke yanzu a tunaninki hakan shine daidai a gareki? Ba zaki yi tunani wanda zai fissheki ba Na’ilah?”.
Na turo baki gaba, “to ni Yaya wai nace muku ina son shi ne? Abun ai sai yayi min yawa, wai shege da hauka. Da wanne zan ji ne? Da rashin so ko kuma zama da kishiyoyi?”.
Yaya ya kama baki, “ni kike fadawa haka Na’ilah? Lallai wuyanki yayi kauri da yawa. To bari kiji in gaya miki, idan ke idanunki a rufe suke, mu namu a bude suke tar, kuma babu ta yadda za ayi muna kallonki ki bi hanyar da bata dace ba kin ji na fada miki…”.
Ya hau fada ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, daga karshe dai ya kare da, “.. don haka tun ma kafin magana tayi nisa, ki sallami mutumin nan. Mu dukanmu hankulanmu basu kwanta dashi ba, balle me ma zaki yi da mutum mai auri saki? Kina da tabbacin zai tsaya ne a kanki? Ga responsible mutum irin Bilal? Dan gidan mutunci da karamci, wanda kuma muka sansu suma suka sanmu?”.
Gabadaya haushi yazo ya dabaibayeni wai me yasa ni ba zasu duba dalilina ba, zasu dinga concluding rayuwata kamar idan nayi auren su ne zasu yi min zaman auren ba ni ba? Na tashi zan wuce daki da sauri ina gunguni har da buga kafa a kasa.
Yaya ya daka min tsawa data gigita ni, tunda nake dashi ban taba jin yayi makamanciyar ta ba, musamman wa ni. Yace “dawo nan ki zauna Na’ilah tun kafin ranki ya baci wallahi!”.
Ba shiri na koma inda nake zaune na zauna, hawayen da nake kokarin dannewa suka shiga zarya akan kumatuna.
Yaya ya kama baki, “ikon Allah! Kuka kuma kike yi? Lallai kin samu waje da yawa. Akan wannan yaro ne kike nema ki bata mana rai, me kika gani a jikinshi?”.
Fatsu tayi caraf ta tare shi, “ni anya ma ba tsaface ta yayi ba? Naji ance wajajen nan sun kware wajen bin malamai”.
Babu wanda ya tanka mata a tsakaninmu, Yaya ya cigaba da cewa “ni ba zan takura ki ba Illo, amma Allah ya gani zamu yi iyaka bakin kokarinmu. Amma tunda ke kina ganin hakan yafi miki, to sai kije kiyi tayi, babu wanda zai sake damunki. Sai dai ko mai zai faru, kiyi kuka da kanki”. Ya tashi yana kakkabe jikinshi ya kalli Fatsu, “ni zan wuce gida Inna, sai da safenku!”.
Tace “to Mudan, a gaida su yan biyu”. Yasa kai ya bar gidan. Ya barni a zaune ina share hawaye.
Yana fita Fatsu ta juyo kaina, “wannan taurin kai naki, ban san daga inda kika kwaso shi ba. Ni dai duk tarihin danginmu babu mai taurin kai wallahi, balle kuma mahaifiyarki. Mace mai saukin kai, hakuri da ladabi da biyayya. Allah ya kyauta miki”. Ta tashi ta hade kan kayanta ta shige daki.
Ni da Janan muka cigaba da zama a wajen, cikin ni da ita babu wanda yayi magana. Har na gama yan koke-koke na na share hawayena. Sai dana gama sannan ta kalleni, tace “kiyi hakuri, banyi zaton abin zai kai haka ba wallahi. Tambayata tayi, ni kuma I was just carried away, amma banyi da niyya ba”.
Nasan halin Fatsu sarai da bugun ciki da iya manipulating, nasan kadan daga cikin aikinta ne. Amma ban tanka mata ba, nima tashi nayi na fada dakin, nayi shirin barci na kwanta abina.
*
Wato tunda nake zuwa Gashua, ban taba zuwan da bai yi min dadi kamar na wannan karon ba. Gabadaya Fatsu da Yaya sun dauke min wuta, kai hatta da Malam sai in ga kamar shima dai ya daina kula ni. Duk da cewa bai fito fili yayi min maganar ba, amma ta cikin hira da nasiha yakan sako zancen cikin dabara irin tasu ta manya. Shi yasa naji gabadaya na takura. Tunda farar safiya muke saka kafa mu bar gidan ni da Janan da muka shirya da ita a washegarin ranar da abin ya faru, ba zamu dawo ba kuwa sai dare yayi. Ta yadda da mun dawo, babu lokacin zama hira, zamu nemi makwanci.
Ranar Lahdi na zagayowa kuwa, yadda kasan na sauka daga kan kaya haka naji lokacin da muka fita daga garin Gashua. Nasan yanzu sai a hankali, sai nayi kokari sosai kafin in samu in shawo kan Fatsu da Yaya. Da wannan kudirin muka isa Zaria.
Cikin yan kwanakin kuwa na samu na shawo kansu din da kyar, duk da cewa har yanzu dai da suna dan tado min maganar musamman ma dai Fatsu, amma dai hakan yafi da.
Bamu yi cikakken sati uku da dawowa ba, muka tafi gida hutun sallah.
*☆⋆31⋆☆*
Komawata wannan karon naga alamun canji sosai a gidan. Misalin yadda na samu Anty Alawiyya cikin fara’a da walwala, tana ta shigi da ficinta cikin annashuwa. Su Ramata kuma ana zaune a kofar daki, an coge daurin dankwalin nan an kawo shi goshi, ana ta zubda ruwan habaici da bakaken maganganu kamar wata jikar mahauta.
Nayi sallama na shiga gidan, hannuna dauke da Auwal da muka hadu dashi a waje, sun dawo daga makarantar islamiya, ya gudu ya baro sauran. Anty Alawiyya ta amsa min sallamar da nayi cike da fara’a, tace “a’ah, mutanen Zaria ne? Sannunku da zuwa, ai bamu da labarin kuna kan hanya”.
Nayi dan murmushi ni kuwa tare da gaidata, ta amsa tare da shigewa dakinta. Na juya na gaida Ramata, yau ko albarkacin amsa gaisuwar ban samu ba, ta cune baki waje daya, ta dauke kai daga kaina ta maida shi gefe. Na tabe baki na ciccibi akwatina na fada daki Auwal yana bina a baya.
Dakin a share a kimtse, abin har ya bani mamaki. Maryam dai ba irin masu son yin gyaran nan bane, saboda haka zuwa in ga daki a share a goge, yana kamshi, abin mamaki ne da tambaya.
Na zuge jakar hannuna na ciro cakuletin dairy milk dana siyo ledar guda saboda yara, na dauki daya na ba Auwal. Ya karba ya fita waje a guje, nasan sauri yake ya tari yan uwanshi ya basu labari. Nayi murmushi ina girgiza kai tare da tashi na hau cire kayan jikina.
Ina nan sai ga Alawiyya da gorar zobo da kunun aya, tace “ga mai dan sanyi ki kora kafin mu gama abinci, yanzu aka dora amma ba mai wahalar damuwa bane”.
Allah sarki, sai naji abin wani banbarakwai. Duk da hakan bai hana ni jin dadin hakan ba, ko ba komi kasan cewa wani ya damu da kai a cikin gidannan, abin jin dadi ne da alfahari.
Na kai hannu na karba cikin murmushi, nace “babu komi ai, na ma ci abinci ai kafin in taho. Nagode sosai”. Bata ce komi ba ta juya ta bar dakin.
Sai dana linke kayana na gyada su, sannan na sake fita tsakar gida, daidai lokacin yaran sun dawo, nan fa aka hau guje-guje da rige-rigen wanda zai riga zuwa wajena. Na taryo su gabadaya na rungume, sai da suka gama dokin su, sannan suka kyaleni. Na shiga bandaki na dauro alwala saboda yamma tayi sosai har rana ta kusa faduwa, na fito na sallami masu jiran tsaraba.
Na zauna kenan na fara shan zobon da Anty Alawiyya ta kawo min mai sanyi sosai, naji an fado kaina ta baya ana ihu. Muka fadi a tsakiyar dakin, gorar zobon tayi can nata waje, ni da Maryam da take kaina muma muka yi namu wajen.
Sai data ga barnar da tayi sannan ta tashi da sauri, ta fita ta dauko tsumma da mopper ta goge wajen da zobon ya zuba, sannan ta dawo ta sake rukunkume ni.
Tace “haba Yaya Na’ilah, ke kullum haka kike zuwa babu sanarwa? Me yasa ma kullum na kira wayarki bata shiga ne? Har a whatsapp bana samunki”.
Tun ranar da muka yi waya da Yaya Bilal ta karshe, washegari na sayi sabon sim card nayi register. Kafin in ba Janan lambar wayar, sai data sha jan kunne da gargadi iri-iri akan kada ta kuskura, koda wasa Yaya Bilal yasan da zaman wannan lambar.
Amsarta a lokacin itace, ‘kina tunanin zai damu da rashin samun wayarki ne bayan duk abubuwan da kika mishi?’.
Raina yayi rashin dadi da jin haka, amma sai na dake, nace “wani abu kuma na mishi?”. Bata amsa ni ba, taci gaba da kallonta da take yi a lokacin.
Bayan nan kwata-kwata mantawa nayi da zancen Maryam, yawancin sauran abokanmu ma sai daga baya idan mun hadu sannan zasu yi korafin sun daina ji daga gareni, sai dai kawai in kawo wani dalili can in basu, muyi exchanging din numbers.
Na bata hakuri tare da cewa sim din aka yi blocking, na bata sabuwar lambata tayi saving.
Na kalli gorar zobon data ajiye a gefena, babu komi a ciki duk ya zube, na harareta nace “kin ga kin zubar min da abu, bayan ko sha ban yi ba”.
Ta kyalkyale da dariya, “ai in dai ta wannan ne, baki da matsala Yaya. Ke da kika zo inda ake sarrafa zobon?”. Ta tashi ta fita da sauri, ta dawo da wata gorar ta miko min, na amsa na bude tare da kafa kai.
Muna nan a zaune muna taba hira da ita, har aka kira sallah. Ita ta dauki wayata zata yi game saboda bata yin sallah, ni kuma na tada kabbarar sallah. Bayan na gama na amshi wayar, na turawa duk wanda ya kamata sakon na sauka gida lafiya, na dauki Al-Kur’ani mai girma na fara karantawa har aka kira sallar isha’i.
Sai bayan na gama sallar ne sannan na bude mata tata tsarabar. Takalmi da gyale da jaka wadda ake yayi ta yanmata irinta. Murna wajenta har ta rasa inda zata jefa ni, gefe kawai na koma ina mata dariya.
Bayan na tabbatar Baba ya gama cin abinci na yiwa dakinshi tsinke. Yana zaune matan sun dabaibaye shi, Alawiyya na zuba mishi hira, su Ramata kuma ana gefe ana ta cika da batsewa. Da alamu kambun a hannun Alawiyya yake wannan karon. Abinda yake faruwa kenan a gidan, su ganin walwalar miji a wajensu juyi-juyi ne. Wadda ta samu ta shawo kanshi, ko ta tsibbunta ko ta malaman, ta fa ita da ‘ya’yanta su suke cikin jindadi, ita dayar kuma sai dai ta koma gefe ta kwashi takaici, kafin itama nata tenure din yazo.
Naja daga gefe na gaida shi, ya amsa fuska babu yabo babu fallasa. Nayi zaton zai yi min maganar Yaya Bilal, amma har na tashi na fita daga dakin, bai ce min komi ba. Duk da abin ya bani mamaki, amma naji dadin hakan.
Na shiga gidan su Kulsum, muka gaisa dasu Inna. Mun jima muna hira dasu, har wajen karfe goma, sannan na musu sai da safe na koma gida.
Kayan barci kawai na saka na lalubi shimfida na kwanta. Kamar wanda yake jira, ina kwanciya sai ga kiran wayar Dr. Na Abba ta shigo, dole na katse barcina ba don naso ba na dauki kiran.
*
Washegari kamar yadda na saba, nayi duk wasu abubuwa da yakamata inyi da safen nan. Kasancewar yara sun samu hutun sallah daga makaranta, yasa ban dora abin kari da wuri ba. Wajen karfe tara na gama, kowa ya amshi nashi kason. Na hada kan kayan na wanke, na share kicin din, sannan na koma daki nima nayi nawa karin. Gobe in Allah ya yarda ake yin hawan arfah.
Ina cikin cin abincin, Aliyu ya fado dakin kamar an jefo shi, tunda na dawo gida sai yanzu na ganshi. Yace “babbar Yaya, to ya ne?”.
Nayi dan murmushi nace “lafiya lau Aliyu. Ya kake?”. Nan muka dan sha hira dashi ya bar dakin.
Da yamma bayan na gama duk abinda zan yi, muna tsakar gida a zaune ni da Maryam muna hira, tana bani labarin zuwan da Yaya Bilal yayi gida.
“Har nan cikin gida fa Baba ya shigo dashi in fada miki..” take fada. Wanda hakan ya tabbatar min da cewa ba karamar tarba Baba din yayi mishi ba. Idan kaga yayi baki ya shigo dasu cikin gida, to ba kananun masu muhimmanci bane.
“… Su Mamarmu dubu goma ya raba musu, muma ya bamu dubu goma muka raba, shi kuwa Aliyu aka bashi dubu biyar”.
Mamaki ya kamo ni, ban taba jin labarin hakan ba sai yanzu. Wato so yayi ya saye su da kudi ne ko me? Na godewa Allah daya kasance ba Gashua yaje yayi barin kudin nan ba.
Maryam ta dago ta kalleni, tace “amma da gaske ba zaki aure shi ba?”.
Ban san yadda aka yi labarin yaje kunnensu ba, amma nafi kyautata zaton Baba ne ya fadawa iyayen, su kuma suka basu labari. Ban iya ce mata komi ba sai kafada dana daga mata.
Tayi pouting, “amma Yaya Na’ilah mai yasa? Kinga da idan kika aure shi, sai in zauna a gidanki idan naje Zaria karatu, kinsan nima fa can zan je”. Na gyada mata kai.
Tsulum, sai ga bakin Ramata cikin maganar, da a daki take, bamu ma san lokacin daya fito daga dakin ba, “ke ja can sakaryar banza! Me ake da gidan mai mata? Ai wallahi kada ki kuskura ki yarda, kudin mutum su rufe miki idanu kiyi zaben tumun dare. Ke zaman nan gidan ma kadai bai isheki ishara ba? Kina dai ganin yadda muke fama, babu farinciki ko na anini sai akasinsa. Kullum cikin taraddadi da zullumin abinda makiya, makagauta zasu maka. Don haka wallahi ki auri dan saurayinki shi ya fiye miki kawai”. Ta saurara tana kallona, ko amsa take jira in bata da godiyar shawarar data bani? Ban ce mata komi ba, amma a can kasan zuciyata sai da nace ‘ishara ta nawa kuma?’.
Da dai taga bani da niyar tanka mata, sai ta kara gaba, tana fada tana kara nanatawa, ina amfanin auren gidan kishiya? Ina jin Anty Alawiyya daga daki tana ihun, “a hakan dai kuma ake zaune ake shuka rashin mutunci ba!”. Babu dai wanda ya tanka musu a cikinmu, sai ma hirarmu da muka cigaba da yi.
Washegari muka tashi da azumin nafilar arfah a bakinmu.
Washegari kuma Baba yayi yankan layya. Dama kowace shekara, ya kan yanka raguna guda uku, daya matan su raba, daya nashi shi da abokai da yake yiwa rabo kasancewar shi mutum na mutane, dayan kuma na yara ne.
Kwananmu biyu muna aikin suya, aka kammala aka raba kowa ya dauki nashi. Wanda ranar rabon ma sai da su Ramata suka raba hali kamar za ayi dambe, sannan da kyar suka hakura.
Ni dai naci gaba da jindadin hutuna kafin ya kare.
Bayan sallar da kwana biyu, su Dr. Na Abba suka kai kudi can Gashua, wanda Baba ne yace hakan. Gabadaya suka kai kudin, aka kuma sanya ranar aure. Nan da watanni uku masu zuwa. Wanda yayi daidai da lokacin dana gama exams dina kenan.
Ban san a cikin wani yanayi nake ba a cikin wannan lokaci, abu daya kadai na sani, shine zuciyata bata maraba da wannan biki koda wasa.
Bayan kwana uku da kai kudin, na tattara na koma Zaria abina. Na hadu da angona to be, muka fara shirin yadda zamu gudanar da bikinmu. A gefe guda kuma na maida hankalina ga karatun exams din dake gabatomu nan da dan kankanin lokaci.
🙏🙏🙏🙏🙏
*☆⋆32⋆☆*
Kwanci tashi kamar yau ne a wajen Allah. Gashi har yau ya rage mana sati daya kacal mu gama da karatunmu gabaki daya. Hakan kuma yake nufin nan da sati biyu masu zuwa zan amarce. Kowa ya ganni a cikin irin wadannan lokutan, ya ga ‘a walking zombie’. Kama ce ba wadda ake zaton gani a jikin amarya ba, amarya daya kamata ta zama mai kazar-kazar, da doki, da komi ma kai, ni kam komi nawa ya zama babu laka a jikinshi. A kowace matsowar rana, ji nake dama kara ranakun ake yi ba rage su ba. Amma babu wanda na ba wannan labari, na kama bakina na dinke babu wanda ya sani. Nasan duk wanda yaji kalar tashin hankalin da nake ciki, wanda babu wanda ya jefa ni ciki sai ni kaina, zai kira ni banza, sakara, kila ma har su kara da wadda bata san ciwon kanta ba. But I know better.
Kullum excuse dina daya, wanda nake kara ba kaina, cewa hidimomi ne suka yi min yawa ba wani abu ba. Zan wartsake, zan dawo daidai, abinda nake yawan ambatawa kaina kenan. Kodayake, naji ance dama yawanci haka amare suke ji idan aurensu yana gabatowa. Don haka it’s normal.
Da Janan muke ta shigi da ficin harkar bikinnan, tayi ruwa tayi tsaki kamar yadda yakamata tayi, duk da cewa itama nata bikin nan da watanni hudu ne masu zuwa. Kasancewar Almunta ya tafi wani course kasar Germany na watanni biyar yasa aka saka ranar auren tasu bayan ya dawo da sati biyu.
Duk wasu shirye-shirye mun riga mun yi su. Rabon IV, daga gida Katsina, zuwa nan Zaria da kuma Gashua, duk wanda yakamata ya samu ya samu. Haka anko, kai da dai duk abinda ya dace, munyi sai sauran abinda ba’a rasa ba.
Yau muka zana jarabawarmu ta karshe a cikin Shika, nan da kwanaki uku zamu yi practicals din exams din, daga nan zamu yi induction, kamar graduating ne a wajen nurses ko kuma in ce oath-taking. Idan muka yi shi, za’a bamu nursing license dinmu, daga nan kuma zamu yi applying internship a inda muke so.
Bayan mun fito daga jarabawar, a gajiye muka koma dakina ni da Janan. Muka zube akan katifa muna ajiye numfashi da maida labarin yadda jarabawar ta kasance mana.
Saboda tsabar gajiyar dana kwasa cikin yan kwanakin nan, ban san lokacin da barci mai nauyi ya kwashe ni ba.
Kafin in tashi har Janan ta dafa mana jallop macaroni, lokacin dana tashi na gansu ita da Esther suna hira. Nayi mika tare da tashi zaune ina binsu da kallo, Janan ta kalleni “ki tashi ki wanko baki ki zo ki ci abinci. Ki gama muje wajen masu dinkin wancan mu gani idan sun gama mu amso”.
Na tashi tsaye da kyar, ina jin jikina kamar an nada min dukan tsiya. Na dauki kettle na fita waje na daurayo bakina, na dawo na zauna a inda plate din abinci yake jirana. Na janyo abincin cikin mutuwar jiki na fara ci, ina ji suka ci gaba da hirarsu akan wajen da zasu je suyi nasu internship din, ita Janan a Kaduna zata yi, ita kuma Esther anan Shika zata yi. Nima dai nasan Shika dinne, don mun riga munyi maganar da Dr., ina karbar license dina zan mika mishi, zai yi applying internship din da kanshi anan Shika din.
Daga baya kuma sai hirar ta gangaro kan abinda zasu yi da abinda zasu saya idan suka dauki albashinsu na farko. Ina daga gefe ina jinsu, sai dai inyi dariya idan sun fadi wani abin daya bani dariya. Ko kuma in girgiza kai da jin absurdity din abubuwan da suke fada.
Ina gamawa, na maida kwanukan gefe. Esther ta jefo min wayata, nayi sauri na cafe. Tace “hubbynki ya kira lokacin da kike barci”.
Na jefa mata harara cikin wasa, “shine kuma sai yanzu kika ga damar fada min? Kina so hankalin mijina ya tashi ne ko me?”.
Ita da Janan suka yi dariya, tace “come on mana, nasan dana baki wayar nan daga tashinki daga barci, ba lallai kici abincin nan da wuri ba. Ko baki ga kokarina bane?”.
Na daga baki zan bata amsa, aka amsa kiran dana dannawa wayar Dr., don haka na rufe bakina tare da kara wayar a kunne.
Tun kafin inyi magana ya riga ni, daga jin shi cike yake da doki da farinciki, “hey, guess what?”.
Yanayin yadda yayi maganar kanshi ma, kasan cewa wani abu ne babba kuma muhimmi ya same shi, don haka naji na saki murmushi ba tare dana shiryawa hakan ba, nace “me ya faru ne?”.
“Tafiyar nan fa ta samu, nan da sati biyu! Oh God!! I can’t really believe this is happening!!”. Ya karasa fada cikin karajin murya.
Naji na balle da murmushi nima kamar lebuna na zasu rabe biyu. Wani course ne asibitin zasu tura manyan doctors na department din su biyar kasar London duk bayan shekaru biyu, course ne na shekara biyu. Yace idan kaci sa’a, idan can asibitin da kaje yin course din suka ga kwazon ka, zasu iya daukar ka aiki kamar yadda suka dauki likitocinsu biyu aiki wadanda suka je waccan shekarar. Idan kuma baka samu aikin a can ba, idan ka dawo, zasu kara maka matsayi da kuma albashi anan. Wannan ba ma shine abin birgewar kadai ba, idan ka tafi can asibitin zasu dinga biyanka albashinka, su baka wajen zama, haka babu ruwanka da biyan kudin makaranta idan kaje. Tsarin shine, idan ka tafi yanzu, zaka yi wata takwas a makaranta kana daukar darasi abinka, a hakan ma kana da albashinka a hannu, bayan ka gama da nan zaka koma asibitin kayi aiki dasu na watanni goma sha biyu. Daga nan kuma sai su yanke shawarar yadda zasu yi da kai.
Yace min yanzu sau uku kenan yana applying ana hana shi, wannan karon ma kwata-kwata ya cire ranshi daga samu, sai kuma gashi yanzu babu zato babu tsammani, ya samu din.
Nace “Masha Allah, Alhamdulillah! Kai amma naji dadi wallahi, Allah ya tabbatar da alkhairi, Allah ya albarkaci aikin wannan”.
Yace “ameen ameen amaryata. Ni har na rasa wace kalar murna ma yakamata inyi, ji nake kamar mafarki nake yi!”.
Na saki yar dariya, “right! Kawai ka kalli alkibla yanzu, ta nan kadai zaka nunawa Allah godiyarka. Idan ka bar nan kuma, sai kayi sadaka”.
Yace “haka ne, nagode dear. Bari in tafi yanzu”.
Na girgiza kai fondly, wani lokacin kamar yaro haka yake gudanar da dabi’un shi, wasu lokutan ya baka dariya, watarana kuma takaicinshi ya cika maka ciki kamar kayi me.
Wani tunani ya darsu a raina, nace “to amma ya zamu yi ne? Bikin ma nan da sati biyu ne, kenan hakan yana nufin tare zamu tafi kenan?”.
Ya danyi jim, zuwa can yace “har yanzu ina kan wannan tunanin ne. Yanzu zan shiga gida in sanar dasu, zan kira ki zuwa anjima”. Nace mishi “to ka gaishe dasu Hajiya”. Yace “zasu ji”, ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo, ko menene abin yin tunani a cikin wannan maganar? Na tabe baki tare da daga kafada.
Su Janan da tunda muka fara wayar suka katse hirarsu suke kallona jifa-jifa, suka zubo min idanu, na kallesu cikin murmushi, “dudes, London ta kira mu yanzun nan!”.
Habawa, suka saki ihu da shewa tare da fadowa kaina, sai da muka fadi kasa.
Janan tace “da gaske?!”.
Esther kam, “Oh my God!” Kawai take fada tana nanatawa.
Sai da suka gama ihun murnarsu sannan Esther ta tashi zaune, muma muka tashi. Janan ta sake sarkafo hannunta ta rungumo ni, “Na taya ki murna wallahi dear… Allah yasa hakan shi yafi alkhairi. Yanzu sai kiyi tafiyarki ki barni?”.
Nayi dariya, “sis, maganar fa bata tabbata ba. Ni fa ina assuming abubuwa ne kawai”.
Ta kai min duka a kafada, “maganar banza kenan! Ke yanzu kina tunanin zai tafi ya barki anan har na tsawon shekaru biyu? Wasa kenan. Balle ma, su da ana basu gidajensu acan, ai babu ma wani dalili da zai hana mu zuwa kai amarya kasar London”. Ta kyalkyale da dariya bayan ta gama fadin haka, ni da Esther muna taya ta.
Sai wajen karfe biyar na yamma sannan muka fita zuwa amsar dinkin. Har Esther muka tafi. A hanya Janan take tambayata, “su fa kayan lefen da ba’a kawo ba har yanzu, ya za ayi dasu?”.
Na kalleta, “ke da kika san zamani ya canza, yanzu lefe da zaki ga har ana saura kwana biyar daurin aure ba’a kai ba. Balle shi fa yace kamar haka al’adar gidansu take, sai bayan aure ake kai kayan lefe”.
Janan ta jinjina kai, “haka ne. Mu dai ya taimaka ya kawo kafin mu kaiki, idan haka ne, bamu da damar daukar turamenmu kenan”.
Na kai mata duka ina dariya, “ke fa baki da M wallahi, wawashe min kayan zaku yi kenan?”.
Muna wannan hirar har muka fita waje, muka hau bus zuwa inda muka kai dinki.
Dancing Banana, nan ne wajen da muka kai dinki. Duk da wasu kayayyakin suna can Katsina, Maryam ta kai min su, kai wasu ma suna Kaduna. Wadannan wadanda Ummahn su Janan ne ta bamu, manyan atamfofi guda biyu iri daya, da wani lafiyayyayen yadi ni da Janan din. Da kanta ta kai dinkin, namu kawai tura measurement dinmu ne.
Wadanda muka kawo nan, wanda angon ne ya kawo, tunda ba’a riga an kai lefe ba. Na Katsina kuma, wanda muka fitar ne a matsayin anko.
Kai tsaye wajen wanda yake mana dinkin muka wuce, muka samu ya dinka kala na mutum daya, na dayan kuma ya yanka bai dinka ba. Esther ta fara fuming, dama ita ta hada mu dashi, “yanzu kana nufin kusan sati biyu wai har yanzu baka gama mana dinkin ba? Mike meye hakan wai?”.
Yace “na fa yi kokari, yanzu haka aikin wata na maida gefe nayi wannan din fa. Nayi alkawarin nan da kwana biyu zan gama muku, kin san bama yin haka dake Esther”.
Muna nan tsaye, sai ga Haleemo a gabanmu. Bata ko yi acknowledging dinmu ba, ta hau zazzagawa mai dinki masifa. Apparently, ita ce wadda ya ture dinkinta dake kan layi ya mana namu. Tun yana bata hakuri, har shima ya hau sama ya fara zuba mata tata kalar masifa, mu kam muka koma gefe muna kallonsu.
Ta ja tsaki, “matsalarku kenan dama wallahi, ku kwata-kwata baku san mutumci ba. Su waye suka fito da martabar wannan shagon idan ba mu ba?”.
Yace “ke kada fa ki kawo min rainin wayau nan wajen. Kada ki manta ko wancan dinkin dana miki, baki cika min kudina ba. Wannan ma kika wani ciccibo kaya kika kawo min babu ko sisi, an gaya miki ni din bawanki ne wai?”.
Sai lokacin ta kallomu, ta fara borin kunya, “to ni nace ba zan baka kudin ka bane? Kada ka wulakanta ni a gaban mutane mana!”.
Ni da Janan muka danne dariyar data ke neman subuce mana.
Shi kuwa Mike yayi dan tsaki, “whatever, kin san ni bana irin wadannan tone-tonen. Su ma don dinkin aure ne shi yasa ma na ajiye nakin gefe guda”.
Ta kallemu ido a zare, “aure zaku yi?”.
Nayi murmushi nace “eh”.
Tare da bude jakata na dauko iv na mika mata, ta amsa ta karanta. Tace “to Allah ya sanya alkhairi”. Muka ce ameen.
Bayan mun tabbatar da cewa zuwa jibi zamu dawo mu amshi dinkin mu, muka tafi muka bar su suna cigaba da sa’insar su.
A kofar wajen, muka samu Umar tsaye a jikin motar shi, da alama budurwar tashi yake jira. Muka yi kallon-kallo dashi, muka zagaye shi muka wuce abinmu ba tare da wani yayi magana ba. Janan gida ta wuce, ni da Esther kuma muka koma cikin asibiti.
Muna shiga daki sai ga kiran wayar Janan, wai Anty Sarah tayi yar diyarta kamar Mimah. Na mata fatan samun sauki da barka muka yi sallama.
Ranar juma’ah muka yi induction dinmu, bayan an rantsar damu, mun karbi nursing license dinmu, aka shiga shagalin ciye-ciye da shaye-shaye. Allah kadai yasan irin farincikin da muke ciki a wannan ranar. Duk da cewa convocation dinmu nan da satika biyu ne, amma kuma induction ya ma fi muhimmanci ga nurses nesa ba kusa ba. Yinin ranar guda, kira ne kawai yake shiga yana fita daga wayata, sakonni na taya murna daga yan uwa da abokan arziki.
Da yamma bayan mun gama shagalin, ni da Janan muka dauki hanya zuwa barka. Kasancewar gobe asabar zan wuce gida. Gashua zan fara zuwa inyi kwana biyu, sallama da yan uwa da abokan arziki, sai in wuce Katsina daga can.
Napep din da muka hayo daga bakina titi yayi parking a kofar gidan, muka biya shi, sannan muka fita daga ciki.
Na daga kai na kalli gidan da kallo, yan kadan daga cikin memories dana tara a gidan, suka dinga flooding suna shiga cikin kwakwalwata. Na girgiza kai a hankali, ina kokarin shaking din komi daga cikin kaina.
Ni da Janan muka shiga gidan, bayan mun gaisa da maigadin gidan. Kai tsaye dakin Anty Sarah muka wuce. Da yake yamma ce, babu cunkuson mutane sosai. Muka gaisa na mata barka, ta amsa tare da min godiya. Yanayin yadda take fara’a da tambayata bayan rabuwa, sai kayi tunanin irin mun saba sosai dinnan ne.
Aka miko min diya na amsa, kamar yadda Janan tace, kamar su daya da Mimah babu banbanci. Na kura mata idanu ina kallo kamar in sude ta saboda birgewa. Yadda ta nade cikin towel din da aka nadeta a ciki, kamar irin magen nan sabin haihuwa, very adorable.
Mun jima sosai dasu ana yar hira, ba karamin mamakinta ta nuna ba akan maganar aurena da taji ba. Musamman ma da wani, ba… Bata karasa ba, naji Janan tayi saurin ta katse mata maganar. Na bisu da kallon mamaki, ban tsaya tambayarta wa take nufi ba, duk nayi zaton da Umar take, don haka na share maganar don nima bana son tuni akan irin rayuwarmu da Umar, da irin cin amanar da yayi min.
Ina shirin tashi da niyar yi musu sallama in tafi, kawai naji tashin sautin muryar data matukar rikitar dani. Da sauri na koma cikin kujerar dana fara tashi dabas, wata irin rawar jiki ta ziyarce ni. Ba shiri na fara janyo salati da hailala ina ja ina karawa a cikin raina.
Yaya Bilal da Yaya Jameel suka shigo cikin falon. Yaya Jameel sanye da casual jeans and T-shirt, yayin da kamar kodayaushe, Yaya Bilal yake sanye da shadda ruwan sararin samaniya, rataye a kafadarshi ta dama, brief case dinshi ce, da alamu dawowarshi kenan daga wajen aiki.
Suka samu waje suka zauna, kallon nan daya dana musu, ban sake daga kai na kallesu ba. Falon daga mu, maijegon, sai kuwa wata makociyarsu Ikilima data shigo bayan mun shigo muma.
Ina jin tashin muryarsu suna gaisawa da mutanen falon, nasan nima dole ne in gaida su.
Na daga baki da kyar na gaida su, ba tare dana iya daga kai na kallesu ba. Tashin muryar Yaya Jameel kadai naji ya amsa, hakan yasa naji jikina ya kara yin sanyi.
Ko lokacin da Janan ta karbi diyar daga hannuna da niyar mika musu, ban iya daga kaina ba.
Na yan wasu lokuta, dakin ya dauki shiru, babu motsin abinda kake ji, sai tashin muryar Yaya Bilal kawai da kake ji yana tashi, yana yiwa jaririyar addu’o’in tsari da kariya kala-kala.
A lokacin ne na samu na iya daga kaina a hankali, na saci kallon inda Yaya Bilal din yake zaune dauke da yarinyar. Rabon da in saka shi a cikin idanuna ko kuma inji muryarshi, run rana daya tsare ni a hanya a asibiti da kuma lokacin da muka yi waya dashi ta karshe.
A yanzu da nake kallonshi, yadda ya rike yarinyar nan a hannunshi kan-kam, kamar wanda yake tsoron wani abu ya faru da ita. Tsananin soyayya da zaka gani a cikin idanunshi, tsantsar adoration da wani irin hope, hope wanda ya kasa boyuwa a cikin kwayar idanunshi, ya sanya naji wani matsi a cikin zuciyata har sai da naji kwalla ta cika min idanu. Ba zan iya jurar wannan abu ba, na zabura na tashi tsaye da sauri, har wayata da take kan cinyata ta fadi. Nayi sauri na wawureta tare da sungumar jakata na rataya, na kalli Janan da Anty Sarah da suka bini da kallo cike da mamaki.
Nace “zan tafi ne, Anty Allah ya raya baby, Janan, sai mun hadu ko?”. Anty ta amsa da ameen, Janan kuma ta matso kusa dani da niyar taka min zuwa waje.
Ina tunanin sai lokacin Yaya Jameel ya kula da nice a cikin falon, yace “a’ah! Wai dama Na’ilah ce?”.
Na daga kai a hankali ba tare dana kalli inda yake ba.
Yace “ke kuma sai kawai muji labarin aurenki daga sama babu sanarwa kamar saukar aradu?”. Mutanen falom suka saki dariya da jin haka, nima sai dana dan murmusa.
Yace “da gaske fa! Da har munyi fushi ai, daga baya dai na hakura. Allah yasa ranar asabar din zamu je daurin auren wani abokinmu, tunda shi nashi da safe ne ba kamar naku na rana ba, in Allah ya yarda zamu yi kokari mu leka”.
Na gyada kai a hankali, nace “Allah ya yarda”. Ban tsaya jiran jin wani yace wani abu ba, na daga kafa na fita daga cikin falon da sauri Janan tana bina a baya.
Muna fita, Allah ya taimakeni naga dan adaidaita sahu, na tsayar dashi da sauri na haye. Ko tsayawa muyi sallamar kirki ni da Janan banyi ba, dan adaidaitan yaja muka tafi.
A cikin adaidaitan, na saka fuskata cikin hannuwana, ina kokarin slowing down irin gudun da zuciyata take yi. Nayi tunanin na manta da Yaya Bilal a cikin raina. Nayi zaton na binne shi a cikin raina gabadaya. Ashe I was wrong. Innalillahi, na shiga uku. A haka zanyi auren?.
Cikin wannan tashin hankalin na sauka garin Gashua washegari. Ganin su Fatsu da kuma yan biyun Sailu da suka yi wayo bul-bul abinsu, shi ya sanya gabadaya na manta da ganin Yaya Bilal da abinda hakan ya haddasa min a cikin raina.
Tunda na sauka ban huta ba, Fatsu bata bari ko rintsawa inyi cikin sauki. Ina sauka, masu gyaran jiki suka tare ni da kayansu na tsuguno da turaruka. Washegari kuma aka yi su dilka da halawa. Kwana biyun nan da nayi, ba karamin gyara na sha ba. Ni a karan kaina sai da naji canji a jikina ba na wasa ba.
Ko a ranar da zan tafi, tare muka tafi da wata mai gyaran jikin, zata cigaba da gyaran data fara har zuwa ranar da za’a kaini gidana. Daga Maiduguri tazo, diyar wata aminiyar Fatsu ce wadda suke mutunci da ita sosai.
*
Tun ana saura kwana uku biki gida ta fara cika da yan’uwa na nesa. Mutanen Gashua da yawansu sun zo, sauran kuma sun tsaya a gida da yake suma can kalar nasu bikin zasu yi.
Janan ana saura kwana biyu fara biki tazo, muka hadu dasu Kulsum da sauran abokanmu muka cigaba da planning harkar bikinmu.
Da yake akwai dakuna biyu manya spare a cikin gidan, nan aka gyarawa yan biki. Duk da haka, ranar da aka fara harkokin bikin, sai da wasu bakin suka dangana da dakin Anty Alawiyya da namu dakin. Su Hajiya Ramata kam kane-kane tayi, babu wanda yayi gigin tunkarar dakinta ma saboda yadda ta cune fuska.
Ranar bikin ma haka ta yini tana ta shiga da fita tana zubda habaici, sai dai duk cikinmu babu wanda ya tanka mata. Muka cigaba da gudanar da bikinmu.
Wani abin mamaki shine, har ranar da muka yi walima, babu wanda muka gani ya leko daga cikin dangin anguna. Shi dama ango sai ranar daurin aure muka yi dashi zai zo, kwana uku ne kadai aka dauka ana shagulgulan bikin Koda na mishi korafi, cewa yayi kada in damu, zasu zo ne. Har ranar daurin aure shiru.
Maganar tafiya ma bai sake tada min ita ba, kuma a yadda muke tunani, an daura aure ranar asabar, jirginsu zai tashi ranar Lahdi da yamma. Dana taba tambayarshi yadda za ayi, naga yana neman manna min hauka, wai me yasa na cika wutar ciki ne da gajen hakuri? Na ga an daura auren ne ya dauki kafa ya barni ne? In zuba idanu mana in ga abinda zai faru. Na bashi hakuri a lokacin, na kuma kawo idanun na zuba mishi kawai.
Ranar assabar, ranar da za’a daura aure. Karfe goma sha biyu na safiyar ranar za’a daura auren a babban masallacin juma’ah dake nan cikin unguwarmu. Da safen muna can gidansu Kulsum saboda yadda gidanmu ya cika da jama’a babu masaka tsinke.
Na lume akan katifar Inna a can uwar daka, duk da uwar kwalliyar da nasha, da kuma zufar da ake yi, hakan bai hana ni fita ko nan da falo ba. Tunda garin yau ya waye, ko in ce tun a daren jiya ma, nake jin wata irin faduwar gaba akai-akai. Zuwa yanzu gabadaya jikina yayi sanyi lakwas kamar an watsa min ruwan sanyi a jiki.
Idanuna kur akan agogon bangon dake cikin dakin makale a jikin bango. Duk wucewar dakika daya, da karuwar faduwar gabana take wucewa. Har lokacin da hannuwan agogon suka hau kan sha biyu, suna nuna karfe sha biyu ce daidai a wannan lokacin. Jikina ya hau rawa yana kadawa, shikenan, na zama danyar nama.
Karfe goma sha biyu da rabi, na jiyo muryar Malam a tsakar gida da sauran muryoyi. Ban san abinda yake faruwa ba, ban kuma yi yunkurin tashi inji mai yake faruwa din ba, na cigaba da zamana. Sai da Inna ta shigo dakin ta ganni, tace “kina nan ashe? Ai an daga auren zuwa karfe hudu na yamma”.
Daga farko ajiyar zuciya naji ta ziyarce ni, kafin na kalleta a rikice, “me yasa?”.
Tace “wallahi nima Malam bai fada min ba, kawai dai yace sun ce an daga”.
Ina ji da yawa suna fata da addu’ar Allah yasa hakan shi yafi alkhairi, a zuciyata nace ameen.
Idan haka ne, kenan yana nufin sai gobe sannan za’a tafi Zaria da ni. Tsarin dama shine idan aka daura auren yanzu, zuwa bayan azzuhur kuma sai yan kai amarya su dauki hanya. Nayi kokarin tuntubar angon nawa ta waya inji yadda ake ciki, waya bata shiga. Tun da yau tayi ban samu wayar shi ba, nayi tunanin ko network ne ya hana tunda a jiya da rana da muka yi wayar mu ta karshe dashi, yace yau da sassafe zasu taho da abokan shi.
Na sake kokarin tuntubar babban amininshi, Salisu inji ko me yake faruwa, wayar shi ta karaci kara har sau biyu bai daga ba. Daga karshe na maida wayar cikin jaka.
Haka kawai naji wani kuzari ya shige ni, na mike na fito tsakar gida, muka cigaba da harkar mu ni da ‘yanmata na.
Kafin yammar tayi, gabadayanmu mun canza kayan jikinmu. Ni da Janan muka saka yadin da Ummahnsu ta dinka mana, su kuma sauran yanmata suka sanya ankon da muka yi.
Duk kokarin su shirya suke yi, saboda saurin kada anguna su zo damar hoto ta wuce su. Angunan da har yanzu banji wani yace yaji daga garesu ba. Har yanzu muna gidan Inna ne.
Bayan gotawar karfe hudu da mintuna kadan, muka jiyo sautin guda daga cikin gidanmu. Naji kafafuna sun yi wani irin lakwas, na fara kokarin zamewa kasa da sauri na jingina da bango.
Duk da haka, sai da naji wasu irin black spots suna kokarin dabaibaye idanuna lokacin da wata zabiya, irin marokan nan, ta fado gidan tana rangada guda.
“Ina amarya, amarsu ta ango! A zo a bani tukuicin wannan daddadan sako da zan isar, nima kakata ta yanke saka. Wa ya sani ko daga kanki sana’ar roko ta barni? Allah ya yarda, alkawarin Allah ya tabbata, aure ya dauru….!!”.
✌✌✌😉😎
*☆⋆33⋆☆*
Marokiya bata kula da halin hargitsi da amarya ta shiga bane da alama. Sai data gama jan kirarinta, ta kara gaba. Duk cikinsu bana tunanin wani ya kula da halin da nake ciki ma gabadaya.
Tana fita, wani marokin ya leko shi har da yar karamar gangar shi a hannu, ya tsaya daga soro yana zuba nashi kirarin.
“Ina amarya, tazo ita kuma ta bani kujerar makkah. Ranar farinciki da murna ga masoya, Allah ya nufa, alkawarin Allah ya cika, aure ya dauru tsakanin Muhammadu Bilal da Malama Na’ilah!! Allah ya bamu ikon dawowa badi war haka mu sake shafa wata fatihar ta ‘ya’yanku! Eh, a gayawa amarya, maroki dan na Halimeme na jiran nashi kason, ango Bilalu ya burge shi da sababbin kudi babu ko kari, farare tas bugun Abuja!….”.
Ai lokacin amarya Na’ilah babu ita. Tunda ya furta kalmar sunan Bilal, naji duk wata dauriya ta rike kafafuna su tsaya a tsaye ta bar jikina, karshe dai sai dana kai ga silalewa kasa.
Abu na karshe dana gani, shine confused fuskokin mutanen da suka yo kaina a rikice, suna kwala min kira, duhu ya mamaye ni gabadaya…!
*
Ban tuna komi ba lokacin dana tashi. Mutane hudu ne a kaina lokacin dana farfado daga suman da nake kyautata tunanin nayi. Janan da Anty Halima kadai na iya ganewa, sauran biyun tare suka zo da Anty Haliman daga Gashua, ban gane su ba.
Na tashi zaune, Janan tayi saurin tara filo a bayana yadda zan ji dadin jingina duk da protests dina na cewa kada ta damu.
Dakin da muke ciki daga gani babu tantama asibiti ne, ko kuma karamin clinic.
Janan ta bude gorar ruwan faro ta tsiyaya a cikin kofi ta miko min, na amsa na kafa kai na sha tare da mika mata, ta amsa ta ajiye.
Na dafe kaina da yake sarawa tunda na tashi, ina kallonsu.
“Me ya faru ne?”. Na tambaya cikin sarkewar murya, wincing lokacin da naji kaina ya kara sarawa kamar ana buga ganga.
Janan tace “Wanda zaki aura ne ya faru!”, duk yadda taso ta nuna tsana da venom a cikin muryarta, fuskarta dauke take da murmushi mai tsananin taushi.
Sai lokacin komi ya fara dawo min cikin kai daki-daki.
Na fara girgiza kai a hankali, kafin na fara da karfi ina ja da baya har sai da bayana ya hade da allon gadon. Na dora hannuwa biyu kai, ihu naso kurmawa, amma babu abinda ya iya fita daga bakina. Daga karshe dai na samu sautin, “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Na shiga uku na lalace!!”.
Kafin naji na barke da wani irin kuka.
Anty Halima ta matso ta rungumeni jikinta ta fara shafa gadon bayana cikin alamun lallashi. Tace “ke ‘yar nan, ki kiyayi kanki ke kuwa, menene na shiga uku? Allah ya dube ki, ya baki miji na nunawa sa’a. Kowa yasan dama hakan da mamaki, ka auri wanda baka shiryawa ba, amma bai kamata kalma ta shiga cikin uku ta fita daga bakinki ba. Ki godewa Allah, Allah kadai yasan irin hikimar da take cikin wannan juyin lamari daya faru”.
Amma kuma kukan naci gaba dayi, har ma na yanzu yafi na dazu sauti.
Tun tana lallashi, har ta gaji, ta koma gefe ta zubawa sarautar Allah ido, tana kuma mitar ai sai inje inyi tayi, a kaina farau?, amma ban kulata ba.
Sai da nayi ya ishe ni, kuka share-share har da majina, ‘sai kace wadda aka aiko mata da sakon mutuwar uba, ba aure ba!’ a cewar Anty Halima bayan taga yadda fuskata ta baci da hawaye.
Janan tana gefe, kallona take daya bayan daya, babu alamun damuwa ko digo daya akan fuskarta sai ma amusement rather. Hakan ya kara tunzura ni.
Ta zari tissue ta miko min, na warta na share hawayen fuskata da majina, nayi jifa da tissue din can gefe guda.
Janan ta kasa danne dariyarta, tace “a’ah, baiwar Allah. Ba fa shi ya kar zomon ba, haka muma da kike wani huhhura mana hanci. Don haka idan ma zaki ware ne yarinya, ki warware”.
Na harareta tare da sake wartar wani tissue din na goge idanuna da suka cika da hawaye.
Nace “wane warwarewa kuma? Ai wallahi zuwa zasu yi su warware aurennan yadda suka kulla shi, don wallahi ba za ayi wannan kwamacalar dani ba! Idan kuma ba haka ba sai dai in bar musu garin wallahi!”.
Su duka suka yi shagara da baki suna kallona, kafin Anty Halima ta daga baki da niyar fara magana, “wannan wace maganar banza ce kike yi? Ke…”.
Maganar ta katse sakamakon kofar dakin da aka turo aka shigo, duk muka kalli kofar. Faduwar gaban data ziyarceni a lokacin da muka hada ido da ba kowa ba illa Yaya Bilal Allah kadai yasan irinta. Nayi saurin kauda kaina na kalli Yaya Mudatthir, daga ganin yanayin fuskarshi kasan cewa sun gama jin abinda na gama fada yanzu. Sai dai ban ji ko dar ba a cikin raina, hasalima can cikin raina cewa nayi gwanda da maganar ta shiga kunnen wanda aka yi dominta.
Fuskar Yaya babu yabo babu fallasa, ya cewa su Yaya Halima “Anty ko zaku dan bamu waje?”.
Babu musu suka fita suka bar dakin, suka barmu mu kadai. Yayan ya kalleni fuska cike da warning tsantsa, kafin ya shima ya juya ya fita, har da maida kofar dakin ya rufe. Na harari kofar kamar ita ta min laifin.
A hankali ya tako cikin taku dai-daya, yazo ya tsaya min aka kamar wani tsohon soja, ya zuba min ido. Ni kuwa naci gaba da kallon kofar da Yaya Mudatthir ya bi stubbornly.
Ganin an dauki lokuta masu yawa ba tare dana sake ko jin motsin shi ba, yasa na daga idanu a hankali na kalli inda yake. Yana tsaye a wajen har lokacin, ko yanayin tsayuwarshi bai canza ba, idanunshi manya tubarkallah dasu kamar na Janan, a kaina. Na turo baki tare da sake dauke kaina.
Ina jin sautin murmushin daya saki, ya ja farar kujera dake can karshen dakin, ya ajiyeta a gefena ya zauna.
Murya can kasa, kamar mai rada yace “ya jikin?”.
Nan ma ban ce komi ba, na kurawa mayafin da aka lullube gadon da nake kai idanu.
Ya sauke ajiyar zuciya, “ko ki amsa, ko kada ki amsa, hakan babu abinda zai sa, kuma babu abinda zai hana Na’ilah. Abinda ya faru dai ya riga ya faru…”.
Nayi saurin katse shi, “bai riga ya faru ba, ni wallahi ban yarda ba, aurennan sai an zo an raba shi, dama tun farko ai sai dana ce ba zan aure ka ba!”.
Yayi wani kicin-kicin da rai, “wannan kuma sai ki samu wanda ya daura auren kiyi mishi bayani, sai ya warware. Tunda nima ina zaman zamana sai kiran waya kawai naji ance za’a karbi wakilcin aurena, in kawo sadaki. Kin kuwa ga nima daga sama na tsinci maganar kamar ke dinnan”.
Nace “to haka ake aure, babu tambayar wadda zata yi zaman auren?”.
Ya daga kafada sama, “kamar yadda nace ne, zuwa zaki yi ki tambayi wadanda suka daura auren. Amma a shawarce, zan baki shawarar ki ma sauke wani girman kai, jiji da kai da jan ajin da kike yi, kamar yadda nace, abinda ya faru dai ya riga ya faru sai dai kuma a tari na gaba. Yakamata ki san irin kalaman da zasu fito daga bakinki, saboda da da yanzu ba daya bane, idan kinyi da na kyaleki, ina mai tabbatar miki da cewa yanzu fa ba zan kyaleki ba saboda a karkashin Ikona kike, saboda haka ki kula”.
Kawai sai na sa kuka, yayi zaune a gefe yana kallona bashi da niyar furta ci kanki, nayi na gama na share hawayena, nace “to dama haka ake auren ne, tun kafin aje ko’ina ka fara cin zalina da gindaya min sharadi”.
Yace “watch it Na’ilah! Yadda fa baki shiryawa auren nan ba, haka fa nima. To meye ma amfanin auren idan babu doka da sharudda? Abinda nake so ki sani shine, lokacin lallashi da bin kai ya kare tsakanina dake, tunda ke kafiyar kai tasa baki fahimtar komi sai an biyo miki ta bayan gida, let’s bring it on then. Ta kowace hanya kika bullo, nasan ta yadda zan taro ki.
Ke yanzu hakan bai isheki ishara ba? Ki hakura ki saddakar, ki mika wuya ga hikima irin ta Allah ba? Ni din dai da kika dinga gudu Na’ilah, kina ihu da sanarwar ba zaki aure ni ba, ni din dai kika buge da aure bayan kin gama kewaye-kewayenki. Dama kin hakura tun farko, kin kauda wannan girman kan da kike ji dashi, da yanzu muna cikin farinciki gabadayanmu. Amma yanzu wa gari ya waya? Saboda tsabar son kai da taurin rai irin naki, kinga abinda kika janyo mana ai. Yaushe rabon da kici abinci ya cika miki ciki? Yaushe rabon da kiyi barci mai dadi? Yaushe rabon da ki samu sanyin zuciya da sukuni a cikin ranki? Yaushe rabon da ki samu wadataccen kwanciyar hankali? Ki duba kiga yadda kika bi kika rame, kika kare kamar kudin guzuri? Ni da kika dinga gudun ma dai sai da nazo na fiki kwanciyar hankali da jindadin rayuwa. Hakan bai isheki ishara ba Na’ilah? Me kuma kike bukatar gani da zai tabbatar miki da cewa ba’a taba tsallake abinda Allah ya riga ya tsara maka? Duk zullewarka, zaka yi ne ka gama. At the end of the day dai, sai ka komawa wannan kaddarar taka!”.
Nayi shiru ina sauraron yadda yake maganar a zafafe, daga ji babu tambaya a matukar fusace yake, dani ko kuma wani.
Naci gaba da shesshekata har da jan majina, yace “ni yanzu haka Zaria zan wuce abina, zan je in fara shirin inda za’a sauke ki. Don haka kina da sati daya, daga yanzu zuwa rana irin ta yau, ki gama yanke shawarar yadda zaki yi, aure tsakaninmu dai ya dauru, babu kuma wani mahaluki da zai sanya ni datse shi, don haka you might as well take heart, shawarata a gareki kenan”.
Ya mike yana gyara link din hannun rigar shi, “duk abinda kike bukata, zaki iya kiran wayata, ko kuma ki fadawa Janan, zata fada min. Sai anjima!”.
Yasa kafa ya fita daga fadin haka, babu ko waiwaye.
I was too shock, ko hannu na kasa motsawa balle gangar jikina. Baki a dage, ido a bude akan kofa, haka su Janan suka shigo cikin dakin suka sameni. Wato ni za’a nunawa attitude? Lallai kuwa.
Janan ta fara tarkata mana kayan da aka baza a dan lokacin, likita ya shigo ya kafa min dokar cin abinci da samun barci isasshe. Ni dai jinshi nake yi, ya gama dogayen bayananshi, ya sallame mu muka kara gaba.
Da yake clinic din anan cikin unguwarmu yake, a kafa muka karasa gida.
Zuwa lokacin kowa yaji labarin yadda daurin aurena yazo da canjin yanayi, kuma canjin ango. Nan da nan mutanen da suka yi saura suka rufa a kaina da kalmomin ‘sannu, ya jiki? Ashe abinda ya faru kenan? Sai ayi ta hakuri, Allah ya nufa shine mijin’, wasu kuma har su kara da ‘ai dama naji ance kun yi soyayya dashi, abin ya kwana gidan sauki ma’, da dai sauransu.
Muka samu muka yakice su da kyar muka shige can kuryar dakin Anty Alawiyya, Allah yasa babu mutane sosai.
Na zauna a gefen gado, Maryam ta tafi nemo min abinda zan ci in sha magungunan da aka bani, Janan kuma ta zauna a gefena.
Nace mata “me ya faru da Dr. Ne?”. Babu wanda naji ya sake tado zancenshi, ga yanayin yadda suke nunawa kuma, basu da alamun yi mun bayanin abinda ya faru.
Ta tabe baki, “hmm, mutuminki ba sai suka shanya yan daurin auren ba? Tun ana jira har aka gaji, babu wani dangin ango da aka gani a wajen daurin aure. Yaya Jameel ne da yazo daurin aure ya kira wani abokinshi yaje har can gidan su angon ya tambayo ko lafiya? Zancen da nake miki, ashe bawan Allah ya kwana ya huce a kasar London, ya bar sakon a gaya miki yana miki fatan alkhairi, amma idan kinga zaki iya jiranshi nan da shekaru biyun, to babu damuwa. Amma a halin yanzu ba zai iya daukar hidindimu masu yawa ba, liability yace. Shine su kuma cikin wadanda ya barwa sakon, daga abokai har yan’uwa, aka rasa wanda zai iya tako kafarshi yazo yayi bayani a mutunce kamar yadda aka faro a mutunce. To ana shirin sallamar mutane ne a basu hakuri, Yaya Jameel yace ba za’a yi haka ba, tunda an san da manemi a gida, ai kawai yazo ya biya sadaki, shine fa aka daga daurin auren zuwa yamma yadda Yaya Bilal yazo ya samu daurin auren”.
Na jijjiga kai cikin sanyin jiki, wato har zabata aka yi akan abin duniya, aka kuma kirani liability? Allah kenan. Shi kuma Yaya Jameel, apparently shine makasudin jefa ni cikin ha’ula’in da nake ciki yanzu kenan?.
Janan ta dafa kafadata, “meye na wani abin damuwa anan? Ai in gaya miki ki kwantar da hankalinki Hajiyata, ki je ku kwashi soyayyarku wallahi. Shima Yayan fa ba karamin dace yayi ba, naji ance kusan mutane hudu suka nemi aurenki a take a lokacin”.
Na ciza lebe kawai ban ce mata komi ba. A haka Maryam ta dawo ita da Kulsum, da kwanon abinci a hannunta. Haka nan saboda damun da suke yi min, na tuttura abincin ba don ina so ba. Kafin in gama an kira sallar magriba, duk muka yi harama suka yi.
*
Zuwa washegari gidan ya baje da yan biki, sai yan daidaiku da zasu tafi washegari. Shima Yaya Mudatthir a ranar ya juya. Janan tana makale a gefena, bana lekawa ko nan da kofar gida sai na sha fada da mita kamar itace mijin gabadaya.
Sai da safe dana je gaida Baba, sannan yayi min bayanin halin da ake ciki. A raina nace ‘ihu bayan hari kenan’. Ya nanata min nan da sati daya za’a tafi dani, in shirya, nace mishi to.
Anty Halima taci gaba da zama damu, wani sabon gyara suka fara min ita da Anty Alawiyya babu kakkautawa. Anty Alawiyya ta kan ce, “zama cikin mata biyu musamman hamshakai yadda naji ana bada labarin matan mijin nan naki sai an dage Na’ilah. Don haka ki dage, ki kama kanki, ki taimaki kanki kafin ki zama saniyar ware”.
Abinda bata sani ba shine, maganganun nan nata babu abinda suke kara min sai tashin hankali da taraddadi.
Wasu lokutan kuma haka zata zaunar dani tayi ta min nasihohi da maganganu, salo iri-iri na kissa da kisisina har mamaki take bani wani lokacin. Sai dai bana bin abinda take fada ko daya, kawai jinta nake yi. Mijin da ba’a so, gidan da ba’a so, meye na koyan makaman zama dasu? A ganina fa kenan.
Cikin dan wannan lokacin ban sake ji daga angon nawa ba, babu kira, babu text, babu komi. Wani lokacin ina ji zasu dinga yin waya da Janan, ya tambayeta ya nake, ko kuma akwai wata matsala ne? Haka zasu yi wayar su gama ya kashe, babu ko sakon gaisuwa.
Hakan ba karamin kona min rai yake yi ba, a ganina tun ma kafin aje ko’ina ya fara wulakanta ni, ina ga yaga na shiga gidanshi? Nima sai na shaka fiye da yadda yakamata, nayi watsi da al’amuranshi. Tashin hankalin da nake ciki ma baya barina tunanin wulakancin da yake yi min.
Kwanakin sai suka dinga wucewa kamar a cikin kiftawar ido da bismillah, kafin in ankare, lokacin barina gida yayi.
*☆⋆34⋆☆*
Kafin zagayowar ranar tarewata, sai dana zama kamar wata matar Malam. Kullum ina fama da carbi da doguwar hijabi a jiki ina ja, cikin dare zan tashi tun daga farkon dare har karshen shi, washegari in tashi da azumi a bakina, addu’a daya ce nake yi ina maimaitawa; ‘gidan Yaya Bilal, Allah ka tsareni da shiga wannan gida, Allah kamar yadda ka raba gabas da yamma, Allah ka raba ni da shiga wannan gida’.
Sai dai a kwana na biyar, dole na gama saddakarwa, na fara addu’ar neman ceto da taimako saboda babu alamu ta ko’ina mai nuna cewa zuwana gidan Yaya Bilal zai fasu. Ranakun kullum kara matsowa suke yi, hakan kuma yake kara saka ni cikin tsananin damuwa. Watakila dai karshen farin cikina ne yazo.
Tunda aka daura auren, na fara wasu irin mafarkai masu ban tsoro. Sai inyi mafarkin wata mata, fuskarta a rufe da bakin kyalle ta biyoni a guje da wuka a hannunta zata caka min, watarana sai inga nayi tuntube na fadi ta cimma ni, sai inga hannu ya zuro ya daukeni. Wani lokacin kuma haka zamu yi ta gudu, endlessly, babu kakkautawa. Haka zan tashi jikina sharkaf da gumi da zufa kamar an watsa min bokitin ruwa.
Don haka na dage kwarai da addu’a da kuma azkar, har su sadaka ban bari a baya ba.
Musamman Malam din su Kulsum, yayi rubutu ya kawo min ina sha safe da rana. Haka Anty Halima da Anty Alawiyya ma basu kyaleni ba, daga Gashua Fatsu ta aiko da sassake-sassake da magunguna iri-iri da addu’o’i, na lazimce su. Duk da cewa daga farko kin yin amfani nayi dasu, a wautata meye amfanin su to? After all, dama ba zaman gidan nake son yi ba.
Anty Alawiyya ce ta saka ni a gaba da fada da nasiha don ita Anty Halima cewa tayi ta gaji da lallashina, ta koma gefe ta kyalemu.
Anty Alawiyya tace “ke sakara ce wallahi, kina yin abu kamar wadda bata san abinda duniya ke ciki ba, ko kuma baki je kinyi karatun zamani ba. Don kina da kishiyoyi sai me wai? An gaya miki karshen duniya ne yazo? Ki shiga cikin kishiyoyi, ku buga ke dasu aga wadda zata sace zuciyar mijinta ta hanyar da manyan matan annabawa suka bi suka kwace zuciyoyin mazajensu, sai ki zama zara wadda tayi zarra. Amma ki zauna a gefe kina bata ranki a banza, wannan ai aikin kawai ne. Me zaki karas nan gaba?”.
Nace “hmm, Anty sai ki dinga yi kamar baki san komi ba wallahi. Ki duba fa irin zaman da kuke yi da taki kishiyar a nan gidan. Sannan ki fa duba yadda yanzu aure yake mutuwa, abin har ya zama kamar yayi. Idan kuma kika yi duba, mafi yawa rabuwar auren kishiya ce take haddasa shi. To idan kishiya daya ta fitar da mace daga gidanta, ni da zan zauna da kishiyoyi biyu fa? Ai ko barbashin toka ta ba za’a gani ba”.
Anty Alawiyya da Janan dake gefena a zaune suka kwashe da dariya, na harareta abinda nafi yi tunda aka daura min aure.
Anty Alawiyya tace “ke yanzu zaman gidan nan namu har zaki iya kiranshi zaman kishi?”, ta girgiza kai, “ba zaman kishi muke yi ba Na’ilah, zamane muke yi irin na mutanen farko. Kafin hasken musulunci ya sauko, zama na rashin adalci, amma ba kishi bane. Ai ba haka kishi yake ba. Kishi shine inda zaki fito ke da kishiya, ku hada kirji ke da ita, ku rikita mijinku da ririta ta hanyar kissa, ladabi da biyayya, domin neman fada a cikin zuciyarshi. Kishi ba bin bokaye da malamai bane domin neman gurbi a cikin zuciyar miji, a kuma muzgunawa wadda ake zaune da ita, wannan jahilci ne.”
“Ni kaina daga farko wannan shine tunanina akan kishi, sai daga baya na fahimci sam ba haka bane, ashe shirme ne. Shi yasa nake matukar kokarina wajen ganin cewa kin fahimci shi zama da kishiya, wallahi ba matsala bace, ba kuma damuwa bace. Matukar kina da gurbi a cikin zuciyar mijinki, kin kuma kama shi kam kin rike, to abinda kike bukata kenan. Me zai yi ruwanki da wata kishiya can? Ita dai ba ita ta zaunar dake ko take ciyar, da shayar dake ba. To menene abin tada jijiyoyin wuya? Yanzu baki ga yadda muke namu zaman ba ne? Ita ce babba, amma wa kika gani yana jan ragamar gidannan gabadaya yanzu?”.
Nayi shiru ina jinta, da gaskiyarta. Yanzu ita ce take juya gidannan son ranta, har shi Baban. Ko hidimar bikin nan da aka yi, komi a hannunta yake, kowa ita yake nema idan wata bukata ta taso. Babu ma wanda yake wani tunkarar Ramata, dama bata saka kanta cikin hidimar bikin. Na kuma kula tunda na dawo gida hutun sallah dama kamar fadarta tayi kasa a wajen maigidan, har yanzu dai Anty Alawiyya ce take murza kambun mulkinta.
Tace “bana so ki bi hanyoyin da zafin kishi ya sanya ni bi Na’ilah, hanya ce halakakkiya mai halaka mutane, sai wanda Allah ya tseratar ne kadai yake tsira. Don haka ne nake so ki kwantar da hankalinki, ki tattara shi waje daya ki mayar kan mijinki, ki maida wata matsalar kishiya gefe, zaki ga duk su din ba wasu abubuwa bane, zaki kuma ce na fada miki watarana. Amma kafin nan sai kin kai zuciya nesa, kin kuma yi hakuri, amma da yardar Allah watarana sai dai ki tuno kiyi dariya kawai. Sai dai hakan ba zai faru ba, sai kin tashi tsaye, dole sai kin nemi taimako da tsari daga ayoyin Allah. Tsafi gaskiya ne, kuma a yadda nake jin labarin wannan kishiya taki, ba karamin dabi za’a sha da ita ba. Dole sai kin dage”.
Wadannan maganganu su suka kwantar min da hankali. Na karbi kofin rubutu data bani, nayi bismillah na sha. Daga nan kuma naci gaba da amfani da sauran magungunan.
Cikin ikon Allah, kafin zagayowar sati, ni a karan kaina naji canji a cikin jikina sosai. Mafarkan da nake yi ba daina yin su. Haka naji a hankali idea din zama da su Raheemah da Ameerah ya daina terrifying dina sosai. Da idan na tuno yanzu sun zama kishiyoyina, kuma zan zauna dasu, sai inji har numfashi nake fitarwa da kyar. Amma a yanzu, sai inji idea don’t is not that bad. Har zama zamu dinga yi ni da Janan muna hira a kansu, tace zata so taga expression din Raheemah lokacin da Yaya zai fada mata ya kara aure, kuma ba wata bace ya aura face ni. Ni kaina da nayi kokarin yin picturing yadda zata yi a lokacin sai naji ina fashewa da dariya. Muka hau kyalkyala dariya ni da ita kamar wasu sababbin kamu, sai da Anty Halima ta leko tana fada sannan muka dan saurara.
Ranar Alhamis aka yi min turaren jiki dana gashi, kasancewar wancan a kurarren lokaci ne, ba’a samu anyi komi ba. Bayan anyi turaren, wata kawar Kulsum tazo ta kama min gashi ta kitse shi sosai, karshen kitson sai data dinga sanya white gel tana kame min shi saboda kada ya warware da wuri. Ranar har dare muna tare dasu muna ta hira. Makitsiyar Nana, tana bamu labarin irin zaman kishin da aka buga a gidansu, su saboda tsabar damben da matan gidansu suka yi, gidan yan dambe ake kiran gidansu a unguwarsu.
“Amma yanzu gashi hakan ya zama tarihi, Anty ma Inna Hadiza take kiran babarmu yanzu”. Duk muka kwashe da dariya. Haka dai muka wuni muna shan hirarmu da abokanmu.
Washegari kuma ranar Juma’ah, Anty Halima da Janan suka riga mu tafiya Zaria jeren kayan daki. Sun ce wasu ma guda biyu da zasu tafi da kayan daki daga Gashua zasu je can Zaria din, zasu hadu. Muka yi sallama dasu.
Ranar assabar, karfe tara na safe, motoci biyu suka fara danna horn a kofar gidanmu. Dama sun ce da safe masu daukar amaryar zasu zo.
Tun da safe Anty Alawiyya tasa nayi wanka, ta dauko wata doguwar rigar gown ta wani yadi na saka.
Tun bayan da aka daura auren, aka mayar da duk wasu kudi da kayan Dr. Na Abba dake hannunmu. Wannan rana rigar ta jikina ma, Anty Sa’a yayar su Janan ce ta kawo min ina washegarin daurin aure da tazo, kala biyar ne ire-iren su masu kyau. Dama tana kawowa Janan ta zare wannan rigar tace ranar da za’a kaini zan sanya ta.
Bayan na gama shiryawa, muka tafi dakin Baba yin sallama. Tun lokacin idanuna suka fara raina fata. A dakin Baba, nasiha yayi min sosai akan rayuwar aure da kuma muhimmancin yin hakuri a cikinta, ya rufe da yi min addu’a da fatan alkhairi a cikin rayuwar aurena. Tun ma kfin ya gama, na kuka sosai na tashin hankali.
Ya dauko kudin da aka biya na sadakina, dubu dari biyu cif babu ragi babu kari, ban ma san abinda zanyi dasu ba, kai kawai na girgiza mishi.
Yace “ba zaki amsa ba nufinki?”
Na gyada mishi kai, yace “ai ba za’a yi haka ba Na’ilah, hakkinki ne. Amma tunda kin nuna ba zaki amsa ba, zan turawa Yayanki kudin, ba za’a rasa abinda za’a sai miki dasu ba. Hakan yayi?”. Na gyada mishi kai.
Yace “to madallah. Sai ku tashi kuyi haramar tafiya, Allah ya kiyaye hanya, Allah ya tsare. Allah yayi miki albarka Na’ilah!”.
Hakan shi ya sa na kara fashewa da wani kukan mai sauti, tunda muke da Baba, sai yau ne na taba jin kalmar sanya albarka ta fita daga bakinshi. Ban san abinda zanyi ba a lokacin, da yafi inyi kuka.
Kafin in fita daga dakinshi, Maryam ta fita da akwatuna biyu da aka shirya min kayana a ciki zuwa cikin mota, da sauran tarkace. Jiya aka tafi da duk wasu kayan bukata, tun daga kayan gara, kayan kicin da sauransu.
Daga dakin Baba, ko dakina ban koma ba, aka yi waje dani. Sai da muka fita sannan muka ga Ramata cikin tawagar masu bankwana da amarya, na matsa muka yi bankwana dasu ita da sauran yara da suke ta ihun kukan sai an tafi dasu, Anty Alawiyya ce take ta aikin lallashi da ban baki.
Baba da kanshi ya bude min gidan baya, na shiga. Kulsum, Maryam da Hauwa cousin dinmu da tazo jiya daga Gashua, suka shiga cikin motar da nake.
Dayar motar kuma sauran masu zuwa suka shiga. Ana ta daga mana hannu da addu’o’i iri-iri, direba yaja mota muka tafi. Kaina yana cikin mayafin da aka rufa min, hawaye kawai nake sharewa babu kakkautawa cikin tausayawa kaina. Ina ji Maryam ta kira Janan ta sanar da ita tasowarmu kenan, amma ko daga kai ban iya yi ba a lokacin.
Har muka isa Zaria idanuna basu daina digar kwalla ba. At some point zan daina kukan da nake yi, sai dai da na tunano yadda rayuwata zata kasance a cikin gidan Yaya Bilal, sai inji wata kwallar tana zubowa babu kakkautawa. Ji nake kamar in cewa direban ya juya damu mu koma gida, zama gaban su Ramata da duk rashin kirkinsu ya fiye min rayuwar dake shirin tunkaroni, sai dai nasan hakan ba zai yiwu ba.
Wajen karfe goma sha biyu muka shiga gidan Yaya Bilal. Motocin suka yi fakin, duk muka firfito. Janan, Anty Sarah da wasu daga cikin yan’uwansu yanmata sa’anninmu, har dasu Harira, suka fito suka tare mu tare da mana jagora har zuwa sashena. Shine na kusa da na bangaren Anty Sarah, duk da haka babu nisa dana Raheemah.
Janan ta tura kofar, na shiga da kafata ta dama kamar yadda suka umarceni, bakina dauke da tarin addu’o’i. Suka ja ni har zuwa bedroom dina, daga nan kuma masu yiwa amarya sannu da zuwa suka fara shigowa. Masu shakiyanci nayi, masu maraba nayi, masu addu’a nayi.
Kayan dakin da aka jera min ba karamin kyau suka yi ba, babu abinda zan ce da Baba da yan’uwanmu sai dai fatan gamawa da duniya lafiya.
Bayan mun gama hutawa, munyi sallah, Janan dasu Harira suka daukemu zuwa tour din gidan. Dakuna hudu ne da babban falo, sai kicin da main toilet, sauran dakunan ma duk suna da nasu bandakunan, inda biyu daga cikin dakunan aka shake su da jeren kayana. Gado, mirror, closet, da dai sauran tarkacen kayan daki. Haka ma falon, ya sha saitin kujeru masu kyau, babbar plasma, dinning table, har da wajen hutawa daga can gefe. Aka shimfida tattausan rug carpet, aka watsa tuntuna da sofa kwara daya jal, sai katoton vase na fulawa.
Kicin kuwa ba’a ma yin magana, duk wasu kaya da ake bukata a cikin kicin an zuba min su, dangin su electronics da sauran kaya na nunawa sa’a. Ban taba tunanin haka gidan aurena zai kasance ba, a yadda Baba yake, nayi tunanin kila gado ma sai an kai ruwa rana zai sai min, dana gayawa Anty Halima haka dariya tayi ta min, wai bani da saiti.
Komi na gida dai yayi Alhamdulillah, sai godiyar Allah kawai. Daga nan kuma suka ja ni zuwa daya dakin na kusa da nawa, shi babu komi a ciki sai tattausan carpet da aka shimfida, katifa, da desktop table da kofofi. Daga gani babu tambaya nan ne dakin maigida Bilal. Nan suka nuna min akwatunan da aka kawo min, Janan tace “Yaya Sa’a ce zai fi a barsu anan kawai, in kin zo kiga kayanki tunda idan ma an kaisu can din hidimar kai da kawowa ce za’a sha”. Na gyada mata kai cikin nuna fahimta.
Akwatuna ne irin na zallar leather dinnan, maroon, dai-daya har guda goma, kowanne shake da kaya. Tun daga na sawa, atamfa ce, laces, materials, yadika masu kyau da armashi, you name it. Kayan kwalliya kuwa kamar za’a bude shago. Harira da suke bude kayan, ta kalleni tana murmushin tsokana, “sai fa kin dage, mijinki mai dan banzan son kwalliya ne, ke kuwa naga alamu kwalliyar ba’a kanki ma take ba, kamar sauran taron matan can nashi daya ajiye dai. Idan kina so kiyi zarra, sai kin koyi amfani da kayan kwalliyar nan”.
Nace mata “to waye yace miki so nake inyi zarra a gidannan?”.
Tace “duh, lokacin da zaki fara shirin yin zarrar waya sani? Kawai ina baki head-ups ne idan lokacin yazo”. Duk suka kwashe da dariya, ni kuma na bisu da harara.
Suka ci gaba da bude akwatunan, dangin jakunkuna, takalma tun daga vincci, gucci, chanels, LV, babu wanda babu. Turaruka, gyale, hijabai, babu abinda babu. Kada ma fannin fashion ear rings da sarkoki su ji labari. Kayan yawansu har yayi yawa, I was very overwhelmed. Yayin da masu ba idanu abinci suke ta zubo addu’o’i, idanuna cike suke taf da kwalla da hawaye, sai fakar idanu nayi na goge su.
Daga nan muka koma dakina, wasu kuma suka tsaya a falo. Aka fara shigo da tarin abinci kala-kala, muka zauna muka ci. Zuwa lokacin da muka gama cin abincin, aka fita da kwanukan abincin, karfe hudu tayi. Lokacin yawancin wadanda suka zo duk sun tafi, ya rage daga ni sai su Janan kawai dasu Maryam da zasu koma Katsina gobe.
Anty Halima ta sanya ni nayi wanka, na sanya riga da zani na atamfa, ruwan goro mai zanen manyan furanni, aka dora min babban gyale a kaina, na saka takalmi flat, muka tafi sashen Raheemah, a cewarsu kai amanar amarya.
Suna zaune a falonta ita da gang dinta, har ma da uwarsu. Taci daurin dankwalinta irin wanda ta saba yi na yan duniya, ‘ya’ya sun zagayeta ana ta hira da shewa babu ko kunya.
Muka yi sallama muka shiga falon. Suka yi tsit, kamar ba su bane masu neman tada falon da hayaniya ba.
Babu wanda yayi mana masauku, suka nemi kujera suka zauna, ni kuma aka zaunar dani a kasan carpet. Kaina yana kasa cikin gyalena, naji su Anty Halima suna gaidasu. Babu wanda ya amsa, sai sautin “hummm” da “uhummmm” daya dinga tashi.
Basu daddara ba dai, Anty Halima tace musu “ga amanar diyarmu mun kawo muku, muna fata za’a rike mana ita cikin aminci da amana”.
Sai da suka shaki iska, sannan naji muryar Adi, “to ku kunji fa, maciya amanan wai sun kawo muku amana”.
Salame ta cafe, “Kaji ma wani rainin wayau fa anan wajen, Momcy. Sai da suka gama shuke-shuken munafurcinsu da kitsa rashin mutunci sannan wai suke kawo amana. Amanar me kuma? Ko roki a maida muku yar ku yadda kuka kawo ta mana, in one piece!”.
Momcyn tasu kuma ta kara da, “ku ne ma kuka zauna wani yi musu karin bayani. Ku bari idanunsu su gane musu mana, kishi da ahalin gidanmu ba karamin aiki bane, kuma duk wanda yace zai ja da gidan iko, to ba jikinshi kadai ba, na uwatai ma da ubanai sai sunji labari!”. Suka kuwa kwashi ihu har da sowa jin abinda tace.
Ganin abin yana wuce gona da iri, Anty Halima tace “to Allah ya baku hakuri, Allah ya gani mun sauke hakkin dake kanmu. Ku tashi mu tafi”.
Sai lokacin Raheemar ta sanya baki, ta tashi tsaye tana wani jijjiga jiki, “hakkin banza dana wofi! Ku har wani hakki kuka sani? Wato dama munafurcin zuwa nan gidan da take yi, tsaface-tsaface take zuwa tana binne mana a gida. Sai da tayi yadda tayi ta tsaface min miji. To wallahi bari kuji, karyarku ta sha karya. Idan kuna cin kasa ku kiyayi ta shuri. An shigo gidan kudi ana ta bude daddaudan baki da ya sha miyar kuka, ana murna an auri mai kudi. To murnar ku zata koma ciki, gwanda ma tun kafin a maida muku diyarku a nakasce, ku dauketa cikin salama ku maidata inda ta fito, idan kuma ba haka ba… tammm!!”.
Anty Halima tace “a’uzubillahi, mai kike fada ne haka? Allah ya tsaremuda aikata wannan danyen aiki. Mu ahalinmu babu masu aikata wannan danyen aiki, bamu taba ba, kuma ba zamu taba ba in Allah ya yarda”.
Nan fa suka yo mana caaa! Da ihu kamar zasu cinyemu danyu. Nan dai muka samu muka bar musu falon, muka barsu suna barazanar sai sun koya mana hankali gabadayanmu.
Muna fita Anty Halima ta kama baki, tace “ikon Allah, Allah sarki mai halitta. Mutane ku sanya kanku cikin uku babu gaira babu dalili? Yanzu banda duniya ta zama abinda ta zama, me zai sako uwa cikin lamarin auren diyanta, har ka ganta ta taka kafa taje gidan surukai tayi dororo?”.
Janan tace “Ai baki ga komi ba Anty Halima, idan har kina tare da mutanen nan, babu abinda zai dinga baki mamaki kuwa”.
Hauwa tace “aikuwa dai Girma ya Fadi wallahi, ba’a ji dadin rayuwa ba. Ai in an girma sai asan an girma, a barwa yara yarinta”.
Daga nan muka shiga wajen Anty Sarah. Nan kam tarba muka samu ta mutunci, aka gaisa a mutunce, aka bada amana suka karba, daga nan muka koma sashen na.
Muna shiga na yaye gyalen kaina na haye can kuryar gado na lafe. Abinda ya faru a sashen Raheemah, ta tabbatar min daga cewa lallai sai na kara daure damara a cikin wannan gidan. Ina cikin wannan sake-sake su Janan suka shigo, dole na mike zaune muka kafa sansanin hira dasu.
Da dare ina daki na jiyo shigowar Yaya Bilal nan sashen, ina ji suna gaisawa dasu Anty Halima da suke falo suna hira. Na zauna a gefen gado sosai, ina jiran ya shigo ciki inji da kalar wadda yazo. Ba’a jima ba na ji hayaniyar gaisuwar ta ragu, sai hirarsu da suka cigaba da yi da kuma karar tv, wato fita yayi babu ko leke? Na kuta tare da komawa na kwanta abina.
Ba’a jima ba suka leko, wasu suka mana sai da safe suka koma daya dakin suka kwanta, wasun kuma kamar su Janan, suka kwanta tare dani anan dakin.
Washegari muka karya da abinci mai rai da lafiya wanda aka kawo daga gidan Anty Sarah. Bayan mun ci munyi nak, muka yi wanka muka shirya.
Ina gaban mirror ina shafa man lebe a bakina, Maryam ta leko kanta dakin, “Yaya Na’ilah motar da zata maida mu tazo”.
Na kalli agogo naga karfe goma, naji jikina yayi sanyi sosai. A sanyayen nace “tun yanzu? Nayi zaton zaku kai ko gobene”.
Tace “haba, daga kawo amarya kuma? Mu daya kamata mu kauce tun jiya, mu ba ango damar cin amarcin sa?”.
Na mike tsaye ina harararta, “yarinyar nan kin baci da yawa wallahi, baki da kunya yanzu”.
Tayi dariya tare da maida murfin kofar ta fita bayan tace “kiyi sauri ki fito ke dai muyi sallama”.
Na saka kaya a gaggauce na fita falon, ganin Anty Halima da kaya a gaba nayi turus, nace “kema yau zaki tafi?”.
Tace “ehh mana, ko zaman daki kike so in zauna in miki?”, duk suka kwashe da dariya.
Nayi narai-narai da ido kamar zanyi kuka, nace “yanzu ba zaku dan kara kwana bane?”.
Huleirah tace “nop, not happening. Gwanda mu tafi tun ana ganin girma da mutumcinmu. Ko kuwa so kike angon ya kai ga korar mu ne?”.
Na jefa mata harara, “dallah can yi mana shiru, waye ya sako bakinki anan?”. Suka sake kwashewa da dariya.
Na shiga inda akwatuna suke, na cicciro kaya na fita na kai mika musu, Anty Halima tayi kir tace babu abinda zata amsa, “ce miki aka yi kyauta ake yi da kayan lefe ne? Mijinki kawo miki yayi don ki mishi kwalliya dasu ba wani abu ba”.
Nace “to ai sanya albarkarku ne nake nema, don Allah ki amsa Anty”.
Da kyar ta amsa, sannan suma su Maryam suka amshi tarkacen kayan kwalliyar dana basu, suna zuba godiya da sanya albarka.
Da yake a hannuna akwai kudin da Janan ta bani tace Yaya yace inyi hidimar biki dasu bayan an daura aure, babu abinda nayi dasu ma sai jikin jaka dana saka su. Na dauko na basu dubu dai-daya, Anty Halima kuma na bata biyar.
Tace “a’ah, har da kari? Kai Allah dai ya sanya albarka. Allah ya baku zaman lafiya ke da mijinki da zuriya dayyiba”.
Na dan yamutse fuska cikin alamun tambaya, “karin me kuma?”.
Tace “au, ashe fa kina barci lokacin daya shigo. Ai dazu da safe ya shigo muka gaisa shine ma ya sanar damu za’a zo a maida mu gida. Bayan haka kuma ya kara mana da kudin mota bayan shi ya bada motar da za’a kawo mu”.
Naji wani abu a cikina ya tsinke. Yaya ya shigo dazu da safe? Kenan hakan yana nufin guduna yake yi ne ko menene? Sanyin jikina ya karu.
Cikin sanyin jikin muka fita zuwa waje, suka shiga motocin da zasu kaisu destination dinsu. Su Maryam Katsina, su kuma su Anty Halima Kano za’a kaisu su kwana gidan yan’uwanmu dake zaune a can, sai su wuce Gashua gobe.
Sai dana ga sun shiga mota har an tayar, sannan naji hankalina ya tashi. Na fara zubda hawaye. Maryam da Kulsum na ganin na fara kuka suma suka fara, dama tunda muka fara sallama suke sharar hawaye.
Janan ta janyo ni gefen jikinta tana shafa bayana a hankali, har aka ja motar suka tafi muna daga musu hannu.
Sai da muka ga sun fita daga gidan, sannan muka juya, ni, Janan, Harira da Firdausi zuwa bangarena.
Muka yi clashing da Salama da Adi sun fito daga sashen Raheemah, sun yi shigar su ta Ala wadai kamar yadda suka saba. Siket din da suka saka a jikinsu ya matse su kam kamar idan suka yi motsi mai karfi zai yage. Adi tana ta taunar cingam. Suka watsa mana kallon taro da sisi, suka ja tsaki suka wuce. Ko kallo babu wadda suka isa a cikinmu.
Su Harira suka zauna a falo suka kunna kallo, mu kuma muka wuce wajen kayana ni da Janan. Ta taya ni muka cire kayan da za’a kai dinki wasu kuma muka ajiye su sai a hankali tunda yanzu kayana masu dinki basu da yawa. Bayan mun gama, ta taya ni daukar sauran kayan muka je dakina muka shirya su a cikin wardrobe.
Bayan mun gama muma falon muka koma muka biyewa su Huleirah muna kallo.
A hankali yinin ranar yaci gaba da tafiya, muna ta karbar baki yan ganin daki. Tun daga kan dangin Yaya Bilal din, abokan karatunmu dake nan cikin Zaria da kuma makota.
Da rana aka sake kawo abinci daga gidan Anty Sarah. Da kanta ta shigo ta kawo mana abincin.
Na karbi jaririyarta da taci sunan Rabi’atul Badawiyya a hannunta, na dorata akan cinyata, Mimah kuma ta zauna a gefena tana jan kumatun yarinyar.
Ko bayan ta kawo mana abincin, zama tayi cikinmu aka sha hira da ita, har muka gama. Su Harira suka wanko mata kwanukan tas, sannan ta karba ta fita.
Yanayin sabuwar halayyarta ya bamu mamaki sosai, canjin halayenta da yawan shiga cikin mutane da take yi yanzu ba abinda muka saba gani bane a tare da ita. Ko bayan first tata, maganar da muka dauko kenan muna yi.
Firdausi tace “kin san fa dama can basa shiri da matar Yaya, sai in ga kamar dalilin da yasa bata shiga cikin mutane kenan sosai. Tunda kinga ai idan harkar dangi ta taso tana shiga ciki sosai”.
Harira tace “nima na fi tunanin haka”.
Daga nan muka karkata hirar zuwa wata daban kafin mu kai ga cin namanta.
Da la’asar Janan ta fita ta kai min kayana wajen dinki. Tana dawowa su Harira suka shirya suka wuce Kaduna, ita Janan zata tsaya ta kara hade kan kayanta zuwa gobe. Nan muka yi sallama dasu, suka tafi suna godiya, nima ina musu da sakon gaisuwa wajen su Ummah.
Bayan sun tafi, muka koma falona ni da Janan. Na kwanta akan doguwar kujera, ita kuma ta zauna a kasan carpet, Mimah kuma tana kwance a gefenta tana barci. Muna ta hirarmu da ita har Mustafanta ya kira, ta dauki wayar ta koma saman kujera ta lafe suna ta hirar su ta soyayya.
Nayi shiru akan kujera ina sauraronta, ina tuno wasu lokuta da hakan ta dinga faruwa dani da Yayan. Lokutan da zamu zauna mu sha soyayyarmu kamar babu gobe, wadannan muhimman lokuta da babu kamar su a cikin rayuwata.
Yanzu fa? Me yake faruwa ne? Me ya faru da tarihin soyayyarmu? Me ya faru da irin alkawurra na tattali da amintacciyar soyayya da yayi min idan munyi aure? Me ya faru da wannan kallon soyayya da yake yi min a duk lokutan daya samu dama da? Da kalmomin soyayya da basu taba barin bakinshi?.
Gashi yanzu na kula ko kallom inda nake baya so yayi balle a kai ga maganar arziki da wani kallon soyayya.
Shikenan kenan? Wadannan alkawurran sun zama empty promises? Dama dai zakin baki ne irin na Maza yake min, tunda kuma yanzu ya ganni a cikin gidanshi, ai yana da damar ya wulakanta ni son ran shi.
Nayi concluding hakan cikin raina ina maida kwallar data tarar min a cikin idanuna.
Har Janan ta gama wayarta, ban yi motsin kirki ba. Ina ji ta dawo gefena ta kwanta a inda take da, tana kiran sunana, nayi shiru kamar mai barci ban tanka mata ba.
Sai da aka kira sallah sannan muka tashi, lokacin Mimah ta koma sashen su. Muka yi sallah, na zauna akan abin sallar ina karanta suratul-Yasin, ita kuma Janan tana lazumi har aka kira sallar isha’i muka yi.
Naci gaba da zama akan abin sallar bayan na gama, har Janan ta kammala tata ta fita, bata jima ba ta dawo da kulolin abinci ta zuba mana. Duk da kamshin da abincin yake fitarwa, da dadin da yayi, kasa wani ci nayi da yawa, sai tsakura na dinga yi. Har sai da Janan ta kai ga tambayata lafiya? Nace mata bana jin dadin jikina ne.
A haka muka gama, ta wanke kayan ta fita dasu zuwa kicin.
Sai data dan jima, har sai dana tashi daga kan abin sallar na koma gefen gado na zauna, sai gata ta shigo. Ina so in bude baki in tambayeta ko Yaya yaci abincin shima? Amma na rasa ta yanda zan fara dauko maganar. Don haka nayi shiru, na bita da kallo har ta zo itama ta zauna a gefen gadon.
Tace “Yaya yace ki same shi a dakin Anty Raheemah yanzu”.
Nace “ban gane ba? Ya shigo gidan ne?”.
Ta girgiza kai, “a’ah, ya dai kira ni ne a waya”.
Da wani haushi yazo ya tokare ni a wuya, duk yadda naso in danne kamar yadda na dinga yi cikin satin idan ya kirata instead of ni, ya bata wani sako kasawa nayi.
Nace, “wai ni meye amfanin wayata ne da ba zai dinga kirana ba sai dai ya wani bada sako a bani? Ko ban kai wannan matsayin bane kuma yanzu?”.
Janan ta daga kafada, “to Hajiya, ni kuma ina zan sani? Shi ainihin maigidan naki zaki je ki tambaya, ni dai yar sako ce, na kuma kawo. Yana can kuma yana jiranki, kin kuwa san shi baya son jira don haka ki kwashi jikinki da kafafunki ki tafi tun kafin ya shaka”.
Na mike tsaye ina guna-guni, “haka kawai sai a dinga wa mutane wani gani-gani da iko-iko? Ace kai da mijin aurenka wai sai an dinga wani kai da kawowa ana ajiye sakonni kamar a zamanin da?”. Na ja tsaki.
Janan data kwanta dai-daya akan gadona, ta kyalkyale da dariya, “ku dai kuka sani!”. Na wurga mata harara.
Na bude wardrobe na ciro hijabi doguwa, na saka.
Janan ta kalleni, “wai sai kace wadda zata je wani bikin gidan malamai, ba wajen mijinki zaki je ba da zaki wani kama hijabi ki zurma a jiki?”.
Na kara jefa mata harara, “to wai ke ina ruwanki ne?”.
Ta sake sakin dariya tare da sake mike kafa har da min gwalo. Na girgiza kai kawai ina dan murmushi. Na fita zuwa inda aka kirani.
Na tura kofar falon nata na shiga bakina dauke da sallama. Na kula da takalmin da na fi kyautata zaton na Yaya ne a ajiye a waje, da kuma wani hadadden bakin takalmi mai tudun duduniya daga ganinshi na mata ne. Ban kawo komi a cikin raina ba, na cire nawa takalmin nima na shiga cikin falon bakina dauke da sallama.
Sai dai ina shiga na danyi turus, ganin mutane a cikin falon. Mutanen da suka kasance uku, Yaya Bilal da matanshi.
Muryarshi kadai naji wadda ta amsa min sallamar, itama a hankali don da ba don shirun da falon yayi ba babu abinda zan iya ji.
A hankali na taka har zuwa tsakiyar falon, ina jin idanunsu a kaina suka biyo ni da kallo. Sai da naje tsakiyar falon, naja tunga na tsaya ina raba idanu a tsakanin kujerun falon da kuma matan nashi dashi kanshi, cikin tunanin inda zan zauna.
Shi zaune yake akan kujera mai daukar mutum biyu, Anty Ameerah kuwa na gefenshi kugu da kugu kamar zata haye kan cinyarshi, tazarar data bari a gefensu, idan aka samu mutum mara kiba tsaf zai yi fitting a wajen. Taci kwalliya kamar wadda zata je wajen biki, dama gata tubarkallah, kyakkyawa ce, kuma fara mai kyawun jiki, kayan data saka ma sun matukar karbarta. Ga mai karamar zuciya, tuni zata juya baya hannunta aka tana ihu, kallonta kadai a hakan nan kan iya tsoratar da mutum.
Ita kuma Raheemah ta zauna a daya kujerar dake gefenshi, itama dai tasha tata kwalliyar. English wears da suka matukar fitar mata da surar jiki. Kitson da aka mata da yasha karin gashin kanti, ya sauka har gadon bayanta da kuma saman kirjinta inda yayi matukar kokari wajen rufe shafaffen kirjinta da ko brazier acuci maza bata iya tado shi, tana ta wani kwarkwasa.
Idan har zan zauna kusa dashi, hakan yana nufin sai dai in zauna akan kujerar da Raheemah take, ko kuma in zauna a daya kujerar da take fuskantarsu, wanda idan nayi hakan ba zan samu damar jin abinda zai dinga fada ba sosai tunda sauran kujerun sunyi nisa da nan center table ya shiga tsakani. Sai dai kuma idan a kasa zan zauna.
Ina shirin neman wuri a kasar in zauna, naji muryar Yaya yana cewa “zo ki zauna anan”.
Na daga kai na kalli inda yake, sai naga ashe ya tashi daga inda yake a zaune, yanzu yana tsaye ne. Na kalli inda yayi min nuni, kusa da Anty Ameerah da uncertainty, kafin na murje nayi ta maza naje na zauna. Sarai na kula da yadda ta matsa daga tsakiyar kujerar ta koma can karshe ta lafe, amma hakan bai dameni ba.
Yaya ya dauko kujerar dinning table guda daya, ya ajiye a tsakiyar falon yadda yake fuskantar mu gabadayanmu, ya zauna.
Da dai kamar inyi shiru yadda su ma suka yi, wani fanni na zuciyata dai ya tunatar dani ba haka aka yi min nasiha ba da zan taho daga gida, don haka na daga bakina da kyar na gaida su, idan sun amsa min, to ban ji ba har ga Allah.
Yaya yayi gyaran murya, tare da bude taron da salatin annabi. Ya janyo wasu ayoyi daga cikin Al-Kur’ani mai girma ya fassara, ya kawo hadisai, yayi sharhi, ya kare da nasihohi. Duk akan zaman aminci da zaman lafiya a tsakaninmu. Kaina a kasa, cikinmu babu wanda yayi motsi a cikinmu har ya gama.
Bayan dogon lokaci daya dauka yana bayanai, ya gabatar dani a matsayin matarshi. Sai lokacin daya ce ni din kamar yar uwa ce a garesu sannan naji Raheemah tace “tabdijam!”, a can kasar zuciyarta. Ameerah kuma ta sake gyara zamanta. Duk yayi kamar bai ga ko ji abinda suka yi ba, yaci gaba da bayanan shi. Ya gama da cewa “kun fahimta?”. Duk muka amsa da ehh.
Yace “good. Sannan maganar zama da zancen girki, ina so gabadayanku ku shirya, ranar wannan Ladin da zata zo zamu koma Abuja gabadayanmu. Komi an riga an tanada a can, saboda haka baku da bukatar daukar wani abu sai yan abubuwan da ba’a rasa ba. Any complain?”.
Na daga baki cikin mamaki na kalleshi, Ameerah ma haka take kallonshi kamar wanda yace lahira zai kaita, ita kuwa Raheemah ta dan saki ihun murna cike da farinciki wanda bana tunanin tasan cewa tayi hakan.
Duk cikinmu babu wanda ya iya yin magana, sai Ameerah ce ta iya daga baki bayan lokaci mai tsayin tace, “amma ni fa Daddy bai san da wannan maganar ba, ka fada mishi ne?”.
Ya kalleta kamar wata sabuwar mahaukaciya, yace “ni da Matata kuma, don zan zartar da hukunci a kanta sai na tambayi mahaifinta? Wai ma, me kike yi ne a Zaria? Ke ba aiki ba, ke ba karatu ba. Kada ki manta wancan karon da na miki maganar, karatunki kika kawo as an excuse, na kuma kyaleku har kika gama, amma baki sake tada min zancen ba. Na kuma kawo idanu na zuba miki, amma saboda baku san annabi ya faku ba, ko a jikinki. Shikenan ni kullum ina yawo da jele akan titi kamar wani mara galihu, an fada miki a kanki zan kare ne? To bari kiji, wannan itace magana ta karshe da zamu yi akan komawa Abuja, idan muka tafi wannan karon, babu abinda zai dawo dani Zaria sai dai idan wata hidima ta taso a cikin dangi don haka ki yanke shawararki”.
Tayi shiru kanta a kasa, da alama bata ji dadin abubuwan daya fada mata a gabanmu ba, murya can kasa kamar wadda aka shake, tace “idan na tambayi daddy, zan fada maka duk yadda muka yi”.
Ya tabe baki, da alamu abin bai dameshi ba, ko kuwa tsananin sabo ne? Yace “wannan kuma ku kuka sani, illa iyaka ina son ki san cewa idan na sanya kafa na tafi, kuma ba’a baki izinin biyo mu ba, kada ki saka ran zaki dinga ganina a Zaria kamar yadda kika saba don na gaji da wannan jigilar. Akwai wani me abin cewa ne kuma?”.
Duk muka yi shiru, yace “idan mutum yana da matsala gwara ya fito tun da wuri ya fadi, bana son abinda sai daga baya za azo ana damuna da wasu kananun maganganu”.
Ina so in tambaye shi maganar internship dina, tsoron abinda zai fita daga bakinshi ya hana ni daga baki. Idan ya yiwa ta gaban goshinshi fada irin haka, ina ga ni kuma da dama yake shake dani a wuya? Nasan kiris yake jira ya min wankin babban bargo. Don haka na ja bakina nayi shiru.
Raheemah ta daga baki itama cike da tsoron yin maganar, amma hakan bai hanata cewa, “uhmm.. har su Salama zamu tafi ne?”.
Ba Yaya Bilal kadai ba, ni kaina sai dana kalleta baki a dage, meye hadin biri da gada kuma?
Yayan yace “a kan me kuma?”. Tayi shiru tana muzurai.
Ya sake cewa “ba karatu suke yi ba wai? Meye na wani biyoki gidan aurenki? Ko kuwa tare aka daura muku auren ne?”.
Sai ta kama in-ina, “dama.. wannan.. Adi nake nufi”.
Ya kalleta sosai, “to wai ita Adin an miki wahayi da ita ne? Ko kuwa dole sai da ita zaki yi zaman aure ne? Wai bata da gidan iyayenta ne ita din? Ke kadai aka daura min aure da ita, ke kadai kuma nake bukatar gani a gidana. Don haka ke kadai zaki shirya ki bimu. Su Salama su koma gida mana? Dama can dalilin makaranta yasa suke zama anan, kuma ba zuwa suke yi ba, ita kuma Adin ta koma gidansu haka nan itama”.
Sai tayi kus, tana gunguni can kasan makoshinta.
Yace “shikenan babu wani mai magana a cikinku kuma?”.
Jin munyi shiru yasa ya gyada kai, ya rufe mana taro da addu’a.
Ya mike tsaye yana kallonmu mu duka, yana cewa, “don haka sai ku fara shiri. Ki tashi ki koma sashen ki, ke kuma zo in maida ki gidanki”.
Ya fara tafiya, Ameerah ta tashi ta take mishi baya. Nima tashi nayi sadaf-sadaf na bi bayansu, muka bar Raheemah har yanzu a zaune a inda take babu alamun zata motsa.
Muna fita suka wuce wajen gareji, ni kuma na nufi sashena.
Janan bata nan lokacin dana koma dakin. Har na shiga bandaki na watsa ruwa, na fito na shirya cikin kayan barci, ban ji motsinta ba.
Na dauki waya na kirata tare da tambayar inda take, tace “makwanci mana”.
Nace “ban gane ba, nayi zaton tare zamu kwana dake?”.
Tace “rufa min asiri mana, in koma wajen Ummah na a yadda nake. Kinga, yanzu naji dawowar angonki, ki dauki jikinki ki tafi kije ki taro shi sai da safe”.
Ta kashe wayar ba tare data bari nace wani abu. Na bi wayar da kallo, kafin na ajiyeta a gefen gado.
Shiru ina zaune ni kadai, ban ma san zaman me nake yi ba, daga karshe dai na fita na kaso wutar falo da kayan kallo, na koma na lalubi gefen gado na kwanta tare da kashe wutar dakin. Addu’ar kwanciya barci nayi na shafa a jikina, na lumshe idanuna.
#F.W.A
*☆⋆36⋆☆*
Ina rufe idanuna, naji an turo kofar dakin an sake kunna wutar dana kashe yanzu. Na bude idanuna da suka fara yin nauyi saboda gajiya da barci, na saukesu a bakin kofa.
Yaya Bilal yayi tsaye a bakin kofar hannunshi harde a kirji, da alama har ya dawo daga maida Anty Ameerah din. Kayan jikinshi ne na dazu har yanzu bai cire su ba, casual outpit ne, shigar da ban saba gani a jikinshi ba. Yawanci daga suits sai manyan kaya, riga da wando na shadda, watarana ma ko hula baya dorawa.
Muka tsaya muna kallon-kallo ni dashi, kafin ya maida kofar dakin ya rufe. Kai tsaye bandakina ya wuce, ina nan a kwance a inda ya barni, ina jin motsin ruwa dai. Ba’a jima ba, ya fito daga bandakin yana gyara links din hannun rigar shi. Na bi shi da kallo.
Sai daya kawo tsakiyar dakin sannan ya kalleni, “kin yi sallar isha’i?”.
Wani kwarjinin shi ya cika min idanu, na kasa daga idanuna gabadaya in kalli tsakiyar nashi idanun. Kai na gyada mishi a hankali.
Ya sake cewa “kina da alwala har yanzu?”.
Na sake girgiza mishi kai, alamun a’ah.
Ya tsaya yana kallona ba tare da yace komi ba, kusan tsayin minti daya, har sai dana kai ga dan dago kaina na kalleshi. Wani irin abu a tattare dashi dana kasa fahimtar koma menene, bugun zuciyata naji ya dauka da sauri da kuma karfi.
A hankali ya juya zuwa wajen da muke yin sallah, da alama dama an tanadi wurin ne saboda sallah.
Yace “ki tashi kiyo alwalar ko? Muyi sallah”.
Ni wannan sabon attitude daya kirkiro na kasa fahimtar shi, kodayake ai dama can ba wani sanin shi nayi ba sosai, zata iya yiwuwa halin shi kenan. Na daga kafada tare da saukowa daga kan gadon. Kayan barcin dana saka a jikina dogon wando ne da riga karama top, wadda bata kama jikina ba. Na shiga bandakin na daura alwala kamar yadda ya umarceni.
Lokacin dana fito daga bandakin, har ya shimfida abin sallah. Na bude wardrobe na ciro doguwar hijabi na saka. Na karasa wajen da yake.
Ya tada sallah, na bi bayanshi. Raka’ah hudu muka yi dogaye, muka dora da shafa’i da wutiri.
Bayan mun gama, ya juyo ya dafa kaina, yayi addu’o’in da annabi S.A.W ya umarcemu da mu yi a lokacin da muka yi sabon aure. Neman alkhairan juna, da kuma neman tsari daga sharrin juna.
Bayan nan juyawa yayi, yaci gaba da janyo wasu addu’o’in, ni kuma na zauna muk’u a bayanshi, ban ma san kalar addu’ar da nake yi a cikin raina ba har ya gama. Ya tashi tsaye tare da linke abin sallar, nima na mike na nade wanda nayi amfani dashi na ajiye a inda muke ajiyewa.
Nayi tsaye anan kaina a kasa, ban san abinda yakamata inyi ba daga nan, it felt very awkward. Subhanallah! Haka kowace mace take ji idan aka barta da mijinta su kadai a dakinta, ko kuwa ni kadai ce nake jin haka?.
Shi kuwa gogan da alama ko a jikinshi, kamar baya jin komi, idan ma yana ji ba karamin kokari yayi ba wajen murje shi.
Yace “kin ci abinci? Kina jin yunwa?”.
Ai ko ina jin yunwa bana tunanin wani abu zai iya shiga cikin cikina bayan numfashi, yadda nake jin shi dinnan yayi knotting da nerves, fargaba da rashin sanin abin yi. Na sake girgiza mishi kai. Ina tunanin dai na zama kurma yanzu, ko kuwa?.
Bai sake cewa komi ba, ya juya ya bar dakin. Na sauke numfashin da ban san na rike ba. Na jima a tsaye sosai, kafin na cire hijabin jikina na linke na maida inda take, na sake komawa na kwanta. Sai dai wannan karon ban kashe wutar dakin ba tunda bani da tabbacin zai dawo ko ba zai dawo ba.
Zuwa can, sai gashi ya sake dawowa. Wannan karon ya canza kayan jikinshi zuwa jallabiya fara kal, hannunshi kuma dauke da leda babba. Ya ajiye a tsakiyar dakin ya sake fita, can ya dawo da plates da kofuna guda biyu, ya janyo karamin carpet dake jingine acan gefe ya shimfida ya zauna.
Ya fara fitar da kayan ciki, tatacciyar madarar hollandia da gasasshiyar k’afaffiyar kaza. Kamshinta ya hade dakin gabadaya, cikina ya fara juyawa saboda yunwa, amma na kasa motsawa. Ina kallo yayi amfani da wuka karama ya yanka kazar ya zuba a cikin plate, ya kuma tsiyaya madarar a cikin kofunan biyu.
Sai daya gama, ya dago kanshi ya kalleni. Nayi sauri na kauda kaina daga kallonshi da nake yi.
Yace “ba zaki ci bane?”.
Nayi shiru ina kallonshi kamar ba zan ce komi ba. Bai sake ce min uffan ba, yayi bismillah ya fara cin abin shi.
Da naga uwar bari, sai na silalo daga kan gadon a hankali kamar wadda kwai ya fashewa a jiki, na lallaba na zauna a gefenshi.
Ina kallon murmushin daya saki a hankali, na turo baki gaba. Ya turo min plate din kusa dani da kofi daya. Kaina a kasa na fara ci bayan nayi bismillah.
Shirun da duk muka yi ni dashi, babu mai motsin kirki a cikinmu shi ya cika min ciki, sai kuwa taraddadi daya kara cika min ciki.
Na kara tsiyayar madarar dake ajiye a gefenmu bayan na shanye wadda ya zuba mana. Ina kallonshi yana cin namanshi hankalinshi kwance, har ya gama. Lokacin nima na shanye madarar dana tsiyaya.
Ya zari tissue ya goge hannunshi, tare da kokarin fara hada kan kayan. Da sauri na riga shi fara daukar kayan, nace “uhm, ka bari zan hada”.
Bai ce komi ba, ya dai sakar min kayan, ya tashi ya nufi hanyar bathroom dina. Na bishi da kallo cikin sanyin jiki, haka kawai naji ina tausayawa kaina. Haka tawa rayuwar auren zata kasance kenan?.
Na dauki kayan dai gabadaya na fita zuwa kicin dasu. Na wanke plates da kofunan, sauran kazar da bamu kai ga cinyewa ba, na nade a foil paper na saka cikin fridge. Sannan na koma dakin.
Wayyo faduwar gaba! Zuciyata tayi wani irin bugawa lokacin dana ganshi kwance dai-daya akan gadona, ya dago daga kan wayarshi ya kalleni da alama cikin mamaki ganin yadda naja tunga na tsaya kyam, kamar wata wadda taga wani abin tsoro. Sai dai bai ce komi ba. Ni wannan silent treatment da yake bani ya fara bani tsoro kuma maimakon haushi.
A hankali ya kauda kanshi ya maida kan wayarshi kamar ma bai ganni ba. Ni kuwa naci gaba da kafewa a tsaye a wajen. A kalla nafi minti goma a wajen har sai da naji kafafuna sun kage. Har ya gama latsa wayarshi, ya kashe hasken tare da ajiye wayar a kan bedside drawer.
Ya kalleni yace “idan kin gama, ki kashe wutar dakin”. Daga haka ya juya min baya.
Na kara wasu mintunan a tsaye ina kallon bayanshi, kafin daga karshe na yanke shawarar wannan tsayuwar da nake yi anan babu abinda zata kare ni dashi, ga barci da gajiya da suka dabaibaye ni. Idan kuma ba so nake yi inyi barci a tsaye ba, ina bukatar wajen da zan kwantar da hakarkarina.
Na lallaba na kashe wutar dakin, a hankali, cikin sanda na taka zuwa kan gadon kamar mai tsoron a kamata, na kwanta a gefen gadon nima na juya mishi baya. Na sake yin addu’ar kwanciya barci tare da lumshe idanuna. Sai dai wannan karon babu alamun yin barci a cikin idanuna, zuciyata cike take da tsoron abinda zai je ya dawo. Ban san lokacin da barci ya kwashe ni ba. Cikin dare na farka na jini kwance luf akan kirjin Yaya, ban san ko ni ce na gangara wajen da yake ba ko kuma shine ya gangaro inda nake ba, ban kuma damu da in janye jikina ba. Sai ma kara lafewa da nayi, saboda a lokacin ji nayi kamar duk duniya babu abinda ya kai kirjin Yaya Bilal dadin kwanciya sai dumi.
Lokacin dana tashi, ni kadai ce kwance a tsakiyar gadon. Sai kuwa tarin fululluka a gefena da ban san yadda aka yi suka zo wajen ba.
Dan hasken da dakin yayi da kuma motsi da naji a bandaki ya tabbatar min da cewa Yaya yana can. Na juya na kalli agogo, karfe biyar babu mintuna goma, asubahi ta riga tayi kenan. Daidai lokacin da naji karan bude kofar bandaki ana fitowa, nayi sauri na koma na kwanta kamar mai barci.
Ina kallon Yaya yazo ya tsaya a gefen inda nake yana kallona ta idanuna dana dan lumshe.
Ya jima a tsaye yana kallona, har dai naji kallon ya isa haka nan, na danyi motsi. Da sauri naga ya ja da baya, na bude idanuna a hankali na sauke su a kanshi.
Ya wani yi kici-kicin da fuska har yaso ya bani dariya, kamar ba shine ya gama kare min kallo ba yanzun nan.
Yace “lokacin sallah yayi”. Na gyada mishi kai tare da tashi zaune, shi kuma ya juya ya fita daga dakin.
Bayan ya maida kofar ya rufe, na sauka daga kan gadon ina yin mika, strangely feeling good and relaxed. Kamar wadda ta samu dadadden barcin data jima bata yi ba. Na shiga bandaki na dauro alwala na fito na tayar da sallah.
Ina nan a zaune har gari ya gama yin haske, Yaya Bilal bai dawo dakin ba. Wani barcin na sake komawa. Sai karfe tara na safe na tashi.
Wanka na fara yi, cikin kayana na fiddo wasu riga da wando na Pakistan na sanya. Na bade jikina tun daga kafa har kaina da turare. Show glass babba guda aka cika min da kayan kamshi iri-iri yan asali irin na mutanen Bare-bari, dama su ba baya ba. Kamshi mai dadi da sanyayar da zuciya. Na dauki gyalen na nada a kaina, na fita falo. Lokacin karfe goma na safe. Babu kowa a falon, kamar yadda naji babu hayaniya a cikin gidan.
Tunda na tashi cikina yake kiran yunwa, na duba kicin da dinning table ko Janan ta shigo da abinci lokacin da nake yin barci, naga wayam. Ina shirin juyawa in koma daki in dauko wayata in kirata, kofar dakin Yaya ta bude.
Ya fito, da alama shima wankan yayi. Ya sanya wandon jeans navy blue da farar rigar top wadda ta dan kama kirjinshi. Sai bada kamshi yake yi. Ya zauna akan kujera yana lalubar remote ya kunna talabijin.
Na duka har kasa na gaida shi, ya amsa yana wani fuskewa. Na girgiza kai a hankali, wannan basarwa ta Yaya Bilal na kasa gane kanta balle dalilinta.
Yace “miko min abinci”.
Nayi shiru ina muzurai, ya kalleni cikin mamaki. “Abinci nace!”.
Yadda yayi maganar cikin rashin alamun wasa, yasa naji jikina ya dauki rawa cike da tsoro, nace “ai.. uhm… Da naga ana kawowa kwana biyu sai banyi ba”.
Ya dago ya kalleni sosai, “to ita wadda take yi girkin, tare aka kawo ku da ita ne ko kuma zata kare ne wajen girka miki abinci? Banda ma rashin tunani, a kawo ki gidan aurenki, ki zauna kina jiran wata ta dafa abinci ta kawo miki? Lalaci kenan ko kuma duk cikin rashin so ne!?”.
Na daga kai da sauri, kuma cikin kaduwa na kalleshi. Shima kallona yake yi, fuskarshi babu alamun nadamar abinda ya fada. Sai a lokacin na fahimci dalilin hade fuskar da yake tayi. Naji wata kwalla ta cika min idanu, a hankali nayi kasa da nawa kan.
Na daga baki da kyar, nace “kayi hakuri… Bari in dafa maka yanzu”. Na tashi cikin sanyin jiki, na shiga kicin.
Tsayawa nayi a tsakiyar kicin din ina share hawayen da suka fara zarya a fuskata, wace irin rayuwar aure ce haka muke yi ni da mijin aurena?. Sai dana dan nutsu, sannan na fara dube-dube ina neman abinda yakamata in dafa mishi mai sauki.
Da yake kicin din shake yake da kayan abinci kala-kala, sai na shiga store na dauko ledar cous-cous. Na bude fridge da yake shake da vegetables da abubuwan gwangwani, na ciro abubuwan da nake bukata. Fridges din guda biyu ne, daya na kayan miya, nama da sauransu, dayan kuma na ruwa da soft drinks.
Cikin sauri nayi vegetable sauce, na dafa cous-cous din, tare da hadawa da ruwan shayi.
Na zuba mishi komi, na dora akan tray na fita na kai mishi. Yana nan zaune a inda yake, na hada komi a gabanshi, na koma gefe na zauna.
Kasa ya sauko, ya dauki cokali zai fara ci, sai ya dakata ya kalli inda nake.
Yace “ba zaki ci ba ne ke?”.
A hankali na girgiza mishi kai.
Yace “me kika ci?”.
Ban ce komi ba, na sake girgiza mishi kai.
Yace “to matso maza ki sa hannu ki ci, bana son zama da yunwa”.
Na matsa a hankali kusa dani, na dauki wani cokalin nima na ci. Wannan karon ma har muka gama babu wanda yayi magana a cikinmu, ya tashi ya kwashi wayoyin hannunshi daya ajiye a kan center table, yace min ya fita.
“Allah ya tsare”, kadai na iya ce mishi. Yasa kai ya fita.
Bayan fitarshi na maida kayan kicin nazo na zauna ina kallo cikin rashin dadin rai. A haka Janan ta shigo ta sameni. Zuwanta ne ma ya dan sanya na saki jikina, muka shiga hira da ita. A bakinta ne naji ashe Yaya da kanshi ya cewa Anty Sarah kada ta kara turo mana da girki nan. Nayi kwafa a cikin raina, amma ban ce komi ba.
*
Yau ma ana yin sallar isha’i ta tsere sashen Anty Sarah. Ashe a can ta kwana jiya ma, wai Raheemah rufe mata kofa tayi. Na jinjina girman al’amarin, nace ‘Allah ya kyauta’, tace ameen.
Yau tun kafin in kwanta Yaya ya dawo. Na kai mishi abincin dana girka mishi, ya ci ya tashi ya tafi dakinshi, ni kuma na dauke kayan. Na koma daki nayi shirin barci, na kwanta.
Ina jin lokacin daya shigo dakin har ya kashe wuta, yazo ya hayo kan gadon ya kwanta shima, ban motsa ba.
Lokacin da naji ya matso zuwa tsakiya gadon, hannunshi yana ratsawa ta kan ruwan cikina, kanshi kwance akan kafadata, ji nayi kamar an tsayar da duk wani gudun jini a jikina. Nayi sak, hatta da numfashina sai daya tsaya cak.
Cikin wata irin murya, kamar ba ta Yaya Bilal din dana sani ba, yace “amarya ta!”.
Naji wasu irin emotions a cikin raina kala-kala, iri-iri, har na rasa da wanne zan ji. Idanuna suka ciko da hawayen dana rasa dalilin su, murya a cushe, kamar zan fashe da kuka, nace “amaryar da ake fushi da ita?”.
Ya sake janyo ni cikin jikinshi sosai kamar zai balla ni biyu, yace “to Na’ilah ya kike so inyi ne kam? Kiri-kiri fa haka kika fito kika nuna duk duniya baki da makiyi kamata, kika ki aurena, saboda tsabar rashin so ma har suma kika yi fa da kika ji labarin an daura miki aure dani ba wani ba. To ya kike son inyi? In dinga binki sawu da kafa, duk da rashin son da kika nuna min? Anya Na’ilah, anya baki so kanki da yawa ba kuwa?”.
Na hadiye wani yawu daya tarar min a baki, nace “wa yace maka na tsane ka?”.
Yace “ko baki fada ba Na’ilah, yadda kika badawa idanunki toka kika ki aurena kadai ya isa ya tabbatarwa da mutum cewa baki so na. Ba wannan ba, tunda abinda ya faru ya riga ya faru, me zai hana ba zamu bar abinda ya faru a bayanmu ba, mu fuskanci gaba? Mu fara rayuwar aurenmu ta hakika? Don in fada miki, aurena dake babu saki. Idan ma zaki hakura ne, ki hakura. Ba ki tunanin jan aji da yawo da hankalin ya isa haka?”.
Na turo baki kamar yana ganina, “wa yace maka jan aji nake yi?”.
Ya kara matsoni jikinshi, kanshi yana kara nutsewa a cikin gashin kaina, yana kara shakar daddadan kamshin da yake yi.
Muryarshi bata fita sosai saboda yadda ya gashin kaina ya rufe mishi baki da fuska, yace “nace miki rashin so, kin ce ba haka ba, shima jan ajin kin ce ba haka ba. To menene? Tsabar so ce, uhmm??!”.
Na daga baki da niyar bashi amsa, hannunshi da yake kan ruwan cikina ya fara zana circles, jikina ya dauki rawa kamar ana kada min mazari, na rasa muryar maida mishi martani.
A hankali naji ya juyo dani, hannunshi daya yana shafa gefen fuskata zuwa bayan wuyana, kafin ya hade bakinmu waje guda. Na lumshe idanuna a hankali, savouring the moment.
Zuciyata tayi nauyi, tunanina yayi nisa, babu abinda nake ji kuma nake fahimta a lokacin sai Yaya Bilal kadai da abubuwan da yake min, da kuma abubuwan da suke haddasa min a jinin jikina.
Zuwa can naji komi ya tsaya cak, kamar da can babu abinda yake faruwa. Na bude idanuna a hankali, na daga kaina da niyar ganin abinda yake faruwa.
Sai dai abinda naci karo dashi ne ya bani mamaki, ta wani bangaren kuma yaso ya sanya ni kyalkyalewa da dariya.
Yaya Bilal barcinshi yake shaka tsakaninshi da Allah akan kirjina, har da jan minshari!.
#F.W.A
*☆⋆37⋆☆*
Da asubah Yaya Bilal ya tashe ni, ban ma san lokacin da barci ya dauke ni ba jiya. Ya fita masallaci, ni kuma na dauro alwala nayi sallah ta.
Yau bai tsaya a waje ba, gari yana fara yin haske ya dawo cikin dakin. Ina zaune ina lazumi ya shigo, ya koma kan gado ya nade, ni kuma naci gaba da lazumi na. Ina gamawa kuma kicin na shiga, na hada breakfast mai kyau, na gyara ko’ina ya fito fes, sannan na koma daki. Har yanzu Yaya barci yake yi.
Na shiga bandaki da niyar yin wanka, kafin in fito Yaya ya bar dakin. Bayan na fito, na shafa mai, yar hoda da man lebe, na janyo wata doguwar rigar buba ta atamfa na sanya. Na bade jikina da turare kamar ko yaushe na fita falo.
Har yanzu Yayan bai fito ba, don haka na zauna akan daya daga cikin kujerun falon ina jiran ya fito. Kafin ya fito dinne na kira Maryam wadda naga missed call din da tayi min jiya da dare yau da safe, muna cikin hira da ita kofar dakin Yaya ya bude, na juya na kalleshi lokacin daya leko daga ciki.
Yace “kawo min abinci na nan Na’ilah”.
Muka yi sallama da Maryam, na dauki kayan na wuce dakinshi. Yana tsaye a gaban mirror yana fesa turare a jiki na shiga, ya ajiye kwalbar turaren, ya matso ya karbi kayan hannuna ya ajiyesu a can gefe. Na koma kicin na dauko babbar ledar cin abinci nazo na shimfida, sannan na zauna na hau zuba abincin.
Ya gama abinda yake yi, yazo ya zauna, na tura mishi abubuwan dana zuba gabanshi. Sai daya zauna sosai sannan na gaida shi, ya amsa min fuska da walwala da fara’a, hakan ya sanyaya min zuciya kwarai.
Ina kokarin zuba nawa abincin, ya katseni, “dauki cokali ki sa mu ci wannan, idan mun cinye sai a kara. Ko ba zaki ci dani bane?”.
Nayi saurin girgiza kaina, “ni ban ce ba”, na dauki cokalin nasa na fara ci, Yaya yayi dan murmushi.
Shiru tunda muka fara cin abincin, babu wanda yayi magana.
Zuwa can yace “an riga an gama komi, a can Abuja zaki yi internship dinki. Ina fata babu matsala?”.
Da sauri na girgiza mishi kai, nace “a’ah, babu. Nagode”.
Yace “meye na godiya kuma? Kunshin hannunki yayi kyau matuka”. Ya canza akalar hirar tamu.
Na dan saci kallon hannuna na hagu dake kan cinyata. Ni kaina da kunshin yake hannuna yana burgeni sosai, don ya tsaru ne.
Ban tantance ba naji ya kamo hannun nawa cikin nashi, na kalleshi a dan kunyace, amma shi ko a jikinshi. Ya cigaba da cin abincinshi a nutse, kamar babu abinda ya faru.
A hankali nayi kokari na zame hannuna daga nashi, sai dai ina maida shi inda yake da, naji ya sake janyo shi. Wannan karon kyam ya rike idanuna cikin nashi kamar wanda yake challenging dina akan in sake janye hannun, sai nayi kasa da nawa idanun, na kuma kyale shi. A haka muka gama cin abincin.
Nayi tsam na tashi, na fara hada kan kayan na kai kicin. Na tsaya na wanke su ma ajiyesu a inda yakamata, sannan na koma falo. Na dauki remote na kunna tv ina kallo har Yaya ya fito cikin shirin fita.
Ya tsaya a gefena yana daura agogon hannunshi, “zan fita, nasan sai zuwa dare zan dawo yau don haka kada kiyi abincin rana dani. Babu wata damuwa dai ko?”.
Na girgiza mishi kai.
Ya sanya hannu ya dago habata yadda muke kallon juna ta cikin ido, kallon tsakiyar idanunshi ba abu bane mai sauki, ji zaka yi kamar an sanya sarkoki an daure duk wasu gabban ka masu motsi, yayin da a gefe guda kuma zaka ji kamar an dauko wani dutse ne an aza maka aka, ka kasa motsi.
Yace “wai kin koyi rashin magana ne yanzu ko kuma rowar muryarki kika fara ne? Kodayake, har da laifina ma. Saboda ba’a sayi bakin ki bane ba ko?”.
Nayi saurin girgiza mishi kaina ina dan murmushi, ya sake girgiza kanshi, “uh uh?!”.
Nace “a’ah, ba haka bane”.
Sai lokacin ya sakeni, yace “to ko ke fa? Ki dinga hana ni jin muryarki, baki san muryarki tana da dadin saurare bane?”.
Ni na rasa ta ina Yaya Bilal ya zama frank and blunt ba, ko kuwa dama can haka yake?. Ina shirin bashi amsa wayata dake gefena ta shiga yin kara, kafin in kai hannu in dauka, Yaya ya riga ni. Ya kalli sunan mai kira, ya kalleni girar sama data kasa a hade.
“Waye kuma wani Hamza cm?”, ya tambaya cikin hade fuska.
Nace “classmate dina ne”, tunda aka daura min aure nake samun kiran waya daga yan ajinmu da muka gama makaranta dasu suna taya ni murnar yin aure.
Bai ce komi ba ya kashe karan wayar, ya saka ta cikin aljihun rigar shi. Yace “bari in fita”.
Na mike na mishi rakiya har bakin kofa, nace “Allah ya tsare, a dawo lafiya”.
Yace “ameen baby na, sai na dawo”.
Ya wuce, ni kuma na maida kofar na rufe ina murmushi kamar wata kuntacciya. Damn, why does it feel so good to be his baby again?!.
Bayan ya tafi, gidan na rufe na tafi sashen Anty Sarah. Janan da Mimah na falo suna karin safe lokacin dana shiga, Anty Sarah kuma da alama tana daki.
Muka gaisa dasu, Janan ta min tayin abinci nace na koshi, na nemi waje na zauna ina kallo har suka gama. Nan Janan ta dawo wajena muna hira da ita, har Anty Sarah ta fito daga dakin Yaya Jameel, Yaya Jameel din yana bayanta hannunshi dauke da Rabi’ah.
Muka gaida su, suka amsa, Yaya Jameel din yana ta tsokanata har dai ya fita. Anty Sarah ta zauna muka cigaba da hirarmu.
Sai da azahar sannan muka koma bangarena ni da Janan. Bayan na dafa mana abinci mai sauki, muka ci. Janan ta tafi karbo min dinkin data kai mana, ni kuma naci gaba da zama anan har ta dawo.
Dinkunan sunyi kyau matuka, tace “sauran sai dai ko zuwa ranar juma’ah ne ko asabar aje a amso miki, na yiwa Is’hak magana zai je ya amso miki”.
Na gyada mata kai cikin daukewar hankali lokacin dana daga wata riga, na hangame baki da hanci cikin mamaki, nace “meye haka nake gani wannan Jan? Wannan show me din ai yayi yawa”.
Tace “ke ja can! Wani irin yawa kuma? Ba mijinki zaki yiwa kwalliya dasu ba?”.
Ban kulata ba na tashi na hau gwada kayan. Na cire wata doguwar riga da tsabar tsagar da aka yiwa hannuwanta, baka banbanceta da vest sai idan kaga dogayen lebatun da aka mata, na ja tsaki, nace “gaskiya baki kyauta min ba Janan, wannan ai bata min kaya kawai kika sa aka yi ba wani abu ba”.
Janan tayi murmushi, tace “kada ki damu matar Yaya, zaki gode min ne nan gaba”.
Haka dai na hada kayan naje na shirya su cikin wardrobe, sai dai bani da niyar sanya su a cikin raina koda kadan. Kawai na riga na gama rayawa raina asarar kaya da kudin dinki Janan tayi.
Na koma falo muka cigaba da hirarmu ni da ita, har yamma tayi, Is’hak da zai kaita gida ya mana sallama da yake yau zata koma gida. Na rakata har bakin motar muka yi sallama da ita cike da kewa da kauna.
Anan muka hadu da Mimah itama tazo mata sallama, naja hannunta muka koma sashena, na kunno mata cartoons tana kallo, ni kuma na shiga kicin na fara hada dinner.
Da dare sai ga Yaya Bilal ya dawo da sabuwar waya kar a kwalinta, da sabin sims guda biyu.
Nace “ita fa waccan wayar tawa?”.
Bai ko kalleni ba, yana ta tura abincin dana girka mishi, yace “nayi kyauta da ita!”.
Na turo baki gaba kamar zanyi kuka, nace “amma fa akwai lambobin mutane da dama da zan rasa, kuma za ayi ta kirana ba’a samuna!”.
Yace “manufar hakan kenan ai dama, ba zai yiwu in zauna in rabbe hannu a kirji ba ina kallo wasu gardawan kawai na kira min mata ba. Ban yarda ki ba kowa lambar wayarki ba sai wanda ya dace, kina ji na?”.
Duk da na jinjina wannan karfin iko da mallaka, hakan bai hana ni amsa shi ba, nace “to, nagode, Allah ya kara budi”.
Ko baiyi tunanin zan amince cikin sauki ba ne? Ya kalleni cikin mamaki, kafin yayi murmushi yace “yauwa baby na, ko ke fa?”. Muka cigaba da cin abincinmu.
Bayan mun gama, ya wuce dakinshi zai watsa ruwa a cewarshi, ni kuma na koma dakina nima. Nayi brush, na fito na sanya kayan barci, nayi shafa’i da wutiri, sannan na kwanta.
Ban jima da kwanciyar ba sai gashi ya turo kofar dakin ya shigo. Ya kashe wutar dakin tare da hayowa kan gadon da nake, ya janyo ni cikin jikinshi.
Gabana dukan uku-uku yake yi, musamman lokacin da naji ya fara aika min nauyayan sakonni a cikin sassan jikina. Sai da tafiya tayi nisa, ni a kaina na fara fita daga hayyacina, naji tausassan sautin minshari yana tashi a kusa dani. Sai dai wannan karon, ban samu kaina da darawa kamar jiya ba, daga kai nayi ina kallonshi cike da mamakin abinda yake faruwa. Wani abu a tattare da wannan lamari just seems off.
*
Wasa-wasa abin dariya fa yake neman juyewa ya zama abin kuka. Kullum haka abin yake kasancewa, wani abin mamaki ma shi Yayan kamar bai san hakan tana faruwa ba. Saboda washegari normal zamu tashi ni dashi, babu wata alama ta ya tuna abinda ya faru a daren daya gabata a tattare dashi. Damuwa ta fara lullubeni, tunani ya fara addabata, tabbas akwai wata a kasa. Sai dai kafin in tono abinda yake a kasan, har ranar Lahdi ta zagayo, ranar dana fita girki, ranar da zamu koma Abuja kuma.
Ranar tun da safe na gama hada duk wasu kaya da zan tafi dasu. Duk wadanda yakamata mu yi sallama dasu, mun riga mun yi.
Karfe hudu Yaya ya leko yace min in fito zamu tafi, tun dazun aka fitar da kayan dana riga na shirya. Su kuma kayan dakin na samu manyan ledoji na lullubesu saboda kura.
Na fito tare da kulle kofata, na saka makullin cikin jakata.
Na leka sashen Anty Sarah na sanar da ita zamu wuce, ta saba Rabi’ah a kafadarta muka fito ni da ita.
Yaya Bilal da Yaya Jameel suna tsaye a gaban motar suna tattaunawa, muka tsaya anan gefensu muna jiran Raheemah ta fito. Sai yau kannen nata suka hada kan kayansu suka tafi. Da safe naga ana ta fita da kaya da tarkace, kusan zaryarsu biyu. Wani saurayin Salame ne yake ta zaryar kai kayan da dawowa ya lodi wasu. Na fito daga sashen Anty Sarah da safen, naci karo dasu sun fito kowacce na jan akwati kamar zasu je ci rani. Suna ta kwashewa mai motar albarkar saboda ya tsaida su suna ta jiran shi, suka daka min harara lokacin da suka ganni, ni kuwa na daga kafada na wuce abina.
Sai da muka kusa yin mintuna biyar muna jiranta a wajen, har sai da Yaya ya kai ga kiranta ya tunatar da ita muna jiranta fa, amma babu ita babu alamunta.
Yaya ya shaka, ya bude min gaba tare da umartata akan in shiga mu tafi, Yaya Jameel yace “kai kuwa ayi haka? Ku dan kara jiranta mana”.
Yaya yace “yo ai ko aikina kenan zaman jira, yaci ace an zo an sallameni. A kanta zan kare ne?”.
Yana tashin motar, sai gata ta fito tana takunta dagwas-dagwas kamar bata shanya mutane suna jiranta ba. Tazo ta gefen inda nake a zaune, ta bude kofar tayi wani kerere, ita bata juya ba, ita kuma bata ce komi ba, sai muzurai.
Yaya ya kalleta cikin kullewa, “idan ba zaki tafi bane, ki maida mana murfin motar mu mu wuce”.
Bata ce komi ba, ta maida murfin motar da karfi ta rufe kamar zata balla shi. Ta bude baya ta shiga tana harare-harare da muzurai.
Su Yaya Jameel suka mana addu’ar Allah ya tsare, Yaya Bilal ya tashi motar muka fita daga gidan.
Daga farko nayi tunanin ko zamu biya ta gidan Anty Ameerah ne mu daukota, amma sai naga Yaya ya dauki hanyar fita daga Zaria straight.
A raina na raya tunda ita din shafaffiya ce da mai, yar gaban goshi, tana da motar hawa ta kanta, kila da kanta ta tafi.
Tafiya muke cikin madaidaicin gudu, bayan sautin radio da take ta aikin yi, baka jin motsin komi a cikin motar.
Yaya ya fara katse mana shirun ta hanyar fara tambayata yanayin yadda tsarin internship dinmu zai kasance. Nan da nan hira ta barke a tsakaninmu. Muna cikin yin hirar, zaka ji Raheemah itama ta tsoma nata bakin a ciki. Duk da ba tamu hirar take sanyawa baki ba, tata kalar hirar daban. Na kula tun karfinta take kokarin janye hankalin Yaya daga kaina.
Daga karshe dai da abin ya ishe ni, sai na kwantar da kaina akan kujera na kyalesu suna ta hirar su kamar ina yin barci.
🙏🙏🙏
#F.W.A
*☆⋆38⋆☆*
Gidan Yaya Bilal babba ne, mai kyau na gaban kwatance. Lokacin da muka fara shiga Abuja barci ya fara daukata, haka na bude idanu ina kallon gari. Duk da cewa ba wannan ne karona na farko zuwa Abuja ba, amma kuma na jima kwarai rabona da garin. Shi yasa yanzu nake ganina kamar wata sabuwar zuwa.
Yaya yayi ta ratsa tituna da ginunnuka har muka isa wata unguwa da tun daga bakin gate naga an rubuta Maitama. Duk yawace-yawacena ban taba biyowa ta nan wajajen ba. Daga gani babu tambaya unguwa ce ta masu hannu da shuni, tun daga kan ginunnukan da kuma tsari da yanayin unguwar. Ba karamin burgeni tayi ba.
Yaya ya tsaya a kofar wani madaidaicin gida, yayi amfani da remote, gate din gidan daya kasance ruwan zuma mai cizawa, da wata irin raga-raga daga tsakiya wadda take baka damar hango tanfatsetsen ginin dake ciki, ya bude da kanshi. Yaya Bilal ya silala kan motar ta shiga ciki, muna shiga gate din gidan ya koma ya rufe.
Wajen ajiye motoci muka fara tararwa, waje na mai fadi da zai cinye motoci akalla guda biyar. Yayi parking din motar, muka fito muna karewa gidan kallo. Motoci biyu ne a garejin, rufe da tampol dinsu. Ya mana jagora zuwa gidan. Daga gefen garejin akwai karamin waje da aka yi shuke-shuken bishiyoyi da furanni da basu fara tsayi ba, da alamu sabon garden ne aka yi. Sai kuwa kofar gidan, kana shiga dogon corridor ne da zai kaika har tsakiyar wani babban falo, kana shiga corridor din zaka ci karo da wata kofa da zata sadaka da kicin.
Babban falon ya dauki saitin royal setting, daga kan kujeru, carpet, labulaye, da fenti, duk golden ne da ratsin royal blue. A cikin babban falon dinning room yake, sai kuwa kicin da kofar su daya da dinning room din, sai babban store.
Kana fita daga babban falon anan dakunan mu suke, suma dai tubarkallah manya ne, daya yana kallon daya, inda nan ne ya nunawa Raheemah daya a matsayin nata, dayan kuma a matsayin na Ameerah da bamu gani ba, kila ita sai anjima ko kuma washegari. Daga gaban nasu kadan nan nawa dakin yake, daga gefen nawa kuma akwai dakuna guda biyu, babu komi a ciki daga carpet sai katifa da labulaye, kila dakin baki ne ko kuma na yara. Daga nan ya jamu, muka bi ta gefen dakunan zuwa master bedroom, inda dakinshi yake. Shima dakine babba mai fadi sosai. Daga dakin nashi muka sake fita zuwa wani falon da bai kai wancan girma ba, shima dai saitin kujeru ne da madaidaiciyar tv, sai tagogin wajen da suka kasance manya, irin daga sama zuwa kasa dinnan na gilasai, kana hango karamin lambun daga nan. Wajen dai ya hadu kwarai, just spectacular. Da ya bude wata kofa daga nan falon, sai muka sake bayyana a babban falo.
Bayan ya gama nuna mana gida da kuma ko’ina da ko’ina dai, sai duk muka wuce dakunanmu domin yin sallah da aka fara kira.
Dakina mai fadi ne, an sanya Italian bed, closet ta jikin bango, dressing mirror da shelves na littafai. Fentin dakin light orange ne, sai daga bangon gado da aka sanya wasu irin wallpapers masu tsananin kyau. Daga can gefe akwai study table da aka shirya, da dan karamin firjin a gefe, can gefe kuma nan ne bathroom yake. An zuba duk wasu abubuwan bukata a ciki. Sauran dakunan ma duk haka suke, hatta da kayan ma duk iri daya ne, kala ce kawai ta banbanta. Na sake bin dakin da kallo ina jinjina kai cikin jinjina namijin kokarin da Yaya yayi. Daga karshe dai na shiga bandaki na dauro alwala, ina fitowa na tadda abin sallah a shimfide yana facing din alkibla, don haka na hau kai na tada kabbarar sallah. Ban tashi daga kai ba sai dana yi sallar isha’i da shafa’i da wutiri sannan.
Kayana da aka taho min dasu na samesu a tsakiyar daki, na fara daga su ina fiddo su daga cikin akwatunan. Cikina ihun yunwa yake yi tun karfinshi, tunda yau na fita daga girki nasan bani da halin cewa zan shiga kicin in dora abinda zan ci. Nayi tunanin fita domin in ga abinda aka girka, daga baya dai kawai naga bari in dakata in gani ko za’a kira ni. Na daga fridge din dakin naga babu komi a ciki sai ruwa, shima babu sanyi saboda firjin din ba a kunne yake ba. Naja tsaki na maida firjin din na rufe. Na koma naci gaba da daddaga kayan.
Ina cikin fito da kayan Janan ta kirani, ni sai lokacin ma na tuna babu wanda na kira, na daga wayar cikin dariya saboda nasan korafi ta kira ta min. Illa kuwa, ina dagawa ta fara, “haba baiwar Allah, dokin sabon gida har yasa kin fara mantawa da mutane ne?”.
Nayi dariya nace “don mantuwa kam na manta dake, sai dai ba santin gida bane yasa na manta dake wallahi, gajiya ce da yunwa, gashi tunda muka sauka bamu zauna bane shi yasa”.
Tace “to sannunku. Nima tun dazu naji Yaya yana fadawa Ummah kun isa lafiya, shine na zauna ina jiran a kirani sai kuma naji shiru, shine na biyo baya. Kun sauka lafiya?”.
Nace “lafiya lau, ya su Ummah?”.
Tace “lafiya. Ya gidan naku?”.
Nan na mike kafa na fara labarta mata labari, har sai data fara cewa in dan saurara sannan na dakata ina dariya, “Allah don baki ga gidan bane Jan, ya hadu fiye da tunaninki. Bana tunanin duk shige-shigenki kin taba shiga gidan daya kai wannan wallahi”.
Tace “ai in Allah ya yarda zamu zo ganin gida ni dasu Yaya kila satin sama, tunda Yaya ya gama ginin kusan shekara nawa yanzu, babu wanda ya taba zuwa sai dai su Yaya Auwal da naji suna fadin haduwar gidan”.
Nace “haba? Dama ba’a taba zama a gidan nan ba?”.
Tace “wa zai zauna? Shi kadai yake zaune a gidanshi. Anty Ameerah dama bata taba zama a gidan ba saboda lokacin da aka yi aurensu tana karatu, kuma yana cikin yin ginin ne, bayan ya gama kuwa taki komawa. Ita kuma Anty Raheemah dama bai taba cewa zai kawota nan ba, don’t know why though!”.
Na jinjina kai, “lallai yayi kokari ba kadan ba. Zama a gidannan kai kadai duk girma da fadinshi?”.
Tace “to yanzu ba gaku nan ba? Dagewa zaki yi ki fara sauke mana yan digwi-digwi yadda zaki ga gidan ya cika nan da dan lokaci, sai ku daina ganin girmanshi”.
Wani abu ya dan ratsa zuciya da tace haka, amma sai na dake, na saki wata sarkakkiyar dariya nace “ke fa baki da kunya wani lokacin Jan, duka-duka yaushe aka yi auren?”.
Tace “tunda aka yi sati kuwa, ai lokaci yayi babe, yakamata zuwa yanzu ace koma menene ya gama shiga. Kin fara jin canje-canje a jikinki kuwa?”.
Na sake fashewa da dariya, wani lokacin haka take kamar wata sintacciya. Ina shirin bata amsa, naji alamun shigowar kira, na duba naga ‘Zhaujee’, kamar yadda ya kawo min wayar da wannan sunan a jikin lambarshi yana tsalle, nace “you are nuts wallahi. Bari in dauki wayar Yaya ya kira, ki gaida su Ummah”.
Ban jira ta gama fadin abinda ta dauko fada ba, na katse kiran tare da amsa na Yaya. Ina dagawa yace “ke da waye ne kuke yin waya tun dazu?”.
Nace “Janan ce Yaya”.
Yace “ok, ki fito mu ci abinci”.
Nace “to”. Na kashe wayar na tashi.
Wani tattausan silifas pink, na dauka a cikin kayana na saka. Na dauki turare na kara fesawa a jikina, na dauki wayar hannuna naja dakin na fita.
Suna zaune akan dinning table, da kwanukan abinci a gabansu na same su. Na musu sallama suka amsa, tare da jan kujera kusa da Yaya na zauna, ita kuma Raheemah tana kan wadda take fuskantar shi. Fuskar nan tasha make up har da na hauka.
Yaya yace mana “bismillah ko?”.
Na ga Raheemah ta ja plate ta bude ta zuba abinci a ciki macaroni ne aka yi jallop, an zuba kifi da nama a ciki. Maimakon in ga ta mikawa Yaya wanda ta zuba, sai naga ta ja shi gabanta zata fara ci.
Na kalli Yaya naga yana fama da cokali da plate, sai na dan matsa, na karbi plate din hannunshi na zuba mishi abincin, na tsiyaya ruwa a cikin cup shima na ajiye mishi, sannan na fara zuba nawa nima. Ya kalleni cikin dan murmushi, tare da furta “jazakillah”, a can kasan makoshinsa. Na maida mishi martanin murmushin.
Ina daga kaina, naci karo da idanun Raheemah tana watso min harara, ni kuwa na daga kafadata sama na fara cin abincin bayan nayi bismillah.
Ban wani ci da yawa ba, na ture kwanon gefe na ajiye. Ban taba cin girkin Raheemah ba tunda nake, don haka ban taba sanin yadda girkinta yake ba sai yau. Kodayake, zata iya yiwuwa yau din rana ce ta kufce mata abincinta yayi gishiri da yaji ya kuma dafe.
Na ci gaba da zama anan duk da cewa na gama, har suka gama cin nasu abincin. Yaya ya tashi ya wuce dakinshi, itama ta mike tayi nata dakin, ta bar kayan abincin anan, suka barni ina zare ido.
Da nima nawa dakin zan koma, sai na jiyo sautin karar talabijin a falon Yaya, don haka na karasa can. Baya cikin falon ma, na zauna tare da daukar remote na latso tashar mbc action na kunna, suna hasko film din Furious 7 kuwa, na gyara zama sosai don ina kaunar film din kwarai.
Ban yi nisa a kallon ba, sai ga Raheemah itama ta shigo. Tana zama, ta dauki remote ta canza tasha, na dan daga kai na kalleta kadan, sai kuma na dauke na maida kan tvn da take ta latse-latse da canza tasoshi. Idan tayi zaton magana zan mata akan haka, zata sha mamaki kam. Daga karshe ma sai na kunna wayata na bude wani document akan pregnancy issues ina dubawa.
Muka cigaba da zama a haka, babu mai ko tari sai sautin wakoki dake fita daga wata tasha data kunna. A haka Yaya Bilal ya fito ya same mu.
Ya umarceta data kashe kallon, yana so yayi magana damu. Nima sai na kashe wayata, na maida hankalina kan shi.
Yayi gyaran murya, ya fara da kara yi mana nasiha da kuma dokoki daya kafa. Yace babu yan aiki a gidanshi, daga maigadi, sai mai ban ruwan fulawa, sai kuwa wata mace da yace zata dinga zuwa tana tayamu da share-share da wanke-wanke, amma bai yarda da girkin yan aiki a gidanshi ba, mun fahimta? Muka ce mishi eh.
Sai kuwa zancen girki, ya tambayemu kwana nawa muke ganin zasu fi zama convenient a wajenmu? Ni dai nayi shiru ina jin suna muhawarar kwana daya ko biyu shi da Raheemag, har sai daya jiyo ya kalleni, Ya tambayeni ya nake gani? Nace ni duk yadda suka yanke daidai ne a wajena. Nan ma na kara karbar wata hararar dai, na nuna kamar ban gani ba. Daga karshe dai suka kare akan kwana biyu.
Yace tunda ita Ameerah bata da ranar dawowa, zamu cigaba da raba girkin a tsakaninmu har zuwa lokacin da zata dawo. Ya kara da cewa bai yarda da fada ba a gidanshi, babu fada kuma babu cece-kuce, yace duk wadda take da matsala game da wani abu, mu tunkari junanmu mu warwareta a tsakaninmu, ko kuma mu fada mishi, sai yasan yadda zai warware matsalar, muka ce to.
Daga nan muka cigaba da kallonmu har dare yayi, sannan na tashi na musu sallama na wuce dakina.
Kayan da ban gama gyarawa ba, na gyara. Na ciro kayan barci na ajiye akan gado, sannan na shiga wanka. Wanka nayi, na wanke bakina da mouth wash mai kamshin berries, na daura alwala na fita.
Yaya Bilal yana bakin gadona a zaune da wayata a hannunshi yana dannawa, ya daga kai ya kalleni lokacin dana fito. Har naja kujerar da aka ajiye a gaban dresser na zauna, idanunshi suna kaina.
Na kauda kaina kamar ban san yana yi ba, na dauki lotion na fara shafawa a jikina. Ta cikin mirror na sake tsintar idanunshi a kaina, wayar ma ya ajiyeta a gefe guda, ya karkato da hankalinshi kaina kacokam. Naji gabadaya na fara takura da kallon kurillar da yake yi min, a gaggauce na karasa shafa man, na mike tsaye da niyar dauko kayan barcina dana ajiye.
Babban tawul ne a jikina wanda ya sauka har kasan gwiwata, na karasa gaban gadon na janyo kayan, ganin har lokacin yana zaune yana kallona yasa na juya na koma bandaki na sanya kayan.
Wannan karon dana dawo, yana tsaye a bakin gadon, hannuwana saye cikin aljihun sweat pant dake jikinshi, idanunshi kyam akan kofar bandakin yana dan murmushi.
Yace “meye na wani guduwa bandaki kuma? Menene ake boye min ne, wanda ban riga na gani ba?”.
Na kalleshi blankly kawai ban ce komi ba, na wuce kan gado kawai na ja bargo na rufa.
Ya matso ya janye bargon daga fuskata, “uh uh!! Shariyar menene ake min haka, baby na kamar baki gane ni ba?”.
Na sake yin banza na kyaleshi. Bai san tunda na baro su shi da Raheemah a falon nan ba wani haushin shi ya cika ni ba taf? Ji nake kamar in koma in janyeta daga kusa dashi, in jefata dakinta in kulle don ma kada tayi tunanin sake fita ta koma wajenshi, haka nan dai na danne zuciyata na dawo daki.
Yanzu kuwa da nake ganinshi a gabana, tunanin wajenta fa zai koma ba wajena zai dawo ba, naji wani irin matsanancin kishi ya rufe min idanu, kishi irin wanda ban taba jin shi ba.
Ya shafo gefen fuskata daga bayan kunnena zuwa kan lebuna na, cikin nuna damuwa yace “wani abu yana damunki ne? Ko baki jin dadi ne?”.
Wani haushin shi ya kara tuko ni, to ko ina ruwanshi ma da wata rashin lafiyata? Koma dai menene, daga karshe dai tafiya zai yi wajen matar shi ya kyaleni anan.
Nace “wai ina ka baro matarka ne ka taho nan? Ta ma san kana nan kuwa?”.
Ya daga gira cikin alamun mamaki, kafin wani murmushi ya subuce mishi, ya zauna sosai a gefen gadon.
“a’ah, bata sani ba, na taho yiwa baby na kuma amaryata sai da safe ne. Ko kuwa nayi laifi ne?”.
Nace “to ni sani zan yi? Sai ka bari sai ka tambayeta, sai kaji ko?”.
Yace “haka ne, bari inje in tambayeta inji kuwa”.
Bai jira ya sake cewa komi ba, ya duko ya bani peck a kumatuna, ya mike tsaye yana kallona cikin murmushi, “sai da safe baby na, kiyi barci mai dadi”.
Bai jira na amsa ba, ya juya ya fita daga dakin bayan ya kashe min wutar dakin. Na sauke ajiyar zuciya a hankali bayan fitar tashi, ina ji wani irin abu yana mintsinin can kasan zuciyata. Daga karshe dai nayi addu’ar kwanciya barci, na shafe jikina.
Cikin yan kwanakin nan shida, ba karamin sabo nayi da kwanciya a jikin Yaya ba, ban san nayi sabo da jikinshi sosai ba sai da barci ya nemi ya gagareni. Na dinga juyi ina karawa akan gadon, Allah kadai yasan iyaka tsawon lokacin dana dauka, kafin da kyar barci yayi awon gaban dani.
o
Kamar yadda ya saba a Zaria, da asuba ya leko ya tasheni inyi sallah, shi kuma ya tafi masallaci.
Bayan na gama sallar barci na sake komawa. Bani na tashi ba sai daya leko kafin ya tafi wajen aiki, lokacin karfe tara saura. Bayan munyi sallama dashi, na bishi da addu’ar Allah ya kiyaye hanya, na tashi na shiga bandaki nayi wanka. Na fito na shirya cikin riga da siket na paper lace. Dinkin ya matukar karbata kamar yadda ya bi jikina ya zauna sosai kamar second skin. Ni kaina nasan cewa ba karamin gogewa jikina da fatar jikina suka yi cikin dan lokacin wannan ba.
Na fita zuwa falo, babu kowa sai kuloli da flask ajiye akan dinning table. Naje na fara dagawa, indomie ce zallarta da ruwan shayi a cikin flask. Na girgiza kaina cike da tsananin mamaki, Allah dai yasa ba abinda Yaya yaci kafin ya fita ba kenan.
Dama can indomie ban maida ta abinci ba, na maida kular na rufe, na wuce kicin na lalubo gwangwanin oats na fara damawa.
Ina tsaye ina jiran ya dahu, Raheemah ta fado kicin din kamar an jefo ta. Ta bude firjin ta hau dube-dube, da kamar in kyaleta, na dai daure nace mata ina kwana?.
Ta wani dago ta kalleni a dage, taja tsaki ta kara tura kanta cikin firjin.
Abin ya bani haushi ba kadan ba, nace “maida wukar mana baiwar Allah! Sai kace na roke ki wani abu?”.
Daga gani dama a wuya take, kiris take jira, ta kalleni, “to na roke ki gaisuwar ne dama? Kaji wani aikin banza ma, har ki wani daga baki ki gaida ni? To an ki a amsa din, ko kina da abinda zaki yi ne?”.
Ni da tsabar mamakinta ya kawo ni wuya ma, kasa maida mata martani nayi, ita kuwa tayi tsamnanin ko tsoro ne yasa na kasa magana ko kuwa wani abu? Ta ciro lemun exotic ta maida firjin din ta rufe garam! Tace “ya dai fi miki kiyi shiru din don baki da karfin gwabzawa dani. Masu kwacen miji kawai, idan ma don kinga Haleemo ta kwacen miki miji ne kika yi haka, to ita build taci, kuma nan da watanni biyu zamu je mu sha bikinta mu rakashe, ehe! Ke kuma sai mun ga takamar kwacen miji, zamu ga abinda hakan zai tsinana miki. Da kanki zaki nemi takardar ki wallahi, ko kuma ki kare a haka!”. Ta fita daga kicin din fuu!! kamar guguwa.
Na bita da kallo cike da tsananin mamaki, me hakan yake nufi ne? Kuma ma daga maganar arziki sai ta koma ta tsiya, akan me? Naja tsaki lokacin da naga har oats din dana dora ya dahu ya dafe. Na sake jan tsaki lokacin dana zubar dashi na sake dora wani. Cikin tsananin tunane-tunane da saka da warwara na gama hada oats din, na juye a cikin mug na cicciba na wuce dakina.
Bayan na karya, na dauko wayata na kira su Fatsu muka gaisa, mun jima muna hira da ita, tana ta mij nasiha da nuna min muhimmancin hakuri, daga karshe ta ba Malam shima muka gaisa. Shi addu’o’i ya bani wadanda zan dinga yi safe da yamma na neman kariya, kafin shima ya dora da nashi waazin da nasiha, daga karshe dai muka yi sallama.
Ina kashe wayar na kira Sailu itama muka gaisa. Ranar dai wuni nayi kiran wayar yan uwa da abokan arziki. Bayan na gama kuma na dauko textbooks ina dubawa da yin bita, nan da sati biyu zan fara yin internship dina.
☆
Yau ma kamar jiya, sai da Yaya ya leko ya min sai da safe kafin mu kwanta.
Washegari na karbi girki, da safe zamu dinga karbar girkin bayan wadda zata fita tayi karin safe. Yaya yana fita na dauki makullin dakinshi daya ba kowaccenmu, na shiga na gyara mishi dakin tsaf. Na yaye zanin gadon dake kai na shimfida wani, shi kuma na hada shi da kananan kayanshi na wanke su tas, bayan sun bushe na goge.
Bayan na gama turare dakin da turaren wuta, na dauko kofi na tofa wasu muhimman addu’o’i da Malam ya koya min jiya, nabi lungu da sako da kowace kusurwa ta dakin na yarfa wannan ruwa. Sauran ruwan kuma nayi girkin abincin dare dashi. Kai hatta da ruwan da Yaya zai sha sai dana tofe shi da addu’a.
Sai dana tabbatar da komi ya hadu lafiya lau, lokacin har Yaya ya dawo daga wajen aiki, sannan na fada bandaki na tsalo wanka.
*☆⋆39⋆☆*
Satinmu uku da dawowa Abuja, na riga na saba da yanayin garin, gidana, mijina, da abokiyar zama na.
Tuni na riga na fara zuwa aikin internship dina, daga aikin safe sai na rana nake yi, bana yin na dare. Har yau dai babu bayanin uwargida Ameerah. Bata dawo ba, Yaya kuwa bai taba tado maganar game da ita ba, nima dai ban taba tada mishi zancen ba. Don haka muka cigaba da raba girkinmu a tsakaninmu ni da Raheemah, wadda har yau bata sake zaki ba, kamar ma kullum kara rura mata wutar masifa da neman magana ake yi kullum.
Kullum a shirye take da fada, kiris take jira taga gilmawata a tsakiyar gidannan, zaka ji ruwan habaici da bakaken maganganu ya fara tashi, malka-malka kuwa. Ban taba tanka mata ba, kai ban ma taba nuna mata na kula da abinda take yi ba. Illa iyaka idan na fito mun hadu da ita a falo, in mata sannu, ta amsa ko kada ta amsa, ni dai na fita hakkinta.
To sai ma ranar girkina ne muka cika haduwa, ranar da take yin girki wuni nake yi a daki abuna. Babu ruwana da ita, in wuni ina shan fruits da kayan makulashe, sai da dare idan Yaya ya dawo daga wajen aiki nake fita mu ci abincin dare, duk da dai shima ba kullum ba, don abincin matar nan is terrible Sam bata iya girkin azo a gani ba. Abinda zata iya dafa maka ya dahu, indomie ce, sai kuwa spaghetti ranar da sa’ar ta ta kai sa’a.
Don haka bata da damar gasa min magana a gaban Yaya, duk da cewa ta dauko hakan, sai da Yaya ya tsawatar mata sannan.
Da ta tsiro da maganar kin cin abincina, sai dai ta shiga kicin ta girka kayanta, a raina ni kam nace mata umma ta gaida assha. Sai da Yaya ya fatattaketa sosai, nan ma ta hau cewa wai ya daure min gindi, yana sawa ina raina mata wayau. Yace wani irin rainin wayau? Yace shi fa ya kula da take-takenta na rashin son sasanci da zaman lafiya, yace kuma ta kiyayi kanta don ba zai lamunci hakan ba. Abinci ne, ya hana wata ta girka nata daban, idan wata ta girka dayar taga bai mata ba, ta bar mata kayanta taje can ta karata ita kuma da yunwa. Da wannna aka tashi dai baram-baram.
Sai kuma lokacin dana fara zuwa wajen aiki. Ranar farko da zan je Yaya ne yayi jigilar kai ni da kanshi, washegari kuma direban gidan ya kaini, zai kuma cigaba da kaini da daukoni daga ranar. Ina daki sai jiyo tashin muryoyi na dinga yi, rigima suka yi sosai akan ya bada mota ana jigilar kaini wajen aiki.
Yace “kina nufin in barta tana kai da kawowa a cikin motocin haya ne, bayan ina da ikon da zan ajiye motar da zata yi jigilarta ne?”.
Tace “ai wannna ma salon munafurci ne da rashin adalci. Ni me yasa baka ajiye min nawa direban ba sanda ina gidanka a Zaria, ka barni ina yawo a motocin hayar? Ko kuwa don ka nuna mana an shanye ka?”.
Daga jin sautin tashin muryarshi a lokacin kasan cewa ranshi ya baci a lokacin, yace “aikuwa sai dai idan ke ce baki yiwa kanki adalci ba, amma clearly, zan iya tuna na ajiye miki da zai dinga yi miki hidimarki. Sannan kada ki manta, karatu take yi na aureta, kishin ki na banza da wofi ba zai sanya ni kasa sauke hakkin da Allah ya dora min ba. Babu yadda za ayi in bar matata ta dinga yawo a motocin haya a cikin garinnan, bayan ga motoci nan a cikin gidana Allah ya hore min. Idan ma abinda kike tsammani kenan, to sai ki daina!”.
Cikin ihu tace “lallai ma! Wato kuma yanzu zagina zaka fara yi akan karatu ko? Wato saboda matanka suna da digiri, ni bani dashi, shine zaka fara zagina har matanka ma su raina ni ko? To wallahi ba’a isa ba!!”.
Yace “zagi dai ke kika ji shi don ni dai ban daga baki na zageki ba. Karatu kuma bani nace ki barshi ba balle yanzu ki zo ki fara tada jijiyar wuya ki nemi ki tara min mutane ba. Wai ina dalili? Ba zaki taba barin rayuwata ta huta bane? Daga yanzu ki tado wannan, anjima sai ki kirkiro waccan?”.
Tace “to saboda meye na katse karatun nawa? Ina jin saboda aurenka ne?”.
Yaya yace “haka dai kike tunani, ni ban sani ba. Maganar direba ce dai, yana nan, kuma ai ba ita kadai na ajiyewa ba ko? Kema zaki iya aikenshi, zai kuma dinga kaiki duk inda kike son zuwa idan zaki tafi unguwa, don haka maganar wannan ta mutu!”.
Ya bude kofar dakinshi a fusace ya shige, ya barta a falo tana masifa da mita, ni kuwa da nake kwance a daya daga cikin kujerun falonshi na kara lafewa akan kujerar, babu wanda ya kula dani.
Idan na tashi da safe ranar girkina, na kan hada abin kari mai rai da lafiya, idan muka ci, wani lokacin tare muke fita ni da Yaya, kowa ya wuce wajen aikinshi, watarana ya riga ni fita, ko kuma in riga shi. Karfe biyu na yamma nake dawowa, sai in dora abincin rana, shi Yaya baya cin abincin rana a gidan sai na dare, na kuma yi dashi akan in dinga dafawa ana kai mishi wajen aiki amma yaki, yace suna cin abinci acan.
Idan na gama abubuwan da nake yi da yamma, sai in dora abincin dare.
Sai ta fara mitar bana dafa musu abincin rana da wuri, ranar kuma da nake aikin rana ina dafa musu abincin rana da wuri, kafin lokacin ci yayi, abincin ya huce, ko ya saki, wasu irin excuses dai da daga jin su ma kasan rigima ce take nema kawai. Yaya yace to daga yau kowa ya dinga dafa nashi abincin da rana kawai.
Ba haka taso ba, maimakon ta bar maganar, sai ta fara masifar ita fa ta gaji da irin rashin adalcin da Yaya yake gwada mata, ya maidata saniyar ware a gida, ya biye min muna wulakantata, duk muka mata shiru dai. Data gaji da fadan, ta wuce dakinta fuu.
To yanzu dai a haka muke, yanzu ina cikin satina na biyar da dawowa Abuja kenan.
***
***
***
Dare ne sosai, baka jin motsin komi a cikin dakin, sai karan ac da kuma labulaye da suke kadawa sakamakon iskan da yake kadawa mai sanyi. Dakin babu haske, sai hasken farin wata daya ratso ta cikin tagogi da labulayen dakin.
Na sauke wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya a karo na barkatai, ni kaina bansan lokacin dana dauka a cikin wannan halin ba.
A hankali idanuna suka sauka kan sumar gashin dake saman kirjina. Tattausan numfashin da yake ja yana shaka yana sauka a saman fatar kirjina, rabin rigar barcin dana sanya yana saman ruwan cikina. Tun dazu numfashin ya fara saukar min da wani irin kasala, ya kuma haifar min da goosebumps a ilahirin sassan jikina. Sai dai duk yadda naso, na kasa samun zuciyar ture shi daga jikina, duk da ihun da zuciyata take yi min kuwa.
Cikin lokutan wadannan da muka yi munyi wani irin sabo ni dashi ba karami ba. Na sabar mishi da daddadan abinci mai rai da lafiya duk ranar girkina, tsabtar jikina da nashi, dakunanmu da kayan sanyawarmu, kamshin jiki, daki, da ma ko’ina, dadadan kalamai da sanyin hali. Ban taba daga sautin muryata tafi tashi ba a halin argument ko kuma hira kawai, ban taba tambayar dalilin wani umarni da zai bani ba koda kuwa ni abin bai yi min ba, shi yasa bana tantama yanzu har dokin zuwan ranar girkina yake yi, domin duk wani abu da zai sanya shi farinciki shi nake yi, bana yin abinda zai sosa ranshi koda wasa, sai dai cikin rashin sani. Sannan duk abinda zai yi ya bata min rai, ban taba confronting dinshi a gaban kishiya ba, kamar yadda naga tana yi ta kuma koya mishi, na kan bari sai mun shiga daki mu biyun mu sannan zamu kashe mu binne abinmu babu wanda ya sani.
Sannan duk runtsi, duk bacin rai, ban taba gigin raba mana shimfida ba, Anty Sarah tace kuskura na farko da mace zata yi wajen taimakawa balgacewa rayuwar aure mai armashi; raba shimfida da miji lokacin da ake cikin fushi.
Idan yanzu zamu yi fada, ko mu yini cikin fushi da juna, at the end of the day dai, zaka hangoni a dakinshi, akan gadonshi a kwance. Ko ban shige cikin jikinshi kamar yadda ya sabar min ba, zaka hangoni can karshen gadonshi. Sai dai da safe in tashi in tsince ni lullube cikin jikinshi, wasu lokutan daga nan zaka ga fadan ya wuce, watarana kuwa a nan kafin in fita dora abincin kari, zamu yi magana akan matsalar data taso mana, mu magance ta.
Matsalar daya ce dai har yanzu, mun kasa amsa sunan cikakkun ma’aurata. Tun yana kokarin yin wasanni dani a wasu ranakun, yanzu har ya ma daina attempting yin hakan.
Watarana haka na shiga dakinshi musamman, ciki da bai, har bayan dakin nashi, na fitar da komi na sharo har kasan gadonshi, true, na ciro layu, abubuwa iri-iri har cikin matashin kanshi naga abubuwa, naje can bayan gidan bayan Raheemah ta leka makotanmu gidan kawayen data fara yi, na kone su gabadaya.
Sannan cikin dabara da kissa irin tamu ta mata, na samu na lallabo kan Yaya Bilal, wani abokin Malam, babban Malami a cikin Suleja, yazo da dalibanshi suka yi saukar Al-Kur’ani Mai Girma a gidan, sannan duk sati yanzu ranar juma’ah yana bada rubutu a kawo mana, mu sha.
Sannan shi kanshi Yayan na dora shi akan hanyar sadaka ta ciyar da gajiyayyu, da marasa karfi. Yanzu haka duk ranar juma’ah, ana dafa abinci mai kyau a gidan su Ummah, a rabawa almajirai. Har Ummah sai data kirani a waya ta min godiya da haka, a cewarta hakan shawara ce mai kyau. Alhamdulliah, da alamun samun cigaba, tunda a hankali ya dawo da yan wasannin da yake min, duk da a yawancin lokuta na kanji dama kyaleni ya dinga yi, Yawancin darare haka yake barina cikin wani mawuyacin hali, darare da dama haka zan kare su cikin sharar hawaye. Sai dai ko a fuska, ban taba nuna mishi hakan yana damu na ba.
Yanzu dai ina cikin shakku ne, anya Yaya ba impotent bane? Musamman idan nayi duba da cewa, did shekarun nan da suka dauka da matan shi, basu taba haihuwa ba. Amma kuma ai Jan tace lafiyarshi lau, Allah ne bai kawo ba, but then, ba lallai Janan tasan yana da cuta ko baya da ita ba, tunda ba lallai ya fito ya fada mata hakan ba. Amma kuma da hakan ne, anya matan shi zasu yarda su zauna dashi? Ko kuwa? Abin har ya fara rikita ni.
Yau kam har na kwanta barci, wasu ayyuka ne suka sako shi a gaba a office kwana biyun nan, yanzun ma da kyar na janyo shi muka ci abinci, ya koma study room dinshi, wani dan karamin daki a cikin dakin nashi, nan yake gudanar da yawancin ayyukan shi. Har na gama duk wasu ayyuka da al’aduna, na kwanta yana kan desktop dinshi yana aiki.
Har wajen karfe sha daya na dare ina jiran ya dawo, naji shiru, na sake tashi na leka shi, he was so immensed a kan aikin da yake yi bai ma kula dani ba, don haka na maida mishi kofar na rufe, na kashe wutar dakin na kwanta abina.
Barci har ya fara daukata, ban san ko karfe nawa bane lokacin da naji ya hayo kan gadon finally, ya janyo ni cikin jikinshi.
Ina jin shi yana bin fatar jikina da shafa sensually, nasan dai karshen alewa kasa, wajen da muka saba tsayawa kullum dai nan zamu tsaya yau ma, amma kamar kullum, yau din ma kasa hana shi yin wani abu nayi. A haka ya taso ni na wartsake, ba’a jima ba naji nauyin kanshi a kirjina. A haka muka kasance tun dazun, na kasa koda motsa yatsa ne, na kuma kasa yin barcin.
Ban ankare ba, naji an fara kiran assalatu.
A hankali naji Yaya Bilal ya fara motsi, ba’a jima ba ya bude idanunshi, bakinshi dauke da addu’ar tashi daga barci.
A hankali ya dago kanshi ya kalleni, mamaki ya kama shi daya ga idanuna biyu.
Yace “tun yaushe kika tashi?”.
Na daga kafada sama, “ban jima da tashi ba”.
Ya kura min idanu kamar wanda bai yarda da abinda nace ba, na dauke kaina daga kallonshi kamar wadda take tsoron zai karanta tsantsar damuwar dake dankare a cikin raina. Sai dai ban tserewa hakan ba, ina jin ya karanci hakan, ko kuma ya fahimce ni.
A hankali naji ya sake janyoni cikin jikinshi, ya sake nutsa kanshi a kirjina kamar wani karamin yaro. Muka jima dashi a hakan, babu wanda yake kwakkwaran motsi, sai numfashinmu dake shiga kawai yana fita.
A hankali, daga can kasan makoshi, naji yace “am sorry baby!”.
Na dan kalleshi in confusion, nace “saboda me?”.
Ya tashi zaune sosai yana kallona, ni kuma nayi amfani da wannan damar na gyara zaman riga ta a jikina.
Ya kai hannunshi na dama ya kamo nawa dake kan ruwan cikina, ya damke cikin nashi yana murzawa a hankali, yace “for all of this, Na’ilah. Komi ma, tunda muka yi aure I was not able to… you know…!”, ya ma kasa fadin kalmar, sai gesturing da yayi a tsakaninmu. Nima naji kunya, nayi kasa da nawa kan.
Yace “kawai ina so ki san cewa ba haka nake ba, ban san me yasa sai dake kadai bane hakan take faruwa, amma ina kan neman magani, don haka don Allah ki kara yi min hakuri, kinji baby na?”.
Irin yadda yayi maganar da tambayar, helplessly, yasa naji wani irin tausayinshi ya rufe ni, haka naji wata irin soyayyar shi ta kara lullube min kirji.
Na kai hannuna daya na dora akan nashi hannun da har yanzu yake cikin nawa, a hankali, (don kunyar yin maganar naji sosai), nace “to ni menene na bani hakuri, laifin me kayi? Ko kuwa kaji ni ina complaining ne?”.
Ya dan zare ido, idanunshi na nuna alamun mischievousness, yace “baki damu ba fa kika ce? Kenan ni kadai ne na damu, ina ta so inyi ajiya a nan!”.
Ya kai daya hannunshi yana taba kasan marata. Na kai hannuna da sauri ina bige hannunshi, na kama idanuna na rufe, a lokaci guda kuma na juya fuskata na binneta cikin filo, “kai Yaya!”. Na fada shrieking.
Ina jin sautin dariyar daya saki, ya mike tsaye yana cigaba da dariyar, “zaki sani ne yarinya, gwanda ma ki shirya tun da wuri, jikina yana bani soon, I mean very soon, wannan kunyar taki zata bar idanun nan naki da jikinki!”.
Ban ce mishi komi ba har ya shige bandaki, sai da naji ya maida kofar ya rufe sannan na mike zaune ina ajiyar zuciya. A can kasan zuciyata kuwa, sai naji wani sanyi ya ziyarce ni. A raina nace ‘at least dai lafiyarshi lau, sai dai mu kara kaimi wajen yin addu’a, idan ma wani abu ne, Allah ya yaye mishi’.
Yana fitowa daga bandakin, ban jira komi ba na fada ciki a sukwane.
Ina fitowa na ganshi akan abin sallah ya gama yin nafila, na dauki zanin dana shigo dashi saboda dorawa akan rigar barcin dana sanya idan zanyi sallah, na kalleshi, “yau ba zaka je masallacin da wuri bane?”.
Yace “ina tunanin tsayawa muyi sallar mu ne a daki kawai yau”.
Nace “ni dai na yafe, ka tafi masallacin ka kawai”.
Yace “wai korata kike yi ne, baby?”.
Na kama baki ina dariya, “ni ban wani koreka ba, kawai dai na fada mata ka tafi masallaci kaje kayi sallar ka ne a can, kasan yafi lada”.
Ya mike tsaye, “ai shikenan, tunda abin ya zama haka, baby na ta fara gajiya dani har wani korata ma take yi daga daki”.
Ban ce mishi komi ba, har ya fita daga dakin, sannan nayi murmushi na fara nafila kafin a kira sallah.
°•°•°
Ina kicin ina fama da yanka vegetables akan cutting board, Yaya yana dinning room akan daya daga cikin kujerun teburin, iPad dinshi ce a hannunshi, a cewarshi ayyukan jiya yake karasawa saboda a yau din ake so ya aika su, amma kuma hankalinshi baya kan wayar, duk motsin da zanyi idanunshi suna kaina.
Da yake yau ranar assabar ce, dukanmu muna gida.
Anty Raheemah har yanzu bata fito daga dakinta ba.
Har na gama hada abubuwan da zan hada, na kai kan table din na ajiye, Yaya yana zaune, sai dana gama hada komi sannan naje na buga mata kofa.
Ta bude kofar, har yanzu kayan barcinta ne bata cire ba, tana ganina ta hau wani yatsina, “menene?”.
Nace “Yaya ne yace kizo mu ci abinci”.
Bata ce komi ba, ta maida kofar ta rufe. Na tabe baki na koma inda Yaya yake.
Na zauna a gefenshi, na hau zuba mishi abubuwan dana dafa. A plate daya nake zuba mana komi, babu ruwana, tunda abinda yafi so kenan, to fa ni babu ruwana. Har muka fara cin abincin, babu alamunta.
Lokacin da tazo, daidai lokacin Yaya ya duka yana kwashe syrup din jam daya taba gefen bakina da harshen shi, sai sautin jan tsaki kawai muka yi.
Ta ja kujera ta zauna, babu ina kwana babu komi, ta mike kafa ta hau zuba abinci, shima Yayan bai ce mata komi ba, balle ni muka cigaba da cin abincinmu cikin shirun daya ratsa har muka gama. Ta tashi ta koma daki, shima Yaya ya koma dakinshi domin ya karasa aikinshi, ni kuma na dauki kayan da muka yi amfani dasu na wanke.
Tun jiya da dare Janan ta kirani a waya ta fada suna kan hanya ita dasu Harira da suka zo hutu. Da yake bikinta yana ta matsowa, nan da sati uku, suna ta aikin rabon katin gayyata da anko. Tace tunda aka kawo ankon, Yaya ya daukar mana ni da sauran abokan zamana, ina tunanin su ya basu nasu, don tace nawa kadai ya bada yace ta hada da nata a kai wajen dinki.
Tunda na shiga kicin din na hau hada musu abubuwan tande-tande da lashe-lashe da lemuka. Na saka lemuka cikin firjin domin suyi sanyi sannan na koma dakina ina jiransu.
Da wannna damar na samu na fara tunano maganganunmu da Yaya a daren jiya, nayi nisa cikin tunani, ban ma san lokacin dana dauko wayata na dannawa Sailu kira ba. Sai dana ji muryarta sannan. Nayi kamar in katse kiran kafin daga baya dai na daure na kara a kunne, muka gaisa da ita na tambayeta yan biyu, tace suna can gidansu.
Mun dan fara hira da ita, amma na kasa concentrating din komi. Da kanta ta fahimci ba lau nake ba, ta tambayeni lafiya? Da daga farko ce mata nayi lafiyata lau, kai tsaye tace karya nake. Ta fara watso min tambayoyi iri-iri, har sai data fara yin fushi, wai ban yarda da ita bane. Nace “wallahi ba haka bane Sailu, kema kin sani kuma”.
Tace “to menene idan ba haka ba?”.
Nayi shiru kamar ba zan ce komi ba, bata yi magana ba itama tana jiran taji abinda zan ce. In ina na fara, da kyar na iya rufe ido nayi summarizing din abinda yake faruwa damu tunda nazo gidan Yaya.
Tunda na fara take jan salati har na gama, tace “wannan ai babbar matsala ce Na’ilah! Kuma sai yanzu kike fada?”.
Nayi shiru ina hararar bango kamar itace a wajen, nace “dama kika samu na samu kwarin gwiwar fada miki ko?”.
Tace “kin taimaki kanki da kika fada da wuri kam, Allah kadai yasan abinda zai faru idan kuka cigaba da kasancewa a haka. Dole su Inna su ji labari!”.
Na zaro ido, “mene? A’ah, don Allah kar ki fada musu”.
Tace “to me amfanin fada min kenan? Ina dama don a nemo maganin matsalar ne a kuma maganceta?”.
Nace “to amma fa yace shima yana neman magani!”.
Tace “to sai me? Ba sai mu taya shi ba? Baki ji yan magana sun ce hannu da yawa maganin kazamar miya ba?”.
Nayi shiru ina jinta amma hankalina bai kwanta da hakan ba, a tunanina da wani ido kuma zan iya kallon su Fatsu idan wannan maganar ta fita?.
Da lallami da nasihu ta shawo kaina na amince ta fadawa Fatsu ta fadawa Malam, sai da tayi alkawarin ba zata fadawa Yaya Mudatthir ba, amma nasan ko bata fada mishi ba, su Malam zasu fada sannan muka yi sallama da ita na kashe wayar.
Falo na koma naci gaba da jiran su Janan.
Sai wajen karfe sha daya da rabi sannan suka iso. Na fita waje na tarosu da doki na. Nan muka rungume juna muna juyi dasu, sai da muka gama dokin sannan naja su muka shiga ciki. Tunda muka dawo, sai yau suka zo. Baki a dage suka dinga kallon ko’ina suna santin gidan, sai dana musu tour din gidan suka gani sannan muka zube a kan kujerun falo. Na dauko cookies din dana musu da dambun nama da lemun kankana, lemun zaki dana yanka fresh strawberries a ciki, na ajiye musu. Kafin na leka dakin Yaya na sanar dashi sun iso, na koma wajensu.
Muna zaune muna ta hira ya fito, duk suka zame daga kan kujeru suna gaida shi. Ya amsa har yana hadawa da tsokanar su Harira suna ta dariya. Kujerar da nake zaune mai daukar mutum biyu ce, a tsakiyarta na zauna, fulullukan kujerar kuma a gefe da gefena, amma a haka ya kutsa ya zauna kusa dani. Na janye filo daya na kara matsawa gefe na bashi waje sosai.
A nutse suke hirarsu ta yan uwa wadda rabinta maganar makarantarsu ce sai kuwa zancen dangi da yan’uwa, bayan sun gama gaisawarsu, ya koma dakinshi bayan ya umarceni da shima in kai mishi cookies da lemun, nace to.
Bayan sun gama, muka koma dakina, sai da suka leka ta dakin Raheemah suka gaidata sannan muka wuce dakin nawa. Nan na barsu suna ta kara santin dakin, na koma na kaiwa Yaya cookies din, da kyar ya barni na koma wajensu. A cewarshi ba haka na sabar mishi ba. Nace “ni da zamu zo ma mu fita dasu yanzu? Ballema, na yau ne fa kawai!”.
Ya wani turo baki har ya bani dariya. A haka dai na samu na zame na koma wajensu muka cigaba da hirarmu.
Tare dasu muka shiga kicin muka yi abincin rana, muna yin sallah azuhur muka fita rabon katin gayyata. Sai wajen karfe hudu muka dawo, don dama ba wasu gidaje masu yawa muka je ba, muna dawowa suka koma.
Washegari sai ga Fatsu ta kira, nasan akan maganar ce, da kyar na iya dagawa, kunya kamar kasa ta tsage in shige. Nan ta bani shawarwari da wasu addu’o’i da tace inji Malam tace mu dinga yi kullum daga ni har Yayan, ta maganin sihiri ce da sammu. Sannan tace akwai wani magani da za’a kawo mana hade da rubutun da aka saba kawowa, wanka ake yi dashi, mu gwada yin amfani dashi mu gani. Nace to, tare da mata godiya. Taci gaba da min nasiha game da rayuwar aure, tun ina jin kunyarta ma har nazo na daina don ita kam babu ruwanta. Mun jima sosai akan wayar kafin muka yi sallama.
A hankali bikin yana ta matsowa, kwanaki kuma suna wucewa. Na samu da kyar da jibin goshi an barni inje wajen biki inyi kwana hudu, daga can in wuce Katsina in musu kwanaki biyu. Zan dawo Abuja inyi sati biyu ko uku, sai in je Gashua. Duk yadda naso akan ya barni inyi ziyarar gabadaya, ki yayi, dole na hakura musamman da naga yana nema ya rufe ido yace bikin ma na fasa zuwa.
Ranar Laraba zasu fara shagulgulan biki, don haka nayi niyar tafiya ranar talata. Idan aka gama biki assabar, Lahdi in wuce Katsina.
Ranar litinin, ana washegari zan tafi. Ranar babu aiki saboda ranar hutun ma’aikata ce.
Da yake girkina ne yau, bayan mun gama karyawan safe, na koma daki na. Na cire kayan barcin dake jikina, na fada bandaki nayi wanka, bayan na fito na tsaya a gaban mirror na shafa mai, yau ko hodar ban shafa ba sai dan wet lips kawai, na bude wardrobe ina laluben abinda zan sanya.
Daga karshe dai idanuna suka sauka akan wata rigar atamfa, cikin dinkin da Janan ta kai min ne, ban taba sanyata ba sai yau.
Na fiddota tana ta tashin kamshin turaren kayan dana sanya a cikin wardrobe din kafin in shirya kayana.
Rigar doguwa ce, hannuwanta kanana ne da suka tsaya a damtsen hannuna, daga saman kafadar rigar an yi wani irin yanka ta yadda duka fatar wajen take a waje, haka daga bayan rigar ma anyi wani irin show me, rabin bayana a waje yake, daga tsakiyar rigar kuma daga baya, anyi tsaga tun daga kasa har tsakiyar rigar, idan na daga kafa ina tafiya tun daga gwiwata har kafafuna a waje suke.
Ni kaina dana saka rigar sai dana tsaya ina kallon kaina kamar ba ni ba yadda rigar ta fito da duk wata kira ta jikina kamar sai da aka auna ni, abin ya bani mamaki ya kuma kayatar dani.
Na kalli waje ta tagar dakin, naga yadda hadari yake ta kara gangamowa, tunda safe a haka muka tashi. Yanzu garin yayi luf, ya kuma dan yi duhu. Na dan sauke ajiyar zuciya tare da daukar comb na taje gashin kaina, na dauki dankwalin na daura kawai, gashina kuma ya tsaya a tsakiyar bayana yana ta sheki.
Ina cikin fesa turare, da niyar ina gamawa zan wuce dakin Yaya da nasan yana can yana jirana, sai naji an turo kofar dakin.,
“Bab…!”
Maganar daya fara ta tsaya mishi a makoshi. Na juya cikin mamaki na kalleshi, yana tsaye a bakin kofar dakin, baki a dage yana kallona, with admiration.
Na saki murmushi a tausashe, ko bai fada ba, nasan kwalliya ta biya kudin sabulu.
Na danyi juyi a gabanshi kamar wata wadda take fashion parade, na sake juyawa ina kallonshi, “nayi ne?”.
Ya girgiza kai kamar yana shaking wani abu daga kan nashi, ya maida kofar ya rufe tare da takowa zuwa inda nake a hankali, ya tsaya a gabana. Hannu yasa ya kamo habata, na daga kai ina kallon idanunshi da suke karewa ilahirin jikina kallo, “Subhanallah! Just Masha Allah, baby na ba zaki gane irin kyawun da kika yi bane wallahi. Fatabarakallahu ahsana khaliqeen!! Dama haka kike, amma shine baki taba yi min irin wannna kwalliyar ba baby!”.
Na saki yar dariya, “to yanzu ba gashi ka gani ba?”.
Ya sake ni tare da ja da baya yana kara kare min kallo, ni kuwa nayi humoring dinshi ta hanyar sake yin wani juyin, na kara wani. Ina juyowa, tun ma kafin in samu damar daga idanuna in kalleshi, in ga wani hali yake ciki, naji saukar lebenshi akan bakina.
Abin ya daukeni a ban shirya ba, na dan yi sak na yan sakanni kafin na biye mishi na kara kawata abin. Lokaci mai tsayi, kamar ba zai bari ba, kafin ya sakeni a hankali tare da sake dagowa ya kalleni. Hannuwanshi biyu yasa ya tallabo kumatuna, “baby…!”, kadai ya iya furtawa cikin wata irin murya dana kasa tantance idan tashi ce, kafin ya sake lalubar bakina. Wannan karon hannunshi yasa cikin gashin kaina yana yamutsawa. Ban tantance ba naji an daga ni sama cimak, anyi kan gado dani.
Wani abu a tattare dashi yau ya banbanta da sauran lokutan da muka kasance tare, bai taba zurfafa wasanninmu irin na yau ba, ban taba jin intense abu irin na yau ba. Haka kawai naji zuciyata ta hau bugu, babu kakkautawa.
Daidai lokacin da naji an saki ruwan sama mai karfi, lokacin na jiyo ana jan wata certain addu’a, kafin in gama tantance ainihin abinda yake faruwa, wani irin zafi da ban taba jin kamar shi ba ya ratsa ni, na dan saki ihu, a lokaci daya yatsun hannuna suna lumewa cikin fatar bayanshi cikin azaba….
…….
(Ehhhemmm!!).
*☆⋆40⋆☆*
Karfe biyu ta gota lokacin dana farka daga barcin daya daukemu. Yaya yana gefena, kaina yana kan hannunshi daya, dayan kuma ya zagayo bayana dashi yadda na shige jikinshi sosai. Yanayin garin yayi sanyi mai dadi sosai, saboda ruwan da aka gama yi.
Nayi dabara na zame a hankali ba tare da nayi motsi mai karfi da zai tashe shi ba.
Zanin sallata dake ajiye a gefen gadon na dauka na daura, na shiga bandaki.
Duk da ciwon da nake ji a jikina, amma ba wani sosai dinnan bane da zai hana ni tafiya. Yaya Bilal was very gentle.
Na hada ruwan wanka, na shiga ciki nayi duk abinda ya kamata. Na dauro alwala na fito Zuwa yanzu kuma normal nake jina, duk gajiya, ciwon jiki da wani zafi ya tafi sai dan kadan wanda zan iya manejin shi.
Har yanzu yana kwance yana shakar barcinshi. Nayi zaton motsina zai tashe shi, amma har na gama dauke kayana da aka watsar dasu can gefen gado, na linke nashi, na dauko wasu kayan na sanya, bai ma san ina yi ba.
Na zauna a gefen gadon, na fara daddabar filon da yayi matashin kai dashi a hankali, ina kiran sunan shi.
A hankali ya fara motsi, ya bude kyawawan idanunshi suka dira a kaina. Murmushi ya saki mai taushi, “baby. meye haka nake gani?”.
Nima na saki murmushin, “lokacin sallah ya wuce”. Abinda nace mishi kenan, na mike tsaye.
Ya fara kokarin tashi zaune shi kuma, ina ganin haka na juya da sauri kamar zan kifa, na wuce inda na shimfida abin sallah na tada kabbara. Ina jin sautin dariyar daya saki a hankali yana wasu maganganu da kunnena bai jiyo ko menene ba, kafin ya shige bandaki na.
Kafin in gama sallah har ya fita zuwa masallaci.
Ina gamawa na yaye zanin gadon dake kai, na jefa shi cikin washing machine na shimfida wani, sannan na fita da hanzari domin in dora abincin rana. Duk da dai yanzu kowa yana dafa abincinshi na rana ne, na kanyi kokari a ranakun da muka samu hutu ko weekends in hada abincin gidan gabadaya.
Ina fitowa daga dakina, Raheemah ta fito daga nata dakin. Tayi tsaye hannu a kirji tana kallona ina kokarin rufe kofar dakina da mukulli, har na gama na wuce ta gefenta, sannu kawai nace mata wadda ban tsaya naji ta amsa bama na wuce.
Cikin sauri na hau yanke-yanken abubuwa, na fara sanwa.
Ina cikin yin girkin Yaya ya dawo, kai tsaye kicin din ya fado don ta karamar kofa ya shigo kamar yasan a kicin din zai sameni.
Ina tsaye ina kada miyar kubewa a cikin tukunya. Ya rungumoni ta baya, kanshi yana sauka a gefen wuyana. Na fara kokarin zamewa daga jikinshi, amma ko motsi bai yi ba.
Yace “bai kamata ace kina aiki ba yanzu, in fact kamata yayi ace yanzu kina kwance ne kina hutawa. Are you okay?”.
Kunya ta rufo ni kamar kasa ta tsage in shige, nayi kasa da idanuna tare da daga kai.
Murmushi yayi, “ni fa kada ki fara min wani sadde-sadden kai, don ba zan laminci hakan ba. Zaki iya yin girkin? Idan ba zaki iya ba kinga ki barshi, bari in tura yanzu a siyo mana”.
Nace “ni fa lafiyata lau, kuma zan iya yin girkin. Yanzu kawai kaje ka zauna, ko kaci gaba da wasu ayyukan naka, yanzu abincin zai sauka”.
Maimakon ya sake ni, sai ma kara janyoni jikinshi da yayi, “na ki wayon”.
Nace “Yaya…”.
Kafin in karasa fadin abinda zan fada, muka ji anja wani irin tsaki, duk muka juya muka kalli Raheemah dake tsaye a bakin kofar kicin din.
Fuska a murtuke take kallon Yaya, “wallahi an dai fadi babu nauyi, girma kuma ya fadi. Ban da tsabar jaraba ma da masifa, da tsakiyar ranar Allah Ta’ala ma ba za’a daina jaraba ba? Mu dai bamu saba ganin wannan jarabar ba, idan ma ta wanke ta baka ka sha ne, to Allah ya tsare ka”.
Ni baki a dage nake kallonta, me yasa matar nan ta saka min idanu ne a cikin rayuwata? Kada dai ace… ta san abinda ya faru yanzu? Na kalleta cikin zare idanu.
Yaya ma bai ce mata komi ba, sai ma kara nutsa kanshi da yayi a wuyana yana peppering wajen da kananun sumba, kamar bata wajen.
Ta sake doka wani tsakin, “wallahi an dai ji kunya, ya biyewa yarinya karama suna shirme a cikin gida!”. Ta fita daga kicin din tana cigaba da mita da zazzaga masifa.
Na ture shi daga cikin jikina a hankali, wannan karon ya ja da baya ya tsaya yana kallona, cikin turo baki nace “don Allah ka tafi dakinka ka huta, yanzu zan kawo maka abincin”.
Ya shafa sumar kanshi, “but ke ce yakamata ace kin huta baby ba ni ba!”.
Abin nashi ya fara kokarin yin yawa, cikin sanyin murya nace “na fada maka lafiyata lau, don Allah ka tafi kawai”.
Ya daga kafada, “shikenan, tunda kin dage. Amma ki tabbatar yau babu wani aiki da zaki kara yi, ina jiran ki a falona”.
Sai daya manna min peck a goshi, sannan ya fita daga kicin din. Na sauke ajiyar zuciya a hankali, na juya naci gaba da ayyuka na.
A takaice sai bayan la’asar sannan muka ci abincin rana yau. A falon shi na shimfida mana ledar cin abinci, muka zauna. Yaya yafi son cin abinci a kasa, sannan cin abincinshi yafi son su ci tare da wani ko kuma matar shi, saboda haka yanzu abincin safe kadai muke ci a kan dinning. Na dare tun kafin ya dawo daga wajen aiki nake kaiwa falonshi in shirya mishi, muci kayanmu. Ita kuma sai in shirya mata nata akan dinning din.
Bayan mun gama cin abincin, hana ni motsawa ko nan da can yayi. Muna nan har aka kira sallar magriba, sannan ya tafi masallaci. Sai lokacin na dauke kayan abincin na kai kicin. Akwai yar aiki da take zuwa kullum ta mana sharar falo, wanke-wanke da kuma goge-goge, tana dai yin sharar ranar girkina, amma sauran ni nake yin komi da kaina. Musamman ma gyaran dakin Yaya Bilal da falonshi. Ranar girkin Raheemah ma Yaya da kanshi ya umarceni akan in dinga gyara mishi, tunda ita ta gwammace ta mike kafa dai-daya akan kujera tana murza channels, ko kuma ta shura takalmi ta bar gidan yawon gidan makota, akan ta zauna ta gyara dakin mijinta. Ni kuwa ban nuna kyashi ko jin haushina ba, na cigaba da gyara mishi daki.
Dakinshi na koma nayi sallah, ina karatun Al-Kur’ani har aka kira isha’i nayi.
Yau Yaya bai shigo da wuri ba, sai wajen karfe tara ya dawo. Muna babban falo daga ni har Raheemah muna kallo, ko in ce tana kallo, ni a zaune kawai nake.
Ya dawo da ledoji a hannunshi, na tashi na tarbo shi. Dama yace kada in damu da yin girki yau. Na bude ledar naga tsire ne da balangu, yoghurt da roll cakes.
Na ajiye su anan, na shiga kicin na dauko plates nazo na zuba mana. Da ya cewa Raheemah ta sauko, sai ta turo baki gaba, cikin alamun mita tace “uhmmmm! Da yake ita yar gaban goshi ce, dama mana. Yanzu ni har na isa in ce ba zan yi girki ba, ka siyo abinda zamu ci ba tare da ka bata min rai ba?”.
Na girgiza kai a hankali cike da takaicin matar. Aikin kenan fa kullum, sam bata da godiyar Allah. Baka taba yin wani abin arziki ba tare data gwasale ka ba, musamman Yaya. Yana iyaka bakin kokarinshi wajen ganin yayi adalci a tsakaninmu, amma bata taba gani ba. Yadda duk karshen wata yake bani dubu ashirin saboda hidimar zuwa da dawowa, musamman cin abinci a asibiti duk da na ce mishi bana bukatar su, amma ya ki, haka yake daukar ashirin dinnan ya bata, maimakon godiya sai ce mishi tayi, “wai ita yanzu shikenan sai ta albarkaci na zata dinga cin kudin hannunshi?”, abin ya bani haushi ya kuma bani mamaki kwarai.
Yaya ya daga baki zai amsa ta, nayi saurin tarar numfashinshi, nace “anan zaka ci ne ko kuma zaka koma karamin falo?”.
Yaya ya kalleni sosai, nima na kara kallonshi, da alama ya fahimci dalilina na tarar numfashinshi, yace “mu koma falona”.
Nayi murmushi tare da kanne mishi ido daya, wanda yasa ya saki murmushin shima tare da mikewa tsaye. Na dauki plate din dana zuba mana namu a ciki,na wuce na kai falonshi, na dawo da niyar daukar yoghurt da cake din.
Tana tsaye a gaban Yayan kamar wadda take tsare shi daga shiga falon nashi, ihu take tun karfinta, wai ya maidata mahaukaciya, tana magana ya dinga shareta.
Yace “wai ke me yasa ba kya son zaman lafiya ne ko kadan Raheemah? Me ma aka yi daya janyo fada da daga murya anan?”.
Tace “dama yaushe zaka gani tunda an rufe maka ido? Ni da ake wa rashin adalci ni nake gani, kuma wallahi ba zan yarda ba!”.
Yace “sai ki dauki mataki…”, ya zagayeta ya wuce. Nima na kwashe sauran kayan na bi bayanshi.
Falon shi kamar nan ne wajen shakatawarmu da hutawa, Raheemah bata cika shiga ba musamman ma ranar da ba girkinta bane, ni kuma ina kokarin kaucewa wajen ranar girkinta saboda shiga hakkinta. Ranar girkina kam acan nake yini musamman idan Yaya yana gida, mu yi ta hirarmu, ko wasanninmu, watarana kuma sai dai mu kwanta kawai, watarana kuma idan yana aiki in barshi yayi aikinshi ni kuma inyi busying kaina da wasu abubuwan.
Yanzu tashar CNN ya kunna yana kallo, ina gefenshi muna cin naman a hankali, lokaci zuwa lokaci zamu dan tattauna akan wani case da zamu ji an fada a tashar ko kuma wani abu. Har muka gama ci, na dauke kayan. Na dawo falon, nayi matashin kai da cinyarshi har dare yayi, ya kashe kayan kallon muka wuce dakinshi.
~~~
Da kyar ya bari muka yi sallama dashi wahsegari na tafi Kaduna. Da kasa ya kekashe akan cewa sai dai in bari mu tafi dashi ranar juma’ah, kamar zan mishi kuka haka na dinga rokonshi ina magiya, nace “idan ma na zauna me zan maka ne Yaya? Ba fa ni zanyi girki ba yau”.
Da kyar dai, muka yi sallama ya tafi wajen aiki. Wajen karfe goma sha daya, muka bar garin Abuja.
Tuni gidan biki ya fara cika da yan biki. Gida ya cika ya tumbatsa Masha Allah. Bayan mun gaggaisa da mutane, wasu yan uwan nasu ba da basa cikin kasar ko kusa da gari, sai yanzu muka samu muka gaisa dasu.
Muka lume can kuryar dakin Yaya ni da amarya Janan muna hirar yaushe gamo. Tayi ta min shakiyanci, wai nayi fresh, meye sirrin, ko har an bani ajiya ne?.
Na kuwa danna mata harara, “wai don Allah meye matsalar ki ne? Kullum kiyi ta lakaba min abinda bani da?”.
Ta kuwa kwashe da dariya, “to Malama, alamu ne suka nuna haka ba wani abu ba. Ki duba fa yadda kika wani ciko tubarkallah, kin kuma yi haske da abubuwa, idan ba ciki bane to menene?”.
Na kada mata idanu, “kiwon Yayanki ne kawai!”.
Ta saki ihun dariya, abinda ya janyo su Harira dake falo kenan suma suka fado, suka cigaba da shakiyancinsu. Dana gaji sai na janyo wayata, na dannawa Yaya kira na koma can gefe muka kwashi hirarmu ta masoya.
Washegari aka yi kamu anan cikin gidan. An dauko masu decoration da masu raba abinci, abokanmu da yawa sun zo, haka dangin ta dana Almu sunyi kara ba kadan ba. Gida ya dauki jama’a sosai. Har karfe goma na dare ranar muna kan kafafunmu a tsaye muna kokarin gyara gidan.
A dakin su muka yi parking, baki duk an kaisu dakunan dake cikin gidan, wasu kuma suna dakin Yaya da Ummah.
Ummah ta kawo mana damammiyar fura da kanta, da tasha nono ga sanyi sosai. Tun bayan aurenmu da Yaya, kamar an kara mata kaunata haka nake gani, tunda nazo take ta nan-nan dani, abincin da zan ci ma daga dakinta ake kawo min. Sai naji nima kimarta da mutuncinta sun karu a cikin idanuna.
Bayan munyi wanka don mu dan warware gajiya, muka sha furar data kawo mana, sannan fa kowa ya nemi makwanci. Lokacin karfe sha daya ta wuce. Naso in kira Yaya kafin in kwanta, tun da safe da muka yi waya dashi bamu kara yi ba, amma sanin suna tare da Raheemah yanzu yasa na daure zuciyata. Sai na rubuta sako mai cike da kalamun nuna kewa da kauna, na tura mishi. Cikin sakanni talatin da shigar sakon wayarshi, ya dawo min da amsa.
Nan muka kwashe kusan mintuna arba’in muna musayar kalaman soyayya, kafin muka yi sallama dashi.
Washegari aka yi mothers eve, sai ranar Anty Ameerah tazo. Anty Sarah ita tun jiya tazo, sai dai bata kwana a gidan ba, gidan Yayarta dake aure anan cikin Kaduna taje ta kwana.
Ana gama taro Anty Ameerah ta koma Zaria.
Sai ranar juma’ah Yaya yazo shi da Raheemah. Tunda suka zo bata ma zauna a gidan ba, ranar walima muka yi. Yau ma kamar jiya, ana tashi wajen karfe shida Anty Ameerah ta wuce, ita kuwa Raheemah da tunda suka zo kayanta ma a dakin Yaya ta ajiyesu, ta wuce can. Bata shiga cikinmu ba mu kawayen amarya, muma kuma bamu nemeta ba.
Washegari aka daura aure, muka kai amarya gidan aurenta dake can unguwar rimi. Gini ne na kin karawa, idan ka shiga kamar kada ka fita saboda haduwarshi.
Yanmatan sun ce babu inda zasu tafi sai anguna sun zo sun sayi baki, duk da da yamma ne aka kaita. Na gama shan dariyata nace bari inyi tagging dai nima.
Wajen karfe shida na yamma sai ga kiran wayar Yaya, na fito daga cikin hayaniyar hirar da suke yi, na amsa kiran.
“ki sameni a kofar gida”, kawai yace ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo cikin mamaki, kafin na sake kiranshi, nace “muna fa gidan Janan yanzu haka”.
Yace “ehh, nan din fa”.
Cikin sanyin jiki na koma gidan. Su Anty Sarah da basu jima da zuwa ba, su ganin gida suka zo yi kafin su koma Zaria, ciki har da Anty Ameerah, suna cikin bedroom inda amarya take suna tasu kalar hirar suma.
Na matsa na radawa Janan zan tafi, tace “ina zan tafi yanzu bayan ba’a zo sayen bakin ba?” Nace mata “Yaya yake nema na, yace yana waje”.
Ta zaro ido, nayi gaggawar kai mata dukan wasa a hannu kafin tayi tunanin fadin wani abu silly, nace “kada ki wani kawo min wata maganar banza anan, sallama ce kawai zamu yi saboda yau zasu koma Abuja shi da Raheemah”.
Amma bata fasa ba, sai data yi commenting din dai. Na dauki jakata kawai na musu sallama akan cewa zan koma can gida, na fita.
Kamar yadda yace kuwa, yana kofar gidan. Na bude murfin motar na shiga, yayi murmushi tare da janyo ni jikinshi, mun dan jima a haka kafin ya dago ni yana kallona, yace “kai baby na, da alama ke ko kewata ma baki yi ba, ji yadda kika yi wani irin kyau kamar ba ke ba?”.
Nace “a haka din?”.
Yace “sosai ma!”. Ya fara kokarin tada motar.
Ban tambayeshi inda zamu je ba, ya fita daga unguwar. Sai gamu a kofar wani gida a can cikin GRA. Na kalleshi cikin mamaki lokacin da naga yayi horn mai gadi ya bude mishi kofar ya shiga.
Muka fito daga cikin motar, kai tsaye ya shige falo dani. Gidan a gyare da komi a ciki, sai dai babu alamun mutane a ciki.
Nace “nan fa?”.
Yana ajiye wayoyinshi akan center table yace “gidan da muke kawo baki ne idan aka yi, musamman ma lokutan biki irin haka”.
Bandaki ya nuna min yace in shiga inyi alwala, shi kuma ya tafi masallaci. Sai bayan isha’i ya dawo da ledar shake da kayan marmari da take away na abinci a hannunshi.
Ganin take-takenshi, nace “wai ba yau zaku koma ba? Kuma kada ka manta fa tare da matarka kuka zo”.
Yace “to sai me? Ina lissafe da yau zaki fita daga girki fa!”.
Na zaro ido ina kokarin ja da baya daga rarumar daya kawo min, amma duk da haka sai daya cafko ni yana dariya, yace “come on, anjima kadan fa zan maida ki”.
Nace “da gaske?”.
Yana murmushi cheekily, yace “da gaske”.
A takaice ban kara tunawa da wannan maganar ba sai da naga mun yi ido hudu kuru-kuru da hasken rana, washegari kenan.
Karfe tara Yaya ya shigar da motarshi gidan su Ummah, kunya kamar zan nutse a kasa, duk da dai babu wanda yasan abinda kenan.
Yana kashe motar, na fita da sauri na fada gidan. Allah ya taimakeni babu kowa a falon, da alamu baki sun wuce, na fada dakin su Harira daban. Nan ma FirdauFirdausi kadai na tarar tana gyara gado, ta kalleni cike da mamaki, “daga ina haka?”, nayi banza na kyaleta.
Karfe biyu na rana, muka wuce Katsina ni da Is’hak da Yaya ya umarce shi daya kaini. Munyi sallama dasu suna ta min sannu da Ala huta gajiya. Shi Yaya sai da yamma naji yace zasu koma.
Yaran gida sun sha ihu da murnar ganina, aka min masauki a dakin Anty Alawiyya. Da yake ranar Lahdi ce, Baba yana gida.
Aka kaiwa Is’hak abinci yaci, a ranar ya koma Zaria, ranar talata zai dawo ya maida ni.
Ranar haka muka raba dare ni da kannena muna ta shan hira. Sai washegari na shiga gari gaishe-gaishe.
Kulsum ta fara zuwa makaranta abinta, wai wani lecturer ya kyalla idanu a kanta yana ta bibiyarta. Nace mata “kema ki saurare shi mana, sai kiga kun daidaita”.
Ta girgiza kai, “ba yanzu ba Na’ilah, ba zan kara yin sake irin wanda nayi ba gaskiya. Ke dai kawia ki taya ni da addu’a”.
Nace “to shikenan”.
Wannan zuwan nawa naji dadinshi sosai, sai da naji kamar kada lokacin komawata yayi.
Ramata kanta wannan lokacin naga ta sassauto sosai, ko kuma zata iya yiwuwa rashin lafiyar da take yi ce ta sanya hakan.
Ranar talata sai da yamma sannan muka yi sallama dasu cike da kewa, muka wuce. Dole sai a Zaria muka tsaya muka kwana, washegari Laraba muka wuce Abuja. Amma sai da na tsaya a Kaduna sannan.
Na koma gida muka cigaba da gudanar da rayuwarmu. Babu abinda ya canza har yanzu, sai ma wata tsirfa. A gidan na tarar dasu Salame ranar dana koma, wai suna ta shirye-shiryen bikin Haleemo. Sai ranar assabar suka bar gidan, habaici dai har sai dana gaji da ji, amma babu wanda na taba tankawa a cikinsu.
*
Ranar Lahdi da yamma, muna babban falo a zaune, Raheemah ce take yin girki, Yaya ya fita zuwa cikin gari da wannan yammar. Don haka daga ni sai ita, duk da ita tana ta zarya ne ma tsakanin kicin da falon saboda girki da take yi.
Kawai sai karar turo kofa muka ji, mu daga kai haka, sai ganin Anty Ameerah muka yi ta fado falon, wasu matasan yanmata biyu na take mata baya, yayin da maigadi da mai ban ruwan fulawowi suke turo akwatunanta.
Raheemah data mike tsaye zata shiga kicin, tayi tsaye kyam tana kallonsu, nima na bi su da kallon.
Yaya har ya fita bai yi magana akan dawowarta ba, ko kuwa bai san da zuwan nasu bane? Oho!.
Ita kuma ko da wacce tazo?.
Suka mana sannu da gida, Raheemah ta zungura baki gaba ta shige kicin, na amsa musu a sanyaye. Muka gaisa kadaran-kadahan dasu, suka ce sunyi waya da Yaya yace su tambayeni makullin dakinta, na tashi na shiga dakinshi na dauko musu, na nuna musu dakin, suka yi godiya suka tura kai suka shiga ciki, ni kuma na koma falo cikin wani irin yanayi.
Sai da dare Yaya ya dawo. Da yake ranar Raheemah zata fita daga girki, aka yanke shawarar Ameerah zata amsa. Da haka muka aka tashi kowa ta wuce dakinta.
Har ta fita daga girkin, wani ya sake zagayowa, babu wata matsala. Zama muke kadaran-kadahan da ita, idan muka hadu a falo, ko a dakin Yaya, za’a gaisa da ita a mutunce, haka babu ruwanta da shiga harkar da babu ruwanta. Ban taba jin bakinta yayi wata mita ba, ko ya tado magana. Kai ita kwata-kwata ma baka ganinta sai ranar girkinta, sauran ranakun a daki take yini cur, idan ta fito sai dai kicin, ta kwashi kayan makulashe ta koma daki.
Sai nake ganin kamar hakan yafi akan ka wuni kana zage-zage da yada habaici. Har nake cewa kila zata fi Raheemah saukin kai.
Little did I know….
*☆⋆41⋆☆*
Ranar Juma’ah na karbi girki a hannun Ameerah. Kamar yadda na saba, idan ina aikin rana na kan yi iyaka bakin kokarina in ga na dawo da wuri domin in dora abincin dare.
Yau ma aikin dare nayi, na samu wata nurse da muka fara gaisuwar mutunci da ita, Hanifa, na roketa akan ta shigo da wuri ta rike min nawa aikin tunda ita aikin dare take yi, ta amince. Bazawara ce in her 30th. Kirkinta yasa muka fara gaisawa sama-sama da ita, har dai aka fara gaisawa ta sosai. Yanzu yawanci ita take taya ni rike aikina idan zan fita da wuri. A gurguje na mata godiya na wuce. Na riga na kira direban da yake kaini, yana waje yana jirana. Don haka ina fita muka wuce.
Sai karfe bakwai da wasu mintuna muka karasa gida.
Cikin sauri na shige daki, ina shiga na hau cire kayan jikina ina jifa dasu a tsakiyar dakin ba tare dana damu akan in linke su ba. Da yake bana yin sallah, a sukwane na fita daga dakin na fada kicin. Babu kowa a cikin falon.
Allah yasa da zan fita da rana nayi miya na ajiye. Ruwan zafi na dora akan wuta, na nufi dakin Yaya da sauri.
Wani lokacin idan ya fita sallar asuba ya kan dawo kafin ayi isha’i ya ci abinci, idan yana jin yunwa kenan. Idan kuma ya ci abinda ya rike mishi ciki a wajen aikinshi ya kan jira sai bayan isha’i.
Yanzu so nake in ga idan yana falonshi, in ga ko yana bukatar ko da snacks ne yaci kafin in sauke abincin kamar yadda nake mishi sau tari, a ranaku irin wadannan idan ban gama abinci da wuri ba.
Tun kafin in karasa falonshi nake jin sautin karar talabijin, sai kuma sautin magana kamar ana yin hira da yake tashi kadan-kadan.
Nayi sallama a kofar falon tare da turawa, kamar yadda nayi zato, Yaya yana falon a zaune akan kujera.
Sai dai zaune a kasa, daf da kafafunshi, don idan ma wani ya kuskure zai iya cewa akan kafafun nashi take a zaune.
Amma ba ma wannan bane ya dauki hankalina ba, ba kuma dariyar dana tarar suna yi ba, kwalliyar data zabga ne kamar zata je gasar sarauniyar kyawu ta duniya, sai kuwa wani zagayayyen kyakkyawan ceramic plate da yake ajiye akan cinyarta shake da waffles da aka kwarara jam daya nutella akai, ga kuma fresh berries. Abin ya bani mamaki har na kai ga dan dakatawa.
Shirun da suka yi suna kallona ne ya sanya na dawo da hankalina kansu. Na danyi murmushi kawai tare da takawa na karasa wajensu. Sannu na mata ta amsa fuskarta da sauran fara’ar dake kan fuskarta lokacin dana shigo cikin falon.
Yaya ya kalleni lokacin da nake zama a gefenshi, akan kujerar kusa dashi, cikin murmushi.
Na gaida shi ya amsa, tare da cewa “har kin dawo? Ya asibitin?”.
Nace “lafiya lau, yanzun nan na shigo. Dama lekowa nayi in ga ko kana bukatar wani abu kafin in gama girki sai kuma naga…”, na kakare ina karewa plate din hannun Anty Ameerah kallo. Daga ganin yadda yayi fresh, kamshi yana tashi, kasan ba’a jima da gama yin shi ba. Probably bayan Yayan ya dawo daga wajen aiki.
Maimakon ya nuna wani abu, ko ita, sai naga yayi murmushi. Yace “ai Yayar ki ta hutar dake, sai ki sanya ranki a inuwa…”, ya dauki daya ya sanya a bakinshi, ya gutsira ya tauna har da hadawa da lumshe idanu, “… kuma yayi dadi sosai. Bismillah, ki taba mana”.
Na girgiza kai a hankali ina kokarin danne wani abu daya taso ya tsaya min a makogaro, kwacen girki kuma da rana tsakiya kiri-kiri?.
Nace “a’ah, na gode. Bari inje in karasa girkin. Anty Ameerah nagode fa!”.
Idanunta akan allon talabijin tace “babu komi Na’ilah… Yiwa kai ne!”.
Ban ce komi ba na tashi na fita daga falon.
Spaghetti na dafa, nayi warming miyar da nayi. Kafin Yaya ya dawo na kai mishi abincinshi falonshi. Su kuma matan nashi na ajiye musu nasu akan dinning table.
Daki na koma, na shirya kayan dana yasar, na gyara dakin nawa sannan na koma falon Yaya ina jiran ya dawo daga masallaci.
Yana dawowa na shirya abincin, na zauna a gefenshi na zuba mana muka fara ci. Yau abincin kadan yaci, a cewarshi Yayata ta cika mishi ciki. Murmushin yake kawai nake binshi dashi, saboda maganar gaskiya abin ya bata min rai. Akan me ni da girkina, ni da mijina, kawai tazo wai ta mishi girki? Ina so inyi magana, sai dai dole haka nayi shiru saboda bana son yace ina neman tada mishi zaune tsaye a gida, ko kuma bana son zama lafiya, ban godewa abinda ta min ba. Don haka nayi ta kauda maganar ina turata can bayan raina.
Ni kaina abincin yau haka nan dai naci shi cikin dauriya kawai. Mun saba idan muna cin abinci, haka zai yi ta yabon girkin da na mishi, wasu lokutan kuma yana ta tsokanata da yan wasannin shi.
Yanzun ma a hankali naji hannunshi yana min tafiyar tsutsa a bayana ta dan slit din da aka bari a bayan rigar dana sanya. Na daga kai na kalleshi a hankali, ya daga min gira challengely, cikin nuna alamun yana jiran yaga reaction dina.
Nayi dan murmushi, ina kokarin ganin cewa ban bari abinda ya faru yau ba ya hana ni samun farincikin raina dana mijina ba.
Don haka na biye mishi. Cikin kankanin lokaci munyi gefe da kayan abincin, sai gani a saman ruwan cikinshi ina kokarin daukar alewar bounty daya boye a bayanshi.
“Baby na…. Zaki karya ni fa, kinyi nauyi da yawa.. Baby, wayyo!”.
Amma kuma dariya yake yi cikin shessheka, nima dariyar nake yi lokacin da naci sa’ar dauko sweet din.
Na koma na zauna a gefenshi ina bare ledar, shima ya tashi zaune yana maida ajiyar numfashi kamar wani wanda ya kwashi wani dambe.
Ina bare ledar na kai baki na hau taunawa, ya kalleni cikin zare idanu, “ba dai cinyewa zaki yi ki hana ni ba ko baby?”.
Murmushin tsokana nayi tare da saka gabadaya sweet din cikin bakina.
Yace “kam, gaskiya ban yarda ba..”.
Ganin yayo kaina gadan-gadan yasa nayi dan ihun tsokana naja da baya, amma duk da haka sai daya damko ni.
Yayi amfani da karfin jikinshi yayi trapping dina a jikinshi ta yadda babu yadda za ayi in kwace, bakina yake kokarin hadawa da nashi da niyar zakulo sauran alewar data rage a bakina, lokacin da aka turo kofar falon aka shigo.. Da sauri na daga kai naga Ameerah ce. Idanuna suka sauka akan agogo, naga karfe tara ce saura. Wani haushi yazo ya cika ni, kowa yasan a cikin gidan nan idan karfe tara ta gabato a cikin gidannan, kowa ya nemi makwancinshi, sai a bar mai girki ita da mijinta. To me kuma ya kawota yanzu?.
Kallon dana bita dashi baki a dage ne ya ba Yaya damar cikashe abinda yayi niyar yi. Sai lokacin ya sake ni, ya koma gefena yana tauna alewar a bakinshi.
Ameerah ta nemi kujera ta zauna, “sannunku da hutawa”. Ta furta cikin fara’a.
Muka amsa mata, ni ciki-ciki, Yaya kuma yana dan murmushi, yace “baki kwanta bane har yanzu?”.
Tayi wani fari da idanu tana rangwada, “wallahi kuwa baby, ban san me yasa na kasa yin barcin da wuri ba yau, shine nace bari dai in zo in rage dare anan”.
Yaya ya daga kai distractedly, hankalinshi gabadaya akan tv, ana hasko wani labari akan wata sharia da ake kwasa tsakanin wani dan uwa da dan uwanshi.
Na mike tsaye ni kuwa na nade ledar dana shimfida mana na kaita inda ake ajiyeta a cikin falon, na dawo ina hada plates da kulolin, sai lokacin na dan saci kallon inda take, ta canza kayan dazu dana barci yanzu, riga da wando na cotton masu kyau da suka bi jikinta, ta dora hular beanie da tattausan silifas mai buzuzun gashi a kafarta. Nayi kwafa tare da kwashe kayan abincin na tafi kicin.
Ina gamawa da kicin na koma dakina. Na shiga bandaki nayi wanka, brush, na dauro alwala. Duk da cewa ina period, hakan baya hana ni kwanciya da alwala a jikina idan zan kwanta.
Bayan na gama, na dauko kayan barci masu kyau da bayyana surar jiki na sanya, na shafe ilahirin jikina da turaruka masu kamshi da nutsar da zuciya, na dora hijabi doguwa akan kayan nawa na fita daga dakin bayan nasa makulli na rufe dakin.
Har yanzu Yaya da Anty Ameerah suna falon suna hira, sai dai yanzu maimakon kujera, ta sauko kasa kusa dashi. Sunyi nisa a hirar da suke yi sosai, basu ma ji lokacin dana shigo ba.
Nima na lalubi waje kusa dashi na zauna. Ban yi kokarin tsoma musu baki a cikin hirar da suke yi ba, na kurawa tv da take ta aiki kallo ba tare da ina fahimtar komi da suke yi, ko suke fada ba.
Hirarsu suke tayi akan wani cousin dinta daya samu aiki da wani babban kamfani da yake kera motoci a kasar Germany, hirar ta gangara ta koma kan businesses da mahaifinta yake yi, har ta sake gangarowa kanta, wai itama tana so ta fara yin business, amma bata san akan abinda zata yi ba. Nan suka fara muhawarar abinda yakamata tayi.
Da dai naga karfe goma ta wuce, sai na tashi na musu sallama na wuce uwar dakan Yaya.
Anan dinma nafi kusan mintuna goma da shigowa kafin naji ya shigo dakin. Ina jinshi ya shiga bandaki yayi abinda zai yi ya gama, sannan ya dawo dakin. Ya kashe wutar, kafin ya hayo kan gadon inda nake, ya janyo ni cikin jikinshi.
*☆⋆42⋆☆*
Gidan shiru, baka jin motsin komi lokacin dana fito daga dakin Yaya na shiga kicin, duk da cewa karfe tara ne lokacin. Nasan hakan baya rasa nasaba da cewa yau din ranar karshen hutun mako ce.
Na tsaya a tsakiyar kicin din ina tunanin abinda yakamata in dora, daga karshe dai na kunna gas na hau aiki.
Sai wajen karfe goma da rabi sannan na gama. Na dauki na Yaya na tafi falonshi na kai na ajiye, sannan na dauki na matan nashi suma na kai falo na ajiye. Lokacin Raheemah har ta fito, tana zaune akan daya daga cikin kujerun falon tana waya da daya daga cikin kannenta.
Na leka dakin Yaya, baya kan gadon amma da alamu yana bandaki yana wanka saboda karan ruwa da naji yana tashi. Na karasa na gyada dakin tsaf, na kawo airfreshner na fesa. Sannan nima na koma dakina.
Kai tsaye wanka nayi, na fito nayi amfani da hand dryer na kafar da gashina, sannan na zauna akan dresser na fara bin duk wani lungu da sako na jikina da turaruka masu kamshi, wadanda nasan suna rikita min Yaya. Kamar kullum, yau ba ban wani tsaya yin kwalliya ba, bayan yar hoda dana goga, wani lip balm kawai na shafa a bakina. Mai kamshi da taste din strawberry. Wani zuwa da Anty Sarah ta taba yi nan, ta kawo min shi. Ban ma taba shafa shi ba sai yau. Na kalli kaina a madubi, nayi dan murmushi ganin yadda na fito tsaf a cikin kayan dana sanya. Riga da siket ne na wani material mai taushi, yanayin dinkin kamar wasu English wears. Rigar mai dogon hannu ce, amma an tsaga hannun tun daga kafada har tsintsiyar hannu, shima siket din anyi tsaga a tsakiyar shi ta yadda bayan kafafuna suke a waje idan ina tafiya. Nayi daurin dankwalina fanka, gashina dana kame a cikin band ya fito yana ta sheki da tashin kamshi. Na fita daga dakin.
Har yanzu Yaya bai fito ba, don haka na wuce dakinshi kai tsaye.
‘oh please!!’, na fada exasperatedly, lokacin idanuna suka sauka akan Ameerah dake zaune akan kujerar hutu dake fuskantar kofar dakin.
Yaya yana gaban dresser da ruwan tokar jallabiya a jikinshi, mai yake shafawa a sumar kanshi, gefe guda abin sallah ne a shimfide, da alamu tashin shi kenan daga kai. Kila sallar walaha yayi.
Yayin da matar tashi take sanye da riga da wando, English wears, kai babu dankwali balle hula, kitson da aka yi mata ya kkwanto har dokin wuyanta. Jarida ce a hannunta tana dubawa, Yaya kuma nata zuba mata hira.
Na girgiza kai a hankali ganin sun zubo idanuwansu kaina, Allah kadai yasan irin takaicin daya ciko min ciki, haka nan na daure na kakaro murmushi tare da karasawa cikin dakin. Yaya ya bini da kallo yana murmushi.
Na karasa gabanshi na tsaya, “Barka da safiya Yaya, har ka tashi?”.
Yayi murmushin nan nashi mai burgewa, “na tashi tun dazu, har na gaji da jiran kizo ki taya ni shiryawa”.
Nayi tunanin yanzu ma cewa zai yi an hutar dani, har na fara plotting irin rashin mutuncin da zan manna musu, nace “kasan fa girki na fita inyi, idan ka gama shiryawa kazo muje ka karya”.
Ya gyada kai, “na kusa, gani nan zuwa. Kinyi kyau fa!”.
Na kalli kayan jikina, kafin na sake kallonshi ina sakin murmushin saye zuciya, na manna mishi peck a kumatu tare da rada mishi thank you a kunne.
Sai dana juya zan fita sannan na kalli inda Anty Ameerah take, nace “oh oh! Anty Ameerah an tashi lafiya? Ashe kina dakin?”.
Dan murmushin da yake kan fuskarta ya yaye, kafin ya sake dawowa, “lafiya lau Na’ilah. Wai ina dan taya shi hira ne ganin shi kadai ne a dakin”.
Na girgiza kai cikin murmushi nima, idan duniyanci ne, gidan shi tazo, nace “babu komi wallahi, kin kyauta. Abinci ya kammala idan zaki ci”.
Ta gyada kai tana murmushi, ni kuma na bude kofar dakin na fita.
Nayi zaton zata biyoni ne, amma shiru har na gama zubawa Yaya abincinshi, bata fito ba. Zuwa can sai gasu sun fito tare, hannunta damke cikin nashi. Na ciza baki cike da takaici da kuma mamakin matar, ina kula da lokacin da Yaya ya zame hannunshi daga cikin nata, amma duk da haka sai data sake yunkurin kamo shi, yayi saurin zama kusa dani. Ni kuwa na fara tura mishi abincinshi gaban shi.
Abincin dana zuba daidai wanda zamu iya cinyewa ne ni dashi, ina kallon yadda ta fara raba kallo tsakanin kulolin dana ajiye a bude babu komi a cikinsu, da kuma plate din gaban Yaya.
Ganin bata da niyar barin wajen, yasa nace mata “abincin a babban falo na ajiye”.
Ga wani mutum daban, ko kuwa shi Yaya dake zaune yana durawa cikinshi abinda na girka mishi, zai yi zaton cewa tuni ne kawai nake mata, amma ita ta sani, nima nasan cewa ce mata nayi ta bamu waje.
Na kura mata idanu ina son tace wani abu, kamar tana son taci gaba da zama anan taga yadda ake fadin ‘bar nan wajen’, gatsar. Kowa yasan cewa ranakun weekend, har azuhur mai girki tana tarr da maigidanta suna hira ko duk ma abinda suka ga dama. Duk sai idan Yaya ya dawo daga masallaci sannan muke haduwa a babban falo, watarana kuma a falonshi, wani lokaci ayi hira, watarana kuma kowa yayi abinda yaga yafi mishi. To meye nata na wani zuwa ta dinga neman batawa mutane jindadin safiyarsu?.
Murmushi itama tayi, daga ganinshi bai kai ciki ba. Ta kalli Yaya tana wani firirita da rangwada, “babyyy… Kasan fa bana jin dadin cin abinci ni kadai musamman idan ina ganinka, gaskiya ni dai bari inje in zubo nawa sai inzo nan mu ci At least idan ina jin motsinku a kusa dani zan fi jin dadin abincin”.
Yaya ya danyi hesitating, da alama shi kanshi bai yi maraba da hakan ba, sai dai sanin halin Yaya na rashin son disappointing mutane, ba zai iya cewa a’ah ba.
Ban ce komi ba, kaina a kasa ina tura abincin cikin bakina kamar bana ma jin abinda suke fada, sai dai gabadaya hankalina yana kansu ina jiran abinda Yayan zai ce mata.
Kallona yayi, yace “babu matsala?”.
Na daga mishi kafada kaina a kasa, “wai ni? Noo, babu komi. Meye a ciki?”.
Yaya bai fahimci yadda nayi maganar cike da dacin rai ba, yace mata “to ki je ki zubo din”. Ta kuwa juya ba musu ta fita daga falon.
Na bita da kallo ina sake-sake a cikin raina, wata idea ta sauka a cikin raina. Nayi murmushin mugunta.
A hankali na matsa kusa da Yaya, na tabbatar kamshina yana kaiwa cikin hancinshi yadda na kamata, cikin salo na karairaya, ina kada idanu nace mishi “kasan wani abu Yaya?”.
Ya dago kai a hankali ya kalleni, ina kula da yadda ya lumshe idanu yana kara shakar kamshin turarena, nayi murmushi. Kai kawai ya iya dagawa ba tare da yace komi ba, daga haka ma kadai nasan cewa ya shiga cikin wani yanayi.
Na kara matsawa saitin kunnenshi, “yanzu nayi wanka”, na rada mishi a kunnen nashi.
Kallon daya watso min cikin zare ido yasa na kusa shekewa da dariya, na dai daureta, nayi murmushi, “da gaske?”, ya tambaya breathless, kamar wanda yake dambarwa da numfashinshi, na gyada mishi kai.
Bai ce komi ba, ya ture plate din abincin can gefe, bai ankare ba naji an daga ni sama cimak, sai dakinshi. Na sheke da dariya ina kokarin zamewa, amma ina, ya maida kofar dakin baram ya rufe kamar tashin duniya. Bai min masauki a ko’ina ba sai akan tattausan gadonshi.
Tun ma kafin in gama tantance abinda ya faru, naji an fara zame min kayan jikina. Dariya kawai nake kyalkyalawa, gefe daya cikin farinciki, ganin yadda mijina ya rikice bayan dududu kwanaki shida ne kawai muka yi ba tare da juna ba, gefe daya kuma ta mugunta ce. Ina ta picturing yadda fuskar Ameerah zata kasance idan ta dawo cikin falon nan taga babu kowa sai kwanukan abinci kawai. Ko zata biyo mu taga abinda yasa muka tashi kuwa? Na sake sakin wata dariyar ina tunanin abinda zata yi idan ta shigo ta ga halin da muke ciki yanzu. Watakila daga yau ta shiga cikin hankalinta.
⋆⋆
Lokacin da muka sake fitowa daga dakinshi, tuni wasu masallatan suka gama sallar azuhur. Falon babu kowa sai kayan abincin da muka bari dazu, nayi murmushi ina girgiza kai. Yaya ya min sallama ya fita zuwa masallaci, ni kuma da yake na riga nayi tawa sallar a dakinshi, na hada kayan na wuce kicin.
Dukansu suna babban falo a zaune, Raheemah na kallo, Ameerah kuma tana wasa da kan wayarta. Na musu sannu na wuce kicin, babu wadda ta amsa min, sai Raheemah data bini da kalmar ‘jarababbiya’, ban ma nuna naji abinda tace ba na fada kicin.
In dai akan farantawa mijina rai ne, babu abinda ba zan iya yi ba, ban damu da duk abinda zasu ce ba, duk wadda taga zata iya jerawa dani, sai ta biyo bayana mu buga.
Yinin ranar haka muka yini, yau mu duka hudun muka hadu a falo ana ta hira, wadda yawancinta ni da Yaya ne muke yin ta, Raheemah bata saka mana baki sai idan harkar korafi ta taso, dama nan tafi auki, ita kuwa Ameerah, kokarinta kawai taga ta janye hankalin Yaya daga kaina, wanda ban bari hakan ta faru ba. Tana bukatar kara zage damtse sosai kafin hakan ta faru. Bata san cewa zaman nan da muka yi dasu ba, don dai ya zame min dole bane? Ni a son samuna, mu zauna mu biyu daga ni sai shi kawai, amma duk da kasancewarsu anan wajen, hakan ba zai taba hana ni yin abinda zai sanya mijina cikin nishadi ba. A haka dai yinin namu ya kare.
Yau ma da dare irin jiya ce ta faru, sai gata ta kwaso kwalliya, wai tazo taya mu hira. Sai dai maimakon wannan karon inji haushin haka, sai kawai nayi murmushi. Naci gaba da yiwa Yaya tausa a kafafunshi kamar yadda ta shigo ta same mu, muka cigaba da hirarmu dashi. Babu jimawa ma Yayan ya tashi yace zai je ya kwanta, muka mata sallama muka shige daki bayan mun bar mata sakon ta kashe wutar falon idan zata fita.
Washegari na fita daga girki, Raheemah ta amsa. Wani abin mamaki, sam Ameerah bata yi abubuwan data fara yi ba lokacin da nayi nawa girkin. Kenan hakan yana nufin ni ce dai take yiwa wannan shirmen? Idan kuwa haka ne, a shirye nake. Wannan shi na kira ‘kishi’.
Kodayake, ban ga laifinta ba, Raheemah dai ba ruwanta da wani kula da tarairayar miji. Idan ta dafa mishi abinda ta dafa, wani lokaci yini take yi tana kallo a falo ko kayan da aka ci abinci bata dauke ba, watarana kuma gidan ma take bari. Saboda haka nafi kyautata zaton Ameerah gani take yi kwace miji a hannun Raheemah ba wani aiki bane, kuma da gaskiyarta. Sai ni kenan.
*
To rayuwar haka taci gaba da tafiya dai. Zaman da muka yi dasu a waje daya ya bani ikon fahimtar su sosai.
Ita Raheemah, tana da wani irin hali na daukar zuga da shawara. Babu abinda zata aikata ko ta gudanar, sai ta nemi shawarar kannenta. Sai ya zama kamar sune ma suke juya mata rayuwar aure gabadaya. Bata tsinanawa miji komi sai dan banzan mita, yawo da lalaci.
Ita kuwa Ameerah, ita ce ainihin ma’anar kissa da iya lallabin miji. Ta kowane fanni ba za’a kirata wadda ta gaza ba, ta iya kwalliya, girki, uwa uba iya kula da miji. Matsalar, bata san miji ya gindaya mata doka ta bi ba, sai dai tayi abinda taga dama kawai, babu ruwanta. Akwai lokuta da dama da zai hana ta fita, amma yana saka kafa ya fita, haka itama zata dauki makullin motarta ta fita Wata latest Benz da mahaifinta ya aiko mata da ita, da Yaya yace ta maida, a cewarshi me zata yi da mota bayan ga motoci nan ya ajiye mana? Sai tace mishi su duk gidansu, babu wanda yake tuka Honda da vibe. Ina wajen lokacin da hakan ta faru, sai na kama bakina kawai ina girgiza kai.
Akwai ma wata rana da zai tafi wata seminar ta kwana uku Gambia, tace mishi zata je gida kafin ya dawo, yace mata a’ah. Sai dai yana tafiya, sai ga wannan yar uwar tata data rakota ranar data dawo, da alama anan cikin Abujar take, suka fita babu ko sallama, lokacin itama Raheemah su Salame sun zo, sun shiga gari yadda suka saba, ban ce musu komi ba nima. Ashe Babanta da kanshi ne ya sai mata tikitin jirgi suka tafi kasar France wajen graduation din dan gidan kanin Babanta. Sai ranar da Yaya zai dawo da yamma, ita kuma ta dawo da safe.
Ire-iren wadannan abubuwan dai, ina kula dasu. Ban taba daga baki na fadawa Yaya ba, saboda na farko bana so ace ina tada rigima da zauni tsaye, na biyu kuma bana son ya kasance daga bakina ya fara jin wannan danyen aiki, nasan zai iya cewa kawai na fada ne, don haka na kame bakina na bame.
Tunda dai yanzu duk na karanci halayensu daya bayan daya, ina zaune da kowaccensu ta yadda ta bullo min. Na kan bi duk hanyar da zan bi wajen ganin cewa na kaucewa cece-kuce dasu, idan daya daga cikinsu ta min abinda bai kwanta ba, na kan san yadda nayi na maida musu da martani a aikace ba tare dana bari fatar bakina ta motsa ba.
Ameerah irin mutanen nan ne macizan sari ka noke, sai lokacin na fara yarda da maganganun Janan akan cewa gwanda zama da Raheemah akan Ameerah. Saboda ita Ameerah, sha yanzu ce magani yanzu, idan abu bai mata ba, zata fito tsab ta fade shi, koda cikin masifa ne kuwa. Ita din kamar budadden littafi ce, mai saurin karantawa. Ameerah kuwa ba haka take ba, baka taba fahimtar inda ta sanya gaba. Hakan kuwa yana da nasaba da halinta na danne komi da murmushin da bai idanunta ba, ita ba kamar Raheemah bace sam. Raheemah idan mutum bai mata ba, to kawia bai mata ba, ko kallon inda mutum yake bata yi balle kayi tunanin ta damu da kai. Yayin da Ameerah baka sanin tana son ka ko tana kin ka, sai dai kaga hakan a aikace kawai ba tare da hakan ya nuna a fuskarta ba. Hakan yasa mafiya yawancin lokuta Yaya ya kan yi zaton idan ta aikata wani abu, mistake ne, saboda haka baka da damar da zaka yi korafi.
To a kowani hali dai, haka muke gudanar da rayuwar tamu, yau dadi, gobe babu.
Tunda na fara internship dina sai wannan satin suka fara biyanmu, saboda yar matsala da aka samu wajen shigar da takarduna, amma yanzu komi ya gyaru.
Ranar da aka turo min kudin na gansu kamar a mafarki, har sai da nayi hawaye. Yau dai wahalhalun nan da muka sha, sun fara biya. Na shiga kasuwa, siyayya tun daga kan su Auwal, har matan Baba da shi kanshi, babu wanda ban ssiyawa abu ba, haka su Fatsu dasu Yaya.
Anyi hakan da kwana hudu, na tafi Gashua. Yaya ya sai min tiket din jirgi wanda ya sauke ni a Yobe, daga can na wuce Gashua.
Ba karamin jin dadin yadda na samu su Fatsu nayi ba. Yan biyun Yaya suna ta guje-gujensu da surutu. Sai lokacin naji cewa ashe bayan aurenmu, sau biyu Yaya yana zuwa suna gaisawa. Bai kuma taba gaya min ba. Yanzu ma da zan taho haka ya hado ni da kudin tsaraba wadda sai da nazo nan sannan na siya abubuwan da zan raba. Kamar kullum, a gidan Fatsu na sauka.
Kwana na biyu ina yawon gaisuwa da ganin dangi, ana uku ne muka je Kauyen Alkali wajen Anty Halima. Ba karamin murna tayi da ganina ba. Muka mata yini ni da Sailu da twins, sai da yamma sannan muka koma. A gidan su Sailu muka sauka, na zube akan kujera ina nishin gajiya. Tunda nazo nake a gajiye, barci bai taba isata ba, wanda nafi danganta hakan da gajiyar mota.
Sailu kuwa tunda muka zo ta fada kicin ta hau girki, nan da nan gida ya bade da kamshi. Ina so inje in tayata yin girkin, amma kwata-kwata na kasa motsawa. Wani irin barci ne ya fara fuzgata ba tare dana shiryawa hakan ba.
Sailu ta fito daga kicin, ganina a kwance yasa ta dakata tana kallona, Malam da Abul-khairi suna ta wasan su a tsakiyar falon. Na dago kai a dan galabaice ina kallonta, tace “wai lafiyarki lau kuwa? Tunda muka dawo kika wani langwabe a kan kujera kamar wata mara lafiya?”
Nace “wallahi nima ban sani ba, ina ga kamar gajiyar hanya ce har yanzu bata sake ni ba”.
Ta kyalkyale da dariya, “hahh, ina ruwan ba sabon shiga ba! Idan ma zaki warware ki san abinda yake damunki, ki mike. Ko in zo inyi palpating dinki ne?”.
Na tashi zaune da kyar, “palpat… me??”, na zaro ido, “ba fa haka bane, bani da komi, da gaske”.
Ta gyada kai tana dan murmushi, “kada ki wani gaya min ba haka bane, duk ga alamu nan sun bayyana a jikinki?”.
Nace “kin dai san wannan abin fannina ne ko? To bani da komi da gaske”.
Tace “to ai shikenan, kada dai ki koma barci don an kusa kiran sallah”. Ta koma kicin, nima haka nan na tashi na bita kenan din ko jikina ya dan warware.
Kwana na biyar cur anan, sannan na musu sallama na tafi. Wannan karon motar Kaduna muka wuce kai tsaye, sai wajen karfe hudu muka shiga cikin Kaduna. Jikina yadda kasan an yi min dan banzan duka haka nake ji, ban taba jin wuyar tafiya ba sai yau.
Direban gidan su Ummah yaje ya dauko ni daga tasha zuwa gidan. Nan na samu tarba mai kyau daga wajensu. Su Firdausi suna makaranta, aka kaini dakinsu nayi wanka da sallah, sannan naci abincin da aka kawo min. Saboda gajiya ma ban iya cin komi ba, na koma na baje anan kusa da kayan.
Sai da Yaya ta leko sannan na tashi da kyar, ganin yadda nayi daidai yasa tayi dariya, tace “ki koma kan gado mana ki kwanta, kwanciya a kasa ba dadi, ga sanyin tiles. Ke kuwa yanzu sanyi zai iya cutar daku a halin da kike ciki”, ban fahimci komi take nufi da mu ba, na tashi na koma kan gadon na kwanta dai.
Washegari a gidan Janan na yini. Itama tunda na isa, zancenta daya, na harbu. Duk yadda naso in fahimtar da ita akan ba haka bane, kin yarda tayi.
Tana dariya tace “wai ki hakikance akan abinda baki gwada kin tabbatar da gaske bane ko ba haka bane? Ni naga abinda na gani, ke dai da idanuwanki suka rufe kika kasa ganin komi, sai kije kiyi tayi”.
Na kada mata idanu sama, na dauki kankarar da ta dalilinta ne maganar ciki ta taso, na kai baki ina harararta, “sai kuci gaba da lakaba min abinda bani dashi ai, ku zaku yi disappoiting din kanku!”.
Tace “to ai shikenan, zamu gani”.
Sai da nayi sallar la’asar sannan na mata sallama, muka wuce Abuja.
*☆⋆43⋆☆*
Saboda tsabar gajiya washegari ko asibiti kasa zuwa nayi. Yini nayi cur akan gado, ga yunwa da take ta rarakar min ciki amma na kasa samun kuzarin fita. Sai yoghurt da maltina nayi ta durawa a cikin cikina wadanda na jera su a cikin firjin, har sai da naji kamshinsu yana neman sanya ni amai sannan na kyalesu.
Sai can da yamma sannan na iya tashi, wani abin mamaki kuma babu gajiya balle ciwon jiki, sai lokacin nayi wanka, na dauki wata doguwar riga yar Saudiya, ruwan madara na saka a jikina. Nasan lokacin Yaya ya kusa dawowa daga wajen aiki, ranar Raheemah ce take yin girki.
Falon Yaya na wuce, wayar hannuna a hannuna. Sai da yammar nan sannan naga tarin kiran dana rasa da sakonni, tunda na dawo wayar take cikin jaka, ban daga ta ba sai yanzu.
Yaya Bilal naso in fara kira ganin kiranshi har sau uku, da sakonshi da yake tambayar lafiya ban dauki wayarshi ba? Sai dai ina zama, sai gashi ya fado falon. Da alama yau ya tashi da wuri daga wajen aiki.
Na mishi sannu da zuwa, daidai lokacin da Raheemah da Ameerah suka shigo suma kusan a lokaci guda. Ya amsa yana kokarin cire neck tie din shi, “lafiya nayi ta kiran wayarki baki dauka ba?”.
Nace “gajiyar hanya ce ta hana ni ko motsi yau wallahi, sai yanzun nan na gani”.
Yace “ok”, ya shiga daki, Raheemah ta bi bayanshi, Ameerah kuma ta samu waje ta zauna.
Babu wanda yayi magana a cikinmu, ni Janan ma na kira da naga nata missed call din, muka sha hirarmu da ita har sai da Yaya ya fito zai tafi masallaci, sannan muka yi sallama. Nima dakina na wuce da niyar yin sallar na bar su anan.
Sai da naji motsinsu a babban falo sannan na fita nima.
Yaya na zaune akan kujera, su kuma sun sanya shi a tsakiya. Sai naja kujerar dake fuskantarsu na zauna.
Raheemah tana bude kwanon abincin, wani kamshin kifi daya bugo min hanci, ba shiri na ja da baya ina yatsina fuska. Wani irin yawo naji diyan hanjina suna min a cikin cikina.
Kwana biyu na kula yanzu tana kokarin zubawa Yaya abinci da kanta ba kamar farkon dawowarmu ba. Ko kuwa don taga daga ni har Ameerah ba ma barinshi ko ruwa ya zuba da kanshi? Ita dai ta sani.
Sai dana bari duk suka zuba nasu, ina kallo Ameerah tayi wancakali da nata plate din, ta tsoma cokalinta a cikin abincin Yaya. Na jinjina kai kawai tare da jan plate nima na fara zubawa kaina. Macaroni ne jollop, da ya sha kifi da nama sai lemun exotic na abarba da kwakwa, da ruwan gora. Duk yadda nayi ganin cewa na hana warin kifin nan damuna, kasawa nayi, don haka abincin ma kadan na zuba kawai. Idan da ba don yunwar da nake ji bama, babu abinda zai saka ni cin abincin nan. Haka nan dai na cije baki na kai cokalin farko bakina. Tun ma kafin in saka shi a bakin nawa, wani irin amai ya tuko ni kamar me.
Da sauri na ja kujerata baya na tashi cikin sauri na fada bandakin dake nan cikin falo, ina shiga na fara amayar da duk abubuwan dake cikin cikina.
Yaya daya biyo bayana da sauri, ya fado bandakin shima. Shi ya taimaka min na tashi saboda yadda nake jin gabadaya gabban jikina sun kasa motsi ga wani jiri da ciwon kai. Ya taimaka min na wanke bakina, ya gyara wajen dana bata sannan ya tallabo ni muka koma falon. Matan nashi na zaune, suka biyo mu da kallo har ya kwantar dani akan kujera.
Ya juya ya kallesu yace “Raheemah miko min ruwa”.
Bata ce komi ba, ta dauko gorar ruwa daya ta tashi ta kawo mishi. Ya tallabo ni na dan tashi zaune, ya kafa min gorar a baki, dan kadan na sha na koma na kwanta. Ya rufe gorar ya ajiye, ya dafa kaina da tunda muka fito nake dafe dashi.
Murya cike da damuwa yace “me yake damunki ne? Dama baki da lafiya ne?”.
Na girgiza kai a hankali, “a’ah, ciwon kai ne dai nake ji kadan, da alamu na gaji ne da yawa”.
Yace “me zaki ci to, zaki iya cin abincin in kawo miki wani?”.
Gabadaya na rasa kuzarin yin magana, kai kawai na iya girgiza mishi.
Yace “to me kike son ki ci?”.
Nan ma na sake girgiza mishi kai, ya dan yi frowning, “kin san ba zan taba barinki ki kwana da yunwa ba ko baby? Ki fada min abinda kike son ci idan na dafawa ne sai a dafa miki”.
Nayi shiru ina tunanin abinda zam ce mishi amma kuma ji nake kamar duk duniya babu abinda zai iya shiga cikin cikina yanzu. Ya fara jero sunayen abinci kala-kala, har da su Chinese da Italian, daga karshe dai nace mishi salad.
Ya shafa kaina har yanzu damuwar fuskarshi bata bar shi ba, yace “bari yanzu a siyo miki, sannu kinji?”. Na gyada mishi kai, shi kuma ya tashi ya dauki wayarshi. Ban san me yace ba, na dai ji yana maganganu kasa-kasa, yana gamawa ya dawo kusa dani ya zauna. Ba ayi minti talatin ba, aka kawo salad din a cikin take away, na tashi zaune shi kuma ya zauna a kusa dani. Da kanshi ya dinga bani, na kuma samu naci da yawa.
Ina gama ci, na tashi nace mishi zan wuce daki in kwanta, nan na musu sallama, yana biye dani har zuwa dakina. Da kanshi ya taya ni sanya kayan barci sai da yaga na kwanta sannan ya kashe min wutar dakin. Babu jimawa barci ya dauke ni.
Washegari na koma bakin aikina.
*
Kwanana biyu da dawowa, a hankali na fara lura da canje-canjen da jikina yayi. Misalin yadda fatar jikina tayi wani irin smooth da taushin da karya mutum yake yace na mayuka ne, ga wata kasala da nake yawan ji, yawan barci da jin yunwa duk da dai bana wani zabar abinci. Da dai sauran canji da na kasa kawar da kai daga garesu.
Na fara tunano maganganun su Sailuba da Janan, da irin assumption dinsu. Amma na kasa yarda da hakan.
Na fito daga bandaki jikina daure da towel, da kuma dan karami a hannuna ina kafar da lemar jikina. Na tsaya a kusa da doguwar mirror din dake cikin dakin, ina ganin ilahirin jikina tun daga tafin kafata har kaina.
A hankali na kai hannu na shafo shafaffe kuma damammen cikina da yayi kamar ba yanzu na gama dura mishi abinci ba. Saman hancina, kumatuna da kuma kasan habata sun fara fitar da wasu kananun fararen abubuwa, su kuma ba kuraje ba, (blackheads), lokaci zuwa lokaci na kan yi su, amma sai a halin da nake cikin stress, damuwa, ko kuma lokacin sanyi. Sai dai yanzu ba sanyi bane, bana cikin wata damuwa kuma ko stress, saboda haka fitowarsu a fuskata a halin yanzu, abin mamaki ne. Cikin wadannan tunanikan na kammala shiryawa. Na fito da uniform dina da suke a wanke a goge, na saka.
Ina cikin gyara zaman hijabita a jikina, Yaya ya turo kofar dakin ya shigo hannunshi rike da brief case dinshi.
Yace “kin gama shiryawa?”, nace “ehh, nayi zaton har ka tafi ne?”.
Yace “a’ah. Yau direban ba zai shigo da wuri ba, muje in sauke ki ko?”.
Ba musu na dauki jakata na rataya, muka jera ni dashi muka fita. Ya tsaya na rufe kofar dakina, sannan muka wuce. Ina ganin Ameerah tana lekenmu ta tagar dakinta lokacin da muka wuce, Raheemah kuma tana falo a zaune kamar wadda take jiran Yayan.
Da yake yau Ameerah ta fita daga girki, ni kuma na amsa, nasan ba lallai sun hadu ba.
Tana ganin fitowarmu ta tashi tsaye, a tsaitsaye ta amsa gaisuwar dana mata, ta kalleshi, “kasan bikin Haleemo next week ne ko?”.
Ya kalleta cikin nuna alamun rashin damuwa, yace “sai aka yi yaya kuma?”.
Tace “dama ina so ne inje in amso dinkin dana kai mana, daga can kuma zan shiga kasuwa in sayo wasu kayayyaki”.
Ya gyada mata kai, a lokaci daya kuma yana daga kafa ya fara tafiya, “sai kin dawo to!”. Ganin haka nima yasa na bi bayanshi.
Da sauri ta biyo mu, “bani da ko kwandala fa, kuma kudin dinkin da yawa”.
Ya dan dakata, kamar ba zai ce komi ba, kafin yaci gaba da tafiya, “babu cash a hannuna, zan turo miki idan na karasa office”.
Babu godiya kamar wadda ta bashi ajiya, ta juya ta koma ciki, mu kuma muka fita.
Har ya kaini asibiti yanayinshi ba irin wanda ya shigo dashi bane yau da safe duk sai naji na damu. A haka dai ya ajiye ni ya wuce.
Bayan na tashi daga asibitin, na tsaya a wani babban pharmacy anan cikin asibitin. Nayi zarya a wajen tafi sau ashirin, daga karshe dai na tattaro duk wani kwarin gwiwata na shiga ciki. Na sayi abinda zan saya, sannan na wuce gida.
Ina zuwa ko hutawa ban yi ba, na dora musu abincin rana. Ni ko ci ma banyi ba, kankanar dana siya a kofar asibiti, ita na yini ina sha abuna.
Sai dana gama duk abubuwan da zanyi, sannan na fada bandakina na rufo kofar.
Gabadaya jikina rawa yake yi lokacin dana bare ledar teat strip din dana siya a pharmacy, na sakata cikin kwalbar dana dauki sample din fitsarina, na tsaya cikin rawar jiki ina kallon tsinken kamar ina jiran yayi magana.
Ina tsaye, har na kula da canjin da abin yayi. Na dauko shi tare da dubawa.
Ban san lokacin dana koma jikin bangon da nake tsaye ba na jingina. Na kasa yarda da abinda idanuwana suka gani, da gaske? Ya Allah, ko dai mafarki nake yi?.
Ban san iyaka lokacin dana dauka anan ba, har sai dana ji karan turo kofa an shigo dakin, ina jin Yaya yana kwala min kira, amma na kasa motsawa balle in amsa mishi. Daga karshe dai ya turo kofar bandakin ya leko.
Ganina a haka, ya rikice. Da sauri ya saki kofar ya fado bandakin, ya tallabo ni cike da matsananciyar damuwa, “baby, lafiya, me ya faru ne?”. Ya jero min wadannan tambayoyi.
Amma na kasa motsawa har yanzu. A hankali na daga hannuna da yake rike da tsinken awon, na mika mishi.
Ya amsa, fuskarshi dauke da alamun tambaya da mamaki, “menene wannan kuma?”.
“Positive… positive…”, kadai na dinga fada ina nanatawa kamar wani karatu.
Ina ga a hankali ya fara fahimtar abin, saboda daga baya naga ya kamoni yana jijjiga ni cikin zakuwa, “me kike son fada min ne baby? Are you…??!”, muryarshi ta katse ya kasa cewa komi, yayi gyaran murya tare da sake cewa “…cikina? baby…?”.
A hankali na hau daga mishi kai alamun ehh.
Rasa bakin magana yayi, sai kallona daya tsaya yana yi. Mun jima a haka, kafin daga baya ya daga ni sama cak, sai gani ina shawagi a sama yana juya ni. Ban san lokacin da muka fita daga bandakin ba, sai dana ji ni a tsakiyar gadona.
Ya janyoni cikin jikinshi ya kankame, jikinshi yana masifar rawa kamar ana kada mishi mazari, “baby da gaske? Da gaske kina dauke da cikina? Ya Allah, me zan ce maka ni kam? Ya Allah… Ya Allah…”.
Nayi shiru ina saurarenshi yana sambatun godiya ga Allah ina ta murmushi.
Ya dago yana jero min tambayoyi, “me kike so? Me zaki ci? Kina marmarin wani abu? Ki fada min duk abinda kike so baby kinji?”.
Na girgiza mishi kai, “barci nake ji”.
Da sauri ya hau gyara min wajen kwanciya, ya kwantar dani akan gadon tare da sanya bargo ya rufe ni, “kiyi barcinki kinji? Sannu baby na…”.
Ina yada kai akan filo, barci ya dauke ni.
Washegari wayar Janan ce ta tasheni daga barci, daga nan nasan babu wanda bai ji labarin samuwar cikina ba.
Da alama matan nashi kuma basu sani ba. Idan ma sun sani ni ban ga alama ba. A ranar Raheemah ta tafi wajen bikin Haleemoh, sai tayi kusan sati biyu lokacin an gama bikin sannan zata dawo. Gida ya rage daga ni sai Ameerah da Yaya.
Yadda yake lallashina, yana riritani, yana nan-nan dani kamar wata karamar yarinya, Ameerah da kanta ta cafko da wani abu a kasa, da kanta ranar naji tana tambayarshi lafiyata lau kuwa? Shi kuwa yace mata cikine dani. Tunda muke da matar, sai ranar ne naga bacin ranta. Ranar ko dan murmushin yaken data saba yi, kasawa tayi. Da kyar ya iya kakaro sautin “Allah ya raba lafiya”, ta tashi daga wajen da sauri.
Wata tafiya ta kama Yaya zuwa Niamey, wani bincike da aka tura su wajen aikinshi. Da kyar ya iya tafiya ya barni, a cewarshi sai dai mu tafi tare, ni kuma nace mishi a’ah, da kyar dai ya tafi da har yace ya fasa zuwa sai dai wani daga wajen aikin yaje a madadinshi, na dai samu ya tafi da kyar.
Yana barin gidan, itama Ameerah ta janyo akwati ta bar gidan, daga gani dama jiran ya tafi take yi. Gida ya rage sai ni kadai.
*☆⋆44⋆☆*
Satin Yaya daya da tafiya, sai gashi ya dawo. Babu sanarwa kawai sai ganinshi nayi a cikin gidan.
Lokacin ina kwance ma a falonshi, kallo nake yi da plate cike da dambun nama a gabana ina ci, ban ma san lokacin da barci ya dauke ni ba. Ji nayi kawai ana shafa gefen fuskata a hankali.
Na bude idanuna da suka yi nauyi, na sauke su a kanshi a nutse. Mamaki ya kama ni, a yadda muka rabu dashi a jiya ta waya, sai gobe da safe sannan zai dawo. Cikin mamakin na fara kokarin tashi zaune, yayi sauri ya maida ni na koma na kwanta, “uhm uhm koma barcinki abinki, I’ll join you in a bit”.
Sai lokacin na kula da suits din dake jjikinshi da kuma akwatun kayanshi da yake ajiye a gefe, da alama ko daki bai karasa ba.
Ya tashi ya ciccibi akwatinshi ya shige daki. Bayan tafiyarshi kuma sai na kasa komawa barcin, na tashi zaune da kyar ina hamma da mika. Idanuna suka sauka akan agogo, karfe daya na ranar Laraba. Kamata yayi ace Ameerah ce kuwa da girki ranar tunda ranar daya tafi girki ya fita a hannuna.
Na tashi na zauna akan kujerar tare da daukar filo na rungume naci gaba da cin dambun nama na ina kallo.
Zuwa can sai gashi ya fito sanye da kayan hutu, jar rigar T-shirt mai buttons da bai yi buttoning duka maballan ba, ya bar guda biyu na sama, hakan yasa ake iya hango fara kar din singiletin daya sanya daga ciki. Sai ya sanya car-go pants baki, na kuwa daga baki na bishi da kallo cike da burgeni din da yayi.
Zama yayi a gefena yana dan murmushi, “kada dai ace na tashe ki?”.
Na girgiza mishi kai a hankali, idanuna manne da talabijin inda suke nuna film din ‘Gentleman’, “ko kadan, dama can ba wani barci bane. Ya hanya Yaya?”.
Yace “Alhamdulillahi, mun iso lafiya lau, shine kawai”.
Na dan turo baki gaba, “kuma shine baka fada min zaka zo ba?”.
Ya janyo ni cikin jikinshi yana yar dariya, “kada fa kice zaki fara yi min rigima yanzu. Ganin mun gama muhimman abubuwan da suka kaimu, yasa na baro sauran a baya na taho. Na kasa jira har sai gobe kafin in ganki. Ya baby na, baya takura ki dai ko?”. Na girgiza mishi kai.
Yace “yau baki leka asibiti bane? Naga kamar morning kike yi wannan satin ko?”.
Nayi hamma tare da kara komawa cikin jikinshi na langwabe, shi kuwa ya kara rike ni, nace “sister Hanifa taga ina ta layi saboda barci, shine tace in taho gida kawai zata kula min da nawa aikin”.
Ya shafa sumar kaina, “ta kyauta gaskiya, ki tuna min idan muka hadu da ita nan gaba in mata godiya sosai. Wai ina Ameerah ta shiga ne, ko barci take yi? Naji dama tana cewa kwana biyun nan ta cika yin barci”.
Nayi shiru ina muzurai don ban san me ya kamata in ce mishi ba, bana so yaji mutuwar sarki a bakina. Ganin yadda nayi shiru ina kallonshi, yasa ya fara dube-dube kamar wanda yake neman wani abu.
“me ya faru ne? Ko bata jin dadi ne?”.
Naga dai duk wani boye-boyena babu abinda zai sa ko ya hana, Ameerah dai bata gidan, Yaya kuma gashi nan a gidan, idan ma nace zan kareta zata iya karewa in kwana a ciki, tunda babu ranar dawowarta.
Nace “bata fada maka ranar da zata dawo bane?”, Allah ya gani, banyi don in hada su ba, don dai babu yadda za ayi in kaucewa hakan shi yasa.
Yace “ban gane bata fada min ba, ina ta tafi, kuma yaushe?”.
Na dago na kalleshi, haka kawai naji tausayinshi ya ratsa ni. Ban ga amfani, ko dalilin da zai sa haka kawai mata ta bar gidan aurenta ba tare da ta nemi izini daga mijin aurenta ba, akan wane dalili? Kodayake, rashin tsoron Allah yayi karanci a zukatan mutane a yanzu. Rayuwar auren an maidata kamar wata wasan yara, matan aure basa girmama mazajen aurensu. Gani suke yi kamar yan kananun abubuwa kamar tambayar miji zuwa anguwa wani kankanin abu ne. Bayan babbar magana ce, kuma babbar matsala wadda idan muka yi da wasa, zata iya kaimu wuta. Balle kuma, fita unguwa har ki kwana ki wuni a wani waje can daban? Shi mijinki yana can ya bude baki da hanci, yana tunanin ya baro ki a gida a zaune, cikin tsarewar bangon gidan aurenki, ba tare da yasan abinda yake faruwa ba. Ko tunanin yanayin rashin tsaro da wannan duniyar tamu take ciki bata yi, idan ace wata matsala ta samu, misali hatsari ko kidnapping Allah ya kiyaye, me zata ce mishi; me kuma zata cewa Allah?.
Nace “ai kamar tun ranar da ka tafi itama ta tafi, bata dawo ba har yanzu”.
Rubutaccen mamaki ya zanu a fuskar Yaya, ba karami ba kuwa. Bai ce komi ba sai kai da ya girgiza, yace “ok!”. Sai dai daga jin yadda yayi maganar kasan cewa ranshi yayi matukar baci.
Nima ban samu na iya cewa komi ba saboda bani da abin cewar, sai kawai na kara kwanciya a jikinshi. Muka cigaba da kallonmu ni dashi, babu wanda yake iya magana a cikinmu, sai sannu da yake yawan jefo min a duk lokacin da na motsa.
Sai da aka kira sallar La’asar sannan muka tashi, kafin ya fita ya umarceni da in sama mishi abinda zai ci kafin ya dawo. Bayan nayi sallah, na shiga kicin na dafa mishi abinci mai kyau, daya dawo muka ci tare. Shi ya dauko laptop dinshi ya fara aika bayanai akan ayyukan da yaje yi a Niamey, ni kuma na zauna a gefenshi.
Anan ne Maryam ta kira ni daga gida, mun jima muna hira da ita, har su Anty Alawiyya da su Kulsum sai da muka gaisa dasu. Tunda labarin cikin nan ya same su, kusan kullum sai munyi waya dasu, ko su ko Janan. Ummah ma da Yaya kusan kullum muke yin waya dasu, kullum maganarsu daya, yadda zan kula da kaina da dan cikina, abinda ya kamata in ci da wanda bai kamata in ci ba, kulawar da muke samu daga wajensu ni da abinda ke cikin cikina ma kadai ta isheni, balle kuma ta wajen uban gayya, Baban baby na.
Karfe shida ta dan gota na yamma, lokacin da muka ji an shigo cikin falon. Lokacin mun koma kasan carpet din falon, har yanzu Yaya yana fama da rubutu a laptop dinshi, ni kuma nayi matashin kai da cinyarshi. Ayaba ce a gefena ina barewa ina ci, shima idan na ci na kan kai wata bakinshi ya ci.
Ameerah ta shigo da waya sarkale a kunnenta tana amsa kira, hannunta mai rike da wayar rataye da jaka, dayan kuma yana jan karamin trolley.
“… Yanzun nan na shigo gida fa ko daki ban karasa ba. Idan na huta zan kirak…”, ta kasa karasa maganar da zata yi sakamakon ganin Yaya zaune ya zuba mata idanunshi.
Bata san lokacin da wayar hannunta ta zame daga hannun nata ta fadi a tsakiyar dakin ba, tayi sak kamar wadda aka kafe da wani abu a wajen.
Da kyar sautin “baby….!!”, ya fita daga bakinta. Daga ganinta kasan cewa ta rikice, ta kuma tsorata da ganin Yayan a gida.
Yaya yayi zaune very calm and collected, yana kallonta yadda kasan ranshi ba a bace yake ba. Ganin babu wanda yayi yunkurin ce mata kala, yasa ta durkusa ta dauki wayarta data fadi, ta tashi tsaye tana kallonmu fuska dauke da wadataccen murmushi kamar ba ita bace aka kure tayi satar hanya ba. Tace “baby… Banyi zaton cewa yau zaka dawo ba ai, ya hanya? Yaushe ka da…??”.
Yaya yayi saurin katseta ta hanyar cewa, “daga ina kike?”.
Ko kadan bata girgiza da tambayar daya jefo mata ba, tace “kasan cousin dina Mubeenah ko? Kanwar Mommy. To ita ce tazo ganin gida daga Switzerland, na fada maka ai ko?”.
Yaya ya hade fuska iya hadewa, ban taba ganin zallan bacin ranshi irin na yau ba, ko lokacin da muke cikin je-ka-dawo kafin mu shirya kuwa.
Yace “zan kuma iya tuna abinda na fada miki a lokacin, ban yarda ki taka kafa ki bar nan gidan ba, ko ba haka na fada miki ba?”.
Ta wani marairaice fuska kamar karamar yarinya, “amma Baby… Sai dana fada maka fa daddy ne yace inje mu gaisa da ita saboda mun jima bamu hadu ba. Kuma ma, kai da baka gidan, menene a ciki?”.
Ran Yaya ya baci iyaka baci, ya tashi tsaye cike da matsanancin bacin rai, jikinshi har wata rawa yake yi, “akan meye zaki tsallake dokar dana kafa miki kamar wani sa’an wasanki, ko kuma wanda baki dauki maganar shi da mutunci ba, kodayake, dama yaushe kika taba girmama wani abu dana fada miki? Wai saboda Allah, ke nake aure ne ko kuma iyalan gidanku gabadaya?? Kwata-kwata an maida min rayuwar aure wasa, ni da matata, amma ban isa in zauna in gindaya mata sharadi ba tare da an san yadda aka yi, aka yi watsi da lamarin ba? Shin ni din ba mijinki bane? Idan ma baki sani bane, ki san cewa yanzu duk wata hidima da dawainiya da komi naki ya tashi daga hannun iyayenki, ya dawo hannuna. Baki da wani hurumin bin maganar mahaifinki ki tsallake tawa. Amma gabadayanku kun rufe idanunku, kuna abusing kalmar aure, saboda kun dauketa a ba a bakin komi bane ko me? Kin dauka rayuwar auren, abar wasa ce? Rashin sani ne yasa haka ko kuma rashin sanin yakamata??!”.
Ameerah bata iya cewa komi ba saboda yadda taga ran nashi ya baci fiye da tunaninta.
Yaya yaci gaba da cewa, “na gaji da yadda kuke take min rayuwar aure haka nan. Ban isa dake ba, ban isa da komi naki ba. Saboda haka daga yau a gidannan, zaki zaba, umarnina ko kuma na mahaifinki? Idan har kin ce ba zaki bi umarnina ba, to tun kafin tafiya tayi nisa, ki koma inda kika fito. Idan kuma kin shirya yin zaman rayuwar aure kamar yadda yakamata, to daga yau sai yau, ban yarda ki taka kofar gida ba tare da kin nemi izinina ba Ameerah idan kuwa har hakan ta sake faruwa, duk abinda ya biyo baya, ki zargi kanki!. Zabi ya rage naki!”.
Ya hada kan kayanshi ya wuce daki a fusace.
A hankali ta duka ta janyo akwatinta ta shigo cikin falon sosai, na mata sannu da zuwa, bata amsa ba, sai ma la’adar harara da nasha. Taja akwatinta ta wuce dakinta kamar tashin duniya, na bita da kallo cikin tabe baki. Meye laifina anan, ni da bani na kar zomon ba? Na sake tabe wani bakin.
Yaya bai fito ba sai da aka kira sallar magriba.
Kiri-kiri yaki cin abincin data dafa ranar, a gabanta ya kira wata hadaddiyar restaurant ‘cloirassantz’ daya saba yi mana odar abubuwan tande-tande, yayi placing order aka kawo mishi abinci, ya zauna yaci kayanshi ya wuce daki abinshi.
Washegari ina daki ina shirin fita ya leko dakin, na gaida shi. Yace min idan na dawo inyi girki, in kuma cigaba da yi har sai shi da kanshi yace min in ajiye. Ban iya cewa komi ba sai ‘to’, na kula hukuntata yake so yayi tun karfinshi.
Ban sanya bakina cikin fadansu ba, ko tambayarshi dalilinshi na damka min girki gabadaya ban yi ba.
Kwana biyu suna ta fadansu, fadan masoya hutu, ban san ta yadda ta samu ta shawo kanshi ba, naga dai sun koma sun dinke kamar tif da taya, nan ma ban ce komi ba, na damka mata girki taci gaba da yi.
Ya karbe motar hannunta yace ta maidata gida, ya kuma hanata yawan fita gatsar, dokoki sosai ya kafa mata, duk tace taji ta amince.
A haka Raheemah ta dawo muka cigaba da bugawa dai. Ta kawo mana souvenirs na bikin, ga hoton Haleemo nan da Umar ya sha uniform dinsu na sojoji radam a jikin komi, memo ne, jaka ce, calender ce, kai tarkace dai. Lokacin data bani, dariya nayi tare da musu fatan alkhairi na kai daki na ajiye. Ko tayi tsammanin haushi zan ji ko kishi??.
*
Cikin jikina yana ta tasawa cikin koshin lafiya, yanzu yana cikin satikan shi na goma sha daya.
Har yanzu muna cigaba da gwabzawa da matan Yaya, duk da cewa yanzu da Ameerah muke yi. Raheemah sam yanzu ba na ta tata, fada ne, bana biye mata.
Wata tsirfa data dauko ma sabuwa, haka zaka ganta a dakin Yaya ranar girkina tun da safe, ta kuma ci kwalliya ba ta wasa ba. Har magana sai da na yiwa Yaya akan haka, nace ya daina biye mata suna yin haka, suna shiga hakkin mai yin girki.
Amma maimakon yace wani abu, sai yayi dariya, wai “menene abin shiga hakki anan Baby? Mu da babu abinda muke yi sai hira kawai? Idan kika tafi yin girki, kadaici yana damuna, kinga tana taya ni dauke kadaicin”.
Da naga dai bashi da niyar daukar mataki, sai na gyada kai nace “to babu laifi”.
Da ranar girkinta ta zagayo, sai naci kwalliyata ta gani ta fada da safe, English wears mini skirt da wata vest, na gyara gashin kaina ranar ko hula ban saka ba, na yiwa dakin Yaya tsinke. Na samu gefen gado nayi daya kan daya, har tazo ta sameni anan, abin ya bata mamaki, amma bata yi magana ba.
Da dare ma da ya dawo haka ta faru, naje na musu zaune har dare ya tsala yadda ta saba yi min.
Zuwa karfe goma ta wani tashi tana mika, cibiyarta tana nunawa ta cikin half vest din data saka, tana wani fari da idanu da rangwada, tace “baby, muje mu kwanta ko?”.
Yaya da yake shan dariyar hirar da nake mishi akan kiriniyar dasu Auwal suka sha lokacin da suna yara, ya kalleta yace “kiyi gaba, gani nan”.
Ta turo baki cikin jin haushi, amma bata ce komi ba, ta shige uwar daka.
Muka kuwa cigaba da hirarmu, har sai da ta sake lekowa ta mishi magana, wai ai ita ta kasa yin barci saboda baya kusa da ita, lokacin karfe sha daya ta kusa.
Ina dariyar mugunta a ciki, nace “Yaya kaje ka kwanta mana, kasan fa gobe akwai aiki”.
Yace “ke fa?”.
Na girgiza kai, “bana jin barci, kaje ka kwanta abinka, idan na gama barcina zan je in kwanta. Sai da safe…”, na dan juya ina kallon Ameerah da take tsaye a jikin kofa har lokacin, nace “sai da safe Anty Ameerah!”.
Ta hadiye wani yawu da nafi kyautata zaton na takaici ne da bakin ciki tace “Allah ya tashe mu lafiya”, ta juya cikin dakin. Yaya ya bani peck a kumatu tare da dukawa ya shafa cikina, sannan ya min sai da safe ya bi bayan matarshi. Na bishi da kallo ina murmushin mugunta. Matarshi tayi tsamnanin taci bulus ne? Ashe kuwa tana da sauran aiki a gabanta, domin kuwa ba’a buga irin wannan wasan da ni.
Washegari ma abinda ya faru kenan, hakan kuma yaci gaba da faruwa na wani dan lokaci.
Ranar Alhamis girki a hannuna yake. Tun da na dawo daga wajen aiki, nake shirya abincin dare. Dambun shinkafa nayi, mai kyau, na yanka hanta, carrots, kabeji, da sauran tarkacen veggies a ciki. Nayi sauce itama da na wadatata da su nama da kifi. Nayi lemun kankana da lemun zaki wanda na dan diga lemun tsami da zuma a ciki.
Lokacin dana gama girkin, yamma tayi. Don haka na bar miyar akan wuta domin ta karasa yi, na tafi dakina inyi wanka.
Ina cikin yin wankan naji dawowar Yaya daga wajen aiki, jin ina yin wanka yasa ya wuce dakinshi.
Daga bandakin na dauro alwala saboda lokacin sallah yayi. Na koma duba miyar, na ga har yanzu da sauran ruwa a cikinta, abin ya bani mamaki kwarai. Zan iya rantsewa akan cewa ruwan da na bari dazu bai kai haka yawa ba. Amma sai ban kawo komi a cikin raina ba, na kara rage wutar na koma daki domin inyi sallah.
Ina kan abin sallar, Yaya ya dawo daga masallaci, daga ganinshi kai tsaye dakina ya shigo. Na dago ina kallonshi cikin murmushi, “baby abinci… Abinci baby…”. Ya fada a dan gaggauce, ya juya ya fita.
Na tashi tsaye ina dan murmushi, wato yau da yunwa ya dawo kenan. Na cire hijabin jikina na tafi kicin da niyar zuba mishi abincin.
Miyar dazu, ta koma kamar miyar tanade, ruwa tsululu kamar lokacin na fara dafa ta. Ban san lokacin da naji kwalla ta cika min idanu ba, na maida murfin tukunyar na rufe tare da kashe gas din. Na jingina da counter din kicin ina tunanin abu mai sauki da zan dafawa Yaya wanda ba zai dauki lokaci ba, sai dai duk abinda nayi tunani, sai in ga sam ba zai yiwu ba. Gabadaya duk wata idea ta dauke min, daga karshe dai na yanke shawarar kai mishi dambun a haka, tunda akwai komi a ciki, har maggi da mai sai dana saka a ciki, dama miyar don dai garnishing ne kawai.
Na ciccibi kayan na tafi falon Yaya dasu.
Tunda na fara zuba mishi yake kallona yana murmushi kwanannan abinda yake min kenan, idan na mishi magana yace ai cikin jikina ya canza ni ne shi yasa. Na tura mishi plate din gabanshi tare da tsiyaya mishi lemun a cikin kofi.
Ya ja plate din gabanshi, “yau kuma a haka zamu ci dambun?”. Ya tambaya cikin alamun tsokana.
Na dan yi murmushi cike da fargaba, “uhmm, wani lokacin komi yana bukatar canji ai”.
Yace “haka ne baby na”. Yayi bismillah tare da kai cokalin farko bakinshi, take yanayin fuskarshi ya canza, da kyar ya hadiya. Naji gabana ya fadi cikin fargaba, nace “me ya faru?”. Ban jira ya amsa ba na dauki cokali na kai bakina, yaji ya fara ziyartata kafin wani masifaffen gishiri mai rikita kwalwa ya biyo baya. Da sauri na kai lemun dana zuba mishi cikin bakina da niyar kora abincin dashi, domin ba zan iya hadiya shi ba. Nan kuma wani matsanancin tsamin lemun tsami daya min bismillah.
Ban san na tara kwalla a cikin idanuna ba, sai dana ji tana bin kumatuna. Da sauri Yaya ya kai hannu yana dauke min kwallar, yace “menene abin kuka kuma? Kada ki damu kanki, girki ai ya gaji haka. Bari yanzu in aika a sayo mana wani abincin”.
Ban ce mishi komi ba, naci gaba da share kwallata. Yanzu duk wahalar wannan da naci ta tashi a banza kenan? Babu abin ban haushi da takaici ga matar aure, ace mijinta bai ci abincinta ba ya tafi neman na waje yaci.
Cikin kwallar da nake yi, nace “a’ah, bari in shiga in yi wani abu mai sauki”.
Yace “inaa, ba zaki wahalar min da baby ba. Baki ji ance miki ba’a son ki cika yin aikin wahala ba? Maza daina kukan, kada ki sanya min baby kuka”.
Duk yadda yaso inyi shiru, abin gagara yayi. Har aka kira sallah ya koma masallaci, raina a jagule yake.
Daya dawo sai gashi da ledar take away, har daki ya kaiwa kowa nata. Daya kawo min nawa ko kallonshi banyi ba saboda masifar bacin rai. Allah ya isa kadai nake ja ina karawa a cikin raina.
Muna zaune yana cin nashi abincin, nawa kuma yana gefe, sai ga Raheemah ta shigo falon. Ta kallemu ta tabe baki, “uhhum! Su yan gaban goshi masu juna biyu manya, wato yanzu abincin ma an daina yi sai dai a tafi a siyo na waje? Kwarai kuwa, Allah muma ya azurtamu da namu cikin dai!”.
Kwata-kwata yau bana cikin jin zama in saurari korafe-korafen data saba, don haka na mike na wuce dakina, ban san yadda suka kare da ita ba. Sai wajen karfe goma sannan naje na kwashe kayan da muka bari. Ranar haka na kwanta zuciya a cunkushe.
Cikin dare fa barci ya gagareni, yunwa kamar zata kashe ni. Allah yasa na sanya abincin da Yaya ya kawo min cikin microwave, na zame jikina daga na Yaya a hankali na fita daga dakin. Kusan karfe biyu da rabi na dare lokacin. Shiru gidan, baka jin motsin komi.
Na shiga kicin, maimakon in kunna wuta, sai nayi amfani da hasken fitilar wayata. Na kunna microwave din, na koma falo na zauna akan dinning ina jiran abincin ya dumama. Fitilar na kashe, naci gaba da zama a cikin duhu, a zuciyata ina ta saka da warwara akan wannan sabuwar matsala data tunkaro ni.
Zato zunubi, amma da sai ince ga wadda ta aikata min wannan danyen aiki, sai dai shi zargi bashi da kyau. Kawai dai yanzu zan dinga yin takatsantsan ranar girkina kawai, shine mafita.
A hankali naji an turo kofar daki an fito, na daga kaina daga zuzzurfan tunanin dana fada. Raheemah ta fito itama tana haska fitilar wayarta tana taku sadaf-sadaf kamar barauniya, ganin ta wuce kicin kai tsaye yasa na dan yi murmushi. Da alama itama yunwar ce ta korota.
Ban yi motsin kirki ba balle ta ganni, na kara yin kasa da kaina ina wasa da yatsun hannuna.
Dare da baya raina abin ji komi kankantarshi, duk wani dan karamin motsi da zata yi ina jin shi, zuwa can naji tashin murya kasa-kasa alamun tana waya, hatta da daya bangaren data kira ina ji.
Cikin barci wadda ta kira din ta fara cewa, “ke wani irin shashanci ne haka zaki wani hau kiran mutane da tsakiyar daren wannan?”.
Tayi kasa da muryarta sosai, “Momcy, na manta yadda zan sanya wannan maganin ne. Kin san kuma Malam yace idan ya wuce yau ba zai yi amfani ba”.
Na zare idanu sosai, amma sai na kara lafewa ina sauraronta.
Sai da tayi hamma sannan tace “wanne daga ciki? Na turaren ko kuma na ci?”.
Tace “na ci dai, ai na riga nayi na turaren tun yaushe…”, ta ja dan tsaki, “… amma ni har yanzu ban ga yayi wani abu ba, anya kuwa ba asarar kudi kawai muka sake yi ba?”.
Tace “ina, shi mai nema ai baya gajiya. Ba zamu gajiya ba, balle ina da tabbacin wannan din zai yi. Kin san fa aikin malamin nan kamar yankan wuka, kin dai ga irin aikin da yawa Halima. Ke kanki ba da taimakonshi bane kika shigo gidan ba?”.
Tace “haka ne, kawai naga kwata-kwata aikin baya yi ne yan kwanakin nan. Duk inda muka je sai dai suyi ta cinye mana kudi. Shima wanda nake zuba mishi a abinci fa har ya kare, amma kinga har yanzu shiru kamar an shuka dusa. Bai sallameta ba, bai juya mata baya ba kamar yadda suka ce. Ranar nan ma fa har tambayata yayi me yasa abincin yake wani warin magunguna? Nace mishi maggi ne. Kada fa mu je ya cafko mu Momcy”.
Tace “ke ja can matsoraciyar banza da ta wofi!! Dan ubanki ke har kin fara sarewa tun kafin aje ko’ina? To arr dinki, ni cikin yayana babu matsorata wallahi, ki kiyaye ni. Kina ganin idan kika zauna a gidan wannan tsakanin wadannan matan nashi, zaki ganu? Shi komi ba dan hakuri bane? Da sannu, su duka zamu yi waje dasu. Yanzu abinda zamu kokarta muyi shine mu ga cewa mun karkato da hankalinshi kanki tukun. Yanzu kije ki zuba maganin a cikin danyen nama, ya kwana, gobe ki soya shi ki mishi girki yaci, zaki ga abin mamaki. Amma kada ki kuskura ki kara bari inji kalmar karaya ta fita daga bakinki, kina jina?”.
Cikin sanyin jiki tace “ehh Momcy”.
Tace “to madallah, maza je kiyi aikin gabanki”. Ta kashe wayar.
Na dafe kai da baki a lokaci guda. Kaji fa wata irin tabewar basira. Kai Allah dai ya kara rufa mana asiri, ya kuma sa mu dace.
Ban damu da cewa har yanzu tana cikin kicin din ba, na tashi nima na shiga kicin din. Wutar kicin din na kunna haske ya bayyana, daidai lokacin tana maida danyen nama cikin firjin. Da sauri, kuma a tsorace ta maida firjin din ta rufe, ta juyo tana kallona cikin zare idanu. Ban ce mata komi ba, na bude microwave na ciro abincin ciki, na koma kan dinning na zauna na fara ci.
Ta zo ta wuce ni cikin sanyin jiki kamar kazar da kwai ya fashewa a jiki, tana yi tana satar kallona.
Nima a sanyaye na fara cin abincin hankalina ya kasu gida-gida, har na rasa da wanne zan ji. Da alama sai na kara zagewa da addu’a ba akan kaina kadai ba, har shi Yayan.
Ina gama cin abincin, na je na dauke gabadaya naman dake cikin fridge na zubar. Na koma dakin Yaya. Bandaki na shiga na dauro alwala na fito na fuskanci alkibla ina jero nafilfili.
Washegari da safe ba sai aka maimaita yar gidan jiya ba? Na hadawa Yaya abincinshi na kari ya fara ci cikin nutsuwa, ya kai shayin dana hada mishi, kawai naji ya furzar dashi, a dan zafafe yace “meye haka Na’ilah?”.
Daga farko tsananin mamakin ya kirani da Na’ilah ne ya kama ni, kafin mamakin abinda ya faru da shayin ya biyo baya. Bai ma tsaya yi min karin bayani ba, ya tashi ya bar wajen. Ina nan zaune cikin rashin sanin abin yi, sai gashi ya fito dauke da brief case dinshi, da kyar ya iya cewa “sai na dawo”. A Karo na farko, ranar ya fita ba cikin rakiyata ba, kuma cikin rashin dadin rai.
Sai daga baya na fahimci cewa, robar sugar aka juye gabadaya aka zuba gishiri. Wannan karon ma kadan ya hana ni inyi kuka.
Saboda haka da girki ya sake dawowa kaina, na dinga bin kwakkwafi. Idan na shiga kicin, bana lekawa ko nan da can har sai na gama girkina, idan kuma na gama, tunda nasan na Yaya ne ake hari, sai in shige daki dashi in kulle har sai ya dawo. Duk da nasan cewa da gangan ake min haka, amma ban shirya neman kowacece ba, bani kuma da zuciyar ramawa. Nasan cewa dai, rana dubu ta barawo ce, daya kuma ta mai kaya.
*
Yau da yake ba ranar girkina bace, kuma ina off saboda evening duty dana gama, ban fito daga daki ba sai karfe biyu na rana. Yau da su kayan marmari ma na karya. Kwana biyu yanzu mangawaro kawai nake sha kamar babu gobe, kullum sai in sha fiye da guda biyar.
Yanzu ma abinda ya fiddo ni waje kenan, saboda mangwaron dakina ya kare ne. Yaya da zai fita yace za’a kawo wani.
Ina shiga kicin kuwa, na ganshi an kawo shi har kwali guda. Wani irin dadi ya ziyarceni. Na dauki guda biyu manya masu kyau, na wanke su na yanka. Ina cikin yi, Raheemah da take yin girki ranar ta shigo. Tunda abin nan ya faru, kusan sati daya kenan, bata ko yarda mu hada idanu da ita. Ko hira suke yi, idan taga na shigo waje, haka zaka ji tayi shiru ko ta ma tashi ta bar wajen.
Sannu kawai na mata ciki-ciki, na dauki mangwarona na koma daki.
Na zauna na tada mangwaron nan tas, na bi da ruwa mai sanyi.
Komawa nayi na kwanta naci gaba da barcina.
Wajen karfe hudu, wani irin masifaffen ciwon ciki ya tado ni daga barcin da nake yi.
Na tashi na fara murkususu. Tun ina yi akan gado, har na fado kasan carpet. Gabadaya ciwon ya gigitani, ban taba jin azababben ciwo irin wannan ba.
Da kyar na iya lalubo wayata na kira Yaya, yana dauka ya fara tambayar lafiya? Saboda yasan ban cika kiranshi idan ya tafi wajen aiki ba, musamman ma ranar da ba girkina ba. Ban iya mishi magana ba, sai gurnanin ciwo kawai daya dinga fita daga bakina. Nan da nan ya rikice, yace gashi nan zuwa.
Ina jin lema tana fita daga jikina, amma bani da kuzarin daga kai in ga ko menene. Ban ma san lokacin da Yaya ya dawo ba saboda hankalina ya gushe daga jikina.
Lokacin dana dawo cikin hayyacina, tuni cikin jikina ya zube.
Lokacin da wata likita daga cikin likitocin asibitinmu ta isar min da wannan sako, dauka nayi mafarki nake yi.
Sai da naga Yaya ya shigo, jiki babu kuzari, fuska very defeated, kawai na saki kuka ina jan Innalillahi…
Dr. Anita ta matso ta dafa kafadata tana lallashina har na dan nutsu nayi shiru, nasiha ta dinga yi min mai shiga cikin jiki da nuna min hakan ikon Allah ne, shi ya bamu shi dama tun farko, tunda kuma ya dauke kayanshi ba sai muyi hakuri ba. Sai da taga na daina kukan, sannan ta juya wajen Yaya shima ta mishi jaje, sannan ta barmu ni dashi.
Muna hada ido da Yaya, na sake barkewa da wani kukan. Ja na yayi cikin jikinshi kawai yayi yana shafa gadon bayana har sai da nayi mai isata, sannan ya dago kaina. Shi kanshi idanunshi sun kada sunyi jawur kamar wanda zai fashe da kukan. Nasan karfin hali kawai da jarumta irin ta namiji ce yake yi.
Ya taimaka min na tashi zaune saboda jikina babu karfi, likita tace ya bani abu mai ruwa in sha, a bani magani, amma sam na kasa cin komi. Sai da yayi kamar zai min kuka sannan na samu na dan kurbi yoghurt din daya kawo min. Ya bani maganin na sha.
Komawa nayi na kwanta, shi kuma ya zauna a gefena ya kamo hannuwana cikin nashi ya damke, wasu zafafan hawaye suke ta zirya akan kumatuna. Ya sanya hannu yana dauke min hawayen, cikin sanyin da muryarshi tayi, yake bani hakuri, yana kara yi min tuni akan yarda da kaddara.
Da alama maganin da aka bani har da na barci. Saboda ba’a jima ba barci mai nauyi ya daukeni.
Ban tashi ba sai washegari da safe. Ina bude ido, naga Janan zaune a gefena. Ban san lokacin da tazo ba, nan na sake bude wani shafin kukan tana aikin lallashi. Daga karshe nayi shiru, ta taimaka min na shiga bandaki nayi wanka. Na fito ta bani abinci na karya, na sha magunguna.
Tace Yaya ya zo da safe, yace zai kirani a waya saboda ana nemanshi a office ne, kai kawai na iya gyada mata.
Wajen karfe goma kuwa ya kira ni, na dauka muka gaisa. Dole na ware muryata sosai saboda kada ya karanci damuwar dake nake ciki. Nasan na kwallafa raina akan cikin jikina, amma Yaya ya fi ni. Tafiyar da yayi zuwa Niamey, haka ya dawo da kayan wasan yara kala-kala. Daki guda ya ware, yanzu ya kusa cika da kayan wasan yara dana sanyawa.
Ya tambayeni saukin jikina, nace mishi naji sauki. Nan muka dan sha hira dashi kafin muka kashe wayoyin da alkawarin zai sake kirana idan aka jima.
Yinin ranar cikin amsar waya da mutane yan dubiya muke, har yanzu na kasa yarda da cewa babu cikin jikina, amma idan na tuno hakan yana daga cikin kaddarar Allah, sai in kwantar da hankalina.
Matan Yaya ma sun leko zuwa rana, da dai-daya ma suka zo. Sai da Ameerah tazo ta tafi sannan Raheemah ta zo.
Zuwa can yamma, na dan warware daga jiki har zuci. Likitar data duba ni jiya, ta shigo ta sake duba jikina. Bayan yan tambayoyi data min na amsa, ta tabbatar min da cewa zuwa nan da kwana biyu ma zasu iya sallamata. Nace mata nagode.
Tace “amma barinki ya bani mamaki Nailah (haka yawancin mutanen asibitin suke furta sunana saboda basu iyawa), last time da kika zo muka duba ki, komi lafiya lau daga ke har dan cikinki, ba kwa fuskantar wata barazana. Kin tabbatar baki ci, ko sha wani abu da zai fitar da cikinki ta karfi ba? Saboda daga yanayin abin kamar da karfi cikin ya fita”.
Na girgiza mata kai a hankali, nace “kawai dai kaddara ce Allah ya aiko”.
Ta girgiza kai cikin nuna fahimta, “haka ne, Allah ya mayar miki da mafi alkhairi. Ki kwantar da hankalinki fa kinji? Kada ki sanyawa kanki damuwa”.
Na sake mata godiya, ta mana sallama ta fita.
Tana fita Janan tayo kaina da tambayoyi, nace “ni fa bana son wani tada rigima da maganganu. Idan ma wani abin ne, Janan ina da shaida ne? Koma menene, mutum ai kanshi ya yiwa. Don Allah kada ki bari ma Yaya yaji wannan maganar, Allah kadai yasan abinda zai yi akai. Ni na barwa Allah komi, na kuma yarda babu abinda yake faruwa face cikin yarda da izininsa. Don haka ki manta da maganar kawai”.
Ta rausayar da kanta gefe guda, “to shikenan ai tunda haka kika ce. Zaki ci abinci?”.
Ta watso min tambayar tana nufar kulolin dake ajiye a wajen wadanda yawanci abokan aikina ne na nan suka kawo min su, nasan duk don ta dauke hankalina daga kan zancen ne. Murmushi kawai nayi na gyada mata kai.
[Hello there! 😽].
*☆⋆45⋆☆*
Kwana na biyu ina hutawa a gadon asibiti. Bayan an tabbatar da lafiyata da komi, aka sallamomu muka koma gida. A ranar Janan ta koma Kaduna ina ta mata godiya.
Sai dana kara kwanaki uku ina kara hutawa, sannan na koma bakin aikina na kuma karbi girki. Rayuwa ta koma normal, mun maida komai bayanmu mun fuskanci gabanmu.
Zaune muke gabadayanmu a falon Yaya da misalin karfe tara na dare. Yanzu har Raheemah ta kan fito ayi hira da ita, kafin dare yayi kowa ya nemi makwancinsa kuma.
Na fahimci Yaya a mutum mai son karfafa zumunci da son kusanci ga iyalinshi, hakan yana kara min girmanshi da kimarshi da nake gani a cikin idanuna. Duk da cewa ta fanninsu, ba hakan suke so ba.
Na tashi na shiga kicin, fruit salad din dana hada yayi sanyi karara, na dauko forks guda hudu, na koma falon. A tsakiyarmu na ajiyeshi tare da ajiye cokulan masu yatsu, muka fara shan fruits din aka kuma cigaba da hira. Sai dai hirar kamar kowacce tata kawai take yi, idan Yaya yana hira da daya, baka ji biyun sun sanya baki sai dai su kalli TV ko kuma suyi shiru da bakinsu. Duk yadda yaso ya saka mu cikin hirar gabadaya abin gagara yayi, idan ma ya sanya bakin wata a cikin hirar ta danyi magana, sai ita dayar kuma tayi kim da baki, sai ta jira sun gama hirar sannan ta sako wata. Abin gwanin ban dariya, na dai yi ta kokarin makale tawa a ciki.
Duk da cewa a hakan ma ba karamin kokari yayi ba, tun da yanzu har mu kan zauna mu duka a waje daya ba tare da kaji kananan maganganu suna tashi ba. A ganina hakan kamar an fara daukar matakin farko kenan wajen hade kai.
Sai dai, tunda na dawo daga asibiti, wani shiru da matan suka yi su duka, yanzu babu bataccen girki idan nayi, Ameerah ta daina shiga dakin Yaya tunda safe, haka ita kanta Raheemah ta daina wannan yawan mitar tata. Jikina kawai yana bani ba daidai ba. Sai inji kamar shirun nan nasu, ‘silence before the storm’ ne.
Ko kuwa sun fara shiryuwa ne??.
Kadan-kadan Ameerah ta fara yatsina fuska, tun ana yi babu wanda ya kula har Yaya ya lura, ya kalleta cike da alamar tambaya, “lafiya, baki jin dadi ne?”.
Duk sai muka juya hankulanmu kansu.
Ta girgiza kai a hankali, “cikina nake ji yana juyawa… Kamar zanyi amai…”.
Tana rufe baki, ta tashi a sukwane tayi dakin Yaya, mu duka ukun muka tsaya muna kallon-kallo, kafin muka tashi da sauri muka bi bayanta.
Tana cikin bandaki tana ta kakarin amai, Yaya ya matsa da sauri ya tattagota suka dawo dakin, daga shi har mu sannu muke jera mata wanda take amsawa cikin jan numfashi. Muka rankaya muka koma falo muka zauna.
Muna zama ta fara wani kakarin da yatsina fuska, Yaya yace “wai wani abu yana damunki ne?”.
Tana daga baki, sai cewa tayi, “ai ita warin kankana ne yake tada mata hankali”.
Na daga girata sama cikin tsananin mamaki, Raheemah kam sai ta kama baki. Yaya yace in dauke farantin in maida kicin tunda mun gama shan fruits din. Ban ce komi ba na dauke kayan, a raina ina nanata ikon Allah kenan mai rike zariyar wando.
Na koma muka cigaba da hirarmu, har lokacin kwanciya barci yayi duk muka tashi. Na koma dakina nayi shirin barci, na koma dakin Yaya.
Cikin dare kawai sai karan waya muka ji, Ameerah ce wai cikinta ya dameta da ciwo. Nan muka nufi dakinta muka sameta tana ta birgima akan gado. Yaya yace min “ko kina da maganin ciwon ciki ne ki bata ta sha?”.
Nan na koma daki na lalubo maganin boskafone na koma dakin bayan na biya ta kicin na dauko ruwa mara sanyi.
Nan na sameta kwance shame-shame a jikin Yaya. Ban ce musu komi ba, na mika mishi maganin, ya tallafo kanta zai bata maganin, nan tayi fir tace ba zata sha ba.
Yaya ya fara aikin lallashi, amma ta kafe.
Cikin nuna alamun gajiya da halinta yace “kinsan ba neman magani kike yi ba, zaki tado ni da tsakiyar wannan daren, idan ba zaki sha maganin ba zan tafi in kyaleki yanzu wallahi”.
Sannan fa ta karba ta sha. Har wajen karfe hudu na dare muna kanta. Ni naki tafiya daki duk da sai da Yaya yace in tafi, ban san ko ciwon gaske take yi ko na karya ba. Sai da aka fara kiran assalatu sannan barci ya dauketa. Sai lokacin muka koma daki.
Bayan kwana biyu da yin haka, sai gata wai taje likita ya aunata ance tana da ciki. Nan suka hau murnarsu ita da Yaya, na bisu da addu’ar Allah ya raba lafiya. Wani abin mamakin shine, yanayinta sam bai yi kama dana masu ciki ba. Yadda take da, haka take yanzu, babu canjin komi a tattare da ita. Hakan yasa na fara tunanin anya ba cikin karya bane ba kuwa? Sai dai a yadda Yaya yake ta doki da rawar jiki akan cikin wannan, nasan ko giyar wake na sha ba zan fito in ce mishi ga abinda ake ciki ba. Don haka na kawo idanu na zuba musu, koma dai menene, nasan it’s only a matter of time, zamu ga ciki dai ya bayyana ai ko?.
Ranar nan ina jinsu ita da Raheemah suna gabzawa, ranar Adi tazo gidan ta wuni, a cewarsu itama ta samu wani house of rep dake zaune anan Abujar har an sanya musu ranar aure. Ina tunanin Adin ce ta fada mata kamar ba cikine da Ameerah ba.
Sai gata ta tsareta a kicin, ta kare mata zagi tas, tace “kuma idan karyar cikine zamu zuba ni da mutum anan gidan mu gani. Haba, biri yayi kama da mutum! Ke da kike da ciki, maimakon ki dinga yin kiba ko rama, amma kina nan a yadda kike? To wallahi mu zuba don uban mutum, zamu ga karshen karya!”.
Ta fita daga kicin din ta bar Ameerah tana ihun “tunda ita take bada cikin, ta riga ta san babu shi, ba sai ta fadawa Yayan ba?”.
Ban ce musu komi ba ni kam sai kai dana dinga girgizawa. Su dai suka sani ai.
Ranar assabar a Kaduna na wuni, Yaya zai shigo su gaisa dasu Ummah, don haka nima na biyo shi. A gidan su Ummahn muka fara sauka, duk da sunyi murna da ganina, hakan bai hana su min fadan mai ya kaini fara yawo yanzu ba, jikina har yayi karfin da zan fara yawo ne? Nace musu lafiyata lau, na warke.
Bayan mun gaisa dasu na huta, na tafi gidan Janan. Nan muka wuni muna hira da hirar yaushe gamo.
Lokacin dana mata zancen cikin Ameerah, dariya ta dinga kyalkyalawa har sai data kifa daga kan kujera. Na bita da kallo ina dan murmushi duk da bansan akan meye take dariyar ba. Sai data yi ta isheta, sannan ta dago idanu taf da hawaye don dariya, tace “yanzu kuma Yaya ya yarda da wannan crap din??”.
Nace “me zai hana shi yarda?”.
Tace “haba, tun yaushe suke zarya wajen likitoci ana cewa kwayoyin haihuwarta basu da kwari? Wace kasa ce basu je ba akan wannan matsalar amma magana daya, ba zata iya conceiving ba. Kila dai Yaya mantawa yayi, ko kuma tsabar son yara ne yasa idanunshi suka rufe. Amma daga ma jin labarin da kika bani, ko rantsuwa nayi nasan ba zata taba ci na ba, cikin karya ne!”.
Nayi shiru ina processing abinda tace, daga karshe na daga kafada, nace “kika san ko Allah ne ya dubeta da rahamar shi? Shi ikon Allah ai yawa ne dashi. Idan ma ba hakan bane, wannan matsalarta ce, ina zaune a gefe daya koma menene zai bayyana. Shi ciki ai ba’a boye sa, dole zai fito kowa ya gani”.
Janan ta gyada kai, “haka ne kam. Allah dai ya rufa mana asiri bakidayanmu”. Nace “ameen”.
Da yamma da Yaya ya gama ziyararshi, ya biyo muka juya bayan sun gaisa da Janan da mijinta Almustapha. Ashe har Zaria yaje, sai a hanya yake fada min.
Kafin mu karasa gida sai da muka biya wani fast food joint, ya sai roll cakes, tarkacen hamburger, ice creams dasu chocolate, sakon Ameerah. Muna komawa na kwashi kasona na fada daki saboda girkin Ameerah ne ranar. Sai ya zama wadannan su muka ci abinci matsayin abincin dare, saboda apparently bata da karfin yin girki ranar.
Sai abin yazo ya zama kamar al’ada Yawancin ranakun girkinta sai dai Yaya yayo odar abinci.
Nace mishi me zai sa maimakon yayi ta asarar kudi wajen siyo abinci, mu dinga girka kayanmu duk ranar da taji ba zata iya yin girki ba? Sai cewa yayi idan aka yi hakan, za’a bata mishi tsari da dokar gidanshi. Da na matsa, sai yayi kici-kicin da rai, yace “wai idan ma na batar da kudin, kudina ne ko naki?”.
Mamaki ya kama ni, na kama baki nace “daga maganar gaskiya? To Allah ya baka hakuri!”. Na tashi na koma dakina.
Can kuma sai gashi ya biyo bayana, wai inyi hakuri, kawai yaga yana kokarin dauke mana wahala ne amma kamar bamu gani, maimakon mu mishi godiya, sai mu hau korafi, waye da waye, nan ma dai na kara bashi hakuri aka wuce wajen.
To rayuwar fa kenan, yau dadi, gobe akasinsa.
Kamar yadda duk kokarin mutum wajen kaucewa kaddarar data riga fata, duk gudunka da fata da burinka, baka da wani katabus akan abinda Allah ya kaddara. Shi yasa ita yarda da kaddara take da matukar kyau. Ko babu komi, kowani irin abu ne ya kan zo wa wanda ya yarda babu abinda yake faruwa a doron kasa face da izinin Allah, da sauki.
Gabadaya yinin yau a kasalance nayi shi, tunda na tashi da safiyar yau nake ji na ba daidai ba. Jikina yayi min nauyi, da kyar na dinga gudanar da ayyukan dana saba yi.
Zuwa yamma, abin ya kara tsanani da kamari. Ina zaune ina yin azkar din dana saba yi, idanuna suna likewa saboda wani azababben barci daya mamaye min idanu. Duk yadda naso in daurewa barcin nan, kasawa nayi. Ban san lokacin daya kwasheni ba anan.
Sai gab da magriba na tashi a firgice. Nayi salati ina jan addu’o’i a cikin raina, ban saba barcin yamma ba, kai barcin rana ma gabadaya ban cika yin shi ba, balle na bayan sallar la’asar.
Mutuwar jikina har tafi ta dazu, na lallaba na fada bandaki nayi wanka da ruwan dumi. Kasancewar bana yin sallah, sai na gyada jikina kawai na fito.
Washegari, na shiga gaida Yaya. Yana zaune a falonshi, matan nashi sun zagaye shi yana karin safe. Ameerah da har yanzu ciki bai fara turowa ba, an ci kwalliya ta kece raini, fuskarnan baka ganin komi sai kyallin foundation, concealer da eye shadow.
Raheemah ma taci tata kwalliyar babu laifi.
Na duka a gefenshi na gaida shi, bai ko daga kai ya kalleni ba, ya amsa ciki-ciki kamar wanda aka takurawa, yaci gaba da cin abincinshi. Babu tambayar ‘ya kika tashi’ ko kuma ‘kin tashi lafiya?’. Wasu lokutan ma da yake cikin yanayi mai dadi, ya kan kara da ‘da fatan kinyi mafarkina?’.
Sai ban kawo komi a cikin raina ba, na juya na gaida matan nashi da suma suka amsa ciki-ciki, su dama sun saba, don haka ban damu ba. Yaya ne dai da ba haka ya sabar min ba, duk sai naji abin yayi min wani iri. Amma zata iya yiwuwa ko bai tashi cikin dadin rai bane yau. After all, mu dukanmu mutane ne, we all have our moments.
Ban jima ba, na koma dakina na gama shiryawa nima na tafi asibiti. Aikin safe nake yi wannan satin.
Koda na dawo daga asibitin, kasa zama dam nayi. Jikina tun jiya nan bai dawo daidai ba. Ji na nake yi kawai kamar ba ni ba. Ranar sai dana juya gabadaya tsarin dakina duk don in dan ragewa kaina zaman banza da tunanika marasa amfani.
Har zuwa can yamma ina abu daya, nayi wanka na sanya wata doguwar riga single, na dauki wayata tare da zura takalmi flat a kafata na fita falo.
Raheemah na kicin tana kammala girki, na zauna akan kujera, na dauki remote na kunno wata tasha suna karatun kur’ani. Na kwanatar da kaina akan hannun kujerar ina bin karatun a nutse. A hankali naji nutsuwa ta fara shigata.
Ina nan har Yaya ya dawo daga wajen aiki. Na tashi zaune ina kallonshi cikin murmushi, “Yaya sannu da…”.
Kafin ma in gama mishi sannu da zuwan, ya fada falonshi da sauri. Babu alamun ya kula dani a cikin falon da ya nuna, idan ma ya ganni din, ba karamin kokari yayi wajen share ni ba. Sai na bishi da kallo baki a dage.
Da dare kamar yadda aka saba, na tafi falon Yaya da niyar zuwa yin hirar dare. Suna zaune su duka ukun, Yaya da Raheemah suna hira, Ameerah kuma zaune a gefensu.
Na zauna a kusa da ita na musu sannu, Yaya da Raheemah suka yi shiru da hirar da suke yi suna kallona, babu wanda yace min ci kanki. Kafin suka komawa hirarsu.
Ko minti goma cikakke banyi ba, naji zaman wajen ya isheni. Yadda Yaya yayi kamar babu wata halitta a cikin falon face Raheemah kadai, abin ya sanyayar min da gwiwa. Ita kanta Ameerah din da idan da ne, duk wani motsi da zata yi zai yi ta binta da sannu, yanzu ko yunkurin tsoma baki tayi cikin hirar da suke yi, haka zaka ji yayi duf, sai kallo da zai yi ta binta dashi.
Da abin ya dameni, sai kawai na tashi na musu sai da safe don ba zan iya cigaba da zama a haka ba.
Wasa-wasa fa karamar magana sai ta fara kokarin zama babba. Shi kenan a wannan gidan yanzu babu wadda Yaya yake ganin tsakiyar kanta da gashi sai Raheemah kawai.
Lokacin da girki ya juyo kaina, sai dana kara raina kaina. Ranar Yaya bai shigo gidan ba sai can bayan isha’i. Na mishi sannu da zuwa ya amsa ciki-ciki, ya shige can kuryar daki.
Ban yi fushi ba, na bishi har dakin nace mishi ga abincin shi fa. Sai ce min yayi ai ya koshi.
Nace “ka ci abinci ne a waje ko kuma cikinka ne a cike?”.
Sai ya dago ya kalleni fuskarnan a cune, “to wai idan ma naci abincin ko kuma na kasa ci, menene matsalarki? Cikinki ko nawa?”.
Da yaga nayi shiru ina kallonshi ban ce komi ba, sai ya wawuri towel dinshi ya fada bandaki yana mitar duk na bi na tsangwame shi sai kace wani karamin yaro.
Na zabga uban tagumi har ya fito daga wankan ya sameni a yadda ya barni. Bai ce komi ba, ya fara shafa mai.
Nace mishi “Yaya, ko dai wani abu nayi maka ne? Idan ma haka ne, don Allah kayi hakuri. Ba da sani na nayi hakan ba”.
Murya ciki-ciki yace “to ni nace ne kin min wani abu? Ko kuwa don dai shi mutum bashi da damar yace ya koshi da abinci, sai a hau tuhumar shi. Wai ni karamin yaro ne, iye?”.
Gabadaya sai nake ga kamar Yayan an canza min shi da wani na daban. Wanda ban sani ba, wanda ban san komi nashi ba. Naji kwalla ta fara cika min idanu.
Sai ya dakata da abinda yake yi, ya kama baki yana kallona. Yace “to yanzu kuma me na miki da zaki sanya ni a gaba kina kuka?”. Na girgiza mishi kai alamun babu komi.
Yace “abinci ne dai ko? Bari in zo in ci, shikenan?”.
Na gyada kai ina dan murmushi, ina share kwallar data fara zubar min.
Bayan ya gama, muka rankaya zuwa falo, na zuba mishi abincin. Kadan yaci, hakan bai dameni ba, cin kadan din ai yafi rashin ci gabadaya.
Anan na barsu shi da matan nashi suna shan hirarsu. Har yanzu dai jiya i yau, bata sake zani ba. Ita kanta Ameerah na kula hakan ya dameta, bata fito fili ta fada bane kawai.
Dana koma falon, ban zauna ba, sai na shige can ciki nayi kwanciyata. Har Yayan ya shigo shima, ya gama duk abubuwan da zai yi, ya hayo kan gadon ya kwanta.
Ganin ya juya min baya ba tare da yace komi ba, yasa na gangara zuwa gefen daya kwanta. Nima na kwantar da kaina akan kafadarshi. Daga farko sak yayi kamar wanda lantarki taja, sai kuma ya saki jikinshi. Ana jimawa naji ya zame ya kara matsawa can gefe guda.
Wani irin makaki yazo ya takure min a cikin makoshina, wata kwallar ta sake ciko min idanu. Sai nima na juya mishi baya.
Zuwa can cikin dare na farka, na ganshi zaune a gefen gado, idanunshi kur a kaina kamar wanda yayi nisa cikin dogon tunani. Ban nuna alamun na farka ba, naci gaba da kallonshi ta cikin dan hasken dakin har barci ya sake kwasheni.
*☆⋆46⋆☆*
Har na fita daga girki na sake shiga wani, bata canza zani ba tsakanina da Yaya. Hankalina idan yayi dubu to a tashe yake. Wannan shine karo na farko dana taba fuskantar yace baya daga mijin aurena, bana kuma fatan hakan ta kara faruwa koda wasa ne. Yadda yake yi kamar duk duniya babu abinda yaki jinin ya gani kamar ni, shine yafi tayar min da hankali. Nan da nan nayi rama. Yanzu na samu yana cin abincina ba tare da bacin rai ba, sannan yana dawowa da wuri ranar girkina. Daga wannan shikenan, idan ma na samu ya amsa min gaisuwata da sannu, to naci sa’a.
Inda naji dadi daya ne, duk da dai ba abin jin dadi bane, ganin cewa ba ni kadai hakan take faruwa da ita ba, har da Uwargida Ameerah, duk da cewa dai ita yana dan daga mata kafa saboda cikin jikinta, amma dai babu gwara.
Hakan ya tabbatar min da cewa lallai da wata a kasa. Ta fannin addu’a da kula da jiki, ina iyaka kokarina dama, sai kara dagewa da nayi. Takanas na dauki kafa naje har Suleja wajen Malam Ali, da yake ya daina kawo mana rubutun da yake kai mana duk sati. Bayan mun gama gaisawa da mutanen gidan, aka min jagora zuwa inda yake karbar bak’inshi.
Mun jima muna hirar yaushe gamo, daga karshe dai na mike kafa na mishi bayanin abinda yake tafe dani, tun daga ranar da abin ya faru har zuwa yau.
Nan ya bani wasu addu’o’i yace in lazimci yin su, shima kuma yace zai dinga taya mu. Ya kara da cewa “ku matsalar ku ta yan boko, sai ku ce baku yarda da sadaka irin wadda ake rabawa yaranmu suyi ayi yanka da sauransu ba. Ita kuwa sadaka abu ce mai kyau, koda wani abu mummuna bai faru da kai ba, ta kan kiyaye mutum daga munanan abubuwa da dama, haka kuma tana tsare shi daga kambun baka, sihiri da sharrin jinnu. Baka san bakin mutane ba, akwai wasu zababbu a cikinmu, da idan suka yi mana addu’a zaki ga kamar da bakin yan amin suka yi ta, Allah ya karba. Shi yasa muke rarrabawa, saboda bamu san inda albarkar take ba”.
Na gyada kai cikin alamun fahimta, nace “haka ne Malam. Muma din muna kwatanta yin hakan, amma zamu kara zage damtse in Allah ya yarda. Yanzu zan bayar da kudin sadakar kafin in tafi, in yaso sai ayi duk abinda yakamata dai”.
Ya girgiza kai, “kada ki damu ‘yar nan, babu abinda zai gagara da yardar Allah. Yaran nan namu ne, dan abinda ya rage kuma bai fi karfin aljihunmu ba, saboda haka za ayi duk abinda ya dace. Ke din ai diya ce a wajena, jinin Malam Audu tamkar jinina haka na dauke su”.
Nayi murmushi nace “nasan da hakan Malam, amma duba da cewa sadakar tawa ce, me zai hana ka barni in bayar da kaina?”.
Bayan je-ka-dawo dai, dole na sakar mishi, na mishi godiya tare da mishi sallama na tafi. A cikin gida nabi duk iyalan gidan da kyauta har ma da almajiran kafin na fita waje inda Balarabe direban gidanmu yake jirana, yaja muka koma gida.
Da yake aikin safe nake, sai na tashi da wuri tare da turawa Yaya sakon zan zo wajen Malam Ali wanda ya turo min da to kawai.
Akan hanya ya tsaya na sayi fresh fruits da vegetables, duk da ranar ba girkina bace, naji ina marmarin yin salad. Tunda na fara daukar albashina na daina jiran Yaya ya min, ko ya bani wani abu. In dai na ga babu abu kuma ina so ko kuma zanyi amfani dashi ranar girkina, bana kyashin cirewa in saya tunda dai Alhamdulillahi ina dasu, kuma shima Yaya Bilal din baya kyashin bude mana bakin aljihunshi. Wasu lokutan haka kawai zai kirgo kudi ya bamu, baya kuma banbancewa a tsakaninmu, duk da cewa ni ina daukar albashina, Ameerah ma kuma iyayenta na turo mata, amma hakan bai sa ya banbanta mu ba.
Kashi biyu na sanya Balarabe ya sayo komi, daya kawo nace ya dauki kashi daya shima ya kaiwa iyalanshi. Yayi ta godiya har muka karasa gida, ya zagaya da sauri ya bude min murfin motar na fito, ya biyo bayana da ledojin a hannunshi yana kara wata godiyar.
Yan aikin gidan na matukar girmama ni, kamar yadda nima nake girmama su, yawanci ko wani abu ya taso kafin kaji sun nemi Ameerah data kasance Uwargida sau daya sun nemeni sau goma, musamman idan wata bukata ce suke da ita wajen Yaya. Ban taba kyashin isar da sakonsu ba, tunda Allah yasa yana iyaka bakin kokarinshi wajen ganin ya kyautatawa mutane, kuma ya taimaka musu, meye a ciki idan na taimaka mishi ya cigaba da taimaka musu?.
Ranar nan Hasina wadda take mana wanke-wanke da shara, tace tana ta fadawa Raheemah ta taimaka ta yiwa Yaya tunin kudin albashinta, yace zai bata da wuri saboda aikin da za’a yiwa diyarta a hannu, amma har lokacin bai ce komi ba da alama ya manta. Tace ita fa tana zaton kamar bata fada mishi ba, don data sake mata magana sai ta hau ta da fadan wai ta takurawa mijinta. Nace mata kawai zan fada mishi da kaina. Sam ko sun kawo korafi kan wani halin rashin kirki da suka musu, bana biye musu mu ci namansu, yadda bana so ayi gulmata, nima bana yin ta wasu.
A bakin kofar falon muka tsaya na karbi ledojin hannun Balarabe saboda nan ne iyakacinsu da gidan, na tura kai na shiga falo. Karfe hudu na rana ta gota da kadan. Allah-Allah nake in dangana da dakina in cire uniform din jikina, in watsa ruwa ko naji sanyi a jikina saboda wani azababben zafi da ake zubawa yau.
Zaune a falo, Yaya ne da Raheemah sunyi jigum-jigum, sai wata Hajara cousin din Ameerah da take yawan zuwa gidan. Nayi sallama, suka amsa min cikin sanyin jiki, sai naji jikina ya kara yin sanyi, nace musu “lafiya kuwa?”.
Hajara ce kawai ta iya amsa min, tace “Ameerah ce ta fadi a bandaki dazu, ana tunanin kamar ta samu miscarriage!”.
Sai naji jikina ya kara yin sanyi, nace “Subhanallahi, ya jikin nata? Sun tafi asibiti ne?”.
Tace “a’ah, ai family doctor dinmu tazo, yanzu haka tana ciki tana dubata”.
A raina naji abin banbarakwai. Nayi tunanin idan aka samu akasi irin haka, asibiti ake garzayawa? Amma sai na kame bakina nayi shiru. Na shiga daki na canza kayan jikina, na koma falo nabi layin jiran fitowar likita.
Banyi mintuna goma da zama ba, sai ga likitar ta fito. Duk muka tashi tsaye. A shekarance za’a iya cewa zata yi shekaru arba’in da wani abu, ta kalli yadda muka yi cirko-cirko cikin jimami, tace “sai dai hakuri, amma cikin ya zube saboda tsabar buguwar da tayi”.
Hajara ta hau sallallami da salati cikin kuka, shi kuwa Yaya shiru yayi kawai yana kallon likitar, sai dai daga ganin yadda idanunshi suka kada suka yi ja, kasan cewa zancen ya shige shi sosai. Ban san a wani shafi nake ba, na bakinciki, jimami ko tausayi?.
Raheemah ta kama kugu ta fada karkada jiki cikin tsiwa, “hmm! Allah sarkin baiwa! Wadda aka bullo da ita kuma kenan? Ku dai kuka sani, nan gaba ma zuwa za ayi ace ta haihu an sace mata dan!”.
Cikin nuna alamun gajiya Yaya yace “Raheemah…!”. Amma bai karasa fada ba, kamar wadda maganar ta kakarewa. Da mai hankali ce, ko kuma da masifa bata rufe mata idanu ba da ta fahimci warning din da yake tattare a cikin muryarshi.
Maimakon tayi shiru sai taci gaba, “ai wallahi kaima tabewar basira ce ta same ka. Wadda aka tabbatarwa da cewa ba zata taba haihuwa ba, ita ce zata zo rana daya tace wai tana da ciki? Yo cikin abin banza ne ko kuwa a ruwa ake shan shi? Aikin banza, an rasa karyar da za ayi sai ta ciki. Ai wallahi dama jiran ranar da za’a haife muke yi mu ga uban abinda za’a kawo ace an haifa, sai kuma aka kare da bari. An kira likitar bogi ana wani kukan karya saboda an maida mu sakarkaru, to mun san komi ai wallah kuma idanunmu ba a rufe suke ba!”.
Aikuwa sai Hajara ta shaka, nan da nan ta manta da kuka da salatin da take yi, tace “su waye kike cewa masu yin karyar ciki?”.
Tace “ba ga ku nan ba! Makaryatan banza dana wofi!!”.
Hajara kuwa tace “ke in ana zancen ciki ma har kin isa kiyi magana? Ke da ko batan wata ma baki taba yi ba? Idan fitsari kayan banza ne kaza ma tayi mana mu gani?!”.
Wai! Ai sai Raheemah ta hau ihu, tana yi har tana hadawa da buga kafa a kasa, “ai wallahi na godewa Allah tunda abin bai kaini ga yin karyar ciki ba, kuma lafiyata lau, ina kuma da amfani ba ci nake ina kasayarwa ba!!”.
Hajara tace “idan abin haka ne, me yasa ke baki taba yin cikin ba?”.
Nan da nan falo ya rikice da hayaniya kamar zasu ba hammata iska, sai da Yaya ya tsawatar musu sannan da kyar. Raheemah ta wuce dakinta tana cigaba da zage-zagen.
Ya juya ya ba likitar hakuri, tayi murmushi tace babu komi ai. Ya tambayeta ko nawa ne kudin aikin da tayi? Tace ai kudinta suna cikin albashinta, Hajara ta taka mata ta mana sallama ta tafi.
Suna fita Yaya yayi dakin Ameerah, na bi bayanshi. Tana kwance akan gado tana barci. Idan ba fada maka aka yi ba, ba zaka taba cewa mai jinya ce ba wadda tayi bari. Babu paleness alamun rashin jini, babu alamar cuta ko kadan a tattare da ita. Ni dai na tabe baki a cikin raina, sai me idan tayi karyar ciki? Wannan ai matsalarta ce ba tawa ba. Matsalata ita ce matsalar dake tsakanina da mijina a yanzu.
Na samu kujera na zauna anan, babu mai uhm ko uhm uhm a cikinmu. Na kalli yadda ya dafe kai a zaune, har yanzu kayan aikine a jikinshi, bana tunanin ko sallar la’asar ma yayi. Na danyi gyaran murya nace “Yaya ko zaka je ka canza kayan jikinka ne? Zan kula da ita kafin ka dawo. Kayi sallah ma kuwa?”.
Ya daga kai a hankali ya kalleni kafin ya girgiza kai. Tausayinshi ya cika min zuciya. Nayi takaicin cewa yau ba ranar girkina bace, da na faranta mishi rai, ta yadda zai manta da kowa da komi.
Nace “kaje kayi to, sai ka dawo”.
Babu musu ya tashi ya bar dakin. Ni kuma naci gaba da zama anan har Hajara ta shigo itama.
Zuwa can Ameerah din ta tashi daga barci. Muka matsa muna mata sannu, Hajara ta taimaka mata ta tashi zaune. Na mata ya jiki, ta amsa tana wani yamutsa fuska. Ban kara ce mata komi ba, sai wani kallon dana jefa mata wanda ya sanya ta shiga taitayinta a take, ita tasan ni ba sakara bace, kamar yadda nasan itama ba sakarar bace, ta fahimci ma’anar kallon da nake wurga mata sarai. Nan na barsu na wuce dakina.
Washegari kuwa haka aka yi ta zuwa dubiya da jaje. Janan da Yaya ma sun zo. Bayan sun dubata, muka nutse daki ni da Janan. Tunda tazo take bi na da kallo cikin alamun tambaya, nasan hakan baya rasa nasaba da yadda nayi wuri-wuri ne, na canza kama. Muna shiga daki kuwa ta fara watso min tambayar lafiya? Nayi rashin lafiya ne?.
Na zauna a gefen gado ina kallonta, “lafiyata lau mana, me kika gani ne?”.
Tace “ban gane ba? Baki ga irin ramar da kika yi bane? Kin kuma kara baki”.
Na daga kafadata sama kawai, “halin rayuwa kenan dama, yau dadi gobe madaci”.
Itama ta zauna a gefen gadon tare da dafa kafadata, tace “to Allah ya kyauta. Amma don Allah ki kwantar da hankalinki. Kada ki saka wata damuwa da bata kai ta kawo ba a cikin ranki ki janyowa kanki wata cutar. Komi zai zo ya wuce”. Na gyada mata kai a hankali.
Sanin ba zata ji komi daga bakina ba, yasa ta kawo min hirar wajen da take yin internship. Duk mun kusa gamawa, nan da watannin da basu fi uku ba zamu gama, mu zama cikakkun nurses.
Daga karshe ma dai muka fita ni da ita. A motarta wata madaidaiciyar SUV Lexus UX ruwan toka, da mijinta ya sai mata. Da yake ta riga ta iya motarta tun kafin tayi aure, ita take kai kanta ko’ina, yanzu ma ita ta kawo su da Yaya.
Gidan Yaya Hafiz muka je, matarshi Hauwa, ta karbemu da far’arta. ‘Ya’yansu maza biyu, mace daya suka zagaye mu suna mana sannu da zuwa. Da yake lokuta da dama suna leko mu, amma zumuncinsu yafi karfi da Ameerah, amma muna gaisuwar mutunci da ita.
Bayan mun dan yi kamar mintuna ashirin haka, muka musu sallama muka tafi. Muka nutsa cikin garin Abuja, shiga gidan wannan, fita daga wancan, yawancinsu duk gidajen kawayen Janan ne, wasu kuma gidajen yan’uwansu ne. Sai da Yaya ta kirata akan tana jiranta, sannan fa muka juya.
Bayan sun tafi na koma daki na zauna ina jiran a kira sallar magriba Nasan yau idan na kwanta sai nayi ciwon jiki saboda yawace-yawacen da muka sha.
⋆⋆
Kwana biyu, komi ya natsa, komi ya koma yadda yake, mun ci gaba da gudanar da rayuwarmu kamar da. Ameerah ma ta warware har ta karbi girki abinta.
Ranar Alhamis, ranar satina daya da zuwa Suleja. Abubuwa da dama sun ragu, ina kuma ganin canji sosai a tattare da Yaya, ya sauko sosai. Tunda yanzu mu kan zauna muyi hira cikin raha, muci abinci tare, duk da lokaci zuwa lokaci ya kan dan janye jikinshi, but am not complaining.
Aikin rana nayi yau, kafin in tafi nayi miya na ajiye a dakina, don haka ina dawowa na dafa cous-cous muka ci a matsayin abincin dare. Yau ko hirar da ake yi ban tsaya ba, ina maida kayan kicin, dakina na wuce nayi shirin kwanciya barci, na musu sallama na fada dakin Yaya na kwanta.
Ina kwanciya barci ya dauke ni, yau wuni muka yi akan kafafunmu, saboda haka jin jikina nake kamar wadda aka wa dukan tsiya. Ban damu da jiran Yaya ba, kamar yadda nace, mun dan koma normal ne, amma ba duka ba. Duk da hakan yana damuna, amma ban bari ya dameni sosai ba.
A cikin barcin naji shigowar shi dakin, da alama yau hirar bata yi tsayi ba, tunda ko cikakken minti goma banyi da kwanciya ba. Ina jin motsin shi a cikin dakin, da alama shirin kwanciya barci yake yi, amma saboda tsabar gajiya na kasa bude idanuna.
A hankali naji an zauna a gefen gadon, tattausan hannu ya shafo gashin kaina zuwa gefen kumatuna. Wata siririyar murya, very husky and soothing, take kiran sunana, amma daga can nesa nake jiyo muryar kamar a cikin mafarki.
“Na’ilah… Baby…!”.
“uhm?”, na amsa. Amma na kasa daga idanuna.
“Baby!!”. Aka sake kirana, wannan karon desperately.
Don haka nayi kokari na bude idanuna da kyar, kuma a hankali.
Ban san me zan ce ba, saboda na kasa banbance tsakanin mafarki da farke. Shin wannan ma daya daga cikin mafarkan dana saba yi ne? Ko kuwa da gaske ne?!.
Ba kamar sauran mafarke-mafarken dana saba yi ba, kamar su dinne dai, amma ya banbanta. A maimakon silhouette din mutum dana saba gani, wannan karon sai nayi ido-da-ido da Yaya. Wanda ya saki wani irin tattausan murmushi lokacin da yaga na bude idanuna mun hada ido dashi.
Nayi scrunching eyebrows dina in confusion, mafarki nake yi?.
Ya kara shafa gefen fuskata, “I love you, baby na!”.
Scratch that! Be it mafarki ko rashin mafarki, it doesn’t matter. What matters is that, Yaya ne, mijina, nake gani zaune a gabana, yana furta min abinda na jima banji daga gareshi ba. Sanyin daya mamaye kirjina a wannan lokacin, Allah ne kadai yasan iyakarshi.
Sai dai barcin dake cikin idanuna ya rinjayeni, da kyar nake damben iya daga idanuna da suke komawa suna likewa kamar ana jona su da maganadisu.
Na dafa hannunshi dake kan kumatuna, “Yaya..!”. Na samu na furta hakan a hankali, kafin barci ya sake daukata. Hakan bai hana ni jin warmness din da lebbanshi suka haifar akan goshina ba. Ban kuma daure murmushin daya subuce min ba duk da barcin daya ci karfina.
Kiran sallar farko a cikin kunnena. Na bude idanuna a nutse, a hankali kuma abubuwan da suka faru a daren jiya suka fara dawo min. Tunanina daya a lokacin, shin mafarki ne nayi?.
Sai dai daga jin dumin jikin daya kamo ni ya rukunkunme ni ta baya kamar wanda yake tsoron a dauke mishi ni, ina tantamar idan mafarki ne.
Murmushi ya fara kokarin subuce min, wani irin sanyi, aminci da salama dana manta rabon da inji kwatan-kwacinsu suka dinga kwararawa suna shiga cikin zuciyata. Marata cike take tam da fitsari, dalilin daya tasheni daga barci ma kenan, amma na kasa zame jikina daga nashi. Sai ma kara lafewa da nayi a kirjinshi ina jin bugun zuciyarshi.
Mun jima a haka, har zuwa lokacin da ya farka. Sannan na daga kai, tare da kokarin zame jikina daga nashi wanda sai a lokacin ne ya sake ni.
Sauka nayi daga kan gadon na shiga bandakin. Bayan na gama abinda zan yi, alwala na dauro sannan na fito. Ina fita, shima ya shiga bandakin.
Na gyara jikina tare da fara nafila kafin lokacin sallah yayi. Ina jin lokacin da Yaya ya fito shima, ya shirya ya fita zuwa masallaci.
Ina cikin nade abin da nayi sallar naji ya dawo. Ina jin lokacin daya maida kofar ya rufe. Nayi shiru a tsaye ina jiran in ga abinda zai yi ba tare dana juya ba, saboda ban san abinda zai faru ba. Kawai sai ji nayi an rungumoni ta baya. Ya lalubi kunnena yace “good morning, baby”.
Naji kunya ta rufe ni, nace “ina kwana Yaya?”.
Ya nutsa kanshi gefen wuyana yana humming, “lafiya lau baby na, kinyi barci lafiya?”.
Na gyada mishi kai tare da juyawa ina kallonshi cikin murmushi, “sosai ma!”.
Bai ce komi ba, sai kara ja na cikin jikinshi da yayi, ya kara saka kanshi a wuyana yana shakar numfashi. Abinda yake matukar kauna kenan. Mun jima a hakan, kafin ya dago ni yana kallona, “God, how I miss you!!”.
Na daga hannu na shafo gefen fuskarshi, “I miss you too, Yaya na!”.
Daga nan kuma abinda ya faru sirrinmu ne. Sai can, rana ta fito sosai sannan na raka shi ya tafi bayan na soya mishi kwai ya ci da shayi da biredi.
Ina dawowa daga raka shi din da nayi, naci karo da Raheemah a kofar kicin ta baya ta coge tana watsa min kallon tara saura. Na gaida ta fuska babu yabo babu fallasa. Ta kare min kallo tun daga sama har kasa, taja tsaki, “jarababbun banza da wofi!”. Ta fadi hakan cike da tsana da dacin rai.
Ban ce mata komi ba, ban ma ji komi a cikin raina ba, farincikin da zuciyata take ciki a lokacin ya wuce tunanin mai tunani, babu abinda zan fari ya wargaza min wannan jindadin. Don haka na hasketa da murmushin tura haushi kawai na kara gaba.
Ina shiga kicin ta sake biyoni, “kina nufin yau da abinda zamu karya kenan?”. Ta fada tana nuna flask din shayi da biredin da na ajiye akan dinning table, shekeke kamar wasu kayan kashi.
Nace “ehh mana, me suka yi ne?”.
Kafin tace wani abu, Ameerah ta fado kicin din sanye da rigar barci ta leshi wadda ta tsaya mata a gwiwa. Ta kalli yadda muka yi cirko-cirko damu kamar wasu zakaru, ta dauke kanta ta hau dage-dagen drawers. Ni ce na fara gaida ta, sai data dauki gwangwanin white oats, sannan ta amsa.
Nima na dauki yoghurt daga cikin fridge na koma dakina. Bashin barcin da na ci na biya kafin lokacin tafiya aiki yayi.
***
Shikenan, muka shirya abinmu. Rayuwa taci gaba da tafiya, akwai lokuta da dama da sabani zai shiga tsakaninmu, hakan bai taba affecting rayuwar aurenmu ba. Bamu fari sabani ya kaimu ga bacin ran da zai hana mu jindadin rayuwar aurenmu ba.
A hankali azumi yana ta matsowa. Ranar nan kwatsam sai ga Yaya da albishirin zamu je umra dashi. Wayyo, murna har sai da nayi hawayen dadi. Na fara kiraye-kirayen wayar yan’uwa da abokanan arziki ina albishir.
Washegari sai rigima ta balle, a cewar Raheemah Yaya yayi rashin adalci. Saboda wancan karon ma da zai tafi tare da Ameerah suka tafi wanda hakan yake nufin wannan turn dinta ne kenan.
Yaya yace “wannan nima haka naji shi daga sama yadda kika ji shi kema, bani da alhakin kudin jirginta. Illa iyaka mun tafi tare, mun kuma dawo tare”.
Da taji haka kuma sai tayi shiru ta fara kokarin nade tabarmar kunya da hauka. Wai “ai duk da hakan dai, ai..”, Ta hau kame-kame. Yaya kuwa yayi banza da ita, ya juya yana kallon Ameerah yana gaya mata tayi list din abubuwan da zasu bukata kafin tafiyarmu, tace to.
*
Anyi haka da kwana biyu, sai ga Ameerah da nata biridin itama. Ranar assabar ce, lokacin saura sati biyu mu tafi.
Na tura Yaya falonshi yana karatun jarida, ni kuma na hau gyara mishi daki. Daga bandaki na fara, bayan na wanke shi tas na kyalkyale shi yana ta sheki da tashin kamshi, sai na koma bedroom.
Ban san lokacin da Ameerah ta shigo ba watakila lokacin ina bandaki. Ina jiyo sautin muryoyinsu daga nan.
Wai itama Daddynta ya biya mata umrah, da alamu kenan tare zamu tafi da ita. Tana fadar hakan tana yar dariya. Sai dai daga jin yadda muryar Yaya tayi a lokacin, abin bai bashi dariya ba.
Kai tsaye yace babu inda zata je.
Da taga tayi roko da magiya ya kafe, sai tace to zata bi yan gidansu kawai su tafi.
Yace “ba ina nufin ba zaki bimu bane, ina nufin babu inda zaki je, kina gida”.
Murya na nuna bacin rai tace “kana nufin ayi asarar kudin da aka biya ne ko me?”.
Yace “lokacin da aka biya kudin ai ba’a nemi shawarata ba, ko an nema? Kada ki manta kuma abinda ya dace ayi kenan tun daga farko. Ta inda ake hawa kuwa ta nan ake sauka”.
Tayi shiru, can kuma tace “amma kasan duk shekara muna zuwa Hajji da umara ko?”.
Yace “ba a taba tambayata ba, ko an taba? Nayi iyaka karar da zanyi, na kuma gaji. Saboda haka babu inda zaki je wannan karon, idan kuma zaki yi musu da nine, to mu zuba don Allah!”.
Sai ta kame bakinta ta kulle. Na girgiza kai ina yin dan murmushi. Dama masu iya magana sun ce idan tura ta kai bango…!
Har na gama ayyukana ban sake jin duriyarsu ba, sai sautin karar talabijin ko kuma muryar Yaya idan an kira shi a waya.
Zuwa can na fito daga dakin hannu rike da basket da na matse bed sheets da kananun kayan Yaya dana wanke na wuce su a falon a zaune sunyi jugum-jugum.
Baya na fita na shanya kayan, na koma gidan ta kofar waje.
A kofar shiga falon muka yi karo da wata mata, muka kalli juna ni da ita, kamar na santa amma kuma na rasa a ina na santa. Na dakata ta shigo gidan kafin na rufa mata baya, sai da muka shiga falo naga tayi hanyar dakin Raheemah. Ni kuma na koma falon Yaya.
Lokacin dora girkin rana yayi na fita kicin na hau dafe-dafe, yam porridge nayi, nayi dambun cous-cous, da lemun cocktail.
Ina gama shirya abincin akan dinning Raheemah ta fito ta kwashi abincin da yawa ta koma dakinta, ban mata magana ba saboda bakuwar da nasan tayi.
Dakina na koma, nayi wanka tare da sanya kananun kaya, rigar blouse da dogon wando, na dora hular beanie na sanya silifas mai taushi na fita zuwa falon Yaya.
Ranar haka muka yini, Yaya bai leka ko nan da can ba. Sai can bayan sallar la’asar sannan ya fita.
Sai da yammar ne na fahimci cewa wannan bakuwar ba kowa bace face Haleemo. Na bita da kallo cike da tsananin mamaki, ta rame, tayi baki, duk wannan kwalisar babu ita, baka taba cewa itace Halimon nan. Kayan jikinta ma daga ganinsu sun ga jiya sun ga yau.
Ganin babu wadda tayi min magana a cikinsu, yasa nima na juya musu baya, naci gaba da yanka kabeji da nake yi a kicin. Amma kuma zuciyata cike take da tunanin abinda ya faru da ita, a iyaka sanina da ita Umar ta aura, to me ya faru? Ko sun rabu ne?.
Bayan na gama girkin, kasancewar lokaci ya kure tunda har an gama sallar magriba lokacin, yasa kayan ma a kan dinning na barsu gabadaya, na wuce dakina.
Wanka na fara yi, sai da nayi sallah sannan na zauna zaman shafa mai da hoda. Ina cikin shafar ne naji hayaniya ta fara tashi, na dan dakata, jin abin ya ki ci ya ki cinyewa yasa na dauki doguwar hijabi na zura na fita falo domin in ga abinda yake faruwa.
Raheemah na jingine da bangon falon, Yaya da Ameerah kuma na tsaye a tsakiyar falon sunyi cirko-cirko suna raba idanu kamar wasu zakaru.
*☆⋆47⋆☆*
Kallo daya zaka yiwa yanayin da mutanen falon suke ciki, zaka fahimci cewa babu lafiya.
Ameerah na tsaye nesa kadan da Yaya, in banda rawa, babu abinda ilahirin jikinta yake yi. A tsorace take sosai.
Shikuwa Yaya ya tsaya jimke da hannu, sai dana kare mishi kallo sosai sannan na fahimci cewa wata yar karamar farar takarda ce jimke a hannun nashi, wadda ya kama ya rukunkume har knuckles dinshi sai da suka yi fari, a gefe guda kuma jikinshi yana rawa cikin bacin rai.
Raheemah kam ta coge daurin dankwalin nan nata a tsakiyar ka kamar yadda ta saba, da alama itama hayaniyar ce ta fiddota zuwa cikin falon.
Hankalin Yaya gabadaya yana kan Ameerah, kallon da yake watsa mata kadai ya isa yasa duk girman kai da ji da kai na mutum ya saddakar masa ko da bai yi niyya ba kuwa. Ni kaina da nake gefe sai dana ji gabobin jikina sunyi sanyi. Ban taba ganin wannan side din na Yaya ba. Da alamu ma sam bai san da wanzuwarmu a falon ba, idan ma ya sani to yayi kokari wajen nuna cewa wanzuwar tamu anan bata shalle shi ba.
Ya nuna mata hannunshi da yake rike da farar takardar nan yana nuna mata, cikin wata irin murya da ta sanya ni na kara kallonshi da kyau domin in tabbatar da cewa da gaske shi dinne dai, he sounds deadly. Calm, but deadly. Kamar wani sabon mutum da ban taba gani ba, haka ya juye ya koma a lokacin.
Yace “care to explain, ko menene wannan kike kokarin zuba min a cikin abincina?”. Jin abinda yace yasa na zare ido ina kallonsu, a lokaci daya kuma ina kara matsawa kusa dasu.
Ameerah ta dan ja baya da sauri, tsoron dake shimfide akan fuskarta da baka taba rabata da kwalliya, ya bayyana zane baro-baro, instead, shi ya zame mata kwalliyar yau.
Tace “don Allah kayi hakuri. Wallah na tuba, don Allah!”.
Sai dai bai jira ta gama magiyar da take yi ba, ya daka wata irin gigitacciyar tsawa, “Don’t you dare Ameerah! Tambayarki nayi, damn your sorrys don ba ita nake bida ba. Ki fada min, meye hadinki da shinkafar bera na tsinceta a hannunki kina kokarin sakata cikin abincin da zan ci?!”.
Naji ana min wata irin kururuwa a cikin kunne, kaina yana juyawa kamar ana katantanwa dani, kafin wani irin duka a tsakiyar ka ya ziyarce ni kamar ana buga min guduma a ka. Ala dole na lalubi kujerar dake kusa dani na zauna babu shiri saboda rawar da kafafuna suka dauki yi.
Yanzu kam hawaye ne suke ta zarya akan kumatunta, daya bayan daya suna sintiri babu kakkautawa.
Yaya ya kura mata ido, “shikenan? Kaunar da kike ikirarin kina yi min kenan? Soyayyar kenan? At the end of the day kiyi sanadin raina?”.
Kai ta hau girgizawa, “ba haka bane, wallah banyi da niyar cutar da kai ba, ka yarda dani. Sharrin shaidan ne!”.
Yace “kada ki maida ni sakarai mana! Da idanuna na ganki kina zuba abinnan fa. Ko kuwa kina nufin ki ce sharri na miki, ko kuma idanuna ne basu gani daidai ba?”
Tayi shiru kanta a kasa, sai kai data girgiza kawai.
Yace “kina fa bata mana lokaci, ki fada min dalilin ki, ko kuwa kina so ne kice min gishiri ne wannan a hannuna?”.
Ta daga baki da kyar tace “akwai antidote dinta, da kaci zan baka yadda zaka amayar da gubar da kaci. Wallahi ba zan taba yin abinda zai cutar da kai ba, na rantse da Allah!”.
Sai dai ko kadan rantsuwar da take ja bata dada shi da kasa ba. Instead, sai kallonta daya tsaya yana yi. Babu mamaki tunani da lissafin gidan kula da masu tabin kwalwa mafi kusa yake so ya lalubo.
Da kyar ya iya kakaro sautin, “me yasa?”, daga can kasan makoshinshi.
Bata amsa ba sai daya kara jefa mata tambayar cikin daka tsawar da tafi ta dazu gigitarwa.
Ta ja baya da sauri, “munyi zaton idan ka ci abincin zaka zargi ita ta zuba maka, sai ka sallameta!”.
Na tsayin lokaci, duniyata sai ta tsaya cak. Bansan lokacin da hawaye suka fara zarya suna gangarowa kan kumatuna ba.
Wannan shine karshen kiyayya da wani mahaluki zai taba nuna maka a cikin rayuwa, shin ta tsani ganina har haka ne da abin zai kai ga laka min sharrin kisa? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!!.
Yanzu da Yaya bai shigo ba akan lokaci ya sameta cikin aikata wannan aika-aika ba, mai zai faru? Da haka zan kare rayuwata da laifin attempted kisa, haka kawai ban san hawa ba ban san sauka ba. Da haka rayuwata zata kare, ina tsanar kaina da tuhumar ta yaya hakan ta faru? Yaya da yan’uwanshi da suka zama nawa yan uwan nima suna tsanata?
Me na yiwa wannan matar ne da zan cancanci haka daga gareta?.
Yaya bai ce komi ba sai pacing daya hau yi kamar mai fareti, cikinmu babu wanda yayi gigin yin ko motsi, sai ni da lokaci zuwa lokaci zan ja majina ko in share hawayen fuskata.
Ya dawo ya tsaya a gabanta, “what were you thinking you silly woman?”, ya furta with venom a cikin muryarshi. Kafin ya juya ya cigaba da zagayen da yake.
Falon ya dauki shiru kamar babu wasu halittu da suke numfashi a ciki.
Yace “ban san ko daga ina matsalar nan take ba, amma wannan ba hujja bace. Me kike tunani, kin tsani ganinta ne har haka ko me? Hasbunallahu wa ni’imal wakil!”.
Da alamu ya. kasa iya wrapping kanshi akan wannan matsalar, nima hakan take a wajena.
Yace “kwanaki munyi ta cin karo da matsalar yawan gishiri yaji, tsami, da sauransu a duk ranakun da Na’ilah tayi girki, it was so suspicious I can’t help but wonder, kina da hannu a haka?”.
Ta dago rinannun idanunta da suka rine suka yi jawur saboda tsabar kuka, suka yi clashing da nashi rinannun da tsananin bacin rai, shock da tu’ajjibi suka haifar mishi. “Bab…”, ta daga baki zata fara magana yayi gaggawar katseta, “cut it! Tambayarki nayi don haka amsa zaki bani ehh ko a’ah?”.
Tayi kasa da kanta a sanyaye, “kayi hakuri”.
Ya rumtse idanunshi yana girgiza kanshi kamar yana shaking wani abu daga ciki, “cikin da kika yi b’ari fa kwanan nan?”.
Nan ma wani shirun ya ziyarce shi kafin bada hakuri ya biyo baya.
Shirun daya biyo bayan nan was deafening.
Magana daya Yaya ya iya yi a wannan lokacin, “kin cuce ni Ameerah!”. Wadda daga jin yadda muryarshi ta lullube da zallan bakin ciki da sararwa, daga gani babu tambaya abin data aikata ba karamin girgiza shi yayi ba. Sai dai ni kaina abin ya girgiza ni, sosai ba kadan ba, wa ma zai taba tsammanin haka daga gareta? Da iliminta, da wayonta da komi. Rashin dabara ce ko kuwa tsananin jarumta?.
Daga lokacin da Yaya ya yanke shawara, na fahimci abinda yake shirin aikatawa, niyyarshi a bayyane take, idanunshi sun rufe da takaicin abinda tayi.
“That’s it Ameerah… Kije na…”
Ban san lokaci ko dalilin daya sanya ni mikewa tsaye da sauri ba ina mai ambatar sunanshi, dalilin daya sanya shi dakatawa kenan, ya tsaya yana kallona cikin nuna alamun tambaya.
Nace “Yaya, kada ka aikata abu cikin fushi kazo daga baya kana dana sani, don Allah ka fara nutsuwa tukun”.
Ya kalleni, ya juya ya kara kallonta, ya daga baki kamar zai yi magana, ko kasa yin maganar ma yayi? Kawai juyawa yayi ya fita daga cikin falon da sauri.
Ameerah tayi tsaye a nan inda ya barta, kusan minti daya, kafin ta lallaba ta fada cikin dakinta. Na koma cikin kujerar dana tashi na sake zama. Ba ni na aikata abin ba, amma har yanzu ilahirin jikina rawa kawai yake yi. Ita Raheemah na tsaye a inda take, bata da niyar motsawa. Allah kadai yasan iya lokacin da muka dauka a haka, bayan rawar da jikina yake yi, wani irin sanyi jikin nawa ya dauka ta yadda ko yatsar hannuna kasa motsawa nayi.
Zuwa can sai muka ji karar bude kofa, muna daga kai sai muka ga Ameerah ta dora gyale a kafada, ta ratayo jaka a daya kafadar, makullin motarta a hannu. Babu wanda ta kalla a cikinmu bare muyi tunanin samun karin bayanin inda ta nufa, ta kara gaba. Muma babu wanda yayi gigin tararta bare ya mata magana. Tana fita Raheemah ta juya ta koma dakinta.
Na ci gaba da zama a falon ba ko motsi, ina kallon waje daya kawai; inda Ameerah take tsaye yan mintuna da suka wuce.
Shiru Yaya zai dawo yanzu, amma babu alamun shi. Ba karamin mamaki nayi ba lokacin dana daga kai na kalli agogo naga goma saura. Sai a lokacin ne nayi kokari na koma dakina ina hada hanya. Sallar isha’i na fara yi. Ko bayan na gama sallar, zama nayi akan abin sallar ina kara neman tsarin Allah daga sharrin zafin kishi, kishi wanda zai iya sanya ni aikata mummunan abu ko kwatankwacin wanda Ameerah ta kwatanta yi yau.
Wani irin kishi ne wannan? Wane irin so ne da zai sanyaka aikata abu kamar sanya guba, da sunan son yin framing din wani, kawai don ya bar maka gida? Anya mata zamu so ganin haske a cikin rayuwarmu kuwa?.
Abin bai taba zuwa kaina ba a cikin rayuwata sai yanzu. Nasan nayi kishi, na kuma san na tsani kishiya, sai dai ko da wasa, ko a cikin mafarki ban taba tunanin zan iya aikata abu irin wannan ba. Sai dai dana zauna na kara yin tunani, sai naga ai tun daga farkon fari, abinda ya sanya ni kin kishiyar kenan. Tsoron juyewa in zama abinda ba ni bace yasa, tsoron kishi ya sanya ni aikata abinda zai zo ya zame min abin nadama nake yi, ina tsoron aikata ire-iren wadannan abubuwan ne.
Na kara rokon Allah akan ya kiyaye zuciyoyinmu daga sharrin sake-saken shaidan, da bin shawarar mugayen kawaye, har ma da yan’uwa.
Sai wajen karfe sha daya sannan Yaya ya dawo gidan, lokacin gidan yayi shiru, ko karar tv baka ji a lokacin balle na mutane, har lokacin kuma ina zaune anan inda nake.
Kirana yayi a waya yace in same shi a falonshi. Na tashi na fita, yana zaune akan kujera da ledoji a gabanshi. Sai lokacin na tuna ban dauke kayan abincin ba ma. Ya miko min nawa, buyin kuma yace in mika musu, da alamu bai san Ameerah ta bar gidan ba.
Dana fada mishi Ameerah bata gidan, bai ce komi ba, kai kawai ya gyada tare da tashi ya fada dakinshi.
Na kwashi ledojin na tsaya ta kofar dakin Raheemah na buga mata kofa, ta leko na bata. Bata ce komi ba ta amsa ta maida kofar ta rufe. Sauran kuwa sai kicin na kaisu na ajiye don babu abinda zai iya shiga cikina a lokacin. Na kwashe kayan nan gabadaya na zubar da komi, har lokacin ganin komi nake yi kamar a mafarki, na kasa yarda ya faru.
Sai wajen karfe goma sha biyu nayi sallama dakin Yaya. Yana kwance akan gado, amma ba barci yake yi ba. Na zauna a gefen gadon ina kallonshi, bai yi ko motsi ba.
Zuwa can nace mishi “ba zaka ci abincin bane? Ko zan sama maka wani abu ne?”.
Ya girgiza kai. Sai ban takura shi ba, na tashi na kashe wutar dakin na koma na kwanta.
Nasan yana bukatar lokaci kafin ya samu komi ya zauna mishi a kai. Ko ni kaina abin ya kasa zaunar min, balle shi, da suka kwashe lokuta masu tsayi da ita, to think that zata iya betraying dinshi ta haka, abu ne mai wahala. It must be a big blow. Daga ni har shi babu wanda ya tankawa wani, muna ta sake-sake. Ranar kam barci sai barawo.
*
Washegari karan wayar Yaya ne ya tashemu daga barcin da muka koma bayan sallar asuba. Kaina har juyawa yake yi saboda tsabar ciwo da rashin barci.
Sai da tayi kara sau kusan uku babu kakkautawa, a raina har ina mitar wane mai gajen hakuri ne wannan da bai san ya kira sau daya ya hakura ba? Karfe bakwai da rabi ma bata karasa yi ba lokacin.
Sai da kira na uku na katse, yana katsewa kuwa na hudu ya sake shigowa. Sannan Yaya ya kai hannu ya dauka.
Murya shake da barci ya fara da yin sallama, sai dai da alama mai kiran wayar bai damu da sallamar tashi ba, ya tare shi da “Me Ameerah ta maka ka turota gida tun da sassafe?”. Da alama Babanta ne.
Kasancewar a kusa dani yake, ina jin maganar da ake yi a daya bangaren.
Tashi zaune yayi yana gaida shi, wannan karon ma bai amsa ba, ya kara maimaita mishi tambayar daya mishi. Tashi yayi cimak ya fita daga dakin, na bishi da kallo.
Sai can kusan bayan minti sha biyar, sannan ya dawo dakin. Ya zauna a kan sofa tare da dafe kanshi cikin hannuwanshi. Ganin haka yasa na tashi zaune a tsakiyar gadon.
“Lafiya?”. Na tambayeshi a sanyaye. Yanayinshi bai yi kama da wanda yayi tattaunawar arziki da surukin nashi ba.
Ya girgiza kanshi kafin ya dago kai ya kalleni, “ban sani ba nima, kawai dai Ameerah taje musu gidan da safiyar yau, wai tunda taje take kuka bata ce komi ba. Yanzu dai Babanta yace zai zo nan ya sameni, zamu hadu anjima kadan a Will’s Park”.
Na dan zaro ido, kafin na gyada mishi kai.
Nasan ko na koma na kwanta ma babu wani barci da zanyi. Don haka na tashi kawai na shiga bandaki na dauraye bakina. Na tafi na dora girkin safe.
Abincin sai tsakurar shi kawai aka yi. Karfe daya Yaya ya tafi ganin mahaifin Ameerah. Bai dawo ba sai gab da magriba. Fuska babu yabo babu fallasa haka ya shigo gidan. Ameerah da take girki, ta mishi sannu da zuwa ta bishi zuwa dakinshi.
Sai da dare muna falonshi mu duka, sannan yake bamu labarin abinda ya faru.
Mahaifin Ameerah dai yaki yarda, ko kuma ince yaki daukar laifin da diyar tashi tayi. Daga karshe ma sai ya koma accusing din Yaya kan cewa dama baya kula mishi da diyarshi yadda yakamata, ya maidata ta zama koma baya a cikin dangi. Tafi-tafiya ma sai yace yana bukatar takardar sakinta kawai. Duk yadda Yaya yayi wajen ganin cewa ya fahimtar dashi, abin yaki yiwuwa. Shi a ganinshi abin bai kai ga haka ba, sai ya gangaro yace idan bai sakar mishi diyarshi ba zai iya maka shi a kotu. Sai da ya rubuta mata saki daya sannan ya warci takardar ya kara gaba.
Daga ni har Raheemah babu wanda bai jijjiga da jin haka ba. Muka jinjina maganar sosai, daga karshe nayi fatan Allah yasa hakan shi yafi alheri.
*
Kwana biyu gidan shiru, ita kanta Raheemah ta kame kanta ta kai gefe. A hankali komi yazo ya wuce, ya zama tarihi a wajenmu. Rigima bata kuma tashi ba, kamar hakan ya zamewa Raheemah abin tunatarwa da darasi. Tsakanina da ita sai kallo kawai, ba uhm ba uhm uhm. Habaice-habaice da bakaken maganganu da take yawan jifa na dashi a kullum rana ta Allah babu gajiya, muddin muka hadu sau daya ko sau goma a rana sai an jefo shi kamar wani abin arziki, yanzu ta daina kamar anyi ruwan sama an dauke.
Ko lokacin da tafiyarmu umara yayi, bayan sati biyu da tafiyar Ameerah kenan. Lokacin mun kai azumi na hudu kenan. Yaya yayi mata maganar zamu tafi ranar da aka dauki azumi na takwas, mu tsaya mu kwana a Kaduna, washegari mu wuce Katsina mu kwana. Ranar da aka kai azumi na goma zamu wuce Umra. Daga fari nayi zaton zata hau yin kalar dibar arzikin da tayi kamar da, amma ga mamakina maimakon tayi wani abu, kawai sai gyada kai da tayi ta mana fatan a dawo lafiya.
Shi kanshi Yaya sai da ya nuna alamun yayi mamaki, kafin ya girgije. Yace to tayi list din abubuwan da zata bukata kafin mu dawo. Nan ma tace babu komi.
Wannan karon kam sai da mamakinshi ya fito fili, yace “babu?”.
Tace “to duka-duka ko sati daya fa ba’a yi da kawo kayan provision ba. Bamu yi wani amfanin azo a gani da kayan ba”.
Yaya yace “to shikenan”.
Ranar da zamu tafi, haka ya dauko naira dubu dari cif ya dire mata a gaba. Yace tayi hidimar sallah. Tuni dama tare aka kawo mana kayan sallah da kayan kamun azumi. Manyan atamfofi da leshina, ya kuma hado mana da kudin dinki. Iyayenmu suma haka ya aika musu atamfofi da shaddoji har da kudin dinki. Hatta su Malam ma sai daya aika musu.
Duk da nima sai dana aika musu, da su kayan kamun azumi. Suka yi ta mana godiya da sanya albarka kuwa.
Kamar yadda yace, Kaduna muka tsaya muka musu shan ruwa. Janan ma ranar a gidan ta sha ruwa da yake Almunta baya gari. Muka yini muna hirar yaushe gamo. Da dan yaron cikinta ma kuwa, duk da taki yarda da zancen tana ta min kwana-kwana.
Su dukansu sunyi mamakin abinda ya faru da Ameerah. Abu ne na Ala wadai, amma su dukansu babu wanda yayi mata addu’ar banza ko yayi wata maganar da bata dace ba, sun dai jinjina abin, kafin suka yi addu’ar Allah ya kara shiryata da duk sauran ire-irenta.
Da yake da kayan sallah ta na taho, washegari kafin mu wuce zuwa Katsina, muka je wajen telarta ta auna ni, muka bar kayan dinkin anan.
Muna komawa gida muka wuce Katsina.
*☆⋆48⋆☆*
A gida muka sauka, da yake tare da Balarabe muke, Yaya ya tsaya suka gaisa da Baba, anan ma suka sha ruwa tare da Baban da Balarabe, sannan suka wuce masauki.
Tarba mai kyau muka samu wadda ban yi zatonta ba, ba daga Baban ba, ba daga matan nashi ba, ba daga yaran ba, kowa ya nuna farincikinshi da ganinmu har abin ya bani mamaki.
Sai bayan tafiyar Yaya sannan na fahimci cewa da wani abu a kasa. Tunda muka je, Aliyu da Ramata suna daki, tun lekowar da suka yi suka mana sannu da zuwa suka koma daki, basu kara lekowa ba.
Yanayin yadda na ganta ya tsorata ni, tayi wata irin rama, sai girman shekarunta ya kara fitowa.
Bayan mun kebe a dakin Maryam inda nan na saba sauka, na tambayata abinda yake faruwa da masu gidan. Abinda ta fada min ya girgiza ni.
Wai Aliyu aka kama yana saida ganyen Iblis. Jiya yan sanda suka zo unguwar aka kama gungun yan unguwar da suke shaye-shaye, ga namakinsu sai aka hada dashi. Har wajen karfe ukun dare suna police office din wai, da kyar aka bada shi.
Na kama baki ina jinjina kai kamar zanyi ihu, “garin yaya haka?”, na tambayeta, “ban sani ba”, itace amsar data bani.
Muna nan a dakin nata muna maida magana, Awwal ya leko yace in je dakin Baba yana kirana. Na dauki hijabita na saka na tafi. Shi kadai na samu a dakin nashi. Na zauna a kasan kujera, muka sake gaisawa dashi a nutse ba kamar ta dazu ba da aka yi ta a tsaitsaye.
Kafin ya daga baki ya sake magana, sai ga Alawiyya da Ramata sun shigo dakin kusan a lokaci guda, duk suka samu waje suka zauna. Na kurawa matar da tunda na mallaki hankalin kaina ta hana ni shakar numfashi mai dadi a rayuwata. Akwai wani lokaci a can baya, da ko sautin muryarta naji tana tashi, sai naji faduwar gaba ta ziyarceni. Akwai wani lokaci da zan mata kallo daya, inji babu abinda nake so da kaunar sake gani kamar in daga idanuna in ga gawarta shimfide a kasan.
Sai dai a yanzu da nake sake dubanta sai naji babu wannan tsoron, babu wannan tsanar, sai tsananin tausayinta daya lullube ni. Hakan kuma baya rasa nasaba da yadda naga ta makure a gefe kamar bera a gaban mage, kanta a kasa yake tunda ta shiga dakin, bata yi gigin daga ido ta kalli kowa ba.
Ba’a jima ba, sai ga Aliyu ya shigo shima, ya nemi waje can kusa da Ramata shima ya makure.
Sai da kowa ya nutsu sannan Baba yayi gyaran murya. Hakan yasa duk muka maida hankulanmu gare shi.
Ya fara da cewa “Ke Na’ilah ke da baki gida, ke kadai ce anan da baki san abinda yake faruwa ba…”, nan ya zayyane min duk abinda Maryam ta sanar dani.
Baba ya cigaba da cewa, “saboda haka na yanke shawara, ba zan cigaba da zama da tantirin yaro kamar Aliyu a gidan nan ba. Ba zai lalace ba, kuma daga baya yazo ya lalata min yara, ba zai yiwu ba. Don haka nace mishi ya fita ya bar min gida na tun a jiyan. Ban fada maka kada ka kuskura in dawo gidannan in gan ka ba?”.
Aliyun bai ce komi ba sai kara lafewa da yayi a jikin Mamanshi yana shesshekara kuka, yayin da Ramata din take share hawaye itama.
Alawiyya ta wurwusa ta matsa kusa da Baba, tace “Alhaji kayi hakuri da wannan magana da zanyi, amma matakin daka yanke kwata-kwata bai dace ba, ina ga da dai ka sake shawara”.
Baba yace “shawarar me zan sake? Zubda kimata da mutuncina yaron nan ya riga yayi, yanzu duk cikin unguwar nan kowa zancen yake yi. To zai zauna yayi min a gida kuma? Ba zan iya ba, ya tarkata nashi-i-nashi ya bar min gida kawai”.
Sai lokacin na samu kwarin gwiwar yin magana, nace “Baba kamar yadda Anty tace, wannan fa ba shawara bace. Zancen zubewar girma da sauransu, duk bata taso ba, tunda abinda dai ya faru ya riga ya gama faruwa, kuma ba’a dawo da hannun agogo baya. Abinda ya faru ya riga ya faru, sai dai a tari na gaba kawai. Amma korar Aliyu daga gidannan ba mafita bace, Allah ya gani. Baka tunanin idan ka kore shi din, maimakon ya saduda, sai hakan ya kara sanya shi yabi wata hanyar daban kuma? Duk kuma dai abinda zai yi nan gaba kana da alhaki akai, kuma duk inda zai je ya dawo dai, nan da shekaru goma ko dari, dole ya dawo gareka saboda danka ne, tsatsonka ne. Shi hannunka ai baya rubewa ka yanke ka zubar”.
Baba yace “sai dai in hannun baya damuna. Amma tuni zan yar da dan banza in huta. Tun yaushe Aliyu yake bata min rai? Makaranta baya zuwa daga ta boko har ta islamiyar, bai san komi ba sai daukar magana a cikin unguwa. Yau ya zagi wancan, gobe ya bugi dan wancan, shi kadai ranshi yabi ya addabi mutane ina dalili?”.
Nace “hakuri dai za ayi, shima ba zai kara ba”.
Baba ko in ce iyaye da dama, suna da wani hali na sangarta yaransu, to the extent that sangartawar zata wuce misali. Yara zasu lalace, su daina ganin kan kowa da gashi, wani abin dariya ko tausayi shine yadda hatta da iyayen nasu ma zaki ga basa jin maganar su. Sai labari ya sha banban, yaro yaje ya dauko magana, sai kuma anan iyaye suzo su ce basu san wannan ba. Su zo su kori yaran. To me kenan aka yi? Ihu bayan hari kenan. Maimakon tunda da sanya hannunka hakan ta faru, ka tsayawa yaronka ya koma gagara-badau, lokacin da yayi tashen tsageranci da rashin da’a ka tsaye mishi, maimakon idan sun dauko maganar da tafi karfinsu su sake tsaye musu, a’ah, sai suce sun janye hannunsu daga garesu.
Sun manta lokutan da suka tsaye musu suka dinga yin abinda suka yi din, har suke ganin babu wani ko wata wadda ta isa sai su.
Don bana manta lokuta da dama da mutanen unguwa zasu kai karar Aliyu wajen Baba, akan wani abu da zai musu, muma mun sha kaiwa ba sau daya ba, ba sau biyu ba, amma bai taba daga baki yace mishi don me? Ko kul ba.
To yanzu idan iyaye basu dauki responsibility din laifukan ‘ya’yansu ba, wanda idan aka yi duba tun tali-tali suna da kamasho a ciki, wa zai dauka?
Bayan doguwar muhawara da jeka-ka-dawo, da kyar muka samu ni da Anty Alawiyya Baba ya sassauto. Duk wannan abu da ake yi, Ramata da Aliyu na gefe in banda sharar hawaye babu abinda suke yi.
Daga karshe dai yace ya hakura, akan sharadin idan makamancin haka ta sake faruwa lallai zai kore shi. Ni dana kasance zabiya, ni nace naji na amince. Nan ya sake hada mu yayi mana nasiha mai shiga jiki, yace ya sallamemu.
Ina tashi, Ramata ta kamo hannuna. Kuka take sosai kamar wadda aka yiwa mutane, godiya take jera mana kamar harshenta zai fado kasa, “nagode, nagode, Na’ilah! Yau da ba don ke ba ban san yadda zanyi ba, Allah yayi miki albarka, nagode!!”.
Ni kam na ma rasa abinda zan ce mata, jiki a sanyaye na dinga binta da kallo har sai da tayi radin kanta ta sake ni, sannan na juya na fita daga dakin.
Kai tsaye dakin Aliyu na wuce, na same shi a gefen katifarshi a zaune. Zama nayi dirshan a tsakiyar dakin, magana muka yi mai tsayi ni dashi game da abinda ya faru. Ba karamin mamaki na ci ba lokacin daya fada min wai kudi yake bukata shi yasa ya fara saida tabar saboda yaga abinda yaran unguwar sa’anninshi suke yi kenan, kuma suke samun kudi.
Nace “kai kuwa me ka nema ka rasa haka?”.
Yace “to Baba baya bamu kudi, yanzu ko Mama baya bata. Kudin makarantarmu kusan term biyu bai biya ba, sai da aka koro mu. Kuma Mama bata da lafiya, in taje asibiti aka bata magunguna, Baba baya sai mata. Ya zamu yi?”.
Wannan a halin Baba kam ba abin mamaki bane, haka yake. Duk wadda baya dasawa da ita a cikin matanshi, to ba ita kadai ba, har ‘ya’yanta ma sai sunji a jikinsu. Na gani a kaina, hakan kuma ta faru akan ido na. Ina ga ina bukatar mu sake zama na musamman da Baba. Yana bukatar wani ya fahimtar dashi irin wannan rashin adalcin nashi, ba abu bane mai kyau. Sai dai dana sake tunanawa, sai naga ba hurumina bane hakan. Watakila Yaya dai zai iya shiga cikin maganar tunda duk cikinmu, baya jin maganar kowa kamar tashi.
Nan na zaunar da Aliyu, na fahimtar dashi cewa hakan fa ba mafita bace, sai jefa kanshi daya kusa yi a cikin halin k’ak’a-ni-kayi. Na tunatar dashi muhimmancin hakuri, da cewa ita rayuwar duniya ba lallai bane sai ka mallaki abinda kake so ba. Tunda ba duka kake samun komi ba, kuma idan kace kai sai ka mallaki komi to kai zaka kwana ciki kuwa. Na jima sosai a dakin nashi kafin na tashi na koma dakin Maryam.
Ina zuwa na tadda Kulsum, nan muka hau hirar yaushe gamo. Tana nan har an sanya musu ranar aure da wani lakcaran su. Sai da za’a rufe gida sannan ta mana sallama ta tafi.
Bayan munyi shirin kwanciya, na dauki waya na kira Yaya Mudatthir na zayyane mishi duk abinda ya faru. Yace Baban ya mishi waya a jiyan, amma bai sanar dashi hukuncin daya yanke ba. Mun jima muna tattaunawa dashi, daga karshe muka yi sallama dashi akan cewa cikin satin zai zo. Bayan mun kashe wayar, Yaya na kira muka raba dare muna hira. Muna gamawa ko barcin minti talatin banyi ba, na tashi sallar tahajjud.
Da asuba muka tashi ni da Maryam muka dafa abincin sahur. Bayan munyi sahur, Mazan sun tafi masallaci, mu kuma muka yi tamu sallar a daki. Na dauki Al-Kur’ani mai girma na fara karantawa.
Gari ya fara yin haske lokacin da Ramata ta fado dakin kamar an jefota, ni da Maryam duk muka bita da kallo cike da mamaki. Ta tsaya a bakin kofa muna kallon-kallo da ita. Maryam ce ta tambayeta, “Mama lafiya?”.
“Na’ilah kiyi hakuri!”. Itace kalmar data fara fita daga bakinta. Tsabar mamakin jin kalmar yasa na saki baki hangangan ina kallonta kamar wata sabuwar halitta.
Bata damu da kallon da nake jifanta dashi ba, ta fara cewa “nasan cewa bani da hurumin baki hakuri akan duk wasu abubuwa dana miki, nasan na aikata abubuwa da dama na rashin kirki a gareku, amma wallahi na aikata hakan ne cikin tsananin jahilci wanda kishi ya haddasa min. Amma yanzu na gane, na kuma dawo cikin hayyacina, don Allah ku yafe min abubuwan dana aikata muku”.
Har lokacin bakina a bude, bansan abinda yakamata in ce mata. Strangely, sai naji wata fahimta ta shige ni. Wani fannin na raina ya fahimci abinda tayi din. Ban sani ko hakan yana da nasaba da halin da nake ciki a yanzu bane. Zama tsananin mata irin Ameerah da Raheemah, zai sanyaka ka fahimci abubuwa da dama kamar halin da muke ciki yanzu da Ramata dai.
Akwai lokuta da dama, da tsabar kishi, son zuciya da zugar shaidan suka sha taso ni a gaba da wasu irin shawarwari da muggan sake-sake. Wadanda tsabar tsananin tsoron Allah da abinda zan tarar idan nayi abinda Ramatan tayi ne kawai yake dakatar dani, don haka ne na dage da rokon Allah akan ya yaye min irin wadannan abubuwa. Allah kuwa maji rokon bawanshi ne, a hankali naji duk wadannan sake-saken na daina yin su.
Nasan Ramata tabi zugar shaidan ne da son zuciya. Son zama da tauraruwar da haskenta bashi da wani tasiri balle hasken azo a gani.. Sai dai son zuciya irin nata ya janyo mana yin rayuwar kunci da wulakanci a lokacin daya kamata ace munyi mabanbanciyar rayuwa.
Sai dai idan na sake duba hakan da wani ido na daban, son zuciya irin nata ne ya tseratar dani daga aikata mugun halin data aikata mana ga sauran abokanan zama na. Allah ya sani, ina da damar yin hakan, ina da fadar yin hakan, sai dai tunanin cutar da wani ta hanyar data cutar damu yakI ya zauna min, na kasa yin hakan. Idan na tuna zafin da naji, idan na tuna tsananin kunar da naji, idan na tuno darare da dama da nayi su cikin kuka da bakinciki da takaicin abinda matar nan tayi a gareni, sai inji ba zan taba iya aikata hakan ga kowa ba. Ba zan taba iya so wani yaji rabi-rabin abinda naji ba.
Sai dai ban hakuri daga bakin Ramata, abu ne da ban taba zaton zanji daga gareta ba, ban kuma shiryawa hakan ba.
Don haka naci gaba da kallonta kawai, har ta gama fadin abinda zata fada, ta juya ta fita daga dakin. Shiru ya biyo baya daga nan, ni da Maryam muka hau yin kallon-kallo, kafin na maida kallona ga kur’anin da nake karantawa.
Zuwa lokacin dana gama, gari ya gama wayewa, yara sun tashi suna ta shigowa gaisuwar safe. Sai lokacin na bude gwangwanin alewar eclairs dana kawo musu, bayan sun gama karba sun fita, sannan fa na koma barci. Ban tashi ba sai wajen karfe sha biyu na rana, shima wayar Yaya ce ta tada ni. Bayan mun gaisa dashi, na tashi na fita tsakar gida.
Babu kowa duk suna daki. Nan na fada bandaki nayi wanka. Sai anjima da yamma zamu tashi, hakan ya bani damar gudanar da duk wasu shirye-shiryena a nutse.
*
Kafin mu tafi na kira Aliyu dakina, na bashi kudi nace washegari ya raka Mamansu asibiti a dubata sosai. In yaso koma menene daga baya, zan kirasu inji.
Har bakin motarmu suka raka mu, Ramata har da kukanta tana ta godiya. Aliyu ya bude min bayan motar na shiga, ya maida ya rufe. Har lokacin kalma daya bata sake hada mu da Ramata ba, saboda ban san abinda yakamata in ce mata ba.
Yanzu da nake kallonta, ita da dan nata da a da, babu abin wulakantawa a wajensu kamar ni, abu daya ne yake min yawo a ka, ‘lallai abinda ya baka tsoro, wata rana sai ya baka tausayi!’.
Muna first class ni da Yaya. Bayan jirgi ya gama lodi, aka fara sanarwar tashin jirgi. Kaina yana kan kafadar Yaya, hannuna na dama cikin nashi yana shafawa a hankali. Hankalinshi yana kan jaridar Vanguard yana karantawa.
Na lumshe idanuna a hankali kafin na bude su, ina kallon gajimare da muke ta ratsawa ta cikin tagar dake kusa dani. Na sauke wata doguwar ajiyar zuciya. Dana duba baya, shekara daya data wuce, ban taba zaton cewa yanzu war haka zan kasance akan kafadar mijina, Yaya Bilal, muna tsallaka Nigeria zuwa yin ibada a kasar Makkah ba. Idan na tuna gwagwarmayar da muka sha, da yadda abubuwa suka juye, har zuwa yadda aurenmu ya kasance, sai naji ina girgiza kaina kawai, hikimar Allah da ikonsa suna da ban al’ajabi.
Can kasar zuciyata, na kasa yakice wata murya da take mintsini na, ‘shin ban ga aya ba?!’.
Yaya ya shafo kumatuna da bayan hannunshi, hakan yasa na bude idanun da ban san na rufe ba, na sauke su a kanshi. I can’t help myself, duk lokacin da zan kalle shi, sai naji tali-talin yawon abubuwa a cikin cikina, tunanin how I’ve come to be this lucky yaki barina.
Yace “tunanin me kike yi ne haka, kin barni ina fama da takarda?”.
Babu tunanin komi nace “kai!”. Sau tari bana tauna maganganu irin haka kafin in furta su, Yaya Bilal has that effect on me.
Shi kanshi bai yi zaton amsar da zan bashi ba kenan, ya daga girarshi cikin mamaki, yana wani irin murmushi, “haba? Akan me?”.
Na kara gyara kwanciyata a jikinshi, nace “ta yadda aka yi ka fara so na mana. Tell me, love at first sight ce, ko kuma sai a hankali?”.
Yaya yayi shiru yana kallona kamar mai tunani, amma kuma har yanzu murmushi yake yi. Yace “kin tuna ranar farko da muka hadu dake?”.
Nace “sosai ma. Ranar da kazo ka daukemu ni da Janan ka kaimu Kaduna, lokacin bikinka da Ameerah idan ban manta ba”.
Ya girgiza kai, na kalleshi in confusion, “no? Ba lokacin bane?”.
Ya jinginar da kanshi akan seat din, hakan ya kara bani damar sake makale mishi.
Yace “zaki iya mantawa, amma ni ba zan taba mantawa ba. How could I?”. Yadda yayi maganar ne, yasa na daga kai na kalleshi. Idanunshi na kaina, cike suke da longing da ban taba katarin gani a cikin idanunshi ba.
“Akwai wata rana, da ban san dalili ba, kawai tsintar kaina nayi a cikin mota na tafi Funtua. Ban sani ba, tunanin Yaya Sa’a ne a cikin raina ko kuwa Janan? Na kasa mantawa. Sai dai duk wadannan tunanikan sun bi iska lokacin da nayi tozali da kyakkyawar halittar dana kusa bugewa da motata lokacin dana dora idanuna a kanta a karo na farko. Ban san cewa a take a lokacin tayi awon gaba da zuciyata ba sai da nayi nisa, nisan da ba zan taba iya dawowa daga inda na tafi ba har abada”.
Kallonshi kawai nake yi cike da alamun tambaya don ban fahimci inda maganganunshi suka sa gaba ba.
Ya kalleni yana murmushi sosai, da alamu ba karamin dadada mishi rai abinda ya tuno yake yi ba, yace “kin tuna watarana da kuka shiga staff quarters ke da Janan siyan wani abu, meye ma sunan?”.
Na zare idanu na kalleshi, mamaki kamar zai kashe ni, ta yaya ma aka yi na manta ranar?.
Watarana muka taba shiga cikin staff quarters, makotan gidan su Anty Sa’a a lokacin suna saida iloka, muka je saye. Ga takaicinmu muka samu babu, akan hanyarmu ta fitowa, muka ci karo da wani kare. Nan muka yi cak muna kallon-kallo dashi, yana shirin juyawa ya kara gaba, kawai Janan da dama tunda muka ganshi, ta fara rawar jiki, sai kawai ta dafe keya ta ranta ana kare. Shikuwa kare yace da wa Allah ya hada mu idan ba daku ba! Nan muka kafa tsere.
Tabbas, wannan rana itace ranar farko da muka fara haduwa da Yaya. Saboda kafin in san abinda yake faruwa, naji mota taja wawan burki, hakan ya tsorata karen ya juya a sukwane. Ni da Janan kuma muka tsaya muna maida numfashi kamar zamu amayar da kayan cikinmu.
Bayan mun gayawa Yaya dalilin daya kaimu nan, neman iloka, ya mana fada sosai. Washegari sai gashi ya dawo da iloka cike da bokiti. Daga wannan ranar duk lokacin da zai zo sai ya taho mana da ita.
Na maida kaina na kwantar a inda yake da ina murmushi, wani irin giddiness ya rufe ni, nace “wow! Lallai ka jima cikin tarkon so na. Amma me yasa baka taba fada min ba?”.
Yace “kece dai baki taba fahimtar duk hints din dana dinga nuna miki ba”.
Na kara daga kai na kalleshi, “wasu hints?”.
Kafada kawai ya daga. Don haka nima na komawa previous position dina, wasu sake-saken naci gaba da yi.
*
Zuwanmu Makkah, da sabuwar soyayyar da muka kulla ta sanadiyar confession din da Yaya yayi a cikin jirgi. Hakan bai hana mu yin wasa ko sakaci da ibada ba. Sosai muka dage wajen ibada da addu’a babu wasa balle kakkautawa.
Kwananmu goma sha biyar a Makkah, mun je Madina ziyara kwananmu hudu muka sake dawowa, tuni mun fara shirye-shiryen juyawa gida nan da kwanaki biyar wanda zai yi daidai da washegarin ranar sallah.
Mun fito daga wata babbar mall ni da Yaya, tsaraba ce na fara hadawa. Hannuwanmu cike suke da ledoji masu dauke da tambarin mall din da suna. Muna fitowa hasken rana ya dalle min ido, wani irin jiri ya kwashe. Da ba don Yaya daya taro ni da sauri ba, da tuni na kai kasa.
Ya dubeni cike da kulawa, “lafiyarki lau kuwa? Na kula tun jiya kike jin jirin nan. Ko zamu je asibiti ne?”.
Na girgiza mishi kai da sauri, “a’ah, ba wani abin damuwa bane. Ina ga yanayin weather dinne kawai”.
Ya bini da kallo kamar bai yarda da abinda nace ba, kafin ya gyada kai. Mota ya tarar mana, muka hau muka wuce masaukinmu.
Magana ta gaskiya Yaya bai kula da kyau ba, tun muna gida nake irin wannan jirin sai dai bai kai irin wanda nake yi yanzu karfi ba. Gashi tunda azumin wannan ya kama ban sha azumi ko daya ba, tun ina jiran al’adata yau ko gobe, har na hakura saboda lokacin yin ya wuce.
Ina so in yarda da zuciyata da take rada min ko dai? Kusan kullum. Amma ina tsoron disappointment. Ina tsoron kada in sanyawa raina abinda bashi bane, daga karshe ni kadai zan ji ciwon hakan. Don haka na kasa yarda da zuciyata, duk da signs din da nake gani.
Musamman idan na tuna abinda likita tace lokacin da nayi bari, cewa saboda yadda cikin ya fita ta karfi da tsiya, mahaifata ta dan samu matsala. Saboda haka samun ciki a gareni zai yi wuya, ko zan samu to gaskiya ba a shekarun nan na kusa ba.
Abinda yake kara sanya min sanyin jiki kenan.
*☆⋆49⋆☆*
Washegarin ranar da aka yi sallah muka dira a Kaduna da yamma, nan muka kwana washegari muka wuce Zaria da safe. Kafin mu isa Yaya ya sa an share bangarenmu an gyara shi sosai. Tunda muka isa na lalubi gado nake zuba barci, sai can bayan azzuhur na tashi.
Nayi mika a kwancen da nake, kasusuwan jikina suna amsawa suna tuna min gajiyar dana kwasa a cikin yan kwanakin wadannan. Abu na farko daya fara zuwa raina shine abinci. Kada ma dai cikina da yake ta kugin yunwa yaji labari.
Na samu na mike da kyar na zauna tare da jingina da jikin allon gadon. Kamar tana jirana, ina tashi Anty Sarah ta turo kofar dakin ta shigo. Tayi murmushi ganina a zaune, nima na mayar mata da murmushin.
Tace “har kin tashi ne?”.
Sai dana ja wata doguwar hamma na sauke sannan na amsa mata da ‘ehh’.
Tace “sallah zaki yi kafin ki ci abinci ko kuwa?”.
Na girgiza mata kai ina yar dariya, “barni dai in fara cin abincin. Irin yunwar da nake ji ai bana tunanin zan iya kara minti daya a zaune ba tare da wani abu ya shiga cikina ba”.
Tayi yar dariya, “abincin yana falo, ko zan kawo miki shi nan ne?”.
Na girgiza mata kai da sauri, “a’ah, ki barshi zan fito in ci. Bari in wanke bakina”.
Ta gyada kai, “to shikenan. Ina falon”, ta juya ta fita.
A hankali na zuro kafafuna daga kan gadon, sai dana dan tsaya a haka, jikina ya waye da jiri-jirin daya zame min jiki cikin wannan yan kwanakin, sannan na tashi tsaye. Na shiga bandakina da yake ta tashin kamshin freshner da antiseptic, na wanke bakina.
Falon na fita, kamar yadda tace, a falon na sameta zaune akan kujera. Rabi’ah na ta guje-gujenta a cikin falon. Ga kulolin abinci nan shirye a kasa an shimfida ledar cin abinci. Babu bata lokaci na zauna na fara zubawa, tun kafin in kai abincin bakina yawu ya fara tarar min a baki.
Anty Sarah tace “Yaya Bilal sun riga sun ci shi da Abban Mimah. Sun tafi can babban gida tun dazu”. Kai kawai na gyada mata, yadda gabadaya hankalina ya tafi kan abincin da yake gabana ai bana tunanin zan iya saurarar komi.
Anty Sarah tayi murmushi ganin yadda na dage ina cin abinci hannu baka hannu kwarya, babu sassautawa. Zuba shi kawai nake yi kamar wadda aka ce za’a kwacewa. Tace “ci a hankali, kada ki kware”. Na sake gyada mata kai.
Bata sake cewa komi ba, har na gama ci da shan abubuwan data ajiye min. Na ture kwanukan gefe tare da komawa na jingina bayana da kujera saboda jin yadda cikina ya cika tam.
Nace “ina Mimah kuwa?”, tunda muka iso sai yanzu muka samu damar gaisawa sosai. Saboda mutane da yadda idanuna suke a rufe da barci lokacin da muka iso, a tsaitsaye muka gaisa.
Tace “taje gida weekend”.
Bayan mun dan hiranta kadan, na tashi naje nayi sallah. Kafin in dawo har ta tattara kayan abincin dana bari.
Nace “da kin bari ma ai da na dauke”.
Tace “babu matsala wallahi, meye a ciki?”.
Na zauna akan kujera, wayata a hannu ina maidawa Janan sakon data turo min ina barci, bayan na tura mata muka cigaba da hira har take gaya min makota da wasu daga cikin ‘yan uwan Yaya da suka zo min sannu da zuwa ina barci.
A hankali naji zuciyata ta fara tashi, kamar zan amayo da abubuwan da naci. Nasan ba zan samu lemun tsami a cikin fridge dina ba tunda mun jima rabonmu da gidan.
Na cewa Anty Sarah, “ko zan samu lemun tsami a wajenki? Zuciyata take tashi”.
Anty Sarah ta kalleni cikin tunani, ko bata fada ba nasan ko tunanin me take yi. Nima sai ban tanka ba. Ta tashi ta fita, babu jimawa sai gata ta dawo da lemun tsamin.
Na karba na bare na fara sha. Kallona take tayi, kafin ta nisa tace “kin kuwa fadawa Yaya?”.
Na kalleta cike da alamun tambaya, “na fadawa Yaya me?”.
“Abin arzikin da muka samu mana”, ta fada fuska cike da murmsuhi. Kai na girgiza mata.
Take murmushin kan fuskarta ya bace, tace “me yasa?”.
Na daga kafada, “I just want to be sure. Bana son sanya mana rai akan abinda bashi bane”.
Tace “wata alama kike son gani bayan wadda ta fito baro-baro a jikinki?”.
Nace “na gansu nima, but we could be wrong!”.
Tana shirin dawo min da amsa, aka turo kofar falon aka shigo. Duk muka maida kallonmu ga kofar, ganin Yaya Bilal sai duk muka ja bakinmu muka dinke, daga ganinmu kaga wadanda suka sha jinin jikinsu.
Yaya yayi kasa-kasa da idanu yana amsa sannu da zuwa din da Anty Sarah take mishi, idanunshi kafe a kaina, ni kuwa na kara lafewa a jikin kujera kamar wadda aka kama ta nannaga karya.
Yace “Allah dai yasa ba gulmata kuke yi ba?”.
Anty Sarah tana dariya tace “haba dai Yaya, da girmanmu da komi? Kuma ma akan me zamu yi gulmarka? Kawai dai hirarmu ce muke yi irin ta mata”.
Ya zauna akan kujera tare da ajiye bakar leda a kusa dani, yana yar dariya, “to ina zan sani ne? Na ga daga shigowata kun kame baki kun dinke bayan kafin in shigo naji kuna hira. Idan ban tsammaci gulmata kuke yi ba, me zan ce?”.
Ta mike tsaye tana kade rigar jikinta, “to bari kuga inyi nan tun kafin magana ta zama babba. Na’ilah sai anjima”.
Cikin dariyar da nake yi na amsa mata. Ta sa kai ta fita.
Tana fita Yaya ya kalleni, “har kin tashi daga barcin?”.
Nace “ehh”.
Yace “fatan gajiyar ta sakeki? Don gobe nake so mu koma Abuja. Nasan ayyuka sun tarar min, kema kuma suna jiranki”.
Na gyada mishi kai, “zan iya maneji dai”.
Yasa yatsa ya shafo kumatuna cike da tsokana, kamar wata karamar yarinya, “sarkin langwabu. Ban san yaushe kika zama alangwaba ba wallahi baby, kwanannan kin cika son jiki”.
Na kuwa langwabe din, “kai Yaya!”.
Yayi dariya tare da mikewa tsaye ya fara tunkarar daki, “ga fruits nan hada mana. Bari in rage kayan jikin nan nawa”.
Ya wuce daki ni kuma na tashi na shiga kicin na dauko plate da fork.
Bayan anyi sallar la’asar, Yaya ya fita waje. Nima sai na kulle sashen nawa na tafi na Anty Sarah. Nan yan sannu da zuwa suka yi ta zuwa suna samuna har yamma sosai tayi. Muka shiga kitchen dinta muka dafa abinci. Anan muka yi dinner kafin muka koma sashenmu.
*
Sai wajen karfe hudu na yamma muka dauki hanyar Abuja, ko a wajen su Ummah bamu tsaya ba, kai tsaye can muka wuce.
Tunda garin Allah ya waye Raheemah take kiran wayar Yaya tana tambayar yaushe zamu iso? Akalla ta kira yafi sau biyar, yanzu ma muna daukar hanya sai data sake kira, yace mata yanzu muka taho. Cike da murnarta da doki tace “to Allah ya tsare hanya, Allah ya kawo ku lafiya”. Yace “ameen”.
Na bi wayar hannunshi daya ajiye bayan ya kashe wayar da kallo. Zuciyata na rada min wani abu sounds off da matar nan. Tunda muka bar gidan, kullum sai ta kira waya, ayi hira da ita faram-faram ayi sallama. Duk yadda zuciyata take rada min kan cewa kila ko tayi karatun ta nutsu ne, zuciyata ta kasa kwanciya da hakan. Nasan dai koma menene, tunda gidan zamu koma, idanunmu zasu gane mana.
Yaya bai ma kula da yanayin tunani dana shiga ba saboda yadda hankalinshi yake kan iPad dinshi, tun ma kafin mu koma gidan har ya fara aikinshi. Sai na maida kaina na kwantar akan seat tare da lumshe idanun, babu bata lokaci barci yayi awon gaba da ni.
Ban farka ba sai da muka shiga garin Abuja, sannan. Na gyara zamana ina taba bayan wuyana da naji ya dan rike. Yaya ya kashe hasken wayar hannunshi, da alama shima tunda muka dauki hanya bai ajiye wayar ba, ya bude gorar ruwan sona ya miko min. Babu musu na karba na kafa kai, sai dana shanye shi tas. Ya karba ya rufe gorar.
Balarabe yayi horn, maigadi ya taso da sauri ya bude gate din. Muka gangara da motar ciki, shi kuma ya juya ya maida gate din ya rufe kafin ya kwararo da gudu zuwa inda motar take kokarin yin parking. Ya budewa Yaya kofar motar yana ta zuba mishi ruwan sannu da zuwa, ni kuma Balarabe ya bude min. Duk muka fito daga cikin motar.
Su Balarabe da maigadi suna ta kokarin fito da akwatunanmu da tarkace daga booth, ni da Yaya kuma muka tasamma kofar shiga gidan.
Haka kawai naji gabana ya fara faduwa kamar ana buga ganga, muna tsayawa a kofar falon kuwa naji kaina yana wata irin juyawa kamar zan fadi.
Samuel wanda yake ban ruwan fulawowi da gyaran garden ya bazamo daga bayan gidan hannu rike da tsintsiya, da alamu shara yake ya taho gaisuwar ban gajiya.
Hakan ne ya dakatar damu daga bude kofar falon, muka tsaya suna gaisawa da Yaya. Bayan ya mana sannu da zuwa, ya juya.
Idanuna suka sauka akan matakalar dake manne da kofar wasu irin abubuwa kamar har da danko da lema, babu mamaki wani abu ne ya zuba a wajen. Da sauri na kira sunanshi, ya juyo yana kallona.
Nace mishi “don Allah dan sa tsintsiya ka share wajen nan, kamar yayi datti”.
Babu musu ya matso tare da sanya tsintsiya ya fara shara wajen, “to Haji…”.
Bai gama rufe baki ba aka turo kofar falon da sauri kamar za’a ballata, Raheemah ta fito a sukwane kamar wata sabuwar kamu tana ihun “kada ka share! Kada ka share!!”.
Amma ina! Aikin gama ya gama, tuni ya gama sharewa.
Ta ja tayi turus, muna kallon-kallo. Mu na mamakin abinda ya sanyata yin haka, ita kuma fuska cike da alamun tsoro.
Yaya yace “lafiya?”.
Ta kalleshi a dan firgice, kafin ta girgiza kai da sauri, “me? A’ah, babu komi. Dama turaren wuta ne na zuba a wajen”.
Yaya ya karya kanshi gefe guda yana kallonta, kafin ya tabe baki, “well, to ina ma amfanin sanya turaren wuta a waje? Muje ko?”.
Ya tura kai zuwa cikin falon na bi bayanshi. Strangely, babu wannan faduwar gaban da nayi ta ji dazu. Har Yaya ya gama shigo da kayanmu Raheemah na inda muka barota a tsaye. Sai da na kai akwatina daki na dawo daukar jaka sannan na ga ta shigo falon jiki a sanyaye.
A dan lokutan da muka yi bamu hadu ba, babu abinda ya canza daga jikinta. Ta sha kwalliyarta cikin wani tsadadden paper Swiss lace, daya daga cikin wanda Yaya ya dinka mana na sallah. Babu laifi kuma, sun matukar karbarta.
Kai tsaye dakinta ta wuce da sauri, kamar zata fadi, ni da Yaya muka bita da kallo cike da mamakin wannan halayya. Wa zai yi zaton irin tarbar da zamu samu kenan a yadda take ta faman dokin mu dawo dinnan?.
Yaya ya taimaka min na gama kai kayana daki, shi dama daga brief case dinshi babu abinda ya riko. Daga nan ya wuce dakinshi, ni kuma na fada bandaki don in watsa ruwa ko na warware gajiyar jikina.
Bayan na fito falo na sake fita. Ina zama, Yaya ya fito daga nashi falon sanye da jallabiya baka. Yadda fatar jikinshi tayi wani kyau, da yadda rigar ta bi jikinshi ta lafe kamar second skin, yasa ban san sanda na saki baki ina kallonshi ba har da karkace kai gefe guda. Yadda sajen fuskarshi ya kwanta mishi sosai…
Ban san ya iso kusa dani ba, sai dana ji iskan daya hura min ya sauka a fuskata, na lumshe ido ina murmushi yayin daya zauna a gefena da yake akan two seat nake.
Yace “wannan kallon fa baby? Na nawa ne kuma?”.
Na kyalkyale da dariya ina jingina da jikinshi, “yanzu don na kalleka har sai na wani biya?”.
Yace “ehh mana!”.
Na daga kai na kalleshi, “halalin nawa?”.
Shima ya kalleni, tare da sanya hannu yana dan jan hancina, “zakin baki ne zaki yi mun yanzu?”. Na sake yin wata dariyar ina kara kwanciya a jikinshi.
Raheemah ta fito daga dakinta, ba kamar dazu da take a hargitse ba, yanzu ta warware duk da daga gani zaka fahimci cewa murmushin dake kan fuskarta bai kai can ciki ba. Lullube yake da damuwa.
Bakinta washe da murmushi kamar zai tsage biyu, “marhabun lale sannunku da zuwa. Ya hanya? Kun sauka lafiya?”.
Bata nuna alamun tado zancen abinda ya faru dazu ba, don haka babu wanda ta tayar mata a cikinmu. Muka ce “lafiya lau”.
Tace “abincin ku yana kan dinning, ko nan zan kawo muku?”.
Yaya yace “sai na dawo daga masallaci”.
Ta kalleni, “ke fa Na’ilah?”.
Da fari kallonta nayi cike da mamaki da kuma alamun tambaya, banyi tunanin dani take ba. Da sauri na girgiza mata kai, “a’ah, nima sai anjima”.
Ta zauna akan kujera dake gab data Yaya, ta fara tambayarshi abinda ya wakana yayin zuwanmu umrah, nan suka cigaba da hirarsu.
Ni kuwa kallo kawai nake binta dashi, mamakina ya kasa boyuwa. Shi kanshi Yayan nasan ba karamin kokari yayi ba wajen boye nashi. Bansan abinda ya tsirar da wannan sabuwar halayyar tata ba, koma dai menene nasan raina baya gaya min da dadi. Nasan hakan baya rasa nasaba da yadda na saba da halayyarta ta mita da tankawa duk wani abu daya dangance ni.
Ana kiran sallah duk muka mike, Yaya ya wuce masallaci, mu kuma muka wuce dakinmu.
Bayan nayi sallah na kunce tsarabar da nayi, na dauki turaren kaya, na miski da ruwan zam-zam na leka har dakin Raheemah na mika mata. Ta amsa da fara’arta tana godiya. Na jima a kofar dakinta bayan ta amshi kayan ta rufe kofarta ina kallon kofar, kafin na juya na koma dakina.
Abinci ma a tsaitsaye na ci shi saboda cikine a cike yake. Dambun kifi dana nama Anty Sarah ta hado ni dashi cike da wasu manyan plastic rubbers. Shi nake ta ci tunda muka iso abina.
Muna gama cin abincin na musu sallama na wuce dakina, nasan yau dai Raheemah ce take a turaka. Kayan jikina kawai na cire na saka na barci na kwanta. Ina kwanciya kuwa barci ya daukeni, ban tashi ba sai da asubahi da Yaya ya shigo ya tashe ni sallah.
Da wuri na shirya shiga asibiti. Jakata dam da kananun turaruka da robobin zam-zam na tsaraba. Ina kan dinning ina hada ruwan shayi, Yaya da Raheemah suka fito. Hannunta daya rike da jakar shi ta wajen aiki, dayan kuma ya sarkafo daya hannunshi. Na kauda kaina gefe ina kokarin danne wani abu mai daci da yake kokarin taso min. Idan nace bana jin irin haka a duk lokacin da naga wata daga cikin matan Yaya tayi kusanci dashi, kamar haka, kai koda bai kai haka ba, to nayi karya. Ina ji, sai dai karfin zuciya da tsananin iya danne zuciyar tawa ne yasa nake iya kauda kaina gefe guda.
Nan suka ja kujera suka zauna. Bayan mun gaisa, Ameerah ta zubawa Yaya nashi abincin. Ni kam ina gama ci, na dauki jakata na musu sai anjima. Sai dai tun kafin in kai ga tashi tsaye Yaya ya tsayar dani. Yace “bari in gama sai in sauke ki”.
Ban ce komi ba, na koma na zauna. Again, nayi zaton zata yi magana ko wani abu, nan ma ta bani mamaki da naji tayi shiru. Bai ma dauki wani lokaci ba ya gama cin abincin, nan muka mike muka fita.
A asibiti bayan na gama gaisawa da duk wasu wadanda muke gaisuwar mutunci, ganin babu aiki sosai yau a ward din yasa na yiwa ofishin Dr. Anita tsinke. Bayan mun gaisa da ita a mutunce kuma cike da girmamawa, na yi mata bayanin duk wasu signs da nake gani a jikina. Bayan tayi min wasu tambayoyi da kuma gwaje-gwaje, ciki sati biyar ya bayyana.
Ba karamin mamakinta ta nuna ba, cikin jijjiga kai tace “Allah kenan! Wannan abin mamaki da me yayi kama? A yanayin yadda kike dinnan, ban taba zaton zaki iya daukar ciki a cikin shekaru biyu masu zuwa ba wallahi. Kai congratulations!”.
Nayi murmushi ina jina kamar ina yawo a sararin samaniya. Duk da cewa nayi zargin haka, amma na kasa yarda da abinda naji yanzu gaskiya ne.
Tace “sai dai you’ll have to be extra careful gaskiya, saboda cikin jikinki yana bukatar kulawa da takatsantsan. Kin fahimce ni?”.
Na gyada mata kai. Nan ta zauna ta kafa min dokoki, irin ayyukan daya kamata in dinga yi, da wadanda yakamata in guda, irin abubuwan daya kamata in dinga ci, da dai sauransu. Nan na mata sallama na wuce pharmacy na sayi magungunan data rubuta min. Throughout jin jikina nake kamar ba nawa ba. Da an dan motsa kadan, sai in kai hannuna saman cikina ina shafawa.
Lokacin tashi yana yi, na koma gida.
Bayan na ci abinci na cire uniform dina, na zauna a gefen gado ina tunanin ta yadda zan sanarwa da Yaya maganar wannan cikin. A haka har barci ya dauke ni, sai wajen karfe hudu na tashi.
Nayi sallah na fita waje don samawa cikina abinda zan ci. Babu kowa a falon, sai dai daga jin sautin muryoyin dake fitowa daga dakin Raheemah, nasan baki tayi.
Na bude fridge na ciro fresh fruits da yoghurt na koma dakina. Har Yaya ya dawo ban fita ba.
*
Fiye da kwana uku kenan, amma na rasa ta yadda zan isar da sakon cikinnan wajen Yaya, na kuma rasa dalilin da yasa na kasa din.
Safiyar ranar juma’ah, na gama shirin tafiya wajen aiki. Na fita falo da dan saurina ganin cewa naso in makara yau.
Yaya na zaune akan kujera yana latsa wayarshi, babu alamun Raheemah wadda take yin girki yau, babu alamun kayan kari.
Na dan yi turus, kafin na karasa kusa da Yaya na zauna tare da gaida shi.
Ya amsa yana bina da kallo, nasan yadda na murmure da wata irin kiba dana fara yi ne yake kallo yana mamaki. Bai kai ga amsawa ba Raheemah ta fado wajen kamar an jefota. Tun kayan barcin jiya ne a jikinta bata cire ba. Kanta babu dankwali, gashin kanta ya cure waje guda.
Taje gaban Yaya tayi tsaye har da kama kugu, duk muka bita da kallon mamaki.
Cike da tsiwa da alamun dibar albarka tace “Bilal!”.
Ba Yaya kadai ba, ni kaina sai dana bude baki na bita da kallon mamaki. Bana tunanin ko Ummanmu tana ambatar sunanshi haka balle ayi maganar Yayye ko kannenshi, ayi zancen matar aurenshi. Nasan kila dai abokanshi na kiranshi haka.
Ya kalleta a dage, “lafiya?”.
“Lafiyar kenan, lafiya ce ta kawo haka. Sakina zaka yi!”. Ta furta hakan cikin saurin murya da mazarin jiki kamar wadda take shaking.
Yaya yace “ban gane ba? Ke lafiyarki lau kuwa? Me ke damunki ne?”.
Tace “ka ga bawan Allah, ba wasu maganganun banza na tambayi ka min ba, idan kana son arzikin kanka, to kawai ka miko min takardata in kara gaba. Dole ne? Nace auren naka dole ne wai?”.
Saboda tsabar mamaki Yaya kasa magana yayi, kawai zama yayi yana kallonta, kamar yadda nima na sankame a zaune.
Tace “ni fa bani da lokaci kaji? Ka sallameni don Allah”.
Yaya yace “ba zaki zo kai tsaye ba kawai ki ce in sallameki, akan me? Akan wani dalili?”.
Tace “saboda na gaji da zama da kai, zama da kai haukata zai yi. Kawai ka sake ni, ka sakeni nace!!”. Zuwa yanzu karaji kawai take yi. Tana rufe baki ta juya zuwa dakinta a sukwane, bata jima ba ta dawo hannu rike da takarda, ta jefa mishi jikinshi, “maza maza rubuta min in wuce Malam”.
Wani abu yayi snapping a jikin Yaya, kamar wani wanda aka yi possessing, kawai ya dauki takardar da biro ya hau rubutu, ko sauraren ihun kada ya aikata abinda ba’a so a aikata a cikin aure da nake mishi bai yi ba. Yana gamawa ya mika mata, ta warta tana karantawa cikin yatsina fuska.
“Saki biyu? Karya kake wallahi, wallahi sai ka cike min shi. An gaya maka wata tsiya nake kwasa a gidanka da zata sanya ni son dawowa gidan? Kai yau fa idan baka sallameni ba wallahi sai ayi yakin duniya a cikin gidannan! Kaji ma wani rashin mutunci!”. Ta hau wasu maganganu marasa kan gado da ma’ana.
“…Dama boka sai da yace kada in bari iska ta share wannan maganin, wannan shegen tsinannen mai sharar wannan yazo ya share shi. Dama sai da yace kaikayi koma kan mashekiya ne, kaina zai dawo muddin bata tsallaka shi ba. Saki uku yakamata ka mata, ni me yasa ba zaka min saki ikun ba?”.
Yaya ya tashi tsaye a hankali yana fuskantarta, “me kika ce? Me kike nufi?”.
Ta kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya kamar wata mahaukaciya, “to ina ruwanka da abinda nace? Abinda za ka damu dashi shine karashen saki na. Kasan wani abu? Boka ya bani wani magani yace in jika shi ya kwana uku, sai in tace in ba waccan sakarar matar taka data kunshi ciki, tana wani daga kai sama tana tutiya ita zata haifi magaji…”
Ni da Yaya muka zare idanu muna kallonta, saboda nasan inda maganar ta nufa. Bata damu da yadda muka yi ba taci gaba,
“kasan me nayi? Sirinji na sayo na zuki ruwan maganin, nawa mangwaron da zata sha allura. Hahhha!”. Ta sake wata dariyar. Tuni kwalla ta gama wanke min idanuna.
“Sakara, ina kallonta har wani rawar jiki take yi zata sha mangwaro, bata san cikinta zata fitar ba!”.
Na kai hannu bakina na rufe cikin kokarin danne kukan daya taso min, ita kuwa taci gaba da sheka dariyarta.
Karan marin da Yaya ya zuba mata, sai daya karade falon gabadaya. Yace “dama kece kika zubar min da cikina? Kodayake, I’ve had my suspicions tun daga farko. Saki kike so ko? To kije na karasa miki sakin na uku, meye amfanin zama dake dama? Tunda na aureki na rasa walwala a cikin rayuwata, ban ma san dalilin da yasa na aurekin ba, amma hakanan nake hakuri ina zama dake. Kuma abu dayan da yake sanya ni farinciki ki ce zaki raba ni dashi? Ki fitar min daga gida yanzun nan, kada ki kuskura in dawo gidannan in same ki don wallahi sai na wulakanta ki. Kada kuma ki daukar min ko allura daga cikin kayana!!”.
Yaya ya fita daga cikin falon da sauri kamar wanda zai tashi sama, ya barni sarkafe a tsaye ina kallon Raheemah da take ta dariya babu kakkautawa babu alamun zata daina.
Sai gashi kuma ya dawo, “kin san me? Fitar min daga gida yanzun nan, kada ki kuskura ki sake dawowa!”.
Sai lokacin ta dakata da dariyar da take yi, “yo dama ko baka ce ba fita zan yi. Gidanka da kayanka din banza dana wofi?”. Ta shige dakinta ta fito da gyale a hannu daya, purse da waya a hannunta daya.
Yaya ya saka ta a gaba kamar wata barauniya har bakin gate, sai data fita daga gidan sannan ya juya yana gayawa maigadi kada ya bari ko jingina da gate din gidan tayi balle ta kai ga shiga. Maigadi da rawar jikinshi yace “an gama Alhaji!”.
Kawai sai ta zube kasa ta fashe da kuka, kukan ihu bayan hari, kukan nadama da bata da amfani. Tana ba Yaya hakuri, wai don Allah yayi hakuri ya maidata, sharrin shaidan ne. Yaya ko kallonta bai kara yi ba, ya ja hannuna zuwa cikin motarshi ya tada. Maigadi ya bude mishi gate ya fita a sukwane, muka wuce Raheemah tsugune anan, crying her heart out.
☆
Wajen aikin su Yaya muka wuce. Kai tsaye ofishinshi da yake hawa na goma sha biyu muka wuce. Muna shiga ya dauki land-line ya kira secretary dinshi yace tayi oda din abinci. Ya zauna akan kujera yana maida numfashi.
Tashi nayi tsam na koma kusa dashi na zauna, na kamo hannunshi na rike a hannuna ina shafawa soothingly. Gabadaya ya ma kasa magana, mun jima a haka, kafin ya iya daga baki. Maganganu suka fara fita daga bakinshi kamar ana turo su, duk akan yadda Raheemah ta cuce shi ne.
Ban ce mishi komi ba sai hakuri kawai da nake bashi har ya dan nutsu, nace mishi “ka daina blaming dinta, abinda Allah ya kaddaro dole sai ya faru babu makawa, babu kuma tsumi balle wata dabara ta mutum. Raheemah ta saka min magani ko bata saka ba, dole cikin jikina ya fita tunda Allah bai kaddaro zai taka kasa ba. Don haka ka daina damun kanka don Allah, don’t beat yourself for it”.
Ya kalleni, “for real baby? How are you this calm? Da kunnenki fa kika ji abinda tace, ita ta zubar mana da ciki. Kin kuma ji abinda likita tace, that ba lallai ki iya kara samun wani cikin ba cikin lokutan nan”.
Murmushi na sakar mishi mai sanyaya zuciya, na kamo hannunshi na dora a saman cikina, nace “saboda shi Allah ba azzalumin bawa bane, baya kuma dorawa rai abinda ba zata iya dauka ba. Yasan abinda yake cikin zuciyoyinmu, ya kuma fimu sanin cewa muna bukatar ganin sanyin idaniyarmu a gabanmu…”.
Nayi shiru ina kallonshi, ina jiran yayi calculating din abin da kanshi. Ba’a jima ba kuwa ya gama tarawa da ninkawa, ya kalleni, “kina nufin..?”.
Na gyada mishi kai a hankali ina murmushi, gefe daya kuma ina danne kwallar data ciko min ido.
Bakinshi rawa yake, da kyar ya iya kakaro kalmar “how… wata..?”.
Nace mishi “sati biyar”.
Daga nan bai ce komi ba, sai janyo ni cikin jikinshi da yayi ya rungume. Ba sai yayi magana zan san yana cikin tsananin farinciki ba, saboda na sani, wani farincikin yafi karfin ka daga baki ka bayyana shi, saboda duk kokarinka da iya bayyana abu, farincikin nan ba zai taba iya bayyanuwa ba. Halin da Yaya yake ciki kenan a halin yanzu.
Sai da aka kawo abincin da yace a kawo, sannan ya zameni daga jikinshi, yadda ya maida ni cikin kujerar ma ya ajiye kamar wani kwai kadai yasa na bi bayanshi da kallo cike da murmushi, kaunar mijina tana kara dabaibaye ni.
Ya amso abincin ya dawo, da kanshi ya dinga bani abincin nan har na koshi. Daga nan kuma muhawara muka hau tafkawa akan gida zan wuce in huta ba wajen aiki ba, da kyar na samu na iya fahimtar dashi lafiyata lau, kuma zan iya zuwa wajen aikina. Sannan fa ya saka ni a gaban mota ya kaini har ward dinmu, bayan dogon bayanin in kular mishi da kaina fa da baby, ya juya ya tafi. Ya barni da su sister Hajara da suke ta sheka mana dariya.
*
Janan tafi minti biyar tana ihu da shewa, har sai dana kai ga kauda wayar daga kunnena kafin ta kai ga kassara min ji na ina zaman lafiya. Sai data gama ihun murnar, sannan kuma ta hau zuba hamdala, “kai Alhamdulillahi, Allah na gode maka! Yau ina zan kai farinciki a cikin rayuwata?! Finally, Allah ya raba mu da bakar kaska, zamu huta dai. Gari ya waye dukan duhu na yayewa!!”. Ta karasa maganar da take yi cikin sautin wakar gari ya waye.
Hakan yasa na saki dariyar da ban shirya ba. Na dawo gida daga wajen aiki. Duk da cewa ba yau na saba dawowa na tarar da gidan babu kowa ba, sai dai wannan karon da banbanci. Wannan karon nasan cewa komin dare babu wadda zai dawo, zan ci gaba da kasancewa ni daya, ban sani hakan ko abin murna da farinciki bane a gareni ko kuwa na jajantawa?
Janan itama tayi dariyar, “Malama kada ki fuske mana, nasan ran nan naki yau fari tas kamar likkafani”.
Nace “ke fa baki da kirki wani lokacin wallahi, likkafani seriously?”.
Ta kwashe da dariya. Ina tunanin yau dai ba za’a samu yin hira mai ma’ana da ita ba, don haka nace mata taje taci gaba da abinda take yi kawai.
Tace “shine don wulakanci ranar nan kika ce wai baki da ciki?”.
Nace “waya fada miki ina da ciki ne?”.
“Dalla can, an gaya miki zancen duniya yana buya ne? Zancen cikinki ai ya gama zagaye gari da dangi yanzu, har yaron goye yasan da maganar”.
Na girgiza kai kawaI, na manta ba’a maganar sirri da Yaya, musamman wadda ta danganci wannan.
Nace “to naji, je ki cigaba da soyawa maigidanki cin-cin, nima abinci zan zo in dafa mishi”.
Ina jin tana guna-gunin wai kada in mata gorin miji fa, na kashe wayar kawai ina dariya.
☆⋆50⋆☆
Finale
Watanni goma sha uku kenan bayan haka, na samu kaina tsaye a kofar gidan a can cikin unguwar Tudun Wada cikin Zaria. Gida ne kadaran-kadahan, amma zaka fi saka shi cikin jerin gidajen ya-ku bayi. Gabadaya gine-ginen unguwarma haka take, kwata, bumps, ramuka da bola sunyi yawa a wajen.
Muhaaseen, diyata mai kimanin wata biyar dana haifa watanni biyar da suka wuce, tana sakale a kan kafadata gefen damana. Sunan Mamata marigayiya taci. Hannunta rike gam da gululun kwalliyar dake jikin jakata tana ja tare da yin wakokinta na yan yara wadanda basa taba kin kawo murmushi kan fuskata. Yanzunma murmushin nake yi a tausashe, kauna ce ta uwa da d’iya Allah ya sanya mana, ko a halin da take ciki na yarinta, ta sanni sosai. Na kara sakin wani murmushi a karo na barkatai, tare da manna mata sumba a gefen kumatunta. Tana jin motsi na tayi saurin juyo da fuskarta, tare da kamo lebbana tana tsotsa, na saki dariya a hankali, gefe guda kuma ina kai hannu ina kara buga kofar gidan.
Bayan wasu dakikai, har na fara tunanin kila ko babu kowa a gidan. Ina shirin juyawa kenan, naji ana taba kofar da daga gani wani katon abu aka sanya daga ciki aka tokare saboda yanayin yadda kofar ta nuna, taga jiya da yau sosai, babu alamun zata iya daukar kwado ko makulli daga ciki.
Wata siririyar bakar mata ta bude kofar, muka tsaya muna kallon-kallo da ita. Yadda ta zare idanu tana kallona cikin wani yanayi mai kama da mamaki da kuma tsoro da shock yasa na kara kallonta sosai, a zuciyata ina tunanin ko na santa?.
Murya na masifar rawa ta ambaci sunana, “Na’ilah?!”.
Sai a lokacin ne fahimta ta saukar min, nace “Raheemah ce?”.
Tayi kasa da kanta a kunyace, kafin ta dago tace min “shigo mana!”. Ba musu na daga kafa na bita cikin gidan.
Kwanaki masu yawa da suka wuce, lokacin da naje Kaduna haihuwa, nake jin labarin hatsarin daya aukawa Raheemah din da ‘yan’uwanta a hanyar Nijer. A cewar wadda take bada labarin, mahaifiyarsu a take ta rasu, su kuma sun samu sun fito da kyar, rabin jikin Salame ya kone da wuta, Raheemah kuma Allah ya takaita ta fita ba tare da wasu munanan raunuka ba sai tsagewar kashi da kurjewa nan da nan kawai.
Mummunan hadari ne motar golf din tayi da wata babbar motar mai, Allah ne kadai ya nuna ikonsa da har wasu suka iya fita da rai.
Tun a wancan lokacin naso zuwa yi musu gaisuwa kwarai, Allah bai nufa ba. Sai yanzu da muka shigo Zaria jiya ni da Yaya. Wani babban aminin Babansu ne tun yarinta yayi rashin lafiya har aka kwantar dashi a asibiti. Bayan an sallameshi ne Yaya yace zai zo ya duba jikin nashi ya kuma ga ‘yan’uwa, nima na nuna sha’awar ina so in biyo shi. Ko babu komi nima na jima rabona da Zaria.
Can ainihin gidansu na Hanwa na taba zuwa, aka ce min ai tun bayan rasuwar mahaifiyarsu suka koma wajen mahaifinsu da zama. Don haka na juya akalar tafiyar tawa na taho nan, da kyar da kwatance na karaso. Wai don ma mahaifinsu ba boyayyen mutum bane a unguwar.
Tana tafe ina binta a baya, yanayin gidan kawai da suturar jikinta nake karewa kallo, tabbas, babu wanda zai kalli Raheemar dake gabana yanzu yayi tunanin hadata da Raheemar baya. Wato kawai a duk halin da mutum ya tsinci kanshi a rayuwa, ya godewa Allah ne.
Dakin data kaini yafi kama da akurki maimakon falo, babu komi a ciki sai tarkacen kaya iri-iri, daga kwanukan abinci, bokitai, kayan wanki, gasu nan dai birjik kudaje na bi abin babu kyan gani. Ta dauko wata yamutsattsiyar tabarma ta shimfida min a tsakiyar falon, na zauna ina kara kallon wajen.
Tsayawa tayi kikam a kaina tana kallona tana faman susar kai kamar mai fama da kwalkwata, “me ya kawo ki nan wajajen?”.
Sai lokacin na maida kallona kanta, “naji rasuwar Momcy ne shine nazo muku gaisuwa. Ya hakuri? Allah ya jikanta”.
Maimakon ta amsa min kawai sai naji ta saki dariya, “hahhh.. Su Momcy fa lokaci yayi, hmm!”. Ta wani ajiye numfashi. “Ai in gaya miki, labarin wani zazzafan malami muka ji acan cikin Nijer, shine fa muka kama hanya muka tafi. Muka je ya bamu magunguna, wanda zai sa Bilal ya sake ki ya manta dake da cikin jikinki ni kuma ya maida ni, ita kuwa Halimo ta karkato hankalin wannan shegen tsinannen mijin nata kanta, kawai ba sai muka ci karo da motar mai a hanya ba? Sakaran direba kawai, yana ta wa Momcy surutu akan ta bashi lambar wayarta ya hada mu da motar. Dan iska!”. Ta ja tsaki kafin ta kwashe da dariya.
Ni kuwa da nake ta binta da kallo cike da mamaki, na sake ware idanu ina kallonta. Dama naji Janan tace wai ance tun bayan rabuwarsu da Yaya, kamar kwalwarta ta tabu haka take, ban tabbatar ba sai yanzu. Ta kalli Muhaaseen da tunda muka shiga gidan ta makalkaleni, haka take duk lokacin data ganta a gaban mutanen da bata sani ba.
Ta zare ido, “laa, wannan ce diyar da kika haifa? Amma fa kyakkyawa ce!”. Ta kai hannu kamar zata dauketa, yarinyar tayi saurin kara makalewa a jikina, ni kuwa na sanya hannu na kara riketa tsam a jikina, a can kasan raina ina cewa Tubarkallah. Duniyar yanzu baka san bakin mutane ba.
Ganin na riga na gama yin abinda ya kawo ni, ga wani irin wari da yake tashi a cikin falon da yake kokarin tasar min da zuciya, yasa na mike tsaye ina cewa “bari mu tafi, sai anjima”.
Tace “da wuri haka?”.
Na kalleta cikin rashin abin cewa, idan na tsaya mai hakan zai kareta dashi?
Tace “to shigo ki duba jikin Salame mana”.
Bata jira nace komi ba ta tunkari wata kofa, cikin sanyin da jikina yayi na bi bayanta.
Ina shiga dakin nayi baya da sauri, wannan warin da nake ji a falo sama-sama ya bugo ni full force. Sai lokacin na fahimci daga inda warin yake fitowa. Daga inda nake na hango Salamen kwance acan kuryar dakin kamar kayan wanki akan shimfida, rabin jikinta lullube da mayafi inda aka sakaya private parts dinta.
Naji wani irin tsoron Allah ya kamani a lokacin, lallai shi dai mutum ba a bakin komi yake ba a wajen Allah.
Kamar yau ne fa, suka tareni suna min dibar albarka a cikin gidan aurena, akan mijin da nake aure. Yanzu dana duba baya, lallai ba karamin lokaci bane ya wuce, amma kuma a cikin kaina sai nake ganin kamar yau hakan ta faru.
Da kyar na iya karasawa kusa da ita, da alama ma barci take yi. Itama gefenta kwanuka ne birjik a ajiye, wasu ma daga ganinsu ba karamin lokaci suka dauka anan ba.
Nace “har an sallameku daga asibiti ne?”.
Tace “ina fa! Koro mu suka yi saboda babu kudin gado dana magunguna. Ni kuwa nace aikin banza kenan, muka maidota gida. Ai yanzu maganin gargajiya ma ake mata. Shima kwana biyu dai an daina bata ma”.
Na gyada kai a hankali, ina so in kara watso mata wata tambayar, amma bakina ya kasa budewa, don haka na dinke bakin nawa kawai na mike tsaye. Ina ji Raheemah ta biyo bayana tana wasu surukai dana kasa fahimtar abinda take cewa, na dai tsinci sunan Salamen da kuma zagin da take dankarawa.
Na kara rike Muhaaseen sosai ina kokarin sanya takalmina, wani zagi data saki ne yasa na daga kai na kalleta cikin mamaki. Tace “kan ubar nan!! Wannan shegen hadadden takalmin fa? Zai yi dubu nawa? Kai, wallahi dama ki bani shi in dinga kwalliya dashi abina”.
Ni yanzu tsoro ma take bani kuma, yadda tayi tsaye a kaina tana watso min hakoranta da tsabar rashin wanki yasa suka yi wani yalo-yalo, gani nake kamar a kowane lokaci zata iya kawo min mazga. A karo na farko na fara tambayar kaina tsautsayin daya kawo ni nan. Musamman idan na tuna ta yadda ma aka yi Yaya ya barni na zo gaisuwar nan.
Ban ce mata komi ba, na tunkari kofar fita da sauri, ta biyo bayana. Muna gab da kofar gidan hayaniyar yara ta kusantomu, ihu kawai kake ji da kururuwa.
Haleemo da itama babu banbanci tsakaninta da Raheemah, duk da ita suturar jikinta da yar dama-dama akan ta Raheemah, ta fado gidan hannu rike da fararen manyan plastic bokitai da sauran shinkafa da tarin kabeji a ciki. Tsinin dake cikinta zaka fara gani kana dora idanu a kanta.
Waka da shewar da yaran suke yi ta kara yawa,
_’Yar iska taki zaman aure, daga talla sai yawon iskanci!_
_’yar iska tayi cikin shege…!_
Ita kuma tana korarsu da kayan hannunta tana dankara musu zagi da tsinuwa, har dai Allah ya bata sa’a ta shigo gidan ta maida kyauren ta rufe da sauri tare da daukar wani gingimemen dutse ta jingina da jikin kofar.
Tana juyowa ta kallemu tayi turus! Ta kalli Raheemah tace “wannan fa wacece?”.
Raheemah din ta watsa mata harara da sauri, “to uwar yan tsegumi, ina ruwanki da bakuwata?”.
Ta tabe baki, “jibeta sakara kawai, banza mai tabin kwakwalwa, to sai me don kinyi bakuwa? Daga gani ma kuskuren gida tayi ba wajenki tazo ba don daga gani bata yi kama da irinki ba”.
Raheemah ta tunzura da abinda tace “na dai gode Allah, duk da tabin kwalwar tawa dai ban je nayi cikin shege ba!”.
Ta daga baki kamar zata yi magana, sai kuma ta fasa, tayi cikin gidan tana “oho miki dai, mahaukaciya”.
Ba shiri na kama dutsen nan na janye da sauri na fita daga gidan, Raheemah ta sha gabana tana wasu yan soshe-soshe.
“To Hajiya Na’ilah, na gode ko? Yaushe zaki sake dawowa? Gashi kin zo ko ruwan sanyi ba’a baki ba. Nasan ba zaki iya shan ruwan randa ba, ni kuwa bani da ko sule balle ko na fiya wata ne a sayo miki”.
Ganin take-taken bata da alamar rabuwa dani don wasa da kuma abinda take hinting, yasa na zage jakata na ciro kudin da ko kirga su banyi ba, na mika mata. Ta warta kamar wadda take tsoron zan kwace ta jefa su cikin rigarta. Sai data tabbatar ta boye kudin sannan ta juyo ta hau zuba min godiya, tana lissafo abubuwan da zata sayo taci dasu ta hana ‘yan uwan. Ban kara cewa komi ba na juya da sauri, ina ji kamar ma in sheka da gudu. Jindadina daya, da bata sake biyo ni ba.
Na bude wajen direba a motata Benz, ruwan ash mai haske sosai daya zama kamar white-gold, wadda na saya da kudina da albashina duk da dai sai da Yaya ya min ciko, lol.
Na maida kofar na rufe, na kwantar da Muhaaseen a seat dinta dake bayan motar. Sannan na sauke wani dogon numfashi da ban san na rike ba.
Sai dana nutsu, sannan na tashi motar tare da ja na fita daga cikin unguwar a hankali.
*
Na kwankwasa kofar dakin Yaya sannan na tura kofar na shiga.
Yana zaune a tsakiyar dakin akan carpet, Muhaaseen na kwance akan cinyarshi tana yan wasanninta na yara. Laptop dinshi da tarin takardu da jaridu shimfide a gefenshi suna jiran ya karkata hankalinshi garesu. Hankalinshi baya kan su though, kai gabadaya ma baya cikin dakin. Idanunshi na kan Muhaaseen, kamar wanda yake kula da duk wani motsi da tayi, sai dai daga gani kawai idanunshi ne suke kallonta, amma gabadaya hankalinshi baya ma cikin dakin. Tuni yayi nisa a cikin duniyar tunani.
A nutse na ajiye farantin dana shiga dashi a kusa dashi. Karamar kettle ce dana zuba shayi a ciki, sai fresh grapes da berries a cikin wani bowl.
A hankali na kai hannu na dauke Muhaaseen daga jikinshi. Yayi firgigit! Ya zabura yana kallona a dan rikice.
Na kalleshi cike da alamun tambaya, kusan kwananmu takwas da dawowa daga Zaria, amma na kasa gane kanshi. Duk lokacin da zaka ganshi, a zaune yake ko yayi tagumi, ko kuma yayi zurfi cikin tunani. Haka a yawancin lokuta zan tashi cikin dare in ganshi zaune a tsakiyar gado cikin zuzzurfan tunani, sai dai duk lokacin da zan tambayeshi abinda yake faruwa sai dai ya girgiza kai kawai. Ko yace ya gaji ne, ko aiki ne ya mishi yawa, ko kuma wani abu dai. Wanda daga ni har shi mun san cewa ba haka bane.
Amma gabadaya yan kwanakin nan naga abubuwan nashi sun fara yin yawa, na kula har wasu dark spots sun fara fito mishi a kasan idanunshi alamun akwai abin da yake matukar damunshi.
Ban ce mishi komi ba, na tura mishi plate din dana shigo dashi. Cikin sanyin jiki ya janyo laptop dinshi ya fara aiki, na kula da yadda hannunshi yake dan yin rawa slightly. Nan ma na kauda kaina. Na dauki inabin tare da kaishi saitin bakinshi. Ya dago kai ya kalleni yayi dan murmushi tare da daga bakinshi ya karbi inabin, sai daya hada da yatsata ya dan ciza.
Da sauri na janye yatsar tare da sakin dan kara a hankali, hakan yasa Muhaaseen dake kan cinyata ta zabura. Nayi saurin fara lallashinta ina hararar shi ta kasan ido, yayi kamar bai san abinda yake faruwa ba, sai dan siririn murmushin daya saki na tsokana.
Ina gama lallaba Muhaaseen tayi barci, na kwantar da ita a cikin crib dinta dake gefen gadon da muke kwanciya. Na sake komawa gefen Yaya na zauna, yana aikinshi ni kuma ina cin abubuwan da na ajiye ina kuma bashi, har muka gama su. Sannan na dauke kayan na kai kicin. Sai dana tsaya na kashe duk wasu abubuwan wuta sannan na wuce dakina, nayi shirin da zanyi na kwanciya sannan na koma dakin Yaya.
Har yanzu yana zaune inda yake, sai dai ba aiki yake yi ba, al’adarshi ta tunani yake. Raina gabadaya naji ya dagule.
Na zauna a gefenshi tare da nade kafafuna sosai ina fuskantarshi, cikin sanyin murya nace “Abban Maama, wani abu yana faruwa ne?”.
Yayi saurin girgiza kai yana kokarin mazewa kamar yadda ya saba, “me kika gani?”.
Nace “meye ma ban gani ba? Wani abu ya faru ne a Zaria? Tun muna can fa na kula da canzawar da kayi, ina kuma ta tambayarka amma sai dai kace min babu komi. A tunanina ni din abokiyar shawararka ce, kamar yadda kake abokin shawarata?”.
Da sauri ya hau gyada kai kamar wani karamin yaro, “haka ne baby, na sani. Just… Ban ma san ta inda zan dauko zancen bane”.
Jin haka yasa na kara matsawa kusa dashi sosai, “to menene? Ka fada min, kaji? Idan ma wani abu ne da yafi karfinka zamu iya hada karfi da karfe, idan ma yafi karfinmu dai duk babu abinda zai gagara, kaji? Menene?”.
Yayi shiru yana kallona cikin tunani. Kai ya girgiza kawai, “I’m sorry baby, maybe next time, amma ba yanzu ba”.
Nayi kasa-kasa da ido, “Yaya…!”
Sai dai ban kai ga karasa fadar abinda nayi niyar fada ba, naga ya tashi da sauri kamar wanda aka mintsina yayi hanyar bayi. Na bishi da kallo cike da tsananin mamaki, a hankali wani abu mai kama da takaici ya tsaya min a makoshi. A ganina ina laifin wanda ya damu da damuwarka? Akalla kullum zan tambayi Yaya abinda yake damunshi, yafi sau a kirga. A tunanina, ko bai fada don muyi maganin abin ba, ai zai fada ko don raba damuwarka da wani kamar ka cirewa ranka rabin damuwar ne.
Nayi kwafa a hankali tare da mikewa tsaye ina karkade kayan jikina. Ko kofar bayin daya shiga ban kara kallo ba, na wuce wajen da Muhaaseen take kwance na tofe ta da addu’o’i. Na haye kan gado tare da shafe nawa jikin nima da addu’ar kwanciya barci.
Ban ma san lokacin da Yayan ya fito daga bandakin ba saboda lokacin barci ya fara daukata. Daga can dai naji lokacin daya hayo kan gadon ya kwanta tare da laluboni jikinshi, nayi banza na share shi. Kodayake, shariyar ta dan lokaci ce, babu shiri na manta da dan guntun fushin da nake yi na kara kwantar da kaina akan faffadan kirjin mijina.
Cikin tsakiyar dare na farka, tunda na laluba gefena naji babu kowa nasan cewa Yaya sana’ar yake yi. Na mike zaune da kyar tare da daukar bargo na rufe saman ruwan cikina dashi, saboda sanyin da yake dan bugowa a lokacin.
Kamar yadda nayi zato, zaune yake a gefen gadon, ya zira kafafunshi ta kasa, kanshi a kasa, ban sani ba duk cikin tunanin ne, ko kuwa barci yake yi a haka?.
A hankali na kai hannu na dafa samar kafadarshi, daga yadda jikinshi yayi tensing, nasan cewa idanunshi biyu.
Nace “Abban Maama…”.
Kaico! Masana iya magana dama sukan ce wai rashin sani yafi dare duhu, kuma dana sani k’eya ce.
Da ace nasan kalmomin da zasu fito daga bakinshi, da ban farka ba, da ban yi tunanin yi mishi magana ba a tun farkon fari, dana sani da naci gaba da kwanciyata koda kuwa na kasa komawa barci. Ban shiryawa jin abinda ya fito daga bakinshi ba.
“Na’ilah, aure zan yi!”.
Kalma mafi muni data taba shiga cikin dodon kunnena a cikin tarihin rayuwata kenan. Naji duk wasu ayyukan dake wakana a cikin kwalwata sun dakata da aiki, kai ni a karan kaina sai naji ni kamar wata sassaken sak’ago, ko wata statue. Na kasa numfashi, na kasa motsa komi a jikina, na kasa tuna komi a cikin raina. Wadannan kalmomi hudu daya furta, su kadai nake fahimta, su kadai kuma suke min yawo a cikin kaina.
Ban san lokacin daya juyo ya fuskanceni ba, sai da naji hannunshi da a da, idan ya taba ni dasu na kanji duk wata gajiya da wahala dake tattare dani ta gudu daga jikina a take, amma yau ya banbanta. Sai naji kamar ya dauko duk wata gajiyar duniya ya dora min ne, babu shiri na fara kokarin zame nawa hannun daya kama, amma bai bari hakan ta faru ba.
“Na’ilah, baby, ki saurareni don Allah, wallahi ba wai don bana sonki bane zanyi wannan auren, I love you more than anything in this world, bani da zabi ne, don Allah ki saurareni, kinji?”.
Na daga idanuna da na kasa tsayar dasu waje daya. Daga jin zafin da suke min, nasan cewa cike suke da hawaye, sun kuma canza kala. Cikin muryar da ni kaina sai dana yi mamakin jin ta fita daga bakina, nace “me kace?”.
Ya kara damke tafin hannuna cikin nashi, “please baby, ki bari in fara miki bayani kafin…”.
“aure kace?”, na katseshi ta hanyar jefe mishi wannan tambayar, ba tare da tunanin maganganun da yake fada ba.
A hankali, kamar wanda yake tsoron wani abu, ya daga kai sama.
Ban san lokacin dana kwace hannuna ba, na dira daga kan gadon cikin wani irin sauri da rawar jiki da ban taba zaton akwai irinsu a duniya ba.
Yaya yayi kokarin sake kamo ni, amma ina! Gabadaya duk wani sauran tunani daya rage a jikina yayi kaura. Ture shi na sake yi. Daya matsa da kiran sunana da kokarin kamo ni, sai kawai na kasa da gudu. Na fada dakina na maida kofar da sauri na kulle da makulli na hada da sakata.
Tsaye a tsakiyar daki, hannuwa biyu da suke ta rawa rike da wayata ina lalube cikin jerin contacts dina, amma na kasa ganin komi saboda hawaye da suka cika min idanu har sun fara zuba, balle inyi tunanin wanda zan kira a cikin tsalelen daren wannan.
A gefe guda kuma Yaya yana daga waje yana buga min kofar dakin tare da magiya akan in bude muyi magana.
Daga karshe dai silalewa tsakiyar dakin nayi da hannuwana biyu aka.
An fara kiraye-kirayen sallah a wasu masallatan lokacin da Yaya ya dakata da bugun kofar da yake yi, ina jin karar sawayenshi lokacin da yake barin kofar dakin. Na bi kofar dakin da harara kamar shine tsaye a wajen.
Ba’a jima ba sai gashi ya dawo da Muhaaseen, karan kukanta da naji ne yasa na dan dawo cikin duniyar, daga fari da kamar ba zan tashi ba, naga dai babu laifinta a ciki. Na mike tsaye ina layi da jan kafa na bude kofar dakin, nayi tsaye kyam tare da mika mishi hannu, naki matsawa gefe balle ya samu damar shigowa.
Yana miko min ita na karbeta tare da kokarin maida kofar in rufe, yayi saurin sanya kafarshi daya ya tare ni, “baby please…”.
Ban jira ya karasa ba na katse shi da nawa warning din, “don’t!”.
Babu musu ya janye kafarshi, na maida kofar na rufe garam, da ba don Allah yasa ya matsa da wuri ba da babu abinda zai hana in buga kofar nan a fuskarshi. Too bad, abinda naso ya faru kenan, babu abinda nake tunani a lokacin sai gwara in saba mishi kamanni in gani ko wadda zai aura din zata cigaba da son shi a hakan. Juyawa nayi zuwa cikin dakin na zauna a gefen gado.
Tunani na farko daya fara zuwar min shine asubahi ta farko in kama hanya in bar mishi gidan, in yaso sai ya dauko wadda yake so din ya ajiye a gidan nashi, daga baya dai naga cewa wannan gurguwar shawara ce, idan ma na tashi ina zan tafi? Gida dai nasan ko na sha giyar wake, Baba ba zai barni in zauna ba, in ma ce mishi me? Gashua kuwa… Bana ma sako ta cikin lissafi. Nasan ko numfashi ba zan gama ajiyewa ba zan ganni na dawo Abuja.
Tunda nayi sallar asubahi, na koma na kwanta. Duk da dan banzan barcin daya cika min ido, amma na kasa komawa barci. Ta yaya ma zan iya barci a cikin wannan halin?. Hawaye ne masu dan karen zafi da daci suke min zarya a kumatu. Rabin filon da nayi matashin kai dashi ya jike da lemar hawayena.
Wani sashe na can kasan zuciyata kuwa yana fada min I’m just being a hypocrite.
Bai taba fada ba, amma can wani bangare na tunani na yana fada min cewa ba zan taba zama ni kadai a cikin gidan Yaya ba, na sani. Shi yasa na kasa zama comfortable, na kasa sakin jiki balle har in saba da zama ni daya din, amma me yasa duk da hakan, zafin da nake ji a yanzu ya wuce misali?.
Har gari yayi haske, rana ta fito, ban motsa daga inda nake ba, ganin barcin ba zai yiwu ba yanzu yasa na tashi. Sai dana fara shirya Muhaaseen data tashi sannan nima na shirya cikin uniform dina.
Na nadeta cikin shawul mai taushi, na dauki abubuwan da zan bukata na bude kofar dakin na fita.
A falo na kwantar da ita tare da sauran kayan hannuna na shiga kicin. Duk da bana jin yunwa, amma kuma I can’t find it in me to starve my husband, ba ma zan ji dadi ba idan ban mishi girkin ba. Don haka na kunna gas. Ganin cewa lokaci ya riga ya kure, yasa nayi sauce din kwai kawai na dafa shayi, na kai kan dinning da biredi na ajiye. Har yanzu Yaya bai fito ba, watakila barci ne ya kwashe shi. Nayi kwafa da nayi tunanin haka, watau shi har lokacin yin barci ya samu? Ya mishi kyau.
*
Tunda naje asibiti na kasa tabuka komi, tun safe har lokacin tashinmu yayi. Yan kananun ayyuka kamar su dressing da sauransu, sai sauran abokan aikina ne suka dinga yin su. Sunyi tambayar duniya, ce musu ciwon kai nake yi kawai na dinga yin. Haka nan na koma gida dai ranar.
Kasa daurewa nayi, na kira Sailu a waya ina kuka tun karfina da jan majina, mata ta rikice ta hau tambayata abinda yake faruwa. Na zayyane mata abinda kenan, ban boye mata komi ba.
Ina gamawa taja tsaki, na daga baki hangangam cikin mamaki ina saurarenta, tace “to sai me? Ni Wallahi nayi zaton wani mummunan abu ne ya faru, har kin bani tsoro”.
Na share hawayen fuskata nace “haba Sailuba, yanzu wannan ba mummunan abu bane?”.
Tace “mummuna a ina? Yo wai ita kishiyar karshen rayuwarki ce ko me? Yadda kike yi dinnan sai wani yayi tunanin baki taba zama da kishiyar bane, ke da kika zauna da mata har biyu, kika kuma zauna lafiya balle daya?”.
Nace “to ita dayar kinsan halinta ne? Ko kuwa kinsan da abinda zata shigo? Su biyun kin san kalar gwagwarmayar da muka sha dasu? Wata fa har sanadin rayuwata ta kusa yi, dayar kuma taso laka min sharrin kisan kai. Haka kawai ina zaman-zamana azo a sanya ni a uku!”.
Sailu ta dan saki dariya, “haba dai, kada ki zama raguwa mana. To wai ma, zaki hana shi yin auren nan ne? In fada miki gaskiya, gwanda tun kuna shaidar juna ki hakura, wallahi ki bashi amincewarki. Allah kadai yasan abinda yake cikin auren nan, kuma duk wasu bore-borenki da tashe-tashen hankulanki, babu fa abinda zai hana. Sai dai idan Allah bai nufa ba, ko kuma idan shi din bai ga damar yi bane kawai. Wannan zamani ma Allah na tuba, wa yake wani tayar da hankalinshi akan wata kishiya? Kin san Allah? Ki daina gani yanzu yana wani bin kanki yana lallashinki, na dan lokaci ne. Tun kafin ya daina biye miki, ki bada kai bori ya hau, don ba zaki ji dadi ba wallahi”.
Na daga baki nace, “amma…”.
Tace “amma me? Ni fa in nice ke ko? Wallahi babu wani tada hankalina da zanyi, akan me? Miji ne, nasan yana min son da babu wata ‘ya mace da zata iya kamo kafata. Idan kuma kika iya rawar ki da takunki, wallahi ko ta shigo babu wani abu da zai sauya. Don haka don Allah ki kwantar da hankalinki Na’ilah, nasan cewa baki son kishiya, amma ina tabbatar miki da cewa ba duka fa aka taru aka zama daya ba. Duk wadda kika ga tayi wani da ba daidai ba, dama can halinta ne. Ke yanzu da ya aureki, kin taba tunanin daidai da rana daya akan kiyi yadda zaki yi ki kori kishiyoyinki?”.
Na girgiza kai a hankali, kafin na tuna cewa bata gani na, na daga baki da kyar nace “a’ah”, maganganunta sun sanya min rawar jiki, sun kuma jefa ni cikin tunani.
Tace “to kin gani? Halayenki masu kyau ne, haka kuma niyarki tsarkakkiya ce. Zata iya yiwuwa itama wadda zai aura din, maybe, itama niyarta daya da taki. Ba zaki taba sani ba. Kada ki damu, kinji?”.
Na kai hannuwa ina share hawayen fuskata with determination, nace “haka ne, nagode Sailu”.
Tace “ni ce da godiya Na’ilah, naji dadi da kika fara nema na. Baki nemi wadda zata jefa tunanin da zai jirkitar dake ba. Sai anjima”. Muka kashe wayar.
Na koma na kwanta tare da ajiye wayar a gefena, maganganun da muka tattauna da ita suna kara min tariya a cikin kaina.
⋆
Karfe kusan bakwai Yaya ya dawo daga wajen aiki. Ina kan abin sallah ina lazumi lokacin daya leko dakina, bai ce komi ba ya wuce inda Muhaaseen take kwance yana mata yan wasanni. Ban ce mishi komi ba har ya gama, ya juyo yana kallona with wariness.
Wani abu yazo ya cake ni a kirji, har yaushe ne mijina ya fara kallona da wannan sigar? Har yaushe ya fara kallona a tsorace, kamar wanda yake tsoron yana daga baki ruwan alkaba’i ne zai fita daga cikin bakina? Ko kuma yana tsoron in yanke mishi kai ne? Oho!. Kodayake, wannan ba shine karonshi na farko ba, waya san abinda tsofin matan shi suka mishi lokacin daya tashi yin aurena?.
Wata dariya ta nemi ta kubce min a lokacin, the irony! Wani lokaci can daya wuce, nima fa shirin shigowa gidan nake yi, ba tare da tunanin abinda matanshi suke dandana ba ta dalilin haka. Sai gashi yanzu nima ina dandanarshi. Allah kenan. Kodayake, auren da aka yi bada son raina ba, ina ma hankalina ya kai ga tunanin halin da matanshi suke ciki?.
Yace “madam, barka da war haka”.
Murya a sanyaye nace “sannu da zuwa, ya aiki?”.
Yadda ya kalleni cike da mamaki yasa nima na kalleshi cike da mamakin, ko bai yi zaton zan amsa mishi bane? Yace “uhmm, lafiya lau. Ya asibitin?”.
Na gyada mishi kai.
Muka yi shiru daga ni har shi, kafin yace “Baby, don Allah ki fara saurarata kiji abinda zan ce”. Yayi shiru yana kallona yaga ta yadda zan karbi zancen, ban nuna komi ba, sai idanu dana zuba mishi alamun ina saurarenshi.
Yace “Hajara, diyar Alhaji Musbahu ce, abokin baban nan nawa da naje dubawa a Zaria kwanaki. Cewa yayi kawai ya bani ita, zai aura min ita, ni kuma ban san ta yadda zan yi in ce mishi bana son diyarshi ko kuma ba zan iya aurenta ba. Yayi mana halacci matuka a lokacin da muka bukaci taimako. Don Allah kiyi hakuri, amma idan har ba zaki iya ba, wallahi zan iya cewa na fasa”.
A raina nace ‘kamar gaske!’.
Na kauda kaina gefe ina jin kwalla na ciko min idanu, nace “ni har na isa in hana ka kara aure? Wacece ni?”.
Ban san cewa ya tashi daga inda yake ba, sai da naji ya kamo tafin hannuna, yace “saboda kin isa baby, kin kuma kai matsayin da zaki hana ni din in hanu”.
Wata yar siririyar kwalla ta zubo min a kan kumatu ya kai yatsa ya dauketa. Sai na fashe da kuka na fada jikinshi, cikin kukan nake cewa “nasan cewa fada kawai kake yi, amma ba zaka fasa ba!”.
Yana shafa bayana a hankali, cike da alamun lallashi yake cewa “try me baby, da gaske nake”.
Sai dana lafa da kukan, sannan yaci gaba da cewa, “zata zo ta ganki, idan kika ji bata kwanta miki a rai ba, to sai dai suyi hakuri”.
Na dan jefa mishi harara, “ni bana wani son ganinta!”.
Yayi murmushi a sanyaye, “I’m sorry baby, I love you!”.
Ban ce mishi komi ba, don a lokacin wani sashe na zuciyata rada min yake, ‘ya daina sonki yanzu!’.
**
Ranar Lahdi da rana, ina falo ina duba wasu manyan textbooks akan midwifery, duk da karatu dana gama hakan bai hana ni cigaba da neman ilimi ta textbooks ba, idan ma Allah ya bani dama so nake in cigaba da masters dina. Kofa naji ana knocking. Cikin mamakin wanda zai zo a daidai wannan lokaci na tashi na nufi kofar. Yaya ya fita dazu da safe, kan cewa zai je wani waje ya dawo, nasan ma bashi bane tunda da shine da ba zai tsaya yin knocking ba.
Wasu matasan yan mata biyu naci karo dasu, ba laifi dukansu kyawawa ne. Dayar zata yi sa’ata, fara ce ba can ba, doguwa mai dan jiki, yayin da dayar kuma daga ganinta kasan kanwar dayar ce, yanayin kamanninsu da surarsu kusan daya ce, kawai dai karamar tafi babbar kiba da fari.
Nayi yar fara’a duk da cewa ban san su ba, na musu iso zuwa ciki. Sai da suka zauna akan kujera, sannan naje na dauko lemu da ruwa na kawo musu.
Na zauna muka gaisa dasu, nace “ko kuna neman wani gida ne?”.
Karamar ce tayi saurin cewa “a’ah, Yaya Bilal ne ya kawo mu nan!”.
Na karkata kai ina kallonsu cikin mamaki, me zai hadinsu da Bilal? Na gyada kai a hankali nace “Allah sarki!”.
Karamar ta sake cewa “ni sunana Zainab, wannan kuma Hajara”. Ta nuna babbar.
Sai lokacin na kula da yadda babbar take ta sunke kai tunda suka shigo. Wow!! Sai lokacin na fahimci komi. Ita ce Hajarar dama? What a nerve she has! Da har ta iya kwaso kafafu tazo min gida.
Kafin in iya daga baki in ce wani abu, Yaya ya shigo cikin falon. Ya zauna a gefena, Allah ne ya iya bani ikon samun dauriya, na cije ban dankara mishi harara ba.
Yace “Madam, ga Hajara na kawo miki”.
Na gyada kai ina dan murmushin yake, “aikuwa na ga Hajara”…
Shi ya zama jagorar hirar tamu, ga mamakina cikin dan lokaci kankani muka saki jiki daga ni har su. Ko lokacin da lokacin sallah yayi, tafiya yayi ya barmu. Na kaisu dakina suka yi sallah, muka koma falo. Dana shiga kicin haka suka biyo ni, duk da magiyar dana musu akan su koma falo suyi kallo ko wani abu, fir suka ki. Duk wannan abin da ake yi, Muhaaseen na bayan Hajara a goye.
Kafin Yaya ya dawo mun gama girki. Muka zauna mu duka muka ci ana ta hira.
Anan na fahimci cewa dukansu a Abuja suka tashi, shima Babansu matanshi biyu, in fact, Zainab step sister din Hajarar ce. Ita Zainab tana Abuja uni tana karantar mass com, tana aji daya. Ita kuma Hajara wannan shekarar ta gama degree dinta akan architecture a jami’ar Tafawa ‘Balewa, Bauchi.
A abinda na karanta a cikin dan lokacin, shine suna da wani irin sanyin hali da hangen nesa, haka iliminsu ya tabo ta kowane fanni.
Zuwa lokacin da yamma tayi, suka mana sallama akan zasu tafi, sai naji kamar kada su tafi. Allah ya gani, naji dadin zuwansu sosai. Suma daga ganin yadda suka mike din zasu tafi, hakan take. Shima sai da direban da aka turo ya daukesu yazo, sannan suka tashi.
Na shiga daki cikin drawers dina da nake ajiyar abubuwa saboda bakin ba zata, na ciro musu turaruka masu kamshi, chocolates, kayan kwalliya, cike da leda na fito. Muka musu rakiya har gaban motarsu ni da Yaya. Sai da zasu shiga sannan Yaya ya karbi Muhasseen a hannun Hajara, na kula Allah ya hada jininsu sosai.
Na mikawa Zainab ledar hannuna, da taki karba, na harareta cikin wasa, “ko dai kin raina ne?”.
Ta zaro ido da sauri, a lokaci guda kuma ta sanya hannu ta karba, “haba dai Anty! Mungode sosai, Allah ya amfana!”. Wani halin nasu mai burgewa kenan, akwai godiya. Daidai da abinci wannan dana zuba mana, sai da suka biyo mu da godiya da addu’a.
Nace “babu komi wallahi, ku gaida su Mama Sai mun zo ziyara”.
Hajara tace “sai mun ganku!”. Daga haka direban yaja mota suka fita daga cikin farfajiyar gidan.
Yaya ya sakalo hannunshi daya akan kafadata, dayan kuma yana rike da Muhaaseen. Yace “ya?”.
Na daga kai na kalleshi ina dan murmushi, “uhmm, ba laifi. She doesn’t look that bad!”.
Yaya yayi murmushi a hankali, ya shafo hancinshi da nawa, “haka ne?”.
Na gyada kai ina murmushi. Da gaske ne kuma, haka kawai naji hankalina ya kwanta da ita sosai. Kai duk da cewa tun kafin zuwansu dama na saddakar, amma hankalina bai kwanta ba.
Yanzu kuwa dana ganta, sai naji hankalina ya kwanta da ita sosai, shima auren hankalina ya kwanta dashi.
Watakila maybe, just maybe, ba zata yi halin Ramata, Ameerah ko Raheemah ba. Kila ita za ayi zaman mutunci da ita!.
K’arshe!
‘THE GREATEST HAPPINESS OF LIFE IS THE CONVICTION THAT WE ARE LOVED; LOVED FOR OURSELVES, OR RATHER, LOVED IN SPITE OF OULSELVES!’.
VICTOR HUGO
*☆⋆Epilogue⋆☆*
Bayan Shekaru Biyar…
“Ni abinda yake daure min kai shine, babu fa abinda na mishi, kawai daga sama kamar saukar aradu naji maganar, ya sakar min ita aka kamar tashin bomb!”.
Janan take fada cikin tsananin kunar zuci.
Ni kuwa me zanyi in ba shekewa da dariya ba? Na dinga kya-kyatata kamar ba zan daina ba. Tana gefena tana jefo min bama-baman harara ita kuma. Sai da nayi ta isheni, na gyara zamana ina kwashe kwallar data zubo min.
Tayi kwafa, “baki da kirki wallahi Na’ilah. Saboda ke kina da kishiya, shi yasa kike sheka min dariyar mugunta nima don za’a min?”.
Na daga kafada, “tunda na dandana, kowa ma ya dandana mana. Ke dalla ki kwantar da hankalinki, ki daina wani daga hankalinki akan abinda bai taka kara ya karya ba. Ita fa kishiyar nan, wallahi gane mata ne mutane basu yi ba saboda kawai sun riga sun fadawa kansu ba abokiyar zama bace, amma da gaske abokiyar zama ce. Ke ni yanzu wallahi Abban Maama ko ta uku da hudu yace zai karo, zamana zan gyara kawai ince Allah ya shigo dasu gidan lafiya. Ga fili ga mai doki, to ma wai, a kaina zasu zauna ne? Wasu ayyukan ma zasu rage min karewa. Ko ba komi, kin samu rarar kwanakin girki, kin samu abokiyar tayin ayyuka da hira, kin samu yar tayin raino da hidimar gida, sannan at least, wulakancin namiji ba sai kare a kanki ke kadai ba, ya dinga rabawa biyu yana bata rabi itama”.
Janan ta kame baki, tace “Innalillahi! Na’ilah, kece kuwa ko dai wata ce mai kama dake?”.
Nayi murmushi nace, “shafa ki ji!”.
Ta jinijina kai, “Allah kenan! Kuma rayuwa kenan, babu abinda ta bari. Idan wani yace min akwai rana da zata zo ki tausar da wani akan zama da kishiya, wallahi ba zan taba yarda ba”.
Na gyada kai a hankali, ko ni kaina ina mamakin kaina.
A shekaru biyar ko shida da suka wuce, idan wani ya fada min cewa zan zauna in fadi wani alkhairi game da zama da kishiya, hakika da idan muka fara fada dashi babu wanda zai iya raba mu dashi sai Allah.
Ban taba zaton akwai lokacin da zai zo, in so kishiya ba, in kuma kaunace ta, ban taba ba.
Duk a zato na, kishiyar bala’i, masifa ce, wadda zata kawo maka rashin zaman lafiya da kowa naka, wadda zata kawo maka bakin jini ta sanya maka cuta a cikin jiki da zuciyarka. Ashe duk rashin fahimta ce ta kawo hakan.
A zato na, bata nufar kowa da alkhairi sai sharri. Nayi zaton tana shigowa tunanin fitar dani daga cikin gidan aurena zata fara yi, sai naga banbanci.
Tabbas Anty Sailu tayi gaskiya, da tace ba duka aka taru aka zama daya ba. Duniyar Allah mai fadi ce, ba’a rasa mutanen kirki a cikinta. Kamar yadda ba’a rasa abokan zama na gari a cikinta.
Ina ga ni nayi dace ne sosai, Allah ya hada ni da wadda ban taba zaton zan hadu da ita ba.
Koma dai menene, ta dalilinta sai gashi ina kallon abokiyar zama da wani ido daban, in a different way, in a different light.
Ta saka ni fahimtar cewa, tsanar kishiya dana taso ina yi, saboda banyi dacen haduwa da mai halin kirki bane, wadda take kaunar zaman lafiya da zaman aminci da amana.
Ramata dama can halinta mara kyau ne, irin mutanen nan ne da dama can tun asali basa son wani daban ya rabe su ko wani nasu, sun fi son komi ya kasance nasu ne su kadai, basa son cigaban kowa sai nasu. Saboda haka ne suke yin duk abinda suka ga zasu iya, don su ga cewa sun kawar da duk wani abu da zai yi threatening dinsu da cigaban su. Saboda haka ne su son kishiya ko diyanta, baya cikin lissafinsu, me yasa zaka so abinda kasan cewa ya fika matsayi a inda kake so kaga cewa kafi kowa matsayi?.
Haka Raheemah, haka ma Ameerah.
Na fahimci cewa su irin wadannan mutanen, son zuciya da son kai ya musu yawa. Shi yasa basa tunanin komi, kuma basa tunanin kowa sai kansu.
Ita kuma duniyar yanzu, cike take da mutane masu son kai da son zuciya, yan kalilan ne masu son farincikin wasu da cigaban wasu.
Duk ban fahimci hakan ba sai a dalilin zaman da nayi da abokiyar zama na, Hajara. Yanzu zan iya fada da alfaharina, cewa ita ba kishiya ta bace, ‘yar uwa ce. Ta dalilinta idanu na suka washe sosai, har nake iya dauko uzurirrika akan dalilin da yasa wadanda na zauna dasu a baya suka dinga yin abubuwan da suka yi din, sai naji na dan fahimce su. Duk da cewa naga rashin wayonsu, tausayinsu yafi rinjayata.
Dama sun bi ta wata hanyar da ba wannan ba.
Dama basu biyewa rudin duniya, shawarar abokan banza, da bakar zuciyarsu ba.
Dama sun bi ta hanyar data dace, dama sun sowa wasu daban irin rayuwar da suke sowa kansu.
Watakila da yanzu muna tare dasu cikin aminci kamar yadda muke zaune da Hajara.
Kwanaki naji cewa Ameerah ta samu tayi aure da kyar, bayan manema kusan shida na fitowa suna guduwa saboda zancen dalilin da yasa ta bar gidanta na farko da suke ji. Sai daya zama kamar ma kyautar da ita ma iyayen suka yi. Gidan mata uku aka kaita, itace cikon ta hudu. Ga tarin ‘ya’ya. Hakan yasa ni zama wani tunani, duk wata kauna da iyayenki zasu nuna miki a matsayinki na ‘ya mace, ta dan lokaci ce. Dole dai gidan aure nan ne gidanki na har abada. To ko meye amfanin shiga cikin rayuwar auren ‘ya’ya da iyaye suke yi? Bayan sun san cewa, daga ranar da ka karbi sadakinta, duk wani hidima nata da komi nata ya tashi daga karkashinsu ya koma kasan wanda ka aurawa? Yakamata iyaye su bude idanunsu, su kuma kula da cewa shiga cikin rayuwar auren ‘ya’yansu mata da suke yi suyi babakere, har su dinga karfafa mata gwiwa akan sabawa miji, hakan baya haifar da komi, sai zubewar darajarsu a idon yaransu da mazajensu, wanda hakan zai iya kawo rabuwar aurensu daga karshe. Kunga anyi biyu babu kenan. Tunda ba kowa bane zai iya zama ya iya jurewa a dinga yi mishi wasa da rayuwar aure.
Na sauke ajiyar zuciya a hankali ina kallonta, nace “baki kula da juyin da aka samu bane? Lokacin da za’a min kishiya nima fa haka kika zaunar dani kina min nasiha da bada shawarwari”.
Ta gyada kai tana murmushi, “kwarai anyi haka. Sai dai ni ban taba zaton idan nawa lokacin yazo ba, zaki maidawa kura aniyarta ba”.
Na hau karewa falonta kallo, hotunanta dana mijinta da ‘ya’yansu, Abdul-Azeez kusan sa’an Muhaaseen, da dan kaninshi Sultan, sun mamaye falon. Shekaru uku da suka wuce aka wa mijinta Al-Mustapha canjin wajen aiki, suka dawo Abuja. Tun daga nan muka kara hadewa, kanmu a hade yake sosai. Musamman da wajen aikinmu ya zama daya, tare da ita muka yi masters dinmu anan wata private university. Hajara ma ta shigo cikinmu. Idan ka ganmu kamar wasu ‘yan uku, babu mai cewa ita din kishiyata ce.
Kulsum ma ta auri wani dan kasuwar kayan masarufi, tana Kaduna abinta da danta Suleiman.
Nace “rayuwar kenan, haka take zuwar ma mutum a bai-bai, cike da ban mamaki da tu’ajjibi”. Ta gyada kai.
Nace “to yanzu ya ake ciki ne?”.
Tace “ni fa dama can ban hana shi yin auren shi ba, ce mishi nayi Allah ya sanya albarka. Kawai ina ta tunanin ta inda na gaza ne da har zai yi tunanin kinkimo min kishiya ya kawo min. Naga dai babu abinda na rage shi dashi. Gyaran jikin nan duk karshen wata yin sa nake, watarana ma kafin karshen watan yayi nayi. Ke karewa ma, VIP ce ni a Tee-Tee’s Care. Ki duba fa yadda fatar jikina take taushi da laushi da komi!”. Ta karasa fada tana nuna min hannunta.
Na matsa gefe guda ina harararta cikin dariya, “dalla can matsa Malama. Wai ke an fada miki wadannan abubuwan suna hana maza karo aure ne idan suka yi niyya? Kawai dai nasan suna kara miki wata daraja a idanunsu musamman idan ita wadda aka kawo miki din bata san sirrin gyaran nan ba”.
Ta gyada kai.
Hakan ta tuno min, lokacin da Hajara ta haifi Suhaima, sai data kusa yin yaji saboda yadda Yaya ya dinga mata. A cewarta, ce mata yayi gabadaya ta canza, yace ta same ni in gaya mata yadda ake gyaran jiki idan aka haihu. Wanda hakan shi ya bata mata rai. Ni kaina naji na tausaya mata, sai dana sameshi kuma na fada mishi hakan babu dadi, kuma bai dace ba.
Saboda tsananin gyaran dana samu lokacin dana haifi Muhaaseen, sai da Yaya yayi min kyauta mai girma. Su Anty Haleemah kuwa da su Fatsu sun sha godiya tafi cikin daro.
Sai dana zaunar da ita na fahimtar da ita muhimmancin irin abubuwan nan, duk da hakan ma dai tana dan yi ne kawai. Su ainihin yan boko ne, irin wadannan abubuwan babu su a cikin dictionary dinsu. Lokacin data fada min haka, ba karamar dariya na sheka mata ba. Kitso da kunshi ma, musamman ma dai kunshin, sai idan zamu je ni da Janan muke jan ta muje.
Mawuyaci ne kaji fadan mu ni da ita, idan ma kaji, ba akan son zuciya bane fadan, abu ne ziryan tsarkakke, ko kuma kawai sabawa da zaman tare yake kawowa. Wannan kuwa is natural, fada ce kuma ta ma’aiki, duk zaman da za ayi shi babu ire-iren samun sabanin nan, akwai alamar tambaya a cikinshi.
Nace “ke dai kawai sai dai muyi fatan Allah ya hada mu dana kwarai ne kawai, amma fa wani gyaran jikinki da wasu karairayar ki, babu abinda zai sa balle ya hana wallahi”.
Tace “gaskiya ne, Allah dai yayi mana zabi mafi alkhairi, ya kuma bamu ikon zama dasu lafiya. Allah yasa mu cike ibadunmu lafiya”.
Nace “ameen”.
Tashi tayi ta shiga kicin tana fadin bari ta duba abinda ta dora akan wuta. Ni kuma na dauki wayata na turawa Yaya da yake kan hanyarshi ta dawowa daga kasar Germany, sakon Allah ya kiyaye hanya. Shekara guda kenan da aka maida shi Manajan gidan jaridar Daily Trust. Alhamdulillah, budi ta ko’ina muke samu. Tuni na haura matsayin da zan jira ayi min wata hidima komi girmanta kuwa, sai dai in yiwa wasu. Ko babu aikin da nake yi, Yaya Bilal ya kasance mijine mai tsananin kula da duk wata hidima ta iyalinshi.
Janan ta fito da kwaton bowl a hannunta, tun kafin ta karaso kamshin daddawa da tafarnuwa ya min iso, naja miyau na hadiya mukut!. Cikin da nake dauke dashi mai kimanin wata uku, ya sanya min tsananin son kwadayi da son ciye-ciye.
Ta ajiye farfesun kayan ciki dana sameta tana dafawa a gabana. Na shaki numfashi, dadin kamshin yana ratsa min har cikin kwanyata.
Nace “kyawunta abinnan ace har ‘yar uwata zata samu”.
Janan ta zauna a kusa dani tana zuba farfesun a cikin madaidatan plates, “ai fa, komi ‘yar uwa, ‘yar uwa. Na ajiye mata nata a microwave, don nasan kalar mitar da zan sha idan ban ajiye mata ba”.
Nayi dariya, “kin kyautawa kanki kuwa”, na karbi plate din data miko min na fara ci.
Ina cikin ci wayata tayi kara, hoton Hajara da aka dauka rungume da Muhaaseen ya bayyana, nayi murmushi, “kinga yar halas din ba”, na dauka.
Fada min tayi ta tashi daga wajen aiki, zata biya makaranta ta dauko yara sai ta biyo nan ta daukeni, nace mata sai tazo.
Muna yan hirarrakinmu, har suka iso gabadayansu. Yaran suka zo suka rungume ni, na dauki Suhaima da take rarrafe na dora ta akan cinyata.
Janan ta zubowa Hajara da sauran yaran, suka fara ci. Yaranta sun riga su Muhaaseen samun hutu, suna Kaduna.
Suna gamawa muka fara haramar tafiya, Al-Qaseem da muke kira Papa, yarona mai kimanin shekaru uku da rabi, ya dauki Suhaima ya fita waje da sauri yana cewa bari ya riga mu. Duk muka rufa mishi baya muna dariya.
Janan ta raka mu har gaban motar Hajara, dankareriyar Maybach GLS 650, shigen tawa ce. Ba’a jima ba da Yaya ya canza mana su, ni tawa ruwan maroon ce mai duhu, tata kuma ruwan hoda mai haske. Na shiga gidan gaba, ina zama Papa ya dora min Suhaima akan cinya data mishi tumbud’i, yana yatsinar fuska yana mitar shi fa shiyasa baya son daukarta. Ni da Hajara kam dariya muke ta mishi. Janan ta karbi tissue a hannun Hajara data yago, ta goge mishi gefen riga. Daga nan dai muka daga mata hannu muka harba kan titi.
Muna isa gida, muka tura yaran daki akan su je su shirya kafin lokacin zuwa islamiya yayi. Mu kam shirin tarbar maigida zamu shiga yi.
Hajara tace “Yaya, idan mun gama zan nuna miki wasu sababbin kayan daki, kila wadannan suyi naga suna da kyau”.
Nace “to shikenan”.
Bikin Maryam yana ta matsowa, wannan shekarar zata gama degree dinta akan chemistry a ABU, tana gamawa kuma za ayi aurenta ba da jimawa ba. Ni da Yaya Mudatthir aka dorawa alhakin kayan dakinta, hakan bai dameni ba ko kadan, hasalima naji dadin hakan. Ko babu komi an nuna mana cewa muna da wani gurbi a wajensu.
Shi yasa ni kuma na daurawa Hajara aikin nema mana kayan daki har ma da wasu daga na kicin, masu kyau na garari, tunda fanninta ne. Tana aiki da wani babban kamfani ne anan Abujar, sukan zana abubuwa iri-iri, kayan daki ne, gidaje ne, makarantu, masana’antu, da sauransu. Akwai ainihin kamfaninsu dake Saudi-Arabia, shi yake kera ire-iren abubuwan da suka zana din, a sayar.
Tuni magriba ta fara kawo kai lokacin da muka gama. Muka yi wanka, muka cancada kwalliya kamar masu zuwa fashion show. Dole Hajara ta koya min zana gira da yafa eyeshadow, haka nan nake shafawa duk da ba ko wani lokaci ba. Amma kuma duk lokacin dana yi din na kan sha yabo da kirari wajen wanda aka yi domin shi din. Suma yaran muka shirya su bayan sun dawo daga makaranta. Daga nan zuwa kowane lokaci Yaya zai iya dirowa, tun dazu Balarabe ya tafi dauko shi.
Muka zauna akan manya-manyan leather seats din dake cikin falon da muka canza, muna duba kayan dakin. Har dai muka tsaya akan wasu jajaye da farare da suka mana, tace zata saka su cikin oda, nace mata to. Daga nan muka koma dakinmu muka yi sallah. Tun kafin in gama na fara jiyo hayaniyar yara, hakan ya tabbatar min da cewa maigidan ya karaso kenan. Banyi gaggawar fita ba sanin cewa ba nice da girki ba. Nasan zai fara yin wanka ne kafin ya wuce masallaci sallah.
Ina dakin a zaune ina karatun Kur’ani ya shigo, na mishi sannu da zuwa muka gaisa, ya wuce masallaci.
Sai bayan sallar isha’i muka hadu gabadayanmu a falonshi muka ci abinci. Ni da Hajara muka fara jidar kayan muna maidawa kicin bayan mun gama, Papa da Muahaaseen kuma suka tafi daukowa Abbansu takardunsu na makaranta ya gani.
Na zauna a gefen Papa da yake gaban Abbansu yana duba nashi takardun cikin gyada kai, da yake yaron tubarkallah akwai ilimi, mawuyaci ne suyi jarabawa yaci kasa da casa’in a cikin dari.
Bayan ya gama dubawa, ya janyo yaron cikin jikinshi yana shafa kanshi, yace “good boy, kayi kokari sosai Baba na. A cigaba da kokari ko?”.
Yaron ya gyada kai cikin murmushi, yace “that’s my boy”, tare da bashi peck a kumatu.
Yaron ya wani yatsina fuska, Yayan yana dagawa yasa bayan hannu yana goge kumatunshi, yace “ewww Abba!”. Ni dasu Yayan me zamu yi idan ba dariya ba? Yaya ya kama kumatunshi duka biyun yana ja, yace “Babana har yanzu baka daina jin kyankyami na bane?”.
Na shafa kan yaron ina murmushi, haka Allah ya halicce shi da son jiki da kyankyami.
Ya maida hankalinshi ga Muhaaseen da tayi shiru a zaune tana kallonsu cikin dan murmushi. Ita kuma kunya da kawaici ne da ita kamar me, abinda wani lokacin nake cewa mai sunanta ta biyo.
Yace “Maama fa, ya ake ciki ne?”.
Awa daya da kusan rabi yana ta hira ne da yaran nashi, ya dauko tsarabar su ya kunce musu, kowa aka bashi nashi. Daga nan ne suka mana sai da safe, kowa ya nufi dakinshi. Suhaima kuwa tana kwance akan cinyar Yayan tana barci.
Bayan tafiyar su ne muma aka kunce mana tamu tsarabar. Kaya ne na ado iri-iri, dogayen riguna, takalma flats da heels da kayan su jikkuna masu kyau da burgewa, turaruka da sauran tarkace. Muka hau mishi godiya sosai, Hajara tace “Abban Maama mu kam kana shagawaba mu da yawa wallahi, mun gode, Allah ya saka da alkhairi Ya kara budi mai amfani”.
Yace “ai ban muku komi ba cikin abubuwan da kuke yi min, hadin kanku ma kadai ya isheni, balle kuma tallafawarku a gareni da kulawar da kuke bani. Allah dai yayi muku albarka, Allah ya kara hade min kanku gabadaya”.
Duk muka amsa da “ameen”, a tare.
Abinda ke kara mana kwarin gwiwar kyautata mishi kenan, Yaya baya kyashin yabonmu a ko’ina ne, a kuma gaban ko waye sai dai idan bamu yi abinda ya burge shi ba.
Bayan mun zauna, yace “yaushe yara zasu samu hutun makaranta?”.
Nace “nan da sati hudu muke sa rai”.
Yace “to ku shirya, umara zamu je gabadaya har yaran”.
Muka kalli juna ni da Hajara, kafin muka saki ihun murna muka dira jikinshi muna ihun murna da godiya. Aikin hajji kam mun je shi babu iyaka, mun fara zuwa ni da Yaya, muka koma har Hajara. Haka su Malam ma shekarar data wuce suka je suka sauke. Shi dama Baba yaje ya kai matanshi.
Ranar har wajen karfe sha daya da rabi muna falon ana ta hirar yaushe gamo, kafin na mike tsaye ina musu sallama.
Hajara ta kwashe kayanta ta kai daki bayan ta kai Suhaima ta kwantar a dakin Yaya, Yaya ya taya ni kwaso kayana muka kai dakina.
Yana zube kayan akan gado ya juyo ya janyo ni jikinshi, ya nutsa kanshi a cikin gashin kaina, nayi yar dariya tare da zagaye hannuwana a bayanshi.
Yace “ya kike, ya babynmu, hope baya matsa miki ko?”.
Nayi dan murmushi, “dukkanmu lafiyarmu lau. How was your trip?”.
Yace “Alhamdulillah, mun samo fiye da abinda muka je nema”.
Nace “to madallah, haka ake so”.
Mun dan jima a haka, kafin na dago kaina na kalleshi, “kada fa ka tsaida Hajara da jira, nasan itama tayi kewarka, sai da safe ko?”.
Yace “wato har kin gaji da ganina kenan?”.
Nayi dariya ina kama baki, “ni har na isa in ce na gajii da kai? Ban ki mu dawwama a haka ba. Amma bana so mu shiga hakkinta ne ko kadan”.
Yace “to shikenan, sai da safe”.
Nace “sai da safe, ku tashi lafiya”.
Ya wuce gaba na bishi a baya, a bakin kofa ya juyo ya manna min sumba a goshi, sannan ya juya ya tafi. Nayi murmushi kawai tare da girgiza kai, na maida kofar na rufe tare da murza makulli.
Shirin kwanciya barci nayi, na kashe wuta na bi lafiyar gado.
*_…Alhamdulillahi Rabbil-Aalameen. Masha Allah La Quwwata Illah Billah!_*
*Da haka muka kawo karashen littafin ‘A Zato Na’. Ina fata Allah yasa mu fi karfin zukatanmu, Allah yasa kuma mu amfana da sakon da wannan littafi yake dauke dashi. Kurakuran dake ciki, Allah ya yafe mana, ameen.*