DA KAMAR WUYA CHAPTER 5 BY ZULAIHAT IDRIS MISAU

 DA KAMAR WUYA CHAPTER 5 BY ZULAIHAT IDRIS MISAU

               Www.bankinhausanovels.com.ng 

Allah Allah Mariya ta ke hubby ta dawo, ta gaya mata wani balarabe yazo. Bata ji dadi ba data dawo dauke da ruwa ta samu baya nan.+

Hubby koda ta dawo ta samu malan idi na goge bike din hayder bata kawo komai ba, ta nufi cikin gida.

Ko Jakarta bata ajiye ba, Mariya ta fara bata labarin zuwan balarabe. ” Anty baki ganshi ba, mai kyau sosai. Na ce yanzu zaki dawo, kafin in shiga in dauko masa ruwa, ya tafi.”

Gaban hubby ne ya fadi, hayder ya dawo. Jakarta ta dauka tayi sama.

Wunin ranar basu hadu ba. Da yamma su junaid suka zo, sun shiga sun gaisheta kamar yadda suka saba. Abubuwan sha ta tura Mariya ta kai musu, kafin ta tafi gida. Don in tazo da safe sai 5 take komawa gida.

Yauma a wurin basketball ta jisu, har kusan magrib, sannan suka nufi masallaci.

Yau hubby tun magrib ta rufe dakinta, don har lokacin tana cikin jimamin yadda hayder zai yi reacting kan maganar zuwa islamiyyarta.

Ana sallar ishai, ya nufo gida, yau ko tsayawa karatun da yake dauka bayan sallar ishai bai samu ba. Dakin hubby ya nufa, amma ina yajita a kulle. Kwafa yayi, sannan ya nufi nashi dakin.

                  ****************

Da sauri -sauri, gudu -gudu, kamar yadda ya saba saukowa daga steps ko hawa.

Dinning table din da hubby ke zaune tana break fast ya nufa, kujerar da take facing dinta yaja ya zauna.

Kirjinta sai faman bugun tara-tara yake yi, mu samman kallon da yake binta dashi, yasa jikinta yin sanyi, ga wani faduwar gaba da take ji. Daurewa tayi, ta ci gaba da cin abincinta.

Tambayar daya watso mata ne, ya sata saurin dago ido tana kallonsa. Shima idonsa a kanta. ” ina kika je? Jiya na dawo, bakya gida?”

Tabe baki tayi, tana juya dankalin da fork din hannunta. ” meye damuwarka, don na fita?”

Shiru yayi, yana karantar yanayinta. ” da izinin wa? Kika fita?” Kallonsa tayi tare da waro ido waje, cikin mamakinsa. Musamman yadda yayi tambayar, Tamkar uba a gaban dansa.

” don zan fita sai na tambayi wani?” Ta fada, tana kai dankali bakinta.

” yes, tunda ba zaman kanki ki keyi ba ba?!”

” Allah hayder ka fita a idona! Kai har ka isa, inki fita, sai na tambayi izininka? Ka sani duk lokacin da naji fita, fita zanyi.” Ta fada cikin daga murya kadan.

Jingina yayi, sosai a jikin kujerar. ” ki sake fita bada izinina ba kiga, yadda zamu kwashe, karki rainamin hankali, nasan aure nasan kuma yadda yake. So be careful.”

” baka isa ba hayder kayi kadan! Ka kafamin doka da oder.”

Tashi yayi, ya nufi kitchen ” let see.” Ya fada yana shigewa ciki.

Yana falonsa yaji tashin motarta. Lekawa yayi, ai kuwa fitan ta sake yi.

Murmushi yayi, ” yaro bai san wuta ba, sai ya taka.” Ya fada yana gyara zamansa, ya ci gaba da aikin da yake yi a system.

              *********************

Yau makarantar batawa hubby dadi ba. Don yau basuyi darasiba ko daya. Ilah waazi da aka musu. Daya shafi mata yan wuta, da dalilan shigarsu wuta, kamar hadith’s din da yazo na cewa mafi yawan yan wuta mata ne, kuma sun shiga wuta ne, saboda yawan butulcewa mazajensu, da mazansu zasuyi shekara da shekaru, suna kyautata musu, duk ranar da aka samu sabani, sai ta ce meka taba min. Sannan malan ya gangaro kan sauran dalilan dake sa mata shiga wuta. Sannan ya kara musu da muhimmancin, sallah ga mace, sannan biyayya ga mijinta.  Da yawaita sadaka. Da yawansu sai da suka zubar da hawaye.

Hubby samun kanta tayi, da tambaya. “Shin koda auren dole akawa mace, in batayi biyayya wa mijin ba, zata shiga wuta.”

” so sai ma, muddin an daura mata aure da mutun, dole ne, ta masa biyayya koda bata sonsa. In ba haka ba tabbas azabar Allah zata tabbata a gareta.” Takai tacciyar amsar da malan ya bata kenan.

Jikin hubby yayi sanyi, tsoro da fargaba duk sun cika zuciyarta. ” mafita kawai take tunanowa kanta. Don bazata yadda haka kurun ta jawa kanta shiga wuta ba, gara in ma rabuwa ce, to su rabu. Don bazata iya masa biyayya ba.”

Wata daliba ce ta shigo da sallama, bayan an amsa mata, ta shaidawa muallim ana neman Habiba Munir a office din principal. Nan take muallim yaba hubby izinin zuwa amsa kira.

Gabanta na faduwa, haka ta nufi office din principal. Tana tunanin dalilin kiran.

Gabanta ne yayi mugun faduwa, ganin hayder zaune, a daya daga kujerun gaban table din principal din. izinin shigowa principal din ya bata, tare da nuna mata kujerar dake facing din hayder, alamar ta zauna.

Kanta a sunkuye, ta zauna, ba tare data yadda ta kalli hayder ba.

” gaishe da principal din tayi, cikin rawar murya.”

Fuskarsa dauke da murmushi ” malama Habiba, haka ake, Ashe kinyi aure shine baki gaya mana ba? Da badan mai gidan yazo da kansa ba, da bamu sani ba, Baki kyauta ba gaskiya.”

Kanta a sunkuye, still muryarta na rawa ” ayi hakuri. “

” ba komai malama Habiba, gashi mai gidan ya ce daga yau bazaki sake zuwa ba, da sai in ce muna binki, shinkafa kaza. Na biki da bamu ci ba.”

Da sauri ta dago ta kalli hayder, ido hudu su kayi da juna, da sauri ta dauke idonta.

” naji dadin ganin maigidan naki, hakika ki gode Allah, nasan hayder tun kuruciyarsa, ni na fara koyar dashi ilmin addini, shida sauran yan uwansa. Allah yasa albarka a aurenku, ya baku zama lafiya da zuria tsarkakakkiya.” Nasiha sosai ya musu, kafin ya shige gaba hubby na bayansa, har Hall din da ake waazi. Nan yasa hubby ta musu bankwana. Basu ji dadin barin hubby islamiyya ba. Don sun saba da ita, saboda son jamaarta.

Hubby naji tana gani haka, hayder ya tasota a gaba har wurin da tayi parking din motarta. Hannu ya mika mata alamar ta bashi key. Harara ta watsa masa kafin ta wurga masa. Da mamakinta ya cabe key din.

A hankali yake murza sitiyarin, cikin kwarewa, har suka iso gida, ba wanda ya tankawa dan uwansa.

Hubby takaici ne, ya cikata, data san abinda zai aikata mata kenan da ta hakura da zuwa makarantar har sai tasa Hajiya ta roka mata shi, tana matukar son makarantar, akwai koyarwa sosai, don ita dai, bazata taba iya tambayarsa ba.

Yana tsaida motar tayi cikin gida. Juya kan motar yayi ya fita.

A falonta ta tarad da Mariya da yusra, ai da sauri ta ajiye jakar suka rungume juna, suna murnar ganin juna. Tare da ihun murna. ” baki da kirki ko kadan!!! Sai yanzu kika tuna dani?” Hubby ta fada suna zama a 2 sitter din falon.

Kunne yusra ta kama, tana murmushi ” tuba nake, tun da muka dawo daga abuja banda lafiya, shiyasa ban zo ba. Sai satin nan na fara fita.”

” ayya shine ko a waya baki fada min ba? Ai da nazo dubiya.” Hubby ta fada tana murmushi

Ido yusra tadan zaro. ” ina ni ina fito da Amarya a dakinta. Ko Aisha sai jiya nake gaya mata.”

” to ya jikin? Duk da banji dadi ba da baki fada min ba, ko ba komai ai sannu tana da dadi.”

” sorry. Ya amarci?” Yusra ta fada tana murmushi

Harara hubby ta mata, ” yana wurin amaren asali.”

Mariya ce tama hubby sannu da zuwa, sannan ta bar falon.

” su waye kuma amaren asali, ban da Ku?” Yusra ta fada tana dariya

” su Aisha zaki tambaya.” Ta fada

Murmushi yusra tayi ” har dake, kinga yadda kikayi kyau, kikayi fresh? Gaskiya amarci ya karbeki, kodai mun samu ne?”

Duka ta dada mata a cinya. Da sauri yusra tasa hannu tana sosawa, saboda yanda dukan ya shigeta. Hararar hubby ta yi ” daga fadar gaskiya, sai ki tafasamin cinya?”

” wai ki dawo hankalinki ne, don na lura kamar kin kume, a ciwon nan.” Hubby ta fada tana harararta

” bakya kallon madubine halan? Amma duk wanda ya ganki ai yasan kin canza. In kuma mune baa son musan sirrin ai shikenan. Shi din ai dan duma ne baya boyuwa, da kansa ma zai bayyana kansa.”

Tsaki hubby ta yi, ” zako Ku Dade kuna jira.”

” don Allah kar ki mana bakin ciki. Ki bada hadin kai sosai nan da 8 to 9month muzo suna.” Yusra ta fada tana fuskar tausayi

” Allah ya tsare ni, in ce na haihu da wa? ” da kallo yusra ta tsare hubby

Har hubby ta tsargu da irin kallon da take mata. ” kallon na lafiya.?” A jiyar zuciya yusra tayi, tare da kyara zamanta.

” family planning kike yi hubby? ”  ido hubby ta zaro. ” wane irin family planning kuma?” Ta tambayeta

” gani nayi, in ba family planning kike yi ba. Mu muna da kyautata tsammanin in sha Allah kema ki samu rabonki, ki huta gorin rashin haihuwar da ake jifanki dashi. Tunda ko dama can ance miki komai naki is normal.”

Murmushi hubby ta yi ” zan so hakan, amma situation din, da nake a yanzu, ba maganar haihuwa a gabana.”

Kallonta yake cike da tambayoyi. Ganin kallon da take mata, yasa hubby mikewa, “muje ki canza kaya, ki tayani mu daura girki.” A tare suka nufi sama, ta bata wasu kayan ta canza, sannan suka nufo kitchen.

Fried rice, pepper chicken da coslow. Suka hada. Yusra na kallon ikon Allah, yadda hubby ta zubawa kowa, har mai gadi, bataga  ta ware na maigidanba. Kasa shiru tayi, ” banga kin zuba na hayder ba?” Murmushi hubby ta yi ” in ya dawo zai nemi abinda zai ci.” Da mamaki yusra ke kallonta.

” ta yaya zaki dafa abinci, amma ace ba kwanon mijinki? Anya hubby? “

” karki damu, kema kinsan halin hayder, shi yafi son hakan.” Hubby ta fada tana daukan trey din data zuba musu nasu a ciki.

” Allah ban yadda da ke ba.” Yusra ta fada tana tsareta da ido.

” shi kenan naji, mu ci abinci tukunna, sai muyi magana.” Kada kai yusra tayi, ta dau trey din ruwa da drinks tabi bayan hubby.

” hubby kiji tsoron Allah, ki rike aurenki da muhimmancin. Kar kibi, soye soyen zuciya, hakika zata kaiki ta baro. Menene laifin hayder? Kamar yadda kikayi biyayya, shimafa biyayyar yayi. Amma ace yayi cefane ya ajiye miki, amma ki dafa ki kasa bashi? Har sai lokacin da ya dawo sannan zai samawa kansa abin da zai ci? Bisa dukkan alamu hakkinsa ma na aure  ba bashi kike yi ba. A haka kike tunanin Allah zai barki? Hakkinsa ma kawai ya isheki.”

Ajiyar zuciya hubby tayi ” bazaki gane ba wallahi, its very difficult for me.”

” ehmm!!! Kin zabi kiji kunyar lahira data duniya ko? Fine.” Yusra ta fada

Shiru hubby tayi tana jin jina lamarin. Gaskiya yusra ke fada, amma gaskiya abin da kamar wuya, ita da hayder? Kai ina, bazata sabuba, wai bindiga a ruwa.

” ko zaki cemin ke baki da sauran filling ne?” Yusra ta jeho mata tambayar tana tsareta da ido.

Ido hubby ta zaro, tare da yamutsa fuska. ” a yanzu dai kam babu.”

Murmushi yusra tayi. Cikin ido sosai ta kalli hubby. ” wallahi karya kike, ba yadda za’a yi ki ce baki filling, muma da bamu taba auren ba, ya muka kare, balle Ku da kuka san dadin abun. Ko matan da kike ganin suke kin kara aure, don mazansu sun rasu, ko sun rabu, zaki samu 80%  sun manyanta. Amma mace da kuruciyarta da komai, ta ce bata filling? Wannan tatsuniya ce kawai.  Ki daina cutar dan uwanmu ki barshi ya mori kuruciyarsa. Haka kurun, ga mata komai yaji, amma zaki hana ruwa gudu.”

” sai kiyi kuma ai.” Hubby ta fada

” Allah ya shiryeki, tunda na lura kin zama mai kunnen kashi, baa isa a gaya miki gaskiya ba.” Yusra ta fada cikin bacin rai, tashi tayi ta yafa mayafinta, tare da daukar hand bag, ” ni na wuce, sai wani jikon.”

Agogo hubby ta kalla, 5:23pm ” tun yanzu? Ki bari dan can anjima sai ki yafi, please. “

” nop!!!! Akwai inda zan biya, kafin in koma gida. Nama manta ban gaya miki ba, an sa bikina, in 1 month time. “

Tsalle hubby ta fara, tana murna, tare da rungume yusra. ” congratulation, I’m so happy for u. Woww!!! What a greet news.”

” thanks. ” yusra ta fada tana murmushi.

” aminu ko halil?” Hubby ta tambayeta cike da murna.

” halil.”

” what a nice choice, kun dace, sosai wallahi. Allah ya kaimu lokacin.” Hubby ta fada.

Har mota ta rakota, sujayi sallama cike da kewar juna, Ta tafi.

           **********************

Tana kwance a 3sitter dake falonta na sama. Jira take 9 ya cika taje ta kwanta, kafin hayder ya shigo. Don yanzu ta riga ta karanci lokacin dawowarsa. Rabin hankalinta na kan series din da ake nunawa, a tashar starlife, Rabi ya tafi ga tunanin waazin da aka musu dazu a islamiyya da kuma magan ganunta da yusra.

Kamshin turaren da taji ya bugi hancinta, yasata dago da idonta, da sauri, ta kalli kofar falon……….

Gabanta ne ya fadi, kokarin tashi zaune ta fara, tunowa da kayan dake jikinta, yasa ta koma ta kwanta. Sanye take da aimless gown red. Roba ce, tabi jikinta sosai, kanta ko dan kwali babu, illah kama gashin da tayi donut dashi.+

A hankali ya karaso cikin falon, hannunsa daya dauke da mog, dayan kuma wani kwali ne, karami. Sanye yake da jallabiyya fara Sol, mai gajeren hannu. Zama yayi a kujerar da take facing nata, Ya daura kwalin kan center table.

She is uncomfortable, mu samman da taji, an dau lokaci bai ce mata komai ba. Kasa hakuri tayi, duk da yadda zuciyarta ke faman biting. ” what bring u hare?” Ta fada idonta na kan TV.

Kafarsa daya kan daya, yana sipping Green tea, da yasha kayan kamshi, hankali kwance. Ganin bashi da niyyar tanka mata, yasa ta daga kai ta kalleshi, ido hudu sukayi. ” am talking to u, wai me yasa ka gama raina nine.” Ta fada a lamar ranta ya fara baci.

Murmushin gefen baki yayi, sai da ya kara sipping Green tea dinsa, sannan ya kalleta, idonta a kan TV. ” tunda kika tako gidan nan, a matsayin matar Aliyu hayder ai raini ya kare.”

Ido ta zuba masa, cike da mamakin maganarsa, shi din ma ita yake kallo.

Murmushi tayi. ” kai a tunaninka hubby ta shigo gidan nan don zaman aure? Uhimmm!!! Lallai kam, bude kunnenka da kyau kaji.  u are a big dreamer. I came to your house as your big sister, babu dadi babu kari. Har zuwa time din da zaka samu abokiyar zama, u are free to married your choice.”

Murmushi yayi har tana jin sautin mirmushin nasa. ” I don’t understand u”

Harara ta watsa masa ” bafa da Hausa, ko wani yare nake maganar ba,? Ina nufin dani dakai kowa yayi harkarsa, don’t inter fare in my matters, nima I’m not inter fare in yours. That all.”

” yanzu na gane. Lokacin da zan wani auren, ke kuma inyi ya dake?” Ya fada still idonsa a kanta.

” ina nan a matsayin sister dinka, mana.” Ta fada

Gira ya daga yana tabe fuska, ” what about our parents?”

” ba zasu sani ba, we just pretend.”

Tabe baki yayi, yana jijjiga kai, a hankali. ” hakkokin igiya ukun dake kanmu fa? In mun boyewa iyayenmu, zamu iya boyewa Allah ne?”

Ganin alamar nasara yasa hubby mikewa ta zauna da kyau. Gaba daya tama manta da kayan dake jikinta. Burinta kawai ya amince da bukatarta.

” innalillahi wa inna ilaihir rajiun.” Hayder ke maimai tawa a zuciyarsa. Wani shock yaji, lokaci daya, da wani abu dake bin duk wani bargo da gaba na jikinsa. Lokaci daya hankalinsa ya tashi. Ba wani lafiyayyen namijin da zaiga hubby a lokacin hankalinsa bai kai kololiwar tashi ba. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da dauke idonsa a kanta.

Hubby Sam bata lura da kallon da yake binta da shiba. ” wannan ai abu mai sauki ne,! Na yafe duk wani hakkina dake kanka, kaima sai ka yafe hakkinka dake kaina, kaga shi kenan an zauna lafiya.?”

Kallonta ya kara yi, murya a shake, da kyar ya iya fisgo haruffan bakinsa. ” kinyi tunani me kyau. Ashe zero Head din, wani lokaci yana ja.”

Da mamaki take kallonsa, gani tayi ya canza mata lokaci daya, amma bata kawo komai ba. Illa haushin zero head din daya fada. ” amma kasan ban son rashin kunya ko?” Idon da suka canza kala ya zuba mata. For some time, ya kauda kansa. ” lokacin baccinki yayi.” Harara ta watsa masa ” na fika sani ai. Ba mu gama magana ba. Ka yafe din ko yaya.?

” in ban yafe ba, yazakiyi da ni.?” Ya fada idonsa can tv, kamar mai kallo, nan ko shi kadai yasan halin da ya ke ciki.

” you have your girlfriend right? U love her. Me and u a not in the same page,  We never love each other. So what is the big deal? ” ta fada cikin kosawa

” let me think about it. Zamuyi magana gobe, zan gaya miki abinda na yanke.”

Ba haka taso ba, amma ba yadda ta iya, dole ta bashi lokaci, she hope he accept her idea.

Mika mata kwalin da ya zo dashi yayi, ” from Ummul khair. Nasan zata miki anfani sosai.” Ya fada tare da gyara zamansa.

Amsa tayi tana jujjuya kwalin. Gaba daya ta manta da Ummul khair ta ce mata, taba junaid sako ya bata, tun ranar da aka kai Kowacce gidan mijinta. Ta manta shaf da maganar sakon, bata tambayi junaid ba, da taga shiru bai kawo mata ba. Sai yanzu ta tuna.

Mikewa tayi zata tashi, da sauri ta koma ta zauna, tare da rungume hannayenta duka biyu a kirjinta. Zuciyarta na faman dakan tara tara. ” innalillahi. ” ta fada a ranta. Kunya da jin takaicin kanta ya kamata. Idonta takai kan hayder TV yake kallo kamar bai san abinda takewa ba. Ganin hankalinsa na kan TV, yasa ta kwasa da gudu zuwa bedroom dinta.

Da jikin kofar ta jingina, tana sauke ajiyar zuciya. A hankali ta isa gaban madubi. ” la haula wala kuwwata illa billah.” Ta fada ganin yadda kirjinta ya fito sosai a cikin rigar, hatta nippule dinta kana iya hango shatinsu. A tsaye suke char, kamar sa tsole maka ido. Su ba manya ba ba kuma kanana ba, Masha Allah.  Kunya da takaici ne suka cikata. Tabbas hayder ya gama ganeta tsaf, tana can tana shirmenta. No wonder taji muryarsa ta canza, lokaci  daya.

” Allah ya isana.” Ta fada tana shigewa toilet.

Wani wawan ajiyar zuciya hayder ya sauke. Da ido ya bita, har ta shige bedroom dinta. Sannan ya dauke idonsa, tare da kara kashingida a jikin kujerar, don baya jin yana da sauran kuzarin da kafafuwansa zasu dauki gangar jikinsa zuwa bedroom dinsa.

Kanshi ya dafe da hannu daya. Yasha ganinta ba hijab, amma bai taba tsayawa ya kare mata kalloba. No wonder, shi abun na daure masa kai yadda samarinta ke nunawa a kanta. Abin har haushi yake bashi, yaga me tafi sauran mata da suke nuna hauka a kanta haka? Tunawa yayi, da week din aurensu yadda suraj kangiwa ya zo ya sameshi, lokacin yana masallaci yana daukar karatu. Rokonsa ya fara, harda ko nawa yake so, zai bashi ya saki hubby. Murmushi yayi a lokacin ” bazan iya abinda kake son inyi ba.?”

Tsugunnawa yayi, yana rokonsa ” nasan baka son Habiba, kamar yadda na kwana da sanin bata sonka. Don haka ina rokonka ka saketa. Daga million daya, zuwa billion zan baka in har zaka mun wannan alfarmar.”

Tsugunnawa hayder yayi shima. ” kayi hakuri, tabbas bana sonta, iyaye suka hada mu, bani kuma  da ikon rabuwa da ita. Baka da kudin da zaka bani don in saketa, I have my on business, my on earning. Kudinka bazai sani in sabi mahaliccina ba. In saketa don ka aura, haramun ne, don haka bazan yi don in faranta maka ba. Shawarata a gareka shine ka rungumi kaddara, kamar yadda muka runguma da hannu biyu.”

Tashi yayi, ya barshi a wurin, yana mai jin tsananin tausayinsa.

Tunowa yayi da Abdul Karim, yaya Ahmad, duk da shi bai bayyana nashi soyayyarba, amma ya kwana da sanin dan uwansa na son hubby. Salis da Engr Sahabi. Tabbas yaso hubby ta auri salis, don duk inda kamilin mutun yakai salis ya kai. Yana mutuntashi, da ganin girmansa matuka. Kamar yadda ya kwana da sanin matsayinsa a wurin Yusuf.

Ajiyar zuciya ya sauke, tunowa da irin son da Yusuf yake mata. Magan ganunsa suka fara dawo masa one after the oder. Musamman haduwarsu ta karshe, bazai taba manta wannan lokacin ba. Kamar yadda abubuwan da suka faru a lokacin ba zasu taba gogewa a ransa ba. Mutun baya taba gujewa kaddararsa tabbas haka abin yake.

Tunanin maganganunta na yanzu suka fara dawo masa, Murmushi yayi yana shafa sajensa a hankali. Duk da baya sonta, shi ba jahili bane, yasan tanada hakki a kansa, daga lokacin da aka daura aurensu, kamar yadda yake da hakki a kanta. Dama ya daga mata kafa ne yaga iya gudun ruwanta. Yanzu ne zaa fara wasan. Don ba zai taba yafe hakkinsa ba. Ama tsayinsa na lafiyayyen namiji, wanda yake ganiyarsa. Ba zai iya hakuri ya zuba mata ido ba. Ganinta a yanzu ya kara masa son kasan cewa da ita.

Mikewa yayi, ya kashe komai, ya nufi bedroom dinsa, wanka yayi, tare da shirin bacci. Gaba daya daren baccin hayder kadan ne. Daya rufe idonsa surar hubby ke yawo a danuwansa. Dole ya tashi ya fara nafila.

               ******************

Sai da tayi shirin kwanciya, sannan ta dauko kwalin ta bude. Dariya tayi ta daga bulalar tana kallo. ” ya Allah ka shiryi Ummul khair. ” ta fada tana Ciro karamar takardar dake ciki.

” special gift to my beloved sister. Karki raga masa ko kadan, naji su Anty ummu khulsum na cewa ki bishi a hankali.  In ya miki ba dai dai ba, Zaneshi zakiyi sosai, jikinsa ya gaya masa, ba daga kafa, in ba haka ba rainaki zai yi.”

Dariya hubby tayi tunowa da ranar da hayder ya aunata da bike dinsa. Watan Ummul khair bata manta maganar bulala ba. ” yar banzan yarinya, zamu hadu ne.” Maida bulalar tayi ta ajiye. Maganar hayder ce ta fado mata. ” nasan zata miki anfani sosai. ” me yake nifi? Haka taita kokarin hasaso abinda maganar ke nufi ta kasa, don haka, ta tattara ta watsa tunanin a kwandon shara.

              *******************

Da safe basu hadu ba, kamar yadda suka saba tashi, kusan a tare. Don hayder baccin da bai samu da daddare ba, yake ramawa. Hubby kam abun ya mata dadi, don bata shirya fuskantarsa ba. Har yanzu yana jin kunyar yanda ya ganta.

Sai bayan sallar la’asar ya sameta a falon ta na kasa, ita da Mariya. Shigowarsa Mariya ta fita, bayan ta gaishe shi. Yanzu kam ta San shine mai gidan, saboda yawan ganinsa da takeyi. Sannan tasan duk baki mazan da sukeyi iyakarsu falon gasa, amma shi sau da yawa tana ganinshi ya sauko, ko zai hau.

Zama yayi, tare da mikar da kafarsa daya kan center table din gabansa.

Sun kai 15min ba wanda ya tankawa dayansa. Kunya da haushinsa ne suka hana hubby magana.

Cikin muryarsa mai kama da anmasa dole, don sanyi, da yadda yake fitar da haruffan bakinsa. ” I accept, amma ina son muyi a rubuce, kar daga baya ki canza magana.”

Murmushi tayi, nan da nan farin ciki ya cika ranta. Mikewa tayi da sauri ta nufi of stairs, minti kadan sai gata da pepper da pen, Mika masa tayi. Kallon pepper din yayi, ya kalleta. ” ke kika bukata, don haka ke zaki rubuta.”

” OK. Me kake son in rubuta?” Ta tambaya tana kallonsa

Tabe baki yayi, yana shafa sagensa, alamar ya zama masa jiki, yin hakan.

” fist ki fara jero hakkin mata a kan mijinta, then hakkin miji kan matarsa. U write kin yafe duk kan hakkokinki dake kaina. Then sai kiyi sign. I will write my on, sai kowa yayi sign. Sai muyi photocopy kowa da nashi. Then shi kenan.”

Zama tayi, ta fara jero su, kamar yadda ya bukata. Duk da wasun ta kanji nauyi da kunyar rubutawar.

Hakkin mata a kan mijimatarsa::;-

1. Ya biya ta Sadakinta na Aure.

2. Ya kula da Addininta.

3. Ya daukin nauyin cinta, shanta, suturarta, har da kayan kwalliya nata.

4. Ya ba ta hakkinta na aure.

5. Ya dauki nauyin kulawa da lafiyarta.

6. Ya daukin nauyin karatunta musamman ma na Addini.

7. Ya nuna mata soyayya a fili.

8. Ya rika mu’amala da ita a cikin sauki kamar karamar yarinya.

9. Idan ya shigo gida ya rika sakar mata fuska da fara’a.

10. Ya rika yaba mata idan ta yi abin kirki tare da yi mata Addu’a ta fatan Alkhairi.

11. Ya rika sauraron korafe-korafenta da shawarawarinta.

12. Ya rika yafe mata idan ta yi masa ba dai-dai ba, kuma yana gyara mata cikin hikima.

13. Ya rika yin kwalliya da ado domin ta gani ta ji dadi.

14. Ya ba ta lokaci na musamman a lokutansa domin yin hira da ita kawai.

15. Ya rika cin abinci tare da ita.

16. Ya ringa taimaka mata wajen aiyukan gida musamman idan ta samu rauni na laulayin ciki ko na rashin lafiya tare da tausaya mata.

17. Ya rika nuna damuwa cikin abin da ta damu da shi, da farin a cikin abin da take farin ciki da shi matukar bai saka wa Allah ba.

18. Ya girmama iyayenta da ‘yan uwanta.

19. Ya ringa yi mata kyuata ta musamman domin faranta mata rai.

20. Ya rika fita da ita wurare na musamman kamar ziyara ko wurin karatu ko wurin shakatawa.

21. Ya rika b oye aibinta.

Hakkin miji a kan matarsa::;-

1 – Soyayya ta gaskiya.

2 – Tsare Amana Miji.

3 – Tausasawa miji da wasa da dariya da shi.

4 – Tsare sirrin miji.

5 – Ba za ta fita daga gidansa sai da izininsa.

6- Ba za ta yi azumin nafila ba sai da izininsa.

7 – Ta yarda ya sadu da ita duk lokacin da yake bukata, dan Annabi Mai tsira aminci yace duk matar da taki mijinta ya sadu da ita a duk lokacin da yake so, toh Mala’iku zasu ta la’antar taba zasu su daina ba har sai lokacinda ta yarda da shi. (BUKHARI/MUSLIM).

8 – Ta saurari mijinta kuma tayimasa biyayya matukar ba aikin laifiya umurceta dayi ba.

9 – Mace ta nisanci raina abin da mijinta ya bata, domin Annabi Muhammad mai tsira aminci ya ce “Mata zasu shiga wuta ne saboda kafurce wa mazajensu, wato raina alherin miji” (BUKHARI/MUSLIM)

10 – Ka da mace ta cutar da mijinta da magana ko da aiki.

11 – Mace tayi ado da kwalliya wa mijinta, saboda Annabi mai tsira da aminci yace “Allah kyakkyawa ne, kuma yana son kyakkyawan abubuwa, (IMAM MUSLIM YA RUWAITO).

12 – Mace ta tsare dukiyar mijinta da na ‘ya’yansa harma da na gidansa, dan Annabi mai tsira da aminci ya ce “Mace mai kiwo ce a gidanta, za’a tambayeta abin da ta kiwata.

13 – Mace tayi gaggawan baiwa mijinta hakuri a duk lokacin data ga yayi fushi, Tace masa, dan Allah kayi hakuri, ban san abin da na yi zai ba ta ma ka rai ba, ka yafe mi ni dan girman Allah.

14 -Mace ta yiwa mijinta dukkan irin aikin da ake bukata ayishi a gida.

15 – Mace ta kyautata halayenta ga iyalan mijinta.

16 – Mace ka da ta yi abokantaka da mugayen kawaye, sai su hallakar da ke baki sani ba.

17 – Mace ta zama mai tausayawa mijinta, kamar yadda uwa take tausayin ‘Danta.

18 – Mace ta zama mai Biyayya ga mijinta.

19 – Mace ta zama Abokiyar rayuwa ga mijinta.

20 – Mace ta kusanci dukkan abinda mijinta ya ke so.

21- Mace ta nisanci dukkan abin da mijinta ya ke ki.

22 – Ki yi murmushi a duk san da mijinki ya kalle ki.

23 – Ki yi masa addu’a a duk lokacin da zai fita, ki ce a dawo lafiya Allah ya bada sa’a.

24 – Ki yi masa addu’a kuma a duk lokacin da bakya ganinsa bayan bayanan.

25 – Idan mijinki ya dawo ki karbi abin hannunsa, tare da yi masa sannu da zuwa, dan girmama shi.

26 – A duk samda zakiyi magana da mijinki ki gaya masa magana mai dadi, mai tabshi, kada ki daga muryanki a kan nasa, kuma kada ki masa tsawa har ki harare shi.

27- Ki zama cikin tsabta da kamshi mai dadi duk lokacin da kuke tare.

28 – Ki sanya hijabi a duk lokacin da kuke tare da wadanda ba muharramanki ba.

29 – Ki sa lokaci idon ki, ki kuma shafa jan baki, kuma ki shafa turare, amma sai kuna tare dashi a gida dan mace bata shafa turare ko jan-baki ta fita anguwa dashi.

30 – Ki kaskantar da kai dan biyayyaa gare shi.

31- Ki san lokacin da yake dawowa dan kada ya sameki a cikin kazanta, ki kuma san lokacin cin abincin sa dan ki tanada ba sai ya zo yana nema ba.

32 – Bayan kin gama masa komi ki tambaye shi ko yana da wata bukata a gareki, dan mi biya masa ita.

33 – Kar ki nuna murnan ki idan wata hasara ta same shi, ki nuna masa kamar kece kika yi hasarsar.

34 – hakanan kiyi murna da duk wani alherin daya samu.

35 – Ki zama kamar matan sahabbai, yadda sukewamazajensu. Idan miji zai fita sai su ce a dawo lafiya, kar ka kawo ma na haram zamu iya hakuri dayunwar duniya, amma baza mu iyahakuri da azaba ba gobe lahira.

Kallonta yake yadda ta Dage sai zuba rubutu take. Murmushin gefen baki yayi yana kada kai.  Mika masa tayi.

” I’m don.”  Ta fada tana murmushi

Amsa yayi, yana bin abunda ta rubuta daki daki. Murmushi yayi. ” Ashe ba zaman cika benci kike a makarantar ba?” Ya fada still idonsa a kan pepper din.

Harararsa tayi, ” just sign, ban tanbayeka dogon turanci ba. Koma mai zaka ce, ka dade baka fada ba.”

Kansa ya dago yana kallonta, mika mata hannu yayi, pen din ta sa masa a hannun. Tana watsa masa harara. Don taji haushin maganar daya fada. Badon tana son su rabu lafiya ba, da sun kwashi yan kallo.

Ya daura pen din kenan zaiyi sign sukaji nocking, gaba daya suka kai kallonsu ga kofar shigowa…….

just sign, let me cheek the door. ” ta fada tana nufar kofar.+

Ahmad ne da iyalansa. Yaran na ganin hubby ta bude kofar suka dale jikinta, suna dariyar murna. Itama dariyar ta fara tana kara rungumosu jikinta. Murmushi munaya tayi. ” ni dai aban hanya na wuce, na gaji da tsayuwa.” Dariya hubby tayi ta daga jenior, tare da rike hannun ashraf suka shiga ciki, tana musu bisimillah.

Da sauri hayder ya taso rungume dan uwansa yayi, tare da goga kumatun juna, kamar yadda suka saba. Sannan ya fara daga yaran sama suna dariya.

Tasnim ya amsa a hannun munaya, sannan ya gaisheta.

Jan dan uwansa yayi, suka nufi main falo. A kabar hubby da munaya da yara.

Kitchen ta nufa, yaran na biye da ita, sai zuba mata surutu sukeyi. Kayan sha ta hada a trey taba Mariya takai main falo. Sannan ta dauki na munaya suka fito. Zama tayi bayan ta ajiye trey din. Sannan suka gaisa, cikin mutunci kamar ba abunda ya hadasu.

” a mana afuwa, bamu samu zuwa ganin daki da wuri ba.?” Munaya ta fada tana murmushi

Murmushi hubby ta mayar mata ” ba komai, ai gashi kunzo yanzu.”

Gaba daya hubby ta kasa sakewa da ita, hakan yasa da yawan hiran ita da yaran suke kayansu, sai jefi jefi, munaya ke saka musu baki. Ita kanta kunyar hubby take ji, abinda ya Jamata rashin zuwa tun tuni kenan, sai yau da Ahmad ya matsa mata tukunna.

Mariya ce ta shigo, tama hubby sallama, lokacin tafiyarta yayi. Kallon ta hubby tayi. ” Mariya yau kam, zaki min hakuri, zuwa dare sai in sa a mayar dake gida.”  Kada kai Mariya tayi ” to Anty, amma zaki kira mama ko? Don kartaga shiru.”  Phone hubby ta dauka zata kira mmn Mariya. ” ki barta kawai ta tafi, I will help u” munaya ta fada

Ba yadda hubby ta iya, ta sallami Mariya ta tafi.

Kitchen suka nufa, nan idon munaya ya raina fata. Da kallo takebin ko ina na kitchen din. ” woww!!! Gaskiya Anty hubby gidanki ya burgeni ba kadan ba.” Munaya ta fada tana kara kallon kitchen din.

Murmushi hubby tayi ” na gode.”

” me zamu dafa?” Hubby ta tambayeta.

” abun dadi, kin san nayi missing din girkinki sosai.” Munaya ta fada tana murmushi

Murmushi hubby tayi, tunowa da old-time.

Book ta mikewa munaya ”  duba mu gani, ko akwai abunda zamu iya yi a ciki.”

Wani hadadden drawer hubby ta bude, ba komai a ciki sai chocolate kala kala, da kwalayen Lipton, green tea, black tea, English break fast, flavour tea gasunan kala kala. Chocolate ta zuba a plate, ta nufi falo inda su jenior ke kallon cartoon. Ta basu, ta koma wurin munaya, da ruwan ido ya hanata tsayawa a kan girki daya.

Suna aiki, suna hira jefi jefi. Munaya ta kalli hubby dake soya rice. ” Anty hubby don Allah kiyi hakuri ki yafe min abinda ya faru, wallahi sharrin shaidan ne, da zugar su Anty samira. Sai rikicin aurenki da Abdul Karim nake jin komai, na makircin da take kullawa a kanki. Kunyarki ta hanani zuwa gidan nan. Don Allah kiyi hakuri. “

Murmushi hubby tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. ” na dauka kinfi kowa sanin halina, a lokacin sama da ita? Saboda nafi kusa da ke a kanta. Na dauka ko wani ya fada wannan maganar a kaina, ke me bada shaida ce gareni. Bazan boye miki ba naji zafin abinda kika mun a cikin jamaa, wanda da ni dake ne, bazan damu sosai ba. Amma ba komai na yafe miki, komai ya Riga ya wuce. Sai dai ina son kisa a ranki. Hubby bata taba son wani ba, bayan Yusuf. Tsakanina da Ahmad mutunci ne, da ganin girman juna, Nothing more.”

” kishine ya rufe min ido, a lokacin. An sha kawo min gulmar, ban taba daga kai ba, sai lokacin. I’m sorry “

” ba komai ya wuce. I understand.” Hubby ta fada

Hira suke yi, suna dariya kamar ba abinda ya taba faruwa. Dama can akwai shakuwa tsakanin hubby da munaya. Munaya bata da matsala, barta dai da son class, komai nata irin na big class take yi.

Hayder ne ya leko, ya shaida musu sun wuce masallaci, har da yaran.

Suma lokacin sun kammala komai, hubby na wanke kayan da suka bata, munaya na goge -goge. Sai da hubby ta shirya musu abinci a dinning din main falo, nasu kuma, suka haura dashi falon sama.

Wanka sukayi bayan sun idar da sallah. Wani hadadden arebian dress hubby taba munaya tasa. Sannan suka nufi falo don ba ciki hakkinsa.

Santi kawai munaya ke zubawa. ” Allah kinji da dinki, ina ma ni na iya girki haka. Munyi missing abincinki sosai wallahi. ” murmushi hubby tayi. Don a zamanin baya sau da yawa gidanta munaya take zuwa suyi girki ta dauka zuwa gidanta. Expectially weekend’s. Wani lokaci kuma, hubby ke girkawa ta aika musu.

Bayan sun tattara wurin. Munaya ta dauko Jakarta. Mikawa hubby wata Leda tayi. ” gashi kowanne da yadda zakiyi anfani dashi, suna da kyau sosai. Tun daga Niger aka kawomin su.” Amsa hubby tayi, tare da godiya. Don bazata iya ce mata tabar kayan ta ba. Ko ba komai ta ajiyewa  Aisha ko su ummu sulaim. Duk wandda Allah ya kawo ta.

Wani tablets ta fito dashi, guda biyu tasha daya ta mikawa hubby daya. ” ki sha wannan ki gani, a kwai aiki. In ya miki next time in zaa kawo min, zan ce a kawo kwali biyu.”

Kai hubby ta kada ” ki barshi kawai Maman junior in zaa kawo miki, a kawo mana tare.” Ta fada don karta dagota.

” no. Kin san kalan kyansa.? U have to try it.” Munaya ta fada tana ballo tables din daga gidansa.

Ganin hubby tana mata wasa da hankali, yasa ta bata rai. ” Allah sai kin sha, ke matsalata dama dake kenan. Dole mutun ko yana da kyau ya kara da wanka.” Ruwa ta zuba a cup ta mikawa hubby.

Dole yasa hubby amsa. Ruwa ta kurba, tare da jefa tablet din a baki, da niyyar ta ma munaya wayau ta ajiyeshi a bakinta for some second taje ta zubar. Tana jefawa a bakinta ya wuce. Ido ta zaro. Tare da  fadin ” innalillahi wa inna ilaihir rajiun.” A kasan ranta.

Dariya munaya tayi, ganin yadda hubby keyi da fuska. ” bafa shi da wani taste,” ta fada don a tunaninta, ko taste din ne baima hubby ba.

Hira suke yi sama, sama, munaya ta kalli hubby. ” wai Anty hubby bakya gajiya da wannan zunbulelen hijab din ne? Tun da muka zo kike ta fama, har girki duk dashi, ko zafi bakyaji? Kamar wata matar malan.”

Murmushi hubby tayi, ba tare data tankawa munaya ba.

” au!!!! Sorry, ashefa matar aramma ce. Amma don Allah adinga cirewa ana shan iska. Ni ina zan iya?, sallama Allah- Allah nake in idar in cire.”

Murmushi hubby tayi kawai.

Sai after 8 su hayder suka shigo. Yau ne rana ta farko da hayder ya saka abincin hubby a bakinsa. Shi din ma don gudun kar Ahmad ya gano, irin zaman da sukeyi ne. Yasa shi zuba soup din kaza.

Ahmad kam santi yayi ta zubawa. Tare da gayawa hayder yadda sukayi missing girkin hubby. Shi kansa bai san ta iya girki haka ba. Yasan dai duk lokacin da ta kawo, kamshin girkin na kayatar dashi, amma bai taba marmarin dan danawa ba, duk da santin da yake jin su Hafiz nayi.

Sai after 9 su Ahmad suka musu sallama. Set din sarkar gold mai kyau da girma yaba hubby. A matsayin gudunmawarsa. Godiya sosai ta masa. Tare da cika yaransa da kayan zaki, Leda guda. Suka rakosu har mota.

Cike da kewar juna suka rabu, suna daga musu hannu.

Suna shigowa hayder ya wuce sama, ba tare da sun cewa juna komai ba. Duk da taso ta tambayeshi maganar takardar yarjejeniyarsu. Amma ganin yadda ya hade fuska, yasa itama ta shareshi.

Kayan da suka ci abinci dasu ta tattara, tare da gyara wurin.  Sai da ta wanke su tsaf, sannan sauran abincin ta sasu a containers ta sa a fridge. One this about her. Bata son barin ko cokali, ya kwana ba tare data wanke ba, Matukar anyi anfani dashi.

Direct toilet ta nufa, ruwan sanyi ta sakarwa kanta, Saboda yadda take jin jikinta.

Hadadden man culachum, ta shafa sama- sama, tare da sanya kayan baccinta, Aimless da boom shot. Fink colour. Gashinta ta kama ta nade shi, kafin ta saka hula pink.

Shigewa cikin duvet dinta tayi tare da karanto adduoin kwanciya bacci.

Juye- juye ta fara, tana jero tsaki. ” haka kurun ina managing kaina, tazo ta tsokalomin fitina.” Wata zuciyar Hubby ta fada. Tana kara Jan tsakin.

Zuciyarta ce ta fara mata wasi- wasin anya kuwa tasa key a kofarta? Don shigowarta Allah -Allah take ta shiga toilet ta watsawa kanta ruwa. Ganin ta kasa samun natsuwa yasa ta sakko ta nufi kofar, cike da kasala, da nauyin jiki. Tana kokarin kai hannunta kan kofar, yana turo kofar tare da shigowa cikin bedroom din.

Sanye yake da kayan bacci, marasa nauyi, Riga da dogon wando. Light blue.

Ido hubby ta zaro tana binsa da kallo, don bata taba tsammanin yanada karfin zuciyar da zai sake shigo mata bedroom ba. Matsawa tayi, ganin jikinsu na neman gogar na juna. Hakan ya bashi damar murza key din, tare da zareshi daga jikin kofar.

Zuciyarta ta fara dukan tara- tara, ” what bring u hare at this time? ” ta fada tana mai hadiye yawu dakyar. Don a tsorace take, smacking yayi, yana kara jingina da kofar, hannunsa duka biyu nade a kirjinsa, kamar yadda ya harde kafafunsa biyu. Daga inda take tsaye tana iya hango faffadan kirjinsa dake bude, ga six pack dinnan sun fito sosai masha Allah. Kana ganinsa kasan akwai karfi, yadda damtsen hannunsa suke a murde, ga jijiyoyi sun fito  sai daukar ido suke,  jikinta ne ya dau rawa ganin kallon da yake binta dashi, yasata tunowa da kayan dake jikinta. Da sauri ta juya don ta sa hijab dinta.

Bataji takowarsa ba, sai ji tayi an kwace hijab din. Da sauri ta waigo sukayi ido hudu. Jikinta na rawa kamar yadda muryarta ta dau rawa.

Wurga hijab din yayi can gefe. ” what come over u.” Ta fada cikin rawar murya.

Murmushi yayi, tare da daga mata gira. ” laifine don miji ya shigo dakin matarsa?” Ya fada in husky tone. Zuciyarta ne ya kara tsananta bugawa.

Kallonta sosai hayder keyi tare da furta ” fatabarakal lahu ahsanul khalikin.” A kasan zuciyarsa. Wani irin filling ya ke fisgarsa zuwa gareta. Duk da ba abin daya shigo dashi ba kenan.

Hannunta ta hada duka biyu, jiki na bari. ” don Allah ka fita, koma meye zamuyi magana da safe.”

Bakinta yake kallo zuciyarsa na saka masa abubuwa da yawa kanta. A hankali ya fara takowa zuwa gareta. Ganin haka yasa ta fara ja baya, still hannunta a hade, tana mai maita ” please please. ” gaba daya ta gama rudewa da yanayinsa.

Ritsata yayi, lokacin da takai bangon dakin. Hannayensa duka biyu yasa ya dafe bangon dashi, ya sata a tsakiya. Zuwa lokacin hubby sumane kawai batayi ba don tsananin fargaba, don gaba daya ya canza mata, kamar ba hayder data sani ba.

Fuskarta ya dago da daya hannunsa. Da sauri ta runtse idonta, don bazata iya kallon cikin idonsa ba. Cikin karfin hali ” please hayder don’t do this to me, I’m your sister, Please.”

Murmushi yayi, har tanajin sautinsa a kunnenta. A hankali yakai bakinsa kan nata. Gaba dayansu wani shock ne ya ziyar cesu a tare, ga hubby kan tsananin tsoro, ne ya kara cika mata zuciya. Datse hakoranta tayi, taki bashi damar samun abinda yake so. Tana jin sautin murmushinsa a kan fuskarta. Gaba daya ya rungumota jikinsa, yayin da daya hannunsa ya fara yawo a jikinta. Still bakinsa na kan nata, yana lasan labbanta a hankali kamar yaro ya samu alawa.

Kokari ta fara don ta kwace jikinta, amma ko gezau, hannunsa da taji a kirjinta, yasa ta bude baki, don tayi ihu. Hakan yabashi damar zura harshensa sosai cikin bakinta.

Duk yadda hubby taso kwatar kanta ta kasa, tun tana dan turjewa, har itama sakon ya fara kaiwa ga kwakwalwarta. Abinka da an dade baa haduba, ga aikin munaya.

Gaba daya tsayuwar ta gagaresu, dagata yayi cak, zuwa saman bed dinta.

Sunkai tsawon lokaci, suna sarrafa juna. Hayder yakai kololuwar bukatuwa da ita, yana gaf da cimma burinsa. Tunanin basuyi nafila daya dace suyi ba, ya masa birki, duk yadda yaso yayi ignoring din abun ya kasa. Dole yadan janye daga hubby yana sauke ajiyar zuciya, Tare da gangameta a jikinshi sosai. Kara narkewa tayi a jikin nasa. Don gaba daya tunaninta ya dade dayin kaura daga jikinta. Gaba daya hayder ya gama rikitata da salonsa. Daga ita har shi ajiyar zuciya suke sakewa a hankali.

Iskar bakinsa, ya hura mata a fuska. Far tayi da idonta, wanda ya kara mata kyau. Kar idonta ya sauka a kan hayder. Kamar ringing din bell haka taji a tsakiyar kanta. Ido ta zaro, tare da mikewa da sauri. Kokarin sauka daga bed din tayi, zuciyarta na zafi, da kuna, takaici, da haushin kanta duk sun cika zuciyarta a lokaci daya.

Kara tayi, tare da janye duvet din dake tattare a gefe, ta rufe jikinta, tare da yin toilet da gudunta.

Yana daga kwance yana kallonta, gaba daya jikinsa ba kuzari. Murmushi yayi ganin tayi toilet da gudu.

Tana sa key din kofar, ta jingina tare da fashewa da wani irin kuka, mai cin rai. A zaune take dirshan tana kuka iya iyawarta.

A hankali ya tako zuwa jikin kofar, kwankwasawa yayi, yana kiran sunanta. Daga inda yake yana jiyo sautin kukanta.

Yakai 15 min a tsaye, yana faman kwankwasawa, taki budewa.

” ka fitar min a daki, ban son ganinka, mugu sai Allah ya sakamin.” Ta fada cikin muryarta data fara dashewa don kuka.

” just open the dam dor.” Ya fada in high tone

” anki din. Da in kwana da kai gara na kwana a toilet.” Ta fada

Ranshi ya fara baci, yanzu kam. ” in kin so ki shekara a ciki.” Ya fada cikin bacin rai

” yafi min ganinka ai, mara kunyan banza. Tun mutun bai tafasa ba yana son ya kone.”

Murmushi mai ciwa yayi ” ni kike gayawa wannan maganar, don na nemi hakkina a wurinki? In kin isa ki fito ki gaya min face to face mana.” Ya fada cikin bacin rai

Tsaki hubby tayi. ” duk maitarka wallahi bazan fito ba. Kuma An fada din kayi abunda zakayi. Mara kunyan yaro. Kwalelen kare da hantar kura, nan gani nan bari, kar kuma in kara ganin kafafuwanka a dakin nan, in ba haka ba duk abinda na maka, kai ka siya da kudinka.”

Shi abinma dariya ya fara bashi. Wannan shine, ga tsoro ga ban tsoro. ” ki jika kisha in kin isa!! Keep that in mind da kanki zaki kawomin kanki, ina shararren wurina. Bana bukatar sake zuwa dakinki. Wannan shine alkhawarin hayder to u.”

” Allah ya kiyaye,.” Ta fada tana Jan tsaki.

Murmushi yayi, ” zamu hadu ne, very soon, zakiyi bayani.” Ya fada yana maida kayansa. Sannan ya fita zuwa dakinsa.

Wanka ya sake, sannan yayi shirin bacci. Daya rufe idonsa moment dinsu yake gani a idonsa. Murmushi yake ta sakewa cike da nishadi, don shi kadai yasan garar daya kwasa, duk da bai kai inda yaso ba, amma he’s happy. A haka har bacci ya sace shi.

Hubby kam, jin fitarsa, yasa tai saurin fitowa ta sawa kofarta key. Toilet ta koma, tayi wanka, tare da Dirje jikinta sosai, tanayi tana hawaye, tuno da yanayin da suka kasance ita da hayder. Ihu ta sake tare da durkushewa a wurin. Abune da ko a mafarki bata taba kawawa ba, ta dauka ko giyar wake hayder yasha bazai tunkareta da bukatar shiba, but she is mistaken. Tabbas ta yadda namiji ba kunya, tunda har ya iya shafawa idonsa toka.

Allah ya isa tafi kwando dubu, ta jawa munaya da hayder. A ganinta da badan tablet din munaya ba, ba abunda zai sa tayi losing control dinta irin haka.

Yau gaba daya bacci kaura yayiwa hubby. Tunanin rayuwa, da tunanin Yusuf su suka tsaya mata a rai. After all mamakin hayder da karfin halinsa. Tabbas sai ta dau babban mataki a kansa, in har tana son ta zauna lafiya.Yau da farin ciki hayder ya tashi, rabon da ya tsinci kansa cikin farin ciki haka, tun kan aurensa da hubby.+

Har ya gama break fast, ba hubby ba alamarta. Dama ya kwana da sanin ganinta zai masa wuya kam. Murmushi yayi daga gani na mugunta ne, ya kara kai kallonsa steps din. Key din bike dinsa ya dauka yayi gaba.

Sai da ya dan tsaya typing a wayarsa, yayi sending tukunna, ya tada bike dinsa, malan idi ya wangale masa get, tare da kwasar gaisuwa. Ya fice abinsa.

Tana tsaye daga window taga fitarsa. Tsaki taja. ” jishi sumi sumi, kamar in an sa masa hannu a baka bazai ciza ba.” Ta fada tana sake labulen. Sannan ta dau hijab dinta ta zunbula, ta sakko donta nemama kanta abin da zataci.

Sun gama gyara gidan, tare da sa turaren wuta, mai matukar kamshi. Ta haura sama donta dauko wayarta data manta a bedroom dinta. Miss calls ne, sai sms. A hankali ta fara bin sms din. Har tazo kan wani un save number, kamar bazata budeba wata zuciyar ta ce ta bude tagani. ” ki shirya kije ki gaida su mommy, Hajiya da Hajiya babba, Hayder ”  tsaki taja duk da taji dadi, don ta dade tana son zuwa, amma saboda sai ta tambayeshi, yasa ta gwammace taita zama a gida.

Cike da murna da doki ta fara shiryawa, cikin wani rantsatstsen less light yellow, dinkin doguwar Riga, taji aikin da stones. Light blue na hijab mai hannu, da shoe and bag light blue. Tayi kyau sosai.  gida ta kai Mariya, sannan ta wuce gidan Alhaji babba.

Tarba Sosai ta samu, tayi saa Alhaji babba na gida. Turaruka masu tsada da kamshi, ta kawo musu. Ta dade tare dasu, sannan ta musu sallama, nasiha sosai suka kara mata.

Gidansu ta wuce, a harabar gidan taci ta tarad da su junaid. Ranta bai so ba don yanzu dukansu haushinsu take ji.

Da faraa suka gaisheta. Dole haka ta saki fuskarta ta amsa musu, tare da shigewa ciki. A kofar shiga falon mommy Hauwa sukayi karo da hayder dake fitowa, Da sauri taja baya. Tsayawa yayi, yana kallonta. Kin dago kanta tayi, don haushinsa dosai ta keji, da kunyar ya gama ganeta. Murmushi yayi tare da furta ” sorry ” a kasan makoshinsa. Ya bi gefe ya wuce.

Da harara ta raka shi, har ya bacewa ganinta, sannan ta shige ciki da sallamarta.

Mommy Hauwa na zaune a falo da jafar hubby ta shigo. Tana arba da mommy Hauwa a zaune da gudu ta je ta rungumeta.

Dariya mommy Hauwa da jafar suka sa. Jafar ya ce ” yar halas taki anbato, yanzu dama mijinki yake cewa kina nan zuwa, Ashe ma har kin iso.” Harararsa tayi, jin ya kira hayder mijinta.

Dariya yayi, don bai gane dalilin harararba. ” harara daga zuwa? Allah ya baki hakuri.”

” nayi fushi da kai da jabir. Don haka karma ka kulani.” Ta fada tana turo baki cikin shagwaba.

Kunne ya kama ” tuba mukeyi sis, jiya muke maganar zuwa wurinki da jabir.'”

Harararsa tayi ” ba wani nan!! Don ka ganni ne, shiyasa. Amma na tabbatar kun manta dani kwata kwata, ba zuwa ba waya. “

Mommy Hauwa ya kalla, yana mata alamar tasa baki.

Dariya mommy Hauwa tayi. ” karka sani a ciki, ba ruwana.”

” kai mommy!! Kina wurinfa muke maganar zuwa gidanta.” Ya fada cikin shagwaba, kamar wani karamin yaro.

” zan rama, very soon. ”  ta fada

” very sorry, muna nan zuwa, da zaran jabir ya dawo zamu zo.” Ya fada cikin miryar lallashi.

” ina nan ina jira.” Ta fada

Mommy Hauwa taji dadin ganin yadda hubby ta kwantar da hankalinta, tayi kyau ta murje. Duk inda hubby ta gilma idon mommy na kanta, cike da jin dadi.

Hubby taji dadin yadda mommy Hauwa ta sake da ita, suka sha hirarsu, cikin hikima ta dinga tambayar hubby game da zamanta da hayder. Hubby nuna mata tayi komai normal ba wani problem. Sai after 2 sannan tai sallama da mommy ta nufi main house. Duk da bataji  dadin rashin ganin daddy dinta ba, saboda tafiya da yayi.

Part din Mmn samira ta fara zuwa, kamar yadda ta saba. Sun gaisa, cikin mutunci, hubby bata nuna mata komai ba. Sai dai ta lura jikin mmn samira yayi sanyi, kusan kamar ma kunyarta take ji. Bata dade ba, ta nufi part din Mmn Yusuf.

Itama kadaran- kadahan, ba yabo ba fallasa. Kamar all times, har yau ta rasa abinda ta tsarewa matar. Shin kaso dan mutun Ashe yakan zama laifi? Meye laifinta don ta nuna tsantsar soyayyar danta? Da wannan tunanin ta nufi part din Hajiya.

Zo kaga murna, kamar waanda suka shekara basuga juna ba.  Hajiya ma taji dadin ganin hubby. Sai washe baki take, cike da farin ciki. Da kanta tama hubby jagora zuwa part din Alhaji Jamal. Shima yayi farin ciki da ganin hubby.

Sai 5pm Hajiya ta ce, ta tashi ta tafi yamma tayi, badon taso ba, haka ta ja motarta zuwa gida. Cike da kewar yanuwanta.

               ******************

” Salamu alaikum, malan idi yau ba redio ne.? Wani dattijo dake cikin keken guragu ya fada, bayan ya iso wurin da malan idi ya kafa kujerarsa a wajen get din gidan.

” yau kunne nake son ji, bana son hawan jini ya kamani tun yanzu. Don na lura jin abinda ke faruwa a kasar nan ba abunda zai kara ma mutun sai hawan jini.” Malan idi ya fada cikin dan bacin rai.

” shi yasa in ba a wurinka ba, ba ruwana da redio.” Gurgun mutumin ya fada

Kallonsa sosai malan idi yayi. ” me ya kawoka kuma yanzu? Nafa kusa fara maka rashin mutunci, baka tashi zuwa wurina sai kaji kamshin girkin hajiya na tashi, ka dai daici an kusa gamawa, ka wani lallabo, kai baka koshi ba, ni ban koshiba.”

Marairaice fuska gurgun mutumin yayi. ” bama haka da kai. Kasan ance duk Wanda yaci shi kadai, zai mutu shi kadai. Ci bibbiyu yafi albarka.”

“Ai sai kayi, gaba don yau Hajiya bata nan.” Malan idi ya fada yana harararsa

Dariya gurgun mutumin yayi ” ina fa jiyo kamshi, tun daga dakina. Nakuma san daga gidan nan yake fitowa. Don ni yanzu saboda lakantar kamshin girkin Hajiya, nakan iya ban banta kamshin Jan zakara, da farin zakara, yau kam kamshin kifi na jiyo.”

Dariya sosai malan idi yakeyi ” lallai abin naka, babbane. To da gaske bata nan. Wannan gurkin oga ne, don shi kadai ne a ciki.”

” haba ai nasan daga gidan nan kamshin ke fitowa, don duk Unguwar nan ba inda zaka jiyo kamshin girki, mai sa miyau tsinkewa sai gidan nan. Allah ka mana arziki, mutun ya dace da matar data iya girki, ai ka more zaman duniya. irin matan nan ko ruwa suka dafa maka dadinsa da ban ne. Ashe shima alhajin gwanine a girki. Yau zamuci ma ban bance Wanda yafi wani.”

“Kaga tashi kayi gaba abinka, ban san sa ido. In kuma ka yadda oga yajika kana yaba girkin matarsa ba ruwana”

” gaskiya na fada ai!! Inda ni  na samu ina kwasar girki haka ai  bazan koma  kauye ba.  ko bazasu biyani ko sisi ba, in dai zan kwashi girki bani da matsala.”

Dariya malan idi yayi, don yasan mutumin nasa, kan girki.

” Allah ya shiryeka. Yau dai bamu da kwano a gidan nan. Don haka kai zaka kawo mana naka abincin muyi maneji.”

” sai fa manejin kam.” Gurgun mutumin ya fada yana tabe baki

 

Hango motar hubby yayi, malan idi ya tashi da sauri ya wangale mata get, gurgun mutumin kam sai wangale baki yake yana daga mata hannu. Sallama ta musu, bayan ta dan sauke glass, ta wuce ciki.

             ********************

Tun 4 hayder ya dawo, kitchen ya nufa, bayan ya rage kayan jikinsa. Daga shi sai  short nicka da singlet.

Irish ya soya, da onion source, dayaji attaarugu da kayan kamshi. Sai catfish daya gasa.

Hubby na shigowa, sama tayi. Don ta tabbatar yana gida ganin bike dinsa a compound, sannan gidan a bude, ga kamshin girki dake tashi.

Key tasawa ta kulle kofarta. Wanka tayi tare da dauro alwala, don magrib ya gabato. Ta dau takardun islamiyyarta ta fara mura jaa.

Yana jin shigowar motarta. Dai dai lokacin da ya fito ta kofar kitchen din, ita kuma tana shiga ta falo. Malan idi ya kira ya mika masa plate cike da chips, roasted fish and Onion source. Washe baki malan idi yayi, yana godiya. Don yau ya fitar da rai da abincin gidan, ganin uwar  dakin nasa bata nan.

A wani square plate ya hada nasa kwanin shaawa. Ya sa rapper din Leda  ya rufe, ya daura a kan deepfreeze. Daki ya koma ya watsa ruwa da sauri sauri, ya daura alwala.  ash color din jallabiyya yasa ya nufi bike dinsa, cikin sauri yabar gidan don karatowar lokacin sallah.

Sai da ta idar da sallah tare da azhkhar, ta fito don daukan cake. Don bata jin yau zatayi wani girki. Kamshi ne ya doki hancinta, duk da na’urar fitar da kamshi amma kitchen din a kwai kamshin girki. Idonta ne ya sauka a kan plate din hayder. Murmushi tayi tare da ajiyar xuciya. ” tsuntsu daga sama gasashshe.” Ta fada tare da daukan plate din tayi dakinta. Key tasa ma kofarta, don ta gama fita kuma, sai in Allah ya kaimu gobe.

Abincinta taci hankalinta kwance. Gashi yayi mugun dadi, rabon dataci gashin kifi irin haka, tun zamanin school, Da take cinye masa abinci.

              ******************

Koda hayder ya dawo, yaga babu plate babu dalilinsa. Murmushi kawai yayi, ya bude oven ya dauki wani fish din. Irish ya fito dashi a freezer yayi fraying. Tsaf ya hada plate dinsa ya nufi falo.

Yana kallon  huda tv, yana cin abincinsa cike da natsuwa. Nasrin ce ta kirashi, wani kayataccen murmushi yayi, tare da daga wayar.

Sun fi 30min suna waya, kafin sukayi sallama.

               *****************

Kamar a mafarki, hubby ta fara jin kukan mage ta window dinta. A tsora ce ta tashi zaune, tana raba ido a duhu, jikinta sai bari yake, in akwai abinda take balain tsoro to mage na ciki.

Inuwar abu taga ya gilma ta windonta. Da yake ciki akwai duhu, waje akwai hasken fitila. Ta jikin labulenta tana iya ganin inuwar abu na kaiwa da komowa. Still kukan mage ne, ba imagining take ba. Ai da gudu ta duro daga gadon, har tana buge kafa.

Daga jikinta, har zuciyarta bugawa suka fara yi. Musamman jin magen ta tsananta kuka, na yanzu ma yafi mata kama dana jariri.

Da gudu ta fito a dakin, daya dakinta da tunda tazo, ko sau daya bata taba kwana a ciki ba ta shiga, tare da danna key.

Ajiyar zuciya ta fara saukewa tana dafe da kirjinta, dake bugawa kamar zai fito.

Adduoin ta fara jerowa, daga ta kai wannan ta cafko wannan,.  Kwanciya tayi, still a tsorace take, tana son tashi ta kunna ac amma tsoro ya hanata kwakwaran motsi.

Windows din da yake a Jere suke dana bedroom dinta. Magen ta dawo ta nan, kamar tasan hubby ta gudu a can. Kuka ta fara tare da yakushin window din. Kamar tana son budewa. Ai a 360 hubby ta fito a dakin. She have no idea kawai tsintar kanta tayi a dakin hayder.

Da sauri ya dago kai yana kallonta, da gudu ta karaso kan kujerar da yake zaune, ga system a gabansa,. Zama tayi a kusa dashi, tare da sakalo hannunta a nashi. Jikinta sai bari yake.

” ikon Allah, lafiya?” ya fada  Kofa take nuna masa, still tana makale da hannunsa.

Ganin ta kasa magana, yayi yunkurin tashi, yaje ya ga meye. Da sauri ta janyoshi tare da kara kan kameshi.

Bakinta na rawa ” mag, mage ce.”

” mage?” Ya fada yana kallonta.

Kai ta kada masa. Alamar eh!

” OK. Sakeni in je in ganta. But how come mage a gidan nan?” Ya fada yana kokarin raba hubby da jikinsa.

” please don live me along. I’m scared” ta fada baki na rawa

” what I don’t understand shine, a cikin dakinki kika ga magen, ko ya akayi?” Ya fada yana tsareta da mayun idonsa.

” a window na, tana son ta shigo.”

Tsaki yayi, tare da harararta. ” na dauka ma dakin naki ta shigo ai! Kike rawar jiki haka.”

Sun kai 10min ba Wanda ya kara tankawa dayansa. Zuwa yanzu hubby ta fara samun natsuwa, koba komai tasan she is safe known.

Kallonta yayi, ya kalli hannayenta dake sakale da hannunsa daya. ” sakar min hannu malama.” Ya fada in his husky voice.

Da sauri ta saki hannun tana dan tura baki.  Haushinsa, da haushin kanta, ya kamata lokaci daya. Matsawa tayi, ta takure wuri daya, tare da daura kanta a kan hannun kujerar. Da yake kujerar mutun uku ma zasu iya zama a kai.

Kallonta yayi, yana tabe baki. Sanye take da night dress riga ce dukanta bata kai gwuiwarta ba. Mai dan karamin hannu. Pusher pink da drawing din apple a gaban rigar. Kanta ko dankwali babu, Ta kamashi da ribbon.  Kansa ya dauke, ya ci gaba da aikinsa.

Hannunsa yayi tapping a dai dai, kan hubby da ke bacci, hankali kwance. Ido ta bude a hankali ta sauke su a kanshi. Gaba dayansu sai da gabansu ya fadi.  ” go to your room, zan kwanta.” Ya fada yana mai goge gashin kansa, alamar daga wanka ya fito. Sai lokacin ta lura daure yake da White trowel, sai karamin da yake goge kai dashi. Da sauri ta kauda kanta.

” don Allah ka barni in kwana a nan, tsoro nake ji.” Ta fada cikin siririyar muryarta.

” no!!!! U can sleep here.?” Ya fada yana tsareta da idonsa.

” I sleep right hare, I won’t disturb u.” Ta fada, cikin yanayin ban tausayi.

” what u say yestaday?” Ya fada still idonsa a kanta.

Gabanta ne ya fadi, tunowa da karansu na yestaday night. Kanta ta sunkuyar tana wasa da yatsunta.

Sai da yayi shirin baccinsa tsaf, sannan yakai kallonsa kan hubby data dungule wuri daya.

” Habiba. ”  ya kirata in high tone. Dagowa tayi ta kalleshi, tare da kauda idonta.

” bafa zaki kwanamin a daki ba. Ki tafi toilet dinki ki kwanta. Amma ba nan ba.”

Kwal kwal tayi da ido,  cikin rage murya da lallashi. ” Allah tsoro nake ji. Kayi hakuri ka barni in kwana a nan please. “

Daure fuska yayi, kamar bai taba dariya ba, kallo daya hubby ta masa jikinta ya kara daukar mazari. Tafi kowa sanin halinsa, in yaso rashin mutunci. Tunowa da school tayi, Ita kuwa a yanda take jin tsoron fita, ko yankata zai yi, ba inda zata.

” I say get out!!! Tun kan in dagaki in watsaki waje.” Ya fada ransa a bace

Takowa tayi a hankali zuwa inda yake hannu ta hada ” don Allah hayder kayi hakuri, ka barni a nan, kaifa dan uwana ne, bazaka so abinda zai cutar dani ba.”

Shiru yayi yana kallon yadda jikinta ke rawa, hatta muryarta rawa take. Murmushi ne yakusa kwace masa. The mighty hubby ke bashi hakurin ya barta ta kwana a dakinsa. Wonder shall never end. Rai ya kara hadewa ” on one condition. ” kai ta daga masa baki na rawa ” meye condition din?”

Ajiyar zuciya ya sauke a hankali. ” u do what I ask u to do, without a guying. In ba haka ba I will trow u out. “

Kauda kanta tayi, saboda kallon da yake mata, she can handle it. Hawayene suka fara bin kumatunta. She never been so helpless like this. ” please hayder don’t do this to me, I’m your brother wife, please. ” ta fada tana durkushewa a wurin, tare da sakin kuka mai tsuma rai.

Idonsa ya runtse, yanajin tausayinta, tare da jin kukan har tsakiyar kansa. Bai taba tausayinta kamar lokacin rasuwar Yusuf da kuma yanzu da take gabansa,  so Helpless.  Dan uwansa ne ya fado masa a rai, gaba daya yaji hankalinsa ya tashi. Jingina yayi da bangon dake kusa dashi, still idonsa a rufe, ga jijiyoyin kansa sun fito sosai.

Sun kwashe 12min a haka, kafin ya bude jajayen idonsa. Still tananan a durkushe a wurin.

Sai ajiyar zuciya ta ke saukewa da Jan hanci.

Dagata yayi cak, ya nufi Kofa da ita. Hubby kam ganin zaiyi waje da ita yasa ta fara kokarin saukowa, amma ta kasa. A wajen kofarsa ya sauke ta. Tare da zuba mata jajayen idonsa. ” go.” Ya fada a takaice.

” juyawa tayi, da nufin tafiya dakinta, cikin Jan kafa.

Daga idon da zatayi, sukayi ido hudu da magen tsugun ne a kofar dakinta ta zubo mata manyan  Golding eyes dinta. Ai a 360 ta kwasa ta koma dakin hayder tana ihu, magen ta rufa mata baya………

Da gudu ta banko kofar, har tana bangajeshi. Baki bude yake kallonta, gaba daya ta fada jikinsa, ta gankameshi, jikinta na matsanancin kyarma. Kyakyawar runguma ya mata, yana buga bayanta a hankali. Kanta ta gara cusawa a kirjinsa. Tana Jan numfashi da kyar.  kaman zata shide haka numfashinta ke fisga da kyar.+
Sun dade rungume da juna. Jin yadda take sauke numfashi, tare da ajiyar zuciya, jikinta ya rage rawa sosai. Yasa ya dago fuskarta idonta kam a rufe, gani take in ta bude magen zata kara gani. Iskar bakinsa yadan hura mata a fuska ” its OK. Open your eyes. ” ya fada in husky voice yana ci gaba da hura mata iskar bakinsa.
Kara runtse idonta tayi, tanajin iskar bakinsa mai kamshin strawberry na sauka a kan fuskarta. Gaba daya tsigar jikinta ya fara tashi. A hankali ya zareta daga jikinsa, resting chair din ta kara komawa, ta dungule wuri daya.
Jin alamar taba kofar yasata saurin dago kanta. Hayder ne yasa key, fridge ya nufa, ya zuba ruwa mai sanyi a glass cup ya tako inda hubby ke dungule ya mika mata. Jin mutun a kanta yasata dagowa, ganin yana mika mata cup din. Ta mike ta zauna da kyau tare da amsar cup din, don tanada bukatar ruwan ko don kuka, da tayi. Tsaf ta shanye sannan ta mika masa cup din.
Kwanciya ta kara yi, tare da runtse idonta. Daga nan tana jiyo yanda magen ke yakushin Kofa, kush- khush- kush, tare da kukanta. Ajiyar zuciya ta sauke. Hankalinta ya fara dawowa jikinta, don tasan koma menene ba ita kadai ba ce a dakin. Yana tsaye daga jikin window idonsa na hango malan idi dake baje a kofar dakinsa, yayi shinfida yana kwasar bacci. Tsaki yayi a zuciyarsa yana furta ” ji wai nan a dole me gadi? Mai gadi da aka Sani da sintiri cikin dare don ya tabbatar da tsaro, amma shi ke kwasar bacci hankalinsa kwance.”
Kallonsa yakai kan hubby, yasan harda  sanyin ac yasata dungulewa haka. Takowa yayi, zuwa inda take kwance ” Habiba!! ” ya kira in sweet low voice. Kanta ta dago ta kalleshi, hannunsa ya mika mata. Kallon hannun tayi, mai matukar haske da laushi, dogayen yatsunsa kwanin shaawa. Kallonsa tayi, alama ya mata da ido. Kanta ta dauke tare da mikewa ta zauna.
Ganin bata da alamar kama hannun nasa, da kansa ya kamo nata hannun, tsigar jikintane ya yi wani yar!!! Tare da shock daya ratsa jikinta lokaci daya.
Lumshe idonsa yayi, saboda shock din daya ratsa jikinsa. Bata da zabin da yafi ta mike, kamar rakumi da akala haka ya ke rike janye da ita. A tunaninta wajen zai kara turata, amma sai taga sabanin haka.
Toilet ya nufa da ita, suna shiga wani kamshi mai sanyaya rai ya daki hancin hubby. ya kalleta yana shigar da idonsa in sexy way. ” kiyi alwala, I’m waiting for u outside. “
Kallonsa take ido waje, don yanzu ta fara tsinkewa da lamarin Hayder, gaba daya gani take kamar ba shi ba. Ba karamin aikinsa bane ya kulleta a toilet din. Yana juyawa, da sauri ta riko hannunsa. ” wait please. ” baki ya Dan tabe, ya jingina da kofar.
Cikin Sauri- sauri tayi alwalar. Kallonsa tayi, matsawa yayi daga jikin kofar, da sauri ta wuce zuwa cikin dakin. Hakan ya bashi damar yin nashi alwalar.
Woodruff dinsa ya bude, wani alkabbarsa  mai hade da hula, ya dauko. Carpet din sallah mai matukar kyau da laushi, ya shimfida. Sannan ya mika mata rigar, Kallonsa tayi, cike da fargaba da tsoro. ” nayi sallah.” Ta fada muryarta na rawa.  Murmushi yayi, yana ajiye mata rigar a saman cinyarta. ” I known. This one is special.” Ya fada in sexy voice dinsa, yana murmushin gefen baki.
Gabanta ne ya fadi, da sauri ta dago tana kallonsa. ” don’t forget our agreement? ” ta fada, muryarta na cracking
Murmushi yayi, har tana jin sautin numfashinsa. ” kin San na ce miki no a guying, ko I will trow u out, just do as I say.” Ya fada yana tsareta da idonsa.
Idonta ne suka ciko da kwalla, mikewa tayi a hankali ta saka rigar, kamar mai sharan kasa, yadda ta mata tsawo, da fadi baki daya. Su Kansu hannayen sun mata yawa sosai. Kallonta yayi, tare da Jan hannunta, har kan daddumar, She have no choice.
2 rakaat sukayi, ya musu addua sosai, tare da dafa kanta ya karanto adduar da manzo  S.A.W ya umurci ko wanne ango, da gabatarwa kafin yaje ga iyalinsa.
Allhumma inni as’aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha ala’ih, wa’auzu bika min sharraha wa sharra ma jabaltaha ala’ih.
Kwanciya tayi kan carpet din, zuciyarta da jikinta rawa kawai suke, don ta tabbatar yau Allah ne kawai zai kwaceta a hannun hayder. Tun jiya take tsoron randa zai rutsata don ta lura abun nasa ba sauki.
Dagata yayi, tare da rungumota jikinsa, yana Ajiyar zuciya. Dagata yayi cak zuwa saman bed dinsa. Kokarin cire alkabbarsa yakeyi, ta cukui kuyeta, tare da nade kanta a ciki.
” Habiba don’t make it had for us.” Ya fada yana rage kayan jikinsa. 
Hawayene wani na bin wani, maganar ummu sulaim ne suketa kara kaina a ranta ” kamar yadda Allah ya kaddara Yaya Yusuf ya sanki matsayin matarsa, haka ya kaddara hayder shima ya sanki a matsayin matarsa, so take heart and deal with it. Duk yadda kika kai ga gujewa hakan it won’t work.”
Ko kafin ta tuno amsar data bata a lokacin,. Sai jin  hayder tayi, yana kokarin zare rigar a jikinta. Karfinta tasa tana kokarin hanashi, amma ina hakan bai samu ba. Karfi ba daya ba. Yana zare alkabbar tana dira kasa daga gadon.
Kofa ta nufa, burki taja, ta tsaya. Zuciyarta na bugawa. Tare da wasi wasin, ta fita su kara da mage?ko ta tsaya hayder yayi yadda zai yi da ita. Don tasan bazai taba barinta ba. Kanta ta kifa a jikin kofar ta fashe da kuka mai cin rai. ” how can she help her self know? “
Bataji takowarsa ba, sai jinsa tayi ya rungumota ta baya, yana sauke Ajiyar zuciya. Ta bashi tausayi sosai, amma gaskiya baya jin zai iya hakura da ita, don wani filling yake ji, Wanda bai taba experiencing ba, a rayuwarsa. Ji yake in har bai rabeta ba, tabbas zai shiga matsala. Ta wani fannin kuma, zai sauke hakkinta dake kansa, duk da bata da bukatar hakan.
Wuyanta ya fara kissing, a hankali, shivering ta fara, tare da kokarin zame kanta. Juyo da ita yayi ya hadata da kofar. Yana ci gaba da kissing wuyanta, zuwa ear loop dinta
Gaba dayansu jikinsu yadau kerma lokaci daya. Kanta ya dago, yana kallon kyakyawar fuskarta, data jike da hawaye. Idonta a rufe, don batajin zata iya kallonsa. Bakinsa yakai kan nata, like last time she denied him access to har mouth. Labbanta ya ke tsotsa a hankali, hannun daya na tallabe da fuskarta, dayan na zaga duk kan sassan jikinta. Jikinsa ya mata katanga a jikin door din.
Tun tana kokarin avoiding, har gaba daya jikinta, ya fara amsar sakon ninsa. Dagata yayi bridal style zuwa bed din, tare da sweching  light. Wasanni masu zafi ya fara aika mata, Wanda ta kasa control din kanta, ta fara maida masa.
Gaba daya daren hayder ya hana hubby sakat, Tun tana dauriya, har ta gaza, ta fara masa kuka.
Yana kwance hubby na rungume a jikinsa, Yana jin saukar hawayenta. Shi kanshi hawayen yake zubarwa for 2 think. Fist tunowa da Dan uwansa, second godiya ga Allah bisa niimar bashi hubby a matsayin mata. Yau ya kara tabbatar da maganar Yaya Yusuf, Yau ya kara tabbatar da dalilin da yasa Yusuf ke matukar kaunarta, Yanzu ya gane abunda sauran masoyanta ke hangowa a tare da ita. Bai taba tarayya da ko wacce irin mace ba, a rayuwarsa. Amma yasan she is special, unique and different from others.
Hubby tunanin Yusuf ne, dankare a ranta, gani take tamkar taci amanarsa ne, tare da takaicin kanta, yadda ta kasa control din kanta, da har hayder ya samu dama a kanta, So ita yanzu da wane ido zata kalli hayder? Hayder kanin bayanta? He is know controlling her. She is know his real wife. Ya zatayi da wannan katuwar kaddarar? 
Alarm dinsa ne ya kada 4am, Yana son tashi, amma baya son disturbing nata,. Kanta ya ke shafawa a hankali. Tare da tuno maganar Yaya Yusuf mai kama da wasiyyah, last ziyara daya kai masa Cyprus.
              ********************
Zaune yake a harabar apartment dinsu. Wurine mai yalwar hasken fitilu, da furanni masu kamshi, Wanda su suka zuba kujeru don hutawa da daddare, in sun dawo. Idonsa a sama yana kallon taurari, tare da girmama, girman halittar Allah, da tasbihi a kasan zuciyarsa.
Baiji takowarsa ba, sai dafashi da yaji anyi, da sauri ya juya, don a tunaninsa junaid ne, ko ashir, amma ga mamakinsa yaga Yusuf. Murmushi sukawa juna, Yusuf ya zagayo, ya zauna a kujerar dake fuskantar hayder.
” na dauka ka dade da bacci, saboda gajiya.” Hayder ya fada yana murmushi
Shima murmushi yayi ” baccin yaki zuwa. Me kakeyi kai daya a nan” Yusuf ya tambaya.
” muraja’a and looking at star’s. ” ya fada a takaice.
Murmushi Yusuf yayi, yakai lallonsa sama, yadda stars din suka fito sosai, ga wata da alamar ya kusa 10 to 11 days. ” tabbas kallonsu kansa mutun ya kara tsoron Allah da sanin girmansa.”
Hayder ne ya amsa da ” sosai brother” ya fada a takaice
” you no what, duniya bata da tabbas,  dole mutun sai yanayi yana garanbawul din imaninsa.” Yusuf ya fada still idonsa na kallon sama
” ga mai imani ya dauketa, bata da tabbas, ga Wanda ta aura gani yake matabbatace da zai aikata abinda yaso,”
Murmushi Yusuf ” shin duka duka, farin cikin guda nawa ne? Me ye kesa bawa farin ciki a duniya, da har zai salwantar da lahirarsa a kanta?…….

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *