DA KAMAR WUYA CHAPTER 7 BY ZULAIHAT IDRIS MISAU
Www.bankinhausanovels.com.ng
Shiru kake ji, sai kira’ar sudais dake tashi a redion motar. Mariya na baya, tana faman kalle kalle. Sai hubby dake WhatsApp da Aisha, gaba daya hankalinta na kan wayarta.+
Jin tsayawar motar, yasata saurin dagowa, kallon kofar gidan da sukai parking tayi, sannan ta maida kallonta ga hayder cike da Neman Karin bayani. Kauda kansa yayi, ba tare da yace mata komai ba. Garar rufe kofar motar da taji, yasa tai saurin kai kallonta ga Mariya da already ta fita a motar. Zagowa tayi tanama su hubby sai gobe in tazo.
Cikin sanyin jiki, hubby ta daga mata hannu, ba tare da ta samu ko kalma daya da zata furta ba. Allah – Allah take suje gida ta aiki mariyan ta siyo mata P-Test, ta samu tayi pregnancy test, ko ta samu natsuwar zuciya. Amma lokaci kadan hayder ya rushe mata plan dinta. Ajiyar zuciya tayi, jin ya harba motar a titi. ” a kwai gobe” ta fada a kasan ranta, duk da ba haka taso ba.
Suna gaf da shiga unguwarsu, wayarsa tayi kara. Dagawa yayi, cikin husky voice dinsa yayi sallama Shiru yayi yana sauraron mai maganar. Kafin taji yana cewa. ” koma menene Ku bari sai da yamma.” Shiru yayi can kuma ya danyi tsaki ” i say in the evening. ” — ” OK.”
Yana Karya kwanar layinsu, malan idi da gurgu na zaune a waje. Suna hira. Hango motar na zuwa gurgun ya washe baki. Malan idi, kakarmu ta yanke zaka, uwar dakinmu ta dawo.” Da sauri malan idi ya mike, shima yana washe baki. ” ai kuwa, sune, dama tun da naga yau ana share share, nasan su oga na hanya.” Da sauri ya wangale get, tun kafin ma su iso.
A bakin get din Hayder ya tsaya suka gaisa da malan idi, tare da tambayarsu ya hanya? Hayder ya tambayeshi lafiyarshi da kuma gidan. ” komai lafiya, yallabai. Sai rashinku na kwana da yawa.” Murmushi hayder yayi tare da amsa gaisuwar gurgun mutumin dake ta washe baki.
Shiga yayi, yayi parking. Malan idi ya shiga musu da jakun kunansu.
Dakinta direct ta wuce, komai tsaf a gyare sai kamshi ke tashi.
Kayanta ta shirya ko wanne ta maida shi, inda ya dace. Sannan ta nufo kitchen don daura abincin.
Cook Book, ta dauko tana dubawa. Kamshin turarensa ya tabbatar mata da dosowarsa kitchen din. A bakin Kofa ya jingina tare da dafe kofar da daya hannunsa. Juyowa tayi, tana kallonsa, ” me kake son a dafa?.” Shafa sajensa yayi da daya hannun still yana kallonta, Ba tare daya ce komai ba. Haushi ne ya kama hubby, yana daya daga cikin abinda ke hadata dashi, sai kayi magana yasan dashi ake, amma sai yayi maka banza.
Tukunya ta dauka ta zuba ruwa. Ta daura a kan cooker gas, tana kokarin kunna a shana, bataji takowarsa ba, sai dai taji an rike mata hannu. Hannun ta kalla, kafin takai kallonta kanshi. A shanar ya amsa, ya ajiye a gefe.
” an hutashsheki.” Ya fada yana shinshina wuyanta.
” please hayder, kasan dai baza a zauna baa ci abinci ba, ko don su malan idi. ” ta fada muryarta na rawa
Juyo da ita yayi, ya ci gaba da romancing dinta. Ta bude baki zata yi magana. Ya daura yatsanshi a bakinshi alamar tayi shiru. ” ta rasa wane irin fitinan nen yaro ne, wannan. Ya dawo kenan, yanzu zai hanata sakat da fitinarsa.
” kina son ki batawa Hajiya yaronta.” Ya fada in his husky voice. Yana kara rungumota jikinsa.
” dama can, tasan halin yaronta, shi yasa ta masa aure kafin ya fara tsince yaran jamaa.”
” banda sharri!!! Ke kika gayyatoni, ni kuma na amsa, meye lefina?”
” da yaushe na kiraka?” Ta fada tana dago kanta yanda zata ga fuskarsa sosai.
” Hajiya kanta, ta yaba kwalliyar da aka min, shine naga ya kamata na bada tukuici. Kin ga ke kika bani goron gayyata.” Ya fada yana smacking
” banyi don kai ba, da har kanka zai na fasuwa. Nayi don radin kaina ne? Ta fada tana harararsa.
” really. ” ya fada yana daga mata gira.
” really!!! Ka jira Nasrin ta shigo, na tabbata zatayi don kai, amma banda hubby.”
” kina son Nasrin din nan, naga a lama.” Ya fada
” yes!! I like her, she is a nace girl.” Murmushi yayi cike da jin dadi. ” thanks. ” ya fada
” amma kaman baka damu da ita ba? Do you really love her? ” ta tambayeshi
” why do u ask?.”
” gani nayi tunda kuka rabu, har yau baka taba daukar kafarka kaje ka ganta ba. Bayan an ce garin masoyi baya nisa, in har son da kake mata na gaskiya ne, yaka mata at least by now kaje ka kai mata ziyara.”
Smacking yayi tare da tabe baki. ” kika Sani ko irin namu tsarin kenan?” Ya fada yana shafa gashin kanta.
” ba wani nan, _a kwai katon question mark a kan son da kake mata.? Ta fada
” zaki rakani.?” Ya fada yana daga mata gira
” no.” Ta fada tana kada kai.
” why.” Ya fada
” ask one of your friend. “
” ke nake son ki rakani.” Ya fada cikin very low voice
” no, in capital NO “
” u are jealous of her.”
Harararsa tayi. ” Allah ya kiyaye, da ina kishi bazan ce ya kamata kaje ba.”
” OK.” Ya fada yana tabe baki.
” kinsan yanzu zance ba sai kaje wurin budurwa ba, true phone and you’re system, u communicate and see each other. I’m not like your stalking boyfriend’s, every ware u go, the followe u.”
” that how its suppose to be.” Ta fada
” in my case is different. In ina son ganinta I just tell her, in no time zaki ganta a Nigeria. To tell u the true, ban taba daukar kafata naje wurin mace ba.”
Tabe baki tayi. ” there love u, more than you love them. Amma hakan bashi zai hana ka kula da mai kula da kaiba. Koda yake laifinsu Ne, da zasu tsaya zubar da darajarsu da Allah ya musu, saboda so. Nama rasa me suka gani da basu gani a sauran maza ba, suke wani makale maka? Farin ko dogon hancin? “
Murmushi yayi har tana jin sautinsa ” ke da kike ikirarin bakya son Aliyu hayder bakya iya resisting dina, how do you expect them to resists me?”
Nocking suka fara ji, sai lokacin hubby ta tuna a inda suke. Da sauri ta mike, gyara kwanciyarsa yayi, ya daura kansa a kan hannayensa biyu, fuskarsa na kallon sama. Ta gafen ido, yake kallonta tana kokarin sa riga, cikin sauri. Still nocking din aka ci gaba dayi.
” wait. ” ya fada yana mikewa, ganin tana kokarin fita. Kauda kanta tayi, smacking yayi, tare da zura jallabiyyarsa da short nicker. Sai da yazo zai fita, ya rada mata a kunne ” go and cherk your self in the mirror. “
Haushi ne, ya kamata, kamar ta mangare keyarsa. Dama a cike take da maganarsa ta dazu.
Bai dade ba, sai gashi da manyan ledoji, masu tamarin Eat More restaurant. Still tana tsaye a inda ya barta, sai cika take. Tabe baki yayi. Ya wuce cikin kitchen din. Ya ajiye ledojin. Sauran kayansu dake watse a tiles din kitchen din ya tattara. Hannunta ya kamo, ya damka mata.
Da gudu- gudu, ta haura sama.
Dariya yayi, yana shafa tattausan sumar kansa. Don yasan ya tsokano rigima yau.
Toilet ta wuce, madubi ta kalla, yadda gashinta ya wani baje, tare da wargajewa. wanka ta fara, tana tuno maganar hayder, hawaye ne suka fara bin kumatunta. Ita kanta ta rasa wannan fitinar. Kamar wani magnet haka take rasa duk kan kuzarinta, matukar zai bukaceta, bata iya resisting, ya san weak point dinta, wannan wani sabon babi ne na rayuwarta, da ‘da bata San da shiba. Tana kokarin fitowa yana shigowa. Ta gefensa tabi zata wuce. Rukota yayi da sauri. Masifa ta fara masa, don abun ya fara isarta, duk makullan dakinta, da toilet duk ya kwashe, bata da wani privacy a gidan.
Dagata yayi cak, zuwa cikin barf da hannu daya ya riketa, ya kunna shower. Kokarin kwacewa take, don tayi alkawarin ta daina biye masa, tunda abun harda gori. Amma baa je ko ina ba, ya sakata a saiti. Midik kakeji
Harararsa tayi, ” ban yafe ba wallahi, mugun yaro.” Ta fada tana nufar woodruff.
Dariya yayi, yana ci gaba da goge kanshi da karamin trowel. Lotion dinta ya dauka ya fara shafawa. Duk harare -hararen da hubby ke binsa dasu yana kallonta. Shi dariya ma take bashi.
Sai da ya gama, tare da fesa turarukanta. Still tana gaban woodruff, ta rasa kayan da zata sa, don ta kubutar da kanta, tun kafin yaga bayanta. Duk kayan data dauko sai taga bai yi ba. Tsaki tayi, tana jin haushin Aisha da ta sata yin irin wannan banzan dunkunan. Tasan har dasu ke ja mata murxuwa a wurin hayder.
Wata tsohuwar rigar material dinta ta hango, mai zuwa da hijabinta. Musamman ta siyesu zuwanta umra, don zuwa masallaci.
“Ban wuri,” ta fada cikin siririyar muryarta, tana harararsa. ” let me help u.” Ya fada yana matsa lotion din a hannunsa. ” na rokeka don Allah ka barni in shirya a tsanake.” Ta fada tana kwace lotion din a hannunsa.
Tabe baki yayi, tare da dage kafada, ya fita a dakin. Da harara ta rakashi.
*****************
3 cutter da armless shirt na kamfanin NIKE farare, sun masa kyau, kitchen ya wuce ya dauki Leda biyu, ya nufi waje. Malan idi ya samu yana alwala. Ya mika masa tare da juyawa ciki.
Godiya malan idi yayi, yana Allah Allah ya idar da alwala yaga abinda ke cikin ledar din. Saboda kamshi daya cika hancinsa.
Sai da ta idar da sallah, sannan ta sakko. A falonta na kasa ta sameshi, ya baje a carpet, yana kwasar girki.
Ledar din ta fara bubbudewa, shawarma taci karo da shi, a wani Small paper bag. Zama tayi tare da yin bisimillah ta fara ci. Idonta ta lumshe, saboda dadin daya ratsa mata kwanya.
Tunda ta sauko, idonsa na kanta, ganinta da hijab, tabe baki yayi, ganin yadda take cin shawarma tana faman lumshe ido. Wunin ranar gaba daya haka hayder ya takura hubby, da fitina iri iri, sai yamma ta samu kanta, da su junaid suka kawo musu ziyara.
**********************
Ya dawo daga main house kenan, sun dan tsaya da malan idi. Bayan sun gama magana wayarsa ya zaro daga aljihun Jens dinsa. Kan bike dinsa ya zauna yana waya.
Ledar din hannunta, take shillawa, tare da rere wakar film din Mariya. Ganin hayder a zaune saman bike dinsa. Jikinta ya dau rawa, mu samman da ta tuna da gar’gadin hubby. Ledar din data shilla take kokarin dawo da ita ta boye cikin hijab. Batai aune ba, sai ji tayi ta harde, dan dogon takalmin dake kafarta, ya turgude, sai gata a kasa, ledar tayi can gefe. Ko motsi beyi ba, yana ci gaba da wayarsa. Kallonta yayi, ya kalli leader din. Ya kauda kansa. Da sauri ya kara kai idonsa kan ledar din. P-Test ya hango daya ya fito daga ledar din. Daga inda yake, yana iya karanta jikin dan dogon searchet din.
Da sauri ta mike, ta dau leader din. Tare da dauke wanda suka zubo din. Gaishe shi tayi, ta wuce da sauri kamar munafuka. Kai kawai ya daga mata.
Gaba daya hankalinsa ya kasu kashi biyu, ganin ya ma daina gane me nasrin ke fada, yasa ya mata sallama.
********************
“Kin tabbatar ba Wanda ya gani ko?” Hubby ta fada tana tsare Mariya da ido.
Kai Mariya ta daga mata. Da sauri hubby ta dauki leader din tayi sama.
Har washe garin ranar hayder na jira yaji hubby tace masa wani Abu, amma shiru. Bayan ya tabbatarwa kansa she is pregnant. Ganin tsinkayen datayi anfani dasu har hudu, amma suna nuna she is pregnant, Duk da boyon data musu bai hanashi bin ciko su a kasan dustbin din toilet dinta ba.
Farin ciki a wurin hayder baa magana, ranar ko bacci bai iya yi ba. Sai mika godiyarsa ga Allah tare da nemama yayansa gafara da rahamar Allah.
Hubby kam ranar tasha kuka, da tunanin mafita, rashin zuwan hayder gareta a ranar ya mata dadi, don ya bata damar nazarin abinda zatayi next.
11 dai- dai, hayder ya fito daga dakinsa. Hubby na zaune a gaban mirror. Kanta ta kifa, tana faman saka da war wara. Kamshinsa ta jiyo, tai saurin dago kanta.
” ki shirya ki sameni a waje, zamu je wani wuri.” Ya fada yana juyawa, ba tare da ya jira mai zata ce ba.
Cikin sanyin jiki, ta dauko hijab dinta, kalan da zai shiga da atamfar dake jikinta. Ta saka, tare da daukar jakarta, Already dama shiryawarta kenan.
Yakai 5min a cikin motarta, sai gata ta fito. Gaba ta bude ta shiga, yaja suka tafi. Ba Wanda ya tankawa dan uwansa.
Kallonsa tayi, sannan takai kallonta kan ginin da suke tsaye a gabansa.
Sultana specialist hospital. Kallonsa ta kara yi, bai ce mata komai ba, bai kuma kalleta ba, balle ta sa ran samun karin bayani. Hasalima fuskarsa ba annurin da zata samu damar tambayarsa dalilin zuwansu hospital. Don haka tasa a ranta halan a cikin yan uwane wani ba lafiya, suka zo dubiya.
Fita tayi ta bishi a baya, yana gaba, tana biye dashi suka shiga cikin hospital din…….
Afwan. Rayuwa ba kai kake tsarawa kanka yadda kaso ba, sai yadda Allah ya so kuma ya tsara. Tafiya ce un expected ta kamani, shi yasa kuka jini shiru. Yau na dawo, ga gajiya, amma dunbin comments dinku yasa bazan iya shareku ba, kodon kauna da kulawarku. Shiyasa na daure na muku typing at leas in nuna muku how happy I’m. Na gode da kauna, da kulawarku. Love u all, thanks.Kujera ya nuna mata a Reception din, ba tare da yace mata komai ba. Bata da zabin daya wuce ta zauna. Zama tayi tana binsa da kallo. Ya koma mata kamar ba hayder data sani ba. Wani kwarjini na ban mamaki taga ya kara mata a idonta.+
Wayarsa ya Ciro, ya kira wata number. Minti kadan sai ga wani balaraben doctor ya fito daga wani corridor, wuyansa rataye da abun auna numfashi. Rungume juna sukayi, tare da hade kumatu, as usually gaisuwarsu.
Sun danyi magana kafin, suka dawo da kallonsu kan hubby, da rabin hankalinta na Kansu, rabi na kan yan matan dake gefenta. Tun shigowarsu gaba daya hankalin yan matan, yayi kan hayder.
” I known this guy.” Dayar ta fada.
” kai guy din nan ya hadu karshe, I like this guy.” Dayar ta fada Still idonta a kan hayder
” natuna!! You known Hafiz? Dayar ta tambaya.
” wane Hafiz kenan.”
” our nebour.”
” na ganeshi, Wanda ya dawo daga Cyprus ko?”
” yauwa shi. Friend dinsa ne, ina yawan ganinsu tare.” Dayar ta fada. Ganin hubby na magana da doctor din da suke tare da hayder yasa sukayi shiru.
Gai sawa hubby sukayi da Doctor sabir. Jagora ya musu har office dinshi.
Katon office ne, mai kyau da tsari. Kujeru biyun dake gaban table dinsa ya nuna musu, cike da faraa.
Sun dan dau lokaci, suna hirarsu da hayder, kafin wata nurse ta shigo, dauke da file a hannunta. Cikin girmamawa ta gaisheda su hubby kafin ta mikawa doctor file din ta fita.
Doctor din ya dago yana kallon hubby cike da faraa a kan fuskarsa. Tambayoyi ya fara jerowa hubby, kallon hayder tayi, taga gaba daya hankalinsa na kan wayarsa. Gabanta ne ya fadi, cikin karfin hali, da rawar murya ta ke amsawa doctor din.
Waya ya dauka ya kira wata nurse din. Minti kadan sai gata. Wasu fararen takardu, da yayi rubutu a kai ya mika mata. Tare da kallon hubby ya ce ” madam kuje tare, akwai wasu test da za su miki yanxu.”
Jiki a sanyaye hubby tabi bayan nurse din.
Zaune take, bayan ta dawo daga wurin da aka dauki jini, da fitsarinta. Tana kallon hayder da yayi balance a kujera suna hira, sama- sama da Doctor din. Duk yadda taso su hada ko ido ne abu ya faskara.
Jikinta yayi sanyi, Bata so hayder yasan tana da ciki ba. Don ta gama yankewa kanta hukuncin zubar dashi, don da kunya a ganta da cikin hayder a jikinta. Bata san ya zata iya shiga jama’a da wannan abun kunyar ba. Ta rasa yadda akayi ya gane, tunda ita ba wani laulayi take yi ba, Aisha ce ta fado mata a rai, ta wani gefen kuma tana ganin Aisha bazata taba fallasa sirrinta ga hayder ba, tun da har ta shaida mata bata son ta gayawa kowa.
Nurse din dazu ce ta shigo da envelope a hannunta. Doctor din ta mikawa, ta fita. Zaro farar takardar yayi ya kalla, yana murmushi. ” congratulation ahehh!!!! She is 2month 2 weeks pregnant. Rungume juna sukayi ya na ce masa ” thanks. “
Hubby doctor ya kalla cike da faraa ” congratulation uhtee!!!” Yake tayi tare da sunkuyar da kanta, cike dajin kunya.
” zaki zo every month, don tabbatar da lafiyarki, dana beby din mu.” Doctor sabir ya fada lokacin da ya rakosu har mota.
Kai kawai hubby ta kada, tare da bude kofar motar ta shiga. Sallama sukayi da hayder sannan ya juya ya koma cikin hospital din, su kuma suka kama hanyar gida. Har suka iso gida, ba wanda ya tankawa dan uwansa.
*******************
10 o’clock dai dai, ya shigo dakin hubby, cikin shigar kayan baccinsa, sai kamshin turare ke tashi.
Yau idonta biyu, fargaba da rashin sanin matakin da hayder zai dauka a kanta, da makomar cikin dake jikinta, wanda ta tabbatar yanzu zubar dashi, tamkar yakin duniya na biyu ne a gareta.
Tana zaune a bakin gadonta, wani book din adduoi take dubawa. Ya shigo. Kallo daya ta masa, ta kauda kanta. Har lokacin fuskarsa ba walwala. Kusa da ita ya zauna tare da jingina da jikin gadon.
Nazarinta ya tsaya yi, ganin har lokacin taki dago idonta ta kalleshi. Shi mamakinta ne ya isheshi. A tunaninsa murna zatayi a duk lokacin da ta samu wannan kyakyawan labarin. Amma ga mamakinsa sai yaga sabanin hakan. Tun ranar da tayi anfani da P- test din nan, ya lura gaba daya bata cikin walwala, da natsuwa.
” me yasa baki gaya min kina da ciki ba?” Ya fada in his low voice, da ita kanta ba don tana kusa dashi sosai ba, bazata jiba.
Shiru ta masa, ba tare data ce komai ba, tana kokarin maida kwallar data cika mata ido.
” don’t Tell me, u are not happy about it?” Ya fada yana tsareta da ido.
Hawaye ne suka fara bin kumatunta. Dafe kanshi yayi tare da anbaton ” ya Allah.'”
sai kawai ta saki kuka mai cin rai, wani irin kunya ya rufeta shike nan yanzu ta tabbata matar hayder harda cikin shi a jikinta sannan kowa ya ganta yasan abinda hayder ya mata kafin ta samu cikin ace k’anin ta wai yau shine mijin ta kuma harda cikin shi a jikinta, ita duk a haukanta bata taba tunanin zata iya daukar ciki ba, da tayiwa kanta dabara, duk da baa wa Allah wayau. Yakan zartar da abinda yaso a lokacin da yaso.
Cikin kukan ta matsa kusa dashi, idonta na zubda kallah tace
“Dan Allah kayi hak’uri kar ka gayawa kowa please Na tuba, kasa ya zubar min da cikin ni banson haihuwa wallahi ni dai a zubar da cikin tun da ba wanda ya sani”
Smacking ne kwance a kan fuskarsa, sajensa yake shafawa, yana kallonta. jawota yayi jikinshi cikin lallashi ya hada bakinshi da nata kissing dinta ya fara, jikinta gaba daya tayi sanyi, so bata yi wani yunkurin hanashi yin hakan ba. Tama san in yayi niyya ba yadda ta iya dashi. Sai da ya gaji don kansa, ya zare harshensa tare da gyara mata zama ya kwanto da ita kadan a jikinsa. Fuskarta ya dago ya tsare ta da ido cikin husky voice dinsa yace. ” Kin san sanda cikin ya shiga ne? kinsan me zaki haifa ne? kinsan rayuwar da zaiyi? Ke kika halicce shi?
Ko kyau tar da Allahu S. W. A ya mana kika raina? ki nitsu Habiba cikina fa kike cewa wai ince a zubar ciki da a da da kudima kin nema amma baki samu ba. Sai yanzu da Allah yaji kanki, ya tausaya miki, ya baki, kike neman yi masa butulci.
May child!!! My own flesh and blood kike son in sa a zubar? kinsan wahalar dana sha kafin na sameshi, kin san irin tashin hankalin da na shiga, daga ranar da aurenki ya fado kaina, har ranar da kika shigo gidan nan a matsayin matata ta sunna? Kin san yaki da zuciyata da nayi don kawai in karbeki a matsayin abokiyar rayuwa? U have no idea. My blood my halal kike cewa a zubar me zaki gayawa mahalliccin mu? Ranar da bayi ke girbar ayyukansu?” Ya fada still idonsa a kanta.
Idonta a rufe, don bazata juri kallon kwayar idonsa ba. kauda kanta tayi tare da cewa. “Bana so wallahi ko zan Haihu ba da kai ba, na yadda in haihu da koma waye da na haihu da kai, nace kanina ne mijina ko nace kaninah ne uban yarana?”.
Sosai zantu kanta suka bata mai rai, tureta yayi daga jikinsa. Idonsa cikin nata ya nunata da yatsa jikin shi har rawa yake yana fidda numfashi da karfi yace.
” kar kiga Ina binki ina lallaba ki, saboda ke macece mai rauni da tawayan tunani, Ku mata akan biku a hankali dan a fahimtar daku amman na lura abin naki rainine, dan haka ya zama dole na gyara miki tunanin ki, zuwa yanzu, yaci ace na fi karfin ki kirani da yaro, tunda nayi abinda manyan mazan basu yi miki ba. Naga alamar baki tsoron Allah, sai tsoro da gudun surutun jama’a, da bazai anfaneki da komai ba. Sadaki aka biya, shaidu suka shaida. Ko kin dauka kowama sakarai ne, da zaiyi tunanin zan ajiyeki a gidana ina kallonki ba tare da wani abu ya faru a tsakaninmu ba? ki bude kunnenki da kyau. wallahi kar bakin ki ya kuma furta Kalmar zubda ciki a gidan nan. in kuwa kikayi gagganci furtawa, ko yunkurin aikata ba dai dai ba, akan cikina wallahi zaki gane kuskurenki, lokacin zaki san waye Aliyu hayder. Zan iya karawa da kowa akan cikina. Don shine farin cikina, cikar burin dan’ uwana.”
Mikewa yayi ya fice a dakin, cikin bacin rai, da jin haushin hubby.
Jikinta yayi mugun sanyi da kalamansa. ” tabbas wannan babban butulci ne, ga niimar Allah a gareta. Sunje kasa yakai 6 duk don neman haihuwa. Bakar magana, wulakanci, cin mutunci, wanne ne bata fuskanta ba akan haihuwa? To meye nata na daukar zafi kan haihuwa da hayder? Surutun jama’a? A duniya ka isa ka hana jama’a surutu a kanka? Komai kayi abin magana ne, wani yaga kayi dai dai, wani yaga kayi kuskure. Baka taba burge jama’a. Tabbas farin ciki ya kamata tayi, yanzu ta tabbatar da kanta a matsayin cikakkiyar mace, mai haihuwa. Sabanin da da wasu ke lakaba mata juya, har ake kin aurenta don hakan. Tunowa tayi da Abdul Karim da Abdul fatta, wanda duk dalilinta na zamowa bata haihu da yayansu ba, yasa iyayensu mata kin yadda su aureta. Wanda ya zama sanadin aurenta da hayder.
Tabbas yayi kokari, kuma yayi sadaukarwa. A matsayinsa na yaro mai jini a jiki, wanda yanmata ke rubibinsa, amma ya hakura ya amsheta a matsayin mata. Duk da shekaru 5¹/² years dake tsakaninsu. Sannan a matsayin bazawara, ba budurwa ba. Batayi tunani ba, Allah S.W.A ya mata gata, ya mata canji da hayder wanda a yan watan nin da tayi dashi, ba abinda ta nema ta rasa, abinci, sutura, kudin kashewa, duk wani abu na more rayuwa dai dai karfinsa yana yi. Komai nashi enough zai yi batare da gajiyawa ba. Kamar yadda ya dauke mata dukkan bukatunta na ya mace. Wanda a zamanin nan yana da wuya mutun ya samu wannan.
Jiki a sanyaye ta tashi ta nufi toilet ta wanke idonta. Kara gyara jikinta tayi, tare da fesa turare mai kamshi ta nufi dakin hayder, don ta bashi hakuri. for the fist time. Don tun daga fist night dinsu, sai dai shi yazo dakinta, ko kuma ya dauketa zuwa dakinsa, amma badai da kafarta ta taka zuwa dakinsa ba. Ga mamakinta kamar yasan zata zo, dakin a kulle. Nocking tayi- tayi yaki bude mata, dole ta juya ta koma dakinta. Ran maza ya baci!!
Kwance yake yayi rigin gine, kansa a kan hannayensa yana kallon ruffing din bedroom din. Tasbihi yake da istigfar. Ko zuciyarsa tayi sanyi. Don gaba daya ransa ya gama baci da hubby. ” Ashe bawa zai iya zama mai butulci haka? Allah ya maka Niima ka butulce masa, wasu na nema ido rufe basu samu ba. Amma kai ka samu ka butulce! Bayan da da kudinka ka nema baka samu ba! Tabbas hubby bata sonshi, ko kadan. Yau ya kara tabbatar da hakan, Tunda har bata son hada jini dashi. Don karfin hali da rashin kunya har tana iya bude baki tace data haihu dashi gara ta haihu da wani. Wannan maganar ta masa ciwo fiye da sauran magan ganunta. Ta manta shima bafa sonta yake ba. Ba yadda ya iya, shi yasa ya rungumi kaddara. Duk da wasiyyar Yusuf na ya aureta, Sam bai yi niyyar aurenta ba, don yasan baya sonta, shi yasa ma yaja bakinsa yayi shiru, bai taba furtawa kowa ba, daga shi sai Allah, sai kuma dan uwansa. Don dama koda Yusuf din ya bukata bai amsa masa ba. Don yasan abun da kamar wuya. Kaddara tazo ta hadasu hakan yasa ya amsa da hannu bibbiyu duk da yana jin ciwon abun a ransa. Amma ya kudurta zai zauna da ita don Allah, zai kula da ita ya sata a farin ciki, don Allah, sannan ya cika muradin yayansa na ganin hubby cikin farin ciki ko bayan rayuwarsa.
Yanaji ana nocking, yasan ita ce, amma bashi da muradin ganinta a lokacin. Tsaki yayi tare da gyara kwanciyarsa.
Ranar gaba daya baccinsu ragaggene. Hubby kam tsabar nadama da danasani su suke nukur kusarta. Nafila ta kwana yi tana neman gafarar Allah, tare da ma Yusuf addua. Sannan ta nema musu zaman lafiya ita da hayder. Koba komai yanzu dole ta yadda ta amince. Shine miji kuma uban yayanta. Allah ne ya bashi girman, dole ta saukar da kanta ta nemi aljannarta.
Ga hayder ma kusan hakan ce, sai dai shi addua yama yayan nasa, tare da adduar Allah ya sauki hubby lafiya, ya azurtasu da zuria masu albarka.
*******************
Yau kwalliya sosai hubby ta zage tayi, musamman don oga hayder. Tayi kyau sosai. His favorite tayi masa break fast.
Sai 10 ya shigo gidan. Sai da ya shirya cikin kananun kaya, ya sakko zuwa kitchen. Mariya ya samu tana goge goge. Da sauri ta durkusa tana gaisheshi. Rai ya hade kamar bai taba dariya ba, wanda yasa cikin Mariya kadawa don tsoro.
” meye aikinki a gidan nan?” Ya tambayeta cikin kakkausar murya.
Jikinta da zuciyarta gaba daya suka hau rawa. ” wanke – wanke, shara, mopping, sai taya Anty aikin girki.” Ta fada muryarta na rawa
” good!! Daga yau ta kara aikenki dai- dai da wajen get, kika je sai na kakkarya kafafunki.” Ya fada in warning tone
Jiki na rawa Mariya ta amsa, tare da bashi hakuri.
” bace min a nan.” Ai kafin ma ya rufe baki tayi waje da gudunta……….A falon kasa hubby ta tarar da Mariya ta rakube wuri daya sai rarraba ido takeyi, kamar wadda taiwa sarki karya.+
” kin gama goge kitchen din.? ” ta tambayeta.
Cikin rawar murya ” aa, yallabai na kitchen din. “
Juyawa tayi ta nufi kitchen, cikin takunta na natsuwa da daukar hankali, Zuciyarta na bugawa.
Trey ne a gabansa yana jera bowls mai dauke da soup, sai cup din black tea da toasted bread.
Wani kwarjini ya mata, da kyar ta lalubo natsuwarta, ta karasa ciki.
Jingina tayi da cabinet tana mai fuskantarsa. ” mun tashi lafiya.” Ta fada cikin siririyar muryarta, mai dadin sauraro. For the fist time, sau da yawa shi ke fara gaisheta, ta fatar baki, ko rungumeta ya mata kiss a kumatu ” morning. ” .
Kallonta yayi ya tabe baki, ba tare daya amsa mata ba, ya dau trey dinsa ya fita. Bata daddara ba ta bishi a baya har zuwa falonsa. Sai lokacin ya ga wormers din data jera a dinning.
Ajiyewa yayi, yaja kujera ya zauna. Dafa kujerar kusa dashi tayi. ” na dafa maka favorite dinka.” Ta matsa tana bude masa wormers din.
” thanks!! Take your food and live that place. ” ya fada in warning tone
Rufe wormer din tayi ta dawo kusa dashi. Tare da rike kunnenta biyu, kamar yadda takewa Yusuf in ta masa laifi. ” nasan ban kyauta ba, na bata maka, I’m very sorry. ” ta fada cikin muryarta mai dadi.
Har cikin zuciyarsa yaji sanyi, tare da samun relive a zuciyarsa. Yasan yanzu ta sakko daga dokin shirmen nata. Tabe baki yayi ya ci gaba da cin bread dinsa. Plate ta dauka ta zuba masa abincin data dafa, taja kujera ta zauna, tare da janye plate din bread din ta tura masa daya plate din.
Ganin bashi da niyar ci, yasa ta dibi kadan takai bakinta. ” see!!! yayi dadi sosai.” Dubanta yayi, tare da ture plate din ” then eat.”
Bata rai tayi ” please hayder, musamman saboda kai nayi fah!”
” really!! ” ya fada yana daga mata gira.
Kai ta kada masa, tana shagwabe fuska.
” don’t cook for me again, because I’m not eated.” Ya fada yana sipping din black tea dinsa.
” why?” Ta fada a shagwabe
Jingina yayi sosai a jikin kujerar, hannunsa yasa yana shafa sajensa, idonsa a kanta.
” because I’m apred u poison me.” Ya fada in his husky voice
Ido ta zaro, tana kallonsa, cike da mamakin kalamansa. ” ta yaya zakayi tunanin zan iya poisoning dinka. Haba hayder? Rashin imanin nawa bai kai nan ba. After all me kamin da zafi da har kake tunanin haka daga gareni?” Ta fada idonta ya fara kawo kwalla.
Smacking yayi, yana shafa sajensa. ” kin san in mace bata son namiji komai ma zata iya yi, balle yadda jiya kika kara tabbatar min how trueally hate me.”
” kayi hakuri I regret every word I say to u yesterday. How can I hate u, bayan kai din dan uwanane? Ko ba soyayya ai akwai so irin na yanuwantaka tsakanina da kai.” Ta fada tana share hawayenta.
Tabe baki yayi ” it OK, ya wuce. Ki shirya haifawa hayder yara every year in sha Allah. This is your punishment, no family planing. ” ya fada yana kallonta
Kauda kanta tayi, tana dan tura baki ” in ba wuya ba!” Ta fada
” ko da wuya, daga yau zan fara saki a addua, kiyi ta zazzagominsu. Muga ta karyar son girma.”
Harararsa tayi ” kamar wata akuya? Duk shekara? ina laifin after 5 – 5 years.?” Ta fada cike da shagwaba
“We shall see.” Ya fada
” ka bari in nasrin ta shigo tai tayima duk shekara, tunda kana so.” Ta fada tana kallonsa.
Sagensa ya shafa, tare da murmushin gefen baki. ” ke zaki Haifa min duk shekara. Ita kam matar so ce, 1 zuwa 2 sun isa.”
” watan nice banza, akuya in ta zazzago maka ya’ya ga injin mai jini! Saboda baka san ciwona da zafi na ba ko? Wallahi baka isa ba, tun wuri ka sani I’m not your engine. ” ta fada cikin jin haushi
Murmushi yayi da har dimples dinsa suka fito sosai.
Tashi tayi ta dau plat din data shirya masa abinci, ta tura a gabansa.
” dole ne in ci? ” ya fada yana smacking
” yes!!! Wataran sai na yakushe fuskarka, akan wannan murmushin rainin wayon.” Ta fada
Tabe baki yayi yana shafa sajensa, tare da kara balance a kujerar. Jawo kujerar tayi kusa dashi, ta debo abincin a spoon takai bakinsa. Bude bakin yayi, ta juyemasa. A haka har yaci da dan yawa. Ta kara debowa ta nufi bakinsa ya kada kansa. Ajiye spoon din tayi, ta tashi ta fara tattara wurin.
” ke kinci abincin ne?” Ya tambayeta
” nasha kunu.” Kallonta yayi cikin rashin fahimtar meye kunun?
Ci gaba tayi da tattara kayan. Hannunta ya kama, tare da janyota ya zaunar da ita a saman cinyarsa. ” thanks for the food, its delicious. “
Murmushi tayi, tana kokarin tashi, kara matseta yayi a jikinsa. Hannunsa yasa yadan dage rigarta yana shafa plat Tommy dinta, a hankali. Wani soyayyar abinda ke cikin yakeji yana ratsa shi. Lumshe ido hubby tayi ta kara lafewa a jikinsa. Jikinta ya fara sanyi, saboda yadda sakonsa kebin jinin jikinta.
Wuyanta ya fara kissing a hankali, hannunsa na yawo a jikinta. Abunka da kwana biyu baa hadu ba, Gaba dayansu a bukace suke da juna. Juyowa tayi ta hade bakinsu wuri daya.
***************
Tana gama girkin rana, ta sallami Mariya, kamar yadda hayder ya bukata, don a cewarsa yana takura. In ta gama mata aikinta in har yana gida ta tafi kawai, basai ta kai 5 ba.
Cikin nishadi suka ci abinci, shi yajasu jam’in sallar azahar. Dakinta ta nufa don bacci takeji, jiya bata samu ta runtsa ba. Kayanta ta cire ta shiga tai wanka. Doguwar riga armless Mara nauyi tasa ta feshe jikinta da turare, ta kwanta.
Har bacci ya fara daukarta ya shigo dakin. A hankali ya hau gadon tare da mata kyakyawan runguma. Minti kadan bacci yayi gaba dasu.
*******************
” naga sako na gode Allah yayi maka albarka da sauran yan ‘uwanka duka.” Alhaji Jamal ya fada cike da jin dadi yana kallon hayder.
” amen daddy.” Ya fada idonsa a kan TV da daddy ke kallon news.
Kallon dan nasa yake cike da jin dadi, da alfaharin zamowarsa da a gareshi. Yara nawa ne masu irin wannan tunanin? A ce mahaifinka nada hali, amma kai zaka dauki dawainiyar duk wani kayan abinci na gidansa? Shinkafa, taliya, macaroni, semovita, cues -cues, madara, mangyada da sauransu. Yau kimanin wata na uku kenan duk wata haka hayder zaiyi karamin pickup na kayan abinci ya kawowa mahaifin nasa. Hakan ba karamin dadi yakewa Alhaji Jamal ba. Kamar yadda yake masa, haka zai siya ya aikawa Alhaji babba duk da nashi baya kai na mahaifin nasa.
Sun dan dade suna tattaunawa dan gane da business dinsu hayder din, kafin ya nufi cikin gida.
A main kitchen ya samu Mmn Yusuf na aikin abincin dare. gaisheta yayi cike da faraa, itan ma cike da jindadin ganinsa take amsawa tare da tambayar hubby. Sun dan dade suna magana kafin ya wuce part din Hajiya.
A bedroom dinta ya sameta tana nade kaya. Rungumeta yayi, tare da gaisheta. Dariya tayi tana jin dadin ganin autan nata.
” ya Ummi? Ba wani Matsala ko?” Ta tambaya kamar yadda ta saba kullun in yazo, sai ta masa wannan tambayar.
” lafiya kalau, tana gaisheki.” Ya fada yana fadawa kan gadon Hajiya da karfinsa.
” ina amsawa, akwai garin kununta da nasa aka mata, in ka tashi tafiya sai ka wuce mata dashi.” Ta fada
” ba gida zani ba,” ya fada yana gyara kwanciyarsa.
Kallonsa hajiyan tayi ” koma ina xaka ka tafi dashi, tunda baa kanka zaka daura ba.” Ta fada
” makaranta zani, ki bari gobe in sha Allah zan zo in karba.”
Kada kai Hajiya tayi ” shi kenan Allah ya bada saa. Kunje asibiti dai ko?” Ta fada tana kallonsa.
Kallonta yayi, cikin rashin fahimta ” waye bashi da lafiya.”
Ajiye rigar hannunta tayi ta zauna a bakin gadon kusa dashi. ” kar dai ka cemin daga kai har ita, baku fuskanci halin da take ciki ba? Ya kamata ka kaita taga likita, don tabbatar da lafiyarta da abinda ke cikinta. Sannan ba zaa rasa shawarwarin da likita zai baku ba, Ta wurin inganta lafiyarta, duk da ba wani laulayi take ba, amma dai kam ya kamata kuje.”
Kansa ya daura a cinyar Hajiya, cike dajin nauyinta. For the fist time in his life daya ji nauyin Hajiyan. ” munje 2 days ago.”
” yauwa hakan yafi ai.” Ta fada tana shafa sumar kansa.
Murmushi yayi ” na kusa zama daddy, ya fada in very low voice. “
Dariya Hajiya tayi ” na kusa zama kaka, dan’ da namiji shine jika, abin cikin kwan dayafi kwan dadi.” Kai ya dago cike da shagwaba. ” yanzu sai fa kifi son shi, ko ita a kaina ko.” Dariya Hajiya tayi ” soyayyar autana ta dabance, albarkacin autana zasuci.”
Murmushi yayi, tare da kara kwanciya akan cinyar tata.
” ya maganar makarantar naka?” Hajiya ta tambaya
Tashi yayi ya zauna. ” zan dan dakata tukun, dama nida ita gaba daya nake son mu tafi, itama ta fara nata karatun, amma yanzu ina ganin zan bari sai bayan ta haihu sai mu tafi.”
Murmushi Hajiya tayi ” hakan ma yayi, Allah ya sauketa lafiya.”
” amen.” Ya fada
Murmushi Hajiya ta sake yi, ganin tsantsan farin ciki, tattare da autan nata. Hira sosai sukayi da Hajiya sai kusan magrib yabar gidan, ya nufi masallaci inda yake salla, tare da daukar karatun littatafan addini.
*********************
Dawowar hayder ya wuce bedroom dinsa, da mamaki yake bin hubby da tayi dai dai akan bed dinsa da kallo.
Sanye take da kayan bacci silk red, karamar riga da boom shot, sun lafe sosai a jikinta. Kamshin turarenta dana dakin ya bada wani kamshi mai dadi, da sanyaya rai.
Da sauri hubby ta sakko daga gadon, rungumeshi tayi, shima kamar jiranta yake ya kara matseta a jikinsa. Sun kai some minute sannan ya dago da kanta ya manna mata kiss a goshi, da saman labbanta. ” bakiyi bacci ba?” Ya fada in husky voice kai ta kada, cikin shagwaba ta kara makalewa a jikinsa. ” ina kake zuwa ne, kusan ko yaushe baka dawowa sai after 9?” Ta fada cikin shagwaba1
” tadi nake zuwa.” Ya fada yana kallonta kasa -kasa dariya tayi, ” lokacinka ne ai, Allah ya bada saa.” Smacking yayi tare da dago kanta suna kallon juna.
” bakya taya Nasrin kishi kenan.” Ya fada
” taga zata iya ne ai,.” Ta fada
” kamar Yaya?” Ya tambayeta
” tasan kana da yan mata buhu – buhu amma still tana sonka. Tasan kuma bayan ita bazaka rasa wata a gefe ba.”
” banda sharri dai.!”ya fada yana
Kallon yadda take motsi da bakin, cikin shagwaba take magana. A da yana daya daga cikin abunda ya tsani hubby saboda shi. Amma yau da ta fara masa salon shagwabarta sai abun yana burgeshi Kwarai. Lips dinshi ya daura a nata, batayi wata wata ba, ta cafke tare da sarrafa shi cikin bakinta, wani salo take masa da baisanta da shiba. Ai gaba daya sai ga malan hayder ya rikice. Sun dade suna romancing juna, kafin ya zareta a jikinsa.
Wanka ya shiga, yana fitowa ya feshe jikinsa da turare, bai ma bata lokacin sa kayan baccinsa ba, ya nufi hubby dake kwance lamo, gaba daya jikinta ba kuzari. Ajiyar zuciya suka sauke a tare.
********************
Hayder ne ya shigo, sai wasu mutun biyu, dauke da kwali. Sai da ya basu izinin shigowa ganin hubby bata falon.
A falonta na kasa suka ajiye fridge matsakaici mai kyau. Sai da suka jona komai intact sannan suka masa sallama suka tafi.
Fita yayi, suka shigo da malan idi, rike da ledoji. Sannan malan idi ya fita.
Bude fridge din yayi, ya fara jera fresh fruits: apple, orange, pear, grebs peach, banana etc sai da ya cika fridge din da fruit. Sauran ya kwasa ya mikawa malan idi
A hankali take sakkowa daga steps din. Yau gaba daya jikinta bata jin dadinsa, ga tashin zuciya, ko dan kunun data saba sha yau bata sha ba. Tana jin yunwa amma ta rasa me take son taci.
Da sauri ta fada jikinsa. ” morning. ” ta fada tana zagayeshi da hannayenta biyu.
” morning!!! Are u OK?” Ya fada cike da kulawa, ganin yanayinta
Kai ta kada masa ” tun asuba, sai yanzu? Shima tadin kaje?” Ta fada tana tura baki, cikin shagwaba
kiss ya mata a goshinta ” yaushe kika fara samin ido ne?” Ya fada
” ba sa ido bane, ina son sanin inda kake zuwa ne?”
” wurin sweet heart dina.” Ya fada yana smacking
” an jiman nan zan kira Nasrin, in bata bayani.” Ta fada tana zama a kan daya daga cikin kujerun falon.
” please karki kashemin aure, tun baa daura ba.” Ya fada yana kokarin haurawa sama.
Sai lokacin idonta yakai kan fridge din. Tashi tayi tana binsa da kallo, yayi mata kyau sosai, gashi yayi das a wurin, kamar dama don shi aka bar space din. Budewa tayi. Murmushi ne ya bayyana a saman fuskarta.
Bunch din ayaba ta dauka ta koma ta zauna, TV ta kunna tana ci tana kallo, cikin ikon Allah taci sosai. Mariya ce ta shigo ta tattara bawon. Kwanciya tayi tana jiran sakkowarsa, don shi ma baiyi break fast ba, gashi har pas 11 ……….
Wasu na complain na rashin yawan typing, wanda already nayi bayani. Amma nayi tunanin in har pages din baya muku yadda kuke so, mai zai hana in maida update dina every 2 days? Ina jiran ra’ayoyinku. Thanks
Kallonsa tayi tana murmushi, yayi kyau, cikin jamfa da wando, farare. ta mikewa tayi tabi bayansa zuwa falonsa. Kujera ya ja mata ta zauna, kafin ya ja kujerarsa ya zauna.+
Fleet din vegetables chicken toll, ta janyo tare da cire rapper din ledar din. Taja karamin fleet ta sa masa ta tura gabansa. Sai da ta hada masa komai sannan ta kalleshi. Idonsa cikin nata ” bisimillah!!!” Ta fada tana dan harararsa don ta tsani murmushin data sama na rainin hankali da yake mata, gashi ta lura ya zama kamar a jikinsa.
” shukhran!.” Ya fada tare da yin bisimillah ya fara cin abincinsa. Roll daya ta dauka tana ci a hankali, idonta na kan TV tashar CNN.
Wani farin ciki hayder keji a ransa, tare da godewa Allah bisa niimarsa gareshi. Yau shine da iyali, ana tattalinsa da kulawa dashi, abinda bai taba tunani ba daga hubby, amma kwana dayan nan gaba daya ta canza, wani kulawa da tattali na musamman take bashi. In ya tuna nan da few months zai dauki danshi na kanshi, flesh and blood farin cikin baya misaltuwa a zuciyarsa.
” meye matsayarki kan karatu?” Kamar daga sama taji tambayarsa. Juyowa tayi ta kalleshi idonsa baya kanta, Shagwabe fuska jin tayi shiru yasa ya dago yana kallonta. Hada ido sukayi, ya daga mata gira, yana gyara zamansa.
” ni kawai ka mai dani islamiyyata.” Ta fada cike da shagwaba
Tabe baki yayi, tare da sipping din green tea dinsa. ” ba wannan nake magana ba.” Ya fada in husky voice.
Kara shagwabe fuska tayi, tana dan tura baki. ” islamiyya kawai nake so.”
Shi dariyama taso bashi, yadda take yi, tare da burgeshi. lallai yana da aiki! Hubby akwai shagwaba ta karshe ma
” Mace itace jigo na farko na gina al’umma, in aka samu rauni ko sakaci ta wurin bata ilmi da tarbiyya, tamkar an rusa al’umma ne baki daya. Ilmi ina nufin na addini, wanda zai daurata kan tafarkin tsira, wanda zata tarbiyyanci al’umma zuwa ga rabauta. Ilmin zamani shi zai kara haska mata rayuwa da abinda ta kunsa. Mace na bada ingantacciyar tarbiyya yayin da ta hada ilmi duka biyu. Rayuwarta data yayanta zakiga ta fita daban. Karki manta da, Hadisin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, wanda ya ke cewa ‘Dalabul ilmu faridatun ala kulli muslimin wa muslimatin,’ wato neman ilimi farilla ne ga dukkan musulmi na miji ne ko mace.
Mace mai ilimi itace za ta san yadda zata tafiyar da gidanta da kyau idan tana da hankali.
Mace itace uwa, ita za ta sa yaranta a kan hanya, har shi mijinta da kan sa ita kan koya masa dabi’u masu kyau. In kuwa ba ta da ilimi, ba ta san abin da ya kamataba tana iya zama masu makauniyar jagora. Ilimi ke sanya mace ta san yadda za ta tafiyar da kanta a kowane irin hali. Za ta zama wayayyiya mai basira.”
Shiru tayi tana sauraronsa cikin mituwar jiki. Ita kanta bata san dalilinta na rashin son karatun ba, to ita in ma karatun ne me zata karanta kenan? Secondary din ma ya takare balle university!! So kawai yake tayi ta kwaso masa carry over yana tsokanarta zero head. In ba haka ba, bata san ta inda zata fara ba.
Ganin tayi shiru, ya kama hannunta zuwa 3 sitter din dakin. Zama yayi, ya kwantar da ita a jikinsa. Hannunsa ya tura cikin rigarta yana shafa cikinta a hankali, kiss ya mata a goshi.
” think about what i say to u. Masu bincike na duniya ma sun ce duk namijin da ka ga ya yi nasara a rayuwarsa, to akwai mace bayansa – ko uwarsa ko matarsa, I want u to be that woman. “
Tura baki ta danyi, tare da kara shigewa jikinsa. ” to ni inma nace zanyi karatun me zan karanta?.” Ta fada a shagwabe
Sunkuyowa yayi ya summaci dan bakin nata dake daukar hankalinsa, in tana shagwabarta. ” ba komai bane matsalarki, illa rashin maida hankali, wasa ya miki yawa. Amma na tabbata in har zaki cire komai ki maida hankali, ba abinda bazaki iya karantawa ba.”
Murmushi tayi ” ni dai da ka barni a islamiyyata, nafi jin dadi.”
” I will teach u, by my self.” Ya fada
” no my king ma haka ya ce, amma gaba daya karatun a shiririta yake karewa, haka ya hakura ya sani a islamiyya.” Ta fada idonta na cikowa da hawaye
Wani iri hayder yaji a ransa, da ya kasa fassara yanayin. Kasa ce mata komai yayi, mikewa yayi. Ganin yana niyyar fita ta tashi ta zauna ” sai ina?” Ta fada
Har yakai bakin Kofa, ya juyo yana kallonta. Smacking yayi ” main house. ” ya fada in his husky voice.
Tasowa tayi ” bamu gama magana bafa!” Ta fada tana fadawa tsakiyar kirjinsa, tare da zagayeshi da hannayenta biyu.
” zamu karasa in na dawo.” Ya fada cikin low voice don gaba daya jikinsa ya fara sanyi.
” in zo muje please!!? ” ta fada cikin marairai cewa, tana kallonsa.
Gaba daya hayder ya shiga wani hali, wani felling ne ke fusgarsa, musamman yadda yake jin kirjinta na gogan nasa. Ga yadda take marairai cewa tana fari da ido kadan,. Abun ya tafi dashi, abinka da mai jiran kiris.
Hubby tayi murmushi ta dauke fuska, tana mamakin hayder.
Kara jawota jikinshi yayi ya rungumota tsakankanin hannuwanta ya zura hannayenshi ya na shafo kirjinta dake tsone masa ido, yana lumshe ido yana fadin ” I love them, they are so sweet and nice “
Hubby kara shigewa jikinsa tayi, tare da rumtse ido tanajin dadi yadda hannayensa ke yawo a jikinta. hannuwanta tasa tana shafo sumar kanshi shi kuma yana ta faman sunsunarta, yadda take massaging hair dinshi da soft hand dinta yasa yakara shiga mood da a hankali ya rinka yin kasa da hannunshi yana shafa ilahirin jikinta, yana isa wurin Tommy dinta ya rika shafashi yana dan kaiwa ga mararta kadan. Sunkuyawa yayi ya sumbaci plat Tommy din.
Dukansu numfashi suke ta fitarwa,
Idanunsa da suka canza colour, ya dago kanta yana kallon kyakyawar fuskarta, yadda take sauke numfashi, idonta a rufe, iskar bakinsa ya hura a saman fuskarta, tai far da idanta ta bude su a kansa. idanunsu na kallon juna yace ” please I’m in mood”ya marairaice yana kashe mata ido daya.
ido hubby ta zaro, duk da itama ya tsokanota a bukace take. ta bude baki zatai magana ya hade bakinshi da nata ya cafko harshenta yafara tsotsa while hannuwanshi a kan kirjinta yana massaging dinsu nicely,
Gaba daya hubby ta kasa hanashi don she’s loosing her sense se numfashi kawai takeyi, kafafuwanta ne suka gaza daukarta ta tafi luuuu ya yi sauri ya tallabota. Dagata yayi bridal style ya nufi dakinsa da ita. Suna shiga ya ajiyeta saman bed. yasa hannu ya zage zip din rigarta, ya zage na skirt Yayi wurgi dasu, kissing dinta tundaga up, to dawn.
***********************
Mita take cike da shagwaba na wankan da ya sata, bata shirya ba, ga lokacin daura abinci har ya wuce.
Smacking yayi, yana shafa sajensa. ” in har baa daina min irin wannan shagwabar ba, nima yanzu na fara sa mutun wanka a gidan nan.”
Harararsa tayi tana tabe baki ” ka fadi gaskiya!? Dama can haka mutun yake.”
Rike gemunsa yayi kadan yana daga mata gira ” koma meya faru laifin kine. As long as ana min haka, to mutun ya shirya.”
” haka kurun! Kullun mutun cikin ciwon jiki.” Ta fada tana zura doguwar rikarta, hand dryer ta dauka ta fara busar da gashinta.
” karfe daya baya amo, duk wanda ya sai rariya ai yasan zata xubda ruwa.” Ya fada tare da manna mata kiss a kumatu ya fita.
Da kallon rashin fahimtar zancensa ta bishi, har ya fice a dakin. Tabe baki yayi ta cigaba da abinda take.
Dakinsa yaje ya canza kaya, ya dau makullin bike dinsa. Ya fice a gidan, cike da farin ciki. Yana daya daga cikin abunda yake burge hayder dan gane da hubby irin duk yadda zai zo da bukatarsa bata hanashi, koda sau nawa zai zo mata, sai dai daga baya taita mita tare da harare harare, ita a dole jikinta na ciwo, bai hana kuma in ya sake bijiromata ta mika wuya. A rayuwarsa yana son mace mai juriya, saboda yanayinsa. Ta nan kam sunyi mach.
Hubby kam sai da tayi sallar azahar sannan ta sakko da mamakinta ta tarar da Asima da Asiya, zaune a falonta na kasa, Mariya ta cikasu da snacks and juice. Da faraa ta karasa tana musu sannu da zuwa, duk da yadda kirjinta ya buga ganin Asiya, don ta dade tana tunanin yadda haduwar tasu zata kasance. Da faraa suma a kan fuskarsu suka gaisa, hubby na tambayarsu saukar yaushe?
Asiya ce ta amsa da ” jiya.” A takaice tana karewa hubby kallo, ganin yadda ta kara kyau da cika, wani dan banzan kishi ne, ya turnike zuciyarta. A take idonta suka fara cikowa da hawaye.
Hubby ta lura da kallon da suke binta dashi, musamman Asiya. Tausayin asiyan ne ya cika zuciyarta. Tare da jin kunya da nauyinta. Tashi tayi a san yayi, tare da ce musu bari tadan je kitchen ta dawo.
Da kallo Asiya ta bita, har ta bacewa ganinta. Ajiyar zuciya ta sauke. Asima ta kalli kanwar tata cike da tausayawa. ” ki kwantar da hankalinki, ki cire komai a ranki, ki nemi zabin Allah a alamarinki, sai ki samu sauki cikin rayuwa. Kar ki zamo mai kwallafa rai akan abun da baki da tabbas din samunsa.” Kai Asiya ta kada. Tare da bin falon da kallo. Ya burgeta sosai, “ina ma gidanta ne da hayder.” Wata zuciyar ta fada
Girki hubby ta daura, ta dawo wurinsu, hira sukeyi cikin natsuwa da yake akwai shakuwa sosai tsakaninta dasu. Asima ta saki jikinta sosai sai ba hubby labarin wanda zata aura take, da irin dan banzan kishinsa, suna dariya. Asiya kam TV ta kurawa ido. Ta fada duniyar tunani.
Itafa har yanzu bata cire rai da auren hayder ba. Amma ganin hubby a yanzu ya sanya tsoro a zuciyarta. Mai mace kamar hubby mai zai yi da irinta, ita kanta bata gajiya da kallon hubby koda can, saboda tana burgeta, komai nata masha Allah. Balle yanzu da gaba daya taga ta canza, ta kara kyau jinkin nan kamar auduga sai glowing yakeyi, ko ina ya kara cika, masha Allah. Duk da tasan yadda akayi auren hayder da hubby amma. Tasan koba dade- ba jima zasu dai daita kansu. Balle hubby ba irin matan da zaa iya dauke ido a Kansu bane.”
Dawowar hubby daga duba girkinta, ta kira sunan Asiya don tun dazu ta lura bata tare dasu. Juyowa tayi ta kalli hubby, sai yanzu hubby ta kara ganin ramarta.
” kiyi hakuri, nasan irin son da kikewa hayder. Amma gashi yadda kaddara ta zo mana baki daya. In har kina sonsa har yanzu, pyete for your love, I’m happy to have u hare.” Hubby ta fada tana murmushi
Gaba dayansu baki sake suke kallonta, da mamaki. Ajiyar zuciya asima tayi ” kin san me kike fada kuwa Anty hubby? Kishiya fa kike wa kanki tanadi? Duk da ba auren soyayya kukayi ba, ya kamata kina kishin mijinki, ba ke zaki ba da hanyar shigo miki da wata ba.” Murmushi hubby tayi ” asima kenan. Bazan yaudari kai na ba, nasan ko ba dade ko ba jima, hayder zai auro zabin zuciyarsa. Zan so ace wadda na sani ce, ba bare ba. Ko ba komai nasan irin son da Asiya ke masa, zanyi farin ciki ace ita ce zabin zuciyarsa.”
Ajiyar zuciya Asiya tayi ” maganar gaskiya bazan iya kishi da keba. Na riga na yanke hukuncin ba daya daga cikin masoyana dama, zan manta da komai, in shafe babin a zuciyata. Dama bawai yasan zancen bane, a yadda na fuskan ce shima he is not interested about me. So ki rungumi mijinki, ki kula da kayanki. U are very lucky in life, how I wish I was u!.” Ta fada tana share hawayenta.
Tausayinta sosai ya kama hubby, kusa da ita taje ta zauna,. ” kar kiyi saurin fidda rai. Keep trying, I Will help u, like I say before. ” ta fada cikin raunin murya.
” bazan iya kishi da keba. Nasan hayder ma bazai iya hadaki da kowa ba. Me zai nema ga wata, bayan duk abinda yake bukata kin hada?” Ta fada tana kallon hubby ta kara da cewa ” da wata ce, sai inda karfina ya kare!.”
Hannunta hubby ta kamo cikin nata. suna fuskantar juna “Fahimtar mutane gameda kyau ta bambanta, kamar yanda fahimtarsu a dandano ko kala ya bambanta! A yayinda a fahimtarka farar mace itace kyakykyawa, wani zaka samu Baqace jarumarsa, a yayinda kake son mace mai qiba, wani kuma siririyace zabinsa, ayayinda kake fifita doguwa, wani gajera tafi masa, duk sifar da tafi maka, to zaka samu wani baya sonta!
A duk sanda ka samu macenda kake gani duk duniya ba kamarta, baka ganin aibu ko muninta, wani baida abinda ya tsana kamarta!
Shin don bata da kyau ne? Ya akai ta maka kyau har ka zabeta, amma wani ya tsaneta yake ganin muninta? Shin to menene kyau?”
Shiru tayi tana kallonsu, suma ita suke kallo da nazartar maganarta. Murmushi tayi ta ci gaba da cewa
“A tunanina kyau qaryace kawai, tamkar hangen ruwane, ga mai jin kishi. Haka kyau yake gizo a idon masoyi, hakanan muni yake gizo da kawalwalniya a ido da qwaqwalwar maqiyi!
A lokuta da dama, duk sanda muka kamu da son abu, zamuga duk duniya babu mai kyawunsa, ba abinda mukeso sama da shi, bamu ganin muni balle laifinsu, amma da zarar mun rabu, sai muga abun ya koma mummuna abar kushewa, shin kyawun ya barshi ne, kokuwa ta ya sauya kamanni ne, kokuwa Kyau tsuntsune dake sauka akan mutum ya tashi a sanda yaso?
A duk wannan tsawon kai kawon, MACE itace mai shan wahala akan kyau, akullum burinta ta gamsar da MAZA cewa ita kyakykyawace, dukda samun yardar mutane abune mai wahala mara yiwuwa, hakan ke kaisu ga shafe shafe (bleaching), feqe feqen haqora, aske gira, qarin gashi, qari/ciko a
jikkunansu don cike wata gaba dakeda komada ko tawaya a tunaninsu da sauran salo don kama zukatan maza!
Yar-uwa, a sanda kika soma bleaching don ki zama fara, ya zakiyi da mazan da ke son Baqar mace? Kokuwa kinga duk farar mace aureta ake baqa ke kwantai?
Ya zakiyi in kika gama bleaching din kuma baki samu masoyi ba?
Idan kikaje aka feqe haqorinki don kiyi wushirya, to ya zakiyi da wadanda basuson mai wushirya, kokuma masuson wushiryar su gujeki don ba kalar taki suke so ba?
A sanda kikaje kina ta kankare kankare da aske aske da ciko, ya zakiyi da wadanda sukuma duk wadannan abubuwan basuyi musu ba, basu son masu su?
Nawane baqaqen mata da kike kallo munana suke dakin mazajensu sunyi aure, nawane matayenda zakiga kaman aje filin tashe dasu don tawaya da muni, amma sun samu mazajen aure, suna dakunansu? Nawane kin fisu kyau da kamun kai, gashi sunyi aure amma ke baki samu miji ba?
Yar-uwa ki sani WALLAHI KE KYAKYKYAWACE. Ki yarda da kanki, ki yarda kema mace ce, sai kifi burgeshi fiye da yadda zan burgeshi. “…………Kallonta suke cike da gamsuwa da jawabinta. Hannunta dake cikin na hubby Asiya ta kara rikewa da kyau. murmushi tayi mai karawa fuskarta kyau da kwarjini. Asima zatayi magana Asiya ta dakatar da ita, da alama da hannu.+
” I agree with every word u say. Amma da gaske nake na hakura, shawara daya zan baki, no matter how the situation is karki kara cewa wata ta auri mijinki, at the end u regret it. Baki san kishiya ba!! My be don baki ganta a gidanku ba. Shiyasa. Mu da muka tashi muka ganta munsan illarta, da alkhairinta. Bana ma kaina fatan ta, in dai ba kaddara ba, wadda baka wuceta. Nasan ko baki son hayder yanzu, na lokaci kadan ne, tun da har kika so Yaya Yusuf, na tabbata in no time zaki samu zuciyarki cikin kaunar hayder.
A halitta suna matukar kama, in kin dauke tsayi, da suffar karfi da hayder ya fi Yaya Yusuf. Sai ban bancin ido. Na Yaya Yusuf manya, na hayder madai daita. Sai dimples da Yaya Yusuf bashi dashi. Amma hatta muryarsu, da tafiyarsu kusan iri daya ne. Ta Yaya zaki iya kin son hayder bayan kamman nin da ke akwai tsakaninsa da Yaya Yusuf? Ga kuma jini da kuka hada! Halayyarsu wani zaki iya samu iri daya, wani kuma sabanin hakan. Hayder yana da zafi, sabanin Yaya Yusuf mai sanyin hali. Ki nutsu, ki rungume mijinki, ki rike aurenki. Kar kiba kowacce shegiya shigowa cikin rayuwarku.”
” abin harda zagi?” Hubby ta fada tana murmushi
” baki san yan matan yanzu bane shi yasa, bamu da dadi ko kadan. In mun shiga kokari muke mu fitar data ciki. Don haka ki rike wuta, ko wannan kodaddiyar kiyi kokarin mantar dashi ita.”
Dariya sukayi baki daya. ” baki da kirki Asiya, Nasrin din ce kodaddiya? Bari ya jiki kina kiran Sweet heart dinsa da kodaddiya” Hubby ta fada tana dariya
” ai ba karya nayi ba. Ke na lurama Sam baki kishi, bayan ansan mata da kishi, koda ko basa son abu, sukan nuna kishinsu.” Asiya ta fada tana rike baki.
Asima dake sauraronsu tana murmushi ta ce ” ki barta very soon zakiji Anty hubby ta saka gajeren wando.”
Dariya sukayi gaba daya. ” Allah ya kyauta.” Hubby ta fada tana nufan kitchen.
” kin san dama duk soyayya mai tsafta daga kiyayya ake farata, mun ji labarin naku mafarin, zamuga how u end up. ” Asima ta fada tana dariya
Asiya ta kalli Asima tana murmushi ” na gode da shawararki uhtee, jhazhakallahu bi jannah.”
” ba komai, amfanin yan’ uwantakan kenan. Muba juna shawarar da zata anfane shi, lokacin da yake cikin matsala. Allah yasa haka shine mafi alkhairi a gareku baki daya. Amma menene anfanin son maso wani?”
” koshin wahala kam. Allah ka hadamu da masoyanmu na gaskiya.” Asiya ta fada.
” Amen uhtee!..” Asima ta fada dai dai lokacin da hubby da Mariya ke shigowa da wormers din abinci. A dinning suka jera komai kafin hubby ta kallesu tana murmushi ” bisimillah “
Mikewa asima tayi ” kamar kin san kamshin abincin nan ya gama cika min hanci, Allah Allah nake a gama. Sam bana juriya yunwa yanzu.” Asiya ma bayan Asima tabi suka zauna. Asiya ce tayi serving dinsu. Suna ci suna hira da dariya, gwanin sha’awa.
” ban labarin new catch!! ” hubby ta fada tana kallon Asiya
Murmushi tayi ” ba yanzu ba, sai komai yayi normal zakiji.” Bata rai hubby tayi. Dariya Asiya tasa ” bafa abinda kike tunani bane!! Na fi son sai komai ya dai daita, zanzo da kaina na baki labari, ba sai a waya ba. Nasan kuma zakiji dadi sosai!”
Kada kai hubby tayi ” Allah ya sa! Ya zaba mafi alkhairi.”
” Amen.” Suka fada baki daya
” kira junaid, ya kamata mu leka gidan Yaya Ahmed. ” Asima ta fada tana kallon Asiya
Tashi tayi, ta nufi jakarta, ta dau waya ta kirashi.
” dama shi ya kawoku, amma bai shigo ba?” Hubby ta tambaya
” eh! Sauri yake, su hayder na jiransa.”
Kada kai hubby tayi. Sun gama suka tattara wurin, tare da wanke kayan da sukayi anfani dashi, sunayi suna hira.
Dakin hubby suka shiga, don gabatar da sallar la’asar. Sun sakko kenan junaid na sallama daga bakin Kofa.
” yasu mommy? ” hubby ta tambayi junaid cike da kewar iyayayen nata.
” lafiya kalau, dady ne bai ji dadi ba kwana biyu, amma yaji sauki.”
Cikin damuwa ta ce ” amma shine aka rasa wanda zai gayamin?”
Murmushi junaid yayi ” kiyi hakuri, kin san daddy in bashi da lafiya ba son a fada yake yiba.”
” duk da haka, ai ni ba bare bace, balle a kasa gayamin.” Ta fada cike dajin haushi
Ganin ranta ya baci, ya shiga bata hakuri. ” it OK, ka gaishesu sai nazo!” Ta fada tana rakosu wurin motarsa.
Ledar dake hannunta ta mikawa Asima dake baya. ” godiya sukayi mata, junaid yaja motar suka tafi.
*********************
Hayder ta kira, tana son zuwa gida. Bai hanata ba, ya ce ta jirashi, zai zo sai su dawo tare. 5pm ta nufi gidansu cike da jin dadin yau zataga daddy dinta, don sun dade basu haduba sai a waya.
***********************
Ta fito wanka kenan idonta ya sauka a kan wata kyakyakyar traveling bag, pink a kan gadonta. Wurin ta nufa, tare da zage zip din, ajiyar zuciya tayi, don ta dan tsorata, tunda bata san da ita ba.
Laffaya less ne masu kama da saree kusan guda 5, sai irin rigunan India da ake hadasu da jeans 3 masu matukar kyau. 2 set na Indian gold, sai Indian fashion, yankunnaye warwaro, besleet, zobuna, Indian perfumes, Sai riga da wando set 2. Murmushi tayi tasan aikin hayder ne, don shine ya dawo daga India kwanan nan. Zip din taja ta rufe ta dauke bag din ta mata wuri a woodruff dinta.
Taji dadin kyautar don kayan sun burgeta matuka.
Sai da ta gama shirin baccinta tsaf ta nufi dakin hayder. Kamshi mai dadine ya bugi hancinta, ga sanyin AC. Ba kowa a dakin, jikin mirror dinsa ta nufa tana kallon kayan shafansa masu matukar tsada. Idonta ne yakai kan turaren da Nasrin ta masa kyautarsa a Cyprus. Dagawa tayi tana juya kwalbar, tare da zare murfin tana shin shinawa. Da sauri ta zareshi a hancinta. ” ouch!!!.” Ta fada tana maidashi. Don ji tayi ya balain hawa mata kai, sabanin farkon ganinshi da kamshin ya mata dadi.
“What are u doing with my special perfume?” Ya fada yana takowa inda take tsaye, sanye da rigar wanka, fara Sol. Wai gowa tayi tana kallonsa tare da tabe baki. ” turaren da yake wari!” Ta fada a shagwabe
Ido ya zaro ” turaren nawa ke wari.?” Daga ido tayi tana yamutsa hanci.
Hannunsa ya kai ya dau turaren.” Kinsan yadda nake sonshi kuwa?” Ya fada yana sashi a kan kirjinshi, dake bude. “Ina son shi sosai.” Ya fada yana kashe mata ido daya, Tare da daga mata gira daya.
Shiru ta masa tare da daukar wani turaren, Bufewa yayi zai fesa. Da sauri ta kwace a hannunsa. Mika mata hannun yayi ta bashi, ta makale kafada, tare da maida hannnta baya. ” ban son warinsa.” Ta fada a hankali cikin siririyar muryarta.
Hannunsa duka biyu ya daga sama, kamar mai kiran sallah. ” sorry!!!! Na manta fah! Yanzu kin zama tabani kaga sarki.”
Body lotion dinsa ya dauka, hannunta ya kamo ya danka mata. Kallonsa tayi, ta kalli lotion din. Gira ya daga mata ya zauna a chair din mirror.
Murmushi tayi ta fara shafa mishi, cike da natsuwa, Lumshe ido. Mikewa yayi tare da rungumota ta baya,
ji numfashin shi na sauka kan wuyanta, tana juyawa kaman predator ya Kama bakinta da nashi bakin, idanu hubby ta lumshe. hannunshi biyu yasa ya riko waist dinta tare da danneta da kirjinshi giving the access of her chest pressing he’s chest then he’s hand on her well shaped hips, hannu biyu tasa ta zagaye west dinsa dasu. baya baya ya dingayi har saida ya kai bakin gadonsa ya zauna, ya Kama bakinta gan kaman cikin nasa ba tare da ya Saketa ba, he was pushing he’s tongue deep that jikinta ya saki bayan kanta ya rike da hannu daya sannan ya dora dayan hannu kan chest dinta not massag dinsu a hankali, cikin kwarewa. kaman ya samu sweet haka ya dinga shan bakinta, sakin bakinta yayi, ya zare bakinshi, cikin nata, idanuwansu cikin na juna, wani kiss ya Dan dora a kan lips dinta.
A shagwabe hubby tace ” please hayder let me sleep, jikina ba karfi.”
A kunnenta ya rada mata cikin husky voice dinsa. ” bari in baki maganin karin karfi, da kuzari.” Kafada ta makale. ” please mana!!!” Shima kwaikwayon muryarta da yadda tayi maganar yayi ” please habiba.!!!!” Dan harararsa tayi ” banson habiban nan, ka kuma san haka!.” Hancinta ya lakace ” I call u Habiba because it your name. “
” call me Ummi kamar yadda su mommy ke kirana, in bazaka kirani da hubby ba.” Ta fada
Smacking yayi, ” nafi jin dadin Habiba.”
Duka ta kai masa a kirji ” ka gama rainani completely! Koda yake ba laifinka bane.”
Gira ya daga mata ” who’s fault? ” tura baki tayi, cikin shagwaba ” it’s my fault.”
Still fuskarsa na dauke da smacking ” u amazed me some time,!” Ya fada yana kara rungumeta a jikinsa.
Ido ta lumshe cike da kunya ta fara shafa sajensa daya kwanta gwanin shaawa. Ganin hakan ya kara lafewa cikin jikinta, ya fara aika mata da samun ninsa masu wuyar fassaruwa. Gaba daya kowa na kokarin faranta ran daya, na dogon lokaci, kafin suka sararawa juna, bayan kowan nensu ya samu cikakken gamsuwa. A kunnenta ya rada mata “Allah ya miki albarka, Rabbi ya cika miki rayuwarki da farin ciki.”
Lafewa tayi a kan faffadan kirjinsa, tanajin bugun zuciyarsa na harbawa kan nata, a haka suka dau lokaci kafin suka mike don tsarkake jikinsu. Daukanta yayi bridal style zuwa toilet din.
A toilet dinma sun dade suna romancing juna, kafin sukayi wanka suka fito.
Kwanciya tayi tana ” wash Allah nah!!”. Tana yamutsa fuska da tura baki.
” wayyo jikina duk ciwo yake.” Ya fada yana kwaikwayon maganarta, yana rike baya.
Harararsa tayi, ta dau filo ta wurgeshi dashi. Chabewa yayi ya jefa mata kan fuskarta ” lazy Bone’s. ” ya fada yana saka kayan baccinsa.
Kwafa tayi ” zaka dawo ne.” Ta fada cikin dan jin haushin lazy Bone’s din daya kirata dashi.
Kunnensa duka biyu ya rike ” afwan!!! Amin ko wanne horo amma banda wannan!! ” yana murmushin gefen baki.
” zaka ga lazy ganin idonka.” Ta fada tana kara gyara kwanciyarta. Kusa da ita yazo ya kwanta, tare da janyota jikinsa. ” I say I’m sorry ko.?”
Kirjinshi ta fara shafawa a hankali. ” naga kaya a bedroom dina?”
Kiss ya manna mata a goshi,” its for u”
” na gode, Allah ya saka da alkhairi. ” ta fada still tana shafa kirjinsa a hankali.
Yaji dadin adduarta sosai. Mannata ya karayi a jikinsa, kafin sukayi adduar bacci,. A haka suna dan wasa da juna har bacci ya kwashesu.
**********************
Sun gama break fast, hayder ya mikawa hubby ticket. Amsa tayi tana dubawa, Dagowa tayi ta kalleshi. Yana jingine jikin kujera yana shafa sajensa. Fuskarsa dauke da smacking.
Hade fuska hubby tayi, ” no way?” Ta fada tana mikewa………..