HEEDAYA CHAPTER 6 BY By Khaleesat Haiydar

HEEDAYA CHAPTER 6 BY By Khaleesat Haiydar

                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

Parking Junaid yyi kofar gidan Baffa ya kashe motar sa ya bude ya sauka, sanye yake da kananun kaya, walking 

calmly ya isa gate suka gaisa da Mai gadi sannan ya shiga gidan, baya bukatar tambayar entrance don tuni ya hango, 

yana isa bakin kofar yayi knocking, bbu bata lkci aka bude kofar, kanwar Sudais ce ta bude kofar, yana kallonta da 

murmushi fuskarsa yace “Good evening” tana kallonsa irin kallon rashin sanin tace “Welcome…” Muryar Abba suka 

ji yace “Is that Junaid” Junaid yayi kasa da kai yace “Ina yini Abba” Abba yace “Lfya lau, Zainab ki kai sa bangaren Kaka” Zainab na kallon Junaid tace “Toh” bin bayanta yyi suka nufi parlon kaka, Abba kuma ya fita rike da makullin 

motarsa, da sallama Junaid ya shiga parlon kaka, Mami dake tsaye rike da jakarta alamar xata wuce ta juya tana 

kallonsa, Kaka ta kalli Junaid sannan ta kalli Mami tace “wannan ne d’an naki?” Mami tayi murmushi tace “Eh 

Mama” kaka tace “Ahh ba shakka… Kyakkyawan bafillatani da shi wllh, ya ma fi ki kyau ai, da ganin ubansa ya 

yo….” Mami dai na murmushi tace “To sai na shigo da daddare kaka, bari in je” kaka tace “A’a ki yi xaman ki kar ki 

wani wahal da kanki ba gashi ina kula da ita ba tsakanina da Allah….” Mami tace “Toh shkkn mama” Daga haka ta 

fita parlon, Kaka na kallon Junaid dake tsaye har sannan tace “To kai ko ka xauna mana d’an nan” ya xauna smiling 

broadly, with respect yace “Ina yini” Kaka na washe baki tace “Lafiya lau, ya sunan naka?” Yace “Junaid Muhd…” 

Tace “Junaidu sai kaji kuma wai yarinya ta gurde koh? To ni kai na ban san yanda akayi wnn bala’i ya faru ba, amma 

dai na gode Allah tunda ba karyewa tayi ba….” Junaid yace “Allah ya kara kiyaye gaba” Kaka tace “Ameen kai dai…. 

Don ma uwarka na da fahimta na lura ita ta lallaba Amadu bai dau abun da xafi ba, kasan sa da xuciya, Kuma kasan 

shi ya tsinto makauniyar a titin kano tana galantoyi….” Junaid dai bai ce komai ba, kaka tace “To ka leka ta tana 

bacci can uwar daka ka duba ta, amma ta fiye son jiki yarinyar, d’an bugewa fa kafar yyi amma duk makota bbu 

wanda bai shigo gidan nan ba, ke Zainab kai sa ya ganta, kuma bance ki tsaya kusa da kumbo na ba, kinfi kowa min 

sace sace a gidan nan” kasa motsi Zainab tayi, shi dai junaid kansa na kasa, kaka ta ja tsaki ta mike tace “Haka nan 

suke min ban isa in sa su aiki ba, ae dai kaga taki kai ka, to ba ruwana ba biyesu nake ba, tunda ‘ya yana na min 

biyayya ae shkkn” har dakinta ta kai Junaid tace “To ka ganta….” Junaid na tafiya a hankali ya isa gefen gadon kaka 

yana kallon Heedayah dake bacci, kaka ta juya ta fita, durkusawa yyi yana kallon kafarta ya kai hannu kneel dinta, 

kwace kafar tayi tana turo baki alamar ta ji xafi, ta juya masa baya ta ci gaba da baccin ta, mikewa yyi walking 

gently ya koma dai dai fuskarta ya durkusa, bayan seconds kusan goma yace “Ina ke maki ciwo?” Bude fararen idon 

tayi a hankali kamar irin xata gansa din nan tayi shiru staring into space bata dai ce komai ba, lkci daya kuma ta 

mike xaune tace “Ina Abba” Bai ce mata komai ba, ya dau ledan da ya gani gefenta dauke da drugs yana dubawa, 

bude kofar dakin aka yi junaid ya juya, Sudais ne tsaye bakin kofar yana kallonsu, Junaid ya mike shi ma yana 

kallonsa, Sudais ya karasa ya basa hannu nan suka gaisa, sannan ya isa kusa da Heedayah yace “Me ya kai ki wajen 

wanke wanke har kika fadi?” Heedayah na kallon inda ta ji muryar tace “Ita ce ta kai ni wajen tace sai inyi wanke 

wanke” Sudais yace “To ina ke maki ciwo yanxu?” Kafarta na hagu ta nuna masa tace “But…” Yace “But what?” A 

hankali tace “Don’t touch it” kallonsu kawai Junaid yake yi, Sudais ya duka yana kallon kafar sosai yace “Ohkk…” 

Hannu ta kai tana laluba wajen don taga ta inda yake, ta ta6a kirjinsa, shi dai kallonta kawai yake, Bude 32 set of 

white teeth dinta tayi tace “Wannan sweet din naka ya kare ko?” Ya buda ido yace “Kina so ne?” Ta gyada masa kai 

tace “Um” yace “Ohk to bari in kawo maki” tace “Har da short bread??” Juyawa Junaid yyi ya fita daga dakin ya 

rufe kofar, Sudais ya kalli kofar sannan ya kalleta yace “Who is he?” Ta d’an yi shiru sannan tace “Shine ya bar ni a 

middle of road wai in wuce cikin gida da kai na bayan yasan bana gani, I don’t like him” da mamaki Sudais yace “A 

ina kenan?” Tace “A gidansu mana, kuma ina shan strawberry ya dauke min plate din, wai baya son in sha…” Tana 

fadin haka ta turo baki, Murmushi Sudais yyi ya mike yace “Toh bari in kawo maki sweet din in dawo” ta kara bude 

hakoranta tace “Toh” ya isa kofar ya bude ya fita, xaune ya tadda Junaid a parlor tare da kaka, kaka na nuna sa tace 

“To ka gansa, sai dai idan ban ajiye abu ba wllh, shi kuma wancan axxalumin ko magana baya wani yi, sae dai yyi ta 

kallon ka yana fama da mugun abu a xuciya, shureen naji suna kiransa ko wa, shi ma dai Aliyun ne, amma gaskiya 

xan gaya maka xuciyarsa bbu kyau yau na sake gaskata hakan daxu, to dai duk sunan Mai gidana ne da yayi hatsari 

ya rasu” ko kallonta Sudais bai yi ba ya nufi kofa xai fita, kaka tace “Kuma wannan da kake gani yan matansa sun 

kusa dozin har na gaji da xuwan da suke gaisheni, yau fara ta xo, gobe baka, jibi mummuna, kai gasu nan dai, ni dai 

na gaya ma daya a ciki yaudaran ta kawai yake, to ita ce ta goma xuwa gaisheni, to naga tana da hankali tana ta min 

aiki da goge goge” Sudais ya mata wani kallo ya fita ya kulle kofar. Junaid ya d’an yi murmushi yace “To ni xan 

koma…” Kaka tace “Da wuri haka har ina murna na samu abokin hira?” Yace “Xan dawo da daddare” tace “Ahh to 

shikenan, in ajiye maka abinci kenan?” Wani murmushin da ya bayyana dimples dinsa yyi yace “Toh sai na xo in sha 

Allah” tace “Toh Allah ya kawo ka, amma kaddai ka ki xuwa ka bar min abincina yyi kwantai” yace “A’a xan xo” 

mikewa yyi tace “Toh ka leka ko ta tashi yarinyar” yace “Toh” daga haka ya shiga dakin, xaune ya same Heedayah, 

ya karasa kusa da ita ya kai hannu ya dunguri forehead dinta yace “Kina ji ina maki magana kika min shiru daxu 

koh” turo baki tayi bata ce komai ba, yace “Sai na yanke wannan bakin” Tana jin haka ta 6ata fuska lkci daya ta fara 

Shesshekar kuka, xaro ido yyi ya xauna gefenta ya jawota jikinsa yace “Ke wasa nake maki fa” Cikin rawar murya 

tace “Toh shine xaka ce xaka cire min baki?” Yace “A’a baxan cire ba, sorry” tace “Toh ina Farida?” Yana kallon Eye 

balls dinta yace “Ta je Abuja” da sauri ta dago kai tace “Nan ne garinmu mu ma ai” Yana kallonta yace “Where in 

Abuja?” ta bude hannu alamar bata sani ba, sai kuma tace “Yaushe xata dawo?” Yace “Soon” saketa yyi ya mike 

yace “I’m going” tace “To ni baxan sake xuwa wajen Mami ba kuma, ni ina tsoron wannan matar” Junaid ya buda 

ido yace “Me yasa” ta marairaice tace “Tana ma kowa masifa, kuma tana aikana bana ganin hanya” Murmushi yyi 

sosai yace “Mami xata xo ta tafi da ke” Shiru tayi bata ce komai ba, yace “Anjima xan xo da daddare” ta gyada masa 

kai alamar to, sannan ya juya ya fita dakin. Da daddare Junaid ya xo gidan Baffa kamar yanda yyi ma kaka alkawari, Kaka na can uwar daka, Heedayah kuma na xaune parlon da plate din tuwo a gabanta, Da sauri kaka ta fito jin an 

bude kofa, ganin Junaid ta washe baki tace “Ka zo ashe Junaidu” gaisheta yyi ta amsa tana washe baki tace “Bari in 

gama gyaran gadon in fito duk ta yamutsa xanin gadon” daga haka ta juya ta koma ciki, Junaid ya ajiye ledan 

hannunsa ya koma inda Heedayah take tace “Me yasa ba ki cin abincin?” Kamar jira take ta fashe da kuka a hankali 

tace “Ni ban iya ci ba” xaro ido yyi yana kallon tuwo da assorted miyar veg din gabanta, yace “To me xa ki ci?” Tace 

“I want to take tea” ya kara wara ido, bude kofar parlon aka yi ya juya, wani dogon matashi ne just his mate ya shigo 

parlon, sanye yake da 3 qtr da polo, Shuraim ya karasa cikin parlon waving at him without much interest yyi xaman 

sa kan kujera, kaka ta leko don ganin waye, tana ganin Shuraim ta hade rai sosai tace “Dawowa kayi ka kashe mu 

lkcn mu bai yi ba ko ya aka yi??” Dauke idonsa yyi daga kallonta ya fiddo wayarsa ya maida dubansa kai, kaka tace 

“To idan ma mun mutu bayan ka tafi Junaidu na shaida, ehe” daga haka ta koma ciki, ba a dau wani lkci ba sai ga ta 

tafito tana washe baki tace “Sannu Junaidu bari in kawo maka abincin na ka” Junaid yayi murmushi yace “To ngd” a 

gabansa ta jera masa abincin, shi dai bai ce komai ba duk da a koshe yake, xata wuce ta gaban Shuraim kamar ana 

forcing dinsa yace “Ina yini” tayi kamar bata ji sa ba, sai ga ta ta dawo tace “Toh ka ci abincin mana Junaidu” Junaid 

na murmushi yace “Toh” sauka yyi ya bude warmer din ya ga shinkafa ce da lafiyayyen Miya da ya ji nama, sai ga 

wani bowl da aka yanyanka kayan ganye, kallon Heedayah yyi da plate din tuwon gabanta, sannan ya kalli kaka 

dake kokarin share bakin kofar ta, matsawa yyi kusa da Heedayah murya can kasa yace “Xa ki ci shinkafa?” Da 

sauri ta gyada masa kai, Ta gefen ido Shuraim ke kallonsu, Junaid ya dau plate ya diba shinkafar da Miya da nama, 

ya dauke tuwon da ta fara kacalcalawa ya ajiye mata shinkafar, a kan idon kaka da ta saki tsintsiyar hannunta ta 

mike da sauri tace “La la la kar ka bata, gantalalliya ce wai bata iya cin tuwo ba, to uwar me xa a bata, ko gidan 

Amadun da ya tsinto ta ma ai ana tuwo balle nan, mu ba wasu masu kudi bane da xata ce bata cin tuwo har da 

hawayenta, shinkafar kuma iya cikinka nayi nima tuwon na ci, idan aka ce xa a biyeta ai sai ta lalace Allah ya 

tambayemu….” Heedayah dai sai xare ido take kamar xata yi kuka ta dafe plate din shinkafar don kar ma a dauke, 

Junaid yace “Kaka ni na fi son tuwon ne shi yasa” Kaka ta saki baki tace “Allah?” Yana murmushi yace “Ehh” ta 

tabe baki tace “Toh Allah ya raba bawa da wahala don ko na wahala gun neman shinkafar nan da miya, to ai sai ka ci 

tuwon ita kuma sai ta karata da shinkafar duk da ni dai ban bata ba, kaji min yarinya dai da mugun hali” tuni 

Heedayah ta fara cin shinkafar, idan akwai abinda junaid ya fi tsana rayuwarsa tuwo, sai kallon tuwon yake yana 

tunanin ta wani side din xai fara ci, da cokali ya debi tuwon ya kai baki yana ci da kyar, mikewa Shuraim yyi ya 

maida wayarsa aljihu ya nufi kofa ya bi ta gefen kaka ya fita, kaka ta mike tace “Ka dai ga ko? Mugun hali har tsiro 

sai da yyi a jikinsa, tirrr Amadu dai bai yi sa’a ba ya haifi jaraban duniya kawai, to ba gwara min Sudess ba ni dai” 

sake bin kofar Junaid yyi da kallo don ya dai ga Shuraim na kama da Abba amma bai yi tunanin son dinsa bane. 

Hajiya Maryam ce xaune parlonta kai kace rasuwa aka yi mata, duk ta fita hayyacinta, idon nan nata duk a kumbure 

ga su Hajiya Sadiya, Hajiya kyauta, har da Hajiya Amina da dai kawayenta gaba daya sun kusa 7 sai Yan uwanta 

uku, Hajiya Zaliha tace “Ban da ma dodewar tunani da kwakwalwa ke har kya dau shawarar wannan tsohuwar da 

shekara da shekara kuna dauki ba dadi da ita, to duk gari kowa cewa yake ita ce ma karfin auren barristern, ita ta 

matso da auren ma aka yi da wuri wuri” Mumy ta fashe da matsanancin kukan takaici amma ta kasa cewa komai, 

Hajiya safara’u tace “Toh Kuma meyasa duk tsawon lkcn nan kika ki kunna waya fisabilillahi” cikin rawar murya 

Mumy tace “Ita ta sa in kashe wayar wai sai na basa wahala kafin ya gano inda nake da yara, kuma kusan kullum sai 

mun yi waya da ita, tayi ta shirga ni wai Ahmad na nan duk ya daga hankali ana ta nemana gari gari, har rahotu ya 

kai ma yan sanda, ko abincin kirki baya ci, da mun gama wayar kuma sai ta ce in kashe da sauri” Mutanen parlon 

suka kwashe da dariya ciki har da Hajiya Amina, Mumy ta hade rai tana bin su da kallo, Hajiya Sadiya na 

kyakyatawa tace “Ban ta6a ganin makiran tsohuwa irin matan nan ba, gaskiya ta sha ki da yawa, lkci daya ta rama 

duk abubuwan da kika dinga mata tana xaune gidan nan” Mumy ta mike tace “To bari ku ji wani abu, ba don ba ni 

da abinda xan iya yi bane kan tsinannen auren da barrister yyi ya sa nake kuka ko hankalina ya tashi, A’a kuka nake 

saboda takaicin da yarintata ba a min kishiya ba sai yanxu, kuka nake sbda boasting da na dinga yi cikin mutane 

Barrister baxai ta6a min kishiya ba, kuka nake sbda makircin da annamimiyar tsohuwar nan ta hada min, ita kuma 

wnn mata da tayi kuskuren auren mijina ina jiran shigowarta gidan nan, wllh sai ta gwammace bata ta6a sanin 

Barrister ba, ita kuma wnn yarinya da aka min kishiya ta dalilinta….” Wani murmushi Mumy tayi tace “Da farko 

xamanta gidan nan kirgagge ne, sannan kafin ta tafi sai na tabbatar da shaida xata bar gidan wanda har girmanta 

baxata manta ba, sannan a makantan ta xata tsaya har karshen rayuwarta, wllh wllh bana wani jin kishiyar da aka 

min kamar yanda nake jin yarinyar nan a rai na, ita ce sillar rugujewar duk wani farin ciki nawa….” Hajiya kyauta 

tace “Toh nan dai da kwana biyu xa su tare da uwar rikon tata, ke dai gashi kin samu an sauya maki komai na 

bangaren ki kamar ke ce amaryar, amma ni tunda nake ban taba ganin irin haka ba, anya ba aljana barrister ya kwaso 

ba me son ta tarwatsa maki gida, gashi ma tana kan yin haka tunda ta sa an rangada maki kishiya yar boko yar gayu” 

Mumy tace “Za mu ga wanda xai tarwatsa wani ni da ita, na fa ce maku ynxu ni ba ma da kishiyar xan goga ba….Baffa ne ya bude kofar parlon Kaka da sauri jin ihun da Heedayah ke yi ya shiga, shi ma shigowarsa gidan kenan 

daga masallaci an idar da isha, Kaka ce ta danneta sai shafa mata wani magani kamar rub take a kafan da ke ciwo, 

Baffa ya bude baki yace “Meye haka kuma Baaba?” Kaka dake ta hada xufa tace “Toh sai a biye mata tana dingishi 

baxa a san na yi ba, so ake ta dawo gurguwa ga makanta abun ya taru ya ma d’a na yawa? da wanne ake son ya ji, a 

hankali fa nake mata amma da yake munafuka ce algunguma dubi tonan asirin da take min kamar warce nake 

yankawa” Baffa yace “Don Allah ki kyaleta Baaba, ba tana shan magani ba, a hankali xai bar mata ciwon ai” a 

fusace Kaka tace “Maganin banxa maganin bature, ka san daga wani kasa aka kawo min wnn din da nake shafa mata, 

ku dinga kallona kamar ban san me nake yi ba, toh naki kyaletan sai ka kwace ta ai” Ita dai Heedayah bata fasa ihun 

da take tana kiran Abba ba, aka bude kofa Sudais ya shigo parlon da sauri shi ma daga masallacin yake, Bude baki 

yyi yana kallon kakar tasa, tace “Kai ka ji ubanka da wani magana Sudess, daga taimako fa xai min rashin kunya, ita 

kuma yar banxan magani fa nake shafa mata….” Sudais yace “Toh kaka ba ke kika sa ta wanke wanken ba, ai sai bari 

har lkcn da kafar yyi niyyar warkewa ya warke da kansa, ynxu hakan da kike mata idan kika sake ji mata wani 

ciwon fa?” Kaka ta tura Heedayah a fusace tace “Ni dai Allah ya isa wllh, ya xa a dinga cewa ni na sa ta wanke 

wanke, ga yarinya dai da bakinta ko bata da ido ai sai ku tambayeta ta fadi gaskiya mana, kawai kawai an mayar da 

ni karamar mutum a gidan nan sbda ana bani abinci a kwano…. Ban da xalunci me xai sa in sa makauniya wanke 

wanke idan ba ita ta bukaci yin hakan ba da kanta??” Juyawa Baffa yyi ya fita daga parlon, Sudais ya jira har ya rufe 

kofar sannan yana nunata yace “Ke dai kawai baki son gaskiya, ki yarda kawai kin kusa karya yar mutane kin sa ta 

wanke wanken da kika tara an kwana biyar….” Kaka ta fashe da matsanancin kuka tana jawo dankwalinta xata yi 

hankici da shi, Sudais ya daga Heedayah suka fita parlon ya kulle mata kofarta yana murmushi, Heedayah dake 

dingishi tashin hankali a fuskarta tace “Plss ka wuce da ni wajen Abba kar ka dawo da ni nan” kallonta yake bai ce 

komai ba har ya isa stairs, daukarta yyi ya wuce sama, dai dai xai ajiyeta sai ga Ummarsa ta fito daga part dinta, 

tsaye tayi tana kallonsa da mamaki fuskarta, yace “Sannu da gida Umma…” Bata amsa ba tace “Ka sameni a parlona 

yanxun nan” daga haka tayi wucewar ta, bangaren Aunty ya shiga yana rike da Heedayah, Aunty dake xaune saman 

darduma ta idar da sllh tace “Ta ya kaka ta yrda ka fito da ita, daxu da rana kiri kiri taki yarda in fita da ita, wai ba 

ruwanta yar amana…” Sudais yyi dariya yace “Ae tana can na barota tana kuka” Aunty tace “Kai dai baka gudun 

abun magana koh Aliyu?” Ya xaunar da Heedayah saman kujera yace “Danneta fa tayi tana ta ihu wai magani take 

shafa mata a kafar” Dariya Aunty tayi ya juya yace “Ina xuwa Umma na kirana…” Tace “Amma xaka dawo ai” yace 

“Ehh xan dawo” daga haka ya fita, Dawowar da bai yi ba kenan har sha biyun dare yyi, Heedayah har ta gaji da 

tambayar Aunty ko ya dawo, Aunty ta kai ta bathroom dinta tayi fitsari sannan ta kwantar da ita saman gadonta nan 

da nan bacci ya dauketa, yaranta kuma suna dakinsu dama… Aunty na kwance har ta fara bacci ta ji ana kwankwasa 

kofar bedroom dinta, ta mike ta kunna wutan dakin tana kallon agogo ta isa kofar ta bude, Baffa ta gani tsaye kafin 

ta ce komai yace “Yarinyar nan na nan ne?” Da mamaki Aunty tace “Tana nan har tayi….” Hango kaka da tayi tsaye 

bakin kofar parlor tayi kicin kicin da fuska ya sa tayi shiru, Baffa yace “to fito da ita” Aunty bata ce komai ba ta juya 

ta koma dakin, sai a sannan ta girgixa kai ta shiga tada Heedayah, tana rike da hannunta har sannan tana magagin 

bacci suka fito parlon, Kaka tace “A bani amana sbda ance maku ban san girman amana ba xa ku cuceni ku dauketa, 

to uban me xata maki a nan din banda gulma Hauwa? wllh Umaru kasa bacci nayi, gani nake kawai Allah na fushi 

da ni, idan Amadu ya ji wnn me ku ke son ya daukeni? To ba ruwana a maido min da abata….” Baffa dai bai ce 

komai ba, Kaka ta warce hannun Heedayah a na Aunty ta fice daga parlon Heedayah da har baccin ya fice a idonta 

jin muryar kaka ta dinga bin ta kamar xata yi kuka, Baffa ya girgixa kai yana kallon Aunty yace “Toh Allah ya 

kyauta” dariya tayi tace “Halan har ka fara bacci” yace “Nayi bacci mana dama” daga haka yyi mata sai da safe ya 

fita. Kaka na shiga bangarenta ta kulle kofar tace “Gantalallen yaro kawai in sake ganinsa a parlona idan ban ja 

Allah ya isa ba” furan da ta rage ma Heedayah ta dauko mata ta ajiye gabanta tace “Gashi nan baxan shanye ban 

baki ba kar Allah ya tambayeni, duk da mugun halin ki” Heedayah ta ta6a cup din a hankali ta kai baki ta fara shan 

furan kamar xata yi kuka. Washegari juma’ah da safe Mami ta xo tafiya da Heedayah, Kaka ta kwaso kayanta da ta 

wanke ta linke su fesss tace “Sai kin sa ido sosai kan yar nan, shegen son jiki ne da ita kamar mage, baxa a fake da 

makanta ba a cuceta….” Mami tace “Toh mama” Kaka tace “Toh har yanxu baki saka ranan tarewar bane ke kuma? 

Ba a fa wasa da igiyar aure” Mami tace “Yanxu haka can gidan xa mu wuce gaba daya” Kaka tace “Toh alhmdllh,

 kin dai ji duk nasihar da na maki ranan ai ko, yanxu haka matar na can ta dawo, bbu ke bbu ita” Mami tayi 

murmushi tace “In sha Allah” sai kusan sha daya suka bar part din Kaka tare da Heedayah….. Horn Mami tayi dai 

dai gate din gidan Barrister Ahmad, mai gadi ya bude gate din ta ja motar xuwa cikin gidan tayi Parking a space din 

yin hakan, Da taimakon ta Heedayah ta fito a motar, tana rike da hannunta suka nufi entrance din shiga main parlor, 

Shuraim ne xaune balcony din da system a gabansa, tun daga nisa da ya kallesu ya dauke kai ya ci gaba da abinda 

yake a laptop har suka iso balcony din, Mami bata kallesa ba tace “Take off ur shoes Heedayah” Heedayah ta fara 

cire takalmin kafarta, Mami ta ajiye su gefe, ita kam dama bata cire nata ba da shi ta shiga tana bude jakarta don 

fiddo wayarta dake ring, ta daga ta kai kunne, Hajiya Amina mahaifiyar Sudais ce parlon da Mumy sai Hajiya 

Sadiya da Hajiya kyauta, kallo daya Mami tayi masu ta cikin siririn glasses din idonta still holding Heedayah’s hand 

ta nufi bangarenta tana cewa “Ai court ma baxata bada bail dinsu ba, their case is different, baxai yiwu ba ma, so kar 

ku ji komai, pls hold on I will call you later” tana fadin haka ta katse wayar ta fiddo makullinta don bude bangarenta 

wanda aminiyarta da sister dinta suka xo tun jiya suka yi gyare gyaren da ya kamata, tana shiga ciki rike da 

Heedayah ta kulle kofar. a hankali Hajiya Sadiya tace “Tabdijam, lallai kina da aiki babba a gabanki Maryam, idan 

baki yi hankali ba wnn farar matar dai kwace maki gida ta shigo yi, ke kin ji wani kamshi da take xubawa kuwa, 

kalli fa ko kallon arxiki bata mana ba sai xancen kotu da bail take, da takalmi ma ta shigo parlon don rainin wayo…” 

Hajiya Maryam da taji kamar xuciyarta xai fashe don kishi bata dai ce komai ba nan ko naxari iri iri take yi a 

xuciyarta tana tunanin ta ina kenan xata fara….

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *