JIRWAYE CHAPTER 8

JIRWAYE CHAPTER 8

                Www.bankinhausanovels.com.ng 

And?”. Khalifa ya tambaya da yaji tayi shuru in banda jan majina da hawaye ba abunda take yi.+

“Kashe gari da safe, Yasmeenah ta bani kudi eighty thousand na tura gida dun Ummati ta samu ta rage crisis inda family dinmu ke ciki a lokacin. Koh da na tura mata kudin, rashin lafiyar Abba kadai ya cinye dubu hamsin a cikin kudin kan aka zo aka yi bailing din ya Suraj out of prison, da kyar suka anshi dubu ashirin. Sauran dubu goman kuma bazai isa registration din Auta ba, bazai isa Ummati ta kama hayan gida ba tunda ya Suraj ya sayar da gidanmu, ga rashin kudin kula da buqatun su,……”. Ta kuma tsayawa kan after some time ta cigaba.

“Dun haka, a few days after I sent the money to them, Yasmeenah tayi wani baqo wanda a lokacin babban ma’aikacin government ne. Zuwan baqon nan ne ya wayar mun da kai, har na san asalin sana’ar Yasmeenah. She’s a pimp, connecting ýan mata take yi da manyan mutane a biya ta kudi. Dun haka ranar baqon yazo a sama me budurwa kyakyawa that’ll entertain him for the weekend sai ya ganni…..”. Ta fadi murya na rawa.

“He offered me a hundred and fifty thousand naira, I was desperate, I needed the money and afterall there was nothing left of me, tunda I’ve already lost the one thing I’ve always been urged to safeguard, na zama baqar ashana. Out of desperation nayi taking offer din, ya biyani kudina na tura gida na biya wa iyayena buqatun su. And since from that day, sunana ya tashi daga Badejo to Laylah Jaan…… The heartthrob of the whole city, the heart desire of every man. Slowly nayi ta kashe wa ýan mata kasuwa dun duk wanda yazo sai yace shima sai ya dandani zumar Laylah Jaan. It became like a competition to the men, kowa na so ace shi ya fi biyana kudi masu yawa da yayi amfani da ni”.

Dogon numfashi khalifa ya ja, koh kallon ta ya kasa ya buda baki ya tambaye ta “And your parents? Kika ce musu kina samun kudi a ina?”.

“Karya nayi musu, nasan baza su taba jin dadi sanin diyar su ta zama karuwa, me siyar da jikinta dun samun biyan buqatun ta ba dun haka nace musu na sama aiki da wata hajia me kirki kuma ta sani a makaranta sannan zata dinga tura musu kudin da zai ishe su kula da kansu har na gama karatu na fara aiki. A haka na koma makaranta, da kudin karuwanci, nayi sponsoring Auta, da kudin karuwanci, na kai ya Suraj rehabilitation har ya gyaru ya koma karatu, da kudin karuwanci, na kai Abba na kashen waje da dama, da kudin karuwanci, Ummati tayi hajji da umrah, da kudin karuwanci. Da kudin karuwanci na ginawa iyayena gidan da duk Girei ba irin sa. Da kudin karuwanci na ba the people that mean the world to me all the happiness they deserve in the world”. Ta zube qasa tana kuka kamar ran ta zai fita.1

“I sacrificed my love, my body, my conscience just to make them happy. Na sabawa mahallici na just to keep them happy. Na rufe jikina da zuciya ta da Jirwaye just to place food on their table and happy smiles on their faces”. Ya so ya tambaye ta ya rabuwar su da Mahmoud ya kasance amma ganin irin kukan da take yi ya sa shi karaya.2

“You need some rest”. Abunda kawai ya iya fadi mata kenan kan ya bar dakin ya koma living room din suite din ya zauna shuru cikin utter darkness. He was just trying to digest all she told him, yana ta nazarin rayuwa, circumstances and how cruel some people can be and most of all, ba abunda ya mai zafi kamar yadda har da hannun ýar Uwar sa a cikin bacewar rayuwar Laylah.6

Khalifa ya dade a gun zaune shuru yana nazari iri iri, kwata kwata be yi tunanin haka meeting dinsu zai yi turning out ba. Yanzu her story has thrown his heart in confusion, be ma san me yike so ba kuma, ya kasa tunanin da kyau. Can towards subh ya leqa ya sama Laylah a kwance ta ci kuka har barci ya kwashe ta a qasa. Da har kamar zai daga ta ya maida kan gado sai kuma ya sanja mind dinsa kawai ya dau tuxedo dinsa da ya jefar kan gado the previous night ya nufi exit din Suite din. Without second thoughts ya fita daga Suite din. Yana isa lobby din ya anshi car key dinsa ya fi ce. Kwata kwata be damu da koh karfe nawa bane yayi ta driving recklessly a empty streets din Abuja.

STORY CONTINUES BELOW

Badejo kam on the other hand ba ita ta tashi ba sai minutes past 9 the next morning. Koh da ta dudduba bata ga alamar sa ba there and then she got the message. Without being told, ta riga ta san response dinsa.

‘No responsible guy would want to associate with a whore afterall’. Ta fadi a zuci kan ta daga wayarta tayi dialling number din Yasmeenah.

“Send the chauffer”. Ta fadiwa Yasmeenah. Koh gaisuwa bata tsaya sunyi ba ta katse wayar kan ta shiga bathroom to tend to her early morning business. Fitowar yayi daidai da lokacin da driver ya kirata cewar ya isa gaban Al-Haydar empire. Jacket dinta tazo dauka ta ga bundle na kudi, American dollars da ya ije mata. Hawaye masu dumi ne suka sauka daga fuskar ta kan ta dau jacket din ta wuce, leaving the money lying there. Wato shikenan Abdulmalik koh ta ce khalifa shima karuwa ya dauke ta, da har zai ije mata kudi. Toh bata son kudinsa, a da tayi kwadayin cin kudin khalifa Al-Haydar amma yanzu, sanin the real face behind the name has turned down her vibe. A hankula, cike da takama, with her head held up high ta fito daga suit din tana taku dai dai har ta isa parking lot din hotel din inda driver ke jiran ta.

Suna isa gida, bata tsaya ko ina ba sai dakin ta, ta tube kayan jikinta ta fada ban daki. Ta dade sosai a ciki ba abunda take yi in ba rusa kuka ba har sai da Yasmeenah ta yi knocking door din ta ji koh lafia taji ta shuru.

“I’ll be out in a sec”. Ta fadi kan ta miqe daga qasa inda ta zauna comfortably tana ta sharar kuka. For the second time, she has lost her key to happiness….. For the second time in life, she has lost true love all kudos to the path fate and circumstances lead her to.3

Wanka tayi kan ta fito ta izza Yasmeenah zaune bakin gado tana jiran fitowar ta.

“Wannan da kika dade a wanka haka, it seems khalifa Al-Haydar had a wonderful night”. Yasmeenah ta fadi with a hint of mischief in her tone.

“He sure did”. Laylah ta ansa ta fuska ba walwala. Daga nan ba wanda ya kuma cewa komi. Yasmeenah  tayi busying kanta da phone dinta while Laylah took her time to doll up. Mai kawai ta shafa, ta fesa body spray kan ta nufi closet ta nemi wani free gown ta sanya. Kusancin da ke tsakanin Yasmeenah da Laylah ya sa ta sensing something wrong amma kuma bata yi pressing issue dinba dun haka kawai ta fita ta nufi downstairs. Kitchen ta wuce direct ta fara mixing batter zata hadawa Laylah breakfast of one of her fave meals. Tana gama frying pancakes din tayi arranging dinsu neatly a plate kan ta dora a kan tray wanda ke dauke da mug na tea already, ta buda fridge ta dauko dressings for pancake din kan ta wuce dakin Laylah da abincin.

“Come eat”. Laylah ta so objecting amma Yasmeenah bata bata room for that ba “Come on, I made it with so much love”. Tayi convincing dinta. Koh da ta fara cin abinci, Yasmeenah na lura da yadda ta ke ta wasa da pancakes din kawai her mind far off in a trance.

“Something went wrong?”. Ta tambaya amma shuru “It’s okay if you don’t wanna talk about it, I’d just go to my room”. Ta miqe heading for the door.

“Abdulmalik is khalifa Al-Haydar……. Khalifa Al-Haydar is Abdulmalik”. Maganar ta ya sa Yasmeenah Mutuwar tsaye. Ta dade in shock kan ta juyo ta kuma tambayar Laylah, just for confirmation.

“Who is who?”.

“Abdulmalik, the guy I’m crazily in love with. Turns out the poor driver, the single father of one is none but the mysterious khalifa Al-Haydar. khalifa Al-Haydar inda nayi shekaru ina targeting”. Ta fadi kan ta kuma fashewa da wani kuka me ratsa zuci. Da gudu Yasmeenah ta qarasa kan gado ta riqo ta, ta sa kanta a shoulder dinta tana ta shafa mata gashi a hankula, in a soothing way. Sai da kukan ya ragu kan ta kwashe duk yadda suka yi tas ta fadiwa Yasmeenah.

“You think I did the right thing?”. Ta tambaya.

“Right now I’m so proud of you baby”. Yasmeenah ta fadi tana kissing hair dinta “And I’m very certain zai dawo, he loves you. Just give him some space, he needs time to digest all you told him, to clear off his mind. Kin ji, just cheer up. Mu zubawa sarautar subhanahu wata’alah ido”. Ranar dai haka Laylah ta wuni kuka Yasmeenah kuma nata faman bata haquri daga karshe dai tayi making up mind dinta to call the only person that can cheer Laylah up dun haka daukar wayar Laylah kawai ta yi ta fara dialling number din, ana dagawa ta sawa Laylah wayar a kunne ta fita ta basu waje.

Ýar uwa kenan, rabin jiki. Cikin few minutes Auta tayi abunda Yasmeenah ta wuni tana yi ta kasa. Kan kace mai Laylah nata dariya da fara’a, koh da suka gama wayar mood dinta yayi improving sosai. A haka dai kwanaki suka fara gushewa ba khalifa Al-Haydar ba labarin sa. shi be kira ba, be kuma neme ta ba.

Cikin ýan few days dinnan, life lost meaning to Laylah. Kullum bata da aikin da ya wuci zama cikin daki tayi ta tunani. Daga baya da ta gaji da zaman daki sai ta fara fita in the evenings zuwa park for long walks. Koh events planning business dinta bata wani kula da, komi ta bar wa Ameer PA dinta ya dinga kula da business din, sai dai ya kawo mata feedback.

Kamar wasa, aka yi two months Laylah bata ji daga khalifa Al-Haydar ba dun haka ta yi making up mind dinta to take the right step. Ranar da dare ta shiga dakin Yasmeenah dun suyi magana. A hankula ta tura kofar ta sama Yasmeenah zaune a armchair inda ke dakin tana karatu. Murmushi tayi mata kan ta qarasa ta zauna kusa da ita a dayan armchair din. Shuru shuru bata ce komi ba dun haka Yasmeenah ta cigaba da karatun ta.

“I’m leaving”. Maganar ta ya sa Yasmeenah sakin novel inda take karantawa ta dago tana kallon ta. “Hey! Not forever”. Ta fadi tana wata ýar dariya “For sometime, I want the world to forget about Laylah Jaan, just to clear off my mind and stay off the social circle for a while”.

“How long are are we talking about here?”.

“I don’t know; months, one year, 2 years, 5 years. I just don’t know. All I know is zan dawo”.

“Kema barina zakiyi Laylah, leek left and you’re leaving too. Duk duniya ban da irinku”. Kawai ta fashe da kuka.

“Hey, wallahi zan dawo. Kullum zan dinga kiranki, i’m not leaving the world, yola zan koma for a while. You can stop by anytime you miss me”. Ta fadi. Yasmeenah kawai jawo ta tayi jikinta tayi embracing dinta affectionately.

“I am proud of you Laylah”. Ta fadi mata. Koh da Laylah ta miqe zata koma dakin ta sai ta isa bakin kofa ta tsaya.

“Yasmeenah”.

“Na’am”.

“It’ll be good if you go home too you know, atleast su san kina raye”. Ta fadi kawai ta juya ta wuce. Kashe gari da sassafe suka tashi Yasmeenah ta mata rakiya zuwa airport. Sai da taga tashin jirgin su kan ta koma gida zuciyarta fal da tunani. Maganar da Laylah ta fadi mata the previous night ne kawai ke ta mata yawo a kai. Hakika ya kamata ta nemi gida. Tana isa gida dakin ta ta wuce directly ta buda wani drawer ta ciro wani dan envelop wanda yike dauke da details din family dinta da suka rage. About 3 years ago ta sa aka mata investigation amma tunda aka kawo rashin courage ya hanata buda envelop din. Koh da ta ciro envelop din, ta dade tana nazari on whether or not to open it kan tayi making up mind dinta to just open it. Tana budawa contact din farko ta fara dialling, contact din ýar Uwar ta Gumsu.

“Hello…”. Shuru Yasmeenah ta kasa magana.

“Hellooo….”. Aka qara fadi a background tana jin haniya kaman na yara suna argument.

“Yasmeen! Dan Allah kuyi shuru in ji magana”. Ta ji ta fadi kan ta kuma cewa hello amma shuru Yasmeenah ta kasa magana sai wasu hawaye masu sanyi da ke sauka kan kumatunta.

“Yasmeenah….. is that you? Ke ce?”. Ta tambaya amma kuma sai Yasmeenah ta yi saurin katse wayar. Gaba daya ma ta kashe wayar ta kwanta tana kuka. She has never felt so lonely and vulnerable in her life.

Tana isa yola ta kira number din Hamma Suraj wanda in no time ya isa airport daukan ta. Koh da be fito waje ya fadi ba, his expression said it all, he was highly surprised about his sister’s sudden visit kuma gashi yaga tazo da kaya masu yawa, alaman ba irin casual visits inda take yi bane ta gansu ta koma. Be ce mata komi ba, shuru suka zauna a mota once in a while suna dan taba hira. In ka ga Suraj kamar ba Suraj inda ke shaye shaye da fadace fadace ba few years ago, ya wanku, ya gyaru ya koma makaranta yayi starting afresh. Yanzu haka ya gama ya kama business kuma Alhamdulillah he’s making it. Yayi aure da diyar sa daya tal wanda aka mayar mata sunan Ummati, wato Rabi’atu. Ita kam Auta Hidayatu tana final year dinta a university inda take karanta dream course dinta, wato civil law.
Har suka isa gida bata sani ba, hankalinta na can yayi nisa cikin tunani. Sai da Hamma Suraj ya tabo ta kan ta fito daga motar. Masu aikin gidan ne guda biyu maza suka rugo da gudu dun kwasan kayan Laylah, sai gaidata suke a ladabce.  Ta dade tana kallon gidan tana yaba kyaun sa, sabon gida ne wanda baa dade da shigar sa ba dun koh 3 years iyayenta basu yi ba da tarewa a gidan wanda ke cikin garin jimeta, dun yanzu level ya sanja an rabu da zama kauyen Girei.
Dan kwalla da ya zubo tayi saurin sharewa kan ta fara taku a hankula towards main entrance na gidan. Ba komi ne ya sa ta kwalla ba illa tuna rayuwar su a baya da tayi. Hakika da 10 years ago zaa fadi mata cewa ita Badejo watarana zata mallaki irin dukiyar da take da a yanzu ba koh kadan bazata yarda ba. Kasashen duniya nawa taje? Manyan mutane nawa ta hadu da? Motoci masu tsada nawa gareta, gidaje, plots ga successful business empire da take da. Indeed Allah shine abun godewa. Yanzu in life, abu daya ya rage mata; to repent and move on in life.
Tana shiga ta izza Ummati da Abba zaune a living room din downstairs suna kallon news. Cike da murna ta qarasa inda suke ta fada Jikin Ummati sai hawaye kawai suka kufce mata. Ji tayi wani mugun so da kaunar iyayenta na da da shiga zucin ta.
“Laaa yau ina ganin shegantaka”. Fadin Ummati “Badejo yau kika fara zuwa gida ne, da zaki tasa mu gaba kina kuka”. Share hawayen ta tayi kan ta juyo ta zauna kusa da Abba tana fadi musu cewar tayi kewar su sosai.
“Kuma yanzu insha Allah na dawo yola, zan zauna nan da ku”.
“Ke haba”. Ummati ta fadi cike da murna, dama ta dade tana wa Badejo fadan zaman kanta da take yi a Abuja.
“Ehhh Ummati, ina so na buda branch na business dina nan yola sai na zauna kusa da ku koh”. Ta fadi. Ana cikin haka muryar Zubaidah matar Hamma Suraj ya katse su. Tana isa ta miqa 3 months old baby dinta ma Badejo kan ta zauna kusa da Ummati suka fara gaisawa. Ranar murna a gun kowa abun baa cewa komi, kowa yayi Na’am da decision din Badejo na dawo gida cikin ýan uwan ta.
Duk yadda Badejo tayi ta boye damuwar ta, ta gaza. Sai da mahaifiyar ta ta gane da abunda ke damun diyar ta ta dun haka ta taso ta gaba akan sai ta fadi mata matsalar ta.
“Allah Ummati ba komi bane, kawai ina missing Yasmeenah ne”. Tayi karya.
“Karya ne Badejo, ban yarda ba. Yau watan ki daya da dawowa gida amma duk na lura kina boye mana wani abu. Kina da damuwa amma kin kasa fitowa ki fadi mana”. Ummati ta fadi kan ta fara emotional blackmail irin  nasu na iyaye.
“Yanzu ban kai ki yi sharing matsalar ki da ni ba ko Badejo, ni Uwar da na dauke ki wata tara a cikina, ni zaki boye wa problem dinki……”.
“Ba haka bane Ummati, zan fadi muku komi. So nike sai randa family din is full, in Auta ta dawo duk sai mu zauna a tattauna”. Ta fadi mata.
STORY CONTINUES BELOW
“Toh shikenan, next week tana nan zuwa ai, Allah kaimu”. Badejo ta ansa da Ameen “Yawwa sai kuma zancen aure, mun jiki shuru, me ye nufinki ne? Kunya kike so ki bamu? Shekara 26 ba aure Badejo, mates dinki yanzu akwai masu yara ýan shekara goma amma ke gaki nan ba ma miji bare da”.
“Toh Ummati ai komi nufin Allah ne, lokacina ne be yi ba”. Ta fadi mata.
A kwana a tashi, har Laylah ta kai 2 months da dawowa yola and life was moving on quietly smoothly tho not very smooth dun har lokacin son khalifa Al-Haydar da ya mamayi zuciyar ta na nan na azabtar da ita, ta kasa mancewa dashi gashi shi kam tuni ma ta san ya mance da anyi irin ta. Murna a gun Laylah baa cewa komi randa Auta ta dawo gida hutun end of semester. Raba dare suka yi suna ta hirar yaushe rabo, dukan su kowa na cike dare a farin cikin ganin dan uwansa. Kashe gari da safe bayan an gama karin kumallo suka wuce dakin su suka shirya tsaf kan suka fito da niyyar hanging out together, just the 2 of them.
Hadaddiyar Toyota venza dinta wanda gift ne to her from the minister of information as birthday gift da tayi turning 26 suka shiga suka dau hanya. Basu tsaya ko ina ba sai kauyen Girei. Tunda suka shiga garin yara kananu ke bin motar da gudu suna shafa ta. Dariya me qara Laylah ta saki, tana dariya har da riqe ciki.
“Malam a lafia?”. Auta da ke tuqi ta tambaye ta.
“Auta kin tuna sanda muma muke bin mota in mun ga daya?”. Ta fadi duka su biyu suka fashe da dariya.
“Da wannan shegen mutunin da ya taba watsa mana tabo…..”. Auta bata gama magana ba dariya ta kufce mata.
“Muka fasa mai glass din bayan mota da dutse muka guda muka boye gidan malam Jauro”. Laylah ta fadi gami da sauke glass din gefen ta. Dama bata rasa ýan kananun change haka. Bundle din 50 naira fresh mints ta ciro daga pigeon hole din motar ta deba da dan yawa ta watsa waje. Nan yaran da ke bin su suka tsaya suna kwasan kudin, har wasu ýan samari da ke zaune a majalisa suna hira suma suka rugo a guje dun kwasan rabon su. Daga nan suka cigaba da tafiyar su shuru, ba abunda ke tashi a motar in ba waqar Beyoncé ba me suna 7/11. Auta na tuqi tana dan swaying jikinta to beats din waqar while Laylah was sorted quietly, obviously lost in a trance. Suna isa daidai wani tsohon masjid tayi saurin tsayar da Auta.
“Auta remember this place?”. Ta fadi suna saukowa daga mota.
“How can I forget, the place I met my first crush”. Tayi dan dariya kan ta fadi sunansa a hankula “Bawan Allah”.
Wani dan yaro da bazai wuce 12 years ba a shekaru suka hango riqe da donation box. Matsowa gunsa Laylah tayi ta mai magana.
“Me kake yi da box dinnan?”.
“Taimako nike nema dun gyaran masjid”. Ya fadi mata. Auta tawa rada a kunne, nan da nan Auta ta koma mota can ta dawo da dan jakar Laylah wanda kudade ne ciki nan ta ciro wrap na 500 naira ta miqa masa.
“Maza wuce ka kawai wa liman”. Ta umurci yaron su kuma suka juya zasu wuce.
“In je Ince musu in ji wa?”. Ya tambaye su.
“Baiwar Allah”.
“Baiwar Allah”. Suka kalli juna ita da Auta suka fashe da dariya kan suka riqo hannun juna. Suka cigaba da takawa da qafa.
“Auta Saniya”. Laylah ta fadi tana dariya kan ta tunkuda ýar uwarta ta ruga a guje kamar yadda suke yi  sanda suke yara. Ba tare da bata lokaci ba ita ma Auta ta ruga a guje tana bin Laylah. Gudu suke basu tsaya ba, mutane ana ta kallon su ana mamakin koh lafia ýan mata haddadu kamar su zasu kama gudu cikin unguwa. Basu tsaya koh ina ba sai da suka isa kwanar layin su, inda gidansu na da shine na biyu a layin. Kallon Auta tayi ita ma Auta ita take kallo kawai suka fashe da dariya. Ohhh gone are those days. Har cikin gidan suka shiga wanda yanzu ya zama kango, tsakani da Allah Laylah ta zube a qasa tana shan kuka. Ta ma rasa me ke sa ta kuka, tunowa da kuruciyar ta da tayi? Koh kuma rayuwar da ta fada? Koh kuma son khalifa da ke neman jefa ta cikin hadari.
Da taga kukan yayi yawa, a hankula ita ma ta durkusa qasa ga fara rarrashin ýar uwarta.
“Are you alright?”. Auta ta tambaya a hankula “Ina ta lura dake, there’s something that has been eating you up, yaushe muka fara boyewa juna abubuwa?”. Auta ta tambaya. Share hawayen fuskar ta tayi kan ta riqo hannun ýar uwarta zuwa kan wani dakali suka zauna. For about 15 minutes, shuru ba me cewa kowa komi. Sai da Laylah tayi taking time, tayi preparing kanta mentally for what she was about telling her sister.
“I am a call girl”. Ta fadi a hankula “or should I say I was”. Ta qara.
“Wh….a…aaa….at”. Auta ta fara in’ina. “Do you know what you’re saying, a call girl…… karuwa fa kenan”. Auta ta fadi a rude. Nan Laylah ta riqo hannun ýar uwarta kan ta fara bata labari just the way she narrated it to khalifa Al-Haydar. Ba abunda ta boyewa ýar uwarta. By the time she was done, Auta kuka har da majina.
“You went through all that? Alone…… For me…. For Hamma… For our parents. Bade….”. Bata gama ba ta fashe da kuka tana hugging ýar uwarta tightly. “Kin shiga duk wannan ordeals din for us. Kin bata rayuwar ki dun ki gina mana namu.,,, Ya Allah”. Kuka Auta tayi sosai ba kadan ba, irin kukan nan me sosa zuci. Ji tayi wani kaunar ýar uwarta na da da mamaye zuciyarta. A haqiqanin gaskia sacrifice inda Laylah tayi for them bata ganin zata iya yin sa but nevertheless she took the painstaking risk, just to put smiles on the faces of her loved ones. Ta shafawa kanta baqin paint just to support her family, indeed she’s a diamond in the rough, samun mutum irin ta, me irin zuciyarta sai an tona.
Sun dade a gun dun sai da suka yi kukan su ya ishe su kan suka miqe suka koma inda suka yi parking din mota. Wannan karon Laylah ce ta ansa driving din. Suna tafe Laylah na ba Auta labarin haduwar ta da Khalifa Al-Haydar. Auta kam sai mamaki take yi, wai yayar ta ce ta hadu da Khalifa Al-Haydar har soyayya ta shiga tsakaninsu. Khalifa Al-Haydar inda ya fi network fluctuating, yau bashi nan ba shi can, khalifa Al-Haydar inda kowa ke son sanin koh shi wanene. Bayan ta gama bata wanan labarin ta kuma fara fadi mata about plans inta for the future. A haka har suka isa wani qaton shopping mall wanda akwai eatery a ground floor, nan suka shiga siyan snacks. Kawai from nowhere suna tsaye jiran a kawo musu order dinsu Laylah taji an auko mata. Juyowar da zata yi ta ga ýar yarinya ce wadda bazata wuci shekaru 3 ba. Murmushi Laylah tayi kan ta zuquna ta fara yi wa yarinyar wasa dun ita mutum ce me tsananin son yara kananu. Yarinya kam ga kyau sai shegen wayo. Haka yasa nan da nan Laylah ta ji yarinyar ta shiga ran ta.
“What’s your name?”. Ta tambaya. Yarinyar ta buda baki zata yi magana kenan wani murya ya tsayar da ita.
“Kauthar ba nace ki daina gudu ba”. Laylah ta ji muryar kamar saukar aradu a kunnunwanta. Tabbas! ta san wannan muryar, yama zaa yi ta mance muryar. Ai koh daga barci aka tashe ta, zata iya identifying the owner of that voice.
You?”.+
“Mahmoud”. Ta fadi a hankula tana kallon ýar yarinyar wanda sai lokacin ta lura da shegen resemblance dinta to Mahmoud who was obviously her dad. Matsowa kusa da Laylah yayi ya qure ta da kallo, ita ma shi take kallo. Ba me cewa kowa komi. Ita kam dama Auta tuni ta wuce can game arena. A wannan halin wata mata me ciki tsoho ta qaraso inda suke, ýar yarinyar ta wadda daga gani bazata wuci 5 years ba na nan nane da jikinta.
“Mommy!”. Kauthar ta fadi tana tsalle.
“Ina kuka shige muna ta neman ku”. Matar ta tambaya.
“Zainaba?”. Laylah ta fadi. Zuciyar ta nata saqe saqe iri iri. Yanzu zainaba ce ta auri Mahmoud? Haka ne koh kuwa mere coincidence ne? Amma kuma ýar yarinyar ta kira ta mommy ai. Laylah cike da fara’a take masu magana. Shi Mahmoud shock, surprise duk dai gashi nan ya rasa me ma zai ce. Ita kam zainaba ansa gaisuwar take kamar bazata yi magana ba, fuska ba wani walwala.
“Toh ai sai ka taho mu tafi….. Sai anjima”. Zainaba ta fadi tana jawo hannun Mahmoud. “Laylah…. Kauthar be fast”. Ta fadi.
Murmushi kawai Laylah tayi a zuciyarta tana fadin Mahmoud ya cika alkwari, even though alkawarin was in suka yi aure first daughter dinsu will be named Laylah amma even though ba ita ya aura ba ya cika alkawarin. Wucewa ita ma tayi zuwa game arena inda Auta take tace mata su zo su wuce gida. Har suka isa gida Laylah tana can duniyar tunani, kawai tuno 6 years ago take, lokacin da Mahmoud ya buqaci suyi aure.
*”Me kike nufi? Baza ki iya aure na ba? Dun kina da samari masu kudi koh, masu bata ki da kudi koh?”*.
*”Mahmoud…… It’s not like that, you’ll never understand”*.
*”yeah cause I’m that daft! Kinyi asara wallahi, tunda har kika bari kwadayin abun duniya ya rufe miki ido and let me assure baza ki taba samu namiji wanda zai so ki tsakani da Allah kamar yadda na so ki ba Badejo. Wannan manyan mutanen sai dai su lalata miki rayuwa amma tunda ke yanzu kudi ke gaban ki, Allah ya bada saa, a cigaba da karuwanci lafia”*.
Duk da be san sana’ar ta ba, sai da ya kirata da karuwa. Yana ganin cewa rashin kudinsa ne a lokacin ya hanata auran sa, whereas koh kadan ba haka bane, tsoro….. The only thing that stopped her from going for what her hearted yearned for. Ta san dole ta fadi mai gaskia kan suyi aure dun bazata iya yaudarar sa, koh ta ma boye masa dole wataran sai gaskia ya fito. Gudun abunda zai wakana should a day like that arrive ya sa ta qi auran sa amma shi kuma ya ba abun wani fassara daban. Gashi dama tun lokacin da ta kuma dawowa gida sai kawai aka ce mata ya sama aikin lecturing da wata university can katsina state dan haka ya kwashe iyayen sa sun koma can, koh kadan bata ji labarin auran sa ba, kuma wai da aminiyarta zainaba.
Har suka isa gida ranar jikinta a mace, sai tunanin abunda ya faru kawai take da irin yadda zainaba ta dinga treating dinta, sai kace bata taba sanin ta ba. Hmmmm duniya kenan. Koh da ta dade da cire son Mahmoud a ran ta, sai da taji ran ta ya dan so su ganin wadda ya aura.
Shima Mahmoud koh da suka bar gun, ya kasa gane kansa. Ya kasa gane abun da yike faruwa a zuciyar sa, an old flame was surely rekindling. Haduwar sa da Laylah ya farfado masa da so da kaunar ta wanda a da ya dade da tunanin ya mutu. Dama auran sa da zainaba ba na so bane, far from that. Auran huce takaici ne. Tun suna yara zainaba ke matukar sonsa amma shikuma ba wadda zuciyar sa ke muradi kamar Laylah dun haka koh da ta qi auran sa sai ya komawa zainaba, koh dun abun yawa Laylah zafi ma. Gaba daya yayi zoning out of reality, deep down in his heart yana fatar haduwa da Laylah kuma.1
STORY CONTINUES BELOW
Koh da suka isa gida, su Laylah pretending suka yi like nothing happened suka fiddo da abubuwan da suka siyawa iyayen su as tsaraba, aka zauna aka dan taba hira tare kan can duka suka tashi suka wuce bedroom din Auta suka yaada zango. As usual, Laylah na kwanciya ta dauko waya ta fara dubawa koh ya ya kira. Without warning kawai taji Auta ta fisge wayar daga hannunta.
“Yaushe zaki daina haka? Can’t you see, he isn’t worth all the pain and hurt. Wata hudu kenan, da yana sonki kamar yadda yike fadi he would’ve shown up by now. Do me a favour and forget him please”. Auta ta fadi kamar zata yi kuka.
“Ya kike so nayi Auta”. Kawai ta fashe da kuka, abunda ya zama mata new hobby. “I love him and I can’t help that I do so alot. Just a text, one text. I’m not asking for much, koh da he’s calling us off be kamata ya bani silent treatment ba,  ya fito fili ya fadi mun”.
“Kinji ki, kamar wata yarinya karama. Just forget him and move on, shima it’s so obvious he has moved on. Dama masu kudi haka suke, da wulakanci ake haifar su a jinin su. You shouldn’t expect too much from a man of such status”. Auta ta fadi tana hugging din sister din ta. Sai da ta gama rarrashin Laylah tayi convincing dinta akan ta mance da Khalifa Al-Haydar tayi moving on tukun ta rabu da ita. And on that very day, kan Laylah ta kwanta barci sai da ta goge contact dinsa da duk wani hoto nasu da wayarta. Time to move on and focus more towards building a more better future.
The next day da safe, Laylah ta tashi da wuri ta shirya ta wuce wani Islamic foundation kusa dasu tayi enrolling kanta into a weekly Islamic counselling session. Daga nan ta wuce wani book club tayi enrolling kanta to pass time. On her way back ta tsaya a fave eatery dinta in town ta siya snacks, tana komawa cikin mota suka yi video call da Ameer PA, yana mata bayanin wani events da zasu yi planning very soon.
“Ma, the project is a mega one, event din babba ne”.
“Haka ne?”.
“Yeah! It’s worth over a 20 million”.
“Sounds lucrative, wana me kudi ne haka?”. Ta tambaya.
“Khalifa Al-Haydar…… In preparation for his upcoming wedding”. Ya fadi mata.1
“Kh…kha…lifaaah Al-Haydar is getting married?”. Ta fadi cike da mamaki.
“Yes ma’am, it has been kept confidential. Har yanzu press basu sani ba, muma kinga din ana so a bamu contract din organising wedding dinne”.
“A….Aa…. meer i’ll get back to you”. Ta fadi ta kashe wayar cikin hanzari. Kai ta daura akan steering wheel ta fara kuka. Lallaima khalifa Al-Haydar, this explains the reason for the silent treatment. Dama it’s that easy for one to fall in and out of love? Da har khalifa ya mance ta cikin wata hudu har ya sama wata yana shirin aure da ita. Sai da ta ci kukan ta ta qoshi ta goge face dinta zata starting mota sai ga call din Yasmeenah. Sai da tayi ýar murmushi kan ta ansa, she was thinking of her tace sai ta kai gida zata kira.
“Seriously? I think our spirits are connected, was just thinking of you”.
“Awwwwnnnn my baby boo. Ba kin je yola kin mance ni ba”.
“Ni na isa Yas-yas dina guda”.
“Ba wani nan, that trick won’t work on me. So tell me, ya kike?”. Ta tambaya. Suka dan fara taba hira. Har Laylah zata fara magana sai Yasmeenah tayi beating dinta to it dun haka ta bada attention to what she was trying to tell her.
“I think it’s time to pay Borno a visit”. Yasmeenah ta fadi reluctantly.
“Really!”. Laylah ta fadi cikin ihu “Tell me I’m not dreaming, pinch me someone, you’re going home….. finally”.
“Thanks to you, you gave me the little push I needed. Your presence in my life has been nothing but a blessing Laylah”. Ta fadi, muryar ta kamar zata yi kuka, ita kam Laylah dama ta riga ta fara dan zubda hawaye.
“That’s sweet. I love you Yasmeenah”.
“I love you more baby”. Ta fadi kan suka sanja topic kuma. “So tell me, has he called?”.
“Nah nah, heard he’s getting married”.
“Forreal! Amma ba labari”.
“Ummm the press still haven’t gotten hold of the news. I was offered the contract to plan the events”.
“And? You took the offer?”.
“Still thinking about it”.
“Lay….”.
“It’s okay, I’m good. We we’re never meant to be. Zanyi project din, dama i need the finance. Ba na fadi miki plans dina ba. I want to start up a charity foundation”. Sun dade suna hira kan suka bidding each other bye Laylah ta ja mota zuwa wani dan amusement park.
*”Na tsani naga mutane na kuka, barin ma ýar budurwa kyakyawa”*.
Ta tuno first one on one convo dinta dashi kawai sai ji tayi lips din ta na curving into a smile. Things just the mere thought of her good memories with him does to her.
Ta dade tana zaune shuru, tayi game a wayarta ta gaji kan ta kashe wayar ta zauna lost in thought. Kawai from nowhere taji kamar mutum ya zauna a seat inda take zaune.
“Abdulmalik?”. Ta fadi gami da juyo kai.
“Sunan sabon saurayin naki kenan”. Mahmoud ya fadi fuska a hade.
“Ohhh it’s you”. Ta fadi a hankula kan ta dan matsa zuwa extreme end din chair din.
“Ki ce levels ya sanja, baa zama kusa da talakawa”. Ya fadi yana ýar dariya. “Ina saurayin naki? Minister of what? Koh senator ne? Or a governor’s son. Oh my God! Don’t tell me controller din custom ne, koh MD din NNPC”. Ya fadi cike da tsokana.
“Mahmoud please”. Ta fadi murya na rawa, she was trying hard to resist herself from crying. Be san halin da take ciki ba yazo ya kama zolayar ta.
“Kwadayi dai mabudin wahala, gwara mutum ya gane”. Ya miqe ya wuce ba tare da ya juyo ya Kalle ta ba. A hankali hawayen da take ta resisting so hard not to spill ya fara zuba. Kuka ta fara mara sauti. Kalmomin Mahmoud sun mata zafi sosai gashi even in that situation she was still reminiscing about khalifa, how he would always wipe away her tears, how he would always tell her how he hates to see her in tears, how he told her that all her sorrow and miseries are his too…. ashe ashe, duk a baki ne. Miqewa tayi jiki ba qarfi ta yi hanyar motar ta ta hau tuqi zuwa gida.3
Tana isa gida, sai da ta tsaya a garden ta wanke tear stricken face dinta, ta dan yi dabbing powder yadda Ummati bazata gane ta yi kuka ba, abunda da mutum me dan haske, komi ya sai an dan gane alamar kuka a face dinta. Tana shiga gida ta izza Ummati da kanwar ta wadda ta kawo musu ziyara zaune a sitting room suna kallo. Gaida su tayi kan ta wuce zuwa bedroom din Abba. Gaida sa shima tayi kan ta sama wuri ta zauna kusa da shi a kan gado. Can ta kwanta da kanta a kirjinsa suka cigaba da kallon news ba me cewa kowa komi.
*News headline; Alleged future Mrs Al-Haydar sighted today at the Jabi lake mall having a good time with her soon to be son Fadeel Al-Haydar*2
Ji tayi zuciyar ta tayi wani irin bugu at the mention of *future Mrs Al-Haydar*. Yanzu da gaske Abdulmalik dinta aure zai yi, ya mance da ita. ji tayi kamar ta saki ihu dun takaici amma dole tayi controlling controlling kanta.
*The dashing model, Saima Mohammed sighted today together with son of multimillionaire khalifa Al-Haydar at the Jabi lake mall having the time of their lives. The 30 year old model who is allegedly the fiancée of the young millionaire is sure trying to adapt to……….*.
Ba tsaya ta gama jin news dinba kawai ta miqe tayi hanyar kofar. Abba cike da mamakin sudden change in behaviour dinta amma be ce mata komi ba ya cigaba da kallon news dinsa. Da gudu ta ruga zuwa staircase ta fara hawa da sauri, bata lura ba tayi bumping into sister in law inta. Cike da mamaki Zubaidah ke tambayan ta if all is well amma Laylah bata ma tsaya bata answer ba ta ruga zuwa bedroom dinta ta shige ta rufo qofa.Wata ranar Saturday,  ta shirya da niyyar zuwa Islamic foundation inda tayi enrolling kanta. Dama bata taba zuwa ba. Tsaf ta gama shiri at around 10 am, ta sa wata black abaya, veil din kanta shima black. From head to toe dai black ta sa kan ta dau suspender dinta da dark shades ta wuce. Mota ta shiga masu aiki nata gaisuwa. Tana fita gate din mansion dinsu bata tsaya ko ina ba sai Al-Ikhlaas Islamic foundation. Sai da ta ja dogon numfashi kan ta shiga ta izza about 7 women already waiting for counsellor din ta shigo. Cikin matan da ta izza kam har da zainaba zaune da qaton cikin ta kamar kwarya.+
Cike da fara’a ta matsa kusa tana miqawa ko waccen su hannu ana gaisawa suna welcoming dinta to counselling sessions din amma da ta miqawa zainaba hannu sai tayi kamar bata ganta ba dun haka ta gaidata amma shuru kamar ba da ita ba. Hakan ya sa Laylah kiran sunanta dun ta san da ita ake.
“Zainaba ina kwana”.
“Uhmmm”. Kawai ta ce abun ya daure wa Laylah kai. Rana daya ta sanja mata. Koh hushi take cewa bata neme ta ba bayan sun rabu. Anyways ta kawar da wannan tunanin ta sama wuri ta zauna. Haka mata suka ta zuwa. All in all su 15 ne a class din sai counsellor dinsu, making them 15. Tana isowa kam aka fara tattaunawa akan topic dinsu na ranar which was; *Betrayal* wato *Cin amana*. Kowa cikinsu na kawo experience dinsa.
“Malama ke fa?”. Aka tambaya Laylah koh ta taba experiencing betrayal. Immediately mind dinta yayi flying to khalifa Al-Haydar amma kuma what was the use of her narrating the story to them kuma koh ta basu labari karyata ta zaa yi dun khalifa Al-Haydar ba karamin mutum bane dun haka ta gyada kanta alamar aah.
“Nikam I just remembered wani mugun cin amana da na taba witnessing”. Koh bata juya ba, ta san muryar wanda ke magana.
“About 10 years ago, lokacin ina kauye mahaifin mu ya mutu. Saboda wahala da rayuwa ya mana, aka tura ni Abuja aikin gidan wata mata. Da naje na fara aiki sha tara na arziki ana mun a gidan, har makaranta suka maida ni. Saboda tsananin karamci na roqa aka dau qawata aiki a gidan amma tsananin butulci irin na dan Adam, tazo ta ci amananmu; ni wadda na kawo ta da auntie wadda ta riqe mu tamkar kannen ta”. Ta dan tsaya tana duba fuskar Laylah for an expression amma sai taga face dinta was expressionless, there was neither happiness nor grief written on it. Koh alamar tension babu fuskar ta sai ma wata ýar murmushi da take yi.
“Toh ita kam wannan qawa ta ki me tayi ne”.
“Wataran auntie ta fita ta dawo ta kamata a gado da mijinta. Tayi seducing dinsa to bed saboda abun duniya”. Ta cigaba da basu labari wanda duk karya ne ya fi yawa a ciki su kam mata sai tir suke da halin wannan yarinyar without them knowing koh wacece, basu san cewa tana zaune cikinsu ba.
“Amma wannan yarinyar Allah ya tsine mata”.
“Matsiyaciya ce”. Fadin wata.
“Dama shi talaka be iya cin arziki ba”.
“Shegiya karuwa! ýar wuta kawai”. Kowa ya dinga tofa albarkacin bakin sa. Kwalla fal suka cika idanun Laylah jin yadda kowa ke ta debe mata albarka bayan ba haka labarin yike ba.
“Aikam cikin dare auntie ta watsar mata da kaya waje”.
“Ai haka yafi”.
“Taje a cigaba da yawon iskanci a titi”.
Zainaba kuma ta cigaba da basu labarin da over 80% of it karya ne a ciki “Aikam a daren ranar mijin auntie ya sabule, ya fita neman ta kamar zai yi hauka, da yike ta riga ta rufe mai ido da asiri. Haka abun ya ta kawo musu matsala. Har dai daga baya aka fara suspecting ya ije ita yarinyar can wani gu ne as his mistress. A karshe dai in taqaita muku tun randa auntie ta kori yarinyar tashin hankali ya shigo gidanta har ya kai ga mutuwar igiyar auran ta daya”. Ta fadi. Nan ma matan suka tsine wa Laylah, a cewar ta kashe wa wata aure.
STORY CONTINUES BELOW
“Ya isa! Ya isa haka!”. Ta fadi cikin tsawa. “Amma kun bani kunya, har da ke”. Tayi nuni da counsellor din “Da ke”. Ta nuna zainaba.
“Ba kawarki ce ba. kin damu da jin asalin abunda ya faru? Kin damu da bin baya ki san Inda taje? Wani irin rayuwa ta shiga? Ashe yatsar mutum na ruba ya cire ya zubda? Kun bani kunya. Kuma da aka ce miki mijin ya ije ta can wani wuri kin je kin ga hakan da idanun ki? Da har zaki zo kina ya da labarin gaibu. Baki san asalin labari ba, Amma kun zo kun zauna sai faman zage zage kuke. Ashe ciwon ýa mace ba na ýa mace bane? Koh kaddara ne baku yarda dashi ba? Koh kuma jarabawar subhanahu wata’alah. Kuna abu kamar ba masu Ilimi ba. In mutum ya aikata mara kyau a ina aka ce a tsine masa? Addu’ar shirya ya kamata ku na mata. Gaskia in haka wannan foundation din yike ban ga amfanin zamana ba, ba zan zauna in da ake gulma da cin amana ba”. Ta fadi tana kallon zainaba wadda ita ma ita take kallo, jiki a sanyayyaye.
Without much hesitation, tana gama fadin duk abunda zata fadi ta dau jakarta tayi hanyar exit ta wuce ta barsu duk jiki a mace. Wani abun takaici koh da ta isa sai ta samu tyre dinta daya flat. Tsaki kawai ta ja ta fara neman number din mechanic inda Hamma Suraj ya hada ta da. Tana tsaye Jikin motar neman mechanic din ne shikuma Mahmoud ya iso daukar matar sa.
“Wa zan gani haka kamar matar manya”. Har ya dan wuce ya dawo. Dago kai kawai tayi ta kallesa bata ce mai komi ba. Da taga bayi da niyyar wucewa sai ta fara neman adaidaita sahu amma wani abun takaici duk wanda ta tsayar koh akwai mutane a ciki koh bazai bi hanyar da zata ba.
“There’s about 15 more minutes to the end of the session, ki shiga na sauke ki”. Ya fadi.
“Aah yaya Mahmoud na gode”.
“Senator ya hanaki harka da ya ku bayi kenan”. Ya fadi yayi ýar dariya.
“Aah ba haka bane”.
“Toh shiga muje”. Bata kuma cewa komi ba tayi hanyar motar ta shiga. A daidai lokacin zainaba na fitowa ta hango faruwar haka, ji tayi zuciyar ta ta fara wani irin tafarfasa. Tana ta cije cije. Su kam shuru suka kama hanya zuwa gidansu Laylah, ba me cewa kowa komi har sai da aka kusa isa gidan.
“Kin bani kunya”. Ya fadi a hankali. Dago kai tayi tana kallonsa bata ce mai komi ba.
“Duk abunda na zama a rayuwa saboda ke ne, I strived hard dun naga na gina mana rayuwa me kyau amma ke kuma fa? Kika bar kwadayi ya rufe miki ido, daga zuwa aiki kika shiga kwana da mijin Baiwar Allah, kin kyauta kenan? baki tsaya a nan ba aka kore ki amma still you went ahead to be his mistress, kika kashe ma wata aure saboda selfish interest dinki”. Tun da ya fara magana Laylah ke kallonsa bata ce komi ba, kukan ma ta kasa.
“Yanzu kam na san ya miki karami, sai senators da ministers. Wa ke kan layi ne? I won’t surprised in aka ce mun Aliko Dangote ne ma, dun kalar ki ma yanzu be yi kama da na low income earner ba”. Ya fashe da ýar dariya “koh khalifa Al-Haydar ne?”. Ya kuma tambaya “Shegu nawa aka yi flushing? Ehhhh matar manya, Allah ya shirya ki, ya ganar da ke. Ni daga nan ma dole naje car wash koh dun Jirwayen da ke neman dabaibaye mun mota”. Runtse idanunta tayi tightly tama rasa me zata ce mai.1
“Allah nagode maka”. Ta fadi cikin wata murya me sanyi “Na gode maka da ka kubtar dani daga fadawa hannun miji jahili, kayi karatu Mahmoud amma da kai da jahili wanda be taba shiga aji ba baku da bambamci. Allah jikan headmaster, gwara da Allah ya dauki ransa da yaga ranar irin ta haka, akan yaga yadda yayi wasting kudinsa a iska. Anyi Ilimi amma har yanzu ana zama cikin duhu. No wonder ka auri jahili irin ka, gashi nan naga bata da aiki sai zuba ýaýa suma a shafa masu cutar jahilci, what I’m I even saying tun a ciki abun ke shigar su”.
“Ke!”.
“Dallah rufe mun baki!”. Ta fadi da karfi.
“Da ka fadi abunda ke ranka waya hana ka? Saurare ni kaji me zance. Koh na rana daya ka tambaya how life was? Ka tambaya koh labarin da matar ka ta fadi maka haka yi ke koh ba haka ba? Ka taba gani na da wani? Da zaka ta watsa mun magana yadda kake so. Ehhh naji nayi karuwancin kuma ya kawo mun kudi, kai da matar ka da kuka sa kinibibi a gaba me ya kawo muku? In kudi kake so ka saukar da kai ka tambaya, in ma aiki ne kayi ladabi in nemo maka, stop barking like a mad dog. No wonder bature yace empty barrels makes the loudest noise. I’m not surprised dun indai gulma da hassada ne a jinin talaka yike. Kuma na gaba yayi gaba wallahi”. Ta zuba dark shades dinta a ido kan ta fita daga motar ta mai banging door dinsa ta shiga cikin gida.2
Da gudu ta ruga ciki, koh tsayawa gaida iyayenta bata yi ba ta wuce cikin hawaye. Dakin ta ta nufa ta rufo qofa ta zube a qasa ba abunda take yi sai aikin kuka. Ummati ce ta biyo ta daki cikin damuwa amma sai taji kofar a rufe, tayi kira tayi kira shuru kawai sai tace Allah ya shirya ta koma qasa inda take zaune da ýar uwarta wadda har yanzu bata koma ba.
Har yamma Laylah ta qi fita daga dakin ta abun tun baya damun su har ya fara damunsu. Ummati tayi knocking dun duniya shuru. Ita ma Auta ta dawo kiyi ta fama shuru. Har sai bayan isha da Hamma Suraj ya leqo gidan duba su aka fadi mai abunda ake ciki nan yaje bakin qofar yana ta faman kiran sunanta amma shima ta qi kula sa kuma ga shesshekar kukan ta suna ji.
“Tun safe bata ci komi ba”. Ummati ta fadi with worry laced all over her voice and expression.
“Ina spare keys din gidan suke”. Ya tambaya.
“Toh ai ta sa sakata daga ciki”. Nan Hamma Suraj ya fi ce ya wuce can saman layi su inda akwai wasu carpenters, cikin saa ya samu basu tashi ba. Dama yana mutunci sosai da su ya masu sallama ya roqa suka zo aka balla qofar. Suna shiga suka izza ta qasa a kwance tayi kuka har ta gaji hawayen basu fita kuma sai ijiyar zuciya da take ta saukewa. Nan Hamma Suraj ya cafki hannunta yata jan ta, down the stairs straight to his car. Ummati na ta famar kiransa amma koh kula ta be yi ba. Ga kan laylahn koh Kallabi babu bare wani abu wai shi takalmi. Tura ta mota yayi sannan ya dakawa me gadi tsawa cewar ya buda qofar. Kwanciya tayi cikin motar shuru, dama gidan baya ya sa ta. Da gudu ya dinga tuqi zuwa gidansa da ba wani nisa dun unguwa daya suke, layi ne kawai ya raba su. Zubaidah tayi matukar ganinsa ya shigo cikin gida da Laylah dauke a kafadar sa, dun a lokacin da suka isa gidan nasa ta riga da ta fara barci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *