KASHE FITILA CHAPTER 4 BY BATUUL MAMMAN

 KASHE FITILA CHAPTER 4 BY BATUUL MAMMAN

                Www.bankinhausanovels.com.ng 

Laminde ta sake cewa “ruwan asiri”

Gimbi ji tayi kamar an sauke guduma a cikinta ganin Laminde zata tona mata asiri.

A daidai lokacin Mama ta shigo kuma ta ji abin da Laminde ta fada. Kawu ne ya kara matsawa bakin gadon zaiyi mata tambaya sai daya daga cikin ‘yan sandan ya dakatar dashi.+

Da sauri Gimbi ta kirkiro kuka harda hawaye. Ita kanta mamakin saurin zubar hawayen nata tayi. Kan Laminde ta fada tana rusa kuka

“Abban Haris kaji wata masifa, Laminde ba dai tabin hankali kika samu ba”

Nafi’u ya matso da sauri yana tambayarta ko ta gane shi. Gimbi ta samu yana tayata kukan duk ta cika dakin da karaji.

“Yallabai ku nemo mutumin nan da ya kadeta. Wallahi bazamu yarda ba idan ta haukace”

Tsawa Awaisu ya daka mata ganin itama ta zama kamar mahaukaciyar

“Meye yake damunki ne, dubi tana son yin magana kin hanata”

Ko motsi batayi ba domin tasan muddin Laminde ta fadi abin da ta gani kowa yarda zaiyi. Musamman Awaisu da ta kula yanzu kamar ma ya tsaneta da Mama da take saka mata ido.

‘Yan sandan suka ce kowa ya fita zasuyi mata tambayoyi. Gimbi ta wani kankame Laminde

“Babu inda zani sai na tabbatar da lafiyarta. Laminde amana ce garemu. Ni satar da na kamata zatayi min na yafe. Ki yafe min, duk laifina ne da na kasa hakuri ban saurari dalilin da yasa kika shigarwa Abban Haris daki ba”

Maganar ta doki kunnen Laminde cikin kaduwa, _sata!_. Yanzu sharrin sata Gimbi ta kala mata. Hawaye ta soma yi tana kallon danta wanda aka zubar mata da mutumci a gabansa.

Sake bude baki tayi zata fadi gaskiyar abin da ta gani Gimbi kawai ta mike tsaye tana dafe kai

“Wayyo kaina, washhhh”

Sai gata ta fadi a kasa gaban Kawu. Duk abin Awaisu da gudu ya fita neman likita. Mama wadda tun shigowarta bata ce komai ba sai lokacin tayi wani murmushi mai ciwo. Iyakar abin da Gimbi tayi a gabanta yanzu ya tabbatar mata da gaskiyar Laminde. Fita tayi jiki a sanyaye tana bakincikin wannan al’amari. Tana shiga mota ta sanar da dreban inda zai kaita.

*****

Da gaske Gimbi taki farfadowa har kusan rabin awa. Likitan ya rasa gane mene ne yake damunta. Da ya auna jininta ya ga ya hau. Awaisu yayi wa bayanin cewa a kula da ita domin ciwon Laminde ya tsaya mata sosai. ‘Yan sanda suka gama bincikensu suka tafi. Iya abin da Laminde ta fada bai wuce cewa ba sata tayi ba kuma bata shiga dakin maigidan ba.

Bayan fitarsu Kawu ya tilasta mata ta fada masa gaskiyar me ya faru. Tana fada tana kuka tace dole zata sanarwa Mama.

“Laminde mutanen nan ba sa’aninmu bane. Wannan matar idan har gaskiya kike fada tafi karfinmu ta ko ina saboda haka ki bar maganar nan”

Kokarin zama tayi Nafi’u ya tayar da ita sosai “iyalin mutumin nan musamman mahaifiyarsa suna cikin hatsari. Da ace kana ganin irin yadda uwar mijin take rayuwa a gidan bazaka ce nayi shiru ba. Ba sharrin sata ba ko me zata yi min sai na fadawa ‘yan sandan nan gaskiya”

Kafin Kawu ya bata amsa yace Nafi’u ya basu wuri. Ya kama kofar zai fita Gimbi ta shigo fuska cike da hawaye.

“Laminde ki rufa min asiri. Abubuwan da kika gani sharrin shaidan ne. Kada ki tona min asiri ki raba sunnar Annabi SAW. “

“Kinga Hajiya daga nan garinmu zamu wuce da ita. Ina rokonki da kiyi hakuri ki janye satar da kika dora mata. Daga yau kin dena ganinta ma”

Farinciki ne ya bayyana a fuskar Gimbi har ta kasa boyewa Kawu. Kudi ta debo a jakarta ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu.

STORY CONTINUES BELOW

“Bama neman komai daga gareki. Kina iya tafiya amma kada ki taba mantawa rana dubu ta barawo….”

Dan dakatawa tayi tana auna maganarsa sai kuma tayi saurin  fita saboda Awaisu yana wurin likita ta fito daga dakin da aka bata. Laminde ta kalli Kawu zata yi magana yace ta bar komai a hannunsa. Irinsu Gimbi baka musu fito na fito lokaci guda, musamman idan baka da shaida. Zaiyi iya kokarinsa wurin taya Awaisu da mahaifiyarsa da addu’ar neman tsari.

*****

Naman kaza take ci tana kurbar juice a kofin glass taji an banko kofar dakinta. Duk gidan hatta Shuhada da take iya yi mata rashin kunya wasu lokutan bata isa tayi mata haka ba. Shiyasa tana jin karar kofar ta zabura ta tashi. Kusan karo suka yi da Mama kafin taji saukar mari zazzafa a kuncinta.

“Bebi sai Allah Yayi mana shari’a ni da ke. Me nayi miki haka kika lalata rayuwar ‘yata”

Duk da radadin da kumatunta yake yi bai hanata dariyar keta ba.

“Su Aminatu salihan bayi. To ai kinsan ba’a daya a dangi. Wannan Gimbiyar taki kina ganinta haka ba karamar fitinanniya bace.”

Mama ta kara harzuka “kada kiyi tunanin zan bar maganar nan haka. Naji komai daga wurin Laminde. Nasan kece kika kaita wurin shaidanun bokayenki.”

“Kin kuskuro ‘yar uwa. Wannan karon Gimbiya gaban kanta tayi. Shawara ta daya gareki shine ki nemi Awaisu ya mayarda uwarsa garinsu. Idan ta cigaba da zama to ina mai tabbatar miki yanzu ta fara kwanciya a asibiti. Gimbi ba karamin tsana tayiwa wannan matar ba”

Kallonta Mama tayi sosai. Anti Bebi ko kadan zuciyarta bata rissina ga abin da tayi niyya. Idan aka cigaba da haka watarana ba  auren Gimbi ne kadai zai mutu ba. Su ma iyayenta mutumcinsu sai ya zube a idanun al’umma.

“Bebi ki dubi Allah ki kyale Gimbi tayi rayuwarta. Idan tazo gidanki kici mutumcinta ki koreta. Ke kin sani bin boka da malaman tsibbu haramun ne amma kike takewa. To akan mene ne sai kin hada da ‘yata?”

“Masu ‘ya manya, abin da nake so ki sani shine yaran yanzu idanunsu a bude suke. Kowa ya waye da sanin rayuwa. Idan baki nemi taimako ba kina kallo bakincikin da namiji zai kasheki a banza. Ko zaki ce kin manta irin bacin ran da Innarmu tasha wurin Baba? Tun lokacin nasan cewa namiji zuma ne sai da wuta. Ban ga wani shegen da zan ragawa ba yazo yana cin zarafina”

Mama ta saki baki tana sauraron kanwarta da tayiwa duniya gurguwar fahimta.

“Ba duka aka zama daya ba Bebi. Yanzu kina jindadin zama da mijinki ya zama kamar hoto sai yadda kika juya shi?”

“Wannan ne mulkin, ko da wasa bai isa ya takani ba. Gimbiya kuma ki dena ganin laifina ita ta kawo kanta. Mata da dama a zamanin nan sai da haka suke samun damar cimma burinsu a wurin mazajensu. Me za’ayi da uwarmiji banda takura da sanya idanu”

Anti Bebi tayi nisa. Mama gani tayi cigaba da yi mata magana bacin lokaci ne sai kawai ta juya ta fita daga gidan. Ba abin ta fadawa Innarsu ba tasan babu wani mataki da zata dauka. Komai Anti Bebi tayi daidai ne. Tana zuwa gida ta kira Alh Mudi a waya ta fada masa. Ya rinka fada kuwa kamar ya ari baki. Allah Yasa yana gari yace ta kira masa Gimbi kafin ya karaso gidan.

*****

Sai yamma Gimbi ta sami damar amsa kiran Alh Mudi. Lokacin ta tabbatar Laminde da ‘yan uwanta bazasu cigaba da zama barazana a gareta ba. Shi kuma Awaisu ya wuce kasuwa.

A tsorace ta shiga gidan domin tun fitar Mama daga dakin asibitin jikin Gimbi ya bata akwai matsala. Sama ta hau dakin Alhajin ta samesu duka su biyun babu wanda yayi mata kallon arziki. Haka ta sami wuri ta zauna can gefe. Alh Mudi ne ya fara magana

“Gimbi ki fada min tsakaninki da Allah mijinki yana tauye miki hakki ne?”

A hankali ta girgiza kai alamun a’a. Ya sake tambayarta

“Ita Maamu ko sau daya ta taba nuna bata sonki da danta?”

Wannan karon ma girgiza kai tayi. A take ta ji Alhaji ya daga murya ya soma fada.

“Bakin gwargwado Gimbi mun baki tarbiya daidai iyawarmu. Mun baki ilimi domin ki bambance daidai da abin da yake ba daidai ba. Amma sai kika zabi biyewa son zuciya da hudubar shaidan. To ki sanu komai ka shuka da sannu zaka girbe duk daren dadewa”

Da yake ba kunya gareta ba sai ta dago kai tana tambayarsa me yake faruwa ne.

Hakan ya kara batawa Mama rai ta tashi zata kai mata duka. Alhaji yace ta zauna

“Bar ta Amina, Gimbi duk abin da kike yi domin ganin Maamu ta bar gidan danta mun gane. Banyi zaton akwai ranar da zan wayi gari ‘yar cikina tana mu’amala da malaman tsibbu ba. Saboda haka na shirya sanar da Awaisu halin da ake ciki zan kuma umarce shi da ya sakeki muddin baki chanza hali ba”

Da sauri ta dago kai tana kallon iyayenta.

“Alhaji saki fa kace.”

“Rufa min baki mara kunya, har kina da bakin magana. Alhaji kace ya saketa kawai ya huta. Idan kina son shi da gaske babarsa ko musaka ce wallahi zaki taya shi kyautata mata” cewar Mama

Gimbi ta matso kusa da Mama jin abin da tace tana kuka “don Allah kuyi hakuri bazan kara ba.”

Fada sosai suka rinka yi mata tare da cigaba da barazanar zasu saka Awaisu ya saketa. Da suka ga hankalinta ya tashi sosai shawarwari suka bata da nasiha akan hukuncin da zata tarar nan gaba a lahira. Ita dai rokonsu takeyi kada Awaisu yaji maganar. Da ta fito daga gidan ko tunanin kirki batayi ta wuce gidan Anti Bebi.

Da kuka ta shiga ta fada jikinta. Anti Bebi ta tureta tana fadan me ya kawota gidan.

“Ki taimakeni Anti Bebi kada su Mama su kashe min aure. Awaisu shine farincikina. Komai nawa ya rikice tun bayan rabuwarmu a asibiti.”

“Gimbiya kenan, ai nayi zaton karanki ya kai tsaiko har zaki iya hada kafada dani”

A ladabce ta kalli Anti Bebi “kiyi hakuri, bana son duk wani abu da zai gifta tsakanina da Awaisu mara dadi. Yanzu baki ga irin wulakancin da yake min ba. Gashi su Mama sun gano”

Anti Bebi tayi murmushin samun nasara akan Gimbi. Lallai Wangesi ibilishi ne. Cewa tayi kawai yayi duk yadda zaiyi Gimbi ta dawo karkashin ikonta. Gashi ta gani kuwa.

“Yanzu me kike so ayi?”

Da yatsu ta fara kirgawa

“so nake Awaisu ya koma kamar mijinki, kada ya rinka min musu ko gardama, Maamu ta koma garinsu ko kuma ya fita harkarta ni kuma zanyi yadda na ga dama har sai ta tafi don kanta, su Alhaji su dena yi min fada duk abin da zanyi babu ruwansu, sannan a wurin aiki kowa ya rinka shakkata hatta oganmu”

Ita kanta Anti Bebi ta jinjinawa dogon burin Gimbi. Shiyasa baa so mutum ya fara shige shige. Idan akayi rashin sa’a imani yayi karanci shikenan kuma an soma kenan. Ko don ta rama marin da Mama tayi mata zata karbi Gimbi hannu bibbiyu. Amma kuma tayi alkawarin sai itama tayi kuka a gaba. Bata ga wanda ya isa ya takata ta kyale ba.1

Bayan tafiyar Gimbi dakin Alh Maitama ta shiga. Yana zaune shi kadai a takure a gefen gado kamar wanda akace kada ya motsa. Yana ganinta ya sake gyara zama. Sakin fuska tayi bayan yasan dazu ya bata mata rai saboda ta nemi kudi yace ta jira ayi albashi. Shine tace ya zauna a daki. Sassauta murya tayi tana masa murmushi

“Alhajina yaushe Shuhada zata tafi ne?”

“Ke nake jira dama ki fadi rana sai na sanar da ita. Kamar yadda kika nema na hanata fitar”

“Na samar mata miji ne. Idan ta gama idda sai ayi auren.”

Kamar yayi magana sai ya kasa saboda bakinsa da yayi masa nauyi

“Baka ce komai ba, ko banyi gwaninta bane?”

Dolensa ya kirkiro murmushi “kinyi min komai Bebi, nagode sosai.”

Tashi tayi har ta fita tana jiyo muryarsa yana mata godiya. Tana zuwa daki ta dauki waya ta kira Wangesi. Duk bukatar Gimbi ta zayyana masa sannan ta kara da cewa bata so Alhaji Maitama ya bar Shuhada ta tafi. Kuma tana gama iddah ayi aurenta da Awaisu ko ta wane hali ne.

Bayan sati uku*

+

Babu kowa a ajin kasancewar ko bakwai da kwata batayi ba. Rumana ta shigo kayan makarantarta kamar an kwato a bakin kare. Sun yamutse gashi da alamun ko wanki basu samu ba. Zama tayi akan kujerarta ta hada kai da teburin gabanta tana kuka. Tunda take a gidan kawunta Awaisu bata taba ganin wulakanci irin na safiyar yau ba. Ji take yi kirjinta kamar ya fashe don bakinciki. Shi kuwa Awaisu ya fice fit daga ranta bata ko kaunar ganinsa.

Tana wannan kukan wasu mutum biyu suka shigo taki dago kanta balle a ga idonta. Yusra ce ta hudun shigowa  ajin. Ko ba’a fada ba tasan aminiyarta ce a zaune shiyasa tana ajiye jakarta ta kai mata dundu a baya. Maimakon ta dago tace zata rama yadda suka saba sai taji shiru. Dago kan Rumana tayi da karfinta sai ga hawaye suna sintiri a kumatunta.

“Rumana kiyi hakuri, ko zaki rama ne?” A zatonta dundun da tayi mata ne yasata kuka.

Ganin an fara kallonta yasa ta fice daga ajin Yusra na bin bayanta. Bayan SS3 da babu kowa saboda daliban sun gama WAEC suka je. Nan Yusra ta rinka rokon Rumana da kyar ta fada mata irin zaman da takeyi a gidan kawunta da kuma sabon salon wulakancin da ake yiwa Maamu.

“Yanzu ita matar Uncle din naki don wulakanci idan ita ce aka yiwa haka zata ji dadi?”

Rumana ta goge idonta da yake faman radadi saboda kuka

“Don ma ba a gabanki akayi bane Yusra.”

“Ni shawara daya zan baki wallahi ku tattara ku koma gida.  Ki fadawa Maamu tace zata koma Fika. Idan kuma taki Allah kiyi tafiyarki. Ga yunwa ga wulakanci….tabdi, wallahi da nice watarana sai na zuba mata miyar danyar kubewa a bakin kofa tayi zumulmula.”

Dariya ce ta kwacewa Rumana harda kyakyatawa. Amma har suka koma aji zuciyarta tana mai kara samun karfin gwiwar aiwatar da shawarar kawarta.

*****

Maamu ke zaune a daki ita kadai. Irin yadda take ji a zuciyarta ko kuka tayi bata tsammanin samun sassauci. Ta rasa me ta tsarewa Gimbi har take yi mata irin wannan cin kashin a cikin gidan dan da ta tsugunna ta haifa. Kwanakin baya da tayi rashin lafiya Awaisu ya dawo mata yadda yake a da. Tattali da mutuntawa da ya dace da mahaifiya babu inda ya rage ta. Lokaci guda kuma kamar anyi ruwa an dauke. Shigowa dakinta ya gaisheta dama har ta hakura. Abin da yafi damunta bai wuce yadda Gimbi take mata wulakanci a kan idonsa ba amma kallon wayarsa ko tv yafi masa mahimmanci. Tunawa tayi da yadda suka rabu da safe taji wani siririn hawaye yana bin idonta.

Rumana Gimbi ta sa firar dankali mai yawa irin kananun nan masu cin rai tun dare. Bata kwanta bacci ba sai daya saura. Karfe biyar ta tashi yaranta ta aiko Daula ta tashi Rumana. Cike da fitsara tasa kafa ta hauri Rumanan da take bacci a kan abin sallah a ciki, caraf a idon Maamu. Ta kuwa kai mata duka tana mata fadan abin da tayi. Daula ta bude baki ta saki wata irin kara kamar wadda aka sokawa wuka.

Da sauri Gimbi ta shigo tana tambayarta me aka yi mata.

Maamu bata ma san da yarensu take magana ba don haushi ta nuna mata Rumana rike da ciki tana sanar da ita me ya faru.

Gimbi ta wani kankance ido “ke dallah ba ke na tambaya ba sai son zance ke da ba’a gane yarenki”

Maamu har dan firgita tayi da tsawar, ita kuwa Rumana jikinta yayi sanyi don abu ne da bata taba gani ba yiwa babba tsawa. Kafin ta gama tunani taji Gimbi ta rike mata kunne ta murdeshi sosai. Rumana sai kuka tana kokarin kwacewa.

“Mummy kiyi hakuri” ta fada da kyar

“Ke kuma idan kika sake taba min yara sai jikinki ya gaya miki. Kuma daga yau sai yau kada ki kuma kirana Mummy. Uwarki na kyauye kwadayayyu masu kama da may…”

STORY CONTINUES BELOW

Kasa karasawa tayi saboda shigowar Awaisu. Maamu tayi saurin fada masa yadda akayi

“Kace matarka ta sakar min jika haka. Ba Rumana bace ta daki Amina nice na dake ta”

Ya juya ya tambayi Daula ta gyada kai tana cigaba da kuka. Gimbi ta saki Rumana kunnenta yana radadi kamar ya tsinke. Awaisu ta kalla fuskarta babu alamun wasa.

“To ka yiwa Maamu magana wallahi babu ruwanta da yarana. Duk ta bi ta tsanesu kamar ba ita ta haifeka ba”

Daga shi har Rumana shiru sukayi na dan lokaci. Sai daga baya kamar an tsikare shi ya hau Maamu da fada yana jaddada mata bai ga wanda ya isa ya taba masa yara ya kyale ba. Yana gama fadan ya fita daga dakin. Gimbi ta galla musu harara ta bi bayansa.

Da suka gama shiri Rumana ta fito ta kwashe kayan da sukayi amfani dasu ta wanke kamar yadda Gimbi ta shardanta mata kullum kafin ta tafi makaranta. Tana cikin wankewa Amir ya shiga kitchen din da nasa kofin tea din ko rabi bai sha ba. Jin muryar Gimbi kuma yasan zata masa fadan kin shanyewa yasa shi saurin jefa kofin cikin sink tea din ya watsowa Rumana a gaban hijab da rigar makaranta. Ta bude baki zata yi magana sai ta tuna yadda akayiwa Maamu shiyasa ta fasa. Wannan dalilin yasa ta dauko dayan uniform din a kayan wanki ta saka saboda yadda wancan ya baci.

*****

Ana tashi daga aiki Gimbi ta wuce gidan Anti Bebi. Yanzu sun kara dinkewa sosai. Gimbi ta ma dena tsoron me su Mama zasu fada. Harkar gabanta kawai take yi. Yau ma labarin yadda tayiwa Maamu da Awaisu da safe taje bata. Anti Bebi tayi dariya sosai da taji labarin.

“Me akayi akayi maza dama…dadin aure fa a zamanin nan bai wuce ki wawuri duk abin da zaki iya a hannun dan iska ba. Mazan yanzu kina tarairayarsu da ladabi da biyayya suna kunsa miki bakinciki da ciwon zuciya. Mace na shekara a gidan miji sai ki ganta a layin karbar maganin hawan jini”

Dariya Gimbi tayi suka tafa da Anti Bebi

“Kuma fa hakane, kawayena biyu duk kafin haihuwar fari sun kamu da hawan jini. Nagode da kika bude min ido wallahi. Mijin da nake aure ma yayi kadan ya daga min hankali bare wata tsohuwa”

Faffadan murmushi ne ya bayyana a fuskar Anti Bebi

“Da kyau Gimbiya. Da ace mata sun fahimci meye aure da bakincikin da namiji bai kashesu ba”

Hira suka sha sannan Gimbi ta tashi ta tafi gida ana kiraye kirayen sallar Isha. Lokacin Rumana ta dawo ta gyara gidan tsaf sai dai baa bata izinin shiga store ba bare girki.

Da abinci a leda Gimbi ta dawo ta bawa yaranta. Bayan sun gama da kanta ta tukawa Awaisu tuwo ta dibarwa Maamu da Rumana dan kadan a kwano daya wuraren goman dare. Suna ci Maamu dan kadan take tsakura saboda Rumana ta koshi. Haka suka gama cikinsu babu nauyi sai ruwa da suka sha sosai domin kada yunwa ta hanasu bacci.

Shadayan dare Awaisu ya dawo a gajiye. Ko hanyar dakin Maamu bai kalla ba ya wuce nasa. Gimbi don zolaya harda cewa ko zaije taya Maamu hira yau. Rai a bace yace bata ganin yadda ya gaji. Murmushi tayi tana bashi hakuri shi kuma yana wani hade rai.

*****

Haka rayuwa ta juyawa su Rumana. Kullum da fargaba suke tashi domin yanzu Gimbi bata boye musu mugun nufinta. Burinta kawai su bar gidan taci karenta babu babbaka.

****

Kwanan Shuhada biyar da gama iddah. Anti Bebi harda dauko wasu mutane wai malamai ne zasuyi mata adduar neman tsari. Alh Maitama kamar kullum bashi da bakin magana sai ma godiya gareta saboda kula da yarsa  da taje yi. Suhail ya gama jarabawa amma rashin kudi a hannunsu yasa Shuhada tace ya zauna kawai har a koma hutu ya cigaba da karatunsa .

Daga dakinta ta fito zata kwaso kayan shanyarta don mai wankin gidan daga na Alhaji sai Anti Bebi yake wankewa.

Daya daga cikin malaman karyar ne ta gani da Anti Bebi a wani karamin falo suna magana a hankali ta lallaba ta tsaya a gefe babu mai ganinta. Daga ciki take jiyo muryarsa a hankali

“Wannan maganin Wangesi yace ki zubawa ita babar taki a abin sha. Yadda zata shanye haka duk wani fushi ko bacin ran da zaki haddasa mata zata shanyeshi tas”

Juya maganin tayi tana dan murmushi.

“Shi Alhajin yace na barshi haka ko”

“Yaji tsoron kada yawan asirin ya haukata shi shine yace a saka masa ido na dan lokaci”

Dafe kirji Shuhada tayi don tasan da babanta ake. Barin wurin tayi niyar yi taji mutumin ya ambaci sunanta.

“Ita yarinyar nan Shahada take ko me ga nata maganin. A abinci zaki zuba taci. Da zarar taci yace ko sunan mutumin kika kira sai taji gabanta ya fadi sonsa ya karu a ranta. Ki kwantar da hankali bazata yi musu ba har ayi auren”

Karbar wannan magani yasa Anti Bebi nishadi da murna sosai.

“Sai na koya musu hankali su duka. Awaisu dama nasa matarsa ta gama juya masa tunani. Abin da ya rage bai wuce na aura masa Shuhada ba kuma na tsaya mata har sai ya saki Gimbi. Ni da ka ganni nan bana yafe rashin mutumci ko kadan”

“Kiyi yadda yace zaki ga biyan bukata”

Daga haka ta karbi maganin kafin su fito Shuhada ta bar wurin da sauri.

Dakinta ta koma ta hau kuka. Ta rasa wace irin mutum ce Anti Bebi. Share hawayenta tayi ta shiga tunanin neman mafita. Wurin rabin awa ta kwasa a dakin kafin ta fita.

Kitchen ta dosa dauko abinci ta tarar da Anti Bebi a falo.

“Ke ina zuwa?”

“Abincina zan dauko ko shima an hana ne?”

“Aa Shuhada, ni bana jindadin yawan rigimarmu kamar ba mata ba. Ga abinci can akan dinning table kije kici.”

Ba musu Shuhada ta wuce ta diba ta cika plate har yayi tsororo. Hanyar dakinta ta nufa Anti Bebi tayi dariya

“Shegiya mai cikin zani. Baki iya komai ba sai ci da kashi. Ji wannan tulin abinci kamar mai aikin karfi”

Shuhada tayi kamar bata ji ba ta wuce. Leda ta samu a gabanta tana juye abincin cokali cokali kamar ci take. Ba zato taji an turo kofar dakinta. Anti Bebi ke son tabbatarwa ko taci.

Ita kuwa Shuhada sai ta wayance tana kokarin kai cokalin baki. Anti Bebi bata ce komai ba ta juya ta fita. Shuhada ta juye fiye da rabin abincin a leda sannan ta mayar da sauran kitchen.

Anti Bebi ce ta biyota har kitchen ta dafa mata kafada. Shuhada don tsoro kamar ta saki fitsari. Bata kaunar hada inuwa da ita. Ji tayi Anti Bebin tace

“Kina son Awaisu mijin yar nan tawa Gimbi?”

Da kyar ta iya hadiyar yawu kafin ta tattaro hankalinta ta nutsu. Kai ta sunkuyar ita a dole kunya take ji tayi murmushi

“Kai Anti har kin gane”

Anti Bebi tayi wani juyin farinciki sannan ta sake maimaita tambayar. Wannan karon Shuhada hannu tasa ta rufe idanunta tana wani fari

“Ni dai Anti kunyarki nake ji”

Daga haka ta kwasa da gudu ta bar kitchen din.

Anti Bebi taji dadi mara misaltuwa ta kama dariyar mugunta. Da Shuhada zata wargaza rayuwar Gimbi.

Shuhada na shiga daki rufe kofar tayi tana numfashi da kyar. Tunda ta tari Anti Bebi da wannan karyar ya zama dole tayi amfani da wannan damar wurin sanin sirrinsu da kwatarwa kanta da duk wanda suka kafawa takunkumi ‘yanci.Ladabin karya da biyayya Shuhada ta cigaba da nunawa Anti Bebi. Ita kuma dadi ya isheta ta sami hanyar ganin hawayen Gimbi cikin ruwan sanyi.+

Bayan kusan sati biyu tana sanya ido akan Shuhada wadda ta dage sosai wurin nuna ita idan ba Awaisu ba yanzu sai rijiya. Hakan yasa Anti Bebi fara tunanin hanyar da zata bi domin ganin sun hadu ta fara aiwatar da kudirinta.

******

Kiran sallar magriba akeyi Rumana ta shigo gida da sauri rike da ledar kosai. Kitchen ta wuce inda take jin muryar Gimbi tana tashi taje ta mika mata ledar.

Gimbi ta karba ta bude hade da zaro idanu ita ta ga abin mamaki.

“Yanzu wannan kosan dari ne? Lallai wake ya soma arha. Wannan kosan ya yiwa Maamu yawa ai. Cikin tsofaffi sai ana sa ido sosai”

Plate din roba ta dauko ta debi kosai guda bakwai ‘yan miri-miri ta mikawa Rumana.

“Maza ga kunu ki dauka ki kai mata an sha ruwa tun kina hanya.”

Rumana ta kalli dan siririn kofin da ko cika baiyi ba da plate din kosan sai ji tayi hawaye na barazanar kwace mata. Wai yanzu wannan ne abincin shan ruwan Maamu a gidan danta.

Gimbi na kallon yadda yanayinta ya chanja a ranta tace mayu masu zuciyar kare. Zaman gidan sai kace dole sunki tafiya.

Haka Rumana ta tafi dakinsu ta ajiyewa Maamu abincin shan ruwanta wanda yasa idanunta kawo ruwa itama. Kunun kansa bai wuce kurba hudu zuwa biyar ba kwarara bare kuma kosan. Rashin wadatuwa da abinci ya sanya Maamu azumin dole kusan kullum yanzu shi take yi. Abincin da aka basu rana da dare sai su hada su ci lokacin shan ruwan don su fi koshi. Wani lokacin Rumana tana yi itama. Yau kamar gaske ganin idon Awaisu da safe Gimbi tace zata yi mata kayan buda baki. A yadda ta nuna kamar ranar Maamu ta fara azumin shi kuwa ya fita yana kara jin babu macen kirki sama da matarsa.

Maamu na kallo Rumana ta shige bandaki taci kukanta na tsantsan bakinciki da nadamar zuwa Abuja. Da ta fito wayar Maamun ta dauka tana shashshekar kuka ta kirawo babanta. Da yake wayar ba’a ji sai an  sakata a speaker Maamu tana jin muryarsa ta karbe wayar daga hannun Rumana kafin ta tona asiri.

“Harisu”

Dadi yaji na samun kira daga garesu saboda kwana biyu idan ya kira ta wayar Awaisu baya rasa uzurin da zai fake dashi a matsayin dalilin rashin bata waya su gaisa. Ita kanta muryarta raunana tayi da taji yace

“Maamuna”

“Harisu yaushe zaka zo ka kaini Fika? Kewar mutanen gida nake yi sosai. Ina Baaba da sauran mutan gidan?”

Dadi yaji domin suma suna kewarta yace “Zanyi magana da Awaisu sai ku taho idan anyiwa su Rumana hutu. Ko nazo da kaina mu taho tare”

Za tayi magana ya katseta ta hanyar yi mata tambayoyi akan lafiyarta da kuma kula da cin abinci akan lokaci.

“Bana so ki sake kwanciya kamar wancan karon”

A ranta tunani take yi idan ba a yi saurin mayar da ita cikin dangi ba kila gawarta za a kai Fika. Bayan duk sun gaisa da ‘yan uwa domin Harisun kashewa yayi ya sake kiransu Maamu rokon Rumana tayi akan ta rufawa kawunta asiri har Allah Ya kawo karshen zamansu a gidan. Ita dai Rumana ko magana ta kasa yi saboda bacin rai. Maamu na gama magana ta fice daga dakin ta nufi kitchen. A yau dole ta dauki shawarar Yusra ko don ta huce takaici.

Inda ake ajiye kayan kadi na miya ta bude ta debo karkashi ta zuba a kofi wanda rabinsa ruwa ne. Tana juyawa da yatsanta bata sani ba ashe Daula ta ganta. Dakin Awaisu ta nufa inda suke hira da Gimbi ta fada musu ga Rumana tana kwaba milo da ruwa zata sha.

Da sauri Gimbi ta tashi tana kallon Awaisu.

“Kana ji dai da kunnenka yarinyar nan ta fara sata duk irin kokarin da nake yi akansu ita da Maamu”

“Ki kyaleni da ita zanyi mata magana” shi tashin hankali ne baya so musamman da yake ya kwaso gajiya.

STORY CONTINUES BELOW

Bata saurare shi ba ta bi bayan Daula. Yau sai ta koyawa Rumana hankali kila da safe ta bar mata gidanta.

A bakin kofa suka hadu Rumana zata je dakin Gimbi ta juye kwabin karkashin a bakin kofarta. Ba karamin tsorata tayi ba da suka hada ido da Gimbi. Kofin ta fizge tayi wurgi dashi abin ciki ya watse don ma na roba ne. Sannan ta kwashe Rumana da mari.

“Barauniya kawai kwadayayyiya. Wato dama kece kike karar min da madara da milo ban sani ba”

Rike kumatu tayi tana kukan sharrin da akayi mata sai ga Daula ta yo kan Gimbi santsin karkashin da ta taka ya kwasheta tana neman faduwa. Garin haka bata kula ba tana kokarin rike ‘yarta itama ta taka suka yi sulu a kan tiles duk su biyun suna ihu. Daula tsoron faduwa yasa ta damki kan Gimbi wanda aka yiwa kananun kitson barebari. Jela ukun da ta damko tana ja yasa Gimbi sanya wata muguwar kara, hakan yayi daidai da cizgewar kitson sai gasu a hannun Daula. Su duka biyun suka fadi a kasa jikinsu dame da karkashi.

Rumana kuwa me zatayi banda dariya. Kana kallon kan Gimbi sai kayi dariyar yadda ya kwashe. Sai fada take yiwa Daula. Da kyar suka iya tashi santsi na kara dibarsu. Sai da Rumana ta ji tahowar Awaisu yana tambayar ihun me akeyi ne ta durkusa ta rike ciki. Duk da bukata ta biya amma tsoron hukuncin da zaiyi mata take yi.

“Me ya sameku haka, ku duk kun zube a kasa ke kuma kina rike ciki”

“Abba faduwa mukayi da wannan abin da Rumana ta hada” cewar Daula

Taimakawa Gimbi yayi ta tashi amma kafarta kamar bazata iya daukanta ba don buguwa. Runtse ido kawai take yi ta kalli Rumana

“Uban mene kika hada a kofin nan”

Fuska Rumana ta kwabe ita abar tausayi

“Cikina ne yake ciwo tun a makaranta shine wata tace min ana jika karkashi da kanwa”

“Karkashi da kanwa kuma Rumana? Baki da lafiyar bazaki fada min ba sai ki hada wani karkashi”

Awaisu yana magana yana kallon Daula mai kawo rahoto.

“Na zata fa milo ne” ta fada kai a kasa. Dama ita ce mai zuwa hada milo da madara ta sha duk dare. Lokacin da ta ga Rumana ma abin da ya kawota kenan.

Baice komai ba ya tallabo Gimbi suka tafi daki ciwo a kafarta ta hagu ya isheta. Daula sai harara take dokawa Rumana ta tafi dakinta. Ita kuwa da murna ta tafi harda danewa jikin Maamu. Bacin ranta duk ya kau saboda dadin da take ji a lokacin. Maamu bata san me yake faruwa ba amma canjin yanayin da ta gani wurin Rumana ya dan kwantar mata da hankali.

*****1

Daren nan Gimbi batayi baccin kirki ba saboda ciwon kafa ga kanta yana zugi. Gari na wayewa kafar ta kumbura suntum daga wurin gwiwa. Awaisu da kansa ya tashi Rumana tayi abincin safe  zai kai Gimbi asibiti.

Ta dan ji faduwar gaba ko a dalilinta wani abu ya sami Gimbin. Amma da ta tuna gasuwarsu a gidan sai ta share. Da kyar ya taimaka mata suka fita waje tana jan kafar. Kwakkwaran motsi idan tayi sai taji kamar ana soka mata wuka.

Bayan fitarsu Rumana ta shiga fadar Gimbiya matar Awaisu inda ake horasu ta dafa shayi ta soya kwai ta zubawa su Daula nasu ta hada mai yawa a flask ta kaiwa Maamu. Ga kwai ga bread.

“Rumana wannan daga ina?”

“Allah ne Ya bamu Maamu. Kiyi sauri ki ci kafin su dawo daga asibitin”

Dan fito da ido tayi “waye babu lafiya?”

Rumana tana dariya ta labarta mata yadda sukayi jiya. Maamu ta soma yi mata fada akan kada ta kara. Amma Rumana ta kula fadan bai kai zuci ba don har dan murmushi tayi.

Ranar sun ci sun koshi suna gamawa taje ta dora na rana da wuri kafin goma ta gama ta sake zuba musu mai yawa. Sai da ta koma gyara kitchen Awaisu ya dawo ya sanar dasu an kwantar da Gimbi a asibiti kashinta ne ya goce ga buguwa kafar tayi tsami.

Haka nan yaji yana son ganin Maamu bayan kusan sati ko hanyar dakin baije ba. Yana shiga ta fito daga wanka. Ji yayi jikinsa duk yayi sanyi saboda wata muguwar rama da Maamu tayi. Hankalinsa yayi mugun tashi yace

“Maamu baki da lafiya ne?”

So take tayi kuka sai ta dake “Ka kaini Fika”

Muryarta ma ta kankance kamar yadda ta rame. Duk yaji ya tsani kansa da rashin kulawa da ita.

“Kiyi hakuri a dan kwana biyu ki kara warkewa sai na kaiki. Amma a haka kowa ya ganki yasan baki da lafiya”

Daga murya tayi ta soma fada

“Ubanka ne ya samin ciwon da zaka ce bani da lafiya? Ka mayar dani inda ka dauko ni tunda ka gagara kula dani da yar amana Rumana”

Jin kansa yake kamar wanda ya tashi daga bacci a lokacin. Me ya faru tun tafiyar su Baaba ya dena bibiyar halin da Maamu ke ciki bayan yasan yadda Gimbi take wulakanta masa dangi .

Kamar wani yaro ya soma hawaye a gaban Maamu amma ya rasa me zaice mata. Tausayinsa ya kamata itama sai kukan.

Sai da suka yi mai isarsu sannan tace ya tashi ya fita bata son ganinsa. Jiki a sabule ya fita ransa yana kuna. Mamakin kansa yake yi da yadda yake sakaci da mahaifiyarsa. Shi Awaisu manajan banki kuma babban dan kasuwa shine Maamunsa take wadannan kasusuwan kamar wadda ta shekara ciwo.+

Tun shigarsa daki tunani kawai yake yi karshe bacci mai nauyi ya dauke shi.

A asibiti sai shabiyu likitan kashi yazo aka gyara kafar Gimbi. Tasha azaba gumi ya rinka bin jikinta saboda ciwo. Ga kanta inda Daula ta tsige mata kitso ya tashi sosai kafar gashin da ya fita ta kumburo shima ciwon yake mata. Duk wannan ya taru da rashin dawowar Awaisu daga cewa zaije gida ya dawo. Tayi ta kiran wayarsa shiru baya dauka. Nan fa ta damu sosai ta fara tsoron ko aikin Wangesi ya soma rabuwa dashi ne yau daya da batayi masa turare ba. Abu kamar wasa har azahar bai dawo ba kuma babu waya. Ganin haka hankalinta duk ya tashi har ta fi damuwa da rashin dawowarsa akan ciwon da jikinta yake yi. Takurawa wata likita tayi akan lallai sai an sallameta suka ki. Da ta rasa abin yi sai ta kira Anti Bebi.1

“Gimbiya ta Awaisu yaya akayi ne?” ta fada tana dariya

Gimbi ta amsa mata da kyar ta labarta mata halin da take ciki. Kamar gaske Anti Bebi ta nuna damuwarta ta shirya ta taho asibitin.

Da tambaya ta gane dakin ta shiga. Tana budewa ta ga kan Gimbi sai dariya har ta kusa kaiwa kasa.

“Gimbiya wannan kyan ki hoto wallahi a kafa shi a kofar gidan Awaisu.”1

Daure fuska Gimbi tayi “wannan ciwon fa ba na wasa bane Anti Bebi”

Da gayya ta kaiwa kafar da aka nade duka cikin wasa  ita kuwa Gimbi ta saki kara har tana jin fitsari na barazanar fita saboda azaba.1

Anti Bebi ta dauke kai kamar bata kula ba “nima ban ce na wasa bane, wai….  wannan kai naki kamar na budurwar zabuwa a lokacin da ta fara kora. Awaisu ya caba da Gimbiyar mata”

Ran Gimbi in yayi dubu ya baci har ta fara dana sanin kiranta.

“Idan dariya zakiyi min ki tafi kawai na nemi taimakon wani”

“Dadina dake tsiwar tsiya. Me kike so dai yanzu”

Tunanin yadda zatayi maganin Gimbi a nan gaba take yi. Dauriya ce kawai yanzu take kafin lokacin da zatayi dariya.

“Saboda wannan ciwon yau banyiwa Abban Haris turaren nan ba. Kinga tun fitarsa har yanzu shiru. Ina tsoron kada hankalinsa ya fara komawa kan uwarsa”

Anti Bebi ta murmusa “Gimbi Allah dai Ya baki suruka irinki. Nasan ba karamin dadi zaki ji ba ke me ‘yan maza har uku su auri mata masu jajircewa akan mazansu kamar ki”

Gimbi ta dafe kirji jin wannan muguwar addua daga bakin Anti Bebi.

“Ba Amin ba wallahi, wai me nayi miki ne haka kike min mugun baki?”

“Auuuuu, ashe babu dadi kike yiwa Maamu baiwar Allah? To maida wukar wasa nake yi. Amma ni kam gaskiya da ina da da namiji wallahi bazan bari ya aureki ba.”

Ganin cewa cin fuska Anti Bebin take yi mata tace ta tafi kawai ta fasa. Anti Bebi taji dadi ga dama ta samu na hada Shuhada da Awaisu tace tayi hakuri. Kwantar da kai sosai tayi tana bata baki Gimbi na hura hanci ita a dole ta isa. Bayan sun gama magana akan cewa Anti Bebi za ta je har gidan da sunan dauko mata kaya tayi masa turare ta dauki jakarta.

“Ki jirani da kansa zai zo har nan ya sameki ki sille shi ciki da waje.”

******

Gidanta ta wuce kai tsaye tana murmushi. Da yake ita ke tukin motar ko yaya ta tuna irin mugun tanadin da ta yiwa Gimbi sai ta daki sitiyari tana dariya. Da isarta Shuhada ta umarta da ta shirya zasu fita. Ita kanta wanka ta sake yi tamkar kanta zata kaiwa Awaisu ta saka riga da zani na mutumci harda hijabi. Shuhada ma doguwar riga ta saka mai kyau yalwatacciya da hijab wanda ya wuce kirjinta da kadan. Ganin shigar da Anti Bebi tayi abin ya daure mata kai sosai tuni ta sha jinin jikinta. Dole ta san yadda zata gabatar da kanta ko ma ina zasu je don kada asirinta ya tonu. Wayar da tayi da mamanta da safe ta tuna inda ta nuna tafi son ‘yarta ta dawo gabanta ita kuma tayi ta lallabata akan ta kara hakuri na dan lokaci. Ajiyar zuciya tayi ta bi bayan Anti Bebi.

Kasuwa ta biya ta sayi kaji manya manya guda shida danyu sai kayan marmari. Daga nan suka wuce gidan Awaisu.

Yana kwance a daki har lokacin sallar azahar da ya makara a gida yayi. Rumana ko tunanin ta zuba masa abinci bata yi ba. Girki dai tayi yau a koshe suke a ranta a shirye take da duk hukuncin da Gimbi zata yi mata idan ta dawo. Har ayyanawa take idan ma dukanta tayi itama ramawa zatayi sai dai yau a korata gida kamar yadda take so. Kamar daga sama taji dirar mota. Haba a take jikin Rumana ya dau mazari tayi zaton Gimbi ce. Yau tasan mai rabasu sai Allah yadda tayi barna a kitchen. Maamu kanta da ta ga naman da ta zuba mata a miya sai da tayi mata fada akan tayi wauta.

Tashi tayi daga falo zata gudu daki neman ceto a wurin Maamu taji muryar Anti Bebi da wata siririyar murya suna sallama.

Su Haris ne suka fito tarbarta. Rumana tana rarraba idanu taso ta ganeta amma da yake ba haduwa suke yi sosai ba ta manta inda suka hadu. Anti Bebi na ganinta ta ware hannu ta tafi da sauri ta rungumeta.

“Rumanan Maamu ina Maamunki?”

Rumana tayi sakato tana duban su daya bayan daya.

Dafa ta Anti Bebi tayi

“Baki ganeni ba ko, Auntyn Mummyn su Haris ce. Ina Maamu kaini na fara gaisheta kafin na nemi ‘yata”

Hannun Amir ta ja tana masa hira wai ina mamansu take ne ko don yau lahadi tana can tana bacci.

Har kasa ta kai gwiwarta ta gaishe da Maamu. Itama Shuhada gaisheta tayi tana tausayin rayuwar dattijuwa da aka asircewa da ya kama ta.

Waige Anti Bebi ta soma yi tana neman Gimbi. Daula ta sanar da ita tana asibiti tun safe. Mamaki ta nuna tare da dafe kirji

“Me ya sameta haka?”

Yaran kusan a tare suke bata labarin hatsarin Gimbi da ruwan karkashi. A haka Awaisu yazo ya samesu ya fito sanye da shirt da wando da gani wanka ya sake.

Ganin Anti Bebi ya sanya shi sake hade fuska ita kuwa ta dan taba Shuhada wadda tayi saurin gaishe shi tana binsa da kallo wanda a zahiri mutum kamar Anti Bebi zaiyi zaton na soyayya ne.

Murmushi Anti Bebi tayi tana nuna Shuhada

“Ka ganta nan ita ta hanani sakat wai zata zo gaishe da Maamu. Tun zuwanmu asibiti dubata take sonta.”

Kafe Shuhada tayi da ido ita kuma tayi saurin kallonsa tana rausayar da kai tare da murmushi.

“Don fitina kaji tasa muka saya wai a nan zata dafa mata irin yadda take so. Yini taso yi ni kuma bana jindadi gashi yau dreba yana hutu dole na daure muka fito” ta kare zancen da fara’a kamar yau take sallah.

Maamu dai kallonsu take yi bata ce komai ba har Anti Bebi tace da Rumana su tafi kitchen da Shuhada su gyara naman kada ya lalace. Da ido Awaisu ya bi bayan Shuhada da kallo ya kasa gane me zuciyarsa take ji a lokacin. Suna fita Anti Bebi ta zauna a kasa kusa da Maamu.

“Maamu don Allah ki rinka hakuri da ‘yar tawa. Nasan zama tare da sukuka sai an daure anyi hakuri. Dan yanzu ka haifeshi ne baka haifi halinsa ba” Tana magana tana rike da hannun Maamu wanda take ta mammatsawa a hankali kamar mai tausa. Maamu ta dago suka hada ido a take taji wani irin firgici ya ziyarceta. A yadda zuciyarta ke rawa bata jin akwai wani abu da Anti Bebi zata nema a gareta ta gagara yi mata. Wani murmushin gefen baki Anti Bebi ta sake yi tana kara murzawa Maamu sauran maikon maganin da Wangesi ya bata na mallake mata zuciya.2

Awaisu da ke tsaye yace da Maamu zaije asibiti idan an gama su dawo. Fada ta soma yi masa na rashin komawa bare ayi batun abinci. Rumana ta kwalawa kira taje ta hada abinci ya tafi dashi. Anti Bebi taji suna yaren da bata ganewa ta tashi wai itama asibitin zata je amma zata bar Shuhada idan ta dawo su tafi tare.

“Maamu bari na bishi na gano jikin nata”

Ba don yaso ba suka tafi tare tana ta yi masa hira duk ta ishe shi. Abincin ma ita ta dauka ta shiga dashi dakin.

A kwance Gimbi take suka shigo tayi saurin tashi zaune. A zatonta an gama yi masa turare ne Anti Bebi ta sako shi a gaba suka taho.

“Ni zaka yiwa haka Abban Haris? ka kawoni asibiti don wulakaci tun safe babu ci babu sha sannan ka ki dawowa. Ina ma ka shiga tun dazu ina ta kiran wayarka ka ki dagawa.”

Bata jira amsarsa ba ta cigaba da cewa “akan wannan me billen daga goshi har kan hanci zan huce. Bari na koma gida sai sun gane kurensu”

Zuciyar Awaisu ce take masa wani irin tafasa yana tunanin ko dai Gimbi ta sha kwaya ne ko kuma kitson da aka tsige mata ya taba mata kwakwalwa.

Anti Bebi kuwa ta lumshe ido tana jin cewa lallai hakanta zai cimma ruwa indai Gimbi ta cigaba da hawa dokin zuciya tana sakin layi a tunanin asiri ke aiki.Abubuwa da dama ya rinka tunawa a lokacin wandan da suka gabata. Kamar yadda ya dauke kai daga mahaifiyarsa da kuma wasu abubuwan da Gimbi take saka shi yana yi babu ko tambaya. Ba tare da cewa komai ba ya juya ya fita tana ta kwala masa kira.+

Tana ganin fitarsa ta fara kokarin tashi a tsorace Anti Bebi ta daga mata hannu alamun ta zauna. Fita tayi ta bi bayansa ita kuma Gimbi duk ta gigice tana neman yadda zatayi ta sauko daga kan gadon ta bi bayansa.

Mugun saurin da yake yi yasa Anti Bebi sai da ta danyi gudu ta iya taddo shi.

“Awaisu dakata don Allah”

A fusace ya waigo Anti Bebi ta fashe da kuka irin mai tsuma zuciyar nan ta dago kai tana kallonsa.

” Ashe haka kake fama dan nan?  kayi hakuri ka ji Awaisu.”

Wani kallo shekeke ya bita dashi sannan ya juya ya shige motarsa ya buga kofar da karfi ya fita daga harabar asibitin a guje.

Me Gimbi ta dauke shi ne? Har yaushe raini ya shiga tsakaninsu irin haka? Sannan garin yaya ya sakar mata ragamar gidansa har ta kai zata iya kiran mahaifiyarsa mai bille? Yau ba don a gadon asibiti take ba yana jin babu wani abu da zai hanashi yi mata duka a wurin. Kafin ya karasa gida zuciyarsa ta cika da tsanar kansa da dana sanin auren Gimbi.

*****

“Mai babbar kujera Wangesi na kan tudu na yarda na amince idan ina da kai duk wata matsalata ta kau”

Yayi wata dariya mai sautin kukan rikakken alade daga inda yake kwance wata mata wadda akalla zata kai shekaru hamsin da biyar tana yi masa tausa. A kowane hannun matar yatsu uku sanye suke da zobba na gwal manya. Leshin jikinta mai matukar tsada da kyau.  Fatar jikinta kadai ta isa ta nuna arzikinta. Hannu ya daga yana yi mata nuni ta dakata haka sannan ya cigaba da waya da Anti Bebi.

“Idan kina shakku a da yanzu nasan kin tabbata aljanu na sun tsaya min. Kamar yadda suka yi alkawarin tayar da rikici tsakanin Gimbiya da mijinta kin gani da idanunki”

Jinta take kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha tayi dariya “na yarda Wangesi na kan tudu. Aikinka yayi kyau sai nazo”

Kusan tare suka ajiye wayar ya dubi matar da take zaune a gefensa.

“Kin gama komai ne?”

Ta dukar da kai a ladabce “na gama Wangesi”

Dakin nasa ya karewa kallo. Ta share ko’ina tas ta goge. Daga gefe inda bandakinsa yake ta wanke shi har ana jin kamshin turaren da ta saka a dakin. Lokacin da ta shiga wani uban zarni da wari yake haka ta rinka amai kamar zata fitar da kayan cikinta. Bayan ta gama ta wanke masa kayansa su ma doyi suke yi babu kyaun gani. Ga kuma girki wanda ita da kanta yasa tayi masa cefane ta dafa masa shinkafa da miyar kaji.

“To Hajiya Dela kinyi duk abin da Aljani Sukku ya bukata. Yace kije sa’a dai a wannan kasuwancin da zaki fara ko tsinke kika daga zaki sami mai saya.”

Murmushi tayi tana kada idanu kamar yarinya.

“Nagode Wangesi, yadda kuke bani sa’a akan dukkan abin da nasa a gaba dole nayi biyayya.”

Wani dan kulli ya miko mata. “Wannan ki samu ki jika su tsumu na kwana uku sai ki hada lemo dashi ki bawa shi maigidan naki. Ina mai tabbatar miki ko nawa kika bukata jarin zuwa Dubai din zai baki kuma bazai taba saka miki ido wurin shige da ficenki ba”

Kullin ta bude inda ya zuba faratansa na hannu da kafa zako-zako masu matukar dauda wanda ta yanke masa kafin ta fara aikace-aikacen da ya saka ta.

Godiya sosai tayi masa ta tashi ta fita tana tofar da yawu saboda warin da take ji yana fita daga jikinta.

******

Anti Bebi ta koma dakin Gimbi inda ta sameta tana ta kokarin sauko da kafarta wadda aka gyara ta kasa. Saurin zuwa tayi tana gyara mata kafar

“Haba Gimbiya ina zaki je haka da wannan kafar”

“Ki kyaleni naje Anti Bebi, ko dai kinyi kuskure a turaren ne?”

Gwalo tayi daga bayanta sannan ta karya murya kamar gaske ” kada ki daga hankali akan wannan. A yau zanje Wurin Wangesi sai na ga abin da Awaisu yake takama dashi. Kada ki bari komai ya daga miki hankali. Gimbiya ko babu mai tsaya miki duk duniyarnan bazan taba bari ki wulakanta ba”.

Da kalamai masu dadi da kwantar da hankali Anti Bebi ta cigaba da hillatar Gimbi har ta sami nutsuwa.

Abu na karshe da ta fada mata shine ta dena yarda da zancen Wangesi shi kadai.

“A matsayinki na mace ban da asiri dole ki hada da kissa. Shigowarsa dazu maimakon ki nuna kinyi kewar rashinsa sai kika saki baki kina diga rashin mutumci. Yayi miki da sauki ma. Nice shi sai na daukeki da mari kafin na fita”

Idanu Gimbi ta ware tana kallon Anti Bebi kafin ta girgiza kai tace

“Lokuta da dama sai na rinka jin kamar ba kya kaunata. Yanzu banda kin kware a mugunta da keta meye na cewa da kece sai kin mareni?”

“Fitsarar ce ta tashi daga yi miki gyara?”

“Admit it Anti Bebi my misery gives you pleasure”

Da yake duk gayu da mugun halin Anti Bebi babu boko don ko sakandire bata gama ba kasa amsawa tayi sai tsaki da ta buga tare da surar jakarta. Gimbi tayi dan murmushi

“Uwata ta kaina tuba nake yi. Idan kika barni yanzu karshenta aurena ya mutu”

Ita ta dawo shawo kan Anti Bebin suka cigaba da musayar bakaken kalamai kafin su daidaita.

*****

Kafin Awaisu ya karasa gida yamma tayi sosai. Yana tsayar da mota su Amir suka tarbe shi da cigiyar Mummynsu. Shafa kawunansu kawai yake rai a bace ya kasa basu amsa.

Falo suka shiga yana sauri ya wuce dakinsa ya kwanta ko zaiji saukin radadin maganganun Gimbi yaji wani kamshi ya doki hancinsa. Bai gama tantance ko na meye ba Shuhada da Rumana suka fito  kowacce dauke da tray din abinci. Ai yana ganin Shuhada ransa ya kara baki ya daka wata tsawa da ta tsorata duka yaran da Rumana har hannunta na rawa zatayi bari. Da kyar ta saita kanta suka taru suna kallonsa.

Fuskarsa kamar bai taba dariya ba ya harari Shuhada “zo ki fice daga gidan nan yanzun nan”

Duk da ta tsorata sosai dakewa tayi ta tsaya a wurin. Ba wani abu take nema daga Awaisu ba face ya bata lokaci ko yaya ne tayi masa bayanin matarsa da kanwar babarta. Uwa uba idan ya nuna kyamarta da wuri yadda Anti Bebi tayi imani da asiri tana iya ganewa karya tayi mata. Daga nan kuma bata san hukuncin da zata yanke mata ba. Neman abin fada ta fara Maamu da ta shiga falon a lokacin ta katseta.

“Menene hakan da kake shirin yi? Ka gama wulakanta ni son ranka yanzu Allah Ya kawo mai tausayina za ka koreta. Tun da kuka fita take yi min hidima kamar ‘yata ba kamar matarka ba”

Kallonsu Shuhada tayi tana mamaki ashe ba Hausawa bane. Shima cikin yarensu ya bata hakuri sannan dubi Shuhada

“Ana yin sallah ki fito ki tafi ita wadda kuka zo taren tana asibiti.”

Bata nuna masa bacin rai ba sai ma marairaicewa da tayi a gaban Maamu.

“Gashi ban iya mota ba kuma bata bar min mukulli ba. Maamu bari na ajiye miki wannan sai na tafi tun yanzu kafin magariba ta karasa na rasa abin hawa”

Maamu tayi murmushi “A’a ‘yata ki bari ayi sallah zai kaiki har gida. Nagode miki sosai”

Bai iya cewa komai ba ya wuce. Duk mutum mai alaka da Gimbi haushinsa yake ji. Yana idar da sallah ya bukaci tazo su tafi. Maamu tayi ta sa mata albarka suka yi sallama da Rumana.

Motarsa ya nuna mata ta shiga ita kuwa ganin su Rumana sun koma ciki ta dago ido tana masa kallon da yasan ko me zata fada babu wasa a ciki.

“Ina son muyi magana da kai ne.”

Ya dan matso inda take domin jin abin da take son fada suka ji alamun an rufe gate.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *