KWARYA TABI KWARYA CHAPTER A
KWARYA TABI KWARYA! 1⃣
Na UMMI A’ISHA
JAN KUNNE duk wanda ya canja wannan
labari ko yayi editing dinsa, ko kuma ya cire
sunan marubuciyar ko ya canja sunan taurarin
ciki Allah ya isa ban yafeba!.
CANAL AWWAB MANSUR ADAM shine sunan
dake manne agaban rigar dake jikin kyakkyawan
sojan wanda ke fitowa daga cikin babban bankin
Nigeria wato CBN acikin garin abuja dogone
kyakkyawa wankan tarwada yanada matsakaicin
jiki, sanye yake cikin uniform din sojoji wanda
suka dace dashi yana rike da waya kirar
BlackBerry bold 2 baka hannunsa daure da
agogon azurfa na Rolex, yar karamar bindiga ce
rataye agefen aljihun wandonsa kansa babu hula
shekarunsa bazasu gaza 29 zuwa 30 ba, kai
tsaye inda yayi packing din motarsa ya hara,
motar tasa yar yayi ce kirar zamani wanda sai
wane da wane ne ke iya hawanta, BMW New
modern itace motar da ya bude yashiga blue
colour, fita yayi daga cikin harabar bankin ya
nufi unguwar wuse kansa tsaye ya tasamma
wani babban gida mai yalwar shuke shuke
kamar akasar India kasancewar unguwar
unguwace ta manyan mutane kuma unguwace
tamasu kudi, yawancin ministers da mukarraban
gwamnatin tarayya ne acikin unguwar, hon yayi
mai gadi ya bude masa yashiga ya Adana
motarsa yafito yana rike da wayarsa ya shiga
cikin gidan tunda ma’aikatan gidan suka
hangoshi suka fara russunawa suna diban
gaisuwa shi kuwa canal sai shan kamshi yake
dahaka yakarasa wani wawakeken falo ginin
zamani wanda ya kayatu da kayan alatu, yar
karamar bindigar dake jikin wandonsa yazaro.
[10/8, 16:52] Admin Aysha:
KWARYA TABI KWARYA2⃣
Na UMMI A’ISHA
Bindigarsa ya zaro daga gefen aljihunsa ya
ajiye akan dan karamin stool din dake ajiye
acikin falon, benen dazai kaishi falon hajiyarsa
yabi har zuwa cikin kawataccen falon nata tana
zaune cikin shiga ta alfarma da Kamala ta
zubawa makekiyar tv din dake manne ajikin
bangon falon ido, wata drama take kallo a
channel din CTV, ahankali yashiga cikin falon
bakinsa dauke da sallama cikin fara’a ta dago
ta dubeshi tana faman murmushi, Awwab barka
da zuwa, yawwa umma sannu da hutawa kusa
da ita yaje ya zauna yafara gaida ta cikeda
sakin fuska ta amsa masa gaisuwar da yake
mata, cikin muryar shagwaba yace umma dan
Allah ki samo min yarinya wadda zata rinka
gyara min bedroom dina domin kullum idan nazo
acikin datti nake ganinsa nikuma banida time
din da zan zauna na gyarashi, murmushi tayi to
awwab akwai wata yarinya da zata zo ta zauna
awurina inyaso ko ita sai ta rinka gyara maka
dakin, yawwa thank you umma, bari naje nayi
wanka saboda ina son na dan kwanta na huta,
gobe da sassafe zan koma ibadan jirgin 6 nake
son bi, kallonsa tayi soja kenan Allah ya kaika
lfy ya tsareka maza aje a huta kafin abbanka
yadawo daga office, yayi min waya cewa 3 zai
dawo gida kaga yanzu kuma 2:20 tayi, to umma
sai nafito, saukowa kasa yayi ya dauki
bindigarsa ya nufi side dinsa wanda yake da dan
tazara kafin kaje, yana shiga dakinsa ya tube
kakinsa ya shiga toilet yayi wanka yafito sallah
yayi sannan ya kwanta akan luntsumemen
gadonsa wanda yasha shinfidu da kaya masu
laushin gaske, bai jima da kwanciya ba bacci ya
daukeshi, acikin baccin nasa yafara mafarki da
wata kyakkyawar budurwa tabiyoshi da wuka
tana cewa sai ta rama abinda yayi mata, gudu
yake itama binsa take daf dazata kamashi ya
farka a firgice, firgigit yatashi.
KWARYA TABI KWARYA3⃣
Na UMMI A’ISHA
Yana tashi yafara kiran sunayen Allah tareda
yin addu’a Allahuma inni a’uzubika min sharri fi
manami an yadurruni fi dini wa dunniyaya,
tunani yafara yi wannan mafarkin shine na 3 da
yayi wannan budurwar tana bibiyarsa da wuka,
to wacece? Tambayar da yayiwa kansa kenan
amma sai dai bashida amsar wannan tambayar,
tashi yayi ya shiga toilet yayi brush yafito, side
din mahaifinsa yanufa ya tarar dashi akishingide
acikin tamfatsetsen falonsa wanda ya tasaru
mutuka gabansa yaje ya durkusa ya
gaidashi,cikin jin dadi mahaifinsa yadafa kansa
yace son kazo lfy? Lfy lau abba nasameku lfy?
Lfy son ya aiki? Alhamdulillah abba, amma dai
zakayi 1 week ko? Girgiza kai yayi no abbba
gobe zan koma dan akwai wani training da
zamuyi har na tsawon 2 weeks kuma daga gobe
zamu fara shiyasa zan koma goben, murmushin
mahaifin nasa yayi dakyau Soja Allah ya tsare
amin Abba, hira suka zauna yi shida mahaifinsa
sai daf da magriba yafito daga falon mahaifinsa
ya dauki wata sabuwar motarshi Prado one door
mai bakin glass yafita daga gidan, wani babban
hotel mai tashe yanufa yana zuwa ya faka
motarsa yashiga cikin club, yanmata da
samarine kawai awurin yaran masu kudi sai
sheke ayarsu sukeyi kowacce ka kalla acikin
maye take, kansa tsaye ya nufi inda ake zuba
giya yaje ya karbo kwalba daya wata kujera ya
nufa yaje ya zauna, yana kurbar giya yana
kallon yanmatan dake chashewa kamar akasar
turai, ji yayi an dafashi ahankali ya waiwaya,
wata kyakkyawar budurwa baka ya gani ta tsuke
cikin riga da wando acikin maye tafara yi masa
magana, kazo…. Muje ka… Kaini… gida luu yaji
tafado kansa cikin sauri ya tureta yatashi yafito
daga cikin club din,cikin motarsa yashiga ya
zauna yanata kallon mutanen daketa kaiwa da
komowa acikin harabar hotel din anan ya raba
dare sai wurin 12 sannan yanufo gidansu.
KWARYA TABI KWARYA4⃣
Na UMMI A’ISHA
Acikin maye sama sama yake driving din har
ya iso unguwarsu yashiga gidansu cikin maye
yafito daga cikin motarsa yana tafiya yana hada
hanya har ya isa dakinsa, mahaifinsa yana tsaye
yana kallonsa ta saman benen dakinsa sai
dayaga yashiga dakinsa sannan yasaki labulen
dakin yana ajiyar zuciya shi dai yarasa a ina
awwab ya dauko wannan dabi’a ta shan giya da
neman mata alhalin da bahaka yakeba, amma
tun lokacin da yazama soja yatare a bariki
shikenan yadauki dabi’u munana bayan shikuma
yasan yabashi dukkan tarbiya wacce uba
yakamata yabawa dansa, runtse ido yayi tareda
yi masa addu’ar shiriya. Awwab yana shiga daki
yafada kan gadonsa yakwanta nan wani irin
nannuyan bacci yayi awun gaba dashi sai karfe
5 na asubha yasamu ya iya farkawa, cikin rashin
kwarin jiki yashiga toilet ya watsa ruwa yafito
yatafi masallaci, bayan sun fito daga masallaci
ne mahaifinsa yakirashi suka shiga falonsa cikin
damuwa uban ya furta son meyasa kake haka?
Yaushe zaka canja saga mutumin banza zuwa
na kirki? Son sam baka iyo halina ba kuma baka
iyo halin mahaifiyar kaba, tunda kazama soja
kazama dan iska, cikin sauri yadago ya kalli
mahaifin nasa, yes kazama dan iska awwab
baka tsoron haduwarka da Allah ko kadan domin
zuciyarka tagama bushewa, sunkuyar da kansa
yayi yayi shiru batare da yace komai ba sai da
akayi yan mintuna sannan yace kayi hakuri abba
insha Allahu zan daina, cikin alamun damuwa
uban yace to my son Allah yanufeka da dainawa
amin abba, yanzu zanje nashirya natafi Ibadan
domin jirgin 6 nake son bi, to son Allah yakaika
lfy sai munyi magana amin abba nagode.
KWARYA TABI KWARYA5⃣
Na UMMI A’ISHA
Jikinsa a sabule yafito yashiga side dinsa yayi
wanka yashirya yasaka kakinsa wanda sukayi
mutukar yimasa kyau yadauki yar karamar
bindigarsa ya soketa a muhallinta kamar kullum,
dakin ummansa yaje yasameta zaune akan
sallaya tana jan carbi zama yayi ya gaisheta
sannan yayi mata sallama yafito kai tsaye
airport driver ya kaishi yashiga jirgin kabo air
line ko minti 10 ba ayiba jirginsu yatashi zuwa
Ibadan tafiyar data daukesu 15 minutes, yana
sauka wasu sojoji guda 4 suka zo suka sara
masa tareda kamewa kai kawai yadaga musu
yashiga cikin motar da aka gindaya agabansa,
gidan baya yashiga sauran sojojin sukuma suka
shiga tasu suka nufi barikin sojoji, suna zuwa
aka bude musu gate suka shiga kofar wani gida
sukaje suka tsaya anan dagudu sukazo suka
bude masa kofar motar yafito batare da yayi
musu magana ba cikin gidan ya shiga har wani
dan madaidaicin falo inda wani babban mutum
yake zaune hannunsa rikeda jarida yana
karantawa, sallama yayi tareda sarawa mutumin
yace Weldon sir! Dagowa mutumin yayi welcome
canal awwab, atsaye ya zauna batare da ya
zauna ba, sir nakaraso, ayimin afuwa banzo da
wuriba, no problem canal, zo ka karbi wannan
taswirar kagani, wani map ya mika masa
kaduba kagani wannan dan kauyen natsakiya
ana fama da tarzomar yan tada kayar baya so
yanzu yanzun nan ina so kaje kahorar da sojoji
guda 40 katurasu suje su kwantar da tarzomar
tunda ina ganin 40 ai zasu isa saboda kauyen
bashida wani girma, yes sir yafada tareda fita
daga cikin falon kai tsaye wajen dandazon sojoji
yanufa inda ya cika umarnin da aka bashi daga
nan yatafi wani babban fili wanda iya masu irin
uniform dinsa ne kawai awajen sai wani guda
daya nasa daban da alama yafisu mukami, nan
suka fara wani training irin nasu na sojoji sai
yamma likis suka tashi, gidansa yanufa wanda
yake cikin barikin sojojin yana shiga kiran basma
yashigo cikin wayarsa basma itace budurwar sa
wacce zai aura yanzu haka tana can a babban
birnin london a Oxford university tana karantar
mass com, cike da kasala da aji ya dauka hello
basma daga daya bangaren ta amsa hy Darling
yakake am fine basma yanzu haka daga wani
training nake duk nagaji shigowana gida kenan,
sonake nayi wanka nahuta, ayya to shikenan
bari nabarka sai kajini bye, kashe wayar yayi
tareda ajiyeta agefe yashiga wanka bayan yafito
ne wani kiran yashigo wayarsa yadauka hello
canal yakub ya akayi? Canal awwab ga
yanmmata fa ansamo shine nace ko zakazo
kaduba? No yau wlh babu abinda zan iya kawai
kubarsu ni kasan bana son yan hannu nafi son
virgin, ok to ba damuwa, wayar tasa yakashe
domin baya son adameshi, salla yayi yaje
falonsa ya bude fridge din dake ajiye giyace kala
kala aciki ba don kar ummi A’isha tayi karya ba
to danace muku babu lemo ko daya duk giyane
aciki,kwalbar guilder ya dauko da cup yazo
yasamu kujera ya zauna yafara tsiyaya yana
sha.
[1/12, 8:20 AM] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA6⃣
Na UMMI A’ISHA
Sai da ya shanye kwalbar giya 2 sannan
yatashi yana hada hanya yana tangadi yashige
dakinsa yana zuwa ya fada akan gado nan bacci
yayi gaba dashi bashi ya tashi ba sai karfe 3
nadare. Asubha tanayi yayi salla kasancewar
barikice babu masallaci ko church aciki, yana
idarwa ya fita motsa jiki bai dawo ba sai 7 koda
yadawo wanka kawai yayi ya sanya uniform
dinsa wanda yadace dashi yafita zuwa office,
office din nasa ya tsaru sosai komai najin dadi
an tanadar masa sai 5 yabaro office yadawo
gida, nan ya zauna yakira basma suka fara hirar
soyayya sai da aka kira sallar magriba sannan
sukayi sallama. Salla yayi yayi wanka ya saka
dark blue din t shirt wadda aka rubuta i can i
will ajiki yasa blue din jeans yadauki bindigarsa
yasoke ajikin wandonsa yafito yadauki motarsa
sai wani club wanda ya kasance matattarace ta
yan iska. Yana zuwa yayi parking din motarsa
yafito ya nufi inda ya hango abokansa zazzaune
kowannensu da kwalbar giya a hannunsa wasu
kuma taba sigari suke busawa gefe daya kuma
yan matan bariki ne kowacce taci ado tayi
kwalliya cikin kaya matsattsu. Karasawa yayi ya
basu hannu suka gaggaisa sannan yakoma gefe
ya zauna yayi order giya kwalba 2 masu tsada,
ana kawo masa yafara tuttulawa cikinsa sai da
ya shanye tas sannan ya ajiye kwalbar namfa
tafara aikinta jin jikinsa yayi ya mutu murus
dakyar ya tashi yashiga motarsa yarufe amma
bai baro wurinba sai karfe 3 nadare yana tafe
yana hada hanya abinka da mai kaki babu
jami’in tsaron da ya iya tareshi dahaka ya
karaso cikin barikin yabude gidansa ya shiga,
yana zuwa ya zube acikin kujera sai barci.
KWARYA TABI KWARYA7⃣
Na UMMI A’ISHA
Barci yake kamar wanda ya mutu sai da
asuba tayi sannan ya iya tashi yagabatar da
dukkan abubuwan da ya saba gabatarwa abisa
al’adarsa sannan yafita office. Kwanansa 6
agarin ibadan ya shirya tafiya zuwa garin abuja,
jirgin karfe 7 na dare yabi 7:30 ya isa gida yana
zuwa side dinsa ya wuce yana shiga dakinsa ya
ganshi tsaftsaf an gyarashi yadda ya kamata
komai an ajiyeshi a muhallinsa ga wani kamshin
dadi da dakin yake yi, bathroom yashiga nanma
kalkal an wankeshi tas, wanka yayi yafito yayi
salla ya saka wata riga karama dark brown
yasaka wando baki iya gwiwa ya nufi dakin
ummansa yana shiga yasameta kishingide
akasan carpet tana kallon wata drama atashar
CTV kusa da ita yaje ya zauna tareda gaisheta
ta amsa cikin kulawa kallonta yayi umma naga
an gyaramin dakina ko har kin samo min mai
gyaran ne? Murmushi tayi awwab kenan dama
ai nace maka kanwarka zatazo ko? To itace
tagyara maka, ras yaji gabansa yafadi, mikewa
yayi umma bari naje wajen abba dan bai ma san
nazo ba, fitowa yayi daga dakin umman adai dai
kofar fita yahadu da ita farace doguwa yar
siririya kamar baturiya amma tafi kamada yan
kasar indiya kallon ta tayi gabansa yaji yayi
mummunar faduwa take yaji ya tsaneta tsana
marar misaltuwa, ina wuni tafada cikin zazzakar
muryarta, bai amsa ba yawuceta yashige side
din abbanshi yana shiga yasameshi zaune yana
signing ajikin wasu takardu idonsa sanye cikin
medical glass, gabansa yaje ya zauna abba
barka da dare, cikin fara’a ya amsa masa
gaisuwar tareda rufe takardun dake gabansa ya
cire gilashin fuskarsa, yajuyo ga dan nasa
awwab agaskiya nagaji da ganinka haka yanzu
kayi girman da yakamata ace ka ajiye iyali,
yakamata ace yanzu kanada mata, ni yanzu
banida wani buri illa inga ka ajiye iyali dan
hakane ma yasa na zaba maka matar aure
NIHAL arazane ya kalli abbansa haba abba
wacece kuma nihal? Kanwarkace awwab tagama
karatun secondary sch dinta kuma
mahaddaciyar alqur’ani ce, cikin faduwar gaba
yace kayi hakuri abba bazan iya aurenta ba
akwai yarinyar dazan aura next week zata dawo
Nigeria tagama karatunta kuma tana dawowa
maganar aurenmu za ayi, kuma abba auren
yanzu ai ba haka ake yinsa ba kamar ni ace na
auri yar secondary? Gaskiya nafi karfin haka
danni wlh abba matar da zan aura mai cikakken
ilmi ce wadda takeda degree, dan yanzu a harkar
aure ma ana duba bright future, amma me
secondary me tasani na rayuwa? Auren yanzu
abba aurene nazamani kuma na aurene nakowa
da muhallinsa shiyasa ma bahushe yace
KWARYA TABI KWARYA!.
KWARYA TABI KWARYA8⃣
Na UMMI A’ISHA
Tunda yafara maganarsa mahaifin nasa kawai
kallonsa yakeyi har yagama, amma acikin
zuciyarsa fadi yake yaro yarone yaro man kaza,
gyaran murya yayi shikenan awwab naji abinda
kace kuma naji duk bayanin da kayi to amma ita
yarinyar yar inace? Abba yan kanone amma
acikin garin nan suke da zama yanzu haka
tagama karatunta a London dawowa kawai
zatayi, to Allah yadawo da ita lfy, amin abba,
tashi yayi yafito yanata cika yana batsewa haka
kawai wata yar secondary akan me? Yanzu duk
ajin nan nawa ace wai kamar ni na auri yar
secondary wlh bazai yiyuba ni yarinyar da zan
aura me class ce sannan kuma mai degree ce
amma ba illiterate ba da wannan zancen zucin
yakarasa falon umma tana zaune wannan
yarinyar tana zuba mata abinci, barshi haka
NIHAL yaji umma tafada cikin sauri yabi yarinyar
da kallo au dama wannan ce da yarinyar da
abba yake so ya aura? Mts shikuwa me zaiyi da
wannan yar mitsitsiyar yarinyar? Wuce nan
wannan ai sai abokansa ma suyi masa dariya.
Wata irin harara ya wurga mata da mamakinsa
sai yaga itama ta harareshi gamida murguda
masa baki,idonsa yabude cikeda mamaki ya
kalleta a haife bazata fi shekaru 20 ba aduniya
makewa yayi yaje kusa da umma ya zauna yana
babbata rai, kallonsa tayi awwab ya akayi? Kai
da waye? Umma nida abba ne wai wata yarinya
ya zaba min bayan kuma ni inada yarinyar da
zan aura, murmushi umman tayi kar ka damu
awwab abinda kake so shi mahaifinka yake so
nasan bazai taba matsa maka ka auri yarinyar
da baka soba, sai alokacin yayi murmushi
hakane umma amma kema ki kara fada masa
yanda nake din nan ba kowacce kuchakar
yarinya zan aura ba kallon wannan yarinyar
yasake yi saboda dama dan ita yafada harar sa
ta sakeyi akaro na biyu tsaki yaja umma ni
yanzu bana burin nayi auren jahila sam sam nafi
son wayayyiya yar makaranta
KWARYA TABI KWARYA9⃣
Na UMMI A’ISHA
Murmushi umman sa tayi wannan haka yake
awwab Allah yabaka wacce kakeso, me zaka ci
nihal ta zuba maka? Yatsina fuska yayi babu
abinda zanci kuma idanma inaso to da kaina
zan zuba basai an zuba min ba, kallonsa
yarinyar tayi tare mikewa ta fice daga falon,
shima mikewar yayi tareda bin bayanta da
harara fita yayi yaje dakinsa ya dauko key din
motar sa yafice daga gidan sai Rossy Guest villa
yana zuwa yasamu anata chasu mata da maza
sai rawa suke masu shan giya suna sha, masu
rawa sunayi masu rungume rungume suma
sunayi can gefe yakoma ya zauna yana kallon
masu shige da fice kafin daga bisani yayi order
kwalbar giya guda daya Ana kawo masa ya
shanye amma bata bugar dashi ba agogon
hannunsa ya kalla karfe 10:30 gida ya hara
saboda washe gari yake son komawa yana zuwa
yashige dakinsa yaja birki a falo yazauna akan
kujera yana kallon silin, bacci ne yadauke shi
mafarkin wannan yarinyar yafara ta biyo shi
aguje, gudu yake iya karfinsa amma sai da ta
kamashi wukar hannunta tadaga sai sheki take
alamar kaifi cikin karaji tace yau zan
kasheka,zan rama abinda kayi min wukar tadaga
zata luma masa firgit ya farka cikeda firgita
amma dayake soja ne bai wani damuba kawai
dai duniyar tunani ya shiga yana son gano
wacce yarinya ce wannan kuma shin meyayi
mata da har take son rayuwarsa wannan shine
karo na 3 dayayi mafarkinta gashi kuma yanzu
tayi nasarar kamashi, daga kansa yayi ya kalli
agogon dake manne acikin falon karfe 3:30
nadare mikewa yayi tare da lalubar bindigarsa
yawuce cikin dakinsa.
KWARYA TABI KWARYA1⃣0⃣
Na UMMI A’ISHA
Yana shiga yacire kayan jikinsa yazauna iskar
a.c tana shigarsa yana nan zaune yana nazari
har 4 tayi wanka yashiga yayi yafito lokacin
anata kiran salla a massalaci, salla yayi yatafi
dakin mahaifinsa yayi masa sallama yafito
yashiga wurin umma itama sallamar yayi mata
yatafi garin ibadan lokacin dayaje karfe 7 tayi
agurguje ya shiga gidansa ya dauko wasu
takardu yafita zuwa office dinsa. Sai la’asar
yadawo yashiga gidansa yayi wanka ya ahirya
tsaf yafito gidan yakub abokinsa yatafi yana
shiga ya sameshi zaune da wasu yan mata sun
sakashi a tsakiya sai masha’a suke aikatawa
tsaki awwab yayi yasamu kujera yazauna,
kallonsa yakub yayi canal yau zamuje club ne?
Yeah hakan dai zai fi kazo muje ka kyale
wadannan yaran, kana ta bata lokacinka akan
wadannan matan marassa aji kallonsa yakub
yayi yace sorry canal bari nazo mutafi fita waje
yayi yazauna cikin motarsa yana jiran fitowar
yakub, bai jimaba yafito suka tafi akan hanyarsu
ne yakub yadubi anwar yace canal wai me
yafaru ne naga kamar yanzu baka fiya kula yan
mataba? Wani dan karamin tsaki awwab yayi
wlh yakub ni kaina ban san menene dalili ba,
amma kuma ina ji ajikina cewa akwai gagarumin
abunda yake tunkaro rayuwata akwai wani abu
wanda zai faru dani nan bada jimawa ba but
ban san yaushe ne ba, kallonsa yakub yayi cike
da mamaki taya kasan haka? Wlh yakub akwai
wasu mafarkai dana jima inayi kuma har yau
ban daina ba sannan akwanakin baya akwai
wani abu da yataba faruwa wanda bai yiyuwa
na iya fada maka domin sirrine wanda ya shafi
rayuwata,yanzu gaba daya jina nakeyi a wani
irin yanayi, sanin kanka ne ina son mata kuma
ina nemansu aduk inda nasan zan samesu to
yanzun ma dai ba dainawa nayi ba amma inajin
wani irin abune a tare dani, ahalin yanzu nafi
son nasha giya akan nakula mata sai dai zan
kulasu suma nan da wani dan lokaci dai dai
lokacin suka karasa club din, nidai ummi A’isha
nakosa naji wannan labarin na awwab masu
karatu nasan kuma kun kosa ko? Ko baku kosa
ba.
[1/12, 8:28 AM] Ummi A’isha: [1/12, 8:21 AM]
Ummi A’isha: KWARYA TABI KWARYA1⃣1⃣
Na UMMI A’ISHA
Suna isa awwab yayi packing adai dai inda
aka tanada domin packing din motoci, kashe
motar yayi suka firfito suka shiga cikin club din,
nanfa suka fara gwangwajewa sai da dare yayi
sosai sannan suka dawo gida. Ranar juma’a da
misalin karfe 4 na yamma awwab yabar ibadan
ya nufi abuja karfe 4:30 ya isa gida falon
ummansa ya fara zuwa suka gaisa sannan
yafito yashiga dakinsa, wanka yayi yafito
yashirya cikin wani dafaffen boyel baki yasa hula
zannabukar itama baka agogon azurfa na Gucci
ya daura a hannunsa yafesa turaren ice hot
yasa bakin takalmi harp cover yafito hakika yayi
kyau na daukar hankali gashi yanada kwarjini
sosai, side din umma yakoma lokacin da yashiga
ita kuma tana kokarin fita ganinsa da tayi yasa
taja da baya tareda komawa kusa da umma ta
zauna, shigowa ciki yayi take falon ya gauraye
da daddadan kamshin turarensa, umma ya kalla
yace umma zanje gidansu basma,au basman ta
dawo ne? Eh umma tadawo tun shekaran jiya
saboda itama nazo garin yau, to kagaisheta,
zataji umma yafada yana dan murmushi, ta
gefen idonta ta kalleshi yayi kyau mutuka taba
baki tayi acikin zuciyarta tace danma dai adon
iya najiki ne daki kaca kaca yake, shiko awwab
ko kallonta bai yiba yafice daga falon yaje
yadauki wata motarshi black yafita yanufi zone
2 unguwar su basma. Gidansu basma gidane
babba kuma iyayenta yan boko ne nakarshe
asalima su rayuwar turai sukeyi agidansu, yana
zuwa aka bude masa yashiga yaje ya ajiye
motarsa a inda aka tanada, yafito ya shiga
gidan wanda yayi mutukar tsaruwa a falon
manyan baki ya zauna yana jiran isowarta, sai
da yashafe samada minti 20 sannan tafito taci
uwar kwalliya cikin wata bakar doguwar riga ga
uban gashin kanti har gadon bayanta ayangance
take takunta bakace sosai marar tsayi kuma
bata da hanci, oh ikon Allah masu karatu nazata
basma zatafi haka haduwa amma sai naga abin
ba haka yake ba, tana zuwa inda yake ta zauna
ajikinsa tana fadin welcome my man! Kallon so
awwab ya jefa mata sannan yace thank you my
dear! murmushi basma tayi sannan tace
yakake? Lfy my dear ya sch dafatan an gama
lfy? Lfy tafada kamar wadda bakinta yayi mata
nauyi.
KWARYA TABI KWARYA1⃣2⃣
Na UMMI A’ISHA
Kallonta awwab yayi gashi yanzu kin gama
sch saura me? Murmushi tayi saura aurenmu
kuma, yawwa my dear haka nake son ji so
yanzu zan sanar da dad dina cewar yazo suyi
magana da dad dinku ko? Eh hakan yayi,
ammafa inada wani uzuri,name? Ya tambayeta
agaskiya awwab ina son zanyi aiki kuma sannan
duk lokacin dana samu admission zan koma sch
nayi masters dina, to ai duk wannan ba problem
bane ni awajena, babu matsala zakiyi aikinki
kuma zakiyi karatu ai duk mai saukine ni dama
babban burina shine na auri mace mai class
kamar ke domin ke ta dabance, wani malalacin
murmushi tayi thanks my canal, bari naje
nadawo tafada tareda mikewa ta shige gidan
tana cike da farin ciki domin samun miji kamar
awwab tasan sai mace mai sa’ar gaske, kuma
yana da fuskar mutanen kirki dan idan basani
kayiba baka taba cewa yana shan giya balle har
kayi tunanin zai nemi matan banza, shigowa tayi
hannunta rikeda tiren silva ta zubo masa kayan
motsa baki kamar ba acikinsa shi daya zai zuba
ba, agabansa tazo ta dire farantin tana
murmushin jin dadi, tana farin cikin zata auri
awwab duk da cewa ita tasan yana shan giya da
neman mata amma hakan bai sa taji tsanarsa a
ranta ba asalima itace taganshi tana so,kusa
dashi tazauna my man amma idan munyi aure a
anan zaka barni na zauna ko inyaso Kai sai ka
rinka zuwa? Yes haka nake tunani my dear
saboda akwai gidan da dad dina yabani kyauta a
nan kusa da gidanmu so i think anan zamu
zauna saboda dad baya so nayi nisa dashi, kai
amma fa naji dadi sosai, mikewa yayi bari
nawuce gida sai munyi waya ko, tashi tayi tabi
bayansa har zuwa compound din gidan.
KWARYA TABI KWARYA1⃣3⃣
Na UMMI A’ISHA
Tsayawa tayi ta zuba masa idanu komai na
shi burgeta yakeyi domin ya hadu iya haduwa
ita kanta tasan awwab ba ajinta bane yafi karfin
level dinta kawai dai Allah ne yadorata akansa
har ya amince da soyayyarta yake sonta, kofar
motar ya bude yashiga yayi mata sallama tafara
daga masa hannu har yafice daga cikin gidan
sai da taga fitarsa sannan tayi ajiyar zuciya
tareda furta awwab kenan nida kai aurene
zamuyi irin na KWARYA TABI KWARYA tana
gama fadin haka ta shige gida. Shi kuwa awwab
gida yakoma yana zuwa yashiga wajen umma
ya tarar da ita zaune tana cin apple gefe daya
kuma nihal ce take mammatsa mata
kafafuwanta wanda ta dorasu asaman tumtum,
kusa da umma yaje ya zauna tareda cire hular
kansa juice din dake gaban umman ya dauka ya
balle murfin yafara sha amma sai yaji dandanon
baiyi masa dadi ba, dan shi yanzu giya ce take
yimasa dadi abaki amma komai dadin juice idan
yasha sai yaji babu dadi, ajiyewa yayi umma ta
kalleshi awwab kasha juice din mana, no umma
ya isheni inada juice adakina idan naje zansha,
kallonsa nihal tayi ta taba baki, kamar hadin
baki shima ita ya kalla gabansa yaji ya fadi, to
shi wai meyake faruwa ne? Duk tun lokacin
dayafara ganin yarinyar nan yaji gabansa yana
faduwa.
KWARYA TABI KWARYA1⃣4⃣
Na UMMI A’ISHA
Kallonta yasakeyi sosai kamar dai yasan ta
awani wuri amma ya kasa tuna ko a inane,
hakama muryarta kamar yatabaji sai dai ya
manta a inda yaji hararta yayi aransa yana fadin
yarinya karama sai iyayin tsiya da kwainane,
dagowa dara daran idanuwanta tayi ta wurga
masa harara, hararta shima yayi yana daddanna
wayarsa chtn yake da basma ta palm chat,
kallonta yasakeyi baki yaga ta murguda shi abin
nata ma dariya kuma yake neman bashi yarinya
sai kace tababbiya baiyi mata komai ba ta ringa
harararsa? Remote din tv ya dauka ya kamo
MBC Action yafara kallon wrestling ita kuma
nihal tanata aikin daddannawa umma kafafunta
yana nan zaune yana kallo har 9 tayi umma ya
kalla umma kira talatu ta zubo min tuwo dan
kadan,a’a ga nihal ta zuba maka mana, a’a
umma kira talatu dan Allah kira umma ta
kwallawa talatun sai gata dasaurinta tazo ta
durkusa, talatu zubawa awwab tuwo sai dai kin
san cin abincinsa dan kadan zaki zuba masa, to
ranki yadade da saurinta ta tashi zubo masa ta
kawo masa yakarba da cokali yake cin tuwon
yanaci yana kallo, jifa jifa kuma yana duba
sakonnin daketa shigowa cikin wayarsa, dahaka
har ya gama cin abincin ya tashi, dakinsa
yashiga yacire kayan jikinsa domin shi bai cika
mu’amula da manyan kayaba sai dai idan ranar
Friday ne abbansa yayi fadan har yagaji bashida
kaya sai jeans da t.shirt ko kuma boxer, wanka
yashiga yayi yafito yayi salla yaje yabude fridge
dinsa zai dauko giya amma wayam babu ita
babu alamunta tsaki yaja yasan wannan
figigiyar yarinyar ce ta kwashe masa to amma
me zatayi da ita? Wata zuciyar tace babu abinda
zatayi da ita kawai tsabar mugunta ne yasata
kwashe maka, zama yayi afalon zuciyarsa
cikeda kunci, tsaki yayi taja gashi yau baya son
fita club domin so yake yayi bacci ya huta,
dakinsa yashiga ya kwanta dakyar bacci ya
kwasheshi. Washe gari basma tayi masa waya
ta sanar dashi cewa zatazo ta gaisheda
ummansa, tashi yayi yashiga cikin gidan dakin
umma lokacin 11 dai dai yasameta suna yin
breakfast itada abbansa, tsugunnawa yayi
yagaishesu sannan yahau kan dining din shima
yahada tea yafara sha, kallon abbansa umma
tayi tace Alhaji dama ina son fada maka ka
shirya kaje gidansu yarinyar da awwab yake so
ka tambayo masa aurenta saboda iyayenta sun
bashi dama.
KWARYA TABI KWARYA1⃣5⃣
Na UMMI A’ISHA
Dan haka yanzu abin yi yarage garemu sai
mu nemo masa aurenta, kallonsa abba yayi wai
hakane my son? Yes abba hakane murmushi
abbansa yayi ato alhamdulillah insha Allahu
zanje gidansu yarinyar in Allah ya yarda, mikewa
abban yayi to ni zan tafi office hajiya Sadiya
babu wani abu ko? Mikewa tayi tabishi tana
cewa babu komai abba, kallo awwab yabisu
dashi har suka fice, dai dai lokacin nihal tashigo
falon tana sanye da doguwar riga ta shadda, ke
ina abinda kika dauka min acikin fridge?? Wani
mugun kallo ta watsa masa mai nuna alamun
baka isaba, ke nifa ba sa’anki bane kin gane?
Bana son raini idan kin saba rashin kunya kisan
a inda zakiyita amma ba anan ba, dankwalin
kanta ta turo gaban goshinta ma’ana gayawa
keya dan kwali yabaka amsa, nan da nan ya
sake kuluwa dan dai kawai shi baya dukan
matane amma da babu abinda zai hanashi
babballata tashi yayi yabar falon yakoma
dakinsa, sai waya ya yiwa umma ya sanar mata
da zuwan basma anjima. Yamma tanayi basma
tazo gidansu awwab cikin shiga tasu ta yayan
manya, an bazo gashin kanti awwab ne yafito
yayi mata jagora har cikin falon suna shiga
umma tana zaune akan sallaya da alama salla
takeyi ita kuma nihal tana lallatsa wayar umma
sallama basma tayi tanemi wuri ta zauna kamar
ba zata amsa ba ta amsa sallamar tareda
dagowa kanta ta kallesu, tsaki taja acikin
zuciyarta wai dama wannan ce basman? Lallai
ashe jinta yafi ganinta tab su awwab angamu da
aiki akan wannan yake wani rawar kafa? Harara
ta watsa musu daga shi har basman, itama
basman sai faman harare harare take tayi kamar
wacce aka zaga, maganar umma ce ta katsesu
sannu da zuwa basma cikeda yanga tace yawwa
sannu umma ina wuni? Lfy lau umma ta amsa
cikin fara’a ta dubi nihal wacce taketa faman
yatsina fuska da harare harare tace nihal kawo
mata ruwa da lemo, to umma tafada batare da
ta tashi ba sai da tagama jan ajinta sannan ta
tashi hakan ba karamin batawa basma da
awwab rai yayi ba, ruwa roba daya ta dauko da
lemo gwangwani daya sai tsurar cup guda daya
ko a faranti bata doro ba tazo gabansu ta ajiye
akan center table takoma mazauninta wato
kujerar datake kallonsu ta zauna ta dauki wayar
umma taci gaba da lallatsawa awwab ya kulu
ya kulu, ita kuwa basma haushin nihal ne ya
cika ranta kamar taje ta shaketa takeji, kuma ita
a iya saninta awwab bashida kanwa su 2 ne
kadai awurin iyayensu daga shi sai yayarsa Anty
jamila to a ina suka samo wannan yarinyar mai
kama da aljana? Wani kishi taji ya turnuketa
marar misaltuwa kara daga idonta tayi takalli
awwab wanda shi kuma nihal yake kallo cikeda
tsana da jin haushinta itama nihal din su duka
biyun haushin su takeji in banda harara babu
abinda datake aika musu, to meye dalili? Nidai
ummi A’isha banida amsa.
[1/12, 8:36 AM] Ummi A’isha: [1/12, 8:29 AM]
Ummi A’isha: KWARYA TABI KWARYA1⃣6⃣
Na UMMI A’ISHA
Daure fuska awwab yayi yayin da itama
basma ta daure tata fuskar, umma ce tayi
magana tace basma kisha ruwa, to umma
nagode tafada tana mai cigaba da hararar nihal
ita kuwa nihal basu ma isheta kallo ba daga
basman har awwab din gani take bata da
lokacinsu amma haka kawai taji basman nan
bata burgeta ba kamar yadda itama basman taji
sam nihal bata yi mata ba shirune ya dan gitta
afalon kafin umma tace basma ashe kuma an
kammala karatu ko? Washe baki tayi wlh kuwa
umma nagama yanzu sai maganar aiki kuma,
kallonta nihal tayi tareda taba baki daidai
lokacin awwab ya kalleta ya harareta bata
kyaleshi ba itama ta watsa masa harara, ganin
abin yayi yawa yasa basma mikewa umma ni
zan tafi tashi umma tayi to jirani ina zuwa
dakinta tashiga ita kuma nihal ta dubesu ta kara
tabe baki azuciyarta tana cewa wlh sam baku
wani dace da juna ba, umma ce tafito hannunta
rikeda leda wadda tasako turarrurruka da man
shafawa aciki tabawa basma, gashi basma
nagode kigaida mutanen gida Allah yayi albarka,
amin nadawo tafada tana murmushi wucewa
tayi awwab yana binta abaya sai da sukaje daf
da kofa nihal tace agaida gida bakuwa, ko
waiwayowa basuyi ba bare su tanka mata ita
dinma dama tafada ne domin ta tsokane su to
kuma sai akayi sa’a basu kulata ba. Suna
fitowa harabar gidan basma ta dubi awwab my
man wacce yarinya ce waccan? Meye alakarku
da ita? Kai ya girgiza wlh yadda kika ganta haka
nima naganta ban san wacece ba, sai dai ina
son nasan meye alakarmu da ita amma jinina
bai hadu da ita ba saboda bata da kunya
fitsararriya ce ta karshe, baki basma ta taba ai
naga alamar marar kunya ce sai wani kallon
banza take yimana sai kace wasu sa’anninta,
wlh dan kawai nice nazo ne badan haka ba da
sai na tsinka mata mari murmushi awwab yayi
babu ruwanki da ita ki barni da ita ni zan koya
mata hankali,kallonsa basma tayi ina fata dai
baka sakar mata fuska? Haba ina ruwana da ita
nifa sau 2 kawai nataba yimata magana tun
zuwanta gidan nan tsakanina da ita harara ce.
KWARYA TABI KWARYA1⃣7⃣
Na UMMI A’ISHA
Yawwa my man haka nakeso saboda dama
bana so kabata fuska ko kadan domin idan taga
fuska zata iya cewa tana sonka, no no kima
daina wannan tunanin mezanyi da wannan
karamar yarinyar, yarinyar da har yanzu bata
gama cika mace ba murmushin farin ciki basma
tayi shiyasa ko yaushe sonka karawa yake
acikin zuciyata domin kai acikin maza na
dabanne you are special one, kanada class da
iya taku ba irin sauran maza bane murmushi
yayi to yanzu sai yaushe ni kinga gobe nake son
komawa Ibadan, ok to shikenan Allah ya kaika
lfy zamuyi waya later, motarta ta bude tashiga
ta tadata tadaga masa hannu ta fita daga
gidan, juyawa yayi yakoma side din umma,
zaune ya hango nihal tana yankewa umma
farcenta tsaki yaja yaje kan kujera ya zauna
yakalli umma,umma wai me aka dafa agidan nan
ne? Awwab dashishi akayi, to ai umma ni bana
son wannan abin dan Allah sa talatu ta dafa min
indomie duk da ba lallai ne ma in iya ciba ni kin
sanni da tsantsami, to bari nihal ta dafa maka
shiru yayi yadauki remote ya kunna tv, nihal bar
min yankan farcen kije kitchen dina ki dafawa
awwab indomie inji umma, tashi tayi har zata
fita umma tace nihal kar kisa yaji dayawa
saboda awwab bai son yaji, to umma tafita ta
shiga kitchen, acikin mintunan da bazasu fi 5 ba
ta shigo da plate a hannunta da spoon tazo ta
ajiye agabansa ko kallonta bai yiba itama bata
kalleshi ba, kusa da umma takoma ta zauna
lokacin umman har tagama yanke farcen, kamar
kada yaci amma ganin yana jin yunwa yasa
yadauki cokalin yadebi indomien yafara ci jin
harshensa yayi kamar zai cire saboda yadda
tasha attaruhu, ajiye spoon din yayi yatashi
yabude fridge ya dauko juice din gwangwani ya
dan kurba ya ajiye dakyar ya iya magana umma
bari naje naci abinci a restaurant daga can zan
wuce nasha lemo harararsa nihal tayi aranta
tace zakaje kasha giya dai ba lemo ba, to
awwab adawo lfy inji umma.
KWARYA TABI KWARYA1⃣8⃣
Na UMMI A’ISHA
Sai da ya harari nihal sannan yafita cikeda da
jin haushin nihal yanufi dakinsa yayi wanka ya
sake kaya, dark purple din riga mai dogon hannu
da bakin wando jeans yafesa turarensa na ice
hot tadauki gun dinsa yanufi motarsa BMW blue
wadda takasance mai dark black din glass, yana
shiga yadaga kujerarsa ya ajiye bindigar sannan
yatasheta ya fita,nihal kuwa lokacin da awwab
yafita ta kalli umma tace umma bafa Lemo zaije
yasha ba, wlh.. Umma ce ta katseta hanyar
cewa bana son surutu nihal kar nakarajin
wannan maganar a bakinki, shiru nihal tayi
tareda tashi ta wuce dakin umma. Yana fita ya
saki kida a motarsa wakar d banj ya kunna cikin
before in love, a hankali kidan yake tashi har ya
isa wani katafaren wurin cin abinci hot pot
restaurant and catering services, a kan titin mai
tama,a waje yayi packing din motarsa yafito
yashiga,shinkafa da miya yayi order sai dan
salad aka kawo masa yaci ya biya, yana shirin
fitane yaci karo da zaituna, zaituna yarinyarsa
tunda dadewa, kallonta yayi cikin mamaki
zaituna kece? Murmushin jan hankali tayi nice
ranka ya dade, yakake? Normal yagida, gida lfy,
yanzu ina zakije? Zanje gidane ko kana so ne
narakaka?. Yes idan kikayi haka zanji dadi, ok to
muje,jerawa sukayi har inda ya ajiye motarsa
suka shiga bai zame da su ako ina ba sai Dan
Musa guest lodge,suna zuwa yakarbi mukullin
daki suka shiga dubansa zaituna tayi canal
dama bakayi aure ba? Ke yakamata nayiwa
wannan tambayar dan tuntuni nayi zaton kinyi
aure, gefen fuskarsa ta shafa no ina tareda kai
tayaya zan iya auren wani, ai duk maza ganinsu
nake kamar mata yan uwana kai kadaine kawai
namiji a wurina, murmushi yayi tareda riko
kugunta kar fa ki yaudareni zaituna idonta ta
fara sannan tace babu yaudara tsakanina dakai
ka yarda da abinda na fada, janta yayi suka
fada gado. Sai wurin karfe 5 sannan suka dawo
hayyacinsu alokacin awwab bacci kawai yake ita
kuma zaituna tazuba masa ido cikeda so inama
ace awwab mijin tane haka kawai take rayawa
acikin zuciyarta motsi yayi yafarka daga dan
baccin da yayi yatashi yashiga toilet yayi wanka
yafito tareda fara tashin zaituna hannunsa tariko
tareda kara jawoshi jikinta nanfa suka koma
ruwa
KWARYA TABI KWARYA1⃣9⃣
Na UMMI A’ISHA
Sai da suka dada shafe awanni suna
shedancinsu sannan suka shirya suka fito,
abakin wani titi yayi dropping din zaituna tare da
rubuta mata cheque na wasu makudan kudi
masu yawan gaske. Wani gidan saida giya ya
zarce yasiyi wata yar karamar robar giya yafito
yashiga motarsa yadan kurbi giyar kadan
sannan ya rufe ya boye sauran akasan kujera,
gidansu ya wuce lokacin karfe 8 nadare yana
shiga ya wuce wurin abbansa yagaisheshi anan
ne abban yake yi masa albishir da cewa yaje
gidansu basma sun ganada mahaifinta, dadi
awwab yaji domin shidai yana son basma
saboda iya jan ajinta, mikewa yayi yafito zuwa
sashen umma nan ya taradda ita zaune da
fitsararriyar yarinyar nan nihal yana shiga suka
hada ido da nihal take ya dalla mata harara
itama ta rama kujerar da umma take kai yaje ya
zauna kamar wanda zai shige cikinta, awwab
kadawo? Eh umma yanzu daga wurin abba nake
yace min yaje gidansu basma dazu harma sun
gama magana da mahaifinta murmushi umma
tayi eh haka yagaya min ai yanzun nan yafita
daga cikin falon nan, komai ya daidaita saura
yanke ranar aure kawai kansa ya kwantar ajikin
kujera, oh nima nakusa zama mai gida kenan,
dariya umma tayi dadina dakai rashin kunya,
yanzu agabana kake fadar zaka zama maigida?
Dariya awwab yayi sorry ummana ai gani nayi
kece abokiyar shawarata kuma abokiyar zancena
shiyasa kikaji na fadi haka, to ai shikenan
awwab Allah yakaimu lokacin, amin umma
wayar hannun nihal ce tayi kara taduba tareda
dagawa cikeda yanga tafara magana hello
hamid, ok bari zan kiraka anjima, awwab ne yaji
gabansa yafadi kallonta yasakeyi tana sanye da
leshi fari mai ratsin baki ajiki, ta turo dan
kwalinta gaban goshi hakan yabashi damar
hango tulin gashin kanta data tufke,harara ya
jefata mata sannan acikin zuciyarsa yace
wannan yarinyar yar duniyace da alama, ita
kuwa nihal sam bata ma san yanayi ba domin
hankalinta yana ga wayar umma datake
hannunta sai lallatsawa takeyi, ko hararta da
yayi bata gani ba domin da tagani shikansa
yasan sai ta rama.
KWARYA TABI KWARYA2⃣0⃣
Na UMMI A’ISHA
Kallonta yaci gaba dayi ita kuma tanata
daddana wayar dake hannunta da alama sakon
txt massage take turawa, she’s very cute and
beautiful yafada acikin zuciyarsa wata zuciyar
tace yes is true ammafa muguwa ce da alama
saboda dazu taji umma tace bakason yaji shine
tacika attaruhu a girkin dan kar kaci dai dai
lokacin ta dago dakanta ta kalleshi harara ta
cilla masa amma shi sai yayi murmushi karo na
farko dataji ya burgeta domin tun farkon ranar
data fara ganinsa bai taba yimata murmushi ba
sai dai aikin harara amma yau gashi abin
mamaki itace ta harareshi bai ramaba a
maimakon ya rama ma sai ya aika mata da
sakon murmushi mai tausasa zuciya, hararsa
takara yi aranta tace good naji dadi tunda yanzu
ka gane nima ba kanwar lasa bace da alama
kagane cewa u are d one that loose d game
shiyasa kafara sakkowa but naso ace munci
gaba da buga wasan so that sai agane waye
winner, maganarsa mai dadi tajiyo yana yiwa
umma magana, umma wai ni kwana 2 ina baba
mai gadine? Tunda nazo ban ganshi ba, eh wlh
awwab yazo yayi min sallama cewa zaije gida
dansa bashida lafiya, ayya umma inane kauyen
nasu? Wlh awwab sai dai ka tambayi idi mai
gadi ni ban san garinsu ba, ok to idan idin
yasani sai kawai na aikeshi ma ya kai masa
sako, murmushi umma tayi Allah yasaka da
alkhairi Allah yayi maka albarka Allah ya biya
bukata, amin ummana kinyi min babbar addu’a
domin inada wani babban buri arayuwata kuma
inada muhimmiyar bukata awurin ubangijina,
kallonsa nihal tayi ta taba baki ta dauke
kanta,murmushi yayi acikin zuciyarsa yace
yarinya zanyi maganinki ni banida time din da
zan tsaya ina musayar harara dake,umma ya
kalla umma zan sha tea da sauri ta kalli nihal,
nihal tashi ki hadowa awwab tea, mikewa tayi
tana cikeda takaici kinga kisa min lemon tsami
aciki kuma iya sugar da Lipton kawai zakisa
bata kulashi ba tafita tashiga kitchen, lallai
gayen nan dan rainin hankaline nifa ba yar aikin
gidansu bace da zai rinka sani bauta amma
zanyi maganinsa dariyar mugunta tayi dai dai
lokacin data gama hada tea din tadauka acikin
glass cup takai masa yana nan zaune a inda
tabarshi amma umma bata wurin ta tashi, akan
stool din dake gabansa ta dire tea din takoma ta
zauna tazubawa tv idanu tana kallon drama
sahrul asmar a tashar MBC Bollywood sai da
awwab yagama jan ajinsa sannan ya dauki tea
din yakai bakinsa kurba daya yayi yadawo dashi
saboda gafin gishiri da yaji kamar zaiyi magana
dariya nihal tafara kamar me sannan tace yadai?
Murmushi yayi yafara kwalawa umma kira
umma! Umma!.
[1/12, 8:47 AM] Ummi A’isha: [1/12, 8:40 AM]
Ummi A’isha: KWARYA TABI KWARYA
2⃣6⃣
Na UMMI A’ISHA
Shirin biki akeyi sosai agidajen biyu
musamman ma gidan su basma,basma ansha
bleaching anyi fari dau ga tarkacen gyara da
aka tanada domin a damfari awwab, shikuwa
awwab yana can Ibadan bai samu damar zuwa
ba. Ita kuwa nihal bakin ciki kawai takeyi da
wannan auren na awwab domin haka kawai bata
san dalili ba taji ta tsani wannan auren, amma
gidan kullum kaya ake shigowa dasu wadanda
za abukata alokacin hidimar bikin, yanzu ma
kwance take akan dan madaidaicin gadonta duk
ranta abace yake har wata yar rama tayi, karar
saukewa kaya take jiyowa a falo da alama irin
kayan da ake kawo wane na bikin tsaki taja
takara gyara kwanciyarta wato awwab shi
wannan yarinyar burgeshi take? Hmm dama ai
duk namijin da yafiya yaudara to akarshe
mummuna yake aura kwanciyarta ta sake
gyarawa duk tarasa abinda yake yimata dadi.
Satin biki yana kamawa awwab yazo lokacin
nihal ta tattara tabar gidan tayi tafiyarta,an
shirya karya abikin kuma an kashe kudi sosai,
ranar juma’a aka daura auren awwab da basma,
abokansa sojoji suka shirya masa fareti a aminu
kano square agarin abuja, ana tashi aka tafi
dinner akaci aka sha daga nan aka watse.
Washe gari gidajen biyu sukayi wuni da daddare
aka kawo amarya gidanta, gidan dayasha kayan
alatun more rayuwa kamar a turai domin an
kashewa gidan kudin gaske kuma gidan ya tsaru
matuka, ajikin gidansu awwab gidan yake, yan
kai amarya suna watsewa awwab ya shigo inda
amaryarsa take nan suka gabatar da dukkan
abubuwan da Ma’aurata suke gabatarwa adaren
farko, suna gamawa awwab yaje gareta ya fara
nuna mata soyayya amma kuma sai ya sameta
ba a budurwa ba tsaki yaja yatashi ya zauna
yafara nazari, cikin tuhuma basma ta kalleshi
my man meya faru? Banza yayi da ita hannunsa
tajawo ya fisge, haba awwab ya zaka min haka?
Idan kai ka gamsu ai ni ban gamsu ba, harara
ya watsa mata ke malama ki rabu dani kinji, wlh
kin bani mamaki ashe dama ke yar iska ce?
Zabura tayi ta tashi me kake son fada ne? Kaga
awwab kar ka yarda kayi min sharrin zina, to ai
ba karya nayi miki ba kinyi ne domin ba a
cikakkiyar mace kika zo min ba yafada cikin
bacin rai.
KWARYA TABI KWARYA2⃣7⃣
Na UMMI A’ISHA
Mamakine ya kamata yanzu duk wadannan
abubuwan da tayi amfani dasu sai da awwab ya
gane? Boye mamakinta tayi tace look awwab
agaskiya bazan juri wulakanci ba kuma ashe
kenan kaima manemin matane shiyasa kagane
ni ba budurwa bace, domin idan kai cikakken
saurayi ne baka taba kusantar wata mace ba
tayaya zaka san na rasa budurcina? Tashi
awwab yayi yafice yabar mata dakin yakoma
dayan ransa abace zuciyarsa sai faman
tafarfasa takeyi, shidai yasan basma bata zo
masa da martabar ta gidansa ba haka ya zauna
yana cikeda takaici, ita kuwa basma koda
awwab ya fita komawa tayi tai kwanciyarta
babu abinda yadameta ba tareda damuwar
komai ba tafara shakar baccinta yayinda shi
kuma awwab baccin ya gagari idonsa yanda
yaga rana haka yaga dare. Washe da safe aka
turowa da basma yan aiki guda uku daga gidan
iyayenta shi dai awwab bai ce komai ba amma
yasan yafara samun matsala da basma tun
daga daren jiya, mai shara da wanke wanke
daban mai yimata girki daban sannan mai
yimata wanki da guga da sauran ayyuka daban,
kowaccensu aikin da zatayi tafada, yatsina fuska
basma tayi tareda nuna musu B/Q tace suje can
sukai kayansu dan acan zasu zauna babu musu
suka kinkimi kayansu suka fita, suna fita ta
koma ta kwanta yayinda shi kuma awwab yafice
daga gidan yana cikeda damuwa da bacin rai
kansa tsaye ya wuce wani guest lodge yana
zuwa yasiyi giya roba biyu ya karbi mukullin
daki yashiga ya rinka shan giyar nan har sai da
ya shanye sannan ya kwanta akan gadon dakin
yakama bacci. Abagangaren gidansu kuwa baki
sun fara bajewa masu sanya albarka sunyi sun
tafi, alokacin gidansu basma suka aiko da kayan
gara mota guda wanda yawansu zai iya cika
store daya, godiya iyayen awwab sukayi tareda
bada tukwici. Sai da yamma tayi sannan awwab
yafarka daga baccin daya daukeshi yadawo gida
yayi wanka yashiga cikin gidansu umma ya gani
da sauran bakin da basu tafiba, gaisheta yayi
yawuce side din abbansa suka gaisa nan abban
yafara yi masa nasiha kan ya zauna lafiya da
matarsa kuma yayi hakuri akan duk abinda
zatayi masa domin mata sai da hakuri kuma
yazama mai rufe sirrin iyalinsa, kansa ya dukar
akasa yace insha Allahu abba zan kiyaye kuma
zanyi aiki da dukkan abubuwan daka fada min,
Allah yayi maka albarka awwab sannan kuma
dan Allah karage wannan shan giyar da neman
matan da kakeyi domin kaga yanzu ka girma
nan ba da jimawa ba zaka zama mahaifin wasu
to kaga yanada kyau kazama uba nagari irin
uban da kowanne da zai yi alfahari dashi kaji?
Eh naji abba in sha Allah zan kasance mutum
nagari kamar yadda kake min fata.
KWARYA TABI KWARYA2⃣8⃣
Na UMMI A’ISHA
Dafa kansa mahaifin nasa yayi tareda fadin
Allah yayi maka albarka awwab Allah ya
albarkaci rayuwarka, amin abba yafada yana
murmushi tashi yayi yafita yakoma gidansa yana
shiga yasamu basma zaune afalo tana shan
juice ko kallonta bai yiba yashige daki, sai da
tagama shan juice din sannan ta tashi tabishi
cikin dakin tasameshi kwance kan gado yayi
rigingine kansa tafada gamida sakin kukan kissa
dan Allah awwab kayi hakuri wlh ni ban taba
aikata iskanci ba ina jin dai hawan keken da
rinka yine lokacin ina yarinya yaja min haka,
takarasa maganar cikin kuka, rungumeta yayi
yafara share mata hawayen dahaka ta samu
nasarar rudashi har ya amince da ita. Zama
sukeyi na babu yabo babu fallasa har na tsawon
sati 1 alokacin awwab ya shirya zai koma
ibadan itama basman asatin da zai kama zata
fara fita aiki, wanka yayi yafito lokacin basma
tana kwance akan gado ta bararraje shiryawa
yafarayi ya kalleta basma yunwa fa nake ji ki
tashi ki sama min abinda zanci, oh sorry my
man bari nakira mary ta dafa maka indomie, a’a
kibari nadawo tukunna yanzu gidan umma zanje,
brown colour din jeans yasaka da bakar t.shirt
mai kyau an rubuta its a new day agaban rigar,
turaren touch me yafesa yafito kallon burgewa
basma tabishi dashi hakika ka hadu mijina
tafada tana dariya, gidan umma yashiga babban
falon yafara shiga yatarar da yan aikin gidan sai
kai da komo sukeyi, sama ya hau falon umma
anan ya sameta itada nihal suna zaune, sallama
yayi yashiga yazauna yadan duka ya gaida
umma, ina basman? Tana nan lfy ? Lfy lau take
umma yafada yana mai kallon nihal wacce tayi
kicin kicin ta bata rai tareda daure fuska, kanta
ta dauke ta mayar kan tv, murmushi awwab yayi
aransa yace sarkin tsiwa kin dawo kenan, umma
nima gobe nake son komawa ibadan,ah har
hutun naka ya kare awwab? Eh umma itama
basman nxt week zata fara zuwa aiki tasamu
aiki a nta, to Allah ya sanya alkhairi, amin
umma, dan Allah umma arinka dai kulawa da ita
tunda ni kinga ni bana gari, jiyowa nihal tayi ta
harareshi acikin zuciyarta tana cewa kijishi sai
kace wata karamar yarinya wai arinka kulawa
da ita hararshi taci gaba dayi tana mai jin
haushinsa shida basman, dan tsaki taja acikin
ranta kema umma kece kike biyashi ai shiyasa
yake samun damar yiwa mutane iyayi.
KWARYA TABI KWARYA2⃣9⃣
Na UMMI A’ISHA
Kallonta kawai awwab yakeyi shidai a duniya
yarasa me yayi wa yarinyar nan da yasa take jin
haushinsa,hada ido sukayi ta wurga masa
harara,umma ya kalla umma dan Allah bakida
garin kunu? Wlh kunu nakeso, da akwai awwab,
kunun zakasha?eh umma, kallon nihal umma
tayi nihal maza jeki ki damawa awwab kunu
garin kullun yana nan acikin farin dan karamin
bokitin nan, tashi nihal tayi ta wuce binta da
kallo awwab yayi tana sanye da atamfa yelluwa
anyi mata dinkin bubu na zamani tasaka bakar
hula akanta wanda ta bayyanar da gashin kanta
kitchen tashiga ta kunna gas ta dora ruwan zafi,
minti biyar yatafasa tadama kunun gyadar ta sa
sugar tazuba peak milk gwangwani daya tazuba
masa acikin dan madaidaicin kofin tangaram
tanayi tana mita shi wannan mutumin sai son
saka mutane aiki,idan kunun yakeso yaje
matarsa ta dama masa mana dahaka tagama ta
dauko tashigo falon yana zaune inda ta barshi
yanata faman lallatsa wayarsa gaba daya
hankalinsa ya tattarashi akan wayar, mika masa
kofin tayi batareda tayi masa magana ba
shikuma sam bai kula da ita ba tsaiwar taci
gaba dayi shikuma yanata daddanna waya ganin
yaki karba yasata juyawa kitchen tamayar da
kunun ta ajiye itadai bazata yi masa magana ba
balle ya yarfata,domin bazata taba manta
wulakancin da yayi mata ba ranar data
gaisheshi, falon ta dawo zata zauna taji yace ina
kunun? Fasa zaman tayi takoma kitchen ta
dauko takawo masa batareda tayi masa magana
ba karba yayi yace thanks yakai kunun ya kurba
wani irin gardi da dadi yaji kunun yayi masa,
yanasha yana chtn bai san lokacin da ya shanye
ba sai da ya kalli cikin kofin yaga wayam,
kallonta yayi lokacin tana canja tashar satellite
daga tashar zee tv zuwa zee cinema tana
kamowa taga ana rungume rungume baki ta rike
tareda saurin canja tashar zuwa sunna tv hakan
datayi ba karamin bawa awwab dariya yayi ba,
kinga ungo kofin nan mayar kitchen tashi tayi ta
karba ta wuce daga nan bata dawo falon ba tabi
ta kofar baya ta fice takoma dakinta tana cewa
bari yanzu kuma naga wacce zaka aika, nan
awwab yasha zamasa har umma tafito suka yi
hira sai da aka kira salla sannan yayi mata
sallama yakoma side din Abba shima sallamar
yayi masa kasancewar gobe jirgin karfe 7 nasafe
zai bi. Gidansa yakoma yayi sallar mangraruba
yashiga dakin basma tana kwance tana waya da
mominta kusa da ita yaje yazauna yakama
hannunta ya rike cikin nashi, sallama tayiwa
mominta takwanta ajikinsa my man ya akayi
ne? Gobe iwar haka sai ni kadai ka tafi ka barni,
fuskarta ya shafa karki damu my dear babu
komai zan dawo bazan dade ba.
KWARYA TABI KWARYA3⃣0⃣
Na UMMI A’ISHA
Wuyansa ta shafo Allah yadawo min dakai
lfy, amin my dear yafada yana mai nutsa
hannunsa cikin tulin gashin kantin dake kanta.
Washe gari da sassafe awwab yatafi ibadan
aranar da yamma basma tashiga gidansu
awwab dan ta gaishe da umma tana shiga ta
hango nihal afalo ta mike akan kujera tana
kallon wani Indian film mai suna vadaraha, film
din yayi mutukar burgeta tana sanye da bakar
doguwar riga yar kanti mai santsi rigar tayi
mata das kamar dan ita aka dinkata kanta babu
dankwali ta tufke gashin kanta sannan ga wata
katuwar kalaba datayi kwaya daya a gaba tana
daga kwance takamo gashin tayi kalabar, cikin
jin haushinta basma tasamu wuri ta zauna jin
motsin mutum yasa nihal waiwayowa basma
tagani zaune sai cika take tana batsewa mayar
da kanta tayi takwanta taci gaba da kallonta
batareda tayi mata magana ba, suna nan zaune
shiru babu wanda yakula wani har umma
tasauko ganin basma yasa tafara murmushi
barka da zuwa yata, yanzu kika shigo? Eh
umma ban jima da zuwa ba nazo naga falon
babu kowa ne shiyasa nace bari nazauna
najiraki, ayya ai da kin hawo saman ina nan
afalo babu abinda nake saukowa kasa tayi
tagaida umma sannan takoma saman kujera
tazauna taci gaba da aikawa da nihal harara
wadda ita nihal din bata san tanayi ba, shiru
shiru batace zata tafi ba ita kuma nihal burinta
taji tace sai anjima amma shiru dan haka sai ta
tashi tahau sama takoma falon umma takwanta
taci gaba da kallonta ita kuwa basma sai da ta
dade sosai sannan tayiwa umma sallama. Batun
awwab kuwa tun lokacin daya koma ibadan yaci
gaba da shan giyarsa da bibiyar mata duk inda
yaga kykkyawa sai ya bita wasu kuma sune
suke kawo masa kansu da kansu amma duk
wanda yake cikin barikin nan yasan awwab
mugun manemin matane kuma cikakken dan
giya, sai dayayi sati 2 bai zoba asati na uku ne
yashiryo yanufo abuja jirgin karfe shida yabiyo
dan haka shida da rabi agarin abuja tayi masa.
Yana zuwa ya shiga gidansa daga shi sai kayan
jikinsa sky blue din riga t.shirt mai gajeren
hannu da bakin jeans sai yar karamar bindigarsa
wacce baya rabo da ita kamar koda yaushe
kamshin touch me yakeyi, dakinsa yafara shiga
kaca kaca babu gyara sannan yafito ya shiga
dakin basma itama dakin nata ba a kimtse
yakeba kuma da alama bata gidan, falo yadawo
yazauna ya danna kararrawa dagudu mary tazo
tazube agabansa, ina basma? Sir bata dawo
daga office ba, tun yaushe tafita? Sir since
around 11 in d morning tashi kije yafada tareda
mikewa yatafi zuwa gidan umma, amma fa yaji
haushin rashin samun basma ga wata irin
yunwa da yakeji, bari tadawo bazan yarda da
wannan yawon ba.
[1/12, 8:48 AM] Ummi A’isha: [10:21AM,
10/22/2015] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
Na UMMI A’ISHA
3⃣1⃣
Fitowa yayi ransa gaba daya yagama baci
da lamarin basma yana shirin fita yaga motarta
ta kunno kai fasa fitar yayi yakoma cikin gidan
ya tsaya yana jiran shigowarta ahankali tafito
daga motarta tabishi cikin gidan, zaune ta
taredda shi afalo welcome my man tafada tana
farfara idanuwanta thank you yafada yana
kallonta, daga ina kike? Cikin murmushi tace
daga aiki nake, wannan wanne irin aiki ne tun
safe har la’asar? Haba awwab kaima fa kasan
yadda aiki yake dole wani lokacin sai mutum
yayi overtime, look basma agaskiya yakamata ki
canja tsarin aikinki yana dakyau kiyi adjusting
din time dinki, oh sorry my man insha Allahu zan
gyara, to yanzu ni yunwa nakeji me zan samu
naci? Wash nima wlh da yunwar nadawo amma
bari nakira selesina ta sama mana abinda zamu
ci, kararrawa ta danna sai mary dagudu tazo,
mary bake nake nema ba ki turo min selesina
yes ma! Tafada tareda mikewa tafice shidai
awwab shiru yayi yana tunanin halayyar basma
sam bata son yin aiki ko kayanta idan tacire nan
zata watsar dasu sai dai su mary su dauke su
gyara tunda tazo gidan nan bata taba yin wani
aiki ba balle girki hatta ruwan zafi sai dai adafa
akawo mata bata da aiki sai bacci, selesina ce
tashigo tadurkusa gani anty, selesina kije ki dafa
min indomie guda 3 kisa kifin gwangwani guda
daya ok ma! Dasauri tamike tafita ita kuma
basma ta dauki handbag dinta tashiga dakinta
yayinda awwab yamike akujera yafara daddanna
wayarsa shidai mutum ne mai kyankyami da aji
sannan kuma duk inda dan gayu yakai cikakken
namiji mai class da kwarjini to awwab yakai
amma sai gashi basma tana neman maidashi
mai araha.
KWARYA TABI KWARYA
3⃣2⃣ Na UMMI A’ISHA
Yana nan zaune har selesina tagama
takawo tana kwallawa basma kira cewar
tagama, fitowa tayi daga dakin tana daure da
zani daurin kirji tajawo abincin ta ajiye agaban
awwab man muci tashi yayi yasa cokali yadiba
yaci gishiri mal kamar zai yi magana spoon din
ya ajiye yace zaije gidan umma kallonsa basma
tayi, abincin fa? Nakoshi yafada tareda ficewa
yanufi gidansu yana shiga falon umma yatarar
da ita zaune nihal tana yimata tsifar kai, sannu
umma yafada yazauna akusa da ita yawwa
awwab sannu da zuwa, gaisawa sukayi yadan
saci kallon nihal duk tabi ta bata rai kamar
wadda taga mutuwarta ita tunda yayi auren nan
take mitukar jin haushinsa duk taji ta washe shi
sam bata son ganinshi shida mummunar
matarsa,hankalinsa ya maida kan umma, umma
yunwa nakeji wlh, cikin kulawa umma tace to ai
da abinci akwai shinkafa da miya akwai dambun
shinkafa wanda nihal tayiwa abba, wanne
zakaci? Umma abani dambun, to nihal maza
kawowa yayanki abinci tashi tayi ta harareshi
tafita taje ta zubo masa tahado da ruwa da juice
takawo masa ta ajiye, budewa yayi dambun yayi
kyau gashi washar washar dashi sannan yasha
albasa da zogale dambune irin nagargajiya diba
yayi yafara aikawa cikinsa gaskiya dambun yayi
yafada acikin ransa baifi rabi yaci ba yature filet
din domin baya da cin abinci dayawa ruwan
kawai ya kurba amma juice din ko tabashi bai
yiba dan baya shansa sosai, kallonsa umma tayi
har ka koshi? Yakamata ka rinka cin abinci
gaskiya, wlh umma ahakan ma naci dayawa
yafada yana ciro cingum daga cikin aljihun
wandonsa yabare yajefa cikin bakinsa yafara
tauna ahanlali, baki nihal ta tabe azuciyarta
tana cewa jishi sai kace wani mace, kana namiji
kana abu sai kace mace ni nayi mamakin ma ta
yadda ka iya zama soja domin dukkan
kamanninka na yan hutune marassa aikin
wahala, domin kallo daya za ayi maka agane kai
dan hutune, tashi yayi yana maida wayarshi
aljihun jeans dinsa yacewa umma bari naje
wurin abba amma zan dawo kallonsa nihal tayi
ya wani rausayar da kai yafita, yana fita ta kalli
umma, wai umma shi wannan yaushe yazama
soja? Murmushi umma tayi tun shekaru 3 baya
lokacin yagama degree dinshi yana zama soja
kuma yakoma ya iyo masters dinshi,ba karamin
soja bane a babba yafito shiyasa idan kin ganshi
bazaki taba cewa soja bane.
KWAARYA TABI KWARYA
Na UMMI A’ISHA
3⃣3⃣
Girgiza kai tayi hakane kam umma sai dai
idan kaganshi da kaki sannan zakasan sojane,
kuma yadace da zama sojan sai dai shi dan
hutune tafadi hakan acikin zuciyarta suna nan
zaune yadawo ko zama baiyi ba yayiwa umma
sallama yace zai koma gida kuma gobe da
sassafe zai tafi ibadan akwai aikin da zaije yayi
addu’ar neman tsari umma tayi masa sannan
tace adawo lfy, amin umma yafada yajuya
yafita, bayansa nihal tabi da kallo oh kai kam
badai tsayi ba sa’arka daya bakada rama
dayawa, yana fita ko cikin gidan bai shiga ba
yadauki mota yafita bai zame ako ina ba sai
gidan giya anan yadamu ya dan ragewa kansa
zafi injishi da fada, giyar roba yasha yayi tatil
sannan ya dawo gidansa lokacin basma ta dade
da yin bacci, afalo ya zube cikin kujera yafara
bacci irin na mashaya barasa can acikin barcin
nasa yafara wani irin mafarki wannan yarinyar
tana binsa da gudu ga wuka a hannunta suna
cikin gudunne suka shiga wani bakin daji gashi
yagaji ana cikin haka sai ga wata mummunar
mata ta bullo masa hannunta rikeda takobi tana
zuwa ta daga zata sara masa sai ga wannan
yarinyar tazo, tana zuwa ta kareshi suka fara
fada da daya matar har Allah yabawa yarinyar
nasarar kashe wannan matar, tana kasheta ta
juyo gareshi dama alla alla yake ta jiyo domin
ya samu damar ganin fuskarta amma tana
jiyowa yayi firgigit ya farka zama yayi duk ya
jike sharkaf da gumi duk kuwa da cewa falon
katange yake da na’urar sanyaya daki wato a.c
tunani yafara yi aransa wannan mafarkin me
yake nufi? Kodai matan da nake bini? To ai dole
ne nabi mata domin mata ababan sone kuma
sun cancanci abisu, sai dai wannan mafarkin na
yau yafi na kullum razanashi, agogon falon ya
kalla karfe 1 dai dai nadare sai alokacin yatuna
cewa bai yi salla ba tashi yayi yashiga dakinsa
wanda yake a hargitse kamar ba nasa ba wai
duk gayun nan nasa amma dakinsa kamar na
umbo umbo dan rashin gyara shi kansa toilet
din akazance yake haka ya daure yayi wankan
yadauro alwala yafito.
KWARYA TABI KWARYA
Na UMMI A’ISHA
3⃣4⃣
Shiryawa yayi ya gabatar da sallar da take
kansa yatashi ya koma falo domin kyankyamin
dakin yake ji, yana nan zaune yanata faman
tunani har asuba tayi yatashi yayi salla sannan
yafara shirin tafiya, sai da ya shirya tsaf sannan
ya nufi dakin basma inda take kwance sai kace
macacciya sai bacci take yi tabata yayi tareda
girgizata basma! Basma! Cikin magagin bacci ta
bude idonta my man har ka tashi? Eh ni zan tafi
sai munyi waya, ok to Allah ya kiyaye hanya
tafada tajuya ta gyara kwanciyarta, fita yayi
daga dakin babu abinda yadauka in banda
bindigarsa da phones dinsa yanufi airport. Tunda
yakoma ibadan yaci gaba da harkokinsa kullum
sai yaje club, ga neman matan tsiya kamar me
tuni ya manta da basma ko waya baya yi mata
sai dai idan itace takirashi kuma kullum idan
yahau online sai yaganta tana online ya rasa da
wadanda take chtn dan sai takai karfe dayan
dare tana chtn wani lokacin sai yayi mata
magana sannan zata sauka, wasa wasa sai da
yayi wata daya a ibadan bai dawo abuja domin
yasan idan yadawo babu abinda zai yi domin
shi ahalin yanzu baya tunanin zai sake kusantar
basma kwana kusa har yanzu fushi yake sai ya
huce, abbansa ne yayi masa waya yafara
yimasa fada dan me zai ajiye yarinya yatafi
yabarta lallai lallai yazo abuja acikin satin nan
hakuri yabawa abba tareda cewa yana nan
zuwa. Ranar friday da yamma yashirya yabaro
ibadan zuwa abuja 3:30 yazo gida amma kuma
basma bata nan sai yan aikinta, zama yayi
yafara jan tsaki bai dade da zama sai gata
tashigo in banda kamshi babu abinda takeyi, ga
wata uwar kwalliya da taci sannu da zuwa dear,
cikeda takaici yakalleta basma wannan wacce
irin rayuwa ce? Kullum bazaki zauna agidan ki
ba kamar ke kikafi kowa aiki, yanzu kiduba
dakina tun waccan zuwan danayi yake kaca
kaca amma har yau baki gyara ba, am sorry my
man bari nakira mary tazo ta gyara maka, kar ki
kirata kece zaki gyara da kanki, kallonsa tayi
wlh bazan iyaba domin ni banma san yadda ake
yin shara ba balle moping, kuma agajiye nake
wlh kabari kawai mary ta gyara maka, nace miki
a’a ki barshi kawai.
[1/12, 8:48 AM] Ummi A’isha: [12:48PM,
10/22/2015] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
Na
UMMI A’ISHA
3⃣5⃣
Fita yayi daga falon ita kuma basma
cikeda rashin damuwa tawuce dakinta. Gidansu
yawuce kai tsaye yashiga falon umma amma
babu kowa da alama tana sama, benen yahau
anan kuwa yasamesu ita da nihal, umma tana
yiwa nihal kalaba akanta sallama yayi yashiga
cikin murnar ganinsa umma ta amsa nihal tana
jin shine tajawo dankwalinta tarufe kanta umma
bar min haka zan karasa ta tashi tazauna akan
kujera, russunawa yayi yagaida umma sannan
ya nemi wuri yazauna sai da akayi yan mintuna
sannan yace umma dama mata masu fita aiki
haka suke barin gidansu kaca kaca? Kallonsa
umma tayi a’a awwab suna gyarawa, to umma
banda basma domin dakina yana nan kamar
bola nayi nayi ta gyara min taki wai sai dai yar
aiki zatasa nikuma bazan amince mai aiki ta
rinka shigar min daki ba, murmushi umma tayi
to yi hakuri soja ni bana son ka rinka gwada
zuciyar nan taka akan basma saboda macece
mata kuma sai da hakuri, nihal saka hijabinki
kije gidan ki gyara mishi dakin kidawo kallon
umma tayi amma babu damar tayi mata musu
tashi tayi tadau hijab dinta tafita wannan shine
karo na farko da zata shiga gidan dan tunda
akayi auren bata taba sha’awar shiga gidan ba,
cigaba da yiwa awwab fada umma tayi kasan
basma agidansu babu abinda takeyi komai yi
mata akeyi kaga anan ma dole kayi hakuri tunda
tun farko da haka ta taso, to umma bayan
wannan ma hatta girki sai dai mai aiki tayi ita
ko tea bata iya hadawa ba, duk da haka dai kaci
gaba da hakuri, tashi umma tayi dakanta taje ta
hado masa abinci ta kawo masa. Ahankali nihal
take tafiya har tashiga gidan babu kowa afalon
amma duk yadda akayi dakin farko shine na
awwab dan haka shi tashiga taganshi gaje gaje
babu kyan gani har wani karni dakin yake, hijab
dinta ta cire ta shiga bathroom din ta tari ruwa
ta wankeshi tas tadawo dakin ta yaye bedsheet
din kan gadon da alama tun wanda aka shimfida
lokacin biki ne domin gashi nan yayi bakikkirin,
drower ta buda tagansu gasu nan kala kala
wani ruwan toka ta dauko ta shimfida tafara
share dakin tana cikin sharar basma ta shigo
dakin wa zata gani? Nihal tagani tana shara
nanfa basma tasha kunu.
3⃣6⃣
Itama nihal kunun tasha ta daure fuskarta ta
hade girar sama data kasa domin dama bata
son ganin basma ko kadan ,juyawa basman tayi
tafice daga dakin batare da tace komai ba
ammafa aranta masifa ce fal awwab kawai take
jira yashigo dan ta tsattsage shi, nihal kuwa
cigaba da aikinta tayi tagyara dakin sosai yayi
kyau sai kamshi yake domin ga airfeshener nan
sunfi kala 5 amma dan tsabar rashin gyara ba
atabasu balle ayi amfani dasu tsayawa tayi tana
kallon dakin ita kanta dakin ya burgeta yanzu
domin ta ajiye komai a muhallinsa, hijab dinta ta
dauka tafito lokacin basma tana zaune afalon
tacika tacika tayi fam kamar zata fashe ko
kallon inda take nihal batayiba tafita nan fa
basma takara kuluwa, ita kuwa nihal gida
takoma inda tabarsu shi da umma anan ta
samesu kallonta ya danyi ta gefen ido yaga
ranta abace yake dama yasan za ayi haka,
zama tayi umma tana cewa kin dawo, um umma
nadawo satar kallon awwab tayi ya tsurawa
wayarsa ido da alama akwai abinda yakeyi
kallonsa taci gaba dayi yana sanye cikin bakar
t.shirt mai dogon hannu da botira agaban rigar
yasa bakin trouser hannunsa na hagu daure da
agogon azurfa na Gucci dan yatsansa na tsakiya
sanye cikin zoben azurfa mai kyau, agaskiya
awwab ya hadu iya haduwa, girgiza kanta tayi
wlh bakayi sa’ar mataba kwata kwata tafada
acikin zuciyarta me za ayi da basma? Cases
tafada ahankali dagowa da kansa yayi ya kalleta
caraf suka hada idanu gabanta taji yafadi tayi
saurin dauke nata idon shima awwab jin
gabansa yayi yafadi,dama shi ya saba jin
wannan faduwar gaban tun lokacin da yafara
ganinta, tashi yayi yace da umma shi zai tafi
sunkuyar da kanta nihal tayi aranta tana cewa
agaida mummuna fita yayi ya nufi gidansa yana
shiga ya tarar da basma afalo dama shi take jira
yana zuwa ta mike tsaye tafara masifa
3⃣7⃣Kadawo daga yawon tona min asirin?
Shine zakaje ka turo min wannan ficiciyar
yarinyar tazo min gida, to wlh wannan yazama
na karshe duk ranar da tasake gigin zuwar min
gida sai nafasa bakinta aikin banza aikin wofi,
wuri awwab yasamu ya zauna bai tanka mata
ba har sai da tagama sannan yace basma ya
mukayi dake? Saifa dana rokeki kan kigyara min
dakin nan amma kika ki, to da ban gyara ba ai
nace maka zan sa mary tagyara kaki ko?
Yazanyi maka? To ai shiyasa naturo wata ta
gyara min, ai kuwa duk ranar da takara zuwa
sai nadauki mataki akanta wlh kallo yabita
dashi kin nuna min aikinki yafini muhimmanci
ko? Kibar aikin nan kizauna ki kula da gidanki
da mijinki,a’a awwab kada ma kasoma fadar
haka domin alqawari mukayi dakai cewa zanyi
aiki kuma zan cigaba da karatu to shikenan
tunda haka kika zaba kije kiyi, daki ta wuce ta
barshi zaune a falon oh! Mata matsala ne
yafada tareda dafe kansa sai da yadade azaune
sannan yashiga dakinsa yana shiga yaganshi
tsaf fes fes in banda kamshi babu abinda yake
tashi acikin daki gefen gadon yaje yakwanta
haba ai komai yana son gyara yafada tareda
mike kafaduwansa akan gadon, yau baya ra’ayin
zuwa club amma dai yasan yanada giyar kwalba
daya acikin mota.
3⃣8⃣ Da hanzarinsa yafita inda motarsa take
yabude ya dauko yadawo dakinsa ya bude
kwalbar ya shanye ta tas sannan ya tura
kwalbar kasan gadonsa duk da cewa yasan
basma tasan yana dan kurbawa bararrajewa
yayi akan gadon nan bacci ya sureshi bashi
yatashi ba sai tsakiyar dare nan kuma ya zauna
har asuba tayi sai da aka kira salla yayi sannan
ya koma bacci, 11 yatashi yayi wanka ya sanya
kananan kaya wanda sukayi mutukar yi masa
kyau yafito dakin basma yashiga amma bata
nan har tafita aiki wato su aikinsu babu asabar
babu lahadi kenan ransa ne yabaci sosai yafito
babu komai akan dining table da alama dama
bata ajiye masa komaiba cikin bacin rai yafito
yatafi gidan umma, agaskiya lamarin basma da
gyara sai ya seta mata zama zasu daidaita
dakin umma yashiga saboda falon babu umma
tana zaune abakin gadonta tana waya nihal har
kinje malam madorin? Eh to shikenan Allah ya
kaimu sai kindawo, Malam madori kuma?
Yatambayi kansa nikuwa ai nataba zuwa Malam
madori a rayuwata, bazan taba mantawa da
wannan garin ba
3⃣9⃣ Zama yayi agefen gadon umma, umma
ina kwana? Lfy awwab, anfito? Eh umma,kayi
break? Wlh umma banyiba to kaje kan dining
akwai abinci yana nan, to umma godiya nake
tashi yayi yafita yakoma falo ya hau kan dining
yafara zuba farfesun kayan ciki ya hada tea
yasha can kasan ransa kuma tuna garin malam
madori yakeyi, ai kuwa bazai taba manta malam
madori ba da wannan tunanin yagama yin break
din yadawo falon ya zauna acikin kujera
yakunna tashar kwallo yafara kallo. Sai yamma
yakoma gidansa yayi wanka ya shirya yafita har
lokacin basma bata dawo gidan ba shima fitarsa
yayi yatafi club tun lokacin club din acike yake
da yayan manya yan duniya said sharholiyarsu
suke nan shima yashiga sahu anan kuma
yasamu sabuwar budurwa zahar tun daga nan
suka fara holewa bashi yadawo gidansa ba sai
12 nadare lokacin itama basma bata dade da
shigowa ba dakinsa yawuce ya kwanta basma
tana jinsa amma bata tashi ba taci gaba da
kwanciyarta. Washe gari ma lokacin da yatashi
basma ta dade da fita har yamma bata dawo ba
ganin bata dawo ba yasashi shiryawa yaje
yayiwa umma sallama yayi tafiyarsa abuja, ita
basma bata san yatafi ba sai dataga 12 ta wuce
sannan tasan baya gari jijjiga kai tayi tace Allah
ya raka taki gona dama idan ka zauna ma
bawata uwar kake tsinana min ba.
4⃣0⃣Tunda awwab yatafi bai kara
waiwayowa abuja ba sai bayan sati 3 aranar da
yadira basma bata gidan kwanciyar sa yayi yai
bacci domin shigowar dare yayi, ba ita tashigo
ba sai wurin 9 kaji ma’aikata tana zuwa tayi
kwanciyarta da alama bata san awwab yadawo
ba. Wayewar garin sai 11 awwab yatashi yayi
wanka yahade cikin wata Orange din riga t.shirt
yasa blue din jeans yadora jacket asaman rigar
kasancewar garin kwana akayi ana sheka ruwa
gashi weather din ta canja sanyi ya juyo, falo
yafito basma na zaune sannan ga wasu maza
guda 2 suma suna zaune akan daya kujerar cikin
mamaki basma ta kalleshi my man dama kana
nan? Banza yayi da ita? Suwaye wadannan
kuma? Abokan aikina ne akwai abinda muke
tattaunawa dasu ne tsawa ya daka musu tareda
nuna musu kofa sim sim suka tashi suka fice
sannan yadawo gareta ke wacce irin
mahaukaciya ce, dabba marar tunani? Kwata
kwata bakya daraja aurenki saboda tsabar
rashin sanin yakamata cikin masifa itama ta
mike kar ka kara aibantani ai dama sai da
nafada maka zanyi aiki kuma ka aminta dan
haka yanzu baka isa ka hanani ba kallonta yayi
ai kuwa dole sai kin bar aikin nan ko kuma ki
hakura da zaman aurena, wlh bazan bar aikiba
tunda mun yita da bajewa dama kai ka fada min
auren yanzu kwarya tabi kwaryane ma’ana
yimin inyi maka, ka fita aiki nafita aiki, juyawa
yayi yafita yabar mata gidan, gidansu yanufa
yasamu umma itada nihal suna yin break a falo
cikin bacin rai ya gaida umma yafara fada mata
abinda basma tayi masa tareda fadin wlh umma
nagaji da halinta sakinta zanyi dai dai lokacin
abba ya shigo falon yaji abinda awwab yafada
hakuri umma tasoma bashi shikuma abba ya
zauna yana sauraren har suka gama gyaran
murya abba yayi yace awwab! Na’am abba!
Awwab nabaka nihal akaro na 2 ka aura kamar a
mafarki awwab yaji maganar itama nihal kamar
mafarki taji, nima ummi A’isha kamar a mafarkin
naji
[1/12, 8:52 AM] Ummi A’isha: [1/12, 8:50 AM]
Ummi A’isha: KWARYA TABI KWARYA
4⃣1⃣
Na UMMI A’ISHA
Shiru nihal tayi tana son jin yadda awwab zai
karbi zancen amma abin mamaki sai ta jiyo
muryarsa yana yiwa abba godiya tareda addu’ar
Allah yasa yin Allah ne harda cewa abba nagode
nagode Allah yabaka aljanna hakika nasan duk
inda ake neman uba nagari to ka kai Allah
yasaka maka da mafificin alheri, amin awwab
inji umma sannan tajuya ga abba tace nan da
yaushe kake ganin za ayi bikin? Nan da 3
months ai yayi ko? A’a gaskiya ayi nan da
karshen this month domin ba wani taro zamuyi
ba duba da yadda jama’a zasu ga bai wani jima
da aure ba kar azo anayi damu agari, kinyi
gaskiya hajiya aisha hakika kinyi tunani mai
kyau yawwa kaga da zarar an daura aure sai mu
bashi matarsa ya dauketa su tafi, wannan haka
yake hajiya Allah yakaimu lokacin amin, tashi
abba yayi yafita daga falon shima awwab din
tashi yayi yabi bayansa ita dai nihal kanta yana
kasa tunda aka fara maganar ta sunkuyar
dakanta sai da taji fitarsa da abba sannan ta iya
daga kanta ta kalli umma wadda farin ciki
yagama cikata shiru tayi tofa! Awwab zai zama
mijinta basma kuma zata zama kiahiyarta wani
bacin rai ne ya ziyarci zuciyarta ashe dama miji
daya zasu aura da basma? Shiyasa taji ta
tsaneta tsana mai yawa tashi tayi tashige
dakinta ta kwanta. Abangaren awwab kuwa
abba yabi ya sake yimasa godiya sannan yafita
zuwa golden touch hotel anan ya Shafe awanni
yana holewarsa sai daf da magriba yadawo gida
ko lokacin da yashiga bai samu basma ba dan
har yanzu bata dawo daga aiki ba, bai damuba
yashiga yayi wanka yashirya yafito yau wankan
nasa na daban ne kamar wanda zai je zance
farar shadda mai mutukar tsada yasaka tareda
saka farar hula ga agogon fata fari ya daura
sannan yasanya harp cover dinsa shima fari,
turaren secret amber yafesa nan yadauki kamshi
kamar wani sabon ango.
[1/12, 8:51 AM] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
4⃣2⃣
Na UMMI A’ISHA
Gidansu ya hara yana tafe yana waya da ogansa
da haka yashiga gidan, falon umma yayiwa
tsinke tana zaune itada su talatu mai aiki gefe
kuma nihal ce ta mike akan doguwar kujera
idanuwanta arufe kujerar kusa da ta umma yaje
yazauna tuni masu aikin suka firfice, hira suka
farayi da umma sama sama nihal taji
sanyayyiyar muryarsa ahankali ta bude
idanuwanta tafara kallonsa yayi kyau sosai
kamar bafulatani gashi kayan da yasa sun
amshe shi sosai, yaune karo nafarko da tayi
masa kallon kurulla dataji zai zama
mijinta,komai nashi acikin sanyi yake yi ita
kanta maganar sa asanyaye take kallonsa taci
gaba dayi daga kansa har zuwa kafarsa
agaskiya yayi bala’in haduwa matsalarsa daya
shan giyar da yakeyi domin bata san yana
neman mataba, sai da yashafe sama da minti
40 sannan yayiwa umma sallama tareda fadin
tunda ita wannan bacci take umma natafi da
sauri ta rufe idanunta yatashi yafita. Gari yana
wayewa aka kirashi a ibadan dole ya shirya
yatafi lokacin karfe 6 nasafe ko umma ma sai
awaya yafada mata dan bai samu damar shiga
gidan ba. Tunda yatafi ayyuka sukayi masa
yawa bai samu damar zuwa abuja ba ganin
bashida isasshen lokaci yasa yayiwa yayarsa
waya tareda tura mata kudi mai yawan gaske
domin ta hadowa nihal lefe,dama umma ta
sanar da ita komai dan haka babu bata lokaci
taje ta iyo siyayya Kaya masu tsada ta tarkato
akwati takwas da dan karamin kit nacikon tara
dayake ba wani taro zasuyi ba ita kadai takawo
kayan gidan umma lokacin nihal tana gyarawa
umma dakinta sai kawai gani tayi anata shigo
da akwatina masu kyau ko ba afada mata ba
tasan nata ne aka kawo sai dai gidan tsit babu
wata hayaniya hakan ya tabbatar mata da cewa
iya anty jamila ce ita kadai ta kawo kayan har
kasa ta tsugunna tagaida ta kamarsu daya da
awwab sai dai ita tafishi hasken fata, tashi tayi
tafita daga falon taje dakinta tafada gado wai
dagaske itace zata zama matar awwab? Ganin
abin take kamar a mafarki tunanin irin zaman da
zasuyi da basma tashiga yi saboda ta tabbatar
shi awwab bashida matsala domin baima cika
son hayaniya ba balle ya tsaya zaman fada da
mace dan a yadda ta fuskanta ma basma itace
take cutar dashi bashine ke cutarta ba, Allah dai
ya sausauta min zuciyata domin nayi mutukar
tsanar basma tafada aranta.
[1/12, 8:51 AM] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
4⃣3⃣
Na UMMI A’ISHA
Umma ce ta leko tace taje ga kayanta can
na lefe tagani cikin jin kunya tace umma ni basai
nagani ba kyaleta umma tayi tafita tana cewa
kya gani ai idan Jamilan ta tafi ita dai nihal
shiru tayi takwanta. Sai da biki ya rage saura
sati 1 sannan awwab yasamu kansa yakarbi
hutu nasati biyu yadawo abuja yana zuwa
gidansa yafara shiga yauma komai a hargitse
babu gyara kamar babu masu aiki agidan gashi
basman bata nan itadai ta barwa masu aiki
gidan bata dawowa sai dare kuma tun safe take
fita dakinsa yawuce yayi wanka yasake dressing
ya shirya cikin kananan kaya dark brown din
riga da light brown din wando yafeshe jikinsa da
turaren touch me yafito yanufi gidan umma tuni
ita ta dade dafara shirye shiryen bikin duk da
cewa dai bawani taro zatayi ba sai nakusa ne
kawai zasu zo falon abbansa yaje suka gaisa
daga nan yafito yashiga falon umma babu kowa
afalon sai nihal datake kwance akan doguwar
kujera take bacci tana sanye cikin atanfa mai
box kalarta yeluwa da baki kanta ba dankwali
tasa dantsen hannunta ta rufe fuskarta kallonta
yatsaya yi gaskiya yarinyar nan kyakkyawa ce
sosai gata da gashi waje yasamu ya zauna yaci
gaba da yimata kallon kurulla sai da yashafe
wajen minti goma yana kallonta sannan ta dan
motsa ahankali ta dauke hannunta tabude
idonta caraf suka hada ido sake kallonsa tayi
kamar a mafarki ta ganshi kamshinsa duk ya
baibayeta tashi tayi taja dan kwalinta ta daura
ahankali tace sannu da zuwa, yawwa sannu
yafada yana kallon tv, ina wuni? Lfy yagida? Lfy
tafada ta tashi tashiga kitchen ta dauko masa
ruwa da lemo tazubo masa dambun nama ta
doro akan tire takawo masa hakan datayi ba
karamin dadi yaji ba, yanzu yaga wani
girmamashi take tun lokacin dataji an bashi ita
tadaina yi masa tsiwa wadannan harare hararen
ma duk ta daina yimasa thank you yafada
ahankali sama tahau taje dakin umma takirata,
tare suka dawo falon, yaci dambun naman
kadan yasha ruwa amma bai sha lemon ba
domin shi baya harka da lemo babbar harka
yake sha gaisawa sukayi da umma anan take
tambayarsa ko ya sanar da basma zancen
aurenshi? A’a umma ban fada mata ba amma
yau dai nake son sanar da ita, tashi nihal tayi
tabar falon shi kuma suka cigaba da tattauna
maganar shida umma.
[1/12, 8:51 AM] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
4⃣4⃣
Na UMMI A’ISHA
Sai wurin karfe 8 awwab yabar gidansu yayi
niyyar yaje club amma yafasa yashiga gidansa
lokacin basma tadawo tana zaune da yar best
da dogon wando baki tana cin indomie tana
kallo sallama awwab yayi yashiga cikeda
mamaki ta amsa tana kallonsa my man yaushe
ka sauka agari? Akusa da ita yazauna yana
cewa tun yamma nashigo lokacin bakya nan,
ayya wlh gidan bikin friend dina naje shiyasa,
kallonta yayi shine baki fada min ba? Oh sorry
nakira wayarka bata shiga ba, murmushi yayi ok
no problem yanzu kin san me nakeso dake?
Girgiza kanta tayi dan Allah ki rinka gyara
dakina da naki,oh my man munyi maganar nan
fa wlh banida time din gyarawa kuma ban iya
bama amma nace maka zansa Mary tashare, no
nace miki ban yarda suna shigar min dakina ba
haba basma ni shikenan banida sirri komai nawa
sai mai aiki tasani? To amma ai naga wannan
yarinyar ma tashiga dakin naka ita kuma
awanne matsayi take? Ni yanzu duk ma ba
wannan ba gobe zan tura miki 5 hundred
thousands acikin account dinki, murmushi tayi
kai amma fa nagode, ki sai dukkan abinda
kikeso domin zan kara aure ne, zumbur ta tashi
kamar wadda aka mintsina aure awwab? Me
kake nufi? Wulakancin naka har yakai kamin
kishiya tun yanzu? Yaufa watanmu 5 da aure
kwata kwata, me kakeso duniya tadaukeni?
Domin duk matar da akayi mata kishiya bata
shekara ba dole axargeta, look basma ki
kwantar da hankalinki babu wanda zai zargeki
domin duk duniya babu wanda yasan sirrin dake
tsakanina dake wlh babu wanda nataba yunkurin
fadawa kuma kar ki damu kanki bawata bakuwa
zan aura ba nihal ce kuma abba ne yabani ita
kinga bani da halin da zan musanta abinda yace,
cikeda masifa basma ta dubeshi dama ai
nadade da sanin haka zata faru tunda kana
zaune da munafukai, zunbur shima ya mike
suwaye munafukan? Su wadanda suka hada
auren tas! Yadauketa da mari iyayen nawa ne
munafukai basma? Dama bakida mutunci? Gaka
nan marar mutunci macuci wlh idan kayi auren
nan sai nakasheku kai da ita domin natsaneta
natsaneta bana son ganinta amma saboda
tsabar rashin adalci ace da ita za ahada ni
kishi? Wlh bazan yafeba Allah ya isa tsakanina
daku Allah ya dora maka masifa da bala’i acikin
rayuwarka, bai sake kulata ba yajuya yashiga
dakinsa, dakin ta bishi tana mai ci gaba da tsine
masa amma ba saurareta ba yashige toilet don
yin wanka duk da haka bata fasa zaginsa shida
iyayensa ba har yafito duk da haka rabuwa da
ita yayi saboda shi baya son fada da mace da
maza yasaba fada sune daidai shi amma yaushe
zai wani zauna yana kace nace da Mace sai
kace wani soko? Shi aganinsa duk mai musayar
yawu da mace bai cika namiji ba.
[1/12, 8:51 AM] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
4⃣5⃣
Na UMMI A’ISHA
Kayan baccinsa ya saka yahau gado ya
kwanta amma basma bata barshi yayi baccin ba
saboda ruwan rashin mutuncin da tayita xuba
masa, munafuki shiyasa ka turota tagyara maka
daki saboda kana so ka nuna mata banida kima
da daraja a idonka to wlh sai kayi nadama, ashe
dama an san abinda ake kullawa shiyasa tunda
nazo gidan nan sau daya kataba hada gado dani
daga karshe kabini da sharrin cewa ni ba
budurwa bace, to ai kaima ba saurayi bane
tunda manemin mata ne kuma mashayin giya
rayuwar auren yanzu kuwa sunanta KWARYA
TABI KWARYA kayi min inyi maka, haka taci
gaba da maganganu da zage zage har gari
yawaye, tana ganin yafita masallaci tashiga
dakinta tasa kayanta tadauki wayarta tafito
tadau motar ta tanufi gidan iyayenta. Tana
zuwa tafada jikin momynta tafashe da kuka
tafara labarta mata abinda yafaru, cikeda masifa
momy tace wulakancin dazai yimana kenan?
Yayi miki kishiya tun yanzu salon a rainaki to
wlh bai isaba zai zo gidan nan yasameni wlh sai
naci mutuncinsa sai naga waye ya tsaya masa
kuma ma ai da laifin iyayensa dan me zasu
kyaleshi yayi aure tun yanzu? Cikin kuka basma
tace wlh momy sune ma suka sashi yin auren
amma da bashida ra’ayin ajiye mata 2,kiyi shiru
basma nasan laifin uwarsa ne itace zata sashi
to wlh bazaki koma gidansa ba har sai yagane
kurensa, kuma aiki ne dole sai kinyi ko yaki ko
yaso karatu ma kina samun admission zaki
koma, sannan ko agidan nan bakya yin shara da
gyaran daki dan haka bazaki fara agidansa ba,
dafatan kin sanar dashi ke ko agidanku bakya
dafa ruwan zafi bare girki? Eh momy duk nafada
masa yawwa kinyi min dai dai shalele na dan
haka kishare hawayenki daidai lokacin dadynta
yashigo ai nan ya tambayi abinda yafaru momy
tasanar dashi fada shima yafara ni alh mansur
zai ciwa mutunci? Yayi kyau zamu hadu dasu
wlh sai nadau mataki akansu. Agidansu awwab
shirin biki kawai aka sa agaba kuma awwab bai
sanar daasu umma cewar basma bata nan ba
shi kansa shareta yayi duk kuwa da cewa
mahaifinta yayi masa waya yace yazo yana son
ganinsa bayan ya zazzaga masa masifa dan
hatta gaisuwar da yayi masa bai amsa ba ganin
haka yasa awwab ya sharesu, shirin aurensa
kawai yasa agaba wanda yanzu ya rage saura
kwana 2 kacal.
[1/12, 8:55 AM] Ummi A’isha: [1:29PM,
10/25/2015] Ummi A’isha: [10:05AM,
10/25/2015] Ummi A’isha: KWARYA TABI
KWARYA
4⃣6⃣
Na UMMI A’ISHA
Ranar juma’a bayan an taso daga
masallaci da misalin karfe 2 aka daura auren
awwab da nihal akan sadaki naira dubu 50
babban limamin masallacin shine yayiwa awwab
walinci yayin da abba yayiwa nihal walinci,
awwab yasha kyau sosai cikin farin yadi mai
mutukar tsada komai mai tsada yasa tundaga
yadin jikinsa har agogon hannunsa da
takalminsa kamar auren fari dan idan ba sani
kayi ba zata zakayi wannan shine aurensa
nafarko, ana dawowa daga wurin daurin auren
yawuce gidansa amma sai me? Gidan duk anbi
an kukkulle ko ina da manyan padlocks babu
inda aka bari abude nan fa yaji yakulu yafito ya
tambayi mai gadin gidan ina masu aikin?. Alh
yanzu duk hajiya da mahaifiyarta sukazo suka
rufe gidan suka debesu suka tafi juyawa kawai
yayi yafita yashiga gidansu babu kowa agidan
sai yayarsa jamila da umma da nihal cikin
takaici yafara fadawa umma,umma kinga
yarinyar nan ita da mahaifiyarta sunzo sun rufe
min gida ko? Yi hakuri awwab bari na tura nihal
ta gyara maka side dinka nada tunda ba wani
dadewa zakayi ba kwana nawane, wuri yasamu
ya zauna yana huci, tashi nihal tayi tatafi side
din nasa ta gyara masa tadawo tawuce dakinta
daga nan bata sake ganinsa ba sai dare tana
zaune afalo wayar umma nakusa da ita yakira
tadaga hello umma ahankali tace ba umma bace
ok to ki kawo min abinci dan Allah to tafada ta
ajiye wayar tashiga kitchen tahado masa akan
tire takoma dakinta ta fesa turare dama tafi
amfani da Arabian perform irinsu nashwa,
aroosa, shaikah, lailatul sahara da sultan abyad
duk sai da fesa su ta yafa gyale tafito tadauki
tiren tanufi side dinsa. Ahankali ta tura kofar
falon tashiga yana zaune yana waya takai kayan
gabansa ta ajiye takoma kujerar nesa dashi ta
zauna. Kusan minti 5 sannan yagama wayar
yajuyo ya kalleta dawo nan ki zauna yanuna
mata kusa dashi, babu musu tadawo kusa dashi
ta zauna kamshinta kawai yaji yajishi ya rude
ahankali yashiga jikinta, hawayene suka fara fita
daga idonta shar shar da sauri ya kalleta meye
abin kuka? Dan Allah kayi hakuri da abinda
zakaji daga bakina sannan dan Allah kayi min
alkawari bazaka sakeni ba kallonta yayi yaga
jikinta sai rawa yake hannunta yakama kar ki
damu wlh nayi miki alkawari bazan sakeki ba
kuma bazan rabu dake ba kome zanji daga
gareki i promise you! Cikin kuka tace ni ba
budurwa bace wlh wanine yayi min fyade
shekaru uku da suka wuce awani dare nataso
daga islamiyar dare ina cikin tafiya naci karo da
wani saurayi dayake duhu ne ban ganshi ba
nataka shi kawai sai ji nayi ya mareni zafin
marin yasa nazageshi nace Allah ya isa ban
yafeba shege mugu yana jin yajani wani kango
ya toshe min bakina yace yau sai yayi maganin
rashin kunyata anan yayi min fyade dayake duhu
ne banga fuskarsa ba.
[10:45AM, 10/25/2015] Ummi A’isha: KWARYA
TABI KWARYA
4⃣7⃣
Na UMMI A’ISHA
Ji tayi awwab ya rungumeta ahankali ya
lalubi kunnenta yace lallai Allah shine gwanin iya
hikima, nine saurayin da nayi miki fyade dayake
Allah gwanin hikima ne sai yahadani dake anan
yabani ke a matsayin matata, zunbur ta tashi
tafara ja da baya dama kaine macuci azzalumin
da ya bata min rayuwata? Yayi sanadiyar barina
gidan ubana, yayi sanadin da ubana ya tsine
min albarka yayi tir dani mutanen gari suka
tsaneni, wlh bazan zauna dakai ba kai mugune
sai ka sakeni sai ka rabu dani natsaneka
natsaneka bana son ganin kome kama dakai
bazan zauna dakai ba kuma wlh sai kaima ka
dandana bakin ciki kamar yadda ka dandana
min,alkawari nayi duk ranar danaga wanda ya
gurbata min rayuwa sai na kasheshi kuma har
yanzu ina nan aka bakana yanda ka rusa min
rayuwata kaima sai narusa taka idonta ne yakai
kan yar karamar bindigarsa wacce baya rabuwa
da ita zaraf ta dauka ta riketa taseta shi wlh
kaima sai na nakasa ka kamar yadda ka nakasa
ni sai alokacin awwab yayi magana ki kasheni
sai ki huce amma wlh bazan sakeki ba domin
nayi alkawari bazan rabuda ke ba duk tsanani
bindigar ta danna ji kake tau ta harbeshi a cinya
duk dauriya irin tashi sai dayayi yar kara tuni
harsashin ya huda cinyar sa jini ya fara fita tana
ganin haka ta yarda bindigar tafice da gudu
shikuma awwab dakyar ya dau wayarsa yafara
kiran abbansa yasanar dashi nan da nan sai
gashi arude,ya taimaka masa suka fito suka
shiga mota sai wani private hospital anan aka
shiga dashi theatre kwararrun likitoci suka yi
masa chaaa!. Acan gida kuwa nihal tana fita
dakin umma tashiga tana kuka tafada jikin
umma tana fadin wlh umma bazan zauna
dashiba sai ya sakeni shine mutumin da ya cuci
rayuwata wlh natsaneshi bana sonsa cikin bacin
rai umma tace dama awwab ne yayi miki fyade?
Wlh bazai taba yiyuwa domin nafi son farin cikin
yata akan dan wani, ni ina nan ina tattalin
rayuwarsa ashe shikuma yana can ya rusar
dataki rayuwa yazama dole na kwato miki
yancinki yata.
[12:13PM, 10/25/2015] Ummi A’isha: KWARYA
TABI KWARYA
4⃣8⃣
Na UMMI A’ISHA
Cikin kuka nihal tace umma nidai kawai
kisa yasakeni domin bazan zauna dashi ba
kanta umma tashafa itama hawayen take nihal
sai yasakeki mutukar hakan zai samar miki farin
ciki domin nafi son farin cikinki dana sa.
*********************** Acan asibiti kuwa cikin
mintuna kalilan likitoci sukayi nasarar cire
harsashin sukayi masa allurar bacci awwab
yasha wahala mutuka, baccin minti goma sha
biyar yayi yafarka abbansa ne ya matso wurinsa
ji yake kamar yafashe da kuka dan tausayin
dansa hannun awwab yakama son waye ya
harbeka? Hawaye ne yaziraro daga idon awwab
abba ka taimaka min bazan iya rabuwa da nihal
ba wlh ina tsananin sonta idan narabu da ita
mutuwa zanyi, kadaina kuka my son kaifa soja
ne ko kamanta ne? Kai yagirgiza abba kar
karabani da nihal dan Allah bamai rabaka da ita
son mutukar bakai ne ka saketa ba wayarsa
yadauka yakira umma yafada mata asibitin da
suke yace tazo yanzu yanzu, mintuna kadan sai
gata lokacin awwab yasake komawa bacci tana
shigowa tace Alh ina fata dai takardar sakin
nihal ya rubuta min shiyasa ka kirani? Cikeda
mamaki abba yace haba hajiya aisha awwab fa
bashida lfy harbinsa akayi gashi kuma yanata
yimin wasu maganganu cewar kar narabashi da
nihal,ai kuwa dolensa yasaketa dan tace bazata
zauna dashi ba kallonta abba yayi kin san kuwa
abinda kike fada? Eh nasani ko kana nufin zan
goyi bayan danka nafaranta wa danka na
kuntatawa tawa yar? To wlh bazan taba bawa
danka farinciki na kuntatawa yata ba domin
yanda kake son danka haka nima nake son yata
nama fika sonta domin son da nakewa yata
baka yiwa danka dai dai lokacin awwab yafarka
yabude idanunsa yana kallonsu abba ne
yakalleta cikin takaici yace hajiya aisha baki
isaba babu mai raba awwab da nihal duk kuwa
da cewa kina takamar kece kika haifeta to wlh
nafi son farin cikin dana fiyeda nakowa zan iya
yin komai domin naga na sama masa farin ciki,
cikin daga murya tace haka zalika nima zan iya
sadaukar da rayuwata domin naga nayiwa yata
abinda takeso, yanda kake son danka haka nake
son yata wata tara nayi ina dauke da ita acikin
cikina tafasa jikina tafito kaga kuwa ta cancanci
nayi mata dukkanin soyayya, kai kuwa baka san
ciwon nakuda ba baka san zafin haihuwa ba,
bazan taba raya naka dan ni nakashe tawa ba,
to wlh duk abinda yasamu dana sai na daure
yarki indai tayi sanadiyar mutuwar dana, wlh
kana daure min yata nima sai nakama danka na
daure duk abinda kake takama dashi nima ina
dashi.
[12:37PM, 10/25/2015] Ummi A’isha: KWARYA
TABI KWARYA
4⃣9⃣
Na UMMI A’ISHA
Badai dukiya da mukami da mulki kake
takama dashi ba? Kai kanka kasan nafika dukiya
nafika hanya nafika yawan masu daurin gindi,
yanda kake takama kana rikeda mukamin
minster nima na rike wannan mukamin dan haka
dani dakai kar wanda yafasa, KWARYA TABI
KWARYA amma ina mai tabbatar maka nihal
bazata zauna da awwab ba kuma sai nayi
kararsa dalilin keta mata haddi da yayi, cikin
zafin rai abba yace karki fasa kiyi kararsa sai
me? Kidau lawyer nadau lawyer inyaso sai aga
wanda zai yi nasara amma duk fitinarki awwab
bazai saketa ba sai dai idan shine yayi ra’ayin
hakan, ai kuwa dolensa domin yata bazata
zauna da dan giya ba manemin mata tas! Kakeji
abba ya dauke umma da mari kar ki kuskura Ki
sake muzanta dana, karya nayi masa? Duk
wanda yasan danka yasan cikakken mashayin
giya ne kuma kwararre afannin neman mata
wasu hawaye ne suka fara sintiri akan kumatun
awwab gaba daya ji yayi ya tsani rayuwar,da
ace yana iyawa to da yasaki nihal ko dan
yaraba gardamar dake tsakanin umma da abba
amma bazai iya ba jin sonta yake yana ratsa
bargonsa kuma sai yau yasan ashe nihal yar
ummance muryar abba ce tadawo dashi hajiya
aisha ina iya yimiki saki uku akan dana wlh kar
ki yarda ki kureni, cikin kuka awwab yace
umma! Abba! Dan Allah kuyi hakuri, nahadaku
da girman Allah da kuyi hakuri dan Allah kar ku
rabu akan wannan maganar ko kallonsa umman
batayi ba tajuya tafice daga dakin, hawaye
awwab yaci gaba da zubarwa wanda ni kaina
ummi A’isha sai da nayi mamaki ganin soja
kamar awwab yana kuka, kusa dashi abbansa
yazo yazauna yafara shafa kansa awwab kayi
shiru kadaina kuka rabona danaga kukanka tun
ranar da mahaifiyarka ta rasu kayi hakuri kaji?
Abba kar kasaki umma akaina nasan umma
akan gaskiyar ta take duk uwa tagari bazata
aura min yarta ba domin ni bana gari bane ni
mashayin giya ne, manemin mata, ban tsayar da
salla ba bana tasbihi bana istigfari bana salatin
annabi duk wata dabi’a ta mutanen kwarai
banida ita lallai dan kuka shi yake jawa uwarsa
jifa yau gashi ata dalilina ana yimaka gori abba,
tir da hali irin nawa yafada yana kuka kamar
karamin yaro.
[1:14PM, 10/25/2015] Ummi A’isha: KWARYA
TABI KWARYA
5⃣0⃣
Na UMMI A’ISHA
Kadaina kuka awwab bana son kukanka,
kaima da nagari ne kaji kar ka damu kanka bari
nayiwa yayarka jamila waya nasanar da ita halin
da kake ciki fita yayi domin kiran anty jamila
awaya shi kuma awwab ya runtse idonsa yana
jin haushin kansa domin tun lokacin da abba ya
auro umma bai taba jin kansu ba ko musu
basayi amma yau gashi abba ya mari umma
agabansa sabodashi yana ikararin saki, hawaye
ne suka biyo kumatunsa oh! Allah saukaka
wannan masifa badan halina ba ya Allah yana
nan zaune in banda hawaye babu abinda yake
sai kace wani ragon maza har su abba suka
shigo shida anty jamila dasauri takaraso bakin
gadon sannu awwab amma gaskiya umma
tabani mamaki datayi haka amma babu komai
nihal dai bazaka saketa ba sai dai idan ita abba
zai saka kuma wlh idan wani abu yasamu dan
uwana bazan yarda ba tana cewa zataje kotu
ko? To sai gareta muna nan muna jiran
sammaci ko ta manta mijina shine shugaban
alkalan Nigeria gaba daya? Ai bata isa tayi
mana komai ba babu abinda zata iyayi dan tana
takamar ta taba zama minister? Wlh munfi
karfin dauri a kasar nan bazamu dauru ba,
hannu awwab yadaga mata dan Allah anty
jamila kar ki maida hannun agogo baya, kai
awwab kana tunanin zan kyaleta ne taciwa
ubana da kanina mutunci? Wlh bata isa ba ba a
halacci matar da zata zagi ubana na kyaleta ba
yanzu daga nan gidan zanje na mayar mata da
martanin abinda datayi kuma wlh sai tabar
gidanmu dan bata isa tazauna tana yiwa
mahaifinmu rashin mutunci ba shiru awwab yayi
anty jamila kuwa sai fada take tayi tana nan
zaune masu aikinta da driver dinta suka kawo
abinci wurin kala 5 sai wurin 9 tayiwa abba da
awwab sallama tafita bata tsaya ako ina sai
gidan abba tana shiga tasamu umma zaune
afalo hannunta rikeda faranti da fruits akai tana
shan apple ko sallama batayiba ta shiga ta rike
kugu ta tsaya tafara yiwa umma kallon banza
tareda fadin naji sakonki zakiyi karar dan uwana
ko? To ba hakuri nazo nabaki ba illa nazo
nasanar dake cewa har yanzu bakiyi kudin da
zaki iya daure awwab ba sannan bakida arzikin
da zaki tozarta zuri’armu domin munyi miki
nisa! Tashi umma tayi shi uban naki ne yaturo
ki kiyi min rashin kunya? To ki koma ki sanar
dashi karace ban fasa ba sai nayi karar dansa
yasaki yata kuma sai an kwato mata hakkinta
na fyaden da yayi mata, saki yazama dole dan
bazata zauna dashi ba duk wanda yasan dansa
yasan dan giya ne manemin mata haka kawai
yaje ya dauko cuta yasaka mata bazata taba
yuyuwa, cikin rashin kunya jamila tace haka fa,
me za ayi da matar uba? Allah yatsinewa matar
uba aduk inda take sannan awwab zai saki yarki
in yaso ki jikata ki shanye, mari umma
takawowa anty jamila cikin zafin nama tarike
hannun umma wlh kina marina ramawa zanyi
bar ganin kina matar ubana, cikin masifa umma
tace badake zanyi ba da ubanki zanyi me za ayi
da yayan miji? Gayyar masifa sakin hannunta
anty jamila tayi tajuya tafita tana fadin muna
jiran sammaci, tana fita umma tadau hadaddiyar
wayarta tafara kiran wata kawarta wadda ta
kasance babbar lauya mai zaman kanta tare
sukayi school a university of akwaibom inda take
karantar low ita kuma tana karantar medicine.
[6:17PM, 10/25/2015] Ummi A’isha: Nasan
wannan sako zai isa ga mai amfani da wannan
pin din na bbm chat (56523C1F ) duk da ban
sanka/sanki ba naga kin/ka canza min labarina
na MACE GUDA DAYA TILO duk da gargadin
danayi akarshen littafin amma sai da kuka
canza min to ina mai fada da babbar murya
ALLAH YA ISA domin labarin mace guda daya
tilo kirkirarren labarine da nazauna nabata
lokacina nashirya shi amma ki/ ka canza min, to
ban yafe maka/maki ba.
Ummi A’isha
[1/12, 8:56 AM] Ummi A’isha: [7:45AM,
10/27/2015] UMMI A’ISHA: KWARYA TABI
KWARYA
5⃣1⃣
Na UMMI A’ISHA
Kiran barrister laure tafara yi ringing 2
tadauka tana gaidata cikin bacin rai umma tace
barrister kina ina ne? Ranki yadade ina birnin
kebbi ayanzu haka naje wani case amma next
week zan shigo abuja, wani abune yafaru? Yes
barrister yaron mijina nayanzu ne yayiwa
yarinyata fyade kuma yanzu ya aureta ita kuma
tace bazata zauna dashi ba shine nake so ki
kaimin case din kotunku, to ranki yadade kidai
bari nadawo zan zo gidanki mu tattauna, ok
thank you barrister sai naganki, ajiye wayar tayi
tana faman hucin bacin rai.
***********************
Acan asibiti kuwa awwab yana can kwance yau
kimanin kwanansa 5 kenan abbansa shine yake
zama dashi dan yanzu ko office baya zuwa
sa’arsu daya asibitin sune suke kulawa da
patients dinsu ba a bukatar yan zaman jinya,
yayinda anty jamila itama kullum sai tazo itace
take kawo musu abinci da duk abinda zasu
bukata, ita kuwa umma tun ranar da abin yafaru
bata kara dawowa asibitin ba balle taga halin da
awwab yake ciki, yau jikin nasa da sauki don har
yatashi zaune suna hira da abba, turo kofa akayi
aka shigo anty jamila ce dauke da wani food
flask mai dankaren kyau sannu abba, awwab
yajikin takaraso tana murmushi, jiki yayi sauki
anty jamila nan da gobe za a sallamemu, to
Allah yakara sauki amma awwab yazama tilas
ka saki wannan yarinyar dan tunda tayi maka
haka zata iya kasheka watarana,anty jamila
kidaina fadin haka wlh ina son nihal har cikin
raina, taba baki tayi kai dai kasani tunda kaji
abinda uwarta tace sotake ta tozarta mu kuma
wlh bata isaba idan tayi wasa kafin ta daureka
ni sai na daureta,kiyi hakuri anty dan Allah wuri
tasamu tazauna tana fadin ita za abawa hakuri
ai tunda ita aka batawa, shi dai abba yana jinsu
bai ce musu komai ba.
********-*-********-*
Umma ce zaune acikin kasaitaccen
falonta taci ado cikin wata jar atanfa super
tasha gwalagwalai a hannunta da kunnenta da
wuyanta abinka da farar mace nan tafito das da
ita, sallamar barrister laure ce tacika falon
tashigo tana barka da hutawa ranki ya dade,
cikin murmushi umma tace yawwa sunnu da
zuwa barrister, bisimilla ga wurin Zama,zama
tayi suka gaisa tadubi umma tace ranki yadade
ina sauraronki cikin damuwa umma tayi mata
bayani sannan takara da cewa ni yanzu so nake
akwatowa yata hakkinta kuma kotu tasa
yasaketa don bazata zauna dashiba, murmushi
barrister laure tayi tace ranki yadade a shawarce
wannan case din bai kamata akaishi kotu ba
saboda family issue ne zuwa kotu babu alfanu
acikin wannan case din abinda nake so dake
shine kiyi hakuri ki bani dama ni zanyi muku
sulhu, yanzu ina awwab din yake? Awwab yana
asibiti shida mahaifinsa kuma barrister nifa babu
sulhun da za ayi mana domin yayarsa jamila har
gidan nan tabiyo ni taci min mutunci dan haka ni
bazan yarda ba, ranki yadade hakan dana fada
miki shine masalaha domin a ka’ida dama shine
yafi dacewa daya aureta domin ko a kotu
hukuncin da za ayanke kenan kuma hajiya aisha
ai hakan shine babban rufin asirinku domin idan
kukaje kotu to kun tonawa kanku asiri sannan
kuma duk ranar da nihal tayi aure zata fuskanci
matsala dan haka dan Allah kibani dama nida
kaina zanyi solving din wannan case din, girgiza
kai umma tayi shikenan barrister nabaki dama,
sallama barrister laure tayiwa umma tatafi.
[8:09AM, 10/27/2015] UMMI A’ISHA: KWARYA
TABI KWARYA
5⃣2⃣
Na UMMI A’ISHA
Barrister laure bata zame ko ina ba sai
asibitin dasu awwab suke, bayan ta dubashi tayi
musu bayanin cewa gobe zatazo gida tasamesu
tana son ganinsu har anty jamila, babu damuwa
Allah yakaimu inji anty jamila. Washe gari aka
sallamesu daga asibiti awwab yawarke misalin
9:30 suka isa gida lokacin barrister laure har
taje gidan, suna zuwa suka shiga falon anan
suka tarar da umma da barrister laure zaune,
babu wanda yayiwa umma magana acikinsu illa
gaida barrister da sukayi, kallonsu barrister laure
tayi tafara jawabi ranki yadade babu maganar
tashin tashina dan Allah, abinda nakeso daku
shine kubar awwab yaci gaba da zama da
matarsa domin babu wanda ya san tsakaninsu,
maganar fyade dama duk wanda muka samu
yayiwa yarinya fyade to dole ne ya aureta sai
dai idan yaki ne muke kaishi kotu ayi masa
hukunci dan haka ni ina ganin shaidan ne
yashiga tsakaninku ya bata maganar amma
maganar gaskiya shine bai cancanci awwab ya
saketa ba, hajiya Aisha kibawa alhaji mansur
hakuri bisa abinda yafaru umma batayi musu ba
tace Allah yabaka hakuri alh, kallonta barrister
tayi yawwa ke kuma jamila abinda kikayi baki
kyauta ba tsakaninki da hajiya bai kamata ayi
hakaba, kema kibata hakuri domin ada kin
dauketa a matsayin uwa kuma itama ta daukeku
a matsayin yaya idan mutum basani yayiba
bazai taba cewa ba itace mahaifiyarku ba cikin
karamar murya anty jamila tace Allah yabaki
hakuri umma, babu komai jamila Allah yakara
hada kanmu murmushi barrister tayi to komai ya
wuce yanzu abawa awwab matarsa murmushi
umma tayi ai tana malam madori tun ranar da
abin yafaru ta tafi, tashi abba yayi yafada yana
yiwa barrister godiya yawuce side dinsa kallon
umma awwab yayi to umma ai kuwa gobe zan je
nadaukota dariya anty jamila tayi ai kuwa zaka
hadu da basma yaro, ai kuwa dai inji umma, ni
wlh harma namanta da ita, to ai kuwa jiya
momynta takirani amma ban dauka ba inji
umma, garama dabaki dauka ba anty jamila
tafada tana dariya ita dai barrister laure tashi
tayi tai musu sallama ta tafi tabarsu sunata
hirarsu kamar wani abu bai faruba. Daren ranar
awwab bai runtsa ba tunani yake tayi haba
shiyasa yarasa a inda yasan nihal ashe itace
yarinyar daya yiwa fyade lokacin yaje wurin
abokinsa musaddik yanzu ma abokin nasa
yarasu, tun lokacin dayayiwa nihal fyade yashiga
harkar neman mata domin akanta yafara sanin
mace amma har yau baiyi dace da mai ni ‘ima
kamarta ba kullum tunanin yanda zai ganta yake
ashe itace nihal, Allah nagode maka yafada
insha Allah gobe zanzo gareki matata.
[8:28AM, 10/27/2015] UMMI A’ISHA: KWARYA
TABI KWARYA
5⃣3⃣
Na UMMI A’ISHA
Da misalin karfe 9 nasafe awwab yafito
zuwa dakin umma yayi kyau sosai cikin blue din
wagambarin da yasa, yasa hula blue da agogon
azurfa na guess watch, kamshin turaren touch
me da catch me sai tashi yake daga jikinsa, a
daddafe yasha tea da wainar kwai bayan sun
gaisa da umma yayi mata sallama bayan yakarbi
address din gidansu nihal yanufi side din
mahaifinsa suka gaisa yayi masa sallama yafito
yashiga motarsa kirar BMW blue mai bakin glass
yafita, gudu yayi sosai daga abuja zuwa jihar
jigawa daf da azahar ya shiga garin malam
madori awani masallaci ya tsaya yayi salla
yafito yashiga cikin garin bai wani sha wahala
ba yasamu gidansu nihal babban gidane da
alama itama mahaifinta babban mutum ne,
fitowa yayi yashiga gidan mai gadi yayi masa
jagora har falon mahaifinta, shiga awwab yayi
yasamu babanta zaune yana cin abinci kwara ne
kana ganinsa zaka gane hakan domin idan
kaganshi baza ka zata yana jin hausa ba saboda
basu da maraba da indiyawa shi kansa gashin
kansa yalo yalo yake, cikin girmamawa awwab
ya duka ya gaisheshi ya amsa cikin fara’a,
bayani awwab yayi masa na cewar yazo wurin
nihal ne shine mijinta, nan da nan mahaifinta ya
gintse fuska, dama Kaine ka auri yata batare da
sanina ba? Saboda tsabar Aisha bata daukeni da
daraja ba shine ta aurar min da yarinya bata
sanar dani ba to dama ina jirane kazo kabata
takardar ta dan tun dadewa nayi mata miji da
wani yaron kirki, hakuri awwab yafara bashi
amma yaki ya saurareshi daga karshe ma tashi
yayi yashigewarsa gida nanfa awwab yadade
azaune daga karshe shima yatashi yafita yanufi
wani guest house yakama daki ransa adagule,
sallar la’asar yayi, yayi order abinci aka kawo
masa harda kwalbar giya, daukar giyar yayi
yabude har yakai bakinsa zuciyarsa tace amma
idan kasha kacika marar zuciya karfa kamanta
gorin da akayi maka akan kana shan giya,
ajiyewa yayi yaja tsaki domin shi aka’idarsa
indai aka yimasa gori akan abu to yabar abin
nan kenan har abada.
[12:20PM, 10/27/2015] UMMI A’ISHA: KWARYA
TABI KWARYA
5⃣4⃣
Na UMMI A’ISHA
Daren ranar awwab bai iya runtsawa ba
kamar yadda itama nihal batasamu damar yin
bacci ba tunda mahaifinta yasanar da ita zuwan
mijinta, hankalinta yagama tashi kawai addu’a
take Allah yasa kar awwab yayi fushi ya saketa
kuka tasawa mahaifinta cikin sigar lallashi
yafara kwantar mata da hankali ta hanyar cewa
yasan awwab koda yatafi to zai dawo ita dai
shiru tayi dan gani take kamar awwab yatafi
kenan gashi yanzu tana tsananin sonshi, har
aka kira assalatu bata runtsaba. Tunda sassafe
awwab yatashi ya shirya karfe takwas dai dai
yaje gidansu nihal yauma kamar jiya mahaifinta
na nan zaune acikin wani babban falo, har kasa
awwab ya durkasa ya gaidashi kafin yafara
bashi hakuri akan ya kyaleshi da nihal,
murmushin abban nihal yayi yace yaro babu
komai haka Allah ya shirya kuma haka ya
kaddara, nabaka nihal kuma ina so kariketa da
amana idan ka cutar da ita ban yafe maka ba,
awwab kamar zai yi kuka yace insha Allah zan
rike nihal da amana kuma nayi alqawari bazan
cutar da itaba, murmushi mahaifin nata yayi
shikenan, nihal ita kadai ce yata dana mallaka
mun rabu da mahaifiyarta tun tana yar shekara
7 a duniya awurina ta taso amma gashi aure zai
rabani da ita yanzu duk da haka nayi farin ciki
Allah yabaku zuri’a dayyaba shiru awwab yayi
baice amin ba dan yana jin kunyar abban nihal,
tashi yayi yace bari nashiga ciki na sanar da ita
zuwanka domin ta kimtsa tafito kutafi,to abba
nagode madalla Allah yakara girma, mintuna
kadan sai ga wata yarinya da tire tazo ta ajiye
agabansa tareda gaida shi tiren yabude wainar
shinkafa ce da miyar agushi murmushi yayi
wannan shine best food dinsa amma yau dakyar
in zai iya ci saboda dokin ganin matarsa domin
nihal wani bangarece ta rayuwarsa itace mace
tafarko daya fara sani kuma tun daga ita bai
kara jin dadin sex ba gashi dai alokacin ba ta
dadin rai yayi mata ba asalima bai je inda
yakamata yaje ba ga ciwo da ya jijjimata amma
duk da haka yaji sweet shiyasa yadade yana
burin sake kasancewa da ita, ashe itace yarinyar
da yayita mafarki da ita sai yanzu yagano
fassarar mafarkinsa, yana nan zaune shiru yana
jiran fitowarta, ita kuma tana can gida
mahaifinta yana yimata nasiha tunda taji awwab
yazo taji wani sanyi acikin zuciyarta dama tun
jiya tagama shirya kayanta komai yazama
ready,idonta cikeda hawayen rabuwa da abbanta
tafito da katuwar trolley dinta taje jikin motar
awwab ta tsaya, abbanta ne ya leka yasanar da
awwab fitowarta tasowa yayi yafito shima ganin
awwab bai ci abincin ba yasa abbanta yasa aka
saka musu amota saci ahanya, awwab yana
fitowa tafara kallonsa tagefen ido lokacin yana
yiwa abba godiya, yayi kyau yana sanye da milk
colour din dafaffen boyel mai kyau yasa hula
kalarta milk sai kamshi yake kallonsa taci gaba
dayi aboye har yagama yiwa abba sallama yazo
ya bude kofar motar yashiga itama tashiga
tazauna dan kallonta yayi tasa bakar doguwar
riga da dan karamin hijab iya kafadarta shima
baki sai hawayen rabuwa da mahaifinta.
[12:47PM, 10/27/2015] UMMI A’ISHA: KWARYA
TABI KWARYA
5⃣5⃣
Na UMMI A’ISHA
Dan murmushi mai ban sha’awa yayi
yadaura belt yafara driving, har sukayi nisa bata
daina kuka ba kuma bata kalleshi ba murmushi
yasakeyi yasan dama fushi take yi dashi sai da
akayi tafiya mai nisa sannan tayi shiru tashare
hawayenta, dai dai wata bishiya yayi packing
gaba jeji baya jeji yacire belt din yace kifito kiyi