LABARIN RAYUWATA CHAPTER 7 BY Ayeshay bee

 LABARIN RAYUWATA CHAPTER 7 BY Ayeshay bee

                  Www.bankinhausanovels.com.ng 

Rayuwata

Babi na hudu

“Bafferh” na fada ina kallon shi cike da mamaki.

Da sauri ya karaso yana rike min hannu “Adda kuka me kike? Mu je ki kaini wurin Umminmu ni fa na dawo ba zan kara komawa ba kuma” wani irin faduwan gaba naji jin abinda ya ke fadi, kenan shima yana cikin damuwa?+

“Adda mu je mana, ina so in ganta” cike da tausayi na girgiza mishi kai

“Bafferh Ummi ta tafi ance min ba zata kara dawowa ba”

Kallona yayi ya kasa magana, kuka ya fashe dashi. Na jawo mu ka zauna nan muna ta kuka. Anty Amarya ta fito ta same mu a haka. “Suhaima lfy? Kuka zauna kuna kuka haka?” Ko kafin inyi magana ta dau Bafferh tayi dakin ta dashi, ni ma nabi su a baya. Daga alamun ta na gane tana jin tausayin mu. Lallashin Bafferh tayi sannan tace min in daina kuka kar ya cigaba dayi. Matan na da kirki sosai, don duk lokacin da na ke gidan in naje wurin ta, ta dinga min kyauta kenan, sweet kala kala da kayan kwalliya. Sau daya ina jin yan gidan na fadin ta na da rowa ga sa aiki sai dai ni banga hakan ba. Aiki kam tun kafin ta sani ma zan mata, su Lance abinda ya sa ta ke sona kenan. Ni kam ban damu ba, nayi na dole ma balle Wanda za a yaba min? Sau dayawa godiyan da na kanyi wa a Anty Yana kenan, a tunanin ta cuta na tayi. Sai dai duk inda naje ana jin dadin zama dani saboda son aiki na sabanin yaran ta masu son jiki.

Ranar wuni mukayi ni da Bafferh, gani yake kaman na koma mishi Ummin, ko ina nayi yana nanike dani har tsokanan shi ake. Ko da Ajidda ta zo mu tafi wasa fir na ki binta saboda Bafferh nan fa Goggo tayi ta mana dariya, wai an jimu a rana duk son zuwa yawon mu.

Drama bai tashi ba sai da yan Maiduguri su ka tashi tafiya, kuka Bafferh ya sa ka yana cewa “shi fa Ummin shi ya ke so” yin duniya anyi yaki ji yace ba zai koma ba. Ni kam har ga Allah so na ke ya koma saboda ba San gwara mishi can akan nan. Saboda ya tabbatar min ba a dukan shi kuma ba aiki sai dai ba Wanda ya damu ya kula dashi. Karshe dai da karfi Abbah ya sa shi a mota yana kuka ina kuka haka muka rabu.

Ina primary five headmaster inmu ya dauke ni a cikin wadanda za su zana common entrance, a cewar shi INA da basiran da zan iya ci. Ko da naje na na Goggo lbr tayi ta jin dadi, kawata Ajiddah ko cewa tayi “Suhaima kicewa Abban Ku ya kaiki GGC Damaturu kinga nima can zani” zaro idanu nayi nace “sai dai in fadawa Goggo” ko da na Sanar mata kallona tayi tace “anya Suhaima zaki iya makarantar kwana?” Ganin ina shirin mata kuka tace “shknn zan fada mishi, gama ni ban yadda da zaman da kike wurin Yana ba” ban amsa mata saboda INA tsoro, sai ma murnar da mu ka hau ni da Ajiddah,  daman ta fini da aji daya, to yanzu zamu dawo dai dai da ita kenan, gsky na ji dadi.

Common entrance na fitowa naga na ci exams in dai dai yanda ake bukata. Kaman wasa Abbah ya amince, nan fa ya hau min shiri ni ko zumudi na ya ki boyuwa. Ina ji Adda Falmata na cewa “shegiya, daman daga can seniors in makarantan su kashe ki Kowa ya huta, ba dai boarding ba? Ga ki gashi. ” komai ban ce mata saboda nasan za ta fadi abinda ya fi haka ma.

Ba laifi Abba ya min kokari sosai, haka ma Goggon nina biyu. Anty Yana kam ko ranar da zan tafi da na mata sallama, tsaki ta ja tace “kiyi ta tafiya ni kam ba matsala ta bace” salin alin nayi tafiya ta ban ma kowa magana ba sai Al-lawan da ya raka ni har makarantan. Shi ma ce min yayi “Suhaima kiyi karatu kinji?” Gyada mishi kai kawai nayi daga nan ban kara cewa komai ba har mu ka rabu.

Sannu a hankali na fara rayuwan boarding, ban wani maida hankali ga yin kawaye sosai ba saboda tun can daman ni ba mai yin kawayen bane. Balle ma ga Ajiddah. Sai duk da haka akwai wadanda mu ke mutunci da su ba laifi. Senior kuwa tsakanina da su dar dar ne saboda ban San abinda zai sa ni shiga case. Da ke akwai yayyin Ajiddah a makaranta muna samun gata sosai, ko ma ba don yayuin ta, Ajiddah mace mai farin jini sosai, tana da kyau ma sha Allah. Duk wanda yayi boarding ya san yanda seniors ke son shiri da kyakyawa mai gashi, kuma Ajidda ta hada duka.

Duk wani wahalan labor da aiken seniors bai wani damu na saboda nasan ina Wanda ya fi shima.

Sannu a hankali malamai su ka fara gano ni cikin dalibai masu mai da hankali sosai. Musamman bangaren maths da sciences. Ko da mu kayi tests, na ci sosai ba don komai ba sai don dedicating time ina da nayi wa karatu. Malamin maths, malam easy ake ce mai. Duk sati ya ke mana test a bangaren maths. Ganin duk tests in da yake ina kokari sosai ya sa yace yana son sani a wani quiz da ake zuwa duk shekara, ba a daukan yan JSS1 amma zai nemi izinin principal ko za ta iya bari na in Shiga. A yanda malam easy ya fada, da kyar ya samu principal in ta amince don haka dole in maida hankali domin kar in bashi kunya. Lokacin yi min extra lesson ya bani, dole duk abinda na ke lokacin na ke barin shi inje. Gab ake da tafiya hutun sallah kuma ana dawowa za a tafi quiz in.

Yawancin weekend na ke lesson in. Sai dai wannan lahadin na so inyi latti, hakan ya sa na gama shiryawa da sauri sauri na nufi hanyan classes. “Keh dan zo nan” gaba nane ya fadi saboda kiran da wata Senior ta min. Banda wani mafita dole na je. Bucket mika min inje in debo mata ruwa. Wani tashin hankalin na sake shiga Sanin layin da ke wurin diban ruwan. “Dan Allah kiyi hakuri, malam easy ke jira na zan je lesson a class” na fada nayi rau rau da idanu, rashin yanda zan yi ne ya sa na fada mata hakan. Daure fuska tayi tana kallona yayin da sauran kawayen ta da ke wurin su ka fashe da dariya. “Ke ban fa san iskanci da karyan banza wani lesson za kije da weekend”

“Ba karya na ke Allah, yana jira na ne.”

“Au da gaske dai ba za kije ba din” wata kawarta da ke gefe ta fada. Dayan kuma cewa tayi “daman yan JSS1 in nan suna fama da raini wayau.”

Shiru nayi na kasa magana. “Suhaima Adam Bello, Suhaima Adam Bello where are you” da karfi naji ana kiran sunana, juyawa nayi naga wata yar class in mu da tazo daga kudu “Yes” na amsa ina kallon ta.

“Malam easy, the maths teacher is looking for you” ban amsa mata ba sai kallon Senior in da nayi, inga ko ta tabbatar da abinda na fada yanzu.

“Suhaima wai ba ki tafi lesson in ba?” Naji an fada daga baya na, ina waiga wa naga Halima Bello jajere, ita ma ajin mu daya kuma dakin mu daya da ita. Kallon senior in da ta kirani tayi tace “Anty Nainah ke kika kirata? Kawata ce fa, lesson kuma za ta”

“Wuce ki tafi” kawai senior in ta fada, da sauri na karasa kar wata ta kara kira na.

Ranar hutun sallah Abbah da kan shi yazo daukana, shida Ya baba ne Wanda ya fara karatun jami’a a Bayero University Kano. Komawa na gida ne na ji Al-lawan na fadin ya zabi can ne saboda abokin shi Umar sanda ya koma can wurin mahaifiyar shi kuma shima a can ya ke karatu. Ni kwata kwata na manta da wani Umar Sanda can sai da aka fada na tuna na dade ban ganin shi ashe ya bar garin ne, an rage mugun iri, na raya a raina.

Kallon arziki ban samu ba balle tmbyn makaranta da karatu, sai ma aikin da aka cigaba da gasa ni dashi. Wannan karon kam ragaman girkin gidan gabadaya aka sakan min ba mai ta yani sai dai Adama in ta shigo, in ba muyi fada ba kenan, dan kwata kwata ba ma jituwa da Adama abu kadan ke samu fada, gata da saurin fushi nan da nan. Mun fi jituwa da Ummi akan ta. Da ke hutun sallah ne kwana goma nayi mu ka koma school, wannan karon su Bafferh ba su zo ba.

Mun koma ba dade ba mu ka tafi quiz in, a nan stadium inda aka tara makarantu dayawa. Ga mamakina harda wannan senior in da naji Halima Bello jajere ta kira da Anty Nainah. Mun yi kokari sosai da ke kowa dai dai dashi yayi. A ranar aka fadi sakamakon kuma munyi nasara. Tun daga nan nayi fice a wurin malamai kowa ya sanni kuma yana yabawa yanda na ke maida hankali. Ni dai duk wannan bai wani dame ni ba, ni dai burina in san abinda na ke yi ko zan samu in cikawa wa kaina burin zama wani abu a nan gaba.

Haka rayuwan makarantar ta cigaba yau dadi gobe rashin ta. Zuwa yanzu na riga da na sa wa zuciya irin ta wa kaddarar rayuwan kenan, shiyasa ko kadan ba aji na a cikin masu complain in an sa mu abu a makaranta. Watarana da yamma bayan an tashi prep mu ka tsaya share aji dani da Halima da wasu classmates inmu guda biyu. Da ke an yi kura gabadaya ajin ya dauka har desks da chairs. Muna cikin aikin Halima ta ja gefe ta zauna tana maida numfashi. Bintu da mu ke tare ne tace “Halima ki fa tashi mu karasa aikin nan na sanki da ragwanta yanzu sai kice kin gaji bayan kin san duty inmu ne” ban kawo komai a raina ba saboda duk Wanda ya san Halima ya Santa da son jiki da shagwaba, komai yayarta ke mata a makarantar, irin yaran nan ne da basu saba da aiki a gida ba. Kaman da wasa na fara jin nishin yayi yawa irin na Wanda ke kokarin yin numfashi. Da sauri na ajiye duster in da ke hannu na na nufe inda ta ke “Lfyn ki kuwa” lokacin dukkan su biyun sun bar abinda su ke ganin da gaske ba lfyn ba. Kokarin daga ta mu ka fara ganin yanda abin yayi yawa, kaman numfashin na nema kwace mata gabadaya. “Mu wuce dispensary” na fada da sauri mu kayi hanya. Magana naji ta fara yi duk da kyar ya ke fito “in inha inhaler” abinda ya sauka a kunne na kenan. Nan ta ke na tuno ta taba fada mana tana asthma, sai dai ba Wanda ya dauki abin serious ganin bai taba tashi ba. “Yana ina Yana ina?”

“School bag” abinda kawai naji ta anbata kenan na afka da gudu nayi hanyar hostel su kuma su ka wuce da ita dispensary in. Duk nisan hostel da classes area, cikin minti kalilan na isa saboda gudun da na ke faman yi. Naci sa’an dauko inhaler ba tare da na tanka duk wani Wanda ya ke min magana ba. Na kusan fita hostel naci karo da yayar ta tee da assistant headgirl inmu. “Halima” kawai na fada ina nuna mata inhaler, ban saurari me za tace ba na cigaba da gudu. Ko da na isa dispensary in na tarda nurses in tsaye sun rasa mafita, da alamun jira na su ke. Ina mika musu ta shaka sai gashi ta saki ajiyan zuciya ta kwanta. Ruwa ba karba a wurin nurses in na sha saboda gudun da na sha, ban san dalili ba naji kirji na na faman zafi. Baya min haka sai in naje debo ruwa yawancin. Dai dai lokacin sister in nata su ka shigo a rude, wurin haliman ta karasa tana duba ta.

Nishin nishin da na ke tayi yasa nurse in tmby na lfy “kirji na na zafi sosai” na fada.

“Ina ga saboda gudun da kika yi ne, bara na baki magana sai ki kwanta ki huta” Sistern Halima ce ta juyo tana kallo na “sannu koh, mungode” gyade mata kai kawai nayi na amshi magani.

Ban san bacci ya kwashe ni sai farkawa nayi naga su bintu sun tafi sai sistern Haliman da friends inta. “Sannu ko? Kirjin ya daina?”

“Eh” na amsa mata.

“Ba kuma inda ke miki ciwo” girgiza mata kai nayi, inaji tana cewa “nurse za mu iya wuce hostel dasu.”

“Suhaima tashi mu tafi hostel” ta fadi sai dai tun kafin na tashi ta fara dagoni. Tana rike dani, kawar ta ta rike Halima mu ka isa hostel. Maimakon naga mun nufi hostel inmu sai naga ta dau hanyan nasu. Ban samu daman cewa komai ba har mu ka isa. Tea mai kauri ta hada ta bani nasha bayan ta tafasa ruwan zafin a heater. Ga mamakina chips, kwai da kaza ta ajiye mana muci ni da Halima, ina mamakin inda ta samo shi sai dai ba halin tmby. Kasa sakin jiki na ci abincin nayi. “Suhaima kifa ci abin nan da kyau kina jina?” Murmushi kawai nayi na cigaba da turawa.

Tun daga ranar ta fara kyautata min komai za ta wa kanwar ta zata min, har Ajiddah ta fara jin haushin na daina bin ta wurin yayyin ta. Sai dai ko ban so zuwa wurin Senior Nainah ba dole ta ke Sani sai naje. Kullum zata sa a  debo mana ruwan wanka, ba ruwan da layi za mu Shiga har dinning ma haka, da za a wuce gida har wanki ta min. Ana gobe za a tafi ta aiko min hadaddun turare designers da takalmi heels. Abin ya bani tsoro saboda zuwa lokaci na san abinda ake cewa school lovers, ko kuma ince school mummy da school daughter, yawancin sune za kaga suna wannan kyautan wa junan su, gudun tunani abin da ba haka ba. Godiya na mata sosai saboda ba daman in ki amsa. Kowa ya tashi a cikin Damaturu ya San baban su babban mutum ne mai tashan kudi, hakan ya sa ba abun mamaki bane irin kyautar da ta ke. Ni dai kowa na marmarin zuwa gida amma fa banda ni saboda nasan azaban da zan tarar.

Abbah da kan shi yazo daukana, shida Ya baba ne Wanda ya fara karatun jami’a a Bayero University Kano. Komawa na gida ne na ji Al-lawan na fadin ya zabi can ne saboda abokin shi, Umar sanda ya koma can wurin mahaifiyar shi kuma shima a can ya ke karatu. Ni kwata kwata na manta da wani Umar Sanda can sai da aka fada na tuna na dade ban ganin shi ashe ya bar garin ne, an rage mugun iri, na raya a raina.

Kallon arziki ban samu ba balle tmbyn makaranta da karatu, sai ma aikin da aka cigaba da gasa ni dashi. Wannan karon kam ragaman girkin gidan gabadaya aka sakan min ba mai ta yani sai dai Adama in ta shigo, in ba muyi fada ba kenan, dan kwata kwata ba ma jituwa da Adama abu kadan ke samu fada, gata da saurin fushi nan da nan. Mun fi jituwa da Ajiddah akan ta.

A ranar da mu ka koma makaranta da dare, Anty Nainah (kaman yanda Halima ke kiran ta ta Sani nima in dinga kiran ta) har corner ta tazo, provisions mai uban yawa ta kawo min. Girgiza ma ta kai nayi, na ce mata “ni fa Abbah ya siyan min dayawa” hararana tayi tace “na Abbah daban na wa daban, kuma kar ki kara fada min haka sai dai ko in baki dauke ni yayar ki ba” hakanan dole na na amsa, ba don raina na so ba.

Shakuwa mai karfi ne ya shiga tsakanina da Anty Nainah, ba don komai ba sai dan yau da gobe ya wuce wasa. Dole na saki jika da ita, ba irin labarin da ba ta bani, kai har na samarin ta. Wanda ya hada da malam idriss, social master inmu. Sosai ya ke son ta. Ba ma shi kadai ba malamai dayawa, sai dai shi in ta fi bashi fuska. Kowa ma zai so Nainah, ga kyau ga kokari, ga tsafta. Ko min ta fes fes gashi kuma ba abinda ta nema ta rasa.  Akwai wata senior Zainab kyari a SS3, ita ce assistant headgirl, ba karamin dasawa su ke ba. A cewar ta kawarta ce. Dan duk sanda na je wurin ta bata nan to  tana wurin senior Zainab. Ita ke kare mata duk wani sharrin yan SS3, ta tsaya mata sosai, ba Wanda ya isa ya mata abu a makarantar. Kai har malamai ba kowa ke taka ta. Abinda ke bani mamaki shine kowani abu na damun ta tsab za ta same ni ta fada min, ba ta la’akari da ta girme ni ko wani abu kaman tazaran ajin da ke tsakanin mu, tana SS2 ina JSS1. Ganin haka ya sa na ke kokarin bata shawara dai dai gwargwado iya wanda kwakwalwata da tunani na zai iya batan.1

Watarana muna zaune a gaban hostel tana lbrn yayan ta da ke karatu a UK tace min “Suhaima ni kam wani layi kuke a sabon fegi?”

Kallon ta na danyi ina wani nazari tace min “ko baki so in zo gidan Ku in gaida mamanki?” Nan da nan idanu na su ka ciko kwalla, ganin haka ta rude tana tmbyna dalilin kuka na. Shiru na mata karshe ma na tashi na tafi. Ina ji ta na kira na share ta, ai ko ina hawa kan gado naji sallaman ta a hostel inmu. Pretending nayi ina bacci, bisa dole ta hakura ta kyale ni.Rayuwata

Babi na biyar

As usual washegari da safe ita ta samo min ruwan wanka, ban ce mata kala ba itan ba ta tanka ba sai ce min tayi “Suhaima dan Allah Ku dinga karatu da Halima she is lacking behind sosai” turo baki haliman tayi, abin ya ban dariya. Halima irin shagwababbin yaran ne komai ba su San wahala, sau dayawa ina kokarin jawo ta muyi karatu sai dai wasa na janye mata hankali tilas na kyale ta.+

Ba ta taba kawo wani abu a shirinmu da yayar ta ba, a tunanin ma kokarina ya sa yayar ta ke jawo ni a jiki saboda in dinga koya ma ita haliman abu abu. Itana sosai ta ke ji dani, komai Suhaima kaza Suhaima kaza.

Muna cikin prep sai ga Anty Nainah ta shigo har ajin mu. Har seat ina tazo ta same ni ina note. Daukan note in tayi tace min “taso muje” ba musu na bita, hall ta kaini, duk seniors a ciki suna karatu. Gefe daya tasa mana kujera mu ka zauna “cigaba da note inki” tun daga nan ba ta kara ce min kala ba nia ban tanka ba sai dai duk na kasa abun kirki saboda kallon da ta ke bina dashi. Can dai da ta gaji ta ce min “abinda na fada jiya ya bata miki Raine?” Girgiza ma ta kai nayi ba tare da na dago ba.

“Then, why are you not normal, akwai wani abu ne? Ki gaya min kinji” wani iri naji jin yanda ta damu da matsala ta. Ajiye note in nayi nan da nan sai ga hawaye a idanuna. Hakuri ta fara bani, kawai na girgiza mata kai. A hankali na fara bata lbrn halin da na ke ciki a gidan mu. Na sha mamakin yanda ta dinga kuka, daman she is so sensitive. “Kuma ba Wanda ya taba fada miki inda Ummin ta ke?” Girgiza ma ta kai nayi, nan fa ta hau rarrashi na. Sai cewa tayi “I think i have a plan amma kar ki damu slowly zai yi working” bangane me ta ke nufi ba amma dai kawai nayi shiru.1

First visiting in da aka fara yi, mum insu na zuwa ta dauke ni mu kaje “mum ga kanwata fa Suhaima kawar Halima”

“Au itace Suhaiman? Zo yata ki zauna kinji” ban yi wani mamakin yanda ta sani ba considering yanda mu ke da yaran ta. Ban tashi mamaki ba sai da naga provision in da aka musu kashi uku ne, wato har dani a ciki, rasa bakin magana nayi domin a bin yafi karfi na. Gabadaya yan gidan su na da kirki. Banyi tsammanin za a zo min ba. sai bayan la’asar kwatsam na ga Goggo da Adama. Na ji dadin zuwan su sosai, again Anty Amarya ta zo da Anty bilki tare da yan gidan su Ummi. Goggo ta bada sako a bani, ba ta samu zuwa ba saboda kafan ta ya matsa mata kwana biyu kuma. Su Adama ne su ka zo da sakon Abbah. Ba laifi ranar nayi murna sosai.

Na maida hankali na ga karatu sosai, ganin nan yafi Islamic center competition. Muna karatu da Halima da wasu friends inmu Wanda mostly ni ke koya musu abubuwan da na gane a aji. School activities ko irin su labor sau dayawa ba mu cika yi ba saboda Anty Nainah ba ta bari a samu ga senior Zainab kawarta so ba yanda aka iya. Zagi kam muna shan shi, taren latti kam ban yarda a kamani sai randa tsautsayi ya afka. Tsakanina da malamai ko lafiya kalau, domin ba malamin da zai yi pointing ina yace ina da matsala dashi, sai ma yabo na da su ke yawan yi. Har seniors in ma sai dai irin Wanda ke daura ma mutum laifi ba gaira ba dalili. Sai da yan ajinmu da yan gaban mu akwai masu jin haushi na saboda Anty Nainah. Ni dai ba Wanda na ke shiga sabgan shi, kwata kwata ban cikin marasa jin mate, da banda duka ba abinda su ke sha a makarantar, kullum suna cikin case. Halima kam ba ta da wayon da har za ta ma wani rashin kunya amma Ajiddah kam A ce. Nayi nayi ta daina amma ina, abin yafi karfi na, ya zamo sai dai in tazo tana kuka in lallashe ta.

A gaskiya ni dai banji rayuwan makaranta kaman yanda kowa ke ji ba, don na gwammace ayi ta zama a makarantar akan gida. Duk lokacin da nayi tunanin saina yi godiya ga Anty Nainah, domin ita ce silar komai…

A haka muka fara jarrabawa, Karatun na ke sosai bbu kama hannu yaro, duk da duk yawancin karatun koyawa mutane na ke hakan ba karamin taimako na yake ba. Sai dai karatuna na islamiyya kam ya ja baya sosai, duk ina bitan qur’ani amma kuma ban samun kari. Ko da na fadawa Ummi ce min tayi “bakomai in mun koma gida za mu cigaba”

Tun da mu ka fara jarrabawa na rage zuwa gun Anty Nainah, sai ya zamo yawancin sai dai mu hadu kan hanya. Ta kance “lallai kanwar tawa ta manta dani, karatu ya dauke min ke” dariya kawai na ke in wuce, duk da haka ba ta fasa min komai da ta ke min ba.

Ranar da aka gama jarrabawa da yamma, mu ka fiddo wankin mu zamu yi ni da Ajiddah. Ita dai Halima ko gwada wankin ma ba ta taba yi ba, ni ban ma tunanin ta iya ba kwata kwata. Tana gefe da wasu mate inmu, dayawa suna wankin kaman mu wasu kuma muna hira. Sanyi ake sosai da ke farkon December ne masu kokarin wanna na hada hadan daura ruwan zafi a katon murhun da aka kawo da babban tukunya. Anty Nainah ne su ka shigo da senior Zainab, da alamun su ma ruwan wanka su kazo nema. Har ta wuce ba ta ganmu ba, Halima ta fara kwala mata kira. Da sauri ta juyo tana fadin “yauwa daman ina nemanki, Ya Zaid na son Ku gaisa”

“Waya kuka yi dashi?” Ta tmby. Ya Zaid saurayin Anty Nainah, duk cikin samarin ta tafi ji dashi kuma tafi son shi, Family friend in sune. Kuma iyayen su mata first cousins ne. Saboda shi kullum tana gidan su a Abuja Hutu. Shi ma musamman in yana kasar yana zuwa Damaturu kawai don ya ganta. A gida kowa ya Sani, jira ake dukkansu su gama karatu kawai ayi auren.

Magana su ka cigaba da yi tsakanin su. har za ta wuce ta dago kai ta ganni. Harara ta bini dashi sannan ta girgiza kai. Murmushi nayi domin tabbas na san na mata laifi. Kasa shiru tayi tace “abin har ya kai ki ganni ki ki min magana ko?” Hakuri na hau bata tace min “Wayace kiyi wanki? Bana hana ki ba”

“Yi hakuri Anty ba zan iya bari wasu su min wanki na bane bayan zan iya da kai na” sa wa ta ke a mana wanki, ni kuma ban son hakan. Ta yi ta wahalar da yaran mutane a kanmu tana sa ana jin haushi na a banza. Yanzu haka na gaba damu sun fara cin buri wahalan da za su bamu in har ta bar school in.

“Shknn tunda ba kya so ni sai in miki da kaina, ban so kina wahala kwata kwata” dariya nayi nace “kar ki damu ni kam na saba”

“Ai abinda ya sa ma ban son kiyin kenan. In kinzo school sai ki huta kar abun ya hade miki biyu na gidan ma i will tackle it”

Dariyan takaici nayi, a raina ina fadin ko taya za tayi hakan “Allah ki barshi kawai zanyi” na ce mata amma fir taki. Dole na barta, amma kuma nima na cewa nayi sai da mu kayi tare duka har da na Ajiddan mu kayi mu uku, ba laifi tana kokarin yi ma Ajiddan ma abubuwa ganin Kawa ta ce.

Haka satin banzan ya wuce, kullum ba abinda ake banda zama ayi ta hira sai ko masu kokarin karatun novel. Tsakanina da Anty Nainah ko mun saba sosai har ji nake daman ita ce yayata ba Adda Falmata ba. Har Saurayin ta Ya zaid ta na bani muna gaisawa, shima yana da kirki sosai. Har kitso ta sa aka mana kanana masu kyau da lalle.

Ranar hutu da safe, cike da farin ciki dalibai ke ta fita assembly cike da farin cikin tfy gida. Ni dai ganinan ne kawai, ko bakomai ina son ganin Goggo, in ga kafan na ta ko ta samu yayi sauki. Ban wani maida hankali a abinda ake yi ba a assembly sai da naji an kira sunan Anty Nainah a matsayin wanda ta zo na Uku a ajin su. Na San ina da kokari sosai amma ni ina zama in duba abinda aka koya mana, ina bita sosai. Amma Anty Nainah ba ka taba ganin ta tana karatu, kai ba ma tayi. Kawai dai she is naturally brilliant.

Ina cikin tunanin naji ana kiran “Suhaima Adam Bello” ni abin ma mamaki ya bani Saboda ban ma San anzo ajin mu ba. Bayan nan ma har ga Allah ban taba kawo zan zo first position ba Saboda competition in da akwai. Cike da farin ciki na amso result ina da gift in da aka bani. Ina ji a raina daman Ummiyna na nan in nuna mata, na San ba karamin alfahari za tayi dani ba. Anty Nainah ce ta rage min damuwan da na ke ciki Saboda yanda ta nuna jin dadin abinda na ci sosai. Wannan Karon ma da kyautatukan da ta bani.

Ban San wa zai zo dauka na, sai dai shiru hakan ya sa na fara zargin ko Abbah ba ya gida ne? Gashi su Ummi har sun tafi ban bisu ba. Ana zuwa daukan su Halima, Anty Nainah ta sa dole sai da na shiga motar su muka tafi. Ba gida mu kaje ba, gidan su da ke Commissioners quarters mu ka wuce. Sai da muka huta, muka ci abinci, nayi wanka. Mum insu ta bani bakin Abaya mai kyau na sa sannan mu ka tafi da driver in su da Anty Nainahn gidan mu. Ita kam Halima cewa tayi ta gaji, ramakon bacci za tayi ba zata bi mu ba.

A kofan gidan mu su kayi parking sannan mu ka fita. Da Al-lawan na fara cin karo, kallona yayi da murmushi a fuskan shi yace “kin hutar dani wlh Suhaima da yanzu na ke shirin zuwa dauko ki” na kan rasa kirki irin na Al-lawan. Wai a hakan shi kadai ne mai mutunci a gidan, amma har bayan azahar ace sai lokacin za a tafi dauko ni, bayan tun 8:00am na safe ake sakin dalibai. Gaisawa su kayi da Anty Nainah ba tare da ya tmby ni ita ma muka shiga gidan. A kofan shiga na ga Yaya baba, da ke lokacin December ne sunyi hutun school su ma.

Tsayawa yayi da mamaki yana kallon mu. Sai dai suna hada ido da Anty Nainah na ga ya saki murmushi. Daman dai na sa za a rina Saboda son matan shi yayi yawa, mamaki ne ya kama ni jin ta ambaci sunan shi. “Adams kai ne”

“Nainah ke ce a gidan mu?” Ya fada yana zaro idanu. “Mu dai shiga daga ciki” ya karasa, yana binta da kallon mamaki. Akwatina da ke hannun ta yayi saurin amsa, abin ma Sani sakin baki yayi gabadaya. Ba kowa a falon, hakan ya Sa nagane duk suna daki kenan. “Bara kira Anty Yana” ya baba ya fada yana nufan hanyan dakin ta. Girgiza kai kawai nayi na fara kokarin daukan akwatin nawa da ya ajiye na cewa Anty Nainah “bara in kai daki”

“Muje mana” ta fadi tana jan akwatin. Dakin na nan yanda na San shi ba, bai yi wani dauda ba sosai amma kam ba kaman ina nan ba. Kan gadona Anty Nainah ta zauna yayin da na ke nema wa akwatin wurin zama. Da ke daman gadaje biyu ne a dakin, daya nawa daya na Adda Falmata. In har ba ayi baki ba fa amma, domin ko da mutum daya ne ya zo gidan dole na nake sauka kasa in kwanta.

Adda Falmata ce ta fito daga toilet tana bin mu da kallo. Ganin haka Anty Nainah tace mata “sannun ki” kaman Wanda aka sa dole ta amsa da “yauwa sannu” gudun laifi yasa na gaishe ta tana tabe baki ta amsa. Ina gamawa muka fita falon. Ya baba sai murmushi ya ke, Anty Yanan na zaune kan kujera. Faran faran su ka gaisa da Anty Nainah sannan nima na gaishe ta. Ban tabbatar da an amshi bakuntan Anty Nainah sai da naga Sadiya ta kawo ma ta ruwa, zobo da donut. Ba ta wani ci ba tace za ta wuce gida. Ba Wanda ya tmby ta su suka dauko ni daga makaranta ne? Itan ma ba tayi bayani ba. Har Mota na fita rakata Yaya baba na bin mu a baya. “Adams ina abokin ka wai? Still alive?” Ta fada tana murmushi

“Eh dole kice haka ai tunda kin wulla mu a kwata”

“Wane ni? Yanzu ma ba wannan ba ashe Kaine Yayan Suhaima no wonder jinin mu ya hadu da ita ashe kanwata ce” washe hakora yayi yana fadin “kwarai kuwa”

Wayarta ta mika mishi tace “sa min numbanka ina so in dinga jin kanwata”

“Au kanwarki ma kawai ko” dariya tayi tace “after all is your number, we will talk, Suhaima sai munyi magana ko?” Gyada mata kai nayi ina fadin “nagode Anty Allah ya saka da alheri” harara na tayi sannan ta shigo mota su ka wuce.

Muna shiga falon, Anty Yana ta cewa Ya baba “wannan ba yar gidan Barr Bello jajere bane?”

“Eh tace mana Anty Yana” Ya amsa

“To ke Suhaima ina kika Santa?”

“Anty Yana Yayar kanwata ce Halima, su suka dauko ni daga makaranta” tabe baki Anty Yana tayi tace “ke kam kin iya kwashe kwashe” ban tanka ba sai Adda Falmata tace “ni kam ba NTIC mamudo ta ke bane?”

“Baban ta ya cire ta wai ba taji, kinsan lokacin soyayya su ke da Daddy Dafchi Saboda shi ma aka cire ta”

“Yaya baba Daddy abokin ka” Adda Falmata ta tmby. Ni kam wuce wana daki nayi domin in shirya.

Tun daga lokacin na samu sauki daga gun Ya baba, ban San me ya shiga tsakanin su da Anty Nainah ba amma yawancin kullum sai ya bani wayan shi munyi magana da ita. Kai har abubuwa ya kan siyo min hakanan kurum. Adda Falmata kam in dai gaban shi za ta min abu ba ta isa ba. Wani aikin gidan ma dole ya ke sata ta taya ni, hakan yasa na samu dan sauki a abubuwa da dama.

Wani weekend ina gidan Goggo, mun je islamiyya da su Ummi mun dawo, ina shafawa Goggo man zafi a kafan ta kawai naji sallaman mutane. Anty bilki ce ta leko dakin Goggo tace min “Suhaima ki zo wasu yan mata sun zo suna tmbyn ki” “toh fa” na ambata ina tunanin su waye za su zo wurina.

Halima na fara gani sai ko Anty Nainah a gefen ta. Kasa boye mamakina nayi kawai na tsaya ina kallon su ina zaro idanu “Ko mu tafi ne?” Anty Nainah ta fada. Da gudu na karasa na rungume ta sannan na rungume Halima. “Mun zo gaida Goggo ne” Anty Nainah ta fada. Dakin Goggon na kai su, su ka gaisa. Sun kawo mata fruit kala kala. Wasa wasa su kayi ta hira da Goggo, daman na bata lbrn ta ai ko na tayi ta mata godiya da sa mata albarka. Na dauka lokacin za su tafi amma Halima tace min wuni za suyi. Har side in Anty Amarya mu kaje, mun dade a can. Kasa hakuri nayi na tmby ta tsakanin ta da Ya baba “son mata fa gareshi Anty” dariya tayi sosai har da rike ciki sannan tace min “come on am just fooling him around saboda ya kula min da kanwata ni da nake da mijin aure” lallai na jinjina wa idea inta. Tare mu kaci abinci muna ta lbr da ita. Halima ko Ummi na shigo su ka kebe suna hira, daman Halima ta fi shiri dama sabo da Ummi a kaina. Hakan yana da alaka da rashin surutu na, sai Wanda ya San ta yanda zai bi da nine mu ke sakewa dashi. Sai bayan magriba sannan mum tazo daukan su. Ita ma har ciki ta shigo ta gaida Goggo sannan su ka wuce. Har a raina naji dadin zuwan su sosai.

Kaman da wasa har hutu ya kare mu ka koma makaranta. Sau da dama na kan zauna inyi tunanin guduwa nima a nemi ni a rasa kaman yanda mahaifiyar tawa tayi, sai da na kan tmby kaina ina zanje? Na kanji ana cewa duniyan fadi gare ta, ni ko ba wanda na Sani balle in he wurin. Wahalan duniya kam ba Wanda ban sha ba wurin Anty Yana da yaran ta, har sadiya tsab ta ke takani, ta fada min abinda ta ga dama kuma a zauna lfy. Ance ba a sabo da wahala amma nikam ba ya zame jikin a cikin gidan nan. Sai da akayi zamanin da ko tsinke in wani zai dauka sai na zo na dauko mishi. Duk ciki ba abinda ke kona min rai kaman aiken daren da ake hada ni dashi, duk dare kaman aikin farilla dole sai nayi shi duk don a dalilin rashin mahaifiyata. Ummi ba ta min adalci ba a rayuwa, kowani memories inta banda shi na arziki. Wadanda na dan rike ma a hankali su ke tafiya, tun ina yawan tuna t har yazo sai an zage ta ko an aiba ta ta ke fado min a rai.

Rayuwan makarantar ya cigaba da tafiya kaman yanda ya ke a kullum. Class, hostel, dinning, masallaci da sauran su. Still Anty Nainah ta tsaya min sai dai a yanzu ban yarda ta sa a min abubuwa saboda nagane bakin jini hakan ke ja mana. Duk abinda mu ke bukata sai dai muje tare da ita a nemo shi yafi sauki, sannan ko dan Halima da sangarcin ta yayi yawa. Bada ban Anty Nainah i used to wonder yanda za tayi coping da school life in.Kaduna, Nigeria.

Barr Mustapha dauke da dan shi haydar a jikin shi, ajiye manuscript in yayi gefe yana kara kallon yaron nashi da kyau da ke ta faman wasan shi hankali kwance. Bai tunanin duk halun irin na mimin shi zata iya barin dan ta Haydar cikin irin gararamban Rayuwan da Suhaiman tayi fama dashi. Shi kam yafi yarda ma ace littafine dai ta kirkira hakannan ta rubuta. Eh ya sha jin labarin wahalan kishiyan uwa da yara da dama ke sha, sai dai bai taba gani ya faru akan wanda ya sani ba. Shi kam saboda irin haka ne yake jin mimin ta ishe shi rayuwa sai dai irin sabbin halin da take ta faman tsiro dasu ya ke sa shi jin ba shakka zai iya sa ma kudurin alkalami ya ja layi akai.+

Dai dai lokacin kuwa maryam inta farka daga nauyayyan baccin da take ta faman yi. Ya san ta kan yi bacci sosai amma bai kai bacin na yau ba. Shi da ya dawo bayan wasu kwanaki daga wani gari dole yana bukatar matar shi amma ina bai samu daman hakan ba saboda mugun baccin da take tayi. Kallon ta yayi yana wani nazari a zuciyan shi, tabbas mimin haka ta mishi a cikin Haydar. To kuwa ba shakka ya fara zargi yanzun ma tana dauke da ajiyan shi. Hannun shi yasa akan wuyan ta yana kallon cikin idanuwan ta, nan da nan kuwa ta sha mur hade da fadin “Ba zanje asibiti ba lafiya na kalau” tabe baki yayi ya hada mata da harara “ko baki je asibiti ba ni xanje chemist, am suspecting something”

Dan zaro idanu tayi amma dake ta fara sanin kan duniya sai tace mishi “Ba sai ka sha wahala ba ma ai, am two months pregn…” Bai tsaya sauraran karshe zancen nata ba yayi saurin mikewa tsaye, mutna ne yayi saurin mamaye kan fuskan nashi saidai zanceb da ya biyo baya yasa annurin shi gabadaya daukewa. “Ni fa wlh ban shirya kara haihuwa ba, Haydar ma nawa yake? I can’t believe drug in da nake sha bai yi min aiki ba” kallon ta kawai ya dinga yiyana jin kaman yaje ya sheke ta da duka, a gaskiya maryam ta fara bashi tsoro ma shi. Abinda ya daite mishi kai a matsayin shi na lawyer ya sha ganin mata sun kawo karan mijin su akan tilasta musu shan maganin hana daukan ciki bayan su suna bukatan hakan, ko kuma wanda suke son rabuwada miji saboda bai haihuwa. Amma shi nashi matan da kanta mata ke shan maganin ba tare da sanin shi ko yardar shi ba. “Mimi me ke faruwa da ke?” Kokarin danne zafin da ya keji yana taso mishi yayi sanin ba zai amfana mishi komai ya mata wannan tmbyn. Kokarin bayani ta fara mishi,  sai yanzu ya dan fuskance ta. Duk dai bayanan bai wuce na yanda ba taso ta hada yara biyu ba, Haydar ma bai gama girma ba kuma tazo tana wahala biyu. Most importantly a gare ta kuwa shine jikin ta, ya fahimci hakan ne saboda yanda ta ke ta emphasizing abun.3

Murmushin dole yayi yana kallonta yace “ni kam tun yaushe na sanki ne?” Bata bashi amsa ba don haka ya cigaba da cewa “Tun kina ganiyar neman tsokanar ki lokacin kina yar kankanuwar ki don haka ki daina tunanin wani sauyi daga gareni a gaba. Sannan bance miki planning ba abu bane mai kyau sai dai kuma laifin shine zuwa da kika yi kika fara ba tare da shawara dani ba bayan kuma kinsan ina da hakki akan haka” still dai ba tace komai ba don haka ya mike again sannan ya kalle ta da kyau “ki tashi ki wanke idanun ki muyi maganan fahimta a tsakanin mu, ni dai gargadin da zan miki shine in baki canja wannan halayen da kika kirkiro lokaci guda ba to kuwa tabbas zaki ga abinda baki taba tsammani ba. Bazan ce miki ga abinda zai faru ba amma the worst can happen” ta dan tsorta jin yanda yayi maganan iya gaskiyan shi, ita kam ba ta saba ganin hakan a tattare dashiba don haka tayi kokaron maida abun wasa “Wlh gabadaya ka canja” dan turo bakin ta tayi. Bai kuwa san sanda ya saki murmushi ba don duk sanda tayi haka ji yake ta burge shi sosai. Hannun shi yasa ya dan jawo bakin kafin yace “ke ma in canjawa kika yi ai maman baby” maganan yayi yana kai hannun shi kan cikin ta. “Ina son yara sosai maryam sodon’t push me, in har baza ki bani zan nemo su ni kuma daga wani tsotsan” cikin kwanciyar hankali ya mata maganan. Ya kuwa hango tashin hankali kwance a cikin idanun ta, sam mimin shi ba ta kaunar maganar kishiya. To dake shi in ma ba ra’ayi  yi gare shi ba, daman Suhaima ce ta tsole mishi ido da kyawawan halayen ta but kwana biyun nan barin ma da ya san labarinta ya fara ja baya da abun. To daman fa? Kana tsammani abu ne sai kuma kaga akasi mai girma daga wurin shi. Koma dai menene he is still willing to help her. Ba kuma shi ya kara samun sararin cigaba da karanata labarin taba sai da ya shiga office insu da ke a garin Kaduna.

Rayuwata

Babi na shidda

Wani hutu da muka yi JSS2, second term. Wurin karfe Tara da rabi na dare Anty Yana ta bani aiken bread, sugar da lipton. Sanin ba daman mata musu, gashi Abbah bai gari ya sa na amsa na fito a tsorace. A kofan gidan Al-lawan ne. Zaune da abokanan shi suna hira, ban bi wani ta kansu ba nayi Saurin wucewa burina in yi Sauri inje in dawo.

Na wuce su kadan naji kaman ana bina, ban damu in waiga sai ma kara saurin da nayi. “Yayi ke sauri ko baki son rakiyan ne?” Daga baya na naji maganan ta fito. Na San muryan Al-lawan bane saboda haka na ki juyawa. Sauri naji an fara har sai da ya kamo ni yace “ban miki sallama ba ko? Afuwan beauty Assalamu Alaikum” a hankali na juya na kalli gefe na, na dauka daya daga cikin abokan Al-lawan ne ga mamakina wannan kam bakon fuska ne ban San shi ba. Gudun magana ya sa na amsa sallaman nashi. Daganan ba Wanda ya kara magana cikin mu har mu kaje shagon na siyo abinda zan siyo mu ka dawo. Bakowa a kofan gidan, duk abokanan Al-lawan in sun watse. Har kofan gidan ya raka ni “mu kwana lfy Suhaima” bance mishi kala ba na shiga gidan, na kaiwa Anty Yana sakon ta. Kallon Lipton in tayi tace “ke kam na rasa kwakwalwa irin taki kin taba ganin mun sha top tea ne a gidan nan? Kin sanni kin San ban son iskanci don haka ki koma ki canjo maza” sunkuyar da kai nayi cike da takaici na rasa abin yi, gabadaya tsabagen sauri yasa ban tsaya na duba abinda aka bani ba. A hankali na fara magana “Dan Allah Anty Yana kiyi hakuri wlh gobe da sassafe zan canjo”

Wani mugun tsaki ta je “Wlh Suhaima sai kin canjo Lipton in nan, gwara ma ki tashi ki tafi kafin dare ya kara yi, bana cike da iskanci, ke da kika yi gadon yawa ma har ke wani fadawa mutum dare? Uwarki tana can yawon duniya?” Wani tululin bakin ciki ne naji ya tsaya min a kirji. Na kan rasa dalilin da yasa har yanzu ban iya jurewa duk zagin da za ayi wa Ummi sai naji bakin ciki, sau dayawa abinda Adda Falmata ke using kenan tana ba ta min rai. Jiki a sanyaye na tashi na nufi wajen, idanuna sun yi ja kafin kace kabo na hawaye sun fara saukowa. Rayuwa kenan, da na dawo daga islamiyya Ummiy ba ta kara Bari na fita waje sai kuma washegari. Amma yau ni ake aika wurin karfe goma.1

A haka na fita ina share hawayen da ke zuba daga cikin idanuna. Na danyi nesa kadan daga gidan mu naji kaman ana kallo na. Dago kai nayi na hango shi a tsaye, da dan nisa dani yana kallo na. Sauke kai kasa nayi na cigaba da kuka na, “Me kuma kika fito yi again?” Ban ma San ya zo inda nake ba sai maganan shi naji.

Na yi niyyan share shi sai kuma naga illan hakan, ko bakomai zai iya rakani kuma tabbas tsoro na keji.

“Lipton zan canjo, ba shi ne ake so ba” girgiza kai yayi “mu je in raka ki, kiyi hakuri komai lokaci ne watarana sai labari.” Wannan karon ma har mu kaje shagon mu ka dawo ba Wanda ya kara magana, sai da mu kaje kofan gidan mu yace “Sunana Amir, sai da safe” juyowa nayi da murmushi akan fuskana na furta “nagode Ameer” gyada kai kawai yayi ya min alama da hannu akan in Shiga gidan.

Washegari ma haka ya kara faruwa har shagon ya rakani, a dawowa ya ke ce min “Al-lawan yace JSS2 kike a GG?” A hankali na amsa mishi da “eh”

“Beautiful young girl ashe na girme ki ma sosai” murmushi nayi, “ai daga ganin ka ma ba yaro bane”

“Allah da gaske beauty, SS2 fa kawai na ke”

“SS2 ba kawai bane, wani school?”

“New horizon” zaro idanu nayi “amma ba a garin nan ba?” Girgiza kai yayi yace “A Minna ne, Niger state?”

“Kuma tun daga nan kake tfy? Nasan da nisa” dariya ya min yace “beauty kenan da a garin nan nake ai da kin Sanni, Kaduna na ke zama amma mu yan asalin garin nan ne hutu mu kazo” sai a lokacin na gane dalilin da yasa ban taba ganin shi sai lokacin da ya raka ni shagon. Tun daga ranar kullum dare Anty Yana ba ta fasa aike na na haka kuma Amir bai fasa min rakiya ba, muna tafe muna hira dashi. A hankali sabo mai karfi ya shiga tsakanin mu. Ba wani girma na Ameer yayi ba a lokacin ina sha hudu shi kuma yana sha shidda. Tun yana raka ni haka kurum ranar da mu kaje ya Sani dole sai da na dauki drink, ban so amma dole ya tilas tani, a cewan shi ban dauke shi  Yaya ba kenan.

5 days ya rage mu koma school, hakan yayi dai dai da komawan su Amir Kaduna. Ban san na saba dashi sosai hakan ba sai da ya ke fada min tafiyan nasu. Ji nayi gabadaya ba dadi, kaman in hana shi tafiya sai dai ba dama. Ana washegari za su tafi da yamma, ni kuma ina shirin tafiya Ajeyari Goggo ta aiko inje. Hanyan kwaltan da ke tsakiyan layin Wanda ba nisa damu na nufa duk da nasan nan in yafi wahalan samun abun hawa akan babban kwaltan. Har ga zuciya ta ina jin son in ga Amir na karshe dan na san zai yi wuya in kara ganin shi nan kusa. Hakan shine makasudin da yasa na nufi wannan kwaltan saboda kusa ya ke da gidan su. Gida uku ke tsakanin su da gidan su Adama, inda shi kuma gidan su Adaman ana tsallaka kwaltan shine.

Kaman yanda zata nafi minti Bakwai ina jira amma shiru ba abun hawa. “Suhaima ina zuwa?” Daga baya naji maganan. Mamman ne kanin Umar Sanda, shima abokin su Al-lawan.

“Ajeyari” na amsa, da ke ba laifi yana da kirki muna dan dasawa dashi.

“Yaushe za ki dawo?”

“Zan dan kwana biyu gsky” zaro idanu yayi yana kallona kaman Wanda na fadawa abun tsoro. “Suhaima Dan Allah dan jira ni a nan kar ki tafi pls” ko kafin in bashi amsa ya sa gudu sosai ya tsallaka kwaltan. Ikon Allah na tsaya gani ganin gidan kakannin Amir ya nufa.

Hankali na na kan hanyan gidan kwatsam! Naji an daka min duka. Ko ban duba ba na san Adama ce saboda ita kadai ne mu ke irin wasan da ita. “Ke koh ba nace ki bar duka na ba wai?” Harara na tayi sannan tace “ai ban hana ki ramawa ba ko? Ina zuwa?” Na bude baki zan amsa ta kawai naga Amir ya karaso inda mu ke da gudu yana ajiyan zuciya mamman na bayan shi. “Lafiya wannan gudun haka?” Adama ce ta fada tana bin su da kallo.

Nuna ni da hannu Amir ya fara yi yana fadin “ba ita bace za tafi ba ta min sallama ba” dauke idon ta daga kai na tayi tace “Suhaima ina za ki? Miye hadinki da shi?”

“Ajeyari, Goggo ke nema na” nan ta ke ta ba ta  rai “Dan rashin mutunci ki ta ko har titin kofan gidan mu ki wuce ba ki min sallama ba ko? Ni na taso da kokari na zan zo wurin ki, kin kyauta” saurin Fushi irin na Adama yana daure min kai. banga abun fushi a wannan  ba, sai dai tun kafin in yi magana ta tsallaka ta kama gaban ta. “Au ashe bani kadai kike shirin yi wa laifin ba Suhaima, kawar ki ce?” Gyade wa Amir kai kawai nayi.

“To muje ki bata hakuri” girgiza kai nayi “share ta ko naje yanzu ba za ta kula ni ba, in dai Adama ce da kanta za ta sauko ta neme ni”

“Shknn tunda kin ce hakan, ina da magana da ke muje in raka ki sai ki hau motan ta gwange. We need to talk and zanyi picking waya ta a gida”

Banyi musu duk da nasan nisan inda ya ke maganan. Ba wani nisa bane dashi tunda ana zuwa da kafa sai dai ni ban yadda in bi ta wurin saboda zagaye ne. Tun kafin mu karasa wurin gidan su ya kira da karamin wayan shi aka kawo mishi wayan mu ka wuce. “Kin kyauta fa Suhaima, you are planning on leaving babu sallama ko bayan kuma kinsan gobe zan bar garin nan.

” Ni ban san zan je fa, Goggo ta aiko inje. Kuma da na fito ban ganka ba”

“Gskyn ki kuma you have no other way to reach me, I think you need a phone”

“Nayi karama da rike waya fa” dariya ya min sosai sannan yace “wa ya fada miki, kina nufin yanzun in na tafi shknn ba zamu dinga gaisawa ba kenan?”

“Al-lawan na da waya in ka kira shi zamu gaisa ai”

“But, shknn dai” bai kara taso da maganan ba har mu ka isa bakin titin. I wasn’t feeling comfortable for what am doing at that because am so young for that. Sai dai is not like i have anybody to tell me what is good or wrong. Ni dai a lokacin duk Wanda ya ke min faran faran ganin shi na ke a matsayin Wanda bai dauke ni wulakantaciya kaman yanda ake min a gidan mu. Lbr ya dinga bane, mostly duk na school in su ne ko kuma na Kaduna da friends in shi har mu ka isa bakin kwaltan.

“Ko in raka ki ne inje in gaida Goggo?”

“Aa nagode” nayi saurin fada.

Dariya yayi yace “matsoraciya kawai” wani dan karamin zoben azurfa ya Ciro mai matukar kyau a karamin yatsan hannun shi. Bai ce kala ba ya ja hannu na ya saka min a yatsa. “Don’t you ever remove this, it a gift for our friendship” ba zan ce ga abinda na ke ji a lokaci, illa abinda ake kira “Infatuation” dayawa yan mate inmu a school su kan bada lbrn samarin su. Musamman Ajiddah da na fi kusa da ita, tana da saurayi daya da ta ke mugun so, ba a Sani ba a gidan su aboye su ke haduwa. A cewarta sun yi alkawari, so gani na ke kaman wannan ma normal ne kawai ni saboda ban taba bane. Sai dai ni Amir bai ce yana so na ba.

“Ni me za ki bani?” Da sauri na duba hannu na, bakomai sai zoben da ya sa min, haka kayana ba abinda zan iya bashi. “Shknn na biki bashi in na kara zuwa zan amsa” A haka muka rabu na nufi gidan Goggo shi kuma ya koma.

Muna kebewa da Ajiddah na ba ta labari. Dariya tayi da alamun abun ya mata dadi sosai tace “ban lbr ya yake?”

“Fari ne dogo”

“Yana da kyau”

Shiru nayi ina tunani can nace mata “yafi Yaya baba” tunowa da nayi ran da taga Ya baba tana koda min kyaun shi “Suhaima ashe haka Yayan ki ke da kyau? Suhaima Yaya baba kaza, suhaima kaza” sai da na gaji na share ta sannan ta bari. Yanzun ma bude baki tayi “keh! Kawata sai kace a film in indiya?” Ina mamakin yanda Ajiddah ke son mutane kyawawa duk da yanda ta ke matukar kyau. Hakan Anty nainah ta dinga “kinsan wannan Anty ta Ku kyakyawa ce kuwa Suhaima? Allah ta fi Halima kanwar ta kyau.” Nan dai ta Sani a gaba sai da na ba ta labarin Amir da yanda mu ka hadu dashi. Na fada mata ba sona ya ke ba saboda bai fada min ba. Sam ta ki yarda a cewan ta zai fada ne ma.

Sosai Ajiddah ta dinga encouraging ina kan Amir, har sai da naji ya kwanta min sosai a rai. Daman an ce Wai duk abinda ka sa a ranka…

“Ya baki numban shi?”

“Aa amma ya ce zamu gaisa ta wayan Al-lawan”

“Kinga ni daga nan ba sai ki dau numban ba, ko a makaranta sai Ku dinga gaisawa” nan ta ke nayi na’am da shawaran Ajiddah, ban kuma kara neman Kowa da maganan ba. A ganina duk Wanda zai ban shawara ba kaman Ajiddah don ita ce kama na kuma itan ta riga ni fara fuskantan abinda na ke fuskan ta yanzun.

Wannan karon Yaya baba da kanshi ya maida ni makaranta. Ba laifi tunda su ka fara shiri da Anty Nainah ya ke dan kyautata min. Wannan karon ma da alamun Anty Nainah ya ke son gani. Kayana na dauka nayi cikin school, ko da na dawo ba iske su tsaye da Anty Nainan Suna magana. Tana ganin ta saki fara’a, banyi mamaki haka kuma ban hade rai ba sai dai still ban mata dariya ba.Rayuwata

Babi na bakwai

Wannan karon Yaya baba da kanshi ya maida ni makaranta. Ba laifi tunda su ka fara shiri da Anty Nainah ya ke dan kyautata min. Wannan karon ma da alamun Anty Nainah ya ke son gani. Kayana na dauka nayi cikin school, ko da na dawo ba iske su tsaye da Anty Nainan Suna magana. Tana ganin ta saki fara’a, banyi mamaki haka kuma ban hade rai ba sai dai still ban mata dariya ba.+

“Maraba da kanwata” dole nayi murmushin yake na gaishe ta, faran faran ta amsa. Nace “Halima Fa?”

“Ta shiga ciki” ta amsa. Sallama nayi wa Ya baba hade da godiya na dau sauran kayana. Bai wani mai da attention in shi kai na ba saboda daman ba wai danni yazo school in ba.

Banyi nisa ba, Anty Nainan ta biyo baya na. Amsan abun hannu na tayi tace “bara na taya ki ko, ya Hutu?”

“Alhmdlh” na amsa mata, muka cigaba da tfy tana ta min labarin hutun da akayin. “Kinji ni da yayanki” ta fada tana fadada murmushin ta.

“Hala yace yana sonki ne?” Siririn dariya tayi tace “kema kinsan ai dole ne, Adams akwai aljanun mata amma kinsan ce min yayi wai yaji hakan ne saboda kulan mishi da nake yi da kanwar shi, kiji wani zance fa” Ni nauyin zancen ma yasa ni dole sai da na dan dara. “Shi Yaya baba abin nashi khna har da karya ne?”

“Gashi nan ko kingani, kar ki wani damu ina jin duk abinda kike fuskanta zai iya zama tarihi kanwata.” Murmushi nayi na nata godiya kawai. Dan ko na riga na cire ma raina akwai wani rana da wahalan da nake fuskanta a rayuwa zai samu aya

Da alamun huduban da Ajiddah ta ke min akan Amir ya shige ni sosai domin da numban shi a kaina na dawo makaranta. Ranar da yamma ana tashi prep ta jani wai in rakata staff room wurin Daddyn ta. Ba musu na bita saboda nima ina son yawan. Malam Aminu Geography shi ne sunan da ake kira shi. Irin malaman nan ne da duk da suna da budurwa. Ga dukkan alamun a set inmu Ajiddah ya hango, shine ya fakewa da School Daddy. Exam officer ne kuma shi kadai ne a office in shi.

“Ah maraba ku shigo mana” da murmushin shi ya amsa Sallaman Yana mana iso.

“Harda su Suhaima ne” kara fadada murmushin shi yayi. Ban ma san ya san sunana ba sai ranar. Gaishe nayi ya amsa sannan ya juya wurin Ajiddah “mutuniyar ya dai?”

“Waya nazo yi” ta amsa kai tsaye

“Wa za ki kira?”

“Yaya na” hade rai yayi yace “ni dai ban yarda da wannan yayan naki ba jiddah, ko dai abokin takara aka min?”

“Kai Daddy abokin takara kuma?” Dariya yayi ya Ciro wayan ya mika mata. Gabaya fita officer in yayi ya bar mu.

Kasa hakuri nayi na tmby ta “ke Anya Malam Aminu ba sonki yake ba?” Dariya tayi “share shi kinji, zai ma gaji ya kyaleni ne. Don wlh saurayi na ma zan kira yanzu” ina kallon ta tana wayan, na kan yi mamakin yanda Ajiddah ke iya hira da saurayi sosai, musamman da irin Malam Aminu. Ko da yake tana da yayyi mata da yawa, ba mamakin duk daga wurin su  ta ke samun courage in. Ire iren su Malam Aminu na nan da yawa a makarantu, musamman Wanda ya ke da yan mata zalla. Sai dai da principal ko vice inta zasu zan da abinda ke faru to fa tabbas da zasu dau babban matakai, amma da ke benefitting in daga malaman har daliban najin dadi ya sa Kowa ya rike bakin shi. Saukin ta da wuya kaji case in lalata, iya soyayyan kam za a sha ta.

“Suhaima ki kira Ameer wlh zai ji dadi” abinda Ajiddah ta fada kenan bayan ta gama wayan ta. Sake baki nayi ina kallon ta sai dai kafinma nace komai ta fara magana “Haba kawata kaman dai baki san abinda duniya ke ciki ba? Yanxu fa ba a wannan yanga yangan come on ki kira shi” haka ta cigaba da bani baki ta na nuna min fa’idan yin hakan. Wanda ko kadan ban dauke shi a komai ba sai ma ta na bani shawaran da ya dace ne, alhalin itan ma ba wai sani tayi ba kawao abinda taga anayi ita ma ta dauka. Na kira Ameer, ina fada mishi nine ya buga kara hade da danyin tsalle. “I can’t believe you call beauty” yanda ya nuna matukar farin cikin shi ya sa ni kara jin cewa tabbas shawarn Ajiddah shine dai dai. Ai kuwa tun daga lokacin mu ka fara waya da Ameer. Dan wani lokacin shi da kanshi ya ke nema na ta hanyan Malam Aminu, Daddyn Ajiddah wanda na sa wa kaina tabbacin zuwa lokacin soyayya su ke. Abun mamakin kuwa har daukan mu yake muje gidan shi wurin matar shi da ke staff quaters in makarantan, matan na da kirki kuma tana son mu sai dai nasan dan ba ta gane abinda ke faruwa bane.

Abun ya kai ya kawo har waya mu ka siya muka boye muna waya a boyen, duk dai shawaran Ajiddah ne ta gaya min cewa daman dayawa sunayia boyen. A hankali sabo ke shiga tsakanin mu da Ameer, duk da shima makarantan yake. Kaman mu shima a biye yake wayan. Yana da kirki sosai, ga natsuwa sai dai shima abinda na fuskanta wanda sai a yanzu nagane hakan, influence abokai ne kawai yasa shi afkawa cikin soyayya dani ba wai dan yasan abunda ya ke yi Exactly ba. Har Abty Nainerh sai da ta fara gane na daina zuwa wurinta sosai muna zama muna hiran saboda lokacin hiran ne mu ke waya da Ameer. A duk sanda na gama waya dashi kywa wani irin annushuwa na ke ji yana jaiwa can kololuwar zuciyata yana samun wurin zama na musamman. Cikin lokaci kankani na dawo banda tunani sai na Ameer. Ko littatafai na aka duba duk sunan shi ne duk na bi na zana a farko da karshen bangon ko kuma tsakiyan littafina. A lokacin ba wani dan adam da ya kai shi mahimmanci a rayuwata haka nake ji, duk wani motsi na kuwa yana nan a dankare a cikin zuciyana. Na so shi da dukkan  iyawata duk dama ban wani san me hakan ya ke nufi a lokacin. A lokacin kuma maida hankalina akan karatu ya fara ja baya, saboda ko a ajin in ba rubuce rubuce na ke akan sa to tabbas ina tunanin kalaman da ya fada min a waya ne daga haka kuma sai inji kawai na kosa lokacin da muke wayan yayi ko zan kara sauraran daddan kalaman Ameer dina wanda na ke rasa a ina ma yake samo dsu. Don haka karatun nawa duk dai ya fara xama shirirta kawai.

Akwai ranar da mu ke waya dashi yake ce min “Beauty tell me something nice and sweet” na dan dau mintuna ina tunanin me dance mishi nasan dai I’ve to come up with something tunda har yayi demanding hakan da kanshi.

“Kaman me kenan?” Na tmby cike da tunanin me zan fada mishi “Anything my beauty, ki fada min abinda ke cikin ranki about Ameer”

“Abinda ke cikin raina?” Tmbyn da nayi wa kaina kenan bayan some seconds na fara karanto mishi abinda ya bukatan.

“Har abada na, zan so ya kasance tare da kai. cikin rayuwan da nake fatan mu gina, wacce ba ta da karshe ba kuma da nasani.

Har abada na, zan so ya kasance cikin sauraron daddan sautin muryan ka, mai dauke da tsaftattun kalamai masu narkar da gangar jiki izuwa zuci.

Har abada na, zan so ya kasance karkashin iko da kulawar ka, a cikin inuwa daya, mu rayu cikin aminci komin rintsi da dukkan sauki.

Har abada tare da kai, shi ne kawai bukatar da ke cikin zuci.” Ni kaina ban san daga ina kalaman su ka fado min ba sai dai kawai na san abinda ke cikin zuciya na kawai na furta mishi. Bayan wasu yan dakikai ya fara yabo na “Wow! This sounds like a Hausa poem ke mika rubutu? Nan na fada mishi yanzu ma naji kalaman kawai na fitowa daga baki na. Ya yaba min sosai daga nan muka cigaba da wayan mu. Sai bayan na gama sannan na fara tuno duk abinda na fada mishi nayi rubuta a littafin. Since from them na fara rubuta poems amma ta Hausa. Nayi hakan ne kuwa saboda tun can daman na fi iya Hausan akan English ma ko a school. Faman Fulatanci ne ya so tafi Hausan to tunda Ummi ta tafi shikenan sai kuma mun hadu da Goggo.

Na fa rage shiri da Anty Nainerh don yanzu sai muyi ma kwana biyu masu kyau bamu hadu ba tunda tana fushi har ta fara kyale ni. Kwatsam! Ba sai labari ya fara zagaya wa cikin makaranta ba, Wai soyayya ke tsakani na da ita kawai dai muna boyewa ne. Da na fara jin abun Sai da naji kaina yayi wani irin sarawa, ban taba tunanin labarin da na ke ji yana yawo akan wasu zai dawo kaina ba. Kukan takaici ne ya turnike ni a wannan lokacin, Allah ya san na tsani sharrin da banji ba ban kuma gani ba. Ranar nayi kuka sosai dan ko Ameer ba muyi magana dashi ba. Ko da na samu Ajiddah da zancen Sai da ta gama dariya har da nuna ni tana rike cikin sannan tace “Ke dai wlh Suhaima ba ki rabuwa da abun ban dariya. To Sai me in ma hakan ne? Kanki farau? In fact School life ne kawai da anyi an wuce wurin fa shikenan. Wa ya fada miki Wai nima banda School lovers ne?” Kaina a daure na ke kallon ta, ni dai iya sani na duk aka kama irin wannan case in ma cikin school kora ke biyo baya ga dukkan dalibin da aka tarke. Amma Sai gashi Ajiddah ta na fadawa hankalin ta a kwance. “Ki saki jiki Dallah, school life Infa kenan. To Allah na tuba in angama za ma ki kara ganin wata ne? Wani abun ana yin shi for security reason ne, kinga fa ba ruwan ki da aike, zuwa labour, Layin bin ruwa da sauran su.” For the first time dukkan abinda ta fada min bai wani samu wurin zama a kwakwalwata ba, it doesn’t make sense at all. Saboda haka Sai na fara gudun duk wani hanyan da zai hada ni da Anty Nainerh ballantana a ganmu tare har a kara tunanin akawai wani abu a tsakanin mu. Yanda na ke jin dadin makarantan kuwa, yana kwashe min damuwa ta na zan so kora ta zamo sakamakon tonon asiri na ba. Dan zuwa da nake yi ma gabadaya Sai na dauke kafa, ko ta aika in zo ban zuwa gabadaya. Halima kuwa haushi na ma ta fara ji don haka Sai na watsar da kashin su duka biyun.

Sai dai Anty Nainerh ashe kallona kawai take, ta kyale nine in gama abinda nake yi. Ranar kawai ina zaune hostel inmu muna dan abibda ba a rasa ba sai gata sun shigo hostel in ita da Halimatu. Ban ma sani sai da naga kallo ya fara dawowa kaina, ba laifi tunda aka rage ganina tare da ita sai tsegumin ya fara raguwa yanzun ma da na gan ta fuskewa nayi na cigaba da abun gabana. “Suhaima” naji ta sunana, dole ya sa na daga kai na, fuskan ta a hade kaman bata taba min dariya ba ma a rayuwan ta. “Biyo ni” kawai tace ta fita daga hostel in. Masu kallona basu fasa ba, dan wasu har sun fara tsunde suna jiran ganin me zanyi. Ko bakomai ta min mutuncin da ba zan iya share ta a cikin mutane ba. A waje na same ta tsaye tana jira na, tana ganina kuwa ba ta ko min magana ba tayi gaba ni kuma na bita a baya.

Hostel insu mu kaje sai dai ba kwanan ta ba na kawarta ne ta kaini ba dai kowa a ciki. Zama tayi kan gado ni kuma na tsaya bakin kwanan ina jiran jin me zata ce. Tsaki ta ja tace “ban so kisa raina ya baci fa ni zaki tsayawa a kai?” A hasale tayi maganan, dole na shiga naza a kasa dake akwai ledan kasa a kwanan. “Na miki wani abu ne?” Shine abinda ya fara fitowa bakin ta, girgiza kai nayi sannan na cigaba da kallon kasa “ki daina min haka ki dago ki kalle ni” ban dai kalle tan ba amma na daga kan. “Meye sa in na ne miki ba kya zuwa? Infact kawai meye sa kike gudu na?” Rasa bakin magana nayi sai dai yabda ta tsare ni nasan dole Amsa ta ke bukata wanda ban san ta yabda zan fara bada shima. “Ba ki dauke ni matsayin yayarki ba ko?” Wannan karan da baki na amsa ta “Aa fa ba haka bane Allah…”

“To menene?” Tayi saurin taran numfashi na. She is not willingy to give up don haka doke na mata bayanin da zata gane a takaice. “Kawai dai maganganu na ta yawo ne a wurin mutane cewa wai akwai abu tsakanina dake ni kuma nasan mutunci ne kawai shiyasa” wani shu’umin murmushi tayi nan ta ke tace min taso ki zauna kan gadon. Ban mata musu ba na tashi na zauna ta juyo tana dan kallona. “To ke kuma me kike ce musu?” Dan zaro idanu nayi, dan ni tmbyn ma sai ya bani mamaki. “Ai ni ba wanda ya taba tunkarata sai dai inji ana wai wai, shiyasa ma ana rage zuwa wurin ki” shiru tayi na kusan minti daya sannan can tace “You don’t like me kenan?” Mamaki ne ya dan mamaye ni sai kuma na sake nace “I like you as a sister mana” a hankali ta girgiza kai tace “ba haka nake ni fa, as a friend like even more than friends ma. Kinsan me? Kije kawai kiyi tunanin miye relationship inmu da ke zan neme ki” tana fadin haka ta juya ta kwanta, ni kuwa jiki na har rawa yake na mike na bar hostel in.

Abun ya kidima ni don banyi tsammanin haka daga wurin ta ba har ga Allah sai dai har yanzun ma ban gama fahimtan ina ta dosa ba tukun. Kai tsaye Ajiddah na nema, mu ka dan kebe sannan na bayyana mata abinda ya gudana tsakanina da Anty Nainerh. Wannan karon ma dariyan ta kara min har sai da na kule na juya zan tafiyata tayi saurin riko ni amma still bata daina dariyan ba. Takaici ya sa hawaye fita daga cikin idanuna sai lokacin tayi shiru “Relax Dan Allah Suhaima, ni wlh banga abun damuwa kwata kwata a nan ba. I think na fada miki is not like wani abu na faruwa ne tsakani, though wasu nayi amma ke nasan naki ba haka bane, she just like you be kawai kuma na tabbatar ba abinda zai biyo bayan hakan. Da ta gama School in ta tafi fa shikenan” idona taf da kwalla nace “gsky ni ban so, kuma ban son ta ga kaman na nata da rashin mutunci tunda dai tana min kirki sosai”

“Kedai kina da ta taurin kai wlh, tun yaushe nake miki bayani amma gabadaya kin gaza fahimta” ban ce mata komai ba daga karshe dai dole a hakan mu ka rabu.

Bayan kwana biyu kuwa sai ga Anty Nainerh har ajin mu, waje ta kira ni ta mika min wani farin takarda sannan ta wucewan ta. Har ko a ka tashi class ban bude wannan paper in ba. Ina ta zulumin menene a ciki, daga karshe dai sai bayan prep sannan na bude, gashi nan ko baro baro rubutun tane. I don’t wanto to write the letter here amma dai sak irin wasika ne da namiji ke aikawa mace. In summary ta min bayanin abinda take ji game dani sannan kuma tana bukatan in zauna inyi tunanin miye ra’ayi na game da hakan. Ban dandara ba na kara daukan wasikan nan na kaiwa Ajiddah, ba don komao ba sai don  ina ganin banda wani wanda zai bani shawara bayan ita. To daman Ameer, kuma nasan ko meke damuna bazan iya tunkarar shi da zance irin wannan ba.

Tsaf ta karanta sannan ta ja hannu na, kaman sokuwa haka na bita. Corner inta muka je ta ciro papers sun kai biyar. Duk na amsa daya bayan daya na fara karanta wasikun, na mutabe har kala uku, domin dai mutumdaya ne ta tura mata har guda uku sauran da daya daya. Ashe abinda Anty Nainerh ta rubuto min nake ganin bai dace bakomai bane akan wannan “ina fada miki kina ganin kaman karya nake miki ko Suhaima? Ai yanzu dai kin gani ko? To bani kadai duk yawancin Yan class inmu sun amshi irin wannan wasikan, na gaya mimi ba wani abu a ciki wlh, mutunci ne kawai da taimakon juna shima da makarantar kwana ai ya gaji haka” Tabbas a dinga yawan maimaita maka abu ma bala’i ne, domin kuwa a lokacin na fara jin abun ya samu wurin zama a zuciya ta. Daga nan fa shikenan, ban dai amsawa Anty Nainerh amma ina jin action ina ya fahimtar da ita. Kaman dai yanda Ajiddah ta gaya min ne, ba wani abinda ke shiga tsakanin mu banda mutuncin mu dai irin nada,  sai dai shakuwan mu ya kara karfi, mun sha exchanging wasiku a tsakanin mu wanda ke kunshe da dimbin kalamai na so wanda ko har yau ban jin na taba aikawa wani namiji, har ko Ameer. Gifts kam kala kala ina sha a wurin ta, haka kuma ba irin labarin da bata bani. Suprisingly, ko da na bata labarin Ameer kishi kiri kiri ta nuna, ban ko yi tsammanin haja bane saboda tana bani labarin samarinta sosai. Haka kawai na kanji abinda ke tsakanina da Anty Nainerh yafi karfin description in da Ajiddah ta bashi, yanda ta ke kulani wlh duk samarin da take ikirarin tana dasu ba wanda ta ke ma kwatankwa cin hakan. Har kuwa Zayd, dake tabbatar min tasam shi zata aura saboda iyayen su kowa ya san tsakanin su.

1Kaduna, Nigeria.

Dr Fahad zauna a falon gidan sa yana karin kumallo, sai dai attention in shi yafi tafiya kan TV akan abincin da ke gaban shi. Labarai ne ake yi, abinda ya dau hankalin shi kuwa shine. Budurwar da hoton ta ke manne kan screen in ana sanar da rasuwan ta a ranar da Asuba. Fara sol da ita, kyakyawa ce sosai irin wacce kyan ta ya kai a fada har ma a kara. Sai dai ba wai kyan nata ya dau hankalin shi ba. Aa, sunan da ke makale a kasan hoton nata ne ya ja ra’ayin shi sosai. Amal Idriss Hayatuddeen, The Hayatudeens only daughter. Tabbas ita dai ce Friend in Suhaima da su ka zauna tare na tsawon lokutta. Matashiya yar shekara ashirin da uku, wacce tayi kokarin kashe kanta ta hanyan yin alluran kwayoyi, sai dai hakkan ta bai cimma ruwa ba a wannan lokacin, sai dai hakan yayin sanadiyyan doguwan jinyan da tayi a asibitin John hopkins da ke garin baltimore a kasan Amurka. Labarai dayawa sun kawo shaidar samun saukin ta don har ana shirin sallame ta daga asibiti. Kwatsam kuma yau sai aka wayi gari babu ita, to daman dai rai aron shi aka bamu don haka sai dai muce Allah yaji kanta.+

Dr Fahad bai santa amma sai da yaji wani irin bugawan gaba daya tsorata shi, tunanin daya fara zuwa mishi a rai shine yanda Suhaima za ta karbi wannan zancen. Tabbas, mutuwa ba ta dadi balle ma irin mutuwan da ta taba wanda ka shakuwa dashi, ba sai an gaya mishi wannan labarin zai girgiza ta ba. Bai kara maida hannun shi cikin abincin da ke gaban shi sai ma idanun shi da ya kara maida wa kan Telebijin in yana kallon abinda BBC hausa ke cigaba da nunowa. Attajiri Idriss Hayatuddeen ne tsaye, kusa dashi yaran shi maza biyu. Ba an fada cewa suna cikin tashin hankali ba saboda yanayin su kadai ya nuna hakan. Balle ma mahaifin da ya dauki son duniya ya daurawa yar tashi, gabadaya jikin shi rawa kawai yake yana ta faman girgiza kai yayin da likitocin asibitin ke kokarin fiddo gawan Amal in. Mahaifiyar ta kuwa labari yazo cewa ta fadi, yanzu haka likitoci ke kanta domin ganin sunyi nasaran ceto rayuwan ta. Hakan ya kara sa family i  shiga matsinaiciyar tashin hankali wanda kana gani kasan basu taba tsintar kansu a wannan masifan da ta afko musu ba. Kaman daga sama wani ya fado wurin da gawan ke kwance yana ta faman jijiga ta, ba ka iya jin abinda yake furtawa sai dai hawaye da ke ta faman tsiyaya daga idanuwan shi. Da farko Dr Fahad bai gane waye ba, sai bayan ya dago fuskan shi yana ma likitocin magana wanda da alama tsawo ya ke musu su maida ta, dan gashi yana nuna hanyan dakin da aka fiddo ta. Ba ko shakka, Zayd Al-mansur ne. Iya rudewa ya rude a wannan lokacin. Rufaida da ta shigo falon ta fahimci yanayin shi ke faman tmbyb shi “Lafiya” bai ma san tana yi ba saboda wani iri nauyi da yake ji a kanshi. Iya sanin shi Zayd bai da ishasshen lafiyan da har ma zai iya takawa. What is reallay happening? Jar dai framing in yarinya su ke don singa ba ta da wani gata. Rufaida da ta fara rudewan itama ganin yanayin mijin nata yace ma ta kawo mishi wayan shi, ita yasa tayi dialling in Barr Mustapha.

“Kaima kaga news in ko?” Tmbyn da Barr in ya fara mishi kenan.

“Nagani, what are you thoughts?”

“Wlh am confuse, amma koma dai menene da sannu zamu sani. Something is fishy, kunyi magana da Suhaima? Taji rasuwan kuwa?”

“Bara na kirata” Dr in ya amsa, sannan yayi dialling numban da suka samar ma Suhaiman. Ba ta dauka ba har ya ajiye wayan sannan tunanin kiran zeenah ya zo mishi. Daman dai ya amshi numban bata ne sabkda irin hakan. Bai ko tsaya sun gaisa ba ya nemi ta bawa Suhaiman. Da ke yan duniya ce na gaske sai da ta tsaya mishi duniyancin nasu. “ya haka Dr? Har na dauko sabon kamu nayi?” Ko dama suna irin wasa, presently dai he is not in for the jokes. Amma dake dan kwanakin nan yasan halin ta sai bai wani kula ba yace “let me speak to her please”

“Am afraid you can’t” saurin mikewa tsaye yayi “meyesa kika ce haka?”

“Ba ka kalli news bane?”

“Labarin yazo muku kenan?”

“She have been crying wlh, yanzu haka am afraid the worst is about to happen saboda har numfashin ta ya fara samun matsala ma, like i don’t think she can even talk” ji yayi kaman yayi tsuntuwa ya ganshi a Abuja yanzu,  but he knows he have to stay calm. “Zeenah sa mata wayan ko ba ta min maganan ba in dai zata jini ba matsala” yanda yace in tayi. Sai dai wani irin kukan cin rai da dishashiyar muryan Suhaima da ke sauka a kunne shi sai da ya sa jin kafafuwan shi na kokarin gaza daukan shi, domin ba kan shi kadai bane ya ke ji ya mishi nauyi a yanzun ji yake shi kanshi zai iya zubewa. She sound so hopeless and helpless, ga numfashin ta dake kokarin seizing. It takes minutes kafin yayi kokarin maida da hankalin shi. “Suhaima please ki daina kukan nan hakanan, anything can hapoen now. Shin ke ba musulma bace? Baki san kaddara bane” sama sama take sauraron shi sai dai kalman da ya furta na kaddara ya samu wurin ma’adani a kwakwalwanta. Duk da bala’in da take ciki, samun kanta da tmby tayi, shin tasan kaddara kuwa? Amsan ta kuwa shine tabbas bata san ta ba. Duk karatun da tayi tana karama a islamiyya ya tashi a tutan babu kenan. Domin kuwa da ta dau kaddara tun farko ba za ta biyewa rudin zuciyan ta ta fada rayuwan da take ganin ita ke da alhakin sa kanta da tayi a ciki. Da tasan kaddara da tun farko ba ta hadu da Umayamah balle har ta ci burin daukan mata fansa a rana kai tsaye ba. Da tasan kaddara da bata dauki nauyin sa ka masoya cikin kangi da wahaln duniya ba wanda ta ke da tabbacin ita tasa a dukkan wani masifa da mutane dayawa a yanzu ke fuskanta. Da ta san kaddara da ta dauki rashin mahaifiyar a matsayin kaddaran, ta rungumi wahalan ta cikin sauki da tana ganin ba shakka da yanzu abubuwa da dama sun zama tarihi. Amma yanzu ba ta ko kokonta, ita ta ke da alhakin mutuwan kawarta, Aminiyar ta Amal. Wacce ta dauki son duniya ta daura mata, yarinyar da ba ta san asalin ta bama balle inda ta taso. Zuciyan Amal na da kyau sosai, maybe wannan shine laifin ta. Ba da ban haka ba da ba ta samu daman da ta samu ba har ta aikata abinda ta aikata.1

Duk wa’azin da Dr Fahad ke mata bawani ji take ba, saboda tunanin da kanta ya tafi gabadaya. Sai a karshe taji yana fadin “Hakika ba a gyara barna da barna Suhaima, kukan ki da zuwa asibit ba zai aiwa ta miki komai ba. Ki fawwala ma Allah lamarin shi”

Da kyar da sufin goshi ta iya hada kalmomin da ta samu damab fada mai “Na kashe ta, am the one responsible na shiga uku na” rike kanta tayi saboda wani irin zugi da taji hade da runtse idanu tam tam. A lokacin ji take ina ita ma tabi Amal ko ta huta da wahalan rayuwan nan gabadaya. “Ehm ehm kar kice haka mana, kowa da irin yanda ajali zata zo mai  ina so ki sani ko baki san Amal ba a rubuce yake ta haka Allah zai dauki ranta. Ki mata addu’a, ki rokon mata gafara sannan kema ki nemi gafaran Ubangiji domin shi gafuru raheem ne. Ki tashi kije kar ki tsaya kuka don Allah ki min wannan alfarman” Ko bayan ya kashe wayan da kyar ya iya tashi domin aiwatar da abi da ya roke ta tayin. Tabbas duniya ta mata zafi, daci daduhun da ba ta ma ko makiyin ta faman ya fuskanta a rayuwa.

Dr Fahad kuwa bayan ya kashe wayan, sai a lokaci ya dan ji sa’ida sannan ya samu natsuwa yiwa mamaciyar addu’a. A labari kadai amma ya san Amal tana da kirki sosai, a bar maganan wani flawad inta amma samun yaran masu kudi kuma masu zuciya irin nata kalilan ne a duniya. Ganin Rufaida ta rude ma yanayin shi yasa ya dan mata summaru i  abin da ya farun da wanda ya gani, daman ita mutum ce mai tausayi, yana daga cikin dalilan da yasa akaji dadin kasancewar ta ma’aikaciyar jinya a asibiti. Sosai taji ba dadi, amma to ya za ayi? Dukkan mai rai mamaci ne.

Shi dai Dr Fahad gabadaya a ranar ya damuwa da halin da yasan Suhaiman ta shiga. Ba daman tafiya Abuja ne kawai a ranar amma da yaje shi. Yana tausayin yarinya, irin tausayin da bai san iyakan shi ba. Ko bama hakan shi kam tabbas yana jin Suhaiman a cikin ranshi, in har ko zata amince mai bayan karewan case insu to ba abinda zai hana ta zama mallakin shi. Matsala daya zuwa biyu ya ke hangowa, Rufaida sai kuma Ummin shi. Saboda yanzu haka ta fara damun shi akan ya maida hankali kan wani case in da bai shafe ahi, yana likita mihe hadin shi da wani shari’ah. Abinda ba ta sani ba yana jin har ranshi zai uya bafawa cikin case in nan. Shi kam har yanzu bai sare ba, ya yarda da Suhaima sosai sannan ya amince ko dabba itan ba mai iya kashewa bane balle dan Adam. Su bar ganin su masu kudi ne, Allah ya fisu domin a lokacin ya ke jin ya sa kaimin rokon Ubangiji ya fidda baiwa tasa. Bayan haka da dukkan karfin shi da kuma dukiyan shi yake shirin yakin da za ta kaisu ga nasara. Ranar wuni yayi da tunanin Suhaima da kuma case inta mai cike da cakwakiya. Yana son sanin labarin ta, asalin ta da komai nata. Hakan yasa shi dauko Manuscript in da Barr ta bashi copy, ba don komai sai dan yasan shi in ma zai taimaka mishi wurin shari’an. Don haka sai ya cigaba da karantawa daga inda ya tsaya.

Rayuwata

Babi na takwas

Third term inmu JSS2 yayi dai dai da term in karshen yan SS3 a makarantan. Set insu Anty Nainerh kenan. Har yanzu dai muna nan a yabda muke, a kullum duniya abun namu kara gaba yake. Ban zanyi karyan cewa ban taba jin abu game da ita ba domin kuwa najin. Sai ya zamo zuciyana na battling ne tsakanin abu biyu, ta kasa tantace wuri daya. Sai dai dake nasan abinda ke tsakanin mu da Anty Nainerhn ba inda zai kai mu kaman yanda Ajiddah ta sha fada min. Sai hankali na yafi karkata wurin Ameer sosai. Duk ko abinda zata fada kan hakan ba abinda na ke dauka. Akwai ma lokacin da na gaya mata ta kyale ni ni, saboda tana gama school ita ma tasan komai ya kare. A lokacin tayi shiru tana kallona, can kuma tayi shiru tace min “Suhaima daman haka kika dauki relationship inmu kenan?” Jikin ta duk yayi wani sanyi, ni ko zuciya na sai dukan uku uku yake. Tace “Amma baki min adalci ba,  dan ko ni dai ba haka na dauke ki ba wlh” har na fara feeling emotional kaman ita din sai kuma na fuske nace mata “To ai kowa ma haka suke, karshe abin end in friendship ne kuma kowa yasan da hakan”

“Eh ehm ai mu ba kowa bane, I like you kuma kinsan da hakan. Ke daina min irin hakan” kaina kuncewa yayi, daman dai na dade insma susoecting hakan daga gare ta amma yanxu daya faru sai nake jin duk wani sakayau. “To amma me kike nufi? Ina clearly kin fada min kina da saurayin da har an sanku da shi a gida”

Dan shiru tayi a lokacin yanayin fuskanta gabadaya ya canja. “Bara na baki wani guntun labari. Mum in zayd cousin sister in mama nane, though ta girme ta amma tare su ka taso. Baban shi ma abokin baba ne. Iyaye na na da kudi sosai kaman yabda ake dauka cikin garin nansai dai ko kamo kafan iyayen zayd basu yi ba. Suna da irin mugun kudin nan da su kanshi ba za suce gashi ba. Tun muna kanana mu ke zuwa Abuja hutu ni da yan uwa na. Su kam da wuya suzo, ko da sun zo inma kwana biyu ne sun koma amma mu sai dai in ba ayi hutu ba, kinsan masu kudi ba wai sun rike zumunci bane. So zumunci dai a takaice mu keyi, duk cikin yan gidan mu kuma nafi kowa zuwa saboda kannen zayd mata biyu sa’anina nane, daya kanwar shi ce dayan kuma cousin in shi ce sannan akwai wata friend sistern tashi da duk muka je hutu tare a wani lokaci. Dake kanmu daya sai ya zamo muna abubuwa a tare, muyi wasanmu, hira da abubuwa dai da dama. Lokacin ina JSS1 a NTIC mamudo. Siyama, sunan kanwar zayd in kawarta Raudah sai cousin in nasu Zakiyyah. To tun farkon zuwan mu na lura Raudah da Siyama suna dan kebewa wani lokaci in muna wasa sai su ware kansu gafe guda suna magana da ba musan menene ba ko kuma su kwanta su rufe kansu a bargo suna kus kus wanda duk bamu san na menene ba. Don har mun fara jin haushi, Zakiyyah da ta fini zuciya cewa ma tayi za ta tafi gidan su, tunda siyaman ta fi son kawarta akan mu yan uwan ta. Din har ta tafi zata gayawa mum a kura mamarta ita kam tazo ta dauke ta sai Raudah ta jawo ta tana bata hakuri. Nan Zakiyyah ta botsare tana fadin in dai hakane to su fada mana abinda su ke boye mana, nima ko na taya ta nan dai su ka amince zasu nuna manan amma kar mu fadawa kowa. Ba tare da wani tunanin ba muka amince, everybody want to feel belong kawai. At first a tab Raudan ta fara mana browsing pictures tana nuna mana, i was so innocent da ban taba sanin abun ba. Pictures ne kala kala na maza da mata in an intimate ways. Ni na fara tmbyn menene hakan saboda i never know anything like that. Nan fa Raudah ta fara mana bayani ni da zakiyyah akan duk wani abubuwan da ta sani, she show us everything da ke gudana a tsakani mace da namiji harda kari da cewa mace da mace suna ji wa junan su dadin ta hanyan amfani da yatsa ko wani abu dai haka. Zakiyyah ce ta tmbyn ta “amma ina kika san wannan abun?” Neighbor inmu ne ya nuna min, shine amasan da ta bamu. Mostly iyayen ta ba sa gidan so after school yana zuwa zama da ita as she is the only girl. Ba abina bai koya mata ba, dan har oractical abubuwa ya gudana a tsakanin su. “I like having him over, he gives me the best pleasure i can ever have”

“He have sex with you?” Zakiyyah ce dai ta kara tmbyn,  Raydah ta girgiza kai tace “yace sai ba kara girma, but yana sa min ya yatsa, thats call fingering haka kuma yana sucking ina ko kuma yayi kissing ina mouth to mouth” ba tare da wani damuwa ko sanin illan hakan ta ke furta musu abun ba,  Aa hankalin ta kwance la iyaka abun dadi ma yake mata. Ni da zakiyyah dai zaro idanu muja yi muna kallon ta yayin da take cigaba da mana bayani. “Yana nuna min videos dayawa har na mata biyu, lesbians kenan shine nayi deciding muyi trying da Siyama, kuma ai we like it ko Siyama?” Ita ma siyaman yanda ta amsa kadai zai tabbatar maka da she like what is going on. Sai da su ka nuna mana videos in sannan su ka mana practical muka gani ni da zakiyyah kafin suka ce muyi trying a gani. And guess what? We immediately like it dukkan mu da har it gets to a point da bamu da aikin yi sai wasa da junan nu ta hanyoyi da dama. Da ke dakin yara musamman daban yake a gidan sai ya zamo ba wanda yasan abinda ke gudana tsakanin mu har aka yi hutu. To fa bayan an koma school ne,  da ke abin ya riga ya gama shiga kwakwalwar kaina, sai na dinga yawan kallon yan uwana mata more especially insu zo cire kaya or stuffs like that  minsan mu mata yabda mu ke free a gaban junan mu,  a haka wata senior ta ta fahimci halin da nake ciki, ashe ita ma yar layin ce sai mu ka kulle, a hankali a hankali kuma muna kara samun partners. Tsakanin mu da su Zakiyyah duk zuwa na Abuja yana kasancewa su ma su je hutu, sai a ciga a daga inda aka tsaye, we all become addicted sosai da in ba muyi bama ba ma jin dadi. Kuma kin san duk wannan abubuwan ba wanda ya tabaura da wani abu a gidan, na fi alakanta hakan da rashin kula irin na iyayen su, don wlh nasan da maman muce wannan abun ke faruwa a gidan ta da tuni ta ankara sai dai kash, she is too busy for our time. Karewa side inta sai an wuce na yaran gidan, wadanda suke siyaman ke side su inma yawancin ba sa gidan, ko suna nan ma banda shaye shaye ba abinda suka sa a gaba, kuma wai duk abun nan mum fa bata sani ba. Sai ni kuma tsakani na da zayd, tun ina karama yake cewa yana sona, mamanmu kuna tace ta bashi. To ni tun daga nan abun ya samu wurin zama a kaina, domin ina son zayd, da duk wani da namiji sai dai in kalle shi domin banda wani buti mai kyau a kanshi. Duk kowa wannan abun dake faruwa tsakanin mu da kanen shi bai gidan, haka kuma ba a tashi farga ba sai lokacin da zan shiga jss3.Rayuwata

Babi na tara

Shi inma bakuwa su kayi daga side in baban su. Bata shiri da yaran gidan,  dake kuma tayi aure jar da babyn ta kawai sai ta sauka a nan dakin yaran. Ranar we were so sad haka kuma so addicted da ba za mu iya hakura ba. Da ke kuma gado daya duk mutum biyu ne akai sai muka lallaba har sai da tayi bacci sannan muka afka duniyan da muka fi wayau. Hankalin mu duk gabadaya ya tafi a abinda muke yi da har bamu san inda kanmu yakr. Ita kuma ashe babyn ta har ta fara kuka hakan ya sa ta farka, ta gama bata nono kenan ta lura kaman ana mutsu ta cikin bargo, ba abinda tunanin ta bai kawo mata jin abun ya fara yawa. Da saurin ta ta mike ta yaye bargon da Siyamah da Zakiyyah su ka lullube kansu, yanayin yanda ta gansu ya sa ta runtse idon dole. Ba tayi wata wata ba ta dawo kanmu, duk abun nan bamu san meke faruwa ba ni da Raudah har ta yaye namu bargon. Salati ta sake, mu kuwa duk idanun mu sunyi rudu rudu, kallon mu kawai take tana dalati, sai dai daga yanayin ta zaka gane taji zafin abinda ta ganin a yanzu. Mu ko sai xare ido. Ranar dai ba ta kwana a dakin ba, mu kuwa ta kulle mu daga ciki, ta fita idanun duk hawaye tana fadin “Duniya ina zaki damu?” Dan bala’in bayan fitan ta Raudah da duk abun ya fi shigan ta akan mu kamo ni ta fara kokakarin yi tana son mu cigaba. Da ke nima na zama ruwa hakanna kuwa na biye mata, Zakiyyah da Siyama kam tsoro ya hana su tabuka komai.+

Sai bayan sallan asuba ta samu a gaba cikin natsuwa duk da kwallan dake idanuwan ta a tsanake ta mana bayanin illan abinda mu ke,  wa’azi ta mana sosai mai ratsa jiki ba tare da ta tmby mu waya koya ma wani ba. Dake daman hanya ce ya tsaida ita, gari na wayewa tasu mum ta fada mata duk abinda ta gabi domin a sa mana ido sannan ta bar gidan. Mum kuka shabe shabe tazo ta same mu da sauran yan matan gidan. Su kam ba wa’azi su ka mana ba sai ma fada, kai har dama mai dunguri ba dai wanda ya buge mu. Ita kam mum kasa magana tayi, sai can ta fara fadin “ita kam ba zata iya, mun zo ni da zakiiyah zamu bata musu yara don tasan a garin Abuja kam ba inda yaran su zasu samo wannan irin mugun abu. Don haka yanzu zata kira iyayen mu suzo su kwashe mu” wlh matan nan kaman ba mu hada jini da ita ba, ta rufe ido tana ta zazzaga mana bala’i nida zakiyyah. Ba wanda taba ma chance in magana sai ma cewa tayi yaran su na Abuja are so naive da ba yanda za suyi su san irin wannan abun,  sai dai in an wuri dole zasu koya. Ni dai kawai ahinda na fahimta daga baya shine, iyayen Raudah suna da irin mahaukacin kudin da ba zata iya wulakan ta tasu yar ba, saboda kudi shine mutuncin ka. Bayan nan kuma son nata aya muvub rufe mata ido, in akwai abinda ke rusa zumunci a zamanin yanzu kuwa shine son yara da iyayenmu su ka dauka su ka daura ma kansu, komai kawai naka yayi shine dai dai. Matan nan haka ta kira namu iyayen ni da zakiyya tana sanar musu kowa yazo ya dau yar shi. Zakiyyah kano take daman ita. Mahaifiyar ta naji ta sa wani dan uwanta yayi maza ya dauko mata yar ta, dake daman baaban zakiyyan ne dan uwan baban su siyaman. Ni kuwa a ranar dai ba wanda yazo dauka na, illa iya ka naji Mum in ta kira mamana tana ta zazzaga mata masifa kan bata ji abinda ta gaya mata ba ko, ina jin sheshekan kukan maman tana fadin “Wai yaya ya kike so inyi? Na gaya miki ba mota a gida yanzu baban su yayi tafiya gobe zai dawo, jibi ba sai nasa a zo a dauke ta ba? Sai kace Aminan ba yarki bace da ba zaki hukunta ta ba”

Da sauri mum tace “Aa ki barni inji da nawa case in please, gobe zan sa driver ya kawo ta kawai” Hmm, a ranar Kuma ya zayd ya dawo, daya ji abinda ya faru har daki yazo ya same ni inda nake zaune ni kadai domin tuni mum ta kwashe siyama da Raudah zuwa side inta. Idanuwa na sunyi rudu rudu, ina ganin shi na taso da gudu na na rungume shi kaman yanda na saba, shi inma rike ni yayi yana lallashi na jin irin kukan da na fashe dashi. “Yi hakuri kinji kyakywata” share min hawaye yayi sannan ya lallashe ni sosai. Ya zayd na so sosai tun ina karama, wanda na fahimci ba komai yafi ma rudan shi game dani ba kaman kyawun da Allah ya min, ya sha fada min ina da kyaun da bako wacce mace Allah ya ba ma wa. “Don’t ever do that kinji my pretty babe? Inma wani abin ne ya dame ki kizo ni zan yaye miki shi” tsaf abinda ya fito bakin shi kenan. Ranar shi ya sani naci abinci, ya dai tarairaye ni sosai, ranar hakanan ni kadai na kwana a dakin sam mum ta tattara su Siyama ta ma hana ni hada hanya dasu. Duk girman dakin nan hajanan na kwana ji kadai a ciki. haka washegari tunda Asuba muka kama hanyar Yobe, ya raka ni kuwa har Damaturun sai da ma ya kwana washegari ya tafi. Irin dukan da maman ta min ban fatan in kara jin shi a rayuwata, ta min itin dukan da sai da naji duk wani iskanci da ya shige ni ya kau. Don ji nayi a lokacin gabadaya na tsani abinda nake yi in. Haka ko da aka koma makaranta nayi kokarin nisan ta kaina da abun, amma si sebiors in da suke partnera ina suka yi ta threatening ina. I could’nt even expose it. Trap kala kala daga karshe dole na fadawa sharrin su na koma ruwa. Ba a tashi kama mu ba kuwa sai second term ina Jss3. Makarantan tilas su ka dauki mummunan mataki akanmu daga karshe kuma duka yan group inmu aka basu takardan kora ma gabadaya. Wannan shine dalilin zuwa na GG. Wanda shima da kyar mama ta lallabi Baba ya yarda ya sani a school in, domin cewa yayi tunda dai abinda na zaban wa kaina kenan to na gama makaranta har Abada.

All these through muna tare da Zayd a waya, kullum cikin chatting gashi yana yawan sani ina tura mishi hotuna. It become more clearer zayd is after the beauty, as in my physical beauty gabadaya ba wai fuska na kawai ba. At times irin maganganun da yaje nin yasa na gane hakan, my pretty irin wannan boobs haka, kinga yanda hips inki ke karuwa kuwa? Kullum irin zancen shi kenan. Ni dai a zuciyata ina son zayd sosai. Ko bayan hakan ma ina da adding advantage a tare dashi, wato fame, i need that thing sosai domin in har na kasance matar shi to nasan ba irin sunan da ba zanyi ba. Na kuma san zayd na mu’amala da mata ta hanyoyi da dama, dan ko a gidan su ina ganin yan shigowa dasu though yana min claiming friends in shi ne. Wannan kadai ya isa yasa in rabu dashi sai dai nasan shi kadai ne zan iya aura ba tare da na samu wani matsala ba, zaboda ba zan boyr miki ba Suhaima, har yau ban jin wani abu gane da da namiji in ba mace ba to fa ba abinda nake ji wlh. Da na zauna nayi nazari sai na gane kaddara ta ce haka,  beaides in ina karanta wasu littatafai sai na fahimci cewa hakan ba wani laifi bane. Shiyasa nake son auren zayd saboda nasan ba zai hana ji rawan gaban hantsi ba sannan kuwa ina son nuna ma mum iyakan ta.

Ban karawa komawa gidan sai bayan na gama SS1 a nan school in. Shi inma tare mukaje da Halima da kuma Baba lokacin zamu je trip a Dubai. Mama taso hana mu zuwa gidan, sai dai ba yanda ta iya. A lokacin kuwa zayd na gidan, yaji dadin gajina yayi ta nanike min, in dai takaice miki a ranar yaja ni dakin shi dazuman nuna min wani abu. yana dai ta kallona kaman zai hadiye ni, ko kafin na ankara sai jin shi nayi ya rungumo ji jikin shi baki daya yana faman sumbatata duk inda bakin shi ya sauka. Daga nan ya koma yana kissing ina, tun ina botsarewa har na hakura na kyale. “I’ve been thinking of doing this, all my life” shine ahinda bakin shi ke ta faman furtawa “my pretty you are so sweet” a haka kawai muka ji an bude kofa, Abban shi ne kuma four eyes dukkanmu mu kayi dashi. Daha wannan ranar ban kara taka garin Abuja ba, amma kuma Abban yayi alkwarin komai zai faru sai na auri zayd. Shima zayd bai wani budging ba, don har yanzu yana zuwa wurina har nan garin kuma muna waya. Infact duk nacin mum nakin abun, ya riga ya sanar mata ni zai aura.”

Ni dai kallon ta kawai nake har ta gama bani labarin, da farko rashin sanin me zan ce mta ma nayi sai can nace “atleast koma dai miye, you are getting married to him so what do you want from me?” Murmushi tayi sannan tace “i still want be with you Suhaima, nasan ba abinda ya taba shiga tsakanin mu but ina son mu kulla alaka irin wacce duk rintsi zamu kasance tare dake” a idanun ta nake ganin iya gaskiyan abinda ta ke fadan. Bance mata komai ba na mike na bar wurin, ba ta tsaida ni ba har na bace ma ganin ta.

Anty Nainerh tabbas taga rayuwa da ba wani zabin da ya kwanta mata a lokacin wanda ya wuce ta fada cikin halin da tunanin ta ya kawo mata. It all doesn’t matters,  we makes different choices in life and  slowly it leads to our destiny, fate and future. Da a ce sau daya a rayuwanta ta zauna tayi tunanin what she is putting herself into, da tunanin ta ya kawo mata abu mai kyau to ina ganin da rayuwan nata bai kai da haka lalacewa. Sai dai a lokacin ta riga da tayi nisan da, the pleasure around it shine kawai abinda ta ke dubawa. Sadly, she got me under her dilemma. Yeah nayi rashin soyayyan da ko wani irin so da kusanci ya zo min nake karban shi hannu bibiyu. I was just so small to on my own. Shiyasa nace we make different choices, sai dai nawa choice kaman na dayawa daga cikin mutane, is the bad side of it. Though ba abinda ya shiga tsakani na da Anty Nainerh, i continue with the relationship even when i kniw the aftereffect. I mean nayi islamiyya, nasan hukuncin abinda nake jefa kaina a ciki. But it like i’ve already made the bad choice. I wipl have blame Anty Nainerh, saboda ita tasa min interest in sai dai clearly ita ma ta ban labarin nata rayuwan, maimakon in sa tayi realizing bad choice in da ta ma rayuwan ta, though nayi karabta sosai amma duk da haka ina da tunani mai kyaun da zan iya ganar da ita. Amma banyi hakan ba sai ma jona ta da nayi muka afka bakin rayuwan a tare. A daya bangaren kuma zan iya blaming Ajiidah, sai dai i choose not to. Nayi relaying akan duk wani move na rayuwata a lokacin sai dai kash,  sahawaran da take bani fahimtan ta kenan game da rayuwa. Mace ce wacce ta taso gidan su cike da yayyi mata dayawa, focus insu kenan kula duk wani abun kawa da yazo gaban su. So example da aka yi mata setring kenan, ba ko ta da wani abun da ta sani bayan shi. She see the pleasure in it and pain in avoiding it.

A haka graduation in su Anty Nainern ya gabato, kullum muna tare da ita duk da dai zaman labari kawai ya kunsa. We clearly enjoy each others company. irin gifts in da baiwan Allahn nan ta bani har sai da ya girgiza tunanin na, she gives me everythinv that comes her way. Ta sha sanar min tana tausayi na sosai, saboda irin rayuwan da ta san ina living. I don’t really care a lokacin, ba a sabo dawahala tabbas amma kuma yau da gobe dole akwai sabon ko da halin da kake jin kanka a ciki ne. Wlh a daren graduation insu har kuka ta min, zata yi missing ina waye waye kuma a lokacin nayi realizing ta riga da tayi nisan da ba ta hango baya. Kaman yabda ta fada iyayen ta na da zafi amma kuma basu da kula sosai, dan da sun kula dan sun gane rayuwan da yar su ke kokarin dosa a gaba kadan. Daga irin kalaman ta kadai zaka san cewa tana burin Rayuwa mai tsada a gaba, irin na samun yanci kai. Ko kasan ba ta ajiye kanta a kusa ba. ni dai na riga nasa wa raina alokacin tana gama schl in zan janye jiki na daga gareta kaman yabda Ajiddah ta fada tun farko.

A haka su kayi graduation su ka barmu a school in. Duniya dan zaman da mu kayi na jarrabawa bayan tafiyan su kuwa ba karamin asa muka sha ba, musamman yan set inmu sabida irin alaka mai kyau da ke tsakanin mu da wadanda suka fitan. Ni dai bai wani dame ni bama saboda ba abinda ban gani ba a lokacin in dai a duniya ne. Don ma dai malam Aminu da wasu daga cikin malaman sun dan tsaya mana kuma ana tsoron su a school in.

Wannan hutun ba musamman da ya kasance long vacation ne Amir sun zo. Sai ya kasance duk wani aiken da Anty Yana zata min tare muke zuwa dashi mu dawo, na nugun sabawa dashi muna tafe muna hiran soyayya dashi. In ko yana wani abu kaman ba dan sheakarun shi keyi ba, saboda manyanta irin nashi. In ko ina Ajeyari wani lokacin kawai zai debo jiki ya sa Al-lawan a gaba su zo nan gidan Goggo. Haka zamu fake mu sha hiranmu, musamman ma da Ajiddah ke bani goyan baya sabida yanzu tasan Amir, haka kuma tana yawon shi cewa mun dace da juna. Ta sha fada min kar in sake in rabu da Amir sabkda ba zan sake samun wanda ya fishi ba. Kuma nima na amince da hakan. Al-lawan yayi ta tsokana na, abinda na lura yafi sakewa yayi labari dani a gidan Goggo akan can gidan mu. Kaman dai ba ya son yan uwan shi sun san yana juya min baya ne kawai.

A hutun kuma na sake amincewa dashi dari bisa dari. Tabbas ban jin ina da kaman shi in, gabadaya labarin shi ba abinda ya bari bai sanar min ba. Danni a lokacin ma har na fara hango kaina a garin kaduna, kamannyanda muka yi alkawari ina gama secondary shi kuma lokacin ya sau aikin yi sai muyi aure. Everything is perfect kawai according to our own plans, kwata kwata ba wani obstacle da muka taba hangowa.

Anty Nainer kam tana gama school ashe Hajj suka tafi da baban ta da kuma wata antyn ta. Bayan nan tabi antyn nata sudan inda take zaune a can. Shiyasa ba naji ta shiru, a ranar ko da ta dawo washegari sai ga ta gidan mu. Har ga Allah nayi mamakin ganin ta dan na dauka mun riga da mun raba hanya. Da ke Yaya baba baya nan bata wani samu kulawa kaman na farkon zuwan ta ba, sai dai itan ma ba ta dade ba. Tsaraba dai ta kawo min, perfume, Abaya da kuma dan karamin waya. Godiya kawai na mata sannan na raka ta, bamu rabu sai da tasa na nata alkawarin zuwa gidan su. Wayan da ta bani ko cikin sauran tarkacen da duk na samu daga wurin ta na hada na ajiye. Wanda yawanci love letters ne kaca kaca da ta bani lokacin da muke school. Wani abun ma in ina karanta shi sai inga ko Amir bai fada min kalaman da Anty Nainerhn ke dangan tawa dani ba. Dole haka watarana na kashe zuwa ajeyari na ja Adama ta raka ni gidan su da zumman kawayen Halima. Maman su na da kirki tun daman da nasanta, haka wannan karon ma ta amshe mu hannu bibiyu. Da ke da mutane ba wani ajinda muka tattauna tsakanin mu da Anty nainerh illa iyaka ta tana ta roko na in kunna wayan da ta kawo min. Nan Adama ta dinga surutun daman har ina da waya ban kunnawa? Ban dai tanka ta ba. A motan gidan su aka maida mu, Ajeyari muka wuce. Su ma sai da suka shiga su ka gaida su Goggo tukunna suka wuce. Adama dai ranar a nan ta kwana. Abun mamaki sam jinin su bai hadu da Ajiddah ba, a cewar Adaman Ajiddan wai ta cika rawan kai ga kuma irin maganganun da ke fito bakin ta yafi karfin shekarun ta. Ni dai Adaman na bawa kaifi na san ta da saurin fushi daman, ga kuma masifa. Da na fada mata kuwa ba karamin kuluwa tayi ba, sanadiyyan tafiyan ta gida kenan. Ita ma dai Ajiddan sanar min tayi Adaman bata mata ba. Ni dai kawai sai suka sani a tsakiya don kowa ina jin dadin zama dashi dai dai gwargwado. Hutun nan ya min tsawo haka kuma hutu ne da ba zan taba mantawa ba, kasancewar ga Amir a kusa dani.  A kulkum duniya kaman kara kaimin nuna min soyayya yake, duk da so in bata da wani ma’ana a kaina a wannan lokacin. A haka har yan gidanmu su ka fara gano tsakanina da Amir in. Ba kuwa aikin kowa bane sai Adda Falmata, dan na gane abun ma sa ido ya kamo. Ba ma Amir ba har waya da letters in Anty Nainerh sai da ta binciko. Yanda abun ya kasance kuwa shine…Rayuwata

Babi na goma

Ranar gabadaya wuni nayi a kitchen a sandiyyan da bakin da aka yi a gidan. Wandan da kwata kwata ma banda hadi dasu. Amma hakanann na jifgan musu aiki. Abinda na lura kuwa shine kaman duk yan’uwan Anty Yana irin halin ta ne dasu, sam sam ba wanda ke da kirki cikin su. Duk randa mu ka hada hanya banda zagi datsangwama su inma ba abinda ke shiga tsakanina dasu. Cikin wadanda su ka zo ranar kuwa har da wata yar uwar su Safina, mugun halin ta kuwa sak irin na Adda Falmata, shiyasa nake ga tasu yazo daya.+

Bayan na gama kwasan aikin ne, a gajiye likis na nufi dakin da niyyan sannan in nemi gado dan banji zan iya wani abu a ranar. Abun mamaki, kaya na nagani na makaranta sun yi watsa watsa dashi a tsakiyan dakin. Still nayi ina kallon su, a raina kuwa na tsaya neman meya hada su da kayana. “Bakar munafuka karaso da uwar ki gantallaleyi yau dai Allah ya kama ki” Adda Falmata ce take maganan, daga irin kallon da take min nasan yau nai kwata na a wurin ta kuwa sai yabda Allah yayi kawai. Ban karasan ba duk da nasan irin abinda zai biyo baya, bugu ne na riga nasan bawanda bazan sha ba a ranar, don haka gwara inki matsawan ko bakomai a min wanda ke da dalili komin kankantan shi kuwa.

“Ba na fada miki na taba ganin su a Ajeyari da wannan abokin Al-lawan in da suke zuwa daga kaduna ba,  kika ce mai zai yi da ita?” Safinan ce wannan karon ta ke magana tana nuna ma Adda Falmata, pictures inda Amir ya bani ana washegari za su tafi. Wata kam sai a lokacin nasan in bala’i ya maka yawa ba wawanci da baka iya yi. Domin dai a lokacin daren da Amir zai tafi na tuno, yanda yazo ya same ni yana gaya min ba fa a daga tafyn su ba, gobe in sha Allahu za su tafi. Ban san sanda naji kwalla sun ciki min ido ba, akwai shakuwa na musamman kuma na daban da ke tsakanina da shi. Shi kanshi ya fuskanci halin da na shiga amma kuma sai ya dan fuske gudun ya sani kukan gabadaya.

Cikin siririn murya mai dauke da rauni nace “Sai yaushe kuma?”

“Wani Long vacation Suhaima, ai muna waya in sha Allahu ba wani matsala” juya kaina nayi a hankali wasu banzayen tunani su ka fara min yawa a kwakwalwa.

“Long vacation Amir, shekara daya fa kenan kuma kake kiran ba matsala? Abubuwa da dama za su iya faruwa a shekara daya, Haka kuma abubuwa da dama su kan iya canjawa ciki kuwa har da yanda muke ji akan junan mu. Za ka tafi bayan ka riga da ka saba wa zuciyata kusanci da kai, banjin xai iya rashin ka na wannan lokacin” shi din ma jikin shi ne yayi sanyi, juyiwa yayi ya fuskance ni da kyau

“Hakika Suhaima da ina da wani hanyan da zan iya ganin kafin cikan wannan lokacin wlh da nayi, za a iya ganina har yanzu karami amma Wlh ban dau lamarin ki da wasa. Ina sonki irin soyayyan da ban jin zan kara duban wata ya mace a duniya dashi ba fa wai zuciyata kadai ke sonki,  Aa da dukkan dyj wani abu da ke jiki na nake sonki My future wife, Dan Allah ke daina damuwan nan kinsan ban so ko?” A shagwabe na daga mishi kai, tun asali daman ni din shagwabibiya ce,  rashin Ummina ya sa ba wanda ya fuskanci hakan. Amma tun da na samu Ameer na ke sakin abu na kuma shi abun burge shi na yake, ya sha fadin yana kaunar mace mai shagwaba. Don ko Anty Nainerh, she is the weak one among us, shiyasa nan da nan za ta rafke.

“To mai zai hana ka zuwa amma?” Yanzun ma da shagwaban na mishi magana, sai da ya saki wani irin murmushi wanda kana gani kasan sautin muryana ba karamin ratsa shi yake ba. Kai ina son Amir, irin yanda ba zan iya fasaltawa ba. “Final year fa zan shiga, zan yi jamb, waec, Neco ga zaman extensions in da zamu yi kusan uku sannan kuma inyi facing graduation. Kar ki damu i want to focus ya da zan samu admission in University nan da nan inyi kudin da zan aure ki in fidda ki daga wannan kangin, i don’t like your curre t situation Suhaima zan so ace ina da daman fidda ki, i want to fight for us no matter what” Wani irin dadin da na manta rabo na dashi naji yana ratsa ni “My heart can’t never be free for anyone my future, i love you” Cike da kunya nayi maganan, wanda hakan ma yace yana burge shi. Kalaman kuwa duk a wurin ajiddah nake tsinta, ita ce malama ta a kowani fannin na rayuwa. Hannu na ya kamo duka biyu ya daura fuskan shi yana so in dago kaina sai dai na kasa hakan. A hankali shima yace “Na dade da gane we are made fir each other my love saboda tun ranar da na fara ganin ki, zuciya ta ke doka miki” ya fada yana taba saitin zuciyan nashi. Duk yanda na so daurewa ranar sai da nayi kwalla lokacin da zamu rabu. Life is crazy, so as love.2

Rankwashin da Adda falmata ta zabga min akai ne ya dawo dani daga duniyan tunanin abin kaunata da na shiga. Ban ma jin bala’in da take min tsabagen yanda saukan rankwashin nata ya gurgiza kwakwalwata. “Uban wa ya baki wayan nan?” Tmby da ya fito bakin ta kenan. Ban ko yi wata wata ba nace “Amir ne”

“Uban waye shi?”

Kai tsaye nace “Wanda Anty Safina ta fada miki” dukkan su wani irin kallo su ka jefe ni dashi, ko basu furta ba na son so suke suce wato wuyana ya isa yanka. “Dan wani dan iskan barawon ne shi da zai iya saya miki wayan?” Ta fada tana kallon wayan, kallon shi kawai take tana sakewa don ban ma san kudin wayan na da tsada hakan ba sai da naji tana fadan kudin.

“Amma dai kinsan Falmata hakanan dai ba zai dauki wannan abu mai uban tsada ya bata ba ko?” Kaman wacce aka zabura Adda Falmata ta juya tana kallon safina alamun son karin bayani. Algunguman sai cewa tayi “kila dai tana tsammi shi wani abu maza ai basa abu hakanan a zamanin nan wlh” tsaki Adda Falmata taja tace “wai me kike nufi ne ni?”

“Yana kwanciya da ita mana tana buda mishi kafafu”

“Ya subhanallah!” Shine abinda ya futo daga baki na. Adda falmata kam wani gigucewa tayi ba ta ma kalle ni ma sai ma daga kai da take ta faman yi alamun fahimtan abinda yar’uwan nata tace “Tabbas hakan nema” ba ko karamin doubt ta furta hakan daukan wayan tayi ta juyo tana kallona. Kai duniya wanda ya tsane ka ba zai taba son ka ba wlh, kiri kiri matan nan ta dauki wayan nan duk da makudan kudin da ta ambata ya kai, haka tayi sama dashi ta sa iya karfinta sannan ta sake shi a kasa. Hakan ma bai mata ba kaman wata mahaukaciya ta kara zabura ta dauko wayan ta kara hadashi da bango har sai da ya tarwatse. Budan bakin ta kuwa ce tayi “bai ki matsayin da zaki rike wayan da ban taba rike ta ba wlh, na fasa ne don kar ma in nuna ace in bar miki bakin ciki ya kashe ni gwara in dagargazan inki fadawa Abban duk da na sofada mishi ne ya dau mummunar mataki akan ki” Safina kam sake baki tayi tana kallon wayan “Amma Falmata baki da hankali ai da sai ki bari ke din ki amfana da ita” girgiza kai tayi sai wani huci take kaman wata zakan ya “Allah ya kyauta, wlh na fi karfin in rike abinda wannan yarinyar ta rike. Gwara kowa ya rasa” Tabe baki Safina tayi tace “ai to da sai mu saida” wannan karin kam dariya tayi tace “Ayya Safina baki san ni ba ashe, ai duk tsada da mahimmanci abu in dai zai biyi ta hannin wannan yarinyar to wlh ban son shi. Na rifa da nafi karfin ta, kai ban ma yarda dake ba” Tace sannan ta mike ta fara kokarin zubi da sauran kayana, Safinan na taya ta. Ni dai motain kirki banyi ina gani har aka gama fiddo kai, ban ankara ba naga sun hankado jakan da letters in Anty Nainerh ke ciki. Jiki na rawa nayi saurin daukan jakan na rungune shi a jikina, ashe babban kuskurw nayi domin kila da ban dau jakan ba da basu bude ta ba. Amma abinda nayi ya jawo gabadaya hankalin su ya koma kan jakan, wani irin fisgewa da suka yi a jikina sai da yaja nayi wani taga taga kafin na fadi sharban a kasa. Amma ba tani ma suke ba, illa ma rige rigen bude jakan da su ke. Sai da su ka zazzago papera in gabadaya sannan karaman wayan ya fado. “Au kice ba ma shine na farko ba?” Safina ce ta fada sannan tayi saurin kunshe wayan saboda kar Adda Falamata ta fasa. Sarkokin duk da Anty Nainerh ta bani su ke ta fiddowa suna sakan baki. Adsa Fakamata banda kwafa ba abinda take, Safina ko sai faman fadin “Ai na gaya miki daman jikin ta ta bashi, in ba haka ba shi mahaukacine da zai kwashi wadannan duk abubuwan ya bata? Allah ma yasa kanshi kadai ya tsaya” ni ko roka na daya kar su bude takardun nan, don in abun ya tsaya a Ameer kadai to fa komai zai zo da sauki. Sai dai ban gama wannan tunanin ba na gama Adda Falamata ta bude wani takardan tana karantawa. Girgiza kai naga ta fara yi sai ga wani murmushin mugunta yaba fito daga fuskan ta. “Lfy kike murmushi Falmata?” Amsa Safinan tayi da cewa “Kema dauki daya ki karanta you must smile” haka kuwa akayi, ina jin suna karanta letters in a fili. Wanda kiri kiri ke kunshe da kalaman soyayya, gashi kuam sun ga sunann mace a karshen ko wani letter. Daman duk letter in da ta bani a kasa sai ta rubuta Nainerh, sannan ta sa date.

Zaman dirshan kawai nayi a kasa ina jiran the worst ya faru domin ba abinda su ka rage ba su karanta ba. “I can’t wait to hold you, touch you, kiss you and tell you how much of you i want” dariya take sosai tana karantawa. A lokacin kuma na san banda bajin da zan iya defending kaina cewa ba abinda ya tava shiga tsakanina da Anty Nainerh na gogaggayar jiki. Wani kululun bakin ciki naji ya taru ya tsaya min a makoshi, ji nake kaman in na hadiye to rayuwa ta zan hadiye. Ba abinda nake gani a gabana illa tsan duhu, don har abinda su ke fada ma dawowa nayi banjin komai. Sai wani dum da ya taru ya min yawa, hakika bala’in duniya kuma banjin akwai wanda ya rage ban gani ba. Wannan wani irin rayuwa ce? Tmby da na dinga jefo ma kaina kenan. Ban kara jin komai ba sai karan dariyan su sadiya kai ba ma su kadai bane yawan su yasa na gane harda kawayen su, wadanda dayawa daga ciki akwai yan gidan su Sanda. Kafin kace kwabo gidan ya tashi banda ihun yara ba abinda kake ji suna ta faman fadin “An kama yar madigo an kama kazama matsinaciya, la’ananna” kidan da Abty Falamata da Safina ke faman yi yasa yara dayawa ke kara kutso kai cikin gidan mu har zuwa dakin baccin mu, a namin kida a na kira na da sunayen da ko makiyi na ban fatan wani ya ambace shi da hakan. Wlh a ranar na fara sanin kuka na kafe ma mutum yaki zuwa. Su Adama basa nan, nasan da hayaniya ya kai gidan su kuma da ko ita ko Goggo wani sai yazo. A haka Yaya baba su ka shigo shi da abokanan shi guda biyu. “Kai lafiya miye haka? Wannan wani irin waka ne?” Muryan shi kadai naji na gane shine, bakomai kuwa ya sani rike muryan nashi bane sai lokacin da yake duba na a fuska yana gaya min ba shi ya kar zomon ba dan uwata ta tagi in daina hararan shi. Sai kuwa lokuttan da ya dinga min dariya in ina wahala haka wahakan dayake bani dukkan lokuttan da nake zuwa gidan su deban ruwa. Hakika na fi jin haushin shi da irin su Safina, sabida ina jin cewa su baruwan su, don si in su Falmata sunyi kilan uwar su suke tayawa kishi. Ihu yake yana musu tsawa su daina wakan da suke, sai dai shi dinma nasan yana jin abinda nayi dariyan zai min kaman yaran. Da kyar yaran nan su ka fita daga gidan, ni dai gani kawai a wurge a kasa. Bai kuwa ko kalle ni ba naji yana cewa Adda Falmata “lafiya me ya faru?” Sai lokacin naji muryan Yaya baba yana fada min “Wannan baun kuma meya same ta?” Matsayi ma na samu da har ya iya tmbyn abinda ke damuna so dan ya kira ni da abu bai ya zama wani kayan gabbas ba. Shi dai dayan abokin bai ce komai ya juya ya fita. Da shu’umanci ji nayi Adda Falmata na cewa sandan “Ya Umar Sanda baki cairo yaushe ka shigo?” Bai amsa ta ba sai ma kallon da ya watsa mata akamun yana jiran amsan ta. Na dade da sanin cewa Adda Falmata na son Umar sanda, yanayin ta kadai a gaban shi daban ne.

Bata ce komai ba ta dauko letters in nan ta mika musu. Sandan ne yayi saurin amsa ya fara karantawa, girgiza kai kawai yayi sanann yace “To miye na tara mutanen Falamata? Ba kanwar ki bane? Meye sa baki hukun tata ba?” Ba tace komai ba, kuma nafi alakan ta hakan da ba ta son ta fadi abunda zai bata mishi rai ne, har yaga aibunta.

“No wonder munafukai ashe ni kuka sa a corner ko dan uwarki” Yaya baba naji yana maganan yana kwafa “ai gwara da kuka yi ma yar shegiyar haka ita ma Nainerhn sai naci Uwar ta wlh. Yan iska, tsinannu, asararru” Yanda ya fita kaman an kore shi sai kace zai je yayi ma Anty nainerhn wani abi,  bayan nasan ko ganin ta yayi yanzu a gaban shi bai iya tabuka uban komai.

“Taso Suhaima” abinda Umar Sanda ya fada kenan, sai dai kallon banza ma bai ishe ni ba. In taso in mai uban me? Ya cigabada wulakanta ni bayan na baya daya min.

“Taso mana” ko kalla dai ban ce ba. Hakan yasa ya gane ba magana zan mishi ba.

“Shikenan tunda kin zabi hakan” kawai yace ya fita. Ko a jikina kuwa, don nasan shi inma wani muguntan ne a ranshi. Adda falnata kuwa cewa tayi “wlh da kin bishi yau ba dukkan da zan miki sai kin manta kanki” akan abinda ta min yau, wlh ji nayi dama dukkan da ta saba min in tayi.

Ko da Anty Yana ta dawo daga inda taje ta tadda labarin. Ba ta wani girgiza ba tace “to abun mamaki ne? Ku ka san mai Uwar ta take? Ai gado ba karambani ba” Ko kadan kalaman Anty yana bai dameni ba don dai duk tafi min yaran nata. Da ta ita ne ba ta damu Abba yaji zancen ba don letters inma ba wanda ta amsa ta karanta. Kai irin tsanan da Anty Yana ta min irin tsanan nan ne na komai naki baya gaba na, ko kadan ban dame ta ba kuwa. Illa iya ka ta sani aiki in mata kawai shikenan.

A cikin Yaya baba da Adda Falmata bansan waya kai ma Abba letters in ba bayan ya dawo. Ranar irin dukan da yamin ban jin ya taba ma wani a rayuwan shi, dukkan jiki na sai da ya farfashe ba kuma wanda ya bashi hakuri a cikin gidan mu. Ihu na yasa abun dangatawa da makota, Umar sanda shi ya shigo ya fisge ni daga wurin Abbah ko daya nemi kai ni asibiti kuwa na watsa mishi rashin kunya har ma da zagi sannan na gudu gidan su Adama. Goggon ce ta kaini asibiti, tayi jinya na ba wanda ya leko a gidan mu. Yan ajeyari kuma basu sani ba. Baban Adama yayi settling bills ina lokacin da za a sallamo mu. Kwana kusan uku gidan ta sai da ta fuskanci na ji sauki sannan ta sa ni a gaba tana tmbyna me ya faru. Tsab na sanar mata abinda ya faru haka kuma tsakanina da Nainerh. “Asha asha nifa shiyasa ban son makarantan kwanan nan kuma in sha Allahu kin gama ta” daganan ba ta kara min zancen ba. Abbah boye ma Goggon Ajeyari zancen yayi sannan kuma ya gargadi yaran shi akan fada mata in.

Unguwan mu ko gabadaya ya dauka, mata na biki kai har da kirkirarrun labaran da ban san daga ina su ka fito ba duk yawo kawai su ke, duk na bi na tsangwami kaina na rame na zama wani abun. Inda Allah ya taimaka kwata kwata Anty Nainerh ba tazo wurin a ba kaman yabda tasa da nasa ba abinda zai hana Sdda Falmata tasa a bita da jifa. Abu ya kai ya kawo ko fita nayi yaran sun dinga bina kenan suna min wakan da Adsa Falmata ta koya musu. A karashe dai Goggo har guda ta taka taje ta warware wa Abbah, nasan hakan ne sabida yanda ta dawo tana ta masifa. Daganan kuma ranar da dare yazo ya dauke ni, sai da na shiga motan na ga gabadaya kaya nane a ciki. Duk yands na so ko dariya ya min ba fuskan hakan. Ajeyari ya kaini, bayan sun gaisa da Goggo naji yana fadin “Goggo ga Suhaima na kawo miki za ta zauna a nan har tsawon wani lokaci” Wlh a loakcin naji wani irin sangi na ratsa ni.

“Ince ko makaranta za ta koma?” Goggon ta bida. “Na canja mata makaranta, za suje da Garba ya mata Register a Nana Aisha”

“Ma sha Allah” kawai Goggo  ta fada. Bai wani dade ba ya bar gidan. Daga lokacin kuwa na fara rayuwata a ajeyari.Abuja, Nigeria.

Gabadaya Al’amura sun cabe mata tun daga lokacin da taga sanarwa rasuwan Amal, tayi kuka ta yanda har take ganin ba ta da ragowan hawayen da ya rage bai fito ba. Sai dai har yanzu ta jasa gasgata zancen duk ko da yanda yake ta yawo a kafaffan yada labarai. Sai yanzun ta ke kara tabbatar ma kanta da gasken rayuwan ta bai da wani amfani kuma, a duk wani dakika daya da zai wuce tana raye sai ta tuna cewa wai yau Amal bata duniya kuma daga report in da ake ta bayar wa yasa ta gaza gasganta cewa bata da sa hannu a mutuwan Amal in. Abin bakin ciki abin takaici kuma Allah wadai, shine duk abinda ta tara ta aikata sannan kuma gashi ita har yanzun ba ta da wani riba. Dole ma ai taga bala’i da masifa, wannan ma ba a fara ba, sannan kuma ba ta jin ta cancanci neman yanci da Dr Fahad da kuwa Brr mustapha ke fafutakan yi a kanta. Shakka bbu ta cancanci hukunci mai tsanani da horo. Kai ba ma ta jin za ta iya yafe ma kanta in har ba a dauki mataki babba a kanta ba. Ta shiga rayuwan su, farat daya ta rusa musu duku wani farin ciki da suke ciki gashi ita ba ta da wani riba. Ina ma yau zata hada idanu da Faree da kuma Umaymah, to da ba abinda zai hana ta dau wuka ta lafga musu, ya tabbata cewa ta aikata kisan da ake zargin ta dashi, suma sa dandanin mutuwan da suka sa baiwar Allah tayi ba taji ba ba kuma ta gani ba. Shin ma wai ita wani irin rayuwa ne take living? Kulkum daga wannan sai wancan, tun tana karaman ta take ganin ibtila’i kala kala irin na rayuwa. Tun lokacin da mahaifiyar ta ta tafi ta yarda ita a wurin kishiya. “Astagfrillah Allah na tuba, Allah na tuba. In jarabawa ce kuma Allah ka bani ikon cinye shi” a fili ta fada cikin wata irin raunanniyan murya da kana ni kasan ba karamin tashin hankali ta ke ciki ba.1

Yanda tayi maganan ne yasa har zeenah taji ta. Tunda tazo ba wani zama su ke suyi hira ba, duk dai tana kokarin deba mata kewa. Zeenah akwai surutu sai dai kuma ba ta cikin sakewan da har za ta iya zama tayi hira kafiya kalau. “Lfy kawa?” Ba ta tanka ta ba sai kife kai da tayi a jikin kujera, ita ba kuka take ba amma kuma abinda take fuskanta a yanzu yafi karfin tunanin duk wani mai tunani. “Kawa mana” zeenah ta kara fada tana dafa kafadan Suhaiman da still dai ba ta dago ba.

“Kina so mu koma asibiti ko?” Ita kam zata so ma zaman asibitin, ba kuma ta cikin hayyacin ta akan irin wannan azaban da take fuskan ta. Zuciyan ta zugi yake mata, ga kuma wani irin bugawa da yake yi kaman zai fito fili. Ko ba a gwada ta bama ta san tana fama da ciwuka dayawa wadanda take ganin ta cancanci samu. Sai dai ba ta jin za ta iya kuma yadda amma mata wani treatment bayan wadanda aka sha yi a baya, gwara ta sha jinyan ta, ta wahala kaman yanda ta wahalar da yae mutane, in yaso ita ma in abu yazo da ajali sai ta tafi kawai. Sai yanzu ta ke jin ina ma ba ta amincewa Barr mustaoha ya sa anyi bailing ta ba. Tabbas da zaman gidan kurkukun ya fi mata nan da ya kasance fayau ba wani abu farin ciki ko marmari a cikin shi. Duniyan ma gabadaya ji take kaman yana juyi ne, gabadaya ta rasa ina ma zata fuskanta. Ganin har jikin ta ya fara rawa yasa Zeenah ta dan kamo ta. “Relax mana haba, wanda ya mutu yana dawowa ne? Ina ce kece mai min wa’azi why are you acting like this” da kyar ta iya juyawa ta fuskanci zeenah, cikin rawan murya tace “na gaji da duniyan ne, na gaji da rayuwan komai bai dai mahimmanci ko amfani a gare ni. Wlh na gaji, ban jin zuciya ta tana da karfin kara daukan wani abu kuma. I was so weak at first amma irin abubuwan da na fuskanta ya sa zuciyata zama mai nauyi, amma yanzu am crushed”

Kwalla ne ke faman ziyaya a idanun zeenah. On normal circumstancea ya kamata ace suhaima tayi mamakin hakan sai dai ko dar illa ma ganin da take hawayen dadin kawar ta take yi, duk da ma ta san a sanadiyyan tausayin tane.

“Kiyi hakuri kawa don Allah, ki kara juriya komai zai karshe” Hakuri, juriya, karshe. Kalmaomin nan guda uku gabadaya ta tsani jin su a yanzu, ta dade tana jin su sosai sai dai har yanzun abinda ake fada mata bai zo ba, wai to shin sai yaushe ne hakan zai faru?

“Zan baki baki ba wai don ina yi sai don nasan da naci a cikin wannan matsalan shawaran da zaki bani kenan. Kaman dai yabda Dr in ya fada miki, addu’a kawai zaki dinga mata sannan ki cigaba da rokon Allah gafara don tabbas kin kwace mishi. Amal kuma sanadiyyan ajalin ta kenan, ba wanda ya isa ya canja hakan” runtse ido Suhaima tayi tana sauraron ta, haka kawai take jin zata so ace yau shawaran da Zeenah ke bata ita zeenahn za ta iya amfani dashi, hakika da ta godewa Allah. Ko bakomia tana ganin wani kaso na daga cikin laifin ta zai ragu tunda ta iya juya wata zuwa hanyar alkhairi.

“Kinsan duk wadannan abubuwan kawa, duk abinda nake fadi maki yana kwakwalwar ki, to amma meyesa baki yi?”

Dif Zeenah tayi na dan wani lokaci, dan ta girgiza da tmbyn “Nayi kokarin canjawa na yan watanni kawa bayan mun rabu dake. Sai dai matsalan farko banda inda zan zauna, na koma gidan Inna na da na fada miki sanadiyyan azaban da nasha yasa ni barin gida tare da saurayi sai dai koraj kare suka min, ba su zaunda karuwa ba. Ba ma nan duk inda naje zancen kenan, da ama ce ni din banyi karuwanci bane. Amma yanzu ina da bakin tabin da banjin zai taba iya gogewa Kawa. Banda wani source of income, sannan ko na samun ma ban jin akwai dan arzikin da zai siya kaya na. Society, na daga kasa casa’in acikin dari da ke hana mutane dayawa tuba, ba ama ka uzuri balle a fahimce ka. Ba ma ni kadai ba kawa, dayawa daga cikin yn uwana da ke zaman kansu abinda ke hana su komawa hanyan gaskiya kenan. Karuwanci ba ta dadi, kana zaune da mutane bas ganin mutuncin ka balle kuma wani abin tausayi ya biyi baya” da kuka shabe shabeta karasa zancen, tabbas gsky ta fada sai daisuhaiman ba ta jin wannan ya isa hujjan dazai sa mutum yaki komawa hanyan gsky bayan yasan da ita.1

“Wannan ba dalili bane kawa, mutane za su hana ki bautawa Ubangijin ki su tura ki hanyan sabo? Kar kiyi haka, da ma komai na rayuwa cike yake da kalubalai iri iri. Kar ki dube jama’a, Aa ki dubi Ubangijin ki ki nemi yafiyan shi, ki tuba zuwa gare shi sannan ki natsu ki koma gare shi ni kuma na miki alkawarin sai kinga banbanci fiye da na rayuwa da kike ciki a yanzu. Kar mu dawwama cikin laifin da muka dade muna aikata shi kawa, wannaan abinda na ke fuskan ta kadai ya ishe ki aya.”

Sosai maganganun ya shige ta, sai dai duk da haka tana jin wani irin wasi wasi dake yawa a kwakwalwar ta. “In na daina kina ganin akwai wanda zai iya aure na?”

“Wannan ma Allah zaki bar mawa, addu’a fa ita ce komai. Infact ban baki shawaran ki hango duk wani jin dadin da ke cikin duniya ba, Aa ki tmby kanki in kika mutu a wannan halin me zaki shaidawa Ubangijin ki? Wani irin azaba zaki fara fuskanta tunda daga cikin kabari? Kinsan waji irin fushi Alla yake yi dake? Shi fa abun haram bai da wani daraja ko kuma dadi sai dai shaidan ya sa miki shagalan da har zaki iya jin dadin abun. Misali ki duba yanda kike daukan kanki ki bai wa namiji saboda kudi, shin kin taba jin dadin kwanciya da duk wanda kika taba kwanciyan dashi?” Girgiza kai zeenh tayi, Suhaiman ta cigaba da cewa “to ki duba, kin san wani irin dadi mtan aure ke samu daga wurin mazajen su duk sanda su kayi saduwar aure? Saboda me yasa? Sun san darajan su, sun sa kiman su kuma suna mutunta su. Ba kaman ku ba da namiji kawai zai kwanta ya biya bujatan shi ya kara gaba. Baki bukatan wani tunani, don Allah ki fuskanci gsky, za kimin alkawarin hakan?” Duk jikin ta yayi sanyi, da kyar ma sautin muryan ta ya fito tana fadin

“Na miki kawa, in sha Allahu zan canja. Allah ya shirye mu baki daya. Dan Allah kema ki daina kukan nan, tunda kinsan bai da wani amfani a gareki. Ba sai na miki wa’azi ba domin nasan duk abinda zan fada kin san shi amma Dan Allah ki sawa zuciyan ki salama komai mai karewa ne, ba za a dauwwama a cikin shi.”2

“Allah ya bani iko, zanyi yanda kika ce sai dai hakika ina tausayin rayuwata, ina tausayin kaina Kawa. Banda kowa a hakin yanzu bbu wanda ya tsaya min, ban san yanda zan kare rayuwa a haka ba.”

“Allah zai kawo mafita” amsan da zeenah tace kenan, hakan kuma yayi dai dai da shigowan Dr Fahad, gabadayan su ba su san ma ya shigo garin ma. Kalli daya ya ma suhaima yaga duk ta fada, bai san sanda ya hade rai ya fita daga falon ba tare da ya amsa gaisuwa da suke mishi ba. Bai dade ba sai gashi ya shigo da abun gwajin jini. Sai da suka hada ido da Suhaiman, tayi saurin dukar da kanta sanin ba ta da gsky kawai ta mika mishi hannun. Ilai kuwa diastolic da sistolic in duka sun hau. Bai ce komai ba ya kunci abun “Da gaske dai kike kin gaji da rayuwan ko?” Kasa ce mishi komai tayi, ya juya wurin zeenah “tana cin abinci” Da Aa zeenah ta amsa, yanzun ma bai ce mata komai ba ya samu wuri daban ya zauna yana kallon ta.

“Haka za muyi dake?” Tmbyn da ya fito bakin shi kenan. A hankali ta girgiza kanta, sai kuma tayi gum ba ta kara wani magana ba.

“Okay nasan you arw currently facing a lot amma ba shi bane hujjan da zaki cigaba da yin abinda kike yin. Duka shekarun ki nawa Suhaima? Amma kinga yanda kike sa jinin ki yana hawa kuwa? Ba fa wanda ke cire rai da rahman Ubangiji. Ke kike ganin rayuwanki ba ta da wani amfani amma Ubangijin ki da ya bar ki a rayen ai sai ki gode mishi da rahman rayuwan da ya miki ko? Kar ki kasance mai butulci. Jiya da wayewan garin yau kinsan mutane nawa Allah ya amshi rayuwan su? Wadanda kika sani da wanda ma baki sanin ba. Duk cikin su zasu zo sune ke da aron rayuwan da Ubangiji ya mallamaka miki a yau har kike ikirarin kin gaji dashi” tana sauraron shi har ya gama magana ta ma rasa da wani bakin za ta iya fara mishi magana. Hakika tana jin yanda Dr da Barr ke tsaye akanta kullum burin ceton ta kawai su ke. Amma ita fa dame ta saka musu? Shariya da kin bin zancen maganan su? Nan take ta fara jin ba dadi, ita kunyan Dr in ma ta fara ji, don a halin ta ba tayi tsammani akwai wanda zai tsaya akan ta kai da wuya yana kokarin taimka mata ko ta halin kaka ne. Allah Ubangiji ya saka musu, ta fada a zuciyan ta. Dan ko fara’an da tayi, sai ya sanyaye ma likitan rai.

Daga daya barin kuma Barr mustapha ne rike da manuscript in suhaima, yana kokarin fahimtan irin badakalan da ta ci karo dashi a rayuwa. Sai dai duk lokacin da yayi shiru yana tunanin, sai zuciya shi ta dinga sanar dashi amsan tmbyn shi yana cikin takardan da ke gaban shi. Da ke shi ma’abocin karatun litattafai ne sam karatun manuscript bai bashi wahala ba.

Rayuwata

Babi na Sha daya.

Ajiddah ba taji dadin komawa na Nana Aysha sai dai ba yanda ta iya. Duk yanda kuwa ta so a gidan su a maida ta makaranta ita ma, ba wanda ya saurare ta. Hakanan ta hada kyan ta, ta koma GGC ni kuma na fara zuwa Nana Aysha a JSS3. Ba laifi am progressing well there, sai dai har yanzu abinda ya faru tsakanina da su Adda Falmata a sabon fegi na damu na. Amir kam tunda aka fasa min waya kuma ba Al-lawan balle muyi magana, shiru ne kawai a tsakanin mu. Anty Nainerh kam mun hadu sosai, kuma tas na kwashe abinda ya faru na gaya mata. Gudun kar labari yazo ya dawo mata din dai yan garinmu ba laifi akwai aikin wannan. Jin haka itan ma sai ta janye jikin ta daga gare ni sai ya zamo banda wani matsala sai dai na rashin jin Amir. Ina son in samu wayan in kira shi tunda ina da numban shi a kaina.

Ina jin dadin zaman gidan Goggo, saboda banda wani matsala ko kadan sai riritanin da ake yi. Komai tsohuwan nan ta samu in dai ban nan to sai fa ta ajiye min, komin dadewan da zanyi kafin in dawo. Nayi kawaye dayawa a Nana Aysha, sai dai ba wanda muke kut da kut da ita sosai. Ana dai mutunci da kuma harkoki tare. Adama kuwa da ke itan a Royal take, ba mu cika wani haduwa ba sai dai in ita tazo Ajeyarin kawai, tayi ta min mitan ban zuwa gidan su. Ni ko ba ta san sabon fegin ma ji nake na tsane shi baki daya ba.

Kaman yanda na hada target, gun Anty Amaraya na je na amso wayan ta da niyyan zan kira kawata. Sai dai ina fita nayi dialling numban Amir. Ya ko dauka, ko da na mishi magana naji ya amsa min normal ba kaman yanda mu ka saba magana dashi zai da naji wani iri amma kuma sai nayi tunanin bai gabe dani yake magana bane. “Amir Suhaima ce fa”

“Suhaima ai na gane ki, yakk? Ya schl kuma?” Amsa shi kawai nayi da lfy, amma daga yanda ya ke min magana na fara hango matsala.amma dake zuciyata ta dade da yin nisa a bangaren shi sai na fukse na cigaba da kokarin kakalo hira dashi. Daga Eh sai Aa yake amsa ni da. Bawani nayi missing, kwana dayawa kin manta dani, ba kalaman soyayyan da ya saba ma kunne na da sauraron duk lokacin da ya jiyo sautin muryan shi. Tabbas Amir ya canja, sai dai kaman yanda na fada mishi ne, anything zai iya faruwa a cikin shekara daya. Ya dinga musa ni, sai gashi a shekara ba a kai ko ina ba ama an fara samun canji. Hmmm, zuciya mugun abu ne, wlh hakannan na cigaba da zuba mishi surutu yana amsa min da daddaya, ina fa jin ba dadin amma zuciya tata zabi saurarinnuryan nashi a ba dadin fiye darashin sauraron. A haka har katin Anty Amarya ya kare, maimakon ya kira ni kaman yanda ya saba. Tun ina jira kuwa har na gaji na maida mata wayan ta. Bayan nan ma na sha zuwa in duba wayan ko zan ga missed call inshi amma shiru kake ji.

Wani karin sakarcin sai na kara daukan wayan Goggo na kira shi. Ya kara min sak abinda ya min wancan karon, ni kuwa har da ce mishi “Wayan Goggo ne wannan za mu iya magana ta nan” ko toh bai ce min ba, na cigaba da mishi surutu. Ko dan ance kananan yara ba su iya soyayya bane? In ba haka ba taya mutum yana nuna maka he is no longer interested kana cigaba da kara kiran shi? Haka episodes in mu ya cigaba da kasance wa da Amir, sai dai a hankali ana samun kari. Don ya fara cewa, ya gaji bacci yake ji, Aa kanshi na ciwo abubuwa dai gasu nan barkatai mara tushe. Kuma duk wannan bai taba daga waya ya kira ni ba sai dai ni in kira shi. A ganina ai da yana yawan nema na.

Kai daga karshe fa sai da bawan Allahn nan ya fito ya min open kafin na iya kyale shi. “Suhaima are you enyoing this thing a haka?” Ban wani gane inda ya nufa ba, sai dai naji gaba na yayi waji irin faduwa nace “meke nan?”

“This relationship mana, ba kijin kaman this is no longer working?” Duk a zato na , ya fadi hakan ne saboda mu gyara matsalan da ke tsakani “Ina ji mana Amir, i’ve been thinking so wlh. Amma kai me ka fahimta?” Da saurin shi yace “To Alhmdlh tunda kin gane hakan, let not be struggling wurin gayara abinda ya ruga ya rushe. Maybe is not for the best tun daman. I mean we can still be friend” kam bala’i, a take a lokacin naji wani irin zafin a jiki na, zuciyata da kuma kwakwalwa ta. Kai jikina har karkarwa ya fara. Like where have i ever gone wrong? Is it that i care too much? tabbas ba laifin shi bane, kulawan da na nuna mishi ne ya baki shi guarantee in yin hakan.

“Baki ce komai ba?” Ya kara fadi, bai san jin saukan muryan shi nake kaman saukan garwashi a zuciya ta. Ganin dai da gasken jira nake ya ce wani abu “Let not do the friendship ma kawai, i think it will be better”2

“Haka kika ce?” Banza nayi dashi, ga wani irin kuka kuka da nake jin yana zuwa min ina tare dashi, ga kaina da ke wani irin juyawa. “Kalla Suhaima, let not do this. We can still be friwnd kingane, ban son kiga kaman na yaudare ki ne ko wani abu makamancin hakan. Please just understand me mana, kinji” Hmm, ba sakarcin da nayi a wannan lokacin kuwa kaman yanda na dinga jin maganan da muke dashi a lokacin ma, am enjoying hearing his voice. Sai dai kuma ban kara wani magana ba sai ma na kashe wayan. Kukan ma kasa shi nayi, i can’t ask him ya fada min meya faruwa kuma tunda shi din bai min bayani ba. Ya kira ni ya kai kusan sau hudu bayan na kashe amma ban dauka ba. Ranar da zazzabi na kwana na tashi, duk nayi wani iri. Duniya ka guji rashin abinda ka gana sawa a rai. Wannan kuwa shi ya zamto karshen alaka ta da Amir.1Rayuwata

Babi na sha biyu

Rayuwa sam ba ta min sauki ba, imagine a dan kankanun shekaruna na riga na gama sa wani a rai. Sai dai ya tafi ya barni a inda ya tsinci ne tun a farko, cikin kangin wahala ds takaicin rayuwa. Wai din na a lokacin ina zama gidan Goggo. Sai dai ina girma ina kara tuno mahaifiyata, Ummi da ta tafi ta barni ba ko waiwaye balle ta san hakin da nake ciki. Abun jarin haushin, ba ma ni kadai ba hatta yan uwanta ba wanda zai buda baki yace ga inda Ummina ta tafi. Daga ita har Maijiddah. Kanina Baffah kuwa tun yana maganan ta, har ma ya fara mantawa da ita. Sai dai yanzu shi bai ma garin Borno. Kaman yanda naji wai, cousin insu Abbahnmu tazo ta roki alfarman a bar mata shi saboda ba ta taba haihuwa ba. Hakanan kuwa suka dauke shi suka bada. Kasan ma gabadaya ita ba a nan take da zama ba. Shi inma dai rabo na dashi yayi shekaru.+

Anty Nainerh ta tafi school Abuja, musamman ka fin ta wuce tazo ta same ni har gidan Goggo, kaman yanda ta saba wannan karon ma gifts ne kala kala ta kawo min. Da ke Haleematu na makaranta ita da wata kawar ta suka zo, Faree’ah. Lokacin na fara sanin ta, haka kuma daga yanayin kallon da take bina dashi kadai na fuskanci ita in su Anty Nainerhn ne. Ban ma kara tabbatarwa ba sai da naji tana ce mata “wai ke faree miye haka? Wannan wani irin kallon iskanci ne, na dai gaya miki ba irin ki bace ko?” Ba ta ma yi zaton naji zancen ba saboda na fita daga dakin su kayi shi. “To wai ke meye sa baki gwada naki sa’an na she will accept you, i can see she likes you Allah” van san wani irin reaction Anty Nainerh tayi ba na dai ji tace mata “Ba lallai ki gane ba amma Suhaima ba irin wannan son ta ke min. I know she likes me as a sister ko as a friend ko dan saboda kula da itan da nayi a school. Ba zan kuma iya destroying rayuwan ta ba kaman yanda ni nawa rayuwan ya zama. Yarinyar nan da kike gani ta sha enough wahala a rayuwan ta ba kuma tayi deserving rayuwan da mu muje ciki ba. Ina so ko yayane ne taji dadin rayuwa, shiyasa ban takura mata ba.”

“Hmm ehm” shine kawai ahinda Faree’an tace daganan kuma sai na shiga dakin. Sai kuwa a lokacin na gane dalilin da yasa Abty Nainerh bata taba nema na da wani abun banza ba. It so clear she likes me like a sister. Haka dai na raka su suka tafi, wannan karon ma har wani waya ta kawo min, babba ne ma na wannan karon. Amma ni bai dame ni ba sabida wanda bake ganin za muyi wayan tare dashi, we are no longer together.

Ba zance ina da Farin jini ba, i mean ban kai Ajiddah ba. Duk da hakan ina haduwa da maza da yawa da su kan so in basu dama, sai dai ban bada fuska saboda Amir a lokacin sai akan Mai Aliyu, kaman yanda na fada muku sunan shi. Yana da ilimi sosai na arabi da na boko, malaman makarantan na matukar alfahari dashi. Duk mazan da su ke da shekaru 16, 17, 18 zuwa 19 haka za ka same su da matukar rawan kai, rashin ji da sauran su. Sai dai banda Mai Aliyu da ka ganshi ka ga natsuwa sosai a tattare dashi. Mafarin maganan mu ko watarana Mr Auwal, malamin da ke koya mana physics ya shigo ajin, sai dai har ya fita ban gane komai ba, ban ma san ina aka sa a gaba ba. Physics na matukar bani wahala duk da yanda na ke son maths. “If there is something you don’t understand, remember you are free to meet me in my office. See you tomorrow class” charab! Abinda ya fada kunne na kenan, ai ko dole in je in sa me shi. Ana tashi break nayi hanyan office in nida wata kawata Aisha da ta raka ni amma sai ita ta tsaya a waje.

Su biyu ne a office da wani English teacher na SS3 Malam Aminu. Ina zuwa na nemi izinin shiga aka bani, sabon gaisuwa na musu su duka biyun ba tare da na duba daliban aji shiddan da ke zaune a wurin ba su biyu suna magana da Malam Aminu. Bayanin abinda ya kawo ni na mishi “oh okay where and what do you not understand”

“Everything sir”

“Oh! This is serious” shiru yayi ya dan dago yana kara kallo na “do you know what? Please just come back when am less busy i shall try and guide you then”

“Okay, Thank you sir” har na juya zan fita naji ya ce “or Aliyu can you please help me tutor the lady?” Lokacin na juya na kalle shi, murmushi ne a kwance kan fuskan shi yace “No problem sir”

“So please meet him” yana fadin haka ya cigaba da abinda ya ke. Barin marking in da su ke ma Malam Aminu yayi yace min “let talk outside” bance komai ba na bishi, ina jin Malam Aminu na fadawa Mr Auwal “ka dai zo ka kwace min student kawai” dariya su kayi.

“Naji conversation inku da Malam but we have to fix time da zamu dinga haduwa muna lesson” godiya na mai bayan yayi fixing time in. Haka kuwa aka yi ya fara koya ma karatu, kai ba ma physics ba kadai duk subject in da na samu matsala sai dai in ban same shi ba. Yana da kokari sosai, don shi ya fara sa min sha’awan yi medicine da gaske a raina. Shi kuma abinda ya faru, school ne gabadaya ya dauka, ana ganin mai Aliyu da mace kullum suna magana. Kafin dai mu yanke ma alakan mu suna su sun yanke mishi. Tun ana fad a makaranta har abun ya fara shiga kaina ya zauna, dake kuma ban manta abinda ya fadu tsakanina da Amir ba sai nake dari dari dashi. Har watarana ya same ni da zancen mai nake gani akan abinda dalibai yan uwan mu ke fada. Kai tsaya nace mishi “jita jita da kananun magangana tunda dai ba wanda muka taba fadawa hakan” tun daga yanayun fuskan shi na gane bai ji dadin amsan nawa ba. Sai dai i’ve had enough from boys da ba zan iya kaea barin wani yayi breaking heart ina so easily ba. Da na maida zancen wasa shi ma sai ya share. A haka na shafe shekara daya da rabi a nana Aisha har dai na shiga SS1 kenan. Lokacin Mai Aliyu har ya gana nana Aysha amma dake a nan fawari yake sai ya zamto muna yaan haduwa daahi. Don har Goggo ta san a matsayin wanda ke koya min karatu. Jika na ma take ce mishi. Ajiddah ko da ta samu kabarin shi, shi din ma supporting tayi tana fadin “To shi wancan banzan Amir in dan ma ya samu kin kula shi? Ai Mai Aliyu ma ya fishi komai Allah” ni dai ban ce mata komai ba haka kuma ban gaya mata akwai wani abu tsakanin mu dashi. Kiri kiri nasan yana sona amma ban bashi fuskan fadan hakan ba, duk lokacin da yayi yunkuri kuma sai in tare. Ina jin wani sa’in Goggo nace mishi mijina, duk dai na gama gane take taken su amma ban shirya kara shan wahalan da na fuskanta a baya ba.

Kwatsam ba sai ciwon kafan Goggo ya taso gadan gadan ba, tun ina yawan shafa mata man zafi har abun ya zo yafi karfin man zafin. Dole sai da aka hada da asibiti, tun tana daurewa taba tafiya har abun ya fara gagara. Wani lokacin kasa zuwa makaranta nake in zauna jinyan ta, saboda dai ciwon kafa dai yace bai san zance ba sam. Kusan sau uku ina raka ta maiduguri muna zuwa ganin likita, sai an dawo an fara samun sauki sai kuma abu ya koma sabo. Ba Goggo kadai ba ni kaina sai da na sha wahaln jinyan nan.

Bayan na gama exams in second term ne muka nufi Maidugurin baki daya da niyyan zaman asibiti a duba kafan da kyau tun da tashi ma yanzun ya gagara. Na sha zama ni kadai inta kuka abu na a bayan idon Goggon. Haka muka dinga zaman asibiti, ni ke kwana da Goggo sai washegari da safe daya daga cikin matan baffan maiduguri tazo da yarta ni kuma in koma gida in huta. Duk da ma ba wani zaman nake ba, ina komawa gidan zan fara kokarin hada mata abinci dan nasan goggo ba abincin kowa ta ke iya ci ba. Hakanan zan koma mu cigaba da zama, abu sai ya fara sauki sai kuma ya kara rincibewa. Ni kaina sai da nayi kusan kwana uku a na samin drip, rayuwa dai ta dawo da rashin dadin ta. Gashi ko a gidan baffan maiduguri ba sa ana daga wanda ya girme ni sai kannen baya na. Matan gidan duka duka uku ne, biyun manya ne suna ganin sun finkarfi na din ko maganan arziki bai hada ni dasu, dayan ko karama ce sosai don ko magana ba gama iyawa tayi ba.

Daga kafan ma ba abu sai ya fara taba wani abun ba, misalin jinin ta na hawa, ga diabetes da take dashi tun tuni sai yanzu ya hade gabadaya yana bata wahala. Ga kuma yawan zafin jiki da cikin ciki. A cikin tsakan jinyan nan aka koma makaranta. Na so a barni inyi zamana na yafe karatun don banga amfanin shi Goggo tana kwance ba amma haka aka tirsasa ni dole na dawo. Wani bakin aikin, gidanmu na sabon fegi aka sake wulla ni. Ba ko kunya Adda falmata ta cigaba da gallaza min azaban da ta saba. Haka kuma dukkan ayyuka su ka maido min dashi, gashi Abbah kocokam yana Maiduguri dake aikin nashi ma wannan karon yana zama a maidugurin ga kuma jinyan Goggo. Sai ya zamto Anty Yana ma yawan ci tana can, mu kadai ne dai a gida. Ko makaranta da kyar nake samun inje, saboda ba ni da kudi wanda aka bamu kuwa Adda ke dannewa. Gashi yanzu ba ta da wani aiki sai zaman hira da samari, yau wannan yazo gobe wancan yazo. Ni ko rana daya da Mai Aliyu yazo mu ka dan gaisa, sai da ta min shegen duka wai da gaske dai na zama yar iska. Ban dai tanka ta ba amma har ga Allah yanzun ban wannan tsoron nata da nake yi da. Danni na ma raina ta yanzun kawai ina kokarin bata gitman tane amma ita sam bata ganin hakan. Duk weekend in dai Abbau yazo ina bin shi maiduguri in gano jikin Goggo dake ma an sallamo ta ba wai don ta warke ba sai dan taki zaman asibitin. Yanzu a a nan gidan Baffan Maiduguri take zama dake babban gida ne sosai.

Kwatsam ranar sai ga Anty Nainerh wai taje Ajeyari bana nan. Nayi farin cikin ganin ta kuwa domin dai an dade ba a haduwa ba. Katin bikin ta ta kawo min, na koyi mata murna sosai. Ko da na mata magana akan ina fatan ta canja ra’ayin ta data taba bani labarin irin zaman auren da tasan zata yi da mijin ta. Murmushi kawai tayi duk dai yanda na so zancen ba tace min komai ba. “Zaki zo ko suhaima?”

“A nan garin za ayi?”

“Daurin aure kawai za ayi a nan ga sai walima, A Abuja za ayi events in yakamata kije pls kanwata” dariya ma ta bani, saboda sanin kaina ne ba wani wanda zia barni zuwa garin Abuja. Balle ma a halin da Goggo take. Excuse na kawo mata da rashin lafiyan Goggo. Ai ko har zuwa tayi ta dauke ni da weekend mu kaje maidugurin dubo ta. Da zamu tafi Adda Falmata na ta sakin habaicin ta sai dai ni kaina nasan Anty Nainerh kaman ba ta da time inta baki daya. Hakanan mu ka isa maiduguri, ai ko Goggo ta ji dain ganin ta gama ita duk wanda ya ke kyautata min tana son shi. Kai ysohuwan nan ta nuna min kauna iya kauna a rayuwata, ba ni da wani abun da zan iya gode mata. Kafin mu tafi ne ta jani gidan su Faree’ah, kaman wancan karon kallo na kawai take tana fadin ‘kina na dai abinki Suhaima ko” dole tasa sai da muka dan yi hira da ita duk da ni ban ma da wani abun fada mata.

Lokacin bikin Anty Nainerh mu ka kara haduwa da ita. Anty Nainerhn tayi farin cikin zuwana, har ankon ta na kawaye sai da ta min. Halimatu dai har yanzun ba mu wani shiri da ita sosai, to dake ma ba wani dadew aka yi ba a na daura aure aka debi amarya da wasu mutane aka nufi garin Abuja. Anty Nainerh ta tafi gidan mininta ni kuma na koma cikin azaba da wahalan gidan mu. Kuma kwatsam ba sai ga yaya baba ya dawo gidan ba. Ina ganin shi nasan bala’i ya afku gashi kuma lokacin ina tsaka da jarabawa. Bai dade da dawowa ba sai ga Anty Yana ita ma ta zo, ko ta ina dai na gane bala’i kawai ke jirana. In dai suka hadu su ukun nan to fa nasan zancen zai lalace.

July

A duk lokacin damuna a jahar yobe, in dai ruwan mai karfi ne, mafi yawancin lokuta hadarin yana hadewa da kura sosai. Kai wani lokacin ma za a gama kuran sosai ya taso da kasa amma kuma ba ayi ruwan saman ba. In abun yayi tsanani motocin da ke kan hanya har parking in dole su ke sai in an fara ruwa su ke samun ganin hanya da za su iya cigaba da tafiya. Bakomai ke sa hakan ba sai yalwataccen yashin da ke garin, har za kaji mutane na fadin akwai inda in har ba safa kasa ba ko takalmi mai tsawo in har zaka yi tafiya kasa, kafafuwan sai sun yi butu butu da kura kafin ka isa inda za ka. Saboda wannan kasan yasa lokuttan sanyi za kaji sanyi yayi yawa sosai, lokuttan zafi ko har ba a magana, rokon mutane yawancin kar azumi ya shigo ruwan sama bai sauko ba, ba karamin wahala ake sha. Anty Amarya ce ta ke fadin tabbas ladan yan garinmu daban da na wasu garuruwan da basa fuskantan zafin har haka. Goggo ko inna kan ce mata “Amarya am abun ba daga nan ya ke ba” saboda wannan zafin ne za kaga da matukar wuya yaro karami ya ce zai yi azumi kaman yanda yan irin Kaduna, kano da Abuja kan yi.

Ganin irin hadarin da ya fara tasowa ne yasa na ke sauri sauri in gama wanke wanken da ke gabana kafin ruwan ya kai da saukowa. Saboda nasan yanzu kura ya maida min aiki na baya, in dai na gama na kulle kitchen in shikenan. Wanki na sha ranar bayan girkin da nayi na rana da na daren da na sauke kafin na hau wanke wanken. Da ke na maida hankali na kocokam kan aiki nan da nan na gama. Na tattare kitchen nayi saurin shiga cikin gida domin in samu inyi wanka. Sai dai me? Ina shiga cikin gidan naji Anty Yana na wakan “wai kun ga hadarin da ke garin nan kuwa, yanzu za a dauke wuta ba battery a lantern gashi ba candle ba ma mosquito coil gabadaya ya kare” wani irin faduwan gaba naji  domin nasan ko min karfin ruwan nan sai na fita na samo abubuwan da ta lissafa in nan.

“Anty Yana aje a siyo mana to” Adda falmata ce ke maganan tana daddana wayan ta. Gaban na ne ya kara fadi sakamakon karan hadarin da aka iya jiyowa tun daga cikin gida. “Sadiya dauko kudi maza a jaka na ki ba Suhaima ta siyo” salin alin naje na dauko hijabi na na amsa kudin na fita. Kuran ne dai ke tashi sosai, ba Wanda kake gani a waje kwata kwata. Runtse ido nayi na fita daga gidan baki na dauke da addu’a. Ina bude idon domin neman hanya tuni kasa ya cika idona ta yanda har ban iya ganin gaba na da kyau. Dole na nemi gefen gidan makotan mu na rabe, da ke akwai rumfa a wurin. Rakubewa nayi ina rawan sanyi har ruwan saman ya karasa saukowa. Ganin haka nayi saurin fita na shiga ruwan nan da gudu na nufi shagon, ruwa ne mai hade da iska sosai irin Wanda ko da lema ka shiga iskan zai dauke leman. Hakan yasa ina gudun amma kaman ban yi sakamakon iskan. Idanuna har rufewa yayi ban ganin gabana amma dan bala’i aka haka na cigaba da gudun nan. Ban sa na ci karo da bishiyan maina sai da naji abu ya takore ni na kasa tafiya, da kyar na iya bude ido naga bishiyan maina a gabana. Wani irin nauyi kaina ya dauka sai a lokacin na gane kenan kaina nane ya bugi itacen. Na kai minti biyar a cikin shock kafin na farga, kara shigewa ciki bishiyan nayi na rufe ido na da ke matukar zafi, duk da ruwa na zuba sosai nasan yafi akan in kara shiga cikin ruwan nan. Ruwan kam an dauke lokaci ana yin shi sai da aka kira sallan magreeba kafin ya dan tsagaita. Duk na jigata, ga ido na da ke faman radadi, ko ban kalli madubi ba nasan suyi ja ga kuma sarawan da kai na keyi.

A haka na nufi shagon da gudu. Duk na jike, har diga nake yi na karasa. Sai dai kash, ina isa shagon na tarar da an kulle. Ma’ana dai sun tafi massallaci. Wuri na samu na rakube ina rawan sanyi da ya gaman shigan ko ina a jikina, ga kayana da su ke jike gabadaya har ta pant in da ke jikina ma a jike ya ke.Rayuwata

Babi na sha uku

Ina wurin har aka idar da sallah, na fara jiyo hayaniya an fito kenan. “Keh lafiya me kike yi a nan wurin a jike?” Rufe idon da nayi ya sa banga mai maganan ba, a hankali na bude su na sauke jajayen idanun nawa a kanshi. Nan take rai na ya baci na ji zuciya na suyi. Duk da na dade ban ganshi ba zan taba iya manta shi ba. Haka kuma ba zan iya taba cin fuskan da ya min ina karamar yarinya. A yanda na ke a lokacin duk mai imani in ya ganni ba zai zageni ba, inma bai ji tausayi na ba baya ci min fuska ba. Duk da halin da nake ciki bai hana na galla mishi harara ba, ina jin tsanan shi na ratsa ni har cikin gangar jiki na. “Me kika zo siyo?” Banza nayi dashi, ko bai ga kallon da na ke aika mishi bane? Ni kam har zuciya wlh na tsani ganin muguwar fuskan shi. saleh mai shago ne ya karaso wurin mu “Wai Suhaima ce a nan cikin ruwan nan kika fito? Me kike so?” Da sauri na fada mishi, kasancewar yawan zuwa shagon shi da nake yasa munyi mugun sabo dashi. In har zanzo shagon shi ko ya rufe sai ya bude ya bani abinda aka aiko ni. Bude shagon yayi ya dauko min abinda na zo siyo, shiko Umar Sanda ganin naki tanka shi yasa ya kama gaban shi ya shiga shagon domin ya siyo abinda ya kawo shi shima. Sai da Saleh ya kulle shagon shi sannan ya kawo min abinda na siyan, nan ya ke fada min shima kulle shagon zai yi saboda wani Sabon hadarin ne ke faman haduwa. Amsa nayi na mai godiya na kama hanya cikin sauri. Hadarin sosai ne, ina shiga layin gidan mu ruwa ya fara saukowa. Layukan garinmu manya layuka ne sosai, gidan farko layin da karshe ba karamin nisa ke tsakanin su, mu kuma tsakiya don haka akwai tafiya sosai. Garin akwai wadatattun filin da layuka su ke da matukar girma ga fadi sosai. Akwai land kam har ba a magana gashi kuma ba mutane dayawa a garin sosai. Ganin ruwan zai fara karfi ya sa na fara gudu in samu in isa, sai dai ina tuni ruwan ya sauko da karfin shi. Ina neman mafaka naga wani mota a gabana na faman min horn. Bazan nayi da motan saboda ban taba ganin ta balle in San mai ita. “Suhaima! Suhaima! Kizo in sauke ki gida” naji ana fada bayan an sauke glass in motan, sai a lokacin nagane Umar Sanda ne a ciki. Ban sa lokacin da na ja tsaki ba, ganin hakan ma na fasa fakewan na sa gudu sosai, har faduwa nayi tayi a hanya ina tashi, da kyar na samu na karasa gida. Ina ganin yazo ya wuce ni na kara yin tsakin. Ina Sallama zan shiga gidan Adda falmata ta zo fita barander mu ka ci karo. Harara ta bini dashi tana tunkude ni “kefa baki da hankali Allah, a haka za ki shiga gidan ki bata mana ko, duk kina diga” tsabagen takaici ban san Sanda na ce mata “to ai ni ke gyarawa ko na bata” kallo na tayi da mamaki kwance a fuskan ta. Ina ga ba ta taba kawo zan iya maids mata magana ba, amma daman ance yau da gobe sai Allah. Hakanan naji har raina banyi na daman abinda na fada ba. “Ke don uwarki ni kike maidawa magana? To ki shiga in gani, shegiya mai bakin hali irin ta uwar ta. Ki shiga mana Wlh sai dai Uwarki ta haifi wata” ban kula ta ba na nemi wuri na zauna abu na, ina ajiyan zuciya don ba karamin wahala na sha ba. Zagin da ta min bai isa ba sai shiga gidan da tayi tana mitan na maida mata magana. Anty Yana ne ta fito tana cewa “ke dallah ni bani aikin da na miki in kingama dama ki kwana a nan. Kuma wlh in battery in nan ya jike sai kin nemo wani wato ke wuyan ki ya isa yanka ko? Kin fara maida wa yayar ki magana ina ga watarana kaina zaki dawo” mika mata nayi ta tafi tana banbami. Ba ta sake dawo ba sai sadiya da ta zo ta kulle kofan da karfi a gabana tayi shigewar ta ciki. Na kai mintu talatin a wurin zaune har na fara gyangyadi sai ga Al-lawan da hijab da zani. Bai ce min komai ba yayi saurin mika min ya wuce side in Ummiy a da Wanda ya zamo nasu a yanzu kaman yanda Umar Sanda ya taba kawo shawara. Daurawa nayi na shanya kayan jiki na sannan na shiga gidan. Adda falmata na waya hakan ya sa ko kallo ban samu ba, da sauri na shiga wanka. Na samu nayi salloli na sannan na bi lafiyan gado. Na san dole zazzabi sai ya kama ni.+

Washegari Sai wurin la’asar na samu aka bar ni tafiya ajeyari dubo su Anty Amarya da kuma Inna, itan ma dai gsky ba yanda take. Zazzabi na nan amma da ke nayi kazar kazar sai bai kwantar dani ba. Ina isa na gaida Inna,  gidan duk sai ya min wani iri dake Govgo bata nan. Dan ma Ajiida na na sai na shiga gidan su muka zanta,  a nan Mai Aliyu yazo ya same ni.

Sai bayan magriba na tafi wurin Anty Amarya, ita ta bani maganin zazzabin da nake jin yana damuna,  ban boye mata komai hakan yasa na fada mata duk abinda ya faru. Fada ta min sosai na shiga ruwan da nayi “ai da fakewa za kiyi har sai an gama ruwan, yanzu da kika kwanta ciwon asaran su ne?”

“Bakomai Anty in ban shigan ba ma wani matsalan ne za ace na Dade, watarana ai sai labari, zai wuce.” Dole ta hakura ta bani magunguna har da na ido, da ke ma nursing school ta ke ta san abubuwa da dama. Sai da nayi bacci sannan na dan warware.

Da ke jarrabawa muke, dole na koma gida a ranar ko dan in wanke uniform ina ma. Washegari kuwa bayan na dawo exams da yamma na samu daman gama aiki da wuri, don haka na shiga na fadawa Anty Yana ina so in je gidan su Adama. Banza tayi dani sai zuwa can na kara mata magana “na hana kine?” Ta fada da dan tsawa, girgiza mata kai nayi nai saurin fita na wuce gidan nasu. Daman tsifa mu kayi da Adama za ta min, muna hira tana min tsifan tana bani lbrn samarin ta. “Ban fada miki yi nayi sabon kamu ba ko? Ke ince sai a dade ba a ganki, kullum ni kenan jelen zuwa gidan Ku”

“Adama kenan yanzu dai  ba nazo yau ba? Ni dai fada min sabon kamun”

“Kan layin nan mu ka hadu dashi naje shago, babba ne fa. Kuma ma har yazo ya gaida Goggo” zaro idanu nayi ina binta da kallo “Adama yanzu aure zakiyi?” Dariya ta kwashe dashi sannan ta girgiza kai “nace mishi sai na gama makaranta ai kuma yace ya amince domin shi ma karatun yake, ke zama fa ki san shi dan abokin su Ya baba ne kuma unguwan nan su ke”

“Ke ko Adama me za kiyi da abokin su Ya baba?”

“To ke ance duka aka taru aka zama daya ne? Mustapha ne fa, massan gidan Bukar mala” ban san lokacin da na mike tsaye ba nace “Massah dai? Ke ko da Adama ya aka yi kika lallashi Goggo ta yarda ki auri kanuri” tabe baki tayi tace “ai har yanzu case in muke, kinsan halin Goggo da yazo gaishe ta faran faran su ka gaisa amma yana tfy ta fara min fadan na kawo mata kanuri, ni kuma ganina nayi ai Yana so na nima kuma ya kwanta min kuma ma maman shi shuwa ce ai. Anty Fanne ai kin san ta”

  Ba ta fuska nayi “Ke ko waye bai san yan gidan bukar mala ba a unguwan nan? Kuma kar ki manta Anty Yana ma shuwa ne su ai duk da cikin kanurai ta taso amma Allah ya gani ban kaunar yarukannan”

“Ehm ehm Suhaima” tayi saurin katse ne “ba fa duka aka taru aka zama daya ba, ita ma Anty Yana saboda wani dalilin ta ne kawai da kuma matsalan da su ke dashi da Ummi amma Allah ya ganar da su gabadaya” bance komai ba sai sallaman sadiya da naji. Kallon sama da kasa ta mun sannan tace “Ya baba na kira” tana fada ta kwasa waje da gudu ba ta kara cewa komai ba.

Tare da Adama mu ka je gidan, Yana falo ran nan a hade kaman na mishi wani mummunan laifi. “Uban waya ce kiyi miyan kubewa bayan kin san banci”

“Yi yi hakuri ban san za ka ka dawo bane” na fada cikin inda inda. Tsaki ya ja sannan yace “na baki 20 minutes ki dafa min wani abu in ya wuce haka zaki Sani” jiki na rawa na nufi kitchen in Adama ta biyo ni tana jan tsaki “Allah Suhaima it high time ki fara karban wa kanki yanci, matsala na da ke tsoro wlh da naci da anga abu. Ke ni fa yanzu ban son ace ina zuba ki ne?” Murmushi nayi mai ciwo “bakomai Adama komai ma mai wucewa ne, ni kuma wani irin wahala, zagi da cin mutunci ne ban gani ba a gidan nan? Duniya ne fa Wanda bai zo ba ma tana jiran shi balle Wanda ke cikin ta” tabe baki tayi tana fadin “kullum zancen ki kenan” haka ta taya ni mu ka dafa jollof in taliya da dankalin turawa. Ba mu gama ba sai da aka kira Magreeb, don haka muna gamawa ta wuce gida. Daman duk nayi abinci dole sai na kai mishi har dakin, yau in ma direct can ta na nufa. Ni a tunani na ma ya tafi sallah ganin an kira magreeba. Amma ina sallama naji yace min shigo. Zaune ya ke abinda shi hankali kwance a falo yana kallon TV. Ban cika son zuwa side in ba saboda yanda ya ke tuna min memories in Ummiy na. Daurewa nayi na karasa na ajiye mai abincin a gaban shi. Wani kallo na ga yana bina dashi, gabadaya kwakwalwa ta taka sa tantance wani irin kallo ne wannan? Koma dai na menene ni kam ya firgita ni. “Iskanci me yasa zaki dafa min taliya?” Wannan karon kam idanunwan shi dukkan jiki na ya ke bi da kallo ko kunya. ajiyewa nayi da sauri na nufi bakin kofa zan fita, naji ya buga min tsawa “Uban wa yace ki tafi?” Jiki na rawa na dawo, a tsaye na tsaya jikina na faman rawa. “Kizo nan” hade rai yayi ganin hakan ya sa na kara matsawa inda ya ke. Ban ankara ba naji ya jawo hijabin da ke jiki na. Abin ya zo min bazata, gabadaya kwakwalwa ta ta cinku she na kasa fahimtar me hakan ke nufi. Ganin ya kusan nasaran raba ni da hijabi na yasa na fara kokarin hana hakan faruwa. Kokawa mu ka fara yi dashi, ban ankara ba naji lafiyayyun mari ta ko ina a fuska na, da karfi ya yaga hijabin ya wulla gefe, gabadaya ya rikide min kaman ba Yaya na dana sani ba? Kai ba ma shi ba kwakwalwa ta ma ta rikide, ta kasa fahimtar menene hakan. Da sauri nayi bakin kofa zan fita ya jawo ni da dukkan karfin sa ya buga kaina a jikin bango. Kara na sa na razana da kuma na ceto naji ya shake wuyana kaman mai neman ciren numfashi. Wasu abubuwan da bakina ba zai iya furta wa ba ya fara kokarin yi min ina fus fusgewa, gashi ya shake min wuya ba daman anji ihun da na ke ta faman afkawa. Idanuna duk sun firfito waje tsabagen tsafin shakan da ya min. Gashi na ya jawo da dukkan kokarin shi ya wulla ni kasa baya na ya bugu da kujere. Ratsanan kara na saki, ko a jikin shi ya bini ya hau danne ya ja kokarin cimman burin shi. Sai dai fisge fisgen da na keyi ya kasa bashi daman hakan. Cikin wani dasheshiyar murya ya fara magana “ke wlh ba ki isa ki hanani abinda na ke muradi ko ki tsaya salin alin ko kuma kici dukkan banza” kara tsorata ni yayi sai dai hakan bai sa na saduda. Kwalban da ke gefen Wanda na ke da tabbacin na giya ne na fara kokarin daukowa zan kwada masa. Gane hakan yayi, saurin da ke yayi yana fadin “ke don uwarki ni za ki bugawa kwalba? Duka ya fara kai min ko ta ina tun ina ihu ina kuka har na kasa tsinana komai. Ganin hakan ya sa ya fara komawa abinda ya ke hari tun farko, duk fisge fisge na wannan karon bai hana shi ba, gab ya ke da cin wa burin shi.

Ban san Sanda wani karfi ya zo min ba na hankade shi ya fadi kasa. ” lafiya, me ke faruwa a nan?” Umar Sanda ya fada tare da karaso wa ciki, ido hudu mu kayi dashi ina kokarin mikewa sai dai na kasa. Wani kallo ya bi Yaya baba dashi. Idanun shi nan ta ke su ka kada su kayi ja, har jijiyoyin kanshi sai da su ka fito. “Adams ashe daman ba ka daina dabbanci nan naka ba? Dan akuyanci ma ka rasa Wanda za ka far ma sai kanwar ka da kuke Uba daya? Ashe rashin hankalin na ka ya      kai nan, amma wlh kayi asaran rayuwa.”

“Faroukh!” Yayi saurin kiran shi “please let this stay between us please” tsaki Umar Sanda ya ja sannan ya maido hankalin shi kai na, numfashi na na ke kokarin saisaitawa, nayi kokarin mikewa gabadaya na kasa, saboda bugun da nayi a baya. Hannu na na kai baya na fara kokarin jan zip ina, na jawo ribbon ina da ke gefe na daure gashi na. Kaman kujeran nayi duk da jirin da azaban da na keji bai hana ni mikewa ba da taimakon kujeran da na kama. Yagegen hijab ina Umar Sanda ya dauko ya mika min, nayi saurin amsa ina dafe bango na sa. Da jajayen idanu da za ka iya hango tashin hankali kwance a ciki yace “Sannu Suhaima bai taba ki ba ko?” Nayi dan mintuna kafin na gano abinda yake nufi. Girgiza mishi kai nayi don ba zan iya magana ba. “Alhamdulillah Allah zai saka miki” ban ce mishi komai ba na cigaba da dafa bango na fita a haka na karasa cikin gidan. Nayi zaton komin rashin imanin mutum ya ga halin da na ke ciki sai ya tausaya min. Ina shiga falon Anty Yana ta kafa min ido “ke fa tsiya ta da ke rashin ji hala laifi kika yi wa baban ya miki wannan bugun?

“Ai Anty Yana tun dazu na ke jin ihun ta ba karamin bugu ya mata, daman duk Wanda yace shi rashin ji zai yi lallai yana tattare fa wahala” Adda Falmata ce tayi maganan. Tsabagen yanda raina bushe, idanuna ma bushe su ke karara sai tashin hankalin da ke cikin su. Wani irin Kallo na ashe baki da hankali nabi Adda falmata tashi sannan naja tsaki nayi daki. Adda falmata ce ta biyo ni tana fadin “dan uwarki ni zaki wa tsaki?” Ko kallo ba ta ishe ni na hau hada kayana Wanda yace daga Goggo ne sai na Abbah. “Ni zaki share ina miki magana?” Hannu ta kai za ta buge ni nayi saurin rike hannun, ko kallon da na mata ne ya tsorata tayi saurin jan hannun ta tana ja baya. “Ban son iskanci shegiya wacce uwarta ta tafi gantali” dariya nayi, a raina nace “ko me zaki fada ki fada amma kin gama buguna a duniya” haka na hada kayana tana ta banbami ta wuce tana fadawa Anty Yana. “Bar ta mana Abban in ya dawo ta mishi bayanin inda ta je. Kila uwar ta ta zata bi” ban tanka ba naja akwati da hijabi a jikina na fita. Ko kudi banda shi na nufi nemen machine. Motan da na shaida ta da na Umar Sanda ne ya tsaya a gabana “ina zaki Suhaima” tabe baki nayi don ko har yanzu bai gama goge laifin da ya min ba, ban son jan maganan don haka nace “ajeyari gidan Goggo”

“Mu je in sauke ki” girgiza kai nayi na juya ina kokarin tare machine. “To ga kudin mota” ko kallon shi banyi ba na hau machine in da ya tsaya a gabana mu ka tafi. Ina sauka na hango  Ajiddah ta fito daga gida, ita na kira ta biya min kudin machine, mu ka shiga gidan tana tmbyn meya faru. Ban ce mata kala ba saboda duk Wanda ya ganni ya san ba lfy ba. Ban shiga wurin Goggo ba sanin halin da ta ke ciki.

Direct side in Anty Amarya na nufa Ajiddah na bina a baya. Muna ido hudu da ita, na rungume ta na fashe da kuka. Ba ta hanani ba, bari na tayi nayi ma ishi domin wanin lokacin ka na bukatan ka fidda damuwan ka ko da ta hanyan kuka ne. Ajiddah ma ba ta bani hakuri saboda zuwa yanzu ta san duk wani abu da ke faruwa a rayuwa ta. Sai da lokacin Sallah yayi na hakura na tashi yin Sallahn, nayi karatun qur’ani. Alhmdlh hakan ya haifa min saukin kunan da na ke ji. Lallaba ni Anty Amarya tayi in ci abincin, duk da Ajiddah ne kwata kwata na kasa cin abun kirki. “Me ya faru Suhaima?”1

Shiru nayi ina tunanin ta ya zan fara sanar da Anty Amarya bakin labarin abinda ya same ni. Shin za ma ta yarda dani? It was so unbelievable! Ganin ta zuba min idanu ya sa na fara magana. Ko da na gama basu lbrn gabadaya fuskar rudani ne kwance akan fuskan su. Ajiyan zuciya Anty Amarya ta saki hade da girgiza “Tura ta kai bango Suhaima, lokaci yayi da dole ki bar gidan mahaifinki tunda har abu ya kai da haka, Wannan wani irin dabbanci ne daga uwar har yaranta. Ya za ayi suna jin ihun ki amma ba su damu su san me ke faruwa ba? Mutanen nan ba su damu da duk abinda zai faru da ke komin tsanin shi kuwa ba zasu ji kan ki ba.” Sabbin hawaye ne su ka taru a idanuwana. Tabbas duk abinda Anty Amarya ta fada gsky ne, shin amman menene mafita? “Ta ya zan cewa Abbah ba zan koma gidan shi ba?”

Ajiddah da idanuwan ta su kada su canja launi ta juyo tana min kallon lfyn ki “Suhaima ki fadawa Abbah abinda ke faruwa kawai shine mafita”

“Karyata ni za suyi Ajiddah”

“Ki fadawa Goggo toh ko sun karyata na tabbatar ba za ta barki ki koma ba in kika nace” Anty Amarya ce tayi maganan. Nan ta ke ko naji zuciya ta ta amince da shawaran ta amma kuma inda gizo ke sakan ta ina zan fara duban Goggon da wannan magana a irin halin nan da take ciki?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *