LABARIN RAYUWATA CHAPTER 8 BY Ayeshay bee
Www.bankinhausanovels.com.ng
A daddafe na daure na ke rubata jarrabawan da duk rubutawa kawai nake. A ranar papern mun na karshe ne muka hadu da mai Aliyu. Don har cikin school yazo ya same ni, yan makaranta na ta gulman su mu kayi kaman bamu ji su bama muka fita abin mu. Yanda muje yi duk ranar da yazo ya same ni a makaranta, direct wucewa muke ya taka min har zuwa kofan gidan Goggo. Yau in ma hakan ne ya kasance, mostly ma labarin School insu ya ke bani dake ya kwana biyu da fara karatu a garin bauchi.+
“Bai in dan amso abu a wurin abokina pls” Ban kawo komai a raina ba na ce mishi “muje mana” Haka mu ka cigaba da tfy, yana ara jana da hira ina dan amsa mishi sama sama dake matsalolin da ke gabana sun fara fin karfin kaina.
A haka har mu ka karasa kofan wani gida mai dan girma. Wayan shi ya ciro ya kira abokin nashi ni dai ina tsaye a gefe ina jiran ya amshi abinda zai amsan mu wuce dake ma duk hanya ne sai dai kuma ba hanyan da muka saba bi ba. “Suhaima mu shiga please, yana so wai ku gaisa da matan shi” bude baki nayi idanuwa na kyar akan shi. “Matar shi? Kana da abokin da yayi aure ne daman?” Dariya ya min yace “lallai ma suhaima wlh kin raina ni. Kuma ma fa mu maza ba wai irin ku bane, saboda mu muna abokantaka har da wadanda suka girme mu, ba kaman ku da kuke ganin shi a matsayin ci baya ba.” Ban ce mishi komai sabida nasan gsky ya ke fada. “To Amma ya akayi ya sanni da har zai hada ni da matar shi ku gaisa” murmushi yayi yace “Suhaima kenan an gaya miki akwai wanda yake tare dani da bai san ki bane?” Ina shirin magana sai ga abokin nashi ya leko. “Mai ku shigo mana ku tsaya nan, ko madam in taka ba ta son shigowa ne?” Saurin sadda kaina kasa nayi, ina mamakin sunan daya kira ni dashi. Nasan maganar soyayya bata taba shiga tsakanina da shi balle har ma a kirani da madam in shi. Fara’an abokin nashi yasa na basar kawai muka gaisa. “Please shigo ku gaisa da madam sai ku tafi mana” wani nauyin shi naji a lokacin, hakan yasa ban iya musu ba na bi bayan su muka shiga har cikin gida.
Sai bayan mun shiga naga girman gidan sosai. Ashe ta waje nema bai nuna wani girma ba.ga kuma space sosai kafin a kara sa cikin main house in. Haka dai na ta bin su har zuwa falon gidan. Iya haduwa wurin nan nayi don har na fara tunanin baban yarinyar wani attajirin mai kudi ne a cikin Damaturu, in ba haka ba irin wannan kaya kan sai dan wane da wane. Muna zaune kusan mintu uku ya shude, sai ga abokin da tray dauke da drinks da cups. “Sorry Suhaima, ta fito wanka ne tana sa kaya bara tazo” ban ce komai ba, banda murmushin da nayi. Motsin da nake ta faman ji ya sa na aminta akwai mutum a cikin. Duk yanda abokin ya matsa ku sha ruwa, kokallon teray in banyi ba. Ina dai zaune a haka dan har na far kosawa. Abokin ya kara fito, wannan karon kala bai ce min ba yayi hanyan kofan waje. “Ni kam mu tfy kawai” na cewa mai Aliyu sai dai banda murmushi ba abinda yayi min. Ina shirin kara magana naji bude kofa, ban juya ba don nasan abokin ne. Sai dai jin karan mutum a kusa dani, ya sani daga kai. Dum! Naji gaba na ya fada a sanadiyan wanda na gani tsaye gabana, Yaya Baba. Har ga Allah ba abinda ya fara zuwa min a kai sai shi inma kila gidan abokin shi ne. Nan take na murtuke fuska saboda na tsanin ganin shi. Dariya yayi ganin reaction ina “an gaya miki zaki taba guje min ne? Lallai baki sanni ba yarinya” ko kafin hankali na ya gama fahimtan abinda ya ke nufi sai jin wani irin nauyi nayi a kaina. Ban san lokacin da na saki wani irin razanannen kara ba saboda bugun wani abu ds ban iya tantance menene ba ya sauka a kaina. Idanu nane su ka fara kokarin lumshewa, yayin da nake iya jiyo sautin muryan maza dayawa a take a kaina sai babbakewa da dariya suke “Yarinya yau kin shigo hannu, irin wannan nama haka?” Ban san wa yayi maganan ba saboda yanda nayi nisa da fara fita daga cikin hayyacina. Da kyar na iya saita idanuna kan Mai Aliyu da naga wanda ya shigo damu gidan yana mika mishi wasu irin makudsn kudi. “Jeka kuma kar in sake inji wani zance kan wannan abun” da kai ya amsa ya mike, sai da yazo fita mu kayi ido huddu dashi. Wani irin kallo naga yana jifa na dashi, ba zan ce kallon menene ba amma dai nasan bana mugubta bane. He looks so helpless a haka ya fita ya barni a wannan wurin daban san me ke shirin faruwa dani ba. Ga wani irin azaban zugi da kaina har ma gabadaya jiki na ya dauka. Kwakwaran motsi na kasa, haka sautin murya na ba abinda ke iya fitowa. Ban kuma fahimtan duk wani abinda suke fada gabadayan su. Kasa fada nayi dasu lokacin da daya ke kokarin yaga kayan jikina, tun ina bige shi da kafana, yana zuba min wata azababbiyar mari na rafke a wurin gashi dama can kaina bai iya motsi. Amma haka na ciga da kokarin hana shi da hannuna, yana jan kaya ina ja. Hauri na yayi a karahe da kafa, a kuma kan cikina dole yasa na kasa komai har ya cin ma burin sa.4
A cikin irin wannan halin mutanen ba tausayi ko wani digon imani su ka fara far min, bansan su nawa bane haka kuma ban san ko har da yaya baban a ciki ba. Tun na farko da ya fara shiga na, na saki wani irin ihun da nasan ba zan kara yin irin shi a rayuwa ta ba. Ba ko alaman tausayi ya cigaba da abinda yake yi, yayyin da nake jin wani irin dimauta, zafi, azaba da tashin hankali na kewaye dukkan ilahirin jiki na. Karan da nake yi yasa su ka kure sautin waka suna cigaba da kwasan dariyan su, daga baya yana sauka wani ya sake hawa kaina. A ranar na san cewa duniyata tazo karshe, amfani na ya gana karewa haka kuma banda sauran utunci a cikin ta. Na sha azaba irin azaban da nake ganin ba wanda ya san ta, a lokacin duniya ta tsaya min. Tun ina kuka da ihu har sautin murya na ya fara gushewa. Sai ya zaman to gani nan ne dai kawai a raye, ba ehmm ba ehk ehm banda hawayen bala’i da ke ta faman bambali daga cikin idanuna. Rounds suka maida abun, sai da suka gama yin yanda za suyi dani sannan su ka kyale ni a jefe a gefe kaman wata tsumma, dai dai lokacin kuma na fara jin kaman abu na shirin gushewa daga jiki na. Don wlh na dauka mutuwa ce tazo min gadan gadan. Tun ina kokarin tsaida numfashi har na gagara, nimfashin kuwa ya tsaye tak.1
Ban san tsawon lokacin da na kai a hakan ba Wai dai saukan ruwan sanyin da naji a jiki na ya sani farkawa a gigice ina kallon mutumin da ya shigo da mu cikin gidan a tsaye a kaina. “Malama kina iya fita? Ina bukatan kulle gidan” sama sama ba ke jin sai dai ko yunkurin mikewa nasan bazan iya ba. Bala’i ya hau yana ta masifa har yana kokarin harbi na da kafa. Dai dai lokacin kuma naji an turo kofan falon da karfin tsiya. Ina iya jin saukan idanuwan mutum a tsaye a kaina. “Meya faru?” Shine abinda na fara jin ya fito saga bakin shi. Dai dai ban iya tantancewa dani yake yi ba koda Wanda ya iske a tsaye a falon yana kokarin harbi na. Haka kuma tsakanin mu ba Wanda ya iya amsa shi.
“Nace me ya faru” cikin tsawa yayi maganan dan ko ni da nake cikin rai ko rashin shi sai da na girgiza. “Wai ka duba mana” dayan ya amsa shi hade da Jan siririn tsaki “Mu za aka ustazancin karya? Da ba a San ungulu ba…” Bai karasa yayi tafiyan shi ya shige hanyan dakin da ya fito.
Rike kai yayi,ya cire glasses in shi ya ajiye gefe. Sai na ga ya sunkuyo ya tsugunna a gabana yana kokarin juyo da fuskana. Ido hudu mu kayi, said lokacin na gane wanene a gabana. “Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un! Adams ya shiga uku, ya tabe kuma ba zai taba gamawa da duniya lafiya ba wlh” nan da nan naga ya rike da, yayin da idanuwan shi kuma suka sauya kala. Jijiyoyin kanshi kam duk sun taso.
Hannun shi ya dora akan goshi na yana sake min kallo, sosai na ke hango tausayi na kwance cikin idanun shi. Tabbas, ba dan waccan karon shi ya kwace ni saga sharrin Yaya baba da wannan karon ma da in amshi taimakon shi gwara in dawwama a cikin halin da nake ciki har mutuwan tazo ta riske ni a wurin. Tun da na Riga na gama Sanin rayuwata ba ta da wani amfani kuma. Bai kara cewa ya mike. Shiga daya data cikin dakunann yayi sai gashi ya fito da dogon Riga da hijabi. Daman kayan da ke jiki na Uniform ne kuma duk sun yayyage ta inda har ana iya hango wani sashi na jiki na. Ni ko duk hakan ma ban jin ya damene. Tun dai mai afkuwa ya afku ai shikenan komai ya zo karshe kuma,don nasan rayuwata ta tsaya cak. Ganin ba yanda zai yi ya sa Mon rigan ya sa ya ajiye kawai ya dauke dogon hijab in nan ya sa ka min. Kaman jaririya haka ya cincibe ni, yayi waje dani. Saukan nan da ya min ya famo min azaban da nake ji ya mamaye a gabadaya ilahirina. Tun ina sakin wahaltaciyyar kara har ban san lokacin da na kara wani suman ba.
Ban kara Sanin komai ba kuma sai tashin da nayi na tsinci kaina kwance a gadon asibiti. Ga drip nan a hannu na, haka kuma azaban da na keji har ya zu bai gama gushewa ba. Gani ma ban yi da kyau, ga dan banzan nauyin da nake ji kaina ya min. Kokarin daga shi kadan, sai inji kaman dutse aka dauko a ka dasa min a kan.
“Sannu me ke miki ciwo?” Sai lokacin na gane akwai mutum a dakin, taso yayi dagabinda yake zaune, idanuwan shi sunyi ja jawur har yanzu. “Dan Allah ka fidda ni da garin nan” shine abinda ya fara fitowa baki na.
Da tausayi fall idanun shi ya ke kallona, ban san abinda yake ji ba amma nasan abun ba karamin zafi ya ke mishi ba.
“Kiyi hakuri Dan Allah Suhaima, let me follow the appropriate way in kwata miki duk wani yancin da kike bukata. It won’t go free, wannan alkawari na miki. Dukkan tsanani da rashin hankali sai na kwato miki yancin ki”
Runtse idanuna nayi yayin da hawaye yayi saurin fitowa ta cikin idon. Tabbas na Riga da nasan na shiga tashinnhankalin da nasan bai da karshe. An riga an cuceni iyakan rayuwata na duniya.
“Daga yanayin ki kadai Suhaima nasan kina jin dacin da rayuwa ta yi miki. Nasan kina jin da man baki zo duniya ba. Tabbas, abun nan da ciwo irin Wanda ba zan iya misalta shi ba saboda ban san ya hakan yake ba. Amma let us do the right thing” a hankali na bude idanuna ina kallon shi, yayin da zuciya ta ta fara kitso min shin me ye sa Umae sanda ke taimako na a halin yanzun bayan nasan yana daya daga cikin manyan makiyana a da.
“A yayin da kunci, bakin ciki da kuna suka kasance abokan zaman ka.
A lokacin da jigo majigina ya bace ma.
A sanda mahimmanci, natsuwa da annashuwa ya kau
Rayuwa ta zama tamkar guba a gare ka.
komai ya zama tamkar dafi da daci a wurin ka.
Sanadiyyar gushewar Uwa, Mahaifiya a rayuwar ka.” Magana nake ina jin zafin na Dada karuwa a raina haka kuma ina kara jin a raina komai ke faruwana dani mahaifiyar tace ta na min, domin ita ta bada lasisin abinda ke faruwa. “Tun bayan gushwan ta, banda komai kuma mai ma’ana illa mini da ke ratsa rayuwata a ko wani irin hali. Ni kam na gaji, ina ma haka CeCe ni ba, ka barni da team tsan wahala na, kila da na rasa rayuwan gabadaya, ni na huta wadanda su ke burin ganin gushewa ta su huta suma”
“Subhanallah!” Saurin taron numfashi na yayi, yanzu kam ba shakka kwalla ne ke tsiyaya daga idanuwan sa. “Kar ki fadi haka Dan Allah, ki duba rahaman da Ubangiji ya miki Wanda wasu ma basu samu irin shi ba. Suhaima, nima na rasa mahaifiya ta tun ina dan kankani, na taso cikin rashin gata sai dai ba kaman irin naki ba saboda ba Wanda ya tsunguma min amma kuma bani Wanda ya damj da tawa rayuwan. Hakan ya sani kwace hanya, har na fara rashin ji kala kala duk unguwa ya dauke da irin mugun hali na. Nina fara koya ma Adams shaye shaye, wannan yana daya daga cikin dalilan da yasa ni din ban iya barin shi ba bayan ya zama abinda kike gani a yanzun. Sai dai ance dalibi ya kan koya ma yafi malamin, hakan kuwa ya kasance tsakanina da Adams. I used to have a messed up life, a lokacin kowa ya guje ni hatta Anty Yana kyarata take yi sai mahaifiyar ki kawai ke kokarin kira na tana min nasiha at the same time tana kyautata min. Rashin hankali na a lokacin sai ya bani cewa dan aiken da taga tana min yasa take kira na da sunan nasiha, sai na dauke ta a matsayin wanda ya takura min shi yasa lokacin da aka ce ta tafi nake farin ciki, ko bakomai ba wanda zai dinga min fada. Recently, da na koma gun mahaifiyata da zama, da addu’a da daura ni kan hanya na gano hanya mai kyau. Hakan yasa na gane kaina sannan na kuma gane na miki babban laifi a wancan lokacin, ina fatan zaki yafe min?” Kasa amsa shi nayi, ina mamakin lbrn da ya bani wanda ba ko shakka nasan hakan ne.
“Su waye ne?” Abinda na fada kawai kenan ya gane me nake nufi. “Kungiya gare su, da nima ina ciki saboda a lokacin ma ba wanda ya kai ni kaurin suna cikin su. Duk wadanda kika gani yaran masu kudi na a garin nan sosai hakan yasa Duke da daman yin iskancin su son ransu. Sun sha kawo mata suna raping, sai dai kuwa in ba a kyallo ki ba. Ke ma ai tunda suka ga kin fara mutunci da Mai Aliyu su ka fara bibiyan shi. Iyayen shi ba wasu masu shi bane, duk kokarin shi bai da hanyan zuwa jami’a ga kuma mahaifiyar shi kwance rai hannun Allah ba kudin asibiti. Da wannan su kayi amfani da, gabadaya ma su su kayi sponsoring karatun shi haka kuma suka biyawa mahaifiyar shi kudin aiki ta warke. All because daya daga cikin su ya ganki da yake wurin Adams kuma kin biya mishi rai. Ba dan nan garin bane ma, shi ma baban shi babban kusa ne a garin kano.”
Wani irin rudu na kuma shiga jin labarin da yake bani kama shirin film ko tatsuniya. “Amma me yasa shi da kanshi yayi attempting far min?”
“Its all a plan Suhaima, shi wancan in yana daki yana jiran bayan komai ya kan kama yazo. Baki ban daman da zan iya miki magana ba ni kuma ban san in ta bibiyan ki. And don’t think am so innocent, kaman yanda na gaya miki dani aka fara abun nan. I was the first guy da na fara raping daya daga cikin yan matan ba a nan garin ba a kano. Suna hude kungiya ne garin gari suna rabawa matasa kudi dominsu yada manufar su. Sai dai tun abinda ya faru tsakanina da yarinyar nan, naji rayuwata ta dimauce, na natsuwa duk wani tunanin na ya kau. A kullum duniya in na kwanta sai nayi mafarkin yarinyar nan tana min ihu in kyale ta. A haka abun ya fara yawo har ya dawo banda wani tunanin kirki kuma. Dole naje na nemo ta bayan dimbin wahalan da na sha da kyar na same ta. Sam taki ta yafe min duk yanda na nuna mata Dana Sanin sai dai ta sanar min yanzu haka an FASA auren ta saboda abinda na mata. Ta hadani da yan unguwan su, su ka min wani irin duka da zai da na kwana asibiti. Bayan nan aka wuce dani cell, ba karamin wuya na sha duk da haka ji make nayi deserving komai. Ban san ya akayi ba, daga baya yarinyar tazo tace ta yafe min. Ko da na nuna zan aure ta, sai ta sanar min an sa mata rana da cousin inta. It a life changing experience tunda daga lokacin na dawo turban gsky. Sai suka watsar dani duk da haka ban damu ba, haka kuma yanzun ma sun kira ni ne saboda in ga sun ci manufar dana hana su da farko. ” wani irin zufa naji yana keto min a lokacin, da kyar na iya tashi daga kan gadon ko kafin ya ankara ma fisge drip in dake hannu na. “Dan Allah ka fidda ni garin nan. Wlh na tsani in bude ido in mini ina shakan numfashi a cikin ta. Duk da gari nane kuwa”
“Ina zamu je Suhaima? Dole mu tsaya ma a nemo miki yancin ki” girgiza kai nayi na dan cike baki “Baban ka na wani bane a garin nan haka kuma kaima nasan haka da abinda za ka iya jayayya da yayan attajirai irin su. Allah ya isa, Allah ya isa, Allah ya isa.” Ina gama fadin hakan nace “Kai ni Maiduguri, Goggo na can ba lafiya” bai kara cewa komai ba sai wani irin sanyi da jikin shi yayi.
A motan shi mu ka tafi har garin Maiduguri. Ya kaini har cikin gidan Baffah. Hatta kafa na ma da kyar na ke taka ta, ga magunguna kala kala daya hada ni dasu. “Ki kulla da kanki Dam Allah Suhaima, da kuma dukkan abinda nurse in nan tace miki. Bakomai, Allah na nan sannan ina so ki cire damun da nake ganin kin sa kanki a ciki”+
“Damuwa dole ne? Duka duka shekaru na nawa ne a duniya? Amma kasan abubuwan da na fuskanta wani tsohin ma har ya gama rayuwan shi ba zai taba ganin irin su ba” Hawaye shara shara ke zuba a idanuna yayin da na ke magana “Ballantana kuma yanzu da gabadaya rayuwan tawa ma bata da amfani?” Da rudu sosai a fuskan shi ya ke kallona “Ba zan ce kiyi hakuri ba suhaima saboda ina jin baki cancanci wannan kalma ba. Ba a wurina kadai ba, har a wurin kowa ma. Abinda zan ce miki kawai kuma shine, Allah na nan kuma ya san dake” yana fadin haka ya shiga mota yana kokarin tayarwa. Da kyar na iya tsaida shi “Ka gaida Goggo Dan Allah” Hakanan ya bini a baya har zuwa dakin da take zaune. Ina ganin ta na ruga da guda na duk da ciwon da kafafu na keyi, na shige jikin ta. Sai da kuma na shige jikin nata na ji alamun ba karamin ramewa tayi ba. Rudewa nayi in tmbyn ta ba’asi, ba ta amsa ni ba sai datijjuwan matan da ke dakin wacce na gane an kawo tane saboda ta kula da Goggon. “Au Goggona zo da bako bara ya shigo ya gaishe ki”
“Siriki kika kawo min?” Abinda ya fara fitowa bakin ta kenan. Sai da na danyi dariya sannan nace “Aa dan layin mu ne a sabon fegi” ba dai tace komai ba, har Ummar sanda ya shigo su ka gaisa. Har kyautan kudi kuwa ya mata sannan ya fita. Goggo ko taji dadi, dan ita ba dai son mutum mai kyuta ba saboda ita ma gwanace wurin kyautan. Tayi ta sa mishi albarka, sai ce min tayi “Ba zaki je ki raka shi ba?” Ban ce komai ba, haka kuma ban fitan ba har naji tashin motan shi ya wuce. Daganan kullum Goggo sai ta tmbyni gane dashi, ni kam share ta nake yi na kauda zancen. Dan nasan ba wani abinda zai iya taba shiga tsakaninmu dashi a wannan lokacin.
Ba laifi duk da ana yawan zuwa asibiti amma jikin nata yana dan sauki, Alhmdlh. nima naji sauki, saboda duk maganin da aka bani sai da na shanye haka na dinga gasa kaina ina kuka ina zuba Allah ya isa, don har duniya ta kare ban jin zan taba iya yafe ma wadanda suka min wannan abun. Musamman Yaya Baba dashi ne silan komai. In sha Allahu nasan sai sin ga karahen su tun a duniya ma.
Sanda aka koma makaranta ba karmin Dramamu kayi da Abbah ba. Duk dagewan shi, na nuna mishi da in koma Nana Aisha na gwammace in mutu banyi makaranta ba. Goggo ne ta tilasta shi, dole aka siyan min foam in El-kanemi Maiduguri. Haka kuma na fara rayuwa ta a garin Maiduguri, Borno wato birnin Yarwa. Ba laifi rayuwa gidan ya fi na gidan mn sau dubu duk da ko na san saboda Goggo ne abubuwan suka zo min da sauki, to gashi itama fama take. Rayuwa dai gatanan kawai ne, yau dadi gobe akasin ta. Ban wani samun matsala a makaranta saboda ina jin cewa banda matsalan ind dai ta fannin karatu ne. Ga kuwa dalibai masu kwazo ne sosai aka tattara a makarantan. Haka kuwa muke fafatawa son duk da abinda Mai Aliyu yayi sanadi na katse min dukkan wani mahimmancin rayuwa. Ban jin zan iya hakura da karatun likitanci, ko dan ceton mutane dayawa daga cututuka da kuma taimakon Al’umma musulmi.
Wataranar Asabar aka wayi gari da bakin ciki hade da jimamin babban rashin da aka yi na Inna, abokiyar zamn Goggo kuma mahaifiyar mijin Aunty Amarya. To lamarin Ubangiji kenan, duk da tana fama ita ma dajiki wanda tsufa ne ya jawao amma ko kusa ba za a hada ta da abinda Goggo ke ji. Amma da ke lokaci yayi, ko ba ciwon tafoya za ayi. Goggon kuwa ta ji mutuwan sosai. Musamman su mutanen da, duk da ba za ace ba a taba samun sabani ba, amma kuma anyi zaman mutunci. Duk da ciwon kafan ta hakanan ta sa su Abba da Baffah a gaba sai da suka hakura suka kaita Damaturun. Har aka yi zaman gaisuwan kwana uku, sai daida ka ganta kasn abun yana damun ta sosai, karshe dai ciwo ya tashi gadan gadan kuma shi yayi sanadiyyan komawan mu Borno ba shiri. Abinda ake gudu kam hakanan sai da ya faru. Wannan lokacin ma ba karamin jinya tayi a asibiti ba, da ka ganta kasan tan jin jiki. Ni kam duk lokacin da tayi irin wannan ciwonba karamin damuwa nake ba, kai hatta yanayi na bai boye hakan har wani irin rama na daban nake. Na riga na san ita ce gata na a duniyan nan, kuma raahin ta ba karamin girgiza ni zai yi ba. Sai dai alamu na yawan nuna ban da wani zabi a rayuwa kuwa.
Tun bayan tafiya Umar Sanda bai kara waiwayo ni ba sai bayan shekara daya. Lokacin already na riga na shiga SS3. Kawai sai dawowa makaranta nayi na iske shi suna ta hira da Goggo. Da ke jikin kwana biyu ya mata sauki. Ni da farko ma ban gane shi ba sai da na matso kusa sosai. Ya kara fari sosai sai kace wani balarabe ga kuma wani irin kasumba da duk ya cika mishi fuska.
“Baki gane shi ba halan?” Goggo ta fada. Murmushi kawai na mata, daga yanayun muryan shi ne ma ya sa na gane shi da kuma kamannin shi da bai gama bacewa ba. Gaishe shi nayi, ya amsa cikin fara’a. Daga nan na basu wuri da Goggo su ka cigaba da hiran. Sai da yazo tafiya ta sani raka shi. “Ko ki zauna muyi hira” ya fada bayan na taka mishi wurin motan shi. “Ai naga kuna yi da Goggo.” Dariya ya dan yi sannan yace min “Da fatan kina lfy dai ko? Kwana dayawa”
“Alhamdulillah” kawai nace mishi, a raina kuwa ban daina mamakin har irin kiban da ya kara ba. Ni dai ganin nan a yar figigiya ta har yanzu.
“Sorry tun da muka rabu dake ban kasan ne shiyasa ban zo na duba ki ba” ya fada yana kokarin bude motan.
“Lah bakomai, karatu kaje hala” bai amsa ba sai ma ce min yayi “Ya makaranta Suhaima, hope dai komai yana tafiya lafiya ko? Baki da wata matsala?” Da kai na amsa mishi, a raina kuwa ina mamakin mai yasa ya damu da rayuwata. In fact ni tun bayan wancan abun ma ban taba tunanin wai zai kara dawowa wuri na ba. Kallo na ya juyo yana yi sosai kaman mai son fahimtan wani abu a fuskana. Ban san me ya gano ba naji dai yace “Dan Allah ki dinga fawwala wa Ubangiji dukkan lamarin ki Suhaima, Allah ya shige mana gaba. Bara naje kinsan garin naku is not zafe, mutum yayi dare sai kiga yaran can su tare hanyan azo a samu matsala” Yana nufi Boko haram, saboda zuwa lokacin ta’addancin da suka yi a garin Maiduguri har ya baci. Infact har ya ma shiga garin Yobe. Sai dai dake Unguwan su Baffah unguwa manya manya wadanda su ke ji dasu ne. A ta nan wurin gidan yake hakan yasa tarzoman bai ciki ketarowa ta wurin ba. Sai dai kuma zaman kullum ciki fargaba ake, ba daman fita ko makaranta a rufe a bude haka ake yi.
Shi ga motan yayi, Babban leda ya ciro ya miko min “Ga tsaraban Cairo, zan kira ki na wuce” amsa kawai nayi ina kallon ledan ina kallon shi. Sai dai tun kan na samu daman mishi godiya. Yayi saurin jan motan shi ya bar wurin, Allah kenan, abun godiya.
Ko da na shiga gida kuwa banyi wata wata ba na bude ledan. Kayan da na gani a ciki ya sani daukowa da mamaki ina dubawa. Abaya na har guda biyu da veils insu peach da black. Nayi mintuna ina mamakin wannan irin kaya haka, tunda dai ba wannan sabin a tsakaninmu da zai kawo min irin wannan abu. Bayan kayan kuwa, sai wani perfume na larabawa mai dan banzan kamshi sai kuwa yar karaman waya. Na dade a raina ina tunanin dalilin da zai sa ya kawo min irin wannan kyautan. Rudewa nayi, dile na dauke su naje na nuna ma Goggo.
Dariya ma tayi ita kam. Tace “wannan ba dan gidan Umaru Machina bane?” Da kai na amsa ta, tace “to ina ce makocin ku ne daman, dan ya miki kyauta kuma sai ki dinga wani mamaki?” Shiru nayi, dan dai a raina ban yadda da wannan dalilin zai sa ya kawo min kayan nan ba. Musamman da nasan ba wani jituwa mu keyi dashi ba, duk da yanzu ya min abinda bazan taba iya mantawa a rayuwa ta ba. Hakika shi din ya kasance mai tausayi, ban shakkan wannan.
Bayan kusan sati biyu, Hakanan na hada wayan daya kawo min duk da dai nasan ba wanda zan kira ko kuma wani ya kira ni. Banda yan danne danne da rage ma kai kewa ba abinda nake yi a wayan sai ko game amma ko app daya na social media ban sauke ba. Ranar da naji wayan yana ringing, banbarakwai naji abun don ni ko ringing tune in wayan ban san shi ba. Kallon wayan kawai nake ina mamakin numban da ya fito baro baro. “Ki dauki waya mana ana kiran ki” Tsohuwar da ke zama da goggo ta fada. Hakanan dai na daure na dau wayan ganin tana kallo na. Hae na amsa sallaman da akayi ban gane waye bane. Sai da naji yace “Sai yau aka kunna wayan kenan?” A daburce na gaishe shi sannan nace “Ban zauna bane saboda school, kuma ma ni banda wanda zan kira ko a kira ni.”
“Baki da kawaye ne?” Girgiza kai nayi kaman yana kallo na “Ina dasu kawai dai bama magana a waya ne”
“Yakamata ko a dinga gaisawa, Kinga yanzu sai ki amshi numban su. amma dai kar ki kashe wayan, ko su basu kira ki ba ni zan kira ki mu gaisa ai ko?” Shiru nayi, ina neman inda zan ajiye maganar shi.
“Ko baki son in dinga kiran ki?” Ya sake tambaya.
Da sauri nace mishi “Aa”
“To ya jikin Goggo” Brief gaisawa mu kayi kafin ya ajiye wayan. Tun daga nan ya kan kira ni amma dai ba kullum, wani lokaci har wurin bayan kwana uku ma. Sai dai yana yawan tmbyna ko akwai wani abu da nake bukata. Akwai ranar da yayi min irin wannan tmbyn sai kawai nace mishi “Ina son Dan Allah a samo min numban Adama kawata ta layin mu”
“Amma gsky baki da kirki Suhaima, ashe ba kwa ko waya?” Kokarin fara kare kaina nayi yace “Aa fa baki da gsky, ko ince dukkan mu baku kyauta ba. Amma shikenan tunda yanzu kin nema, In Sha Allahu za a samo miki”
Ranar da dare kuwa sai ga text in numban ta ya shigo. Da azama na, na dana mata kira. Aikuwa sai ta dauka.
“Suhaiiima” abinda ta fara fada kenan da dan ihun ta.
“Ya akayi kika san nine?” Tsaki taja tace “Dazu Fa Ya Sanda yazo da kanshi wai yana nema na. Ni abun mamaki ya bani sosai wlh, kin fa san shi ba cika shiga harkan mutane yayi ba tunda ya bar zama a garin nan sosai. Gaizuwan mutanema ba lallai ya ke amsawa ba. Sai da na fita yake ce min, wai ke kike son numbana. Ke Allah baki na kasa rufuwa yayi Suhaima, me ke tsakanin ku wai?”
Dariya nayi jin yanda ra dage tana ta min bayani “Kawai dai mutunci mu ke, kinsan kwanaki shi ya kaini Maid shknn tun daga nan mu ke dan mutunci dashi amma fa ba ma wani sosai bane.” Siririn dariya tayi, tace min “Dadi na dake rainin wayau, dan mutunci ne har zai zo ya amsan miki numbana. Shikenan kar ki fada, in yayi tsami maji ai” Kyale ta nayi, dan nasan halin ta sarai komai na fada mata ba yarda za tayi ba daman.
“Ya labarin Saurayin mu? Ko ansa ranar ne?”
“Ke shirya dai kizo, ana gama makaranta da wata daya aka sa.” Tab, wayaga Adama da miji. Lallai zai sha zuciya.
“Zan zo mana ai dole na ma, Kince mun kusa shiga daga ciki muma” dariya tayi sosai tace “ke dai kika sani Allah. Kuma ranar da aka yi graduation inku, washegari ki tabbatar kin kamo hanyan Damaturu daman” Da eh kawai na amsa mata, dan nasan in naki yarda ma yanzu sai muyi fada. Mun dade muna hira da ita, wanda duka duk maganan aurwn nata ne.
To bayan ta kuna sai Ajiddah da ita kam daman tun a wayan Goggo tana kira na, amma da yake tana makarantan kwana sai ta samo waya sannan take iya kira na. Akwai dai amana sosai, saboda har yanzu muna nan da ita yanda mu ka saba.
Rayuwa ta cigaba da tagoya ba tare da wani canji sosai ba. Kullum dai da irin yanda za tq zo ma dan adam. Umar Sanda ya dade da komawa Egypt, tun da ya tafi ko ya kan dade bai kira ni ba. Amma ranar da na fara ganin international number nasan shi ke kira. Har yanzu dai gaisawa kawai muke yi, sai labarai da ya kan kawo min daya biyu.
“Ya Cairo?” Dan jim yayi kafin yace “Gamu nan dai a cikin ta, Ya kamata watarana kizo ki dana kema ai”
“Ni kuma me zai kawo ni Cairo? Ya Sanda” zaro idanu nayi alamun ba zai yiwu ba, duk da ko ba gajina yake yi ba.
“Kika san ikon Allah? Ai ba yanda Allah bai lamarin shi. Ni ba gani nazo ba yanzun. Sannan kuma ki daina kira na da Sanda, shebi na sha gaya miki ban so”
Kiris ya rage ince mishi, ai kai dan gata ne. Duk da baban shi ba wani mugun attajiri bane amma akwai rufin asiri sosai gsky. Amma maman shi na sha jin labarin wanda ta aura a kanon bayan ta fita daga gidan baban shi, ba karamin mai kudi bane domin a garin kano ma duk girman shi sai da aka san dashi. Daman gata shuwa, kyakyawa don har tafi su Ajiddah kyau, sosai. Da yawan mutane sun ce ya dauko tane musamman a fata da kuma yanayin su baki daya.
“In sha Allah ba zan kara ba, kayi hakuri” na fada cikin saukakan murya, ba tun yau ba ya sha sanar min bai son sunan. Daman baban shi ke kiran shi saboda sunan asalin mai sunan shi kenan. Umaru Sanda, kawai sai kowa ya dauka amma tun da can bai cika yarda ya masa ba, musamman ma abokanan shi bai bari su kira shi da hakan. Sai dai kaji ana Umar Faroukh, ko kuma ma UF, using the initials kawai. Da ke baban nashi ma Umar in sunan shi.
“Ai ke ba kya laifi a guri na, you don’t have to apologise ma, kawai ban sin sunan ne” Ba abinda ya fadan bane yayi saurin daure min kai sai irin tune in da yayi amfani dashi wurin fadin. Ba wai yau ya fara ba, amma duk randa yayin sai abun ya zo min wani banbarakwai. Ni fa, ko wayan da muke yi da kyar na saba na dan saki jiki don har yanzu ban gama zama comfortable ba ma.
A haka mu kayi Sallama, sai dai abinda na fara lura dashi kwanan nan hiran namu ya fara yawa. Don wataran hakanan zai kirani ya fara ban labarin abinda ya faru dashi a ranar. Ni dai mamaki na nan dan kare a raina.
Ko da muka gama jarrabawan mu na SS3 baki daya, ban yi wani farin ciki ba kaman sauran yan ajin mu. Savodani kam banga miye na murnar ba, ni dai har yanzun rayuwata jiya i zuwa yau ne, ba wani dadin ta na ke ji. Kai rabo na da dandana wani dadi ma, ina ga tun ranar da Ummi na ta tsallake jiki ta barni cikin kangin Wahala. Duk da na rabu dasu amma ban taba iya manta azaban da na sha hanun bayin Allahn nan. Yaya baba kam, har abada ban jin zan iya yafe mai. Ya riga da ya cuce ni, cuta irin wanda zai bini har karahen rayuwata. Sai dai kuma ina tunanin tun yanzu a duniya ya fara ganin sakayyan Ubangiji. Domin dai karatyn da yake yi ma, tuntuni yaki gamu wa. Ya bar Buk tuntuni yayi Bauchi amma duk bai dade ba ya kara dawo wa gida anyi withdrawing in shi. Sai Yayi Yobe state uni shi inma dai hakan ce ta sake faruwa. Yanzu dai yana poly, amma batun natsuwa babu shi. Yana nan yana ta watingiri, sai arziki shaye shaye fa bin gindin yaran masu kudi yana musu fadanci. Sakayyan duniya dai, ita kan ta Anty Yana ta na gurban shukan ta yanzu. Adda Falmata kuwa, Nursing ta jona bayan secondary. Sai da tazo jarabawan karahe sannan aka zubar harda su a ciki. Taga takaici kam, yanzu dole ta koma State University nan cikin Damaturu ta fara daga farko. Batun aure kam shiru kawai kake ji, ban san jo ta na da samarin a yanzu ba hsky. Amma tub da nake gidan kam nasan suna nan buhu buhu, ina mamakin dalilin rashin auren nata kuwa. Al-lawan ne dai yake Karatu lafiya kalau a Gombe, state university. Ya kan dan kira Goggo shi kam, kuma muna gaisawa dashi ba laifi, lafiya kalau zamu yi ta hira in dai ya kira tan kenan.
Ba a dade da gama jarrabawan ba Adama ta fara min maganar zuwa Damaturu bayan bikin sauran kusan wata da kwanaki. Fir naki zancen, duk da fushin da tayi tayi. Daga karahe dai, sai gata a maidugurin ita da Goggon ta. Na ko ji dadin ganin su, ballantana goggo da na dade ban gani ba. Ganin su yasa Goggo cewa ai ko dole na in tafi, sai dai Adama tayi hakuri sai ana sauran two weeks bikin tukunna.Sauka na garin Damaturu, ji nayi kaman an sauke min garwashi a cikin zuciyana. Saboda wani irin azababbiyar tafasan da ya fara. Zafi na keji sosai yayin da fabadaya jiki na ya dau rawa. To avoid complication, na dau jiki sai Ajeyari duk can inma a yanzu ya zame min tamkar kabari ne duk da ko ban taba shiga a ciki ba. Har yau na kasa sanar ma Anty amarya dalilin da yasa ranar da muka gama jarrabawa a Nana Aisha na tafi maiduguri ba tare da na dawo gidan ba.+
Tayi farin cikin ganina sosai. Baiwar Allah, duk girman gidan nan yanzu ita kadai ce a ciki. Sai yayi wani iri, duk ba dadi. Sai dai itan ma ta sanar min kwanan za su koma garin Bauchi. Anyu ma mijin ta transfer. Adama da ke ta faman jira na da taji cewa Ajeyari nayi, tayi ta bala’i tana hawa tana sauko karshe dai ta kule kaman yanda ta saba. Ban biye mata ba saboda nasan ina komawa gidan zamu shirya da ita.
Hakan ko ya faru, kwana na biyu a ajeyari na nufi sabon fegi. Duk da nasan ba gidan mu zanje amma kuma na kasa boye damuwan da ke mamaye a zuciya ta. Hakan nan dai na karasa, ko kallon hanyan gidan mu ban ba na wuce gidan su Adama. Na iske ma bata nan, mijin ya zo ya dauke ta sun tafi asibiti test wai. Goggo tayi farin ciki ganina sosai, ni ma kuma naji dadin ganin tan. Don duk mutumin da ya nuna min so, banji Ina da kaman shi kuma. Tarba na mutunci da karramawa aka min a gidan, ba laifi yan biki yan nesa har sun fara zuwa. Daman kuma nasan wasu daga cikin dangin nasu, musamman yan uwan Goggo da suke yan kollere. Duk da ba su da danganta ka, to amma zaman tare ya hada su da su Ummi na. Ballantana wasun ma da aure ya hada. Na dan yi mamakin farin cikin gani na dasu kayi. Ji kake ana “Ai yar gidan Aeeyn Aminaa ne” tuni na sake a cikin su, sai ma na hau taya su dan aike aiken da suke. A haka Adama ta dawo ta sameni. Ba ta ma san nazo gidan ba, sai gani na tayi kawai bakin famfo ina karasa wanke wurin da aka gama wanke wanke. Da farko harara ta bi ni dashi. Can kuma ko kasa basar da ni tayi, sai kuma tazo da gudu ta rungumeni tana dariya tana turo baki.
“To ai sai ki sake ta hakan nan ko, ko sai kin karya ta” Turo baki Adama ta sake yi jin yanda Goggo ta hau sababi. “Ke ko baki da kirki Allah” dariya na danyi, ganin sabon hararan da take min. “Yanzu dai ai nazo shknn” Hannu ta fara ja tana kokarin nufan kofan gidan. Da sauri na fincike hannun “Baiwar Allah lfy?”
“Dallah can zamu je ku gaisa da shi ne” Sarai na gane abinda ta ke nufi barin ma yanda ta sunkuyar da kai wai ita a dole kunya. “Waye shi?” Na fuske na fada, ai kuwa sai da na sha hara wannan karon ma har da Karin tsaki “Ke fa baki da mutunci ko?” Dariya nayi “Ai kya bari in dauko hijab ko? Ko haka kike so inje ba ko dankwalin arziki” itan ma sai lokacin ta fahimci hakan. Tilas ta sake ni na dauko Hijab sannan muka nufi wajen, Inda ya ke jiran ta a motan shi. Ai ko yana ganin ya fito, yana dan kara fara’an da already yake kwance a fuskan shi. Gaishe shi nayi, bai amsa ba yace “Maraba da babban kawar mu” Dan dukar da kai nayi, Ina mai cike da murmushi.
“Ya makaranta” ya bukata, a daddafe mu ka gaisa har yana tsokana na wai yayi fushi na bar mishi amaryar shi ita kadai. A gsky Adama tayi dacen miji, sai yanzu na fuskanci sanin da na mishi da muna yara ba wani na arziki bane. Ko da yake ma, tunda na gane Ya baba na cikin su, na tsani duk wata mu’amala dasu.
“Ya abokina kuma?” Da mamaki na dago kaina ina duban shi, don har ga Allah ban wani fuskanci inda zancen nashi ya nufa ba ma. Murmushi yayi fuskantan yanayin da na shiga “Ko baki San fada min? Ke fa yanzu kawar mu ce kuma muna fatan abin ma yafi haka soon, ko kuwa amaryata?” Dariya Adama tayi, hakan yasa na kalle ta cike da tuhuma. Sai dai na fuskanci itan ma kwata kwata ba wai tasan me yake nufi bane.
Karar wayar shi ce tasa na katse tunanin da nake “Mutanen Cairo, yanzu ko nake maganar ka ai” ban ji bai aka fada a wayan ba sai naji Mustaphan ya sake fadin “Dagaske gani ga mutuniyar ka ma ai” Tab! Sai lokacin kwakwalwata ta kawo min me yake nufi, Umar Sanda ne kenan? Tabbas shi dinne ma. Sai yanzu na tuna shi din ma abokin shi ne sosai ma kuwa. Kallon tuhuma Adama ta bini dashi, nayi saurin fahimtar da ita ban San komai a kai ba ma ta idanu. Ba dai ta gamsu ba amma.
Bai dade yana wayan ba ya gama “To ke kinji ance in kula dake fa tunda biki na kika zo dole na dau aikin ya zanyi. Sai dai ke ma fa dole ki kula min da amaryata amana har zuwa sanda za a kawo min ita ko mata ta?” Sadda kai Adama tayi cike da kunya, itan ma ashe tsokanan ta yake saboda ya san ta da shegen kunya.
“Ga Suhaiman nan ai ko? Yanzu za a iya fada mana abinda ake bukata?” Hararan Adama nayi jin abinda ya fada “Ni kam ba muyi maganar da ita ba. Amma zamu tattauna sai mu fada maka”
“Ai da nace kizo ki kika yi ina” ban tanka taba kar mu saida hali a gaban shi. “Ku tattauna in dai zuwa gobe sai a sanar mana. Inma ba a iya fada min a gaya ma abokina kinji kawar mu?” Dariya nayi kasa kasa, Adama ta ja hannu na muka shiga cikin gidan. Muna Shiga kuwa ta Sani gaba sai na fada mata abinda ke faruwa.
“Ba fa wani abu bane Adama, Maganan Ya Sanda yake kawai muna dan gaisawa dashi ne” zaro idanu tayi tana kallo na, sai kuma taja tsaki “Zama kiyi bayani yarinya”
Mun fara shirye shiryen biki Adama gadan gadan, don gabadaya ma bamu da lokacin kanmu. Alhmdlh! Yan gidan mu baki daya basa nan, dake ana hutu wai sunje Maiduguri. Ni lamarin dadi ya min sosai, munyi sabani dasu hankalina kwance.
Ana jibi daurin auren, mu ka tafi can gidan baban ta da ya gini sabo, basu dade da tarewa ba a waziru Ibrahim. Yan uwan mamanta ne zasu yi mata kitso da lalle, tunda already daman an Dade da fara gyaran jiki. Har dare kuwa mu ka kai, sai dai tsaf dani da ita da wasu kawayen ta yan uwansu sai da aka mana kitso da lallen. Duk munyi kyau abun mu.
Sai dai ni da it aka bari a gidan, su sun fara gaba. Sai wurin karfe taran dare har Goggo ta fara kira tana fadan me ya hana mu dawowa. Adama ma nan sai kumbura take, ta kira angon nata yace gashi nan zuwa kuma bai karaso ba. Da alama dai fushi tayi sosai, saboda ko da ya kira daga bayan kin dauka tayi sai nice na fisge wayan na dauka. Sanar min yayi da yana waje, don haka duk fushin ta haka ta hakura ta sauko muka fita, ta San sarai Goggo ba zata bar ta ta kwana a nan ba.
Ko da muka fita yana tsaye jikin motan ya harde hannayen shi yana kallon ta Inda zamu fito. Ai kuwa muna fitowan, idanuwan shi na sauka akan ta. Daga murmushin da yayi ya girgiza kai na gane ya fahimci fushi tayi. Duk ta daure fuska ko kallon sashen shi ba tayi. Tun kafin mu karasa ya bude kofan baya. Adama ta gaya min ba abinda ya tsana iron mace ta zauna a baya shi Kadai a gaba. Sanin haka yasa duk lokacin da ya bata mata rai sai ta zauna a baya taki mishi magana. Ko gane hakan da yayi ne yasa direct ya bude mata bayan? “A min afuwa Gimbiya mana, uzuri ne ya rike ni” ba ta tanka ba ta shiga. Ni dai zagayawa nayi kawai na shiga ta daya gefen har ya shiga ya fara tafiya.
“Ai juya akai gaisuwa ko malam” Naji Mustaphan ya fada. Sai lokacin ma na San akwai mutum ne a gaba. Gyaran murya ya danyi “Amaryan mu ina Gajiya?” A daddafe Adama ke amsawa har su ka gama gaisawa. “Au ba za ka juya ka ganta ta tanka ba kenan?” Dan sauti dariyan shi naji “Musty problem, to ance ma bata sanni bane?” Bansan kuma meya faru ba, sai gani ji nayi Adama na kallona. Hakan ya Sani dagawa dan dole domin inga abinda ke faruwa. Da farko abun kaman gizo ya min sai da na cigaba da kallon shi still naga dai shi dinne ba wani ba.
Mamakin da ke kan fuska na ya gane sai naga ya dan fadada fara’an shi hade da kashe min ido daya. “Ke kuma ba gaisuwa baiwar Allah?” Rasa ma me zance mishi nayi, gabadaya sai na zamo am totally confuse. Ya fahimci hakan kuwa saboda irin dariyan da naga ya cigaba. “To ya hidiman biki? Tunda ni ba za a gaishe nin ba?”
“Ya hanya? Yaushe kazo?” Da kyar nayi dambe da zuciyata kalaman su ka iya fitowa.
Zai amsa kenan mustapha ya katse shi. “Kyale shi kinji Suhaima, bai fada miki zuwan shi ba kuma zai matsa sai kin wani gaishe shi”
“Malam ba ruwan Ku damu” Umar Sanda ya amsa. Dariya Mustapha yayi. Daga nan zancen ya wuce kuma aka koma wani hiran daban.
Gab da zamu shiga kwanan layinmu Umar Sanda ya dan jiyo yana kallo na. Sai Kuma ya dauke idon shi ya maida kan abokin shi. “Tafiyan kafa ya Kama ka fa” duk ba wanda ya gane abinda ya ke nufi, saboda haka mustaphan yace “Kaman ya kenan?”
“I have to used your car” Kaman bashi yayi maganan ba haka ya fuske. Mustaphan ma bai ce mishi komai ba har mu ka isa kofan gidan Goggo. Bai motsa Sai shi angon ne ya bude kofan shi ya zagayo ya bude ma amaryan shi Yana fadin “bismillah wify” da alamun har yanzu da sauran fushin ta, ba tace komai ba fita kawai tayi tana kallon inda nake tsaye, don haka nagane tana nufin mu shiga gida kenan. Sallama na musu ina jin mustaphan na fadin “au dawa za kayi zancen ka kwace min mota Kuma kana gani ta shiga ciki” a saitin shiga naji yar guntuwar amsan Sanda “In ruwanka” ban San ya suka Kare ba. Don ni har na saki jiki a cikin gidan na Kama wata sabgan Sai ga wayan shi ya shigo. “Pls Zaki iya fitowa?” Abinda ya fada kenan directly. Shiru nayi in dan wani nazari, ashe shi ya dauka doubting fitowan nake. “Just for some few minute, I promise kinji”
Da “Toh” kawai na amsa shi ya katse wayan. Ko bakomai ina jin Yana da wani kima da mutunci da nake gani nashi saboda da dilalai na. Ya min abinda ba wanda ya taba kwatanta yi min shi Kuma a cikin lokacin da nake matukar bukatan hakn. Sannan ya San sirri na Wanda duk duniya ba wanda ya sani, Amma hakan bai sa ya tsane ni ba ko yayata ni Sai ma kokarin kusan ta kanshi da yake dani a ko yaushe.
Dan gefe kadan na hango motan mustaphan da bamu dade da dawowa a cikin ta ba. Amma gudun inje bashi bane a ciki yasa na fara waige waige. Yana ganin haka naga ya hasko fitilan motan. Tun kafin na karasa naji Karan bude murfin kujeran zaman banza.
Maido hankalin shi wuri na yayi bayan na zauna. “Hope dai ban takura miki ba ko? Nasan an sha hidima” murmushi kawai nayi nace “Bakomai fah, ban ma gaji ba” ban lura hannuna yake kallo ba Sai da naji yace “Ma Sha Allah, Wacce ta muku abun nan tayi kokari” dan dago hannuna nayi Kaman ni lokacin na fara ganin lallen. Tabbas nima nasan yayi kyau, duk da kuwa ni baka ce ya amshe ni.
“An gama makaranta, da fatan jarrabawa yayi kyau?”
“Muna fatan hakan in Sha Allah” na amsa, ina tunanin abubuwa dayawa a raina. Musamman yanda Umar Sanda ke maida hankali kan abubuwa na sosai.
“Which school Zaki yi” ban ji shi saboda tunanin da nayi tsamo a ciki. “Emhm?” Na tmby. Sai cewa yayi “Ko ba zakiyi School ba aure Zaki yi kema?” Bambarakwai ma naji abun don haka nayi saurin girgiza kaina. “Medicine nake son karanta” na fada Kai tsaye saboda ba ni da wani buri face shi in. Hopefully, ina fatan hakan ya kasance, Kuma ban San meyesa ni jina ina bukatar goyon bayan sa ba.
“Nasan you will make a great doctor but tell me a ina kike planning karatun?”
“Unimaid” na amsa Kai tsaye.
“Why?” For some seconds nayi mamakin tmbyn nashi saboda na San there must be reason behind him. Sai dai in ganin komai is so clear.
“Goggo” kawai na amsa. Nodding yayi in an understanding. Kaman ba zai you magana ba can yace “Na so kiyi a Egypt, zai fi miki sauki da kwanciyar hankali. Beside akwai abinda ya kamata ki sani a can in but everything can wait” ban gane me yake nufi da last statement in shi ba amma kawai na basar. Sai ma tunanin da na fara to yana nufin shi zai yi sponsoring ina a Egypt in da yake magana kenan ko me?
“Baki tmby tsaraban ki ba” ya fada idanuwan shi a kaina ko motsi ba sa yi. Rasa abun cewa nayi, har Sai da sakwanni suka shude Sai yace “Shknn ko baki tmby ba na zo dasu ma” wasu fararen leda guda biyu ya miko min. Ka sa amsa nayi saboda a ganina abun na nema yayi yawa Kuma. “Kar ki damu, ba Sai kin nuna min kin gaji da amsan abun hannun na ba domin dai ba ni na aiko miki wannan ba” Da sauri nace “To waye” tsab ya karanci mamakin da ke kewaye kan fuskata. “Calm down mana, just somebody that likes you. Zaki san waye ne a gaba in Sha Allah” zan kara magana yayi saurin girgiza min Kai. “Kar ki tmby ni pls because I will lie to you. Ni Kuma ko a da can da nasan na aikata abubuwan da basu dace ba Sam banda karya a ciki. Ban iya ta ba. Na fada miki ne saboda kawai kinsan cewa there is somebody out there that loves and care about you. So desperate to see you.”
“Saboda shi kake kula da al’amura na” murmushi yayi Sai Kuma ya dan daure fuska “Part of the reason dai. I care about you ko ba dan wannan ba Suhaima. I can’t even explain amma dai ki barshi a hakan kawai. Je ki kwanta, nasan hidiman gobe yafi na yau ko?” Da Kai na amsa mishi, yace “to Allah ya tashi mu lfy”.
Washegari, gabadaya hidima ya shige mana gaba da har na manta da tunanin Umar Sanda da Kuma abinda ya zo min dashi, Wanda har yanzu ban gama gamsuwa. Amma dake am occupied, Sai ban samu lokacin da zan yi ishshen tunani ba. Throughout ranar ba ban gan shi ba. Sai Ajiddah da tazo wurina duk da rashin Shirin da suke da Adama. Na fahimci abubuwa dayawa game da canjawan ta. Ajiddah ta waye sosai yanzu, idanun ta sun kara budewa fiye da da. Ga Uban samarin da ta tara, manya da ya’yansu. Inda Naira ke goguwa da kanta kawai. Irin labaran da take bani ma a yanzu daban ne. Ba a Damaturu ta tsaya ba ma har Maiduguri duk ta San su. Adama dai bamu wuri tayi, dan na riga na gama sanin nasu ba zata taba zama iri daya ba. Bayan tafiyan ta, Adama tazo tana min korafi ni dai ban tanka ta ba. Bikin ba wani hayaniya, Goggo ce ta hana tace Sam ba a gidan ta za ayi wani bidi’a ba. In dai an daura auren suje can suyi fitsaran su. Nima hakan ya min dadi, saboda ba gwanar hayaniya bace.
Washegari da safe da yaka asabar wurin Sha daya da rabi na safe aka daura auren. Zo ku ga kuka gun Adama. Bari ma tun da aka fara bikin da alamu kiris ta ke jira daman. Dan bayan wannan fushin nata Sai da suka kara samun wani issue in Kuma har aka daura auren fushi take dashi. Duk da hakan dai ba abinda aka fasa, ni dai ko da ya Kira ni a waya yana rokona pls in bata hakuri misunderstanding in shi tayi Allah. Dariya kawai nayi nace mishi “Ai mutuniyar ta akwai saurin fushi, Sai ka shirya da kyau” dariya yayi Yana sanar min shi kam Sai da bikin ya kusa ta fara mishi hakan. Jinjina abun nayi, Dan nasan tayi kokari ma a hakan. But now, is time for him to get ready for the real deal.
Tun around four aka zo daukan Amarya. Nan ma dai Sai da tayi complain inta akan saurin me yake. Ita dai tasan Sai bayan magreeb ake ziwa daukan Amarya. Banza na mata, Sai sauran friends inta da suka hau dariya. A hakan dai aka dau Amarya zuwa gidan ta dake nan, Abba Ibrahim. Ba a dade ba aka hau Shirin Dinner, Wanda plan in gidan Angon ne. Amarya da Angon Sai a can suka hadu, Dan na lura Kaman tsoron ganin ta ma yake.
A wurin Dinner in bamu dade da hallara ba, aka fara sha’ani. Ina zaune na wani ya tunkaro ni yana min magana. The next I know, Umar Sanda na gani a kaina Yana ma mutumin magana. Ban san me yace mai ba naga ya juya ya tafi. “Taso muje” kawai yace, nako bishi. Ya bude mota mu ka shiga. Tun ina tsammanin zai ce min wani abu har na lura gabadaya hankalin shi na ga wakan da yake saurara ya kwantar da kujera ya runtse ido. Don haka nima na cigaba da dan danna wayata. Har aka tashi muna waje. Shi da kan shi ya kaini gidan Amaryan back, dake kawaye ranar a nan suke kwana.
Ko washegari ma lokacin siyan baki, ya Kira ni a waya na fito lokacin da suka iso. Ina shiga yaja motan, nima bance komai ba har ya sauke ni gidan Goggo.