MAFARIN SO CHAPTER 7

MAFARIN SO CHAPTER 7

                    Www.bankinhausanovels.com.ng 

Sai dare sosai ya koma gidan, gabanshi na matuƙar bugu don baisan da wacce zata tareshi ba, cikin saɗaɗawa ya shiga gidan, sai da ya shiga ɗakinshi yayi shirin kwanciya, sannan ya nufo ɗakin da take gabanshi na ƙara tsananta bugu, gara yaje ya sameta, yasan iyakarta dai tayita mishi masifarta da rashin kunya.

    Yana tura ƙofar ɗakin ya jita rufe gam, ya murɗa taƙi buɗuwa, ya shiga bugun ƙofar anma kaman babu mutum ciki, saida ya gaji don kanshi sannan ya haƙura ya tafi ya kwanta yana tunanin halin da take ciki, abubuwa da yawa yake hasasowa a ranshi, yasan dai tana cikin damuwa da ɓacin rai, shi kanshi yasan bai kyauta mata ba.+

    Ba wani barci yayi ba daman, tunda yayi sallahn Asuba ya dawo falo ya zauna yana gadin fitowarta, lokaci lokaci yana ɗan taɓa ƙofarta ko zaiji ta buɗe, har kiranta yake a waya anma duk a kashe.

     Wasa-wasa ya share kusan Awa bakwai yana zaman jiranta, fargabarshi na daɗa ƙaruwa da tunanin kodai tafiyarta tayi? To idanta tafi ina zataje? Sai can wani tunanin ya faɗa mishi ai indai tafiya tayi bazata rufe ɗakin ba, da wannan ƙarfin gwiwar Ahmad ya ƙara share wuri ya zauna yana jiran fitowar Rabi’ah.

   Sai gaf da Azahar ta fito, tana miƙa irinta masu barci, kwatsam taci karo dashi, tayi saurin dai dai ta nutsuwarta, kaman tayi baya ta koma ciki takeji, saboda wata tsanarshi data ƙara ruruwa a cikin zuciyarta, ta wuceshi ta nufi kitchen ko kallon inda yake batayi ba.

    Ta ɗan fara hidimarta, ya shigo, taƙi ɗaga kai ta kalleshi, tana shirin fera doya ya matso ganin bata kulashi ba, tun kafin ya ƙaraso ta jefar da wuƙar da doyar harta kusan faɗa mishi a ƙafa, ya janye da sauri.

     Fita tayi tabar mishi kitchen ɗin yabi bayanta, kafin ta maida ƙofar ta rufe yayi sauri ya shiga cikin zafin nama, duk sukayi cirko-cirko suna kallon juna.

       “meye dalilin da yasa zaki fasa girkin?”

    Ta ɗanja numfashi sannan tace,

       “saboda na fasa ci”

     “kin fasa ci kamanya?”

    “na ƙoshi”

         “me kikaci da zakice kin ƙoshi?”

   Ta juya ta ƙyaleshi, ba tare data bashi amsa ba, don gani take magana dashi ma ɓata lokaci ne, aikam yaji haushi sosai, yabi bayanta, ganin hakan ta ɗauko wayarta da sauri ta kira Amrah, sukayita wayansu suna fira harda shewa, kuma tayi sa’a suna tare da Zahra don haka sukayita firarsu.

    Tun yana saka ran zata gama wayan, yaga dai bata da niyyar katse wayan yasa ya haƙura, shida kanshi ya koma kitchen ɗin.

    Doyar ya feraye ya mata sakwara, yasan mutuniyarta ce in baku manta ba, da sauran miyar da tayi yayi warming ɗinta,  duk don gani yake ya mata laifi, shi kanshi har mamakin kanshi yake.

    Sanda ya shigo ta gama wayan, har dariya yaso ya bata, ta ƙara gimtse fuska tana latse-latsen wayarta.

      “saiki tashi ga abincin nan”

   Ta ɗan saci kallon abincin, sannan taci gaba da latse-latsen wayarta.

       “dake fa nake magana”

  Taɗan fara waige-waige sannan tace,

       “ni wai?”

          “idan bake ba, wa kenan?”

     “toh ai naga ni nace maka na ƙoshi, da baka wahalar da kanka bama”

     Ya ware ƙafafu zai hau gadon ya kamota,

     “baki isa bafa, dole sai kinci”

    Hannu ta saka ta dakatar dashi,

       “me haka kuma? Karka kuskura ka taɓani, koni na saka ka yin girkin ne?”

     Yayi sakatoto yana kallonta, da mamakinshi saiya tsinci kanshi da kasa ƙarasawa inda take.

    Ƙofar falon ta jiyo ana ƙwanƙwasawa, ta tashi ta tafi buɗewa, yasha gabanta.

      “ina zakije? Idanfa wasu daga cikin dangina ne sukazo?”

    Wani irin kallo ta bishi dashi, da sauri ya bata hanya,

     “idan su ɗinne ma don sun ganki menene?” taci gaba da tafiyanta ba tare data kulashi ba,

    Mai gadine ya kawo mata saƙonta, ta ansa tayi godia, sannan ta nema wuri a falo ta zauna ganin bai fito mata daga ɗaki ba,  takeaway ne mai rai da lafiya, ta zauna ta cika cikinta kaman babu abunda ke damunta sannan ta kunna kallo.

     Haka dai suka yini, sai neman taƙalenta faɗa yake anma taƙi ta kulashi, daman ance tabarmar kunya da hauka ake rufeta, ya gaji da rashin kulashin da take yazo ya mata saye,

       “ke malama, banfason kinibibi, ki fito fili kiyi magana sai wani shan ƙanshi kike kaman wacce akama laifi”

       “nikam laifin me za’amun?”

     “ohon miki! Sai shegen rashin jin magana, duk kashedin dana miki akan karki sake ki fita, tukunna ma dai meya fiddaki daga gida jiya?”

    Sai da tayi murmushin takaici ganin duk yanda ya hayayyaƙo mata,

     “ni kuma na fita? Wani yace maka ya ganni a wajene?”

    “karki rainamun hankali, idan bake ba wacece ta fita?”

       “gaskia badai ni ba, babu inda naje, wani wuri akace maka an ganni?”

   Yayi shiru yama rasa ta inda zai ɓullo mata, nema take da ƙarfi da yaji ta maidashi ƙaramin yaro, gaba ɗaya taa canja mishi kaman ba Rabi’ar daya sani ba, taƙi ta fito fili tayi magana yamasan menene a ranta, ƙarshema ɗakin ta koma ta kulle abinta, har lokacin tafiyarsa yayi bata fito ba, da bazaije bama sai da yaji abokanshi sun fara cewa zasuzo gidan su tafi dashi.

     Bai daɗe da fita ba, tana kwance tana hawaye, kiran Khadija ya shigo wayarta, kaman karta ɗauka don batasan me zatace mata ba, hakanan dai ta ɗauka.

        “Hey! Amarya ya hidima?”

     “Alhmdlh er uwah, yauma bazakizo da wuri ba ko?”

    Murmushi tayi, “kin ganni nan kwance banjin daɗi, ƙila dai sai ranar yinin biki”

    Shiru Khadija tayi tana tunanin ta inda zata fara mata magana, gashi da alama yanda Rabi’a ke magana tana cikin damuwa.

      “er uwah bazaki samu zuwa ba, gashi kuma inason muyi wata magana”  

      “Ayyah! Toh ya za’ai kenan?”

      “ki daure kizo plz er uwah, kinga maganar bata waya bace”

     “Awwh ashe bakijin daɗine, kuma dai inason muyi maganar nan yau”

    “tohm faɗamun ina jinki”

        “bansan ta inda zan fara bane er uwah, bansan yanda zaki ɗauka maganar ba”

     “ki faɗa kawai, ai mun zama ɗaya”

    “yauwah, don Allah sis ki faɗamun miye tsakaninki da Ahmad mijin dazan aura?”

    Er dariya tayi sannan tace,

    “wannan wacce tambayace? Nida ba garinnan nake ba a ina zan sanshi? Babu wani abu dake tsakanina dashi”

      “haba er uwah! Nifa kira nayi donmu fahimci juna, kuma yanzu da bakinki kin faɗamun mun zama ɗaya”

      “Hakane fa, kinsan dai bazan ɓoye miki komai ba”

      “ke ba er Yola bace, daga wanne gari kike?”

    “katsina”

   “yauwah, Yayana Ahmad kuma wanda zan aura, yaje katsina wani biki, ya daɗe sosai sannan ya dawo, kuma dawowarshi tasa ya canja ta fannoni da dama, sannan ranar da muka haɗu dake kinsan motarshi ce kikeja a ranar? Sannan kuma address ɗin da kika bani na gidanshi ne, kuma nazo har gidan na iskeshi, karki cemun duk wannan arashi ne aka samu, bayan kuma ga abunda ya farunan jiya”

     Rabi’ah tayi shiru zuciyarta na bugu, Khadija ta riga ta kamata ta da hujjoji masu yawa, batasan kuma ta inda zata mata karya ba, ta faɗa mata gaskia ko A’ah? Gashi kuma batason ta jefa Ahmad cikin matsala duk da abunda ya mata.Khadija tace,

    “ina jinki yakamata kisanar dani gaskiya, nida ke zuwa yanzu mun rigada mun zama daya tamkar er’uwarta na daukeki kuma  har a zuciyata haka nake jinki jikinta”

    Rabi’ah tayi shiru tana sauraronta yayinda jikinta yayi mugun yin sanyi ta rasa yadda zatayi da Khadija, ita fa bata son duk wani abu da zaiyi sanadin shigarta tashin hankali bazata taɓa manta masifar data shiga a kwanakin baya ba, Amman nacin da Khadija ta rinƙa mata ne yasa taga gara kawai ta sanar da ita gaskiya komai, duk ma abinda zai faru ya faru inyaso tasan matsayin zamanta da Ahmad jikinta a sanyaye muryarta cike da rauni da ruɗanin abinda zai biyo baya ta zayyanewa Khadija komai tun daga kan yadda Ahmad ya aureta har zuwa  yanzu da suke tare.+

A hankali Khadija take sakin ajiyar zuciya gabanta naci gaba da faɗuwa Shikenan ta faru ta ƙare abinda take gudun  jin kenan duk da ita ta nema, taji wani abu mai nauyi ya tsaya mata a ƙirjinta da kyar ta samu ta haɗiye abinda ya tokare mata wuya, tayi shiru ta faɗa duniyar tunani. Har wani gumi ke tsattsafo mata a jikinta tsabar tashin hankali, Jin shirunta yayiwa ne yasa Rabia sake cewa

     “hello! hello!! …kina jina kuwa?” a hankali Khadija dake zaune tamkar an dasa ta, ta ɗan dawo natsuwarta muryata a dashe  tace

    “ina jinki,” Amman gaba ɗaya ita kadai tasan yadda take jin zuciyarta,.

    Rabiah  tace

    “dan haka na roƙeki da Allah Khadija karkisa damuwa a ranki, domin kuwa ni aurena da Ahmad ba mai ɗaurewa bane, nan gaba  kadan zamu rabu da juna  kuyi aurenku, wlh wlh  ni banida wata damuwa tunda daman can  bason junanmu muke ba  nida shi,”

Amman gaba ɗaya kana jin yadda take maganar kasan tana cikin ruɗani da tashin hankalin fiye da wanda Khadija ta shiga,

  Muryarta ta gama canzawa gawani irin dokawa da zuciyarta keyi da sauri da sauri yayinda hannunta ɗaya ke dafe da saitin zuciyarta.

  jinta kawai Khadija take Amman tasan mai mata kamar Rabiah Sam bazai so abinda zai shiga tsakaninsu ballanantana ya kaishi ga rabuwa da ita ba,

    Rabiah taki sam  bazata iya cigaba da magana da Khadija ba dan haka muryarta na rawa  tayi saurin cewa,

     “nagode sosai Khadija  da kaunarki gareni haƙiƙa kin ƙaunaceni batare da kinsan koni wacece ba Allah ya baku zaman lfy da mijinki” sannan tayi saurin yi mata sallama tare da  ajiye wayar.

Itama can ɓangaren Khadija numfashi kawai take furzarwa tana sakin numfashi haɗe da runtse idanunta gam tsawon lokacin tana zaune hannuta rike da waya tana juya maganganun Rabiah Tayi zurfi cikin tunanin dalilin da yasa Ahmad ya iya ɓoyewa iyayensu irin wannan Batu, a hankali a hankali ta soma buɗe idanunta har ta buɗesu  fes, suka sauka kan fuskar Aunty dake tsaye a gabanta da sauri ta gyara zamanta haɗe da dawo da natsuwarta jikinta Sosai, kallo ɗaya zaka mata kasan bata cikin haiyacinta da natsuwarta cikin waskewa ta sakarwa Aunty murmushin karfin hali wanda dagani kasan na dole ne .

idanu Aunty ta zuba mata tana nazarinta tsab , kai tsaye Aunty ta jeho mata tambaya,

     “meke faruwa duk naganki haka?, sannan kuma wacce Rabiah naji kuna waya da ita?”

  dan tun soma wayar Khadija Aunty  ta shigo dakin kuma duk ta gamajin hirarsu da Rabia wacce batasan ko wacece ba ,.

Khadija tace

    “wata ƙawata ce sannan  bakomai hirarmu kawai mukayi” Aunty ta sake tsareta da Idanu,

      “bangane bakomai ba, hira ce kawai ta canzaki haka kika dawo kalar tausayi  bayan ga zahirin gaskiya nan  nagani, kina cikin damuwa gashi fa har hawaye kike yi sannan kice min babu komai, ban son raini wayo zaki gaya min gaskiya ne ko sai naci miki mutuncinki, koni sa’ar wasan ki ce?,

Ganin yadda aunty tayi ne hade da bude mata wuta yasa   Khadija ta firgice dan tasan halin Aunty sarai babu abinda ta tsana sama da karya.

  dan haka kawai ta sanar mata da  komai itama, kamar yadda Rabiah ta sanar mata

Banda Innalillahi wa’inna ilaihirrajiun babu abinda Aunty take iya furtawa, ta samu waje ta zauna jagwab tana kallon fuskar Khadija tamkar abinda taji Khadija ta sanar mata  ba gaskiya bane, Amman tasan Khadija bazata taɓa gaya mata ƙarya ba dan tasan hakan ba halinta bane.

STORY CONTINUES BELOW

Ba wani bata lokaci Aunty  ta miƙe  zata bar ɗakin jikinta har tsuma yake, itama Khadija da jikinta ke rawa tabi bayan Aunty tana kiran sunanta

   Taci gaba da tafiyarta bata juyo ta sake duban Khadija ba har suka bar part din, da sallama suka shiga part din ummin Ahmad.

Ummi dake zaune a gefen  gado bayan ta gama amsa waya, itama tana ganin  yanayinsu taji gabanta yayi mummunar  faduwa  tasan duk yadda akayi  ba lafiya ba, a yadda ta gagansu.

   Waje Aunty ta samu ta zauna dan har wani juwajuwa take Gani ummi tace,

    “lafiya na ganku haka?”   

   Aunty ta sauke ajiyar zuciya tana duban Ummi    ita kanta  Khadija kasa tsayuwa tayi dole ta samu gurin zama dan ƙafafunta bazasu iya daukarta ba ga bugun da zuciyarta keyi, Ummi ta sake dubansu Aunty da kyau haɗe da jeho mata tambaya hankalinta a tashe,

Ba ɓata lokaci nan itama Aunty ta sanar mata abinda ke faruwa kafin kace me gaba ɗaya rabi daga cikin dangi sun ji  abinda Ahmad yayi take surutai yamasu yawo a cikin gidan abinka da gidan taron biki, wasu suce Sam karya akewa Ahmad bazai taɓa yin aure a ɓoye  ba tare da sanin iyayensa ba.

  Yayinda wasu ke cewa ƙila dai ajiyeta yayi kawai matsayin abokiyar shashencinsa tayama zaiyi aure batare da sanin kowa daga cikin daginsa ba.

    Surutai dai gasu nan barkatai kowa da abinda yake faɗa. Take mahaifin Ahmad wanda suke kira da Abba yasa aka nemo masa  Ahmad din .

Ahmad zaune a gaban iyayensa ya tanƙwashe ƙafafuwansa yayinda  kansa ke sunkuye a ƙasa duk da bai san dalilin kiran nasa ba Amma yana a jikinsa komenene yasa Abbansa yasa aka kirasa yasan  ba lafiya ba.

    Shiru tsawon lokacin Ahmad  zaune gaban  mahaifinsa, kallonsa Abba yake kafin daga bisani ya kira sunan Ahmad ɗin cikin wata irin murya, 

   “AHMAD”  ya ɗan ɗago yana kallon Abbansa haɗe da bin yan ɗakin da kallo, Umminsa ce zaune sai Aunty da wasu daga cikin   en’uwan ummi dana mahaifinsa, a kallon da suke masa  yasan akwai abunda ke shirin faruwa  koma yafaru Kuma koma menene yasan akansa ne ganin yadda dukkansu idanunsu na kansa, maida kansa Yayi ƙasa yana karanto duk wata addu’a da yasan zata kawo masa natsuwa dan gaba ɗaya firgice yake da irin kallon da mahaifinsa ke jifansa dashi.

Mahaifinsa ne ya soma magana a fusace yana kallon Ahmad ɗin yace,  

    “haƙiƙa  ka bani kunya da mamaki yaushe ne ka iya yin aure ba tare da saninmu ba?”

   Da sauri Ahmad ya sake dago kansa yana bin iyayensa da kallon jin tambayar da mahaifinsa ya jeho masa gaba ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa  saboda ruɗanin maganar  Abban nasa, take ya fara tambayar kansa  ta yaya Abbansa yasan da wannan ɓoyayyar  maganar.

    Tabbas yasan yau asirinsa ya gama tonuwa tunda gashi sun sani a kallon da suke masa ne gaba ɗayansu suka gasgata lallai ya aikata abinda suke tuhumarshi 

    “uhm muna jinka”, inji cewar ummi

    “ita ɗin waccen Kuma meye matsayita?”

   A dake ya soma magana yana  girgiza  mata kai 

    “A’a … A’a nifa bawani aure da nayi…, asalima ni bansan da wata magana makamanciyar haka ba”

      “ok karuwa ce kenan ka ajiye a gidan?” inji Abbansa bakinsa na rawa jin furucin mahaifinsa ga Rabia duk ilahirin jikinsa babu inda baya rawa a sukwane  yace,

     “Allah ba karuwa bace” sai bayan da Yayi maganar yasan Yayi katoɓara Abbansa yace,

     “OK matarka ce kenan da gaske?”

    Ahmad ya sake gigicewa yace  shi fa sam bai san da wani  zancen wata mata ba,

   mahaifinsa yace,

  “kana nufin babu mace a halin  yanzu a gidanka da take zamanka?”

   Gaba ɗaya jin maganar Abbansa yake tamkar a mafarki bai taɓa tunanin zuwan wannan ranar ba nan kusa ba, gashi ta riske shi ba tare daya shirya amsa tambayoyi da Abbansa ke jifansa dashi  ba.

Yayi shiru ya ya rasa yadda zaiyi da rayuwarsa  tabbas yasan Yayi rashin kyautawa  wajen rashin sanarwa iyayensa, sannan ya aikata babban kuskure wajen amsar auren rabia domin abinda auren nata yaja masa zargi abu mafi muni da ƙyama,

    Abbansa yace,

   “kai fa muke Jira  kamana shiru zantura gidanka yanzu a dubomin” 

    Ahmad ya zubawa Abbansa ido yakasa cewa komai sai haɗiyar miyau da yakeyi da ƙyar tsawon lokacin sannan yace,

    “Abba nifa babu kowa a gidana, duk wacce tace taga wata a gidana ƙarya take”

    Abbansa ya hassala dan jin Ahmad yaƙi amsa laifinshi cikin sauki dan haka  ya cewa wani kaninsa ya tashi  yaje gidan Ahmad ɗin ya dubo masa.

Ganin haka yasa Ahmad a tsorace ya dakatar da Abbansa sannan ya mai da kansa kasa ya soma bawa iyayensa haƙuri sannan ya sanar musu da duk abinda ya faru da yasa har ta kai ga ya  aura Rabiah ya ƙara da cewa shi  ba wai sonta yake ba taimakonta kawai Yayi.

    Gama bayaninsa ke da wuya, suka ji sallamar ƙanin mahaifin Ahmad  dake zaune a katsina wanda yazo ɗaurin auren Ahmad a karo na biyu  Kuma shine  wanda ya tsayawa Ahmad ɗin sanda za’a yi aurensa da Rabiah.

    Ai Ahmad na ganinsa ya saki wata nannauyen  ajiyar zuciya haɗe da godewa Allah a hankali yake furta kalmar   ‘Alhamdulilllahi’ har bai san  adadin da Yayi ba.

     Shima ƙanin mahaifinsa saida ya gama jin komai dan tuntuni yake tsaye a bakin ƙofa  tun fara jin rikincin, yana ƙarasowa ya miƙawa sauran yan uwansa hannu suka gaggaisa sannan ya samu gurin zama  shima ya sake kara yi musu bayani dangane da auren Ahmad ɗin, Amman shi  cewa Yayi abinda yasa ko a waya bai sanar musu  da zancen zatonsa ko shi Ahmad din ya musu bayani  ne.

    A tare iyayen Ahmad ɗin suka dinga sauke ajiyar zuciya bakau ƙaƙƙautawa  dan zatonsu ko wata sabuwar  ƙaryar Ahmad ya sake shirya musu dan haka  Abba yace,  ‘aje gidan  azo masa da rabia’.

Allah sarki Rabia tana kwance tun bayan gama wayarsu da khadija ta sulale nan ta kwanta tana zubda hawayen tausayin kanta da makomarta idan Ahmad ɗin ya rabu da ita a hankali take fidda numfashi mai zafi jin da tayi zazzaɓi na neman rufeta yasa ta miƙe da kyau tana ganin juwa ta shige bedroom ɗinta hijabin sallarta ta ɗauko ta zura har ƙasa ya rufe mata jiki sannan ta faɗa kan bed ta duƙunƙune jikinta waje daya a hankali take fidda numfashi.

    Bata wani jima da kwanciya ba taji ana buga gidan haɗe da sallama taƙi tashi jin anci gaba da bugun ne yasa ta miƙe tana layi taje ta buɗe ƙofar ta wata mata ta gani tsaye a bakin ƙofa ta ɗan janye matar ta shigo tana kallon Rabia sai data mata kallon tsab sannan tace,

     “kece matar gidan?” Rabia ta ɗaga mata kai Aunty tace,

   “ok muje iyayen mijinki Ahmad na son ganinki yanzu batare da ɓata lokaci ba”

  take gaban  Rabiah ya soma faɗuwa dum dum dum… Jikinta ya ɗauki  rawa  amman dayake sanye take cikin hijab sam Aunty bata gane yanayinta ba dan haka ba wani westing time Rabiah ta bita .

Suna shiga gidan idanu caaa! akan Rabia har suka iso babban parlourn Abba jikinta bai bar rawa ba gaba ɗaya jikinta ya jiƙe sharkaf da zufa da sallamarta ta shigo bayan Aunty ta shiga waje Aunty ta nuna mata kusa da Ahmad Amman Rabiah taƙi zama ta samu waje can ta zauna ta sunkuyar da kanta kasaTunda ta sunkuyar da kanta saita kasa ɗagowa, zazzaɓin daya ɗan sauka ne harta fara zufa ya dawo, jin kowa yayi shiru ne gashi matar data kawota bata samu damar sunyi wata magana ba,ta ɗan ɗaga kanta tana satar kallon inda Ahmad yake, shima kanshi a duƙe fararan kayannan nashi duk sun shiƙe kaman wanda aka jefa ruwa, ko ƙwaƙƙwaran motsi bayayi.

    Ta ƙara gyara zama tasan tabbas yau asirin Ahmad ya gama tonuwa, kar dai ace Khadija ta faɗa musu, to meye dalilin tara su anan?

    Abba ne ya ƙara gyaran murya, sannan ya kalla inda Rabi’ah take yace,

      “Rabi’ah ko?”

  A hankali tace, “eeh nice”

     “meye tsakaninki da wannan?” ya nuna Ahmad,

   Muryarta ta ɗauki kyarma, saita buɗa baki anma ta kasa cewa komi,

        “kowa anan ke yake saurare Rabi’ah, kuma daga yanda kikaga yanayin zaman namu nasan kin fahimci abunda ya taramu anan”

   Ta gyaɗa kai, sannan tace,

      “Mijinah ne”

Yanda tayi maganar kowa yayita kallonta, ita kam kanta a ƙasa.+

Abba ya sauke ajiyar zuciya, yana maida kallonshi kan Ahmad daya gama birkicewa,

     “yanzu dai ta gama tabbata kayi aure kenan, duk ba wannan ba, yanzu ka faɗamun meye matsayin wannan auren naka? Sannan kuma meye matsayin auren da zaka sakeyi?”

    Ummi ta gama kaiwa iyakar wuya, tunda take da mijinta bai taɓa magana ta miyar mishi ba, anma yau kam akan Ahmad shi take bazata iya shiru ba, cikin ƙunar rai tace,

      “waini me kake nufi Alhaji? Nifa gani nake ma kaman lallaɓa yaronnan kake, haka ai bazai gane laifi yayi ba,”

      Dakatar da ita yayi da hannu,

     “abun da kwanciyar hankali baiyi ba, tashinsa ma bazaiyi ba, aure daine an riga anyi, koma meye zamuyi bazai canja hakan ba”

Tayi shiru kawai, Abba ya maida kanshi kan kallon Ahmad,

      “kai muke saurare”

   Ya ƙara matse ƙafarshi, irin zamannan an ajje ɗaya ƙasa an lanƙwashe ɗaya don aji daɗin kwantar dakai,

      “Abba ni kamar yanda na faɗa dalilin aurena da Rabi’ah, ko lokacin ba son junanmu muke ba, kuma har yanzu bamu zaman lafiya da ita, shawarar ma rabuwa muke shiyasa ban sanar muku ba”

“ka gama yanke shawarar kuyi aure ku rabu ba tare damun sani ba kenan?”

    Kanshi a ƙasa yace,

         “kuyi haƙuri Abba…”

Ya dakatar dashi ai,

     “shikenan, ni daman bazan maka umarnin ka saketa ba, saboda saki halal ne anma Allah yana fushi idan aka yishi, anma tunda kun gama magana shikenan, ɗaurin aurenka da Khadija babu fashi, sannan kuma bazan kaita gidan mai mata ba, ina fatan ka gane?”

     Wata zufarce ta ƙara kwaranyo mishi, Rabi’ah ma gaba ɗaya ɗakin ne ya fara juyawa da ita,

      Abba ya ƙara cewa,

           “shikenan ai kowa zai iya tafiya”

   A hankali kowa ya fara watsewa.

Har gida aka mayar da Rabi’ah, ashe duk tashin hankalin data shiga a baya sharar fagene kawai babban na tafe, me Ahmad ke nufi daya faɗi gaban kowa ba son junansu suke ba? Kuma ga Umarnin da Abbanshi ya bashi, tabbas ta gane me yake nufi duk da bai fito fili ya faɗa musu ba, abinda takeso ne za’ai mata, anma sai takejin sam kaman wacce za’a raba da rayuwarta.

     Zuciyarta jikinta babu inda ke mata daɗi, dare ya somayi anma bata marmarin kwanciya ballantana tayi tunanin barci, so take kawai Ahmad ya dawo su yita ta ƙare.

Tun tana saka ran shigowarshi gidan, harta fidda, haka ta kwana tana jiranshi bai shigo ba har gari ya waye, tafiso ta tafi da hujjarta, anma ai yasan inda ya ɗaukota.

     Don haka tunda sanyin asuba ta fara shiri, abinda tasan nata ne kawai ta saka a er ƙaramar jikka, sannan ta watsa kuɗin data ɗauko ɗakinshi a cikin jikkar, ta zumbula hijabinta ta fice daga gidan.

Napep ta ɗauka ya kaita tashar katsina, ta iske motar dake layi babu kowa cikinta, batason ɓata lokaci, ta kira direba ta sayi sauran kujerun kawai suka wuce katsina.

       Gudu kawai yake shararawa a titi, itakam ta ɓoye fuskarta a hijab sai kukanta take cikin zuciyah, inta gaji kuma ta share ta ɗan huta sannan taci gaba, da yake tafiya ce mai nisa, ba sune suka isa katsina ba sai kuyan sha ɗayan dare, tana mishi kwatance har ƙofar gidan Yayanta, ya ajiyeta duk ta gama galabaita, ta sallameshi sannan ta rataya jikkarta ta wuce cikin gidan.

Ta ƙwanƙwasa kofar gidan, baba maigadi yazo ya buɗe mata, sannan ya dalle mata idanu da torchlight, ta kare fuskarta,

       “sannu baba”

Sannan ya ganeta,

      “a’aha hajia kune tafe?  Yo aini farko ban ganeki ba, ina maigidan naki?”

    Yana magana yana leƙen waje inda zai hango

Ahmad,

       “ai ni kaɗai ce baba”

    “ke kaɗai kuma wannan tafiya mai nisa? Lafiya dai ko?”

    Wuceshi kawai tayi, a gajiye take ga kuma yunwa harta manta rabon data saka wani abu bakinta, abunda yafi damunta ta samu hutu,

    Ya ɗan ɗaga murya,

        “kuma kinyi sa’a ƴan gidan basunan, halan bakuyi waya ba?”

    Ta ɗan tsaya,

        “ina suka tafine?”

   “yaran aka tafi kaiwa hutu wai dubai”

      “tun yaushe Baba?”

    “jibi dai satinsu biyu, anma ina sakaran cikin satinnan zasu dawo, bara in ɗauko miki mukullan saiki shiga ki huta”

    Ta gyaɗa mishi kai, da sauri yaje ya kawo mata sannan ta wuce gidan.

Da shigarta cikin gidan, kai tsaye ɗakinta ta wuce, ta kunna fitila, yayi kaca-kaca kaman bola, an tula kaya a ciki, kaman wanda ya shekara ba mutum a ciki, duk wasu abubuwanta an canja musu wuri wasu an ɓatasu, ba wannan ne ya dameta ba, daman tayi sallahrta a hanya, ta ture wasu kayan saman gadon gefe guda ta samu wurin kwanciya, tayi kwance tunanin Ahmad na dawo mata, shikenan yana can ya zama ango, ya auri zaɓinshi wacce yakeso ita kuma ya ƙyaleta, wannan ne kalan nashi taimakon kenan? Ta tuna abunda aka mata a gidansu, kuma saboda ya gama tsanarta ko gidan ya kasa zuwa yaga halin da take ciki a jiyan, ƙila yanzu haka suna tare da amaryarshi.

    Ita kaɗai dai take ta tunaninta, sai da yunwa ta matsa mata sannan ta jawo jikkarta ta fiddo takeaway ɗin data siya a hanya ta kasa ci, hakanan tayita turawa saboda yunwar da takeji.

Bayan ta gama tura abincin ta koma ta kwanta,  ta koma ta kwanta, duk yanda taso ta yakice tunanin Ahmad, ta kuma tuna mata zuciyarta tsanace a tsakaninsu fa ba so ba, anma abun ya gagareta, haka tayi ta juyi data runtse idonta saita ringa ganin ga Ahmad nan da Khadija, sunata abunsu cikin raha irin na amare, har cikin sautin kunnanta take jiyo dariyarshi, da sauri ta saka hannu ta doɗe kunnanta.

    Taso ta kira Yayanta ta faɗa mishi zuwanta, anma ta fasa kawai, idan sun dawo sun ganta, don batasanma abunda zata faɗa mishi ya kawota gidan ba.

    Nan kuma ta sake komawa tunanin Ahmad, yaje gidan bai ganta ba anma saboda bai damu da halin da zata shiga ba ko kiranta bazai iya ba, sannan ta tuna da wayarta, ta jawota a kashe ba charge, da sauri ta liƙa charging tana ɗan fara ɗauka ta kunnata tana saka ran kozai kirata.Kwanciya  tayi flat akan gadon dake cikin ɗakinta fuskarta na kallon celling saman ɗakin wayarta kife kan ƙirjinta yayinda   hannuwanta duka ke  rungume da kirjinta,

    A hankali  ta  runtse idanunta,  sanyi taji  yana ratsa ko ina ajikinta, duk da tarin damuwar da take tattare da ita ,hakan bai hanata jin jikinta  Yayi mata nauyi ba,+

Bata son tuna abubuwan da suka faru da ita, amman sam  tunanin Ahmad yaƙi barinta, tunaninsa ya  addabi  zuciyarta  da ruhin jikinta,  Ganinsa take  cikin memory dinta yana mata yawo tamkar ta buɗe idannuta ta gansa a gabanta .

    Batasan lokacin  da abubuwan da suka faru atsakaninsu suka dinga zuwan mata ɗaya bayan ɗaya ba, tun daga  farkon auensu take ganin komai daya faru  har zuwa yanzu datake kwance.

Ta ɗauki lokacin mai tsawo kwance, yayinda ta dinga jin wani iri wani iri a jikinta, bugun  zuciyarta na sake ƙaruwa ta dinga ƙoƙarin ganin ta cire tunansa da shafe babinsa, arayuwarta amman hakan ya gagara,

   Ta kota ina ta juya shi take Gani a hankali ta furta meke shirin faruwa dani ni? Kada dai soyayyar Ahmad ce ta kamani ban sani ba, dako na shiga uku, idan har zuciyata ta Kamu da son Ahmed.

    Hakika zuciyata  bata kyauta min  ba, shi Ahmad ɗin daya hana zuciyarta sukuni da  tashin hankali, ko sau ɗaya  beko yi tunani ya nemeta ba, ballanantana tasa ran ya  damu da ita, dan gashi ko neman ta bai yi ba , that’s means bai sonta kuma bai damu da ita ba, tunanin iri iri tayi shi a ranar, amman gaba ɗaya babu wani mafuta data samawa kanta,  ganin tana da wani opportunity na sake sabuwar rayuwar, yasa tace  zata binne damuwarta da tazo dashi hakan ne zai warware dukkan  matsalata da damuwarta abinda    ya dinga bata mamaki da ɗaure mata kai bai wuce jin  yadda   bugun zuciyarta ke sake yawa  ba,  a duk kowane second sakamakon tuninsa daya addabe ruhinta.

Tana son  tunaninta a yanzu ya ta’alaka ne akan yadda zata Gina rayuwarta ta ingantata, kuma ta more sauran kuruciyarta data mata  saura, tana ji ajikinta dolenta ta shafe babin rayuwata da tayi baya,

da tabbacin binne  al’amura da suka gabata  , bakomai  hakan zai haifar gareta ba illa tashin hankali da fadawa duniyar dabata kaunar tunawa.

Ajiyar zuciya ta sauke tare da gyara kwanciyarta, batayi aune ba, taji  kuka mai ciwo ya kufce mata, jin yadda hawaye ke bin  fuskarta yasa, ta buɗe fararen kyawawan  idannuta da suka gama  rinewa, a hankali ta bude idanunta tana mai sake  zubawa   celling ɗakin ido ta tuna rayuwar da tayi a baya a cikin ɗaki cike da farin cikin da walwala tare da samun soyayyar, Yayanta gareta  da kyar take iya janyo  sauran numfashin da Yayi mata saura , lokaci zuwa lokaci take duba wayarta ko zataci karo da ko massage ɗin Ahmad ne, amman still babu alamun  Sai dai taga  sakon network .

Wata irin masifaffiyar ƙaunarshi ce ta dinga jin yana taso mata tamkar ta halaka  mata zuciya da gangar jikinta wasu hawaye masu zafi da radaɗi suka sake  biyo kuncinta tabbas babu shakka so shine  mafi girman abinda yafi hukunta zukata da sanyasu cikin kunci, raɗaɗi har ma da bacin rai ahankali ta dan mike ta jingina bayan da jikin gado still ta sake duba wayar babu wani labari Ahmad zazzabi mai zafi ne ya rufeta  ta sulale ta koma ta kwanta dafe da Kanta, a hankali take furta ‘wayyo kaina wayo kaina’ abinda Rabiah ke iya furtawa kenan a hankali dan muryarta ta dashe saboda kuka, ‘kaina zai cire’ daman kuma haka take idan bata da lafiya ciwon kaine mai tsananin ya kamata sai juyi take tana kuka daren ranar kasa runtsawa Rabia tayi saboda tsantsar tashin hankali da baƙin ciki rungume take da hannuwanta dukka tana rawar tsanyi  har zuwa washe gari  bata bar jin zazzabi ba, sakamakon rashin samun  natsuwa kwance take tamkar ruwa ,banda sallah babu abinda ke tada ita kwakwaran motsi matse ma da kyar take iya yi haka ta dinga tunanin rayuwarta irin gata da jin dadlɗin data taso a ciki ba’a mata faɗa bare tsawa koda yaushe sai rarrashi bata taɓa zubda hawaye saboda bakin ciki sai na shagwaba da jin dadi amman tunda ta auri Ahmad take zubda ƙwalla da ganin bakin ciki iri iri ta sauke ra’ayin dan shi amman shi itace abar wulakantawarsa, ya  gaya mata duk baƙar  maganar da yaga dama  to meyasa zuciyata ta kamu da sonshi  da yawa?  haƙiƙa zuciyata sam baki min   adalci ba da kika kamu da  soyayyayar wanda bai sonki da rashin nuna  damuwarsa  dake,  ta faɗi haka akasa ranta tana girgiza kai agogon dakin ta duba karfe shida daidai  na yamma tagani ta runtse idanunta da suke mata zugi , sannan ta mike da kyar ta shiga bathroom.

Kullum sai Rabia tasa ran ganin kiran Ahmad ko sakon shi  amman sai taga shiru hakan na matukar tada hankalinta da susuta mata zuciyar yayinda garkuwa jikinta ke sake yin rauni ita kanta tana cike da mamaki jinta haka akan Ahmed duk da tana kwaɓar zuciyarta akan karta kuskura taci gaba da son wanda bai sonta da nuna rashin kulawarsa gareta  al’amarin dake sake ɗaure mata kai bai wuce yadda ƙaunarsa ke nukurkusar zuciyarta da ruhinta ba tare da hanna gangar jikinta samun walwala da kwanciyar hankali ,

Gaba ɗaya Rabia ta canza tayi laushi ta dawo shiru-shiru tamkar ba wannan Rabiar da kuka sani ba, wacce tayi rayuwarta cikin isa da isgilanci da nuna  komai ba wani abu bane a wajenta kana kallonta zata baka tausayi sakamakon yanayinta wani lokaci soyayya kan canza kowani irin hali da isa da duk wani iko da takama ta mai da mutun tamkar ba’a bakin komai tare da karyar da zuciya to hakance ta kasance da Rabia .

Tun tana sa ran ganin wani abu daya shafi Ahmad ɗin har tazo ta soma fidda ranta a kansa ta ɗauki haƙuri duk da son nan shi na nan daskare a zuciyarta ba  laifi zuwa yanzu ta dan soma sakin jikinta taci gaba da rayuwarta ita kadai acikin gidan  sai dai duk da  ta rame sosai hakan bai dusashe kyawunta ba yayinda masu aiki gidan ke kula da komai na gidan hakan ya sake yi mata dadi .

Bayan sati daya

Kwance take akan makeken royal bed dinta bayan tayi wanka ba wani kwalliya tayi ba, sanye take cikin ƙananan kaya pencil jeans da riga Handles, ta zubawa wayar  hannuta  idanu  tunanin take akan ta kira number Ahmad a karo   kusan na goma kenan tana dialing ɗin number sa , da zarar taga number ta kusan shiga sai ta kashe da sauri har zuwa sanda me gadin gida Yayi sallama wanda shima ya daɗe tsaye yana rafka sallama bataji ba, jikinta a sanyaye ta mike zaune  tare da ajiye wayar hannunta, sannan ta amsa sallamar baba mai gadi, bata fito ba daga inda take tace,

     “ya akayi baba?”

  yace,  “Hajiya anyi baƙo a gidan nan”, tayi shiru can kuma tace,

     “to ka shigo dashi mana  ta koma tayi kwanciyarta  ba tare da ta damu da ko wani irin bako sukayi ba,”Daddaden kamshin turare tasoma juyowa mai matukar  tsanyi da sanyaya rai ahankali  ta lumshe  idanunta   , tare da raya abubuwa masu tarin yawa ,

+

sosai kamshi ke sake kusantota har inda take kwance batayi yunkurin motsawa ba .

sakamakon wani zazzabi  mai zafi  da taji yana neman  rufeta hade da matsanancin ciwon kai , wanda take jin tamkar  rayuwarta ce tazo karshe .

Amman hakan bai sa ta daina jin nauyin da jikinta Yayi ba  .

take a lokacin jikinta ya dauki  rawar sanyi gabanta  yashiga faduwa da sauri  .

Zuciyarta da gangar jikinta suka soma amince mata da abinda take tunani wanda a zahirance ita kadai tasan abinda take ji .

duk da idanunta a rufe suke ,hakan bai sa takasa gane mamallakin wannan kamshin ba. Amman ta wani bangare na zuciyarta Gani take tamkar bashi bane kamshi ne kawai yazo the same danashi .

Har sanda ya daura hannunsa kan handle din kofar kamshin turarensa ya sake gwaraye dakin  amman hakan bai sa ta motsa ba , ballanantana takai ga bude idannuta tsoro hade da frigice ne suka taru suka  narkar mata zuciya har yasa jikinta sake daukar  zafi tamkar garshin wuta .

wani iri bugu zuciyarta keyi da sauri kmr ana buga mata guduma a kirjinta .

   “ahankali ta dinga karanto duk wata addu’a datasani  ta   yaye kunci da damuwa a zuci. take taji wani iri natsuwa ya mamaye zuciyarta wanda ta tabbatar albarkaci addu’ar datayi   ne yasa taji haka a boye ta dinga  saki ajiyar zuciya “tare da sake runse idanunta.

  Cikin sanyi jiki tasa Hannuta ta janyo  bargo dake nike a gefen gadon ta lullube jikinta dashi , domin bata jin zata iya tashi taga ko wani iri bako suka yi ,duk da Gani take tamkar karya ne  zarginta bazai taba zama gaskiya ba .

wai Ahmed yazo gareta .

tasan duk ma abinda zai kawo Ahmed ahalin yanzu gurinta ba alkhari bane.

haka kawai ta tsinci kanta dayin addu’ar .

Allah …Allah kasa Ahmed bayazo ne  yakawo min takardar sakina bane hannu da hannu “aiko idan haka takasance da nashiga uku .

take  taji zuciyarta ta tsananta faduwa  tare da bugu mai tsananin .

  hancita ke jiyo mata abinda takasa gasgatawa .

Tabbas kamshin  turaren Ahmed  dai take sake jiyowa daga nisa wanda take jin ko  acikin dubban mutane tajiyoshi zata iya bambanta nashi  dana sauran jama’a .

,to idan shine meyazo yi ?  zuciyarta ce ta bata amsa ,abinda kika dade kina nema   daga gareshi mana shi yazo baki .

   , ba takama kike da nuna isa akan lallai Sai ya sake ki ba .

Wannan maganar da zuciyarta tayi ne yasa   , jikinta ya sake daukar zafi da fargaba mara iyaka  a take zazzabi dake jikinta ya dawo sabo.

jin motsen bude kofar ne yasa  jikinta  sake  daukar kirma.

  , zuwa  yanzu tasoma tunanin kawowa zuciyarta wani abu na daban ” wanda bbu shakka shine din ne dai mutumin da zuciyarta ta kamu  da matsanancin kaunarsa km take azabtuwa akansa  ke tsaye  agabanta,

  Ahankali taji an maida  kofar dakin an rufe ,km  har lokacin idanunta a lumshe suke tana jinsa   .

sanye yake cikin   wasu  kananan kaya masu matukar kyau da daukar hankali, wanda kallo daya zaka masa kaji  yashiga ranka” batare da kashirya hakan ba.

   ,ga  kwantaccen gashin kan nan nasa  sunyi  luf luf dasu ,sai sheki suke yi sakamakon samun gyara da suke samu   akai akai .

kana ganinsa kaga asalin fulanin Yola Ahmed  kyakkyawa gaske km ajin farko acikin maza .

wato first class, fuskarsa zagaye da suma wanda  ke kara fito da ainihin kyaunsa yayi matuka sai dai ya dan rame hakan ya kara fito dagon hancinsa dogo ne sosai mai siffa karfi .

  ,  Tsaye yake hannuwansa duka rungume a saman kirjinsa “hade da  zubawa kyakyawar  fuskarta idanu, ahankali yasoma takowa zuwa bakin gadon da take kwance .

STORY CONTINUES BELOW

Cikin sanyi  yasa hannunsa ya yaye bargon data lullube jikinta dashi  idanunshi fes a kan fuskarta dake lumshe.       “. tayi fayu ,tare da rama ta lokaci kadan .

,jin yadda bargon ya dau zafi ,da   yadda take fidda numfashi ,yasanyashi kai hannushi kan goshinta take yaji  abinda ya sake frigitashi daga gareta zafin dake jikinta ya ratsa tafin hannushi wanda bai san sanda ya zauna a gefen gadon ba.

” wani irin tausayinta  mai tattare da so ne, ya rufe shi alokaci guda har yarasa yadda zaiyi.

  ,shr Yayi yana cigaba da kallon  fuskarta “tare da aiyana abubuwa daban daban  masu tarin yawa wanda shi kadai yabarwa kansa sani “jikinsa bbu kwari ya mike tare da  shigewa bathroom din dake manne  da dakin.

dan duk a tunaninsa bacci takeyi,.

  dakin ya sake dawowa hannushi rike da ruwa acikin wata yar karamar roba ya janyo karamin towel din dake rataye a bathroom din  ya jefe cikin robar.

, sannan ya sake tadowa inda take kwance  yana sake  cigaba da kallon fuskarta.

, Cikin sanyi ya ajiye rabar hannushi   , sannan ya tsaya yana balle botiran gaban rigarsa    ,

Tun shigowarsa dakin taji wani iri sanyi yana bin ilahirin gabobbin jikinta “yayinda gefe daya km tausayin kanta  ya lullubeta   tana ji ahalin yanzu tamkar batada kowa ne a duniya nan  muddin Ahmed yarabu daita batasan halin maseefar dazata shiga ba .

,jikinta ne Ya sake yi mata nauyi ,sakamakon dokawar da  zuciyata keyi da sauri da sauri , .

,duk da ba bacci take ba Amman sam bazata iya  bude idannuta ta kalleshi dasu ba .

  saboda batasan Dame yazo mata ba .

Bugu da Kari ma  bata bukatar yagane halin da take ciki.

,, shiyasa ta sake runtse idanunta gam ta yadda zai dauka bacci takeyi   .

lafewa tayi hade da   kamkame jikinta waje daya ,   kokuwa tashiga yi da numfashinta dake neman tsayawa.

, ahankali take janyo numfashi  har sanda yashiga bayi ya fito still idanunta a lumshe suke tamkar mai bacci gaske  ko kadan bata kaunar abinda zai sa ta bude idannuta akansa .

Ahankali yasoma  Cire long sleeve din dake daure  a saman  rigarsa  ,ya saura daga shi sai Yar karamar white top jeans .

  ” cikin sanyin  jikin nan nasa  yasoma kokarin hawowa kan gadon.

duk motsensa  tattare yake da bugun zuciyata har sanda ya iso gareta bugun zuciyata ya  sake nunku fiyye kowani lokacin .

   hannuwanshi duka yasa  tattarota  jikinsa dasu, yasoma  cire mata hamles din jikinta ,bata hanashi ba  dan bata ji zata iya yin hakan.

gashi km bata da wani kuzarin ajikinta  dazata iya hanashi.

,sai daya tabbatar daya zare rigar hamles din  jikinta ta saura daga ita Sai  Jeans .

Birki yaja  sakamakon cin karo da yayi  da  k’irjintae, shr yayi tare da tsurawa k’irjinta ido kawai yana kallonsu .

take yaji tsigar jikinsa suka mike tsaye , cak  yasoma fita haiyacinsa ya kamo lip’s dinshi na kasa  ya tura cikin bakinsa yasoma tsotsa    ahankali ya dinga jin shauki da sanyi na bin kowani gabba ta  jikinsa. Koda yake hango brest dinta ta saman rugarta

bai tsammaci   haka  suke ba.

, gabanta ne yacigaba da faduwa da sauri jin yadda idanunshi ke tsaye kyam  akirjinta  . yayinda   numfashinta ke fita sauri  wanda hakan yabawa Ahmed saukin Gane cewa  ba wai  bacci take ba, ta dai yi shr ne kawai .

dan haka shima yaki ce mata komai har sanda yasa  hannusa  ya janyo rabar ruwar kusa dashi   yamatse towel din sannan yasoma goge mata fuskarta da wuyanta .

Sannu ahankali  yayi kasa da hannushi zuwa saman   kirjinta inda yafi jin dumin zafi .

,cak yaji ta rike masa  hannu amman har lokacin idanunta a lumshe suke taki yarda ta bude su ballanantana tasan a wani yanayi Ahmed din yake .

shima tsayawa Yayi

yana binta da wani irin mayataccen kallo wanda yasa shi jin wani iri shauki  ajikinsa .

  , jin saukar hannuta    kan nashi  yahaddasa masa  sake jin wani irin shock …

gabadaya yanayin jikinsa yasoma sauyawa.

   . atare zuciyoyinsu suka  shiga dokawa, ajiyar zuciya ya sauke   , sannan ya   zare hannuta daga rikonshi datayi .

  ya hade su waje daya .

sannan yacigaba da goge mata jikinta da hannushi daya batare daya furta koda kalma daya ce ba.

wanda shi kansa yasan ko za’a taru akansa ,a wannan halin dayake ciki bazai iya cewa daita komai ba.

  ,  amman duk sanda yazo wajen dukiyar fulaninta  nan yake susucewa ya lalace   ya dade yana goge wajen ,wani iri tsanyi taji yana ratsata kasanta  kokarin kwatar kanta takeyi , amman sam takasa saboda irin  rikon da Ahmed din  Yayi mata .

STORY CONTINUES BELOW

  yana  gama goge mata jiki ,  ya kai bakinsa ya subuci kirjinta  yana ji tamkar yakai bakinsa kan dukiyar fulaninta saboda yadda suke sone masa ido amman baya son taga zalamarsa,    sai da ya  mayar mata da rigar jikinta tsab ,sannan  ya hadeta  da jikinsa,  wata irin  naunauyen ajiyar  zuciya ,ya dinga saki batare dayasan yayi hakan  ba.

itama hakan ce takasance tare daita.

ahankali yakai bakinsa daidai  saitin kunneta muryasa a sarke tamkar ta mashaya  yace sannu rabiatu ,ya kike jin jikin naki yanzu? Tayi shr

ko muje hospital ne ? Nan ma  Ta sake yi  masa banza taki  cewa komai .

,  Sai ma kokarin kwacewa datake son yi daga jikinsa.

Ya sake matseta tare da  marairaice murya yace ina da Ina  yake miki ciwo  yanzu ,yasake tmbyrta .

,  still shr tayi masa  taki bashi amsa .

Yace please rabia  kiyi min  magana mana ko zanji saukin radadin dake damun  zuciyata .

” Yace idan baza ki min magana ba , to ki  bude idannuta ki kalleni dasu please…

,cikin sanyi muryata tace ni ka sakar min jikina .

  ,jin tayi magana ne yasa ya saketa kmr yadda tace .

,Sai dai  shr yayi tare da  zuba mata idanu kawai yana kallonta.

cikin sanyi jiki  ta mike tana kakabe jinkita  tayi hanyar fita  daga daki   , tabar shi nan zaune bayanta yabi da kallo ,ganin yadda take juya jikinta yasa jin wata azababbiyar sha’awarta ta dira masa take jijiyarsa ta mike sambal.

Tafin  hannushi duka ya kifa akan jijiyarsa , tare da girgiza kai.

Mikewa yayi   yabi bayanta yana kiran sunanta Rabia … Rabia  Amma ko juyowa batayi ba ballanantana ta amsa masa, zaune ya tadda ita a parlour” tana ganinsa ta kawar da kanta gefe .

domin  kallonsa kadai na sake birkita mata brain  wani son shi ne ke fizgarta, ta  ji dazata iya    ta sakar masa   jikinta yayi duk yadda yake so…..

a hankali ya iso ya zauna kusa daita hade da  kamo tafin hannuta cikin nasa  yasoma  murzawa yana lumshe ido , yasa hannushi daya ya juyo da fuskarta suna kallon kwayar idanun juna , zuciyarta tashiga tsalle  tare da  dokawa   ahankali tayi kasa da kanta dan bazata iya jurar  cigaba da kallon cikin idanunshi ba  .

  yace dan girman   Rabia kece min wani abu mana ki duba irin tafiyar da nayo “duk saboda ke .

duk da nasan ba kya sona , amman hakan bazai   hana   ki mutuntani ba, ba  wai ki dinga nuna  ko in kula ba ,.

Sai lokacin ta dan dago kanta ta sake  dubanshi batare data yarda  idanunsu ,sun hade da juna ba.

tace Ai bawani ne  yasaka zuwa dole ba.

, kai ne da kanka kasa kanka” dan haka  ko yanzu kayi Niyya ,kana  iya komawarka bbu mai hanaka.

, ahankali ya dan saki murmushi gefen baki  sannan yace uhmmmm rabia kar muyi haka dake fa, ban cancanci  irin haka daga gareki ba ahankali ta zame yatsunta daga nashi ta mai da bayanta ta jingina da kujerar da take zaune hade da  runtse idanunta tace idan kazo kawo min takardar sakina ne ,kana iya mikomin ,ka kara gaba ,dan banson damuwa.

ya sake kokarin sake kamo hannuta ta zame ,da sauri  tana sakin ajiyar zuciya duk da tarin kaunarsa gareta hakan ba zai sa ta zubda darajarta da kimarta  ,a gurinsa ba .

, Batason ta nuna  tana maraba da zuwansa.

,duk  maganar dayake yi tana jinsa amman tayi masa shr  taki cewa komai .

wani iri tsanyi taji yana ratsa ilahirin jikinta yau  tazo mata da abubuwa masu tarin yawa ciki har da zuwan Ahmed .

Koda bai  nuna yana sonta ba.

, zuwansa kadai yajiyar daita farinciki mara misaltuwa” amman duk da haka a tsorace take dashi ” dauriya ce kawai irin nata”  ,mikewa ta sake yi zata bar gurin.

  ya fizgo hannuta ta fado jikinsa” a tsawace yace wai  meyye haka km? sai wani binki nakeyi kina wani shashshareni , me kike nufi dani ?

Muryarta tamkar me shirin zubda hawaye tace  to ni me nayi km yanzu.

in ba dai kana son katura  rayuwata bane.

,tana son yi masa tsiwa sosai kmr yadda tasaba yi ada  , amman tsoro ya hanata aikata hakan .

,dan tasan bata cikin duniyarsa wanda   ita ahalin yanzu take jin wata irin masefaffen kaunarsa bataki ace sun kasance tare dashi  ba muddin rai .

tana son shi har bata san yadda zata misalta ba, ji tayi ya  sake matseta da kirjinsa ,  yana shinshina wuyanta .

jikinta ya dau kirma  tace kabari fa bana so abinda kakemin …..

yace ke nifa  bangane abinda kike nufi ba meyye  bakya so  din?  Cikin in..inna tace  ,    ni karabudani kawai kadaina hada jikinka da nawa.

,yayi sororo yana kallonta sannan yace saboda me ?

Saboda banaso kawai yace to wlh  baki isa ba dan  kyauta akabani auren ki ba.

sai da nabiya  sadaki  dan haka bbu ta yadda zaki hanani taba jikinta domin halalinane .

,kodab ki ga   Ina daga miki kafa.

Nayi haka  ne saboda rashin sanin matsayin aurenmu ,.

,bai tsaya jin abinda zata sake  cewa ba , yasoma romancing din jikinta cikin zafi zafi  ,ita km tana buge duk inda hannushi ya taba ajikinta ,da furta kalmar  bataso.

    duk yadda yaso rabia  ta saki jikinta dashi ,kiyawa tayi taki yarda .

haka suka kasance da junansu tsawon  lokaci yana nanuke daita .

duk inda tayi acikin gidan Ahmed na biye daita.  Yana susuta mata jiki da salonsa.

,ko gurin  bacci ma datace yaje yaje parlour ya kwanta harara ya zabga mata   yace anan din cinyeki zanyi .

Tare suka kwana  tana manne da jikinsa .

duk yadda taso ta hanashi taba jikinta hakan bai kasantu ba dan  Ahmed kin yard yayi da hakan kwana yayi yana lagudar jikinta har bacci ya dauke shi hannushi na zagaye da Brest dinta .

   Har washegari manne yake daita baya son duk abinda zaiyi separate dinsu ,haka ya dinga like mata har tasoma sakin jikinta dashi  ,

STORY CONTINUES BELOW

Wasa wasa yau kusan kwanan Ahmed biyar agidan daga sai Rabia sosai ta saki jikinta dashi .

Ahmed kwance akan gadon ,yayinda  rabia ke  tsaye gaban mirrow , fitowarta kennan daga bathroom sanye take cikin doguwar , bawani kwalliya tayi ba powder  kawai tashawa fuskarta sannan tasoma kokarin tufke gashin kanta da reborn .

ta cikin mirrow tahango Ahmed   ya kafeta   da  idanunshi  , yana binta da wani irin  kallo gashi dai bawani kwalliya Tayi ba Amma Tayi masa kyau matuka.

hararrashi ta sakar mishi ta cikin mirrow din .

  tace kallon fa na menene ango khadija .

Yayi murmushi ya miko mata hannushi , alamun tazo gareshi .

ta nuke  kafadarta  ,ya dan mike zaune ya fizgota ta fado jikinsa yasoma subatata ta koina sannan  yace kinyi kyau sosai.

ta tabe baki kawai tace har nakai amaryarka ,sarai yaji abinda tace amman ya shareta yacigaba aikawa zafafan wasani  jikinta  ,wanda suke neman zarar da Rabia .shi kansa amatse yake daita dan duk wata gabba dake jikinsa a bukace take da son samun natsuwa .

ahankali ya dinga sauke ajiyar zuciya sannan yakai bakinsa daidai  kunneta yace kinfita    kyau da komai ma ”  tare matse gam yana sakin numfashi , ya dan sausauta rungumar da yayi mata tare da kiran sunanta ,Rabia …tace   na’am  ” yace in tmbye mana ta dan  turo bakinta , sannan yace uhm yace bakya jin wani abu game dani ? Tace kmr ya kennan  ? yace kmr kiji kina sona … Tace uhmmmm ni bana jin komai akanka  yakamata kasoma shirin komawa gida  saboda amaryarka  .

Ya tsaki  yace kin wani  damu, mutun da zance wata khadija khadija  nifa ba’ayi aurena daita ba ,ta zaro idanu waje tana mamaki da alajabi jin abinda yace ,tace  kai dan Allah yace uhm to meyasa aka fasa auren ?

Ya lumshe idanunsa wani lokacin sannan ya bude fes akan fuskarta yasoma baya labarin

Abinda ya faru .

Yace washegari ranar da za’a daura aurena da khadija nida tahir muzo gida     , da niyar na shirya ,zuwa daurin auren.

Muna    shigowa parlour naji gabana ya yanke ya fadi ,ban kawo komai ba sai dai na tsinci kaina da son ganinki  kafin narshirya, dan dakin ki na nufa    kai tsaye nabar tahir anan parlour .

amman abin mamaki ina shiga dakin sai na tarar da komai na sakin  a hargitse km bbu alamunki  a ciki.

,bbu inda ban   duba amman  sam banganki ba .

hakan ya tabbatar min da  guduwa kika yi kika barni .

hankalina  yayi kololuwar tashi narasa yadda zaiyi da raina  wani irin abu  naji ya soki zuciyarta ,sunan Allah kadai na iya  ambata a kasan makoshi .

da muryata kmr ta dan maye ,sannan hannushi dafe da kirjinsa ,take jikinna ya dauki rawa naji tsayuwa ma na neman gagararta da kyar nasamu na iya kawo kaina   parlour .

tahir dake tsaye yana jirana  a rude yakaraso gurinna da sauri ganin yadda  jinkinna  ke rawa tare da  tmbyrta lfy  Ahmed ?

Zaunar dani tahir kaina da kirjina cikin sauri  tahir yaka mashi ya zaunar kan kujera ya dinga jero masa sannu ba kauakautawa.

Yace  daman bakada lfy ne  Ina matar gidan take   ?  Kai kawai Ahmed ya girgiza masa  ji yayi gurin na juya masa hakan yasa ya jingina bayaansa da kujera ya kwanta rigingine   jikinsa yacigaba da rawa .

cikin kankanin lokacin zazzabi mai zafi yayi mishi mugun cafka.

hatta numfashin sa da zafi zafi yake fitowa. Tahir ya sake maimaita tmbyr wai Ina matar gidan ne ?   ahankali ya rantse  idanunshi da suka gama canza kala tamtar garwashi  yace ta gudu ,ta gudu tabarni …..

bakaramin tashin hankali tahir yashiga ba sai tmby yake jiro masa  amman shr Ahmed yayi  hade da silalewa kan kujera  ya mike  yayinda numfashinsa ya tsaya cak .

rude tahir ya dauki wayar Ahmed din   yakira can gidan su kira daya biyu aka daga cikin zafi rai abba yace kana tun dazu nake neman layinka.

  , da kyar tahir yace abba ni ne  daman Ahmed din ne kwance bashida lfy.

nan dai tahir  yayi masa bayanin komai.

innalillahi wa inna ilaihi rajiun  shine kawai abinda abba ke ambato .

,da ma shima hankalinsa atashe yake tun dazu yake neman wayar Ahmed din tana shiga amman ba’a dauka ba , yace shikennan ganin nan zuwa.

   jikin Ahmed yacigaba da jijiga hatta kujerar dayake kwance akai  jijiga yake.

   jin motsen shigowar motaci yasa tahir likawa harabar gidan .

cike take da en’uwa .

Sa sauri tahir ya fito gabadayansu    a rude suke tmbyr me yasamu Ahmed din .

yanayin yadda suka jikin Ahmed din ne   ya frigita su matuka.

wani kanin mahaifin Ahmed din ne yace abinda zai fi muce dashi asibiti kawai.

batare da bata lokaci suka kama Ahmed din suka fice .

Koda labari yakai cikin gidansu Ahmed Gabadaya gidan yakoma tamkar gidan mutuwa .kmr  ba dazu ake murna da farincikin za’a  daurin auren  ba hatta  jama’a   sun fara watsewa dan   jin mummunar labarin abinda ya samu ango .

sai Ahmed yayi kwana biyu bai san wanda ke kasan ba da kyar da taimakon likitoci aka samu numfashinsa ya dawo normal .

Byn likita yagama rubuce rubucensa ajikin file ya dago yana duban abban Ahmed na  wasu yan dakiku sannan yacewa  mahaifin Ahmed alhaji a gaskiya danka  yashiga damuwa ne ko km wani abu ya frigitashi na  farar daya wanda  yasa  zuciyarsa ke gaf  da  bugawa ,amman inshallahu zuwa nan da wani  lokacin komai zai zama dade . Shr abba yayi yana sauraron likinta  Ahmed kadai Allah yabashi da namiji idan wani abu ya same shi bazai jurar ba . doctor ya sake cewa kayi hakuri alhj da yarda Allah zai samu sauki Amman dai yakamata asan abinda yasawa ranshi wanda ke nema yin barazana ga rayuwarsa .

Abba yayi doctor din godeya sannan ya kime ,cikin sanyi jiki  yabar office din likitan.

Yana fita  dakin da aka kwantar da Ahmed din ya nufa ,dakin  cike da enuwa maza da mata har  khadija ,  tana zaune kusa da Ahmed din da sallmarsa yashigo jingine ya  tarar  dashi tamkar dai yadda yabar shi .

,  ya samu guri ya zauna kusa dashi ya zuba masa idanu tsawon lokaci yana  binsa da kallo ,tare da nazarinsa .

ahankali abba ya sauke ajiyar zuciya sannan  nunfasawa  ya kira sunansa… ahmed ya dan dago yana duban ababansa .

Abba  yace meke damun ka haka Ahmed  da har zuciyarka ke gaf da kamuwa da mummunar ciwo . Yayi shr yana duban ababansa yace uhm Ina jinka

,bbu kunya ko tsoro ballanantana yayi shakka  wai khadija tana zaune  kusa dashi , yasanarwa da mahaifinsa komai yakarasa maganar sa yana saukin numfashi.

abba ya nunfasa yace daman baka saki yarinyar nan ba.

Ahmed  ya daga kansa alamun eh .

,cikin fushi abba yace to yanzu zaka saketa ashe ni ban isa ince kayi abu ba kayi .

, Gabadaya numfashinsa ya nemi tsayawa ya koma ya kwanta yana jan numfashi da kyar ,murya kdajijace ta dake kunnenshi  .

Tace dan Allah  abba kabarshi da matarsa ni wlh  na hakura  da auren auren Ahmed  ,daman ni nasan  bawai sona yake ba ,.

ko auren akayi ma ba lallai bane yabani  kulawar da kuke so .

,wani dadi gwaraye da farinciki ne ya lullube zuciyar Ahmed take yaji tamkar an cire masa wani nauyin dake kan zuciyarsa ne .

,abba yayi shr jin abinda khadija din  tace dan haka Vai sake cewa komai ya fice daga dakin ,.

Byn kwana biyu Ahmed yasamu sauki  sosai ya matsawa  likita akan lallai Sai ya salleme shi a cewarsa shi ya gaji da zaman  asibiti .

kai tsaye gidansu aka wuce dashi  idan mahaifinsa yace ya amince masa dayaje ya dawo da rabi .

Km yaci gaba da zama daita .

Ahmed na kawo mata karshen labarin ta

lumshe idanunta tsabar farinciki da tsantsar murna ,har batasan sanda ta sake lafewa  a jikinsa ba shima rungume yayi tsam  yana  lumlumshe idanun ahankali yace Ina sonki rabia …..har ban san yadda zan misalta miki dan Allah ki soni nima ko Yaya ne ,kinji  ban taba tunanin alakata dake zata juye zuwa soyayya mai karfi irin haka ba .

Dan rasa yadda zatayi ,kawai  ta tura kanta cikin kirjinsa tana shakar dadeden kamshin turarensa matseta yayi tsam ajinkinsa tare kissing din duk inda yaci karo dashi a jikinta .

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *