MISBAH BOOK 3 CHAPTER 13 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 13 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

zahiri kuma sai ta yi murmushi ta ce,

To ina jin ku Alhaj ya ce,

“Bahija ina so ki saurare ni da

kyan da kuma fahimta a kan abin da zan fada maki, ba na so ki yi mana rashin fahimta,

“Insha Allah zan fabimta Baba.”

ya ci gaba da ma maganar Deeni ne, Bahijja kin dauke mu iyaye,

Ta da girgiza kai kwarai Baba,

kin yarda

muna son ki kuma muna maki adalci tsakanin ki da Deeni.sosai Baba, alkhairi da mutunci da kuke mani ko iyayena ma sai haka, saì dai in yi ta muka addu’ar Allah ya saka muku da gidan aljanna.”Na ji dadin haka,

” in jì Alhajin ya ce,

«dama wani hukunci muka yanke, ina fata za ki ba mu goyon baya tare da hadin kai.

Iya dai yanzu bugun

zuciyarta ya fara tsamanta, haka nan ta dinga jin wani irin fargaba da tsoro na shigar ta, nan da nan ta fara addu’ a ta neman taimako a gun Allah ya ba

ta karfin zuciya da juriyar karbar ko ma wane

hukunci suka yanke ta ce,

“ina sauraron ku Baba.*

Ya ce Mun yanke hakuncin hada auren Deeni

da Farida.Ras! Ras! Ras! Taji kirjinta ya wani

mummunan bugawa hankalinta

ya nemi barin

jikinta, amma sai ta daure ta cije, kanta sunkaye cikin natsuwa ta ce,

“To Baba ai duk hukuncin da

kuka yanke daidai ne, Allahya sanya alkhairi

Hajiya Aisha tayi saurin karba da cewa

“wannan ba hukuncinmu bane mu kadai har da Deeni da kuma hukanci da kaddara irin

na Ubangiji, ina so ki karbe shi hannu bibbiyu ba tare

da wani tashin hankali ko hatsaniya ba, ba na so ki daga wa Deeni hankali a kan abin da yake so kuma

a kan abin da Allah ya halatta masa, ina son ki

masa adalci, in har kina sonsa, ki bar shi ya samu abin da ya dade yana so yake muradi.

«Farida wata halitta ce da Deeni ya so fiye da

komai a rayuwarsa wanda Allah bai nufa zai

mallakaba har sai yanzu mun yi magana da Deeni

yana son Farida yana son auren ta amma yana

gudun rigimarki don za ki daga masa hankali a

banza, wanda in kin yi haka baki masa adalci ba,baki yi wa ‘ya ‘yansa da mu kanmu iyayensa adalci

ba. Kin kuma so kanki da yawa in kika hana shi

abin da zuciyarsa ke so da abin da Allah ya halatta masa.

Babijja ta ji zuciyarta na zugi da zafì tare da wani irin radadì mai kuna, tabbas akwai tashin hankali ga mace in ta ji za a yi mata kishiya, amma fiye da

wannan shine irin ta inda Deeni ya bullo mata ya hada ta da iyayensa, ya ci amanarta ya yaudare ta

da zuciyarta, lokacin da yake gigin nemanta da son

ta, ya mata alkawarin karya ya munafurce ta ya

cutar da ita da zuciyarta, ya sa ta karaya, a kan

kanta da rayuwa ma gaba daya.

Idanunta suka kada suka yi jawur cikin tsananin kunar zuci da bacin rai ta daga kai za ta yi magana,Deeni ta gani tsaye a wurin suka yi ido biyu, haka

ta dinga ganinsa wani baki kirin, ya yi mata

tananin duhu, ta ji ya fice mata a zuciya, ba ta

kaumar ganisa, ba za ta iya jure kallonsa ko da na minti daya ba.

Saboda tsananin kinsa da ta ji a ranta ta yi saurin

kau da kai daga gare shi, tuni ya rude ya susuce ya

rude maganar iyayensa sun firgita shi matuka sun kara ruda zancen sun kara dagula al’amura da ruruta

wani rashin fahimtar tsakaninsa da Bahijja, ya

dawo gida saboda su yi magana su samu fahimta ya

samu labarin zuwan iyayensa, bayan ya iso gida ya

yi saurin zuwa asibitin zuciyarsa cike da tunani

kala-kala.

“Maganar ta yi zafi har haka, da ya sa iyayensa

tasowa su zo. Nan jikinsa ya ba shi za a samu

matsala, ga shi kuwa yana shigowa ya tarar da zancen da ya dagula komaì. Wanda bai san ta yaya

zai soma gyara shi ba, zufa ya ji yana fito masa ta

ko’ina a jikinsa. Tuni ya jike sharkaf saboda

tsananin tashin hankali. Bahija ta mai da kallonta

kan Hajiya Aisha tuni, ta Maida zaciyarta ta dake ta ce,

“mama ai kuwa Deeni ya min rashin fahimta, niba

zan taba shiga tsakaninsa da farin cikinsa ba ko da

abin da yake so, saboda ni dai mai kaunar Deeni ce

da zuciya daya, don haka ina maraba da duk abin

da yake so da kuma farin cikinsa koda kuwa ni ya saba wa nawa farin cikin.

‘”Dan haka na muku alkawari ba zan taba daga

wa Deeni hankali a kan abin da yake so ba, in dai

Farida abar sonsa ce farin cikinsa ce to, ina maraba

da ita, na yi alkawarin ba shi hadin kai ya aure ta,in dai daga wurina ne ba zai taba samun matsala

ba, ina maraba da Farida da kuma zuciya daya.Alhamdulillah» Alhaji

ya fada yana

murmushi tare da fadin

‘Allah ya yi maki albarka

da kika fahimce mu, kika dubi girmanmu da

darajar son da kike yi wa danmu, kika kawo komai

cikin sauki, Allah ya maki albarka ya ba ki abin da kike nema na alkhairi duniya da lahira, yau na kara

ganin girmanki da kimarki Bahijja.”

Hajiya Aisha ma kalaman Bahija sun sa duk

wani zafi da ta danka ta nema ta rasa, sai ta ji

kaunarta da kuma tausayinta sun shige ta saboda ance ciwon ya mace dai na mace ne, dan haka ta

yaba da namijin kokarin da Bahijja ta yi na yadda

ta amine ta karbi maganar cikin sauki tare da

saukaka lamarin, duka ta ce,

“Allah ya maki albarka Bahijja yarda kika faranta mana, ke ma

Allah ya foramta maki.”bahijjah tayi murmushi a takaice tace Ameen mama

tunda munyi maganar sai mu je gida ku huta sosai

ku kuma yi magana da Deeni a kan auren da

lokacin da za a yi shi.”

“To, insha Allah.

” in ji Alhaji, ya fada suna

kokarin mikewa, sai a lokacin suka ji motsin

Deeni, kasancewar sun ba shi baya, Babijja kawai

ke kallonsa ta kofar shigowa, ya kalli iyayen nasa ya Ce,

“Baba ban amince da hukuncin da kuka yanke

ba, ba ni da ra’ayin kara aure ko yin mata biyu ko ra’ ayin auren Farida, rayuwata ta riga ta ci gaba

yadda baya ba za ta dawo ba, haka dangantakata da

Farida ba zai dawo ba, babu Farida ko soyayyarta a

zuciyata yanzu.

Mama ta yi masa wani mugun kallo ta ce,

“InA wacce kake gudun bacin ranta da tashin hankalinta

ta ce ba ta da matsala, kai meye naka, kana son

Farida ko ba ka sonta, wannan ba na bukatar ka fada min saboda na san meye a zuciyarka game da

Farida, kar ka nemi ka raina mana hankali, ai ba

mace daya na haifa wa kai ba, zan ganì da matsayin

uwarka da na matarka wanne ya fi muhimmanci,

UMARNI na baka da ka auri Farida

Durkusawa ya yi a gaban maman zai yi magana

Bahijja ta yi murmushi ta ce,

“‘mama matsayinki ya wuce na kowa,

matsayinki ya wuce

wasa,

matsayina bai kai rabin naki bama balle har na

fiki, Deeni zai auri Fanida insha Allah, wannan

alkawari na maki,

damuwa da natsuwa, alamar ta riga ta sallama wa

zuciyarta, ta shirya kuma ta karbi wannan hukuncin

daga Allah, ta yarda da kaddarar ta Deeni kuwa ta

sallama shi HAR ABADA ba za ta sake bacin rai ko wani shiga harkokinsa da rayuwarsa ba, illa

iyaka ta sauke hakkokinta na aure a kansa da Allah

ya dora mata, ta fuskanci rayuwarta domin wannan tashin hankali da matsalar kam ta kau da shi daga

rayuwarta insha Allah, ta fada a ranta.

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *