MISBAH BOOK 3 CHAPTER 28 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 28 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

neman mata Kana harka dasu dama kai manemin mata ne maci amana

” Yayi mrmushi yace -naji’ dadi gara da kika

Bincikowa gara da kika ji Yaya cin amanà yake.

Kasan dole akai min auren’ Shämsu ko?

Koma dai menene kin dai ci amanar

kuma kinji  ya ‘akeji  ‘ada iyaye sun’ maki dole kin

auri Shams KiKa bata min Yanzu’ Kuma Kika sa

Kanki dole kika aureni don’ ki cimma burinki kika

bata min’ kika nuna min’ ke din mai ‘tuska biyu ce

well koma dai menene dalili duk sunan” su cin

amana dukkanmu dani da ke’ muna da dalilin mu.

Zan fada maki dalilina ba Wai don ina son kare

Kai na ba kö ina da Bukatar yi maki wani bayani

ba,sai don kawai na baki amsar tambayar da ki kayi min A wancan tokacin ina tsakiyar samartaka ta an tura’ ni Wáta uwa duniya* Karatu ina jin kai na yaro matashi dan gata kyakkyawa lafiyayye ban nemi koma? na rasa ba sai kadaici, bani da mai debe min kewa don haka nayi abokai maza da mata just for fun,just abokan hira

“ne Kawai, duk Wannan neman a wannan lokacin, ne ya wuce gurin A wannan” lokacin duk yan matan sun san dake kuma bawai wani ‘iskanci nake ba just’ nema ne na ayi hira na” fatar baki hakan yana sa’ min nishadi da cire kewa.Wannan shine kawai amma ko sau daya’ ko da wasa? ban hadu da yarinyar da tasha gaban ki ba, ba

macen da naso data taba zuciyata kamar ki duk da kuwa na dawo na tarar kin auri dan’uwana na zafin abin amma son”yana nan sai lokacin

da Bahijja ta shigo rayuwata shine a hankali’na

nemi’ son da nake maki na rasa saijin haushinku da zafin abin da kuka yi min shi ma lokaci guda na nemeshi na rasa na’ tsinci kai na a cikin sabuwar duniyar so, Wanda ban taba ji’da gani ba naji ashe son da nake maki ba komai bane ba mai dadi bane.akan wanda nake ji a Bahijja!

– Dadin son Bähija shaukim son” Bahijja’ daban

yake wani abu ne mai sanyi da dadi mun yi rayuwa mai mutakar dadi da sanya junanmu farin’ ciki wanda lokaci guda kika Shigo rayuwamu kika wargaza shi,kika mai da mana mai cike da kunci da muni cike da sabani da rashin fahimta Wanda ya haifar mana da tsananin kin juna tare da jin zafin juna. Don haka kada ki taba zaton Wani abu daga gareni, Hakkinki na aure zan baki ‘amma kada ki yi zaton da  sauran so ko wani abu da ya taba hada mu,don’ da ina da ikon juya baya na goge son da na yi maki da duk wani abu da ya faru da ya faru’ tsakanin na goge,sai dai bani da ikon haka zan ‘ci gaba da zama dake albarkar iyaye da aure ba zan wulakanta ki ba sai dai ki sani bazan lamunta ba idan kin nemi daga min hankali ko yimin shishshigi a rayuwata? Don haka yau ce rana ta karshe da Zaki sake kara tuhuma ta’ karki sake tara ta kina min magana kamar Wani dan ki, duk abin da Kike so kike bukata kina” iya zuwa ki tambaya Ki’ kuma

nemi duk abin da yake hakkinki a kaina zan yi maki shi zan kuma biya maki bukatarki na debe

maki sha’awarki da kare mutuncinki,sai dai ki sani

ni dai bana bukatar komai daga gareki.yana gama fadin haka ya juya ya tafi, ya kyaleta,

Ta bishi da kallo cikin takaici da mummunan

bacin rai da kunar zuci.A yau ne ta kara ganewa

cewa lallai bata san Deeni ba jinsa kawai take da

kallonsa bata tunanin akwai ramar da zai fuskanceta ya fada mata magana masu daci saboda a yadda ta san shi mutum ne mai tausayi musamman akan diya mace,mutum ne mai kirki wanda a tunaninta ko da baya son ko dan tausayinta zai nuna mata so,yana son kyautatawa mace da son birgeta. yau ina, tausayin nasa da son birgewan nasa ya shiga ko dai dama itance bata fahimce shi ba?

Deeni kayi min yadda kake so ka wulakantani

yadda kake so ka nuna min babu abin da zaka yi

dani.sai dai zan muna maka niba kashin yardawa

bace har yanzu, da sauran kyan hallita ta da yarinta ta a yadda na sanka kuwa ko da halitta zan iya janyo hankalinka,dan ma ba soyyayata zan jefa maka jarabata da sha’awata a zuciyarka da dolenka ka nemi ka kuma bukace ni.

Tun daga wannan ranar Farida ta dage da gyara

kanta ya zamana bata da wani mission sai da yadda za ta janyo hankalin Deeni gareta, tun daga gyaran jiki zuwa sabbin sutura mai ja da tada hankali da kananan kaya tare da turararruka wani ma na mallakane duk idan za ta shiga ace mata na abu, kaza na mallaka né. bata wasa wurin siyensa tare da saye sayen kayan mata na karya da na gaskiya. Sai dai duk wannan kokarin nata da jajircewar nata bai biya mata bukatarta bah aka za ta sha gayunta daga sama har kasa mai daukar hankali ta zo gefansa ta zauna tana rangaji amma ko kai ya daga kai balle ma ya kalle ta sai ya ga dama wani lokacin ya kaleta ya kau da kai saboda ya gane manufarta

Wani yammaci ya dawo daga harkokinsa ta

tareshi da irin shige da abubuwan jan hankali da tasaba ya kalle ta yayi murmushi har abin ya bata

mamki ya ce “*Farida ke nan,Faridan Deeni”

Wani suna da yake gaya mata da a baya ke nan

zamanin kuruciyarsa ta kalleshi tayi fari da

idanunta dadi ya cika tayi saurin adawa jikinsa

tana murna ta ce ®* Allah har ka tuno min da wata rayuwa da mukayi a baya?”

Ya ce “Gashi wannan rayuwa kuwa ta wuce

HAR ABADA”

Haka sai dai kuma ba zai gaza sake gina wata

ba wacce tafi waccan??Yayi mata wani irin kallo ya ce *’Anya kuwa Farida akwai wata rayuwa da nake son ginawa har yanzu ina da muradin da shaukin ginata da wannan macen ta daban wacce ba irinta kuma ba ayi irinta ba,amma a wurina SHAUKI NAce RUHI NAce”ya lumshe ido yana hango kyakykyawar fuskarta me cike da annuri da natsuwa tare da kamala ya dinga jin sabon son ta da kewarsa yana ratsa shi MISBAH na ina kike?7? ya fada, a tunaninsa a zuciyarsa, ya fada ashe bai sani ba a bayyane ya fada, stab

Tuni kishi yayi awan gaba da Farida saboda

Tasan dawa yake sannan ya bude,ido.yace me yasa kika rabani da shaukina da jin dadi, na? me yasa ki ka jawo mummunan, fahimta; da, kashe min dukkan wani shauki da jin, dadi, na?duk wata soyayya da nishadi da jin dadi na zuciya da rayuwa duk, babu shi, a tattare da ni yanzu, ba ki kyauta min ba Farida sunkiyar, da kai tayi kishi da haushi nacinta ba yadda ta iya wai shi har gobe Deeni ba zai taba bata matsayi da burin da take muradin samuba duk kokarinta da nacinta, da hanyar tsiya da arziki ba wanda bata bi ba,To shin  wanne irin so ko kauna ce da shauki da Deeni keji game da Bahijja wanda yasa kullum kwanan

duniya kara karuwa yake.kuma ya kasa

bawa ko wace irin mace matsayinta meye, sirrin

soyayyar Bahijja da Deeni wanda duk mummunan

rashin fahimtar da ya faru da suka rabu amma

shaukin bai gushe ba. Deeni, ya _katse mata tunani dacewa**Farida kishirya zaki rakani wata unguwa” nan da nan ta fita tana murna ta ce bari naje, na shirya,  Cikin kwalliya sosai ta fita, tana yauki,suka fita daga shi sai ita, ta ga dai sun shiga, wani gida, anyi musu iso a falo da gabatar musu da kayan ci da sha kala kala ita dai ta zura, ido, ta ga, gidan su, waye suka zo da alama dai gidan ya nuna, na masu hannu

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *