MOON CHAPTER 5 BY NIMCYLUV

MOON CHAPTER 5 BY NIMCYLUV

               Www.bankinhausanovels.com.ng 

Yadda jinin ki fita a bakin Deen yasa Moon ta rikice,da sauri ta miƙe tare da ƙarasawa wajansa tana zuwa ta rungome sa tana kuka tare faɗin “Noo! Dad please stop kada ka kasheni da raina,idan na rasaka ban san yaya zan yi ba,am so sorry Dad I’ll never ever broke your heart over my died  body”. runtsa idanunsa yay da ƙarfi yana jin yadda zuciyarsa take beating kamar zata faso ƙirjinsa ta fito, yasan she never understand his felling,tayi ƙarama da yawa ba zata taɓa fahimtar abinda yake damunsa a zuciya,Dollynsa she’s still young,yaya zai yi da zafin haɗi da ciwon da zuciyarsa take masa? Ƙara runtsa idanunsa yay yana datse harshen sa haɗi teeths ɗinsa,komai ya fice masa a raie he need her, Dollynsa yake buƙata he need her on his life,baya jin zai ƙara tafiya ya barta kansa ya kifa a bayanta ya shiga fesar da numfashi tare sauke ajjiyar zuciya banda vibration babu abinda jikinsa yake,idan har ransa ya ɓaci

babu mai iya control ɗinsa sai Besty idan kuma baya kusa karatun Alkur’ani kawai ke sawa yaji zuciyarsa tayi masa sauƙi,cikin ƙarfin hali ya shiga ƙoƙarin ganin ya furta mata wani abu yana rawa da bakinsa hƙransa na datse da ɗan ƙarfi kuma yace “Dolly take my phone” Moon na jin abinda yace tayi saurin ɗaukan tabfatsetsiyar wayarsa mai ƙirar iphone 12 max pro, fuskarta cike da hawaye duk jikinta rawa yake tace “Dad gata” fesar da iska ya ƙarayi yana danne ƙirjinsa cikin wata murya very slowly yace “goto audio” da sauri ta fara lalubar inda application ɗin audio yake tana zuwa cikin audio taga kusan rabin audio ƙira’ar Alkur’ani ne ta Sheikh Sudais da kuma sauran malamai sai kuma waƙoƙin larabci dana India, kallon yadda yake dunƙule hannunsa tayi tamkar zai kai mata naushi tace “Dad na shiga” idanunsa a lumshe duk jijiyoyin dake saman kansa sun firfito waje sun yi raɗa²,a zafafe yace “find any  suraah” rasa surar da zata shiga tayi kawai saita nufi Suratul Khhafii kana ta ajjiye wayar saman kujera, lumshe idanunsa ya ƙarayi ya fara sauraran ƙira’ar Alkur’anin wacce ta fara ratsa jikinsa zuciyarsa ta fara sanyi,a hankali ya ware hannayensa da suke a lumshe,da sauri da sauri kuma ya maida numfashi ta tsakanin wuyanta lamoo tayi jin kinsa ta kasa mutsawa sbd wani riƙo da yay mata,gaba ɗaya ta tsorata da yanayin Dad ɗinta,ko dai shima yana da abun da Feenerh ta keyi? wanda idan suka tashi take ta ihun, Lokacin da karatun yazu dai-dai aya ta 9 ina ake cewa

أمحسبت أن أصحب الكه‍ف والرقيم كانوٱ من ءاتنا عجبا.

Jikinsa yay very weak ya shiga lumshe idanunsa yana jin zucyarsa nayi masa sanyi yana samun nutsuwa,a hankali kuma ya gama ware hannayensa da suke a dunƙule ya shiga sauke ajjiyar zuciya da sauri da sauri,sai da karatun yay kusan rabi sannan ya miƙa hannunsa a hankali ya stop na karatun tare da kashe wayar gaba ɗaya sbd message ɗin Damus dake ta shigowa tun ɗazo, kuzarin dake jikinsa gaba ɗaya ya tattaro tare miƙewa tsaye da ita a jikinsa kai tsaye harabar Makarantar ya nufa, ganin yadda students suke kallonsa yasa ya haɗe ransa tamkar wanda aka sanar masa da cewa Besty ya mutu, principal ɗin dake ƙoƙarin shigowa ne yay saurin kallon Deen yace “badai tafiya ba?” Ba tare daya kallesa ba yana lumshe idanunsa yace “Noo! I’ll be back soon”wajan wata Mota bugatti wacce take da kalar blue black,yana zuwa wajan motar ya direta tare da buɗe ƙofa, kallonsa tai taga bama ita yake kallo ba hakan yasa tayi saurin shiga gaba ta zauna, rufe ƙofar yay ya koma side ɗin drever,a zafafe yake taka ƙafafuwansa kamar mai shirin yin gudu,duk yadda ya kejin zuciyarsa babu daɗi amma hakan bai sa ya fasa tafiyar daya saba ba wacce ta zame masa jiki,yana shiga motar yay mata reverse ya jata da wani irin speed yabar makarantar, gudu kawai yake a saman kwalta har ya isa wani haɗaɗɗan park a ciki yay parking ɗan haɗe laɓɓansa yay yana jin yadda kansa yake sara masa,a hankali kuma yaja numfashi haɗi da ware idanunsa waje yana ƙarewa park ɗin kallo, taɓe baki yay a hankali kuma ya fito daga cikin motar bayan yabar motar a kunne sbd baccin daya ɗauke Moon yasan tana da saurin jin zafi hakan yasa habar motar a kunne amma dai ya saka mata key, da blue eyes balls ɗinsa ya shiga kallon wajan kafin a hankali kuma yasa hannunsa ya ware ribbon ɗin daya ɗaure gashinsa dashi,gashin ya sauka har baya da kuma gefen fuskarsa,cikin nutsuwa yake tafiya harya iya reception bai tsaya wani abu ba ya huce vip side kai tsaye wajan Swimming pool ya huce special side ne kusan babu kowa a wajan koda kuɗin ka ba kowa ake bari yaje wajan ba,cikin nutsuwa ya fara cire kayansa ya rage daga shi sai farar singlet da kuma wanda 3gauter ya shiga cikin ruwan yana lumshe idanunsa, bakinsa ya hura kaɗan ya rufe idanunsa slowly ya fara nutsu cikin ruwan baka ganin komai sai fitar numfashinsa shima sanadin ƙananun ƙwaiƙwaye dake ta cikin ruwan zaka fahimci haka,daya tuna hannun Farouk daya taɓa Dollynsa dashi saiya ƙara nutsewa cikin ruwan,masu kula da wajan kowa yana harkar gabansa,amma mutum ɗaya mai suna Joseph yana kula da sanda Deen ya shiga cikin ruwan,a hankali ya duba agogon hannunsa yaga kusan 10minutes left da shigar Deen cikin Swimming pool ɗin amma ko ɗagowa baya yayi, miƙewa yay yaje har bakin Swimming pool ɗin, idanunsa ya fara yawo dashi a cikin ruwan amma ko alamar Deen bai gani ba, Deen idanunsa a lumshe yake nutsewa cikin ruwan har yaje ƙarshen ruwan, tunawa da Maganar Moon da take cewa “Dad nima ance ana sona”kuma ta gwada masa kissing da akai mata yasa da sauri ya buɗe bakinsa da idanunsa ruwa ya fara shigewa cikin su, Joseph mamaki ne ya kamasa amma bai ce wani abu ba yana tsaye yana kallon Sarautar Ubangiji,da sauri ya fesar da numfashi yana sauke ajjiyar zuciya jin numfashinsa, hannunsa ya ware tare ƙafafuwan sa ya fara yin iyo tare da yowa sama,harya fito bakin ruwan,yana fitowa Joseph ya miƙa masa sabon towel ya shiga goge jikinsa,sabbin kaya ya amsa rigace armless da wani long jeans mai kyau,yana gama sawar ya fice daga wajan kansa da sumar ƙirjinsa na ɗigar ruwa,a reception ya bata A.t.m suka ciri kuɗin su,da gudu-gudu ya fito da ciki zuwa wajan motarsa idanunsa yay jajirrr sbd ruwan daya shige masa,sai yanzu yake jinsa fresh ya samu nutsuwa,har yanzu bacci take kallo guda yay mata ya ɗauke kansa,da sauri ya fara murza kan motar har ya fice daga cikin park ɗin. Kai tsaye wajan wani babban Mall ya shige da ita nan ma bai ta sheta ba,babu jimawa ya dawo da wasu securities da suka dauƙo masa kaya a cikin Boot suka sanya masa, kuɗi masu yawa ya basu bai jira jin gdyar da suke masa ba yaja motar da gudu,sai wajan magrib ya dawo da ita cikin makarantar,sai mistsika idanu take wanda sukai mata nauyi  sabida yawan baccin da take,a hankali ta juya kanta zuwa direction ɗin da Deen yake da sauri ya ɗauke idanunsa daga kanta yana ɗan haɗe rai, kwaɓe fuska tayi tana turo ƙaramin bakinta wanda yake ɗauke da jajayen laɓɓa masu kauri da da ɗan faɗi sunyi kyau sosai,tun kafin tai magana yay saurin fita daga motar ganin hakan yasa itama ta fita,da sauri ya fara tafiya zuwa hostel na jss section yayi nisa yaji baya jin ta kunta a bayansa tsayawa yay cak tare da juyawa,tsaye ya ganta ta ɗaga kanta sama tana kallon wata bishiya sai dry take kai ka rantse shira suke da bishiyar, harɗe hannayensa yay ya zuba mata narkakkun idanunsa wanda suke a janye sbd damuwar da yake ciki,a hankali yaga ta fara tafiya zuwa wajan bishiyar tana gaf da ƙarasawa wajan bishiyar yaji ta fasa wata gigitacciyyar ƙara haɗe dayin baya ta faɗi a wajan babu numfashi,cikin zafin nama ya ƙarasa wajan yana faɗin “Lolly!!! No please Dolly!!” Yana faɗin hakan ya ƙara kwasa sa gudu abinka da wanda bai saba tafiya a nutse ba,yana zuwa yasa hannunsa gaba ɗaya ya ɗauke,a hanya suka haɗu da principal daya fito daga side ɗinsa Kasancewar gidansa a cikin makarantar yake, kallon Deen yay wanda yake ƙoƙarin komawa da ita cikin mota yace “ka ɗauke ta lokacin ɗaukan karatu,yanzu kuma ina zaka? Zaifi kyau ka mai data ga makwancinta” ko kallansa Deen baiyi ya nufi hostel ɗin su Moon a  coner farko su kaga Head grill ɗin su Moon ta da tare da Yasmin,da sauri Yasmin ta saki head grill ɗin mai suna Haneefa tabi Deen da kallo tana ƙara ware idanunta, a hankali ta furta “GATEKEEPER” sarai ya jita kuma yasan ko wacece ita,amma ko a jikinsa kai tsaye ya shige part ɗin su Moon yana zuwa ya samu Feenerh tayi bacci kwantar da Moon yay,kana ya ɗura kanta a saman cinyarsa a hankali kuma ya zare hijab ɗin jikin ya fara shafa sumar kanta,kallon principal ɗin yay Murya kamar an masa dole yace “ƙaro A.c,and close the windows” dukkan abinda yace haka yayi,wata wahalalliyar ajjiyar zuciya ya sauke lokaci ɗaya kuma ya fahimci abinda ya samu Lollynsa,buda da yadda yaga goshinta yake fidda zufa, yasubuhanallah! Wacce lukutar masifa ce haka, ƙaramar yarinya da irin wannan abun tayaya zata jure zama da aljanu a jikinta? Bakinsa ya ɗura a saman goshinta da sauri tayi miƙa kafin ya janye bakin ya maidasa saitin kunanta, hijabi ɗin ta ya ɗauka ya ɗura saman goshinta ya shiga murzawa, cikin zazzaƙar  muryarsa mai ratsa zuciya ya fara yin Bisimillah! Kafin ya ɗura da karatun suratul Baaƙhara shafin.

وٱتبعوٱ ماتتلوٱآلشيطين على ملك سليمن.

Miƙa ta farayi bakinta ya shiga fitar da kumfa,duk yadda yay karatun Kur’anin ƙin mutsi sukai sai juyi kawai da take saman cinyarsa gumin wahala na yanko mata,daya matsa da karatun ma kawai sai a tishawa suka gudu hakan na nuna cewa basu ma da Lokacin tsayawa aji dalilinsu na shiga jikinta bare a nemi sulhu dasu,suna guduwa ita kuma bacci yay gaba da ita,da jajayen idanunsa kawai yake kallonta shi sai a lokacin yaga girman data ƙara halittun ta na ƴar mace tun sun bai yana sai raguwar girman,fesar da iska yay a hankali kuma ya zameta daga jikinsa ya kalli principal ɗin kamar bazai magana ba sai kuma yace “okey! Dama akwai su?” Girgiza kai principal ɗin yayi yace “ko kusa ko alama bata taɓa yi ba sai yanzu”taɓe baki yay bai ƙara kallon principal ɗin ba ya nufi wajan wardrobe ɗinta shi kuma Principe ɗin yay waje abinsa,wasu fararan kaya ya ɗaukar mata masu kyau riga da wando,gefen gadon ya zauna tare da jawota jikinsa ya zare mata rigar jikinta yana jin yadda ta sauke ajjiyar zuciya duk abinda yake idanunsa a lumshe suke bai yarda ya buɗe ba,sai da ya sanya mata kayan kana ya ɗauke na jikinta ya ajjiye can gefe guda,tsaye ya yi a kanta yana kallonta ko ƙifta ido ba ya yi, agogon warist ɗin sa ya duba yaga time yaja ko Isshā baiyi ba, durƙosawa yay ya shiga yi mata karatu idanunsa akan fuskarta sai faman haɗe rai take tana turo baki gaba, tattausan tafin hannunsa yasa ya shafa mata addu’ar,hasken ɗakin ya kashe ya ƙaro gudun ac sosai Sannan yaja masu ƙofar ya fita. Washegari da safe ya kasance weekend Moon basu da class tun safe data farka take ta mmkin yadda kayan bacci yaje jikinta, zuciyarta cike da tsoron Allah yasa Dad ɗinta ba tafiya ya kuma yi ba,bayan tayi sallah tai wanka ta ƙara komawa bacci, Feenerh kuma tana shirya wa ta nufi wajan Amira domin tayi mata kitso,can cikin baccinta taji ana ja mata hanci slowly ta fara buɗe idanunta tana rufewa a haka harta samu damar buɗe idanunta sosai a saman fuskarsa,waro ido waje tayi mmki,yana sanya da wani tissue ɗin boyal black wanda akaiwa ɗinkin riga half body mai ƙaramin hannu,ya ɗura wata half ɗin jaddara mai shegen kyau,sumar kansa ta sauka har wuyansa yay wani bala’in kyau tunda take bata taɓa ganinsa a shigar manyan kaya ba sai yau,hatta ga ta kalmin ƙafarsa jaaa ne shima half covert shoe mai gashi,ga wani watch ɗin iphone dake maƙale a hannunsa, idanunsa ya ɗauke a kanta yana faɗin “stop staring at me” turo baki tayi tace “Dad you look like Akbar na film ɗin Joda & Akbar” shiru yay mata ita kuma taci gaba da faɗin “Dad Allah kuna masifar kama sosai” taɓe baki yay yana miƙewa tsaye can kuma yace “ke kika san shi” sakkowa tayi ta kama hannunsa tace “Dad zaka tafi dani ko?nifa na gaji da Wannan makarantar” waro manyan idanunsa yay waje idanunsa a ƙofa kamar da ita yake maganar yace “Au! Lawyern fa?” Hawaye na ya fara sakko mata tace “to stay with me please Dad” Tofa anzu waje,shi yama rasa me zai farayi ga message ɗin Besty saya samesa jiya da yake cewa _Besty i missed you soo much,Nasan kana fushi dani ne but Aliyou ni nasan nai maka gata ne,ina son idan harni na haifeka ba riƙon ka aka bani ba,ba tsintar ka nayi ba to kazo gobe bai ɗauke maka ba, your father *~ENEYE AHUOYZA~*_

Abu na gama message ɗin da Damus yay masa inda yake faɗin. _Oga Deen kayi good 2years amma babu wani impormation about the girls,Oga Taju yace yana buƙatar yin meeting dake a Zoom tomorrow by 12pm zaku tattauna akan ɓatan yarinyar Moon dan kai yake zargi,dan haka ka tanadi hujjarka idan har baka dashi yana iya sanyawa azo tunda daga PAKISTAN zuwa Niger ai cire masa kanka kasan wannan ƙaramin aikin Taju ne, babban kuma zai iya ɗaureka a hankali ya dinga yankan nama jikinka, zan tura baka sa code na meeting ɗin tare da link_

Ga kuma rabuwa da Moon da zai yi yanzu,dole ya sassauta fuskarsa ya tattaro duk abinda ya iya ya bata nishaɗi kafin ya tafi, ajjiyar zuciya ya sauke kafin yace “Lolly ƴan mata sai Aure” ƙafa ta fara diddorewa tana sakin kuka “Dad ni bazan aure babu kyau fa” buɗe ido waje yay yace “laaa injiwa??” Turo baki tayi tace “kawai nidai,bayan ance wasu basu riƙe Aure da daraja, inaji Amira tana faɗin sister ɗinta ko good 3mounth ba tayi da Aure ba mijin ya saketa,wai baya bata abinci sannan baya sauke mata haƙƙinta” fito da idanu waje yay sosai yace “meye haƙƙi” shiru tayi kamar bai tunani sai kuma tace “nima ban sani ba” haɗe rai yay sosai kana yace “look at me Dolly,bana son kina zama kina jin wannan zantukan kinji ko, kuma ko wanne zai maki wani wakan kici masa uwa, bance rashin kunya ba a’a babu kyau rashin kunya gana gaba,ki zama kamala da nutsuwa,ki zama mai hqr da jajircewa,ki zama mai ra’ayin kanki kuma kaifi ɗaya,kada ki yadda wani yace zai sauya maki ra’ayi,ki zama tsare mutuncinta gida da waje, And ki rage wannan surutun naki” ya faɗi maganar yana sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya ya daɗe bai magana bai tsayin wannan ba,kana ya ɗura da faɗin “ko hannu mace ta bari wani ƙaton ya riƙe mata to ciki take ta haihu,wata ma ta mutu”da sauri ta zaro ido tana dafe ƙirjinta dry taso bashi dake bata damesa ba ya haɗiye abarsa yace “Eh! Sosai fa,dan haka ki kama kanki ki riƙe al’ƙawari dukkan wanda ya saɓa al’ƙawari bayan ya ɗauka to shi da Allah!,akwai hijab ɗin dana sauyae maki na makaranta kada ki ƙara sanya wannan guntun hijib ɗin understood?”ya faɗa ya fito da ido waje,kaita gyaɗa masa sakin fuskarsa yay yace “I’m coming Lolly, please keep the promise kada ki saɓa”kuka ta saka masa da sauri ya lumshe idanunsa yace “I’ll be back Dolly, tabbas zan dawo a ko wanne lokaci kisa wannan a ranki Dad ɗinki na tare dake” kuka tasa masa tare da maƙale sa,shiru yay yana bubbuga bayanta cikin nutsuwa Kuma ya fara rera mata waƙa;+

_🎸🎻 I am a Muslim child, I will never see him for my money for Thailand for Daddy was with my neighbour🎻🎸_

Shiru tayi tana jinsa kafin ya ɗura ta

_🎻🎻 tinkle tinkle star up I wonder was just her like a diamond in the sky🎸🎸🎸_

Dry ta farayi tace “Dad kai ma a School ka iya ko?” Gemunsa yaja yana ɗaga mata kai ƙara rungomesa tayi tace “I’m going to miss you Dad ” kanta ya shafa yace “sama to me Lolly ALLAH ya sa maki albarka, barakallahu fikiii Maimunatou” shiru tayi shi kuma a hankali ya ɗago haɓarta tare da sanya mata ƙaramin yatsarsa a cikin bakinta yace “take a sweet” lumshe idanunta tayi a hankali kuma ta fara jan yatsarsa ta suma tsotsa kamar alawa, runtsa idanunsa yay yana jin yadda tsigar jikinsa me tashi ga kuma yadda take jan yatsarsa kamar zata zuƙe masa jinin jikinsa,da sauri ya zare yatsarsa ya rungome ta yana maida numfashi kafin ya bata peak a forehead ɗinta, muryarsa na rawa yace “love You Lolly” kasa magana tayi har ya fita daga ɗakin yana fita ta faɗa saman gado ta fashe da kuka hadda birgima.Da sauri da sauri yake taka ƙafafuwansa a cikin gidan Sarautar duk inda ya ratsa barori da kuyangi da hadimai sai fadawa ne suke zubewa ƙasa suna gaishesa,amma ko kallon arziƙi basu samu ba daga garesa ba,kansa a ƙasa yake tafiya yana baza farar alƙyabbar jikinsa wacce tasha ado da wani kallar zare,ya ɗura hular ƙarfe a kansa daga sama an ɗora gashi,Beaty na zaune shida matarsa Nene suka fara jiyo ana bal da abu,kafin su miƙe Deen ya shigo cikin parlour’n da sauri kamar an cillosa, miƙewa Nene tayi tana kallonsa kafin tayi magana ya nuna ta da yatsa jikinsa duk rawa yake yace “what is this Mom???” kasa magana tai ita ta haifi yaro amma sam bata haifi halinsa ba,ace mutum bashi da aiki sai zafin zuciya baya gani girman kowa sai wanda yay niyya ga rashin hqr da nunƙufarcin tsiya, alƙyabbar jikinsa ya cire yay hurgi da ita kana ya cire hular ya jefar ya rage daga shi sai farar armless mai ƙyau an rubutu Lolly da manyan baƙi a jikinta, kallonsa kawai ENEYE yake yana mamaki zuciya irinta Deen, numfashi ya sauke yace “Wlcm Besty come in” wani kallo Deen yaywa mahaifinsa yace “Ni zan shigo ciki? GOD FORBID” yana faɗin hakan ya juya ya fita da sauri murmushi Besty yay yace “Congratulations Besty now Moon is ur wife Moon matar kace” da wani sauri Deen ya juya ya fara kallon mahaifinsa,kai ya gyaɗa masa yace “Yeah!! Na san i made a mistake but now i understand Maimunatou matar kane tun ranar daka bar gida aka ɗaura maka Aure da ita….

Team Deen where are you????🤣🤣🤣Da Capital letters Moon is your wife Besty,so stay with your parents ko albarkacin hakan”kasa magana Deen yay idanunsa akan bakin mahaifinsa yana jin maganar tamkar a mafarki,tayaya za’ai ace Lolly matarsa ce? Yaushe aka ɗaura auren? Suwaye waliyyan Moon ɗin? Ganin yadda Deen ke kallonsa yasa ya fahimci bai gama gane abinda yake cewa ba,a nutse yake tafiya cikin zallar izza taƙama da haiba yana tafe yana baza alƙyabbar jikinsa,a gaban Deen ya tsaya yana sakin Murmushi kafin ya sanya hannunsa ya kama hannun Deen ya jasa suka fara tafiya har zuwa wajan wata lafiyayyiyar kujera,zama yay kana ya zaunar da Deen kusa dashi,cikin ƙasa da murya da kuma tattausa harshe yace “Aliyou!!!!” Shiru Deen yay kansa a ƙasa yana da sauke ajjiyar zuciya,kalmar matar kace taƙi gushewa daga cikin kunansa, Eneye ya ƙara cewa “Aliyou!!!” Can ƙasa Deen yace “Abba” girgiza kai Eneye yay yace “Noo!! Besty bana son Abban nan,kace kawai Besty nasan idan kace Abba kana fushi dani ne” Jinjina kai kawai Deen yay  ba tare da yay magana ba, numfashi Besty yaja a hankali kuma ya sanya hannunsa ya jawo Deen zuwa jikinsu ajjiyar zuciya suka sauke a tare,cikin lallami Besty yace “Bana da wani sama da kai,kai nake gani kawai naji daɗi,tunani na kai ne,idan nai farin ciki anyi min maganar ka ne,komai na samu Besty na,to tayaya kake tunanin zan bar rayuwarka ta halaka bayan ina da yadda zanyi na fiddaka daga halin da kake ciki? Ni daman burina bai huce naga ranar da zaka furta da bakinka kace kana son yin aure ba,banda ba’a auran mace tana jaririya to tabbas ko jaririya ka nuna kace kana so babu shakka sai na aura maka ita,bare yarinya kyakkyawa kamar Maimunatou,ba haramun bane Auren macen data girmeka haka kuma ba haramun bane auran ƙaramar yarinya, I’ll do anything for you in dai zakai farin ciki,kana da ikon da zaka ɗauki matarka kaje duk inda kakeso ita ɗin mallakinka ce” wani lallausan murmushi Deen ya saki a lokaci ɗaya dimples ɗinsa da teeths gave ɗinsa suka bai yana,kasa cewa komai yay sai tasbihi da yake ga Ubangiji domin shi ne kaɗai ya ƙaddara faruwar hakan bawai wayonsa ko dabarar sa ba, blue eyes balls ɗinsa ya ɗaga ya kalli mahaifinsa nace cikin ƙasa da murya yace “but how can that happen?” Lumshe idanunsa Besty yay kamar yadda yaga ɗan nasa yay domin kusan habit ɗinsu ɗaya yace “is simple question ai,a ranar da naga kana ƙoƙarin mace min akan soyayyar ƴar ƙwailarka a ranar na sanya aka taramin mutane a acikin Masjid ɗin Masarauta,nasa Chiroma ya zama waliyyinka  ni kuma na zama waliyyin Maimunatou my daughter in-law,a ranar kuma sarkin Adamawa yazu so shi ne da kansa ya bada sadakin Maimunatou,ni kaina kuɗin yaban tsoro 5.7m fa? Amma dake ya tara kuma an tara masa sai ban damu ba,kawai na tayashi addu’ar samun cikar muradin zuciyarsa” rungome Besty Deen yay yana faɗin “Wow Best thank you so much, wlh zuciyarta na gab da bugawa” dry Besty yay yace “akan ƙwailar taka?” Baki ya turo kamar ƙaramin yaro tare da kwaɓe fuska yace “Noo!! Ta girma fa look” ya faɗa yana zaro wayarsa ya shiga nuna wa Besty photonan Moon wanda yay mata a School bata sani ba,shi dai Besty ƙuri yaywa fuskar Moon abune da yawa a ransa,sai kawai ya share domin bai son tunanin yay tasiri a ransa, Nene dai sai Murmushin jin daɗi take sbd farin ciki data hango saman fuskar ɗan nata, miƙewa Deen yay ya ƙarasa wajanta yana zuwa ya rungome ta,kansa ta shafa zare jikinsa yay yace “lemme freshen up” murmushi su kai masa yana ƙoƙarin shiga flat ɗinsa da aka rubuta *OSOHINOYI FLAT* (Yarima flat) yaji an zabga salati ana tafe hannaye idanunsa da suke kamar na mage ya shiga juyawa, Yayinda ce tsaye tana sharce majina tana faɗin “Amma ko sallamme kudai wlh baku iya haihuwa ba,ga yadda ya mayar dani gangalliya bayan nice na bada shawarar ai masa auran sbd zuƙewar da naga ya nayi,a tohh zuƙewa mana yaro jaraba nata cinsa a rai amma babu wanda ya gano sai ni sbd baiwar da Ubangiji yay min,banda baiwa ta Ubangiji tayaya zan iya ganowa Danoo aure yake so fisabilillahi? To dai babu ruwana Wlh,duk wanda ya raina uwar wani tasa ya raina,domin uwa ba tafi Uwa ba” tsaye sukai suna kallonta Deen kam haɗe fuska yay bai taɓa jin kunyar iyayensa ba amma yau tasa yaji, juyawa yay ya nufi cikin tamfatsetsan flat ɗinsa, kuka ta saka masu tana ƙara sharce majina tace “kuna dai kallo ko?? Ɗan rungomar da yay maku yake baƙin cikin yay min,to wlh ta Allah ba ta ka ba wannan shegen jikin naka ma me za’ai dashi?kuma shawarar dana bayar kaje ban yafe ba” shi dai ko takan Yayinda bai biba ya shige flat ɗinsa yana taune leɓansa,Nene ce ta kalli Yayinda tace “Ayyaa! Momma ki san halin jikan naki muma baya raga mana bare ke da kike kaka wajansa” cikin kumfar baki Yayinda tace “Yau nake ganin ɓatan nono a ƙirjin budurwa,to ko a suwa? Me akai akayi ko?nace wacce shararce ko? Basai ya gimamani bai girmamaku banda lalacewa ta yaran zamani har Aliyou ne zai mance hallarcin da nayi masa,yay kashi na wanke ya tunbuɗi na wanke,haka zan ɗaga shi sama ina masa rawa ina _caka masinka ɗan Baba,nace caka masa kinka,_ amma yau Danooo ni yakewa baƙin cikin rumgoma dake ya haɗu da sallamammun iyaye suka zoba masa ido,toni ba gantalalliya bace wlh gidan zan bar maku” daga Besty har Nene kasa magana sukai domin sun fahimci yau rikicin tsofanne ya mutsa,dole Nene taja baki tai shiru tana kallon Yayinda ta nufi flat ɗinta tana share majina,Deen na shiga falt ɗinsa shower ya sakarwa kansa,yana jin zuciyarsa tayi masa wasai ciwon daya keji yanzu babu shi,kwanciya yay saman babban royal bed ɗin sa, babu komai jikinsa sai boxer haka yaja pillow ya rungome cikin ƙaramin lokaci bacci yay gaba dashi wanda rabinsa mafarkin Lollynsa ne. Washegari a makaranta ya kasance Monday tun asuba da Moon ta farka bata koma ba,sai ta zama very weak ta zama wata miskila ko magana sai Feenerh tayi da gaske take baya feedback,a haka suka shiga masjid bayan sun fito suka komai Hotel, ruwa ta ƙara sakarwa jikinta kana ta fito a nutse ta fara shirya sai da ta gama sanya uniform waro manyan idanunta waje tayi sbd hijab ɗin da Dad ɗinta yace ta dinga sauya ya zarce tunaninta domin har gwuiwarta ya sakko, dry Feenerh tayi tace “a’a kaga matar malam Mamman,wannan ai da ake bawa Amira domin zaki fi dacewa da ita” harara Moon ta watsa mata idanunta ya cicciko da ƙwalla harga Allah bata son saka hijab ɗin,kaf school ɗin ita kaɗai ce mai babban hijab wasu ma haka suke tafiya babu ko hijab ita kuma sai ta ɓuge da saka wannan kamar wata Malama?yanzu gashi ya riga ya tafi bare tace ya sauya mata wani,ita akan wanne dalilin ba zai ɗauke mata nata ya bata irin na mu’allima,tana cika tana batsewa ta ɗauki school bag ɗinta ta shige class tunda yanzu ba class ɗinsu ɗaya ba,tana zuwa cikin class ɗin data prioud ɗin farko Faizak ne ga mamakin ta kowa ta samesa a class ɗin, agogon hannunta ta duba taga 8 saura 10 minutes at, kanta ta sunkuyar ƙasa ta shiga wasa da yatsun hannunta tama rasa me zata ce  masa,a jikinta taji kallonta yake tana ɗaga idanunta suka haɗa idanu,gira ya ɗaga mata ita kuma ta turo baki gaba kafin cikin siririyar muryarta tace “Morning sir” idanunsa na yawo a kanta yace “mrng late comer, sleeping baby” ba ƙara magana ba ta shige cikin class ɗin wajan kujerar ta ta zauna,kan ta a ƙasa domin dictation yake masu cikin sauri take Rubutun ta cikin good handwriting ɗinta, after 10 suka fita breakfast ita da Feenerh da Amira suka jera a tare suka nufi danning hall, abinda kowa yake so aka kawo masu Moon aka bata arish da tea da kuma dankali da ƙwai,tana jin shirar dasu Amira suke akan abinda su Yasmin su kaiwa wata new student yarinyar hatta faɗa tarkonsu, Murmushin jin daɗi Amira tayi tace “ai Moon ki gode Allah,duk sanda suka so yin abinsu a kanki sai Ubangiji ya kare ki daga sharrin su” Feenerh tace “haka fa,ai shiyasa addu’a tayi a rayuwa kuma Garkuwa ce ga dukkan Musulmi” jinjina kai Amira tayi tace “MANZON ALLAH yace idan muna jin tsoran zaluncin wani mai iko mu ce”.

*بسم الله الرحمن الرحيم، الله‍م رب السموات ورب العرش العظيم،كن لي جارا من (فلان) وآحزابه من خلانقك،ان يفرط على أحد منه‍م أو يطغى،عز جارك،وجل تناوك،ولا إله إلا أنت.*

_(Ya ALLAH! Ubangijin sammai bakwai,da kuma Ubangijin Al’arshi mai girma,ka kasance mai tsari gare ni daga wane ɗan wane,da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni,ko ya ƙetare haddi,kariyar ka ta buyawa,kuma yabonka ya girma,kuma babu abin bauta wa da gaskiya sai kai)_

Shiru sukai gaba ɗayansu ita Moon sai juya tea take ta gagara shan bare taci sauran abun,Amira tace “To! Kowa dukkan wanda ya zamar da addu’a abokiyar faɗan sa a baki tayaya kike ganin zai tuzarta? Ba kuji ance addu’a makarin mumini ba?” Feenerh tace “gsky kam,shiyasa zama da mai ilimi yake da daɗi wlh,ba kowa zai fahimci hakan ba sai wanda Allah! yasa ya gane” karɓar tea ɗin Moon tayi kana ta ajjiye gefe guda tace,kafin taja numfashi ta fesar cikin ƙasa da Murya Moon tace “haka kuma Manzon Allah! yace kayi addu’a yayin gamuwa da abokan gaba kamar haka;”+

*بسم الله الرحمن الرحيم، الله‍م انا نجعلك في نحوره‍م،ونعوذ بك من شروره‍م*

_(Ya ALLAH! Mu muna sanya ka a gabansu,kuma muna neman tsarinka daga sharrace-sharracensu)_

“Ke hakan na nufin babu wata halitta data isa ta cutar dakai a yayinda kayi Wannan addu’ar,koda ta cutar dakai bawai wayonsu ya sanya hakan ta faru ba,haƙiƙa Ubangiji yay mana gata da yayomu a musulmai kuma masu riƙo da addininsu, Uwa ba kuma yadda da ƙaddara,koda su Yasmin sunyi min wani abu ni nasan cewa hakan wata sabuwar ƙaddara ce data bijiromin,kuma ance ƙaddara lokaci gareta wani lokacin sai dai ka bata labarin abinda ya shuɗe,dan kuma ka shiga cikin wata masifar hakan ba yana nufin wai ƙarshen rayuwarka ne yazo ba, a’a nan ma wani lessons Ubangiji yake nuna maka mai hankali ance shike gane ɗin gishin ƙwaɗo,to thank God! Ni Maimunatou idan har addu’a na zama gari ya to tabbas ta zama gari ya gareni domin babu abinda su Sumy suka isa suyi min” gaba ɗaya suka kalleta can kuma Amira tace “Amma wacce damuwar ke hanaki cik abincin?ina lura dake sam baki son cik abinci” murmushi kawai Moon tayi idanunta cike da hawaye tace “wata damuwa tana zama dole kayi ta,domin baka san lokacin da take faɗa maka ba,ji nake kamar zan yi rashi ina jin kamar Dad na bazai dawo gareni ba”. Da mmki Feenerh tace “kmaryay?” Ka faɗa ta ɗaga masu ba tare kuma da tace masu wani abu ba,ganin time na tafiya yasa suka miƙe gaba ɗaya su kowa ya shige class ɗinsa,a last prioud ɗin su Ass-headgril ta kalli Moon tace “Teacher Faizak yana kira a office nasa” juyawa fararan idanunta Moon tayi kamar ba zata ce wani abu ba sai kuma tace “kuma at this time?” Girgiza kai tayi tace “no yace after class” ɗauke kai Moon tayi tare da gyara farin glass ɗinta,suna gama class ta nufi office ɗinsa ta rataya school bag ɗinta,a zaune ta samesa yana operating system ɗinsa shiru tayi masa shi kam duk abinda take yana kallonta ta cikin system ɗinsa,kamar daga sama taji muryarsa yana faɗin “you look like familiar Maimunatou!!” shiru tai masa tana kallon fuskarsa amma a zahiri tunaninta yana ga Dad ɗinta,can taji yace “Yeah! Kina kama da Mai martaba sosai,ban san me yasa ba,ko ni ɗaya nake ganin kamar ohhhu! Amma duk wanda yasan Mai martaba kuma ya ganki dole zai ga kamar” da ƙyar ta buɗe bakinta tace “Ohhh! ALLAH! sarki” miƙewa yay tare da nufar inda take a gabanta yaja ya tsaya, lumshe idanunsa yay yace “su waye samarin jiya??” Idanunta wanda yake ƙara jan hankalinsa ta juya masa kafin tace “samari kuma?”kai ya ɗaga mata yace “Uhm” shiru tai masa ganin hakan yasa yace “da farko kin tsaya da wani har ya riƙe ki,na biyu kuma wani ya ɗauke ya fita dake daga cikin makaranta” sarai ta gane mai yake nufi sai kawai tace “Ohhh! He’s my father” taɓe bakinsa yay still looking in to her eyes yace “Tab, babu kama abin” da rashin fahimta ta kallesa tace “Kamarya?” Ka faɗa ya ɗaga mata yace “nothing” kafin yace “what about your family?” Kai tsaye tace “shi ne ko mai nawa ai, family, friends siblings anything” da sauri yace mata “Out” kamar jira take yana faɗin hakan ta fice,shi kuma saman sofa ya faɗa yana jin zuciyarsa nayi masa zafi,yabar baƙin ciki a can gida,tunda ya kalli Moon yaji soyayyyar ta kamashi amma ya fahimci abubuwa da yawa a tare da ita,me zai mata? Dole ne ya nemi mafita dole ya jawota jikinsa, Moon a coner su ta haɗu da Sumy da Yasmin sun sanya wata yarinya a tsakiya sai shafata suke, Sumy na ganin Moon ta saki yarinyar ta nufi inda Moon take tsaye, harɗe hannayenta tayi tana jiran zuwa Sumy,da farin ciki a fuskar Sumy ta ware mata hannayenta alamar ta isa gareta,wata uwar harara Moon ta watsawa Sumy dry Sumy tayi tace “Yasmin zoki riƙe min ita” da sauri Yasmin ta nufin wajan Moon kafin ta ƙarasa Moon ta saka wata gigitacciyyar ƙara da gudu ta nufi inda Yasmin take tana zuwa ta jata ta haɗa kanta da bango,wata gigitacciyyar ƙara Yasmin tayi sbd zafin daya ratsa ta,nan take kuma kanta ya fashe ganin hakan yasa Sumy tayi waje da gudu domin neman ɗauki,Moon na ihu Yasmin na ihu haka Moon ta danne Yasmin sai duka take.Jini kawai ke fita ta cikin bakin Yasmin da hancinta,banda ihu babu abinda take yadda yake ihu haka Moon ke ihu,gaba ɗaya sun cika coner ɗin da ihu,Sumy na fita tayi wajan teachers section a hanya ta haɗu da Faizak sai je office ɗin principal sbd kiran da yake mata,tun daga nesa yaga gudun da take hakan yasa ya ja tsaya yana kallonta,kai tsaye itama Sumy wajansa ta nufa tana haki,tana zuwa wajansa ta shiga nuna masa hostel ɗin su Moon, kallonta kawai yake yana kallon derection ɗin da take nuna masa,tsaki yaja kaɗan yace “Keee! Lfy? Mene haka kike nuna min?”. Gaba ɗaya a tsorace take da ƙyar ta shiga faɗin “Sir Moon ce,zata kashe Yasmin wlh,har ta fasa mata”. Da mamaki yake kallonta yace “Kamar ya ya kenan?”. Gaba ɗaya ta fice daga cikin hayyacinta cikin haki ta shiga faɗin “Moon ta danne Yasmin sai duka take gaba ɗaya ta fasa mata jiki”. Waro idanunsa waje yay yana mamaki tayaya ƴar Jss zata daki ƴar ss? wacce take final year ɗinta da sun gana exam zasu bar magana,kai ina hakan ba zai taɓa yiyowa ba, kallonta yay yace “muje”. Da sauri tayi gaba yabi bayanta cike da nutsuwa yake taka ƙafafuwan sa a ƙasa,tun a bikin coner yake jiyo ihunsu ga ɗalibai duk sun cika wajan, gyaran murya yay hakan yasa suka fara matsawa suna basa waje,a haka harya isa gareta tana jin alamun yasa ta miƙe da sauri haɗe da gudu, Amira ce tayi saurin cewa “Sir bata hayyacinta fa,mutananta suka tashi kada tai wani wajan”. Bai tsaya bi takan maganar Amira ko ya tsaya taimakon Yasmin ya marawa Moon da sauri harda gudu ya haɗa,yana fita ya hango ta  su principal sun riƙeta shi da wasu teachers guda biyu sai kokawa suke da ita,yana zuwa ya kalleta sai kuma ya daka mata wata gigitacciyyar tsawa da sauri ta saki su principal ta faɗi a wajan bakinta na fitar da kumfa,gaba ɗaya tsayawa sukai suna kallonta da ƙyar principal yace “what’s going on Coupe Faizak?”. Sauke numfashi Faizak yay kafin yace “What am going to say? Kawai ance ta daki wata harda fasa mata baki”. jinjina kai Principal ɗin yay yace “i understand” can kuma ga numfasa yace “ka ɗauke ta” Waro idanuna Faizak yay dan babu abinda yake tsoro irin yaga mutum ya data ALJANU, girgiza kai yay yace “bana iya wa”. Principal yace “a Kira Amira” babu jimawa aka kira Amira kafin ta ƙarasa wajan Moon,Moon ta miƙe tsaye tana goge bakinta idanunta yay jajir jikinta duk ya saki, sai zare idanu take, kallonta Principal yay yace “Maimunatou mene ya haɗaki da senior ɗinki?”.  Shiru tayi masa sai turo baki gaba take tana kumbura fuska da alama dai gama hucewa ba,kallon Amira yay yace “kuje da ita”. Moon na jin hakan tai gama abinta ga tare da ta tsaya Amira ba,da idanu Faizak ya bita shi dai ta tsaya masa a rai komanta irin na Mai martaba, idanunsa yaji ya kawo ruwa da sauri ya ɗauke kansa tare da nufar office ɗinsa,sam koda wasa baya son tuna abinda ya huce,yana jin zafi da kuma raɗaɗi a ransa,yana zuwa ya kwanta saman sofa tare rufe idanunsa yana shafa gemunsa,wayarsa ce ta fara ruri wani kiɗan algaita ya fara tashi ga wata sarewa da musamman a cikin giɗan, answering call ɗin yay cikin ƙasa da murya yace “ALLAH! Ya tai maki Mai martaba” Murmushin jin daɗi Mai martaba yay yana ƙara kwanciya a jikin wasu manyan cosion masu kyau,kana ganinsa kaga na gartaccen mutum,zallar kyau da haiba komansa a nutse yake,cikin muryarsa irin ta masu sauran yace “how’re you son?”. Faizak yace “ALLAHAMDULILLAH!” Jinjina kai yay kamar bazai magana ba sai kuma yace “fatan ka cire damuwar?”. Kamar Faizak zai kuka yace “Eh” Mai martaba ya sauke numfashi yace “Bravo! Ka kula sosai” cikin ƙasa da murya Faizak yace “still babu wani impormation ko Mai martaba?”. Lumshe idanu Mai martaba yay a hankali kuma yace “just pray,komai zaiyi dai-dai” wasu hawaye ne masu zafi suka sakkowa Faizak yace “In sha Allah”. Sai kuma sukai shiru gaba ɗayan su na wani lokaci kafin Faizak yay Murmushi yace “You know what Mai martaba?”. Girgiza kai Mai martaba yay tare da lanƙwasa ƙafafuwansa fuskarsa cike da fara’a yace “uhm” Faizak cikin farin ciki yace “Mai martaba yau ALLAH! ya nuna min mai kama dakai,kamar kayi kaki ka tofar,in da kasan kai ka haifeta” Murmushi kawai Mai martaba yay yace “zaka soma ko?baka tunani zai na abubuwan da suka shuɗe to sai an jima,and ka dawo kafin ranar Fulanin duniya (Fulanin worlds day)yazo” yana faɗin haka ya kashe kiran. Deen kwance a makeken royal bed ɗin sa,yana sanya da farar shirt sai faffaɗan ƙirjinsa dake waje wanda ya cika da yalwataccen gashi,yau kwanansa uku kenan da dawowa,amma gaba ɗaya baya cikin hayyacinsa burinsa bai huce yaga Lollynsa ba,haka kuma baya son takura Besty sbd yay masa halarci,yay masa abinda ya dace a ce duk Uba na gari yaywa ɗan sa, Amma ya ya zai yi da rashinta?? Lumshe idanunsa yay yana fidda numfashi,a hankali kuma yaji ciwon da cikinsa yake masa yana ƙara yawa, mirginawa gefe guda yay tare kifa cikinsa ya rungome pillow, hannunsa yasa ya mararsa dake masa ciwo a hankali kuma ya saki wani sauti mai ɗan ƙara “Auchhhhhi!!! uhmmmm” Yayinda dake bakin ƙofar bedroom ɗinsa ta saki salati tana tafe hannaye tare faɗin “Mahammadur Rasulullah,ashe da gaske ake nima ni Faɗimatu, a’a Wlh babu ruwana ba zaka zame bana masifa a cikin gida ba,azo ana yi damu duk inda muka huce a dinga cuna mana baki ana,gasu can wanda ɗan su ya mutum sbd masifar dake damunsa,Ohh Oohhh! Ai ban yarda zan can Kunyaga Ramla ba sai yau ɗin nan,ai ba gulma gsky zan faɗa maka da kaje ana shunaka gwamma na faɗa maka gsky,uhm rufin asiri dai nada daɗi amma tunda jikana na faɗawa ai na rufa mata asiri, tunda dai har al’ƙawari na ɗauka ai zan tuba ne,Astaga firr firr namijin tuba” da sauri Deen ya juya ya kalleta fuskarsa cike da mmki,yasan cewa ko Besty idan zai shiga flat ɗinsa sai Amintacciyar kuyangarsa tayi masa magana amma gashi da shigo masa,kasa ce mata komai yay sai kansa daya mayar saman pillow tare da lumshe idanunsa kamar mai bacci,Yayinda ta ƙara leko kanta sai kuma ta zauna gefen bed ɗin tare da rafka ta gumi tace “To dai ance idan abu na damunka a rai baka fiddashi ba tsaf za’a wayi gari babu kai, Allah na tuba nikam da ƙuruciya ta da komai ai bazan so na mutum yanzu ba,amma ko ai al’ƙawari na ɗauka gwamma dai nai shiru”shi dai Deen na jinta yay manta banza yaci gaba da pretending kamar bacci yake,da sauri ta girgiza kanta tace “Ina sam sam ba zan iya ba,idan ba faɗa ai sai Allah ya kamani haka nan wutar nan ta duniya me shegen zafi ina ga ta lahira,kana ji na ko? Nidai gsky zan faɗa maka shawara kuma ba basira,ashe da gaske ne duk balagaggen namiji ana jinsa yana ihu shi ɗaya,kamar dai yadda naji kayi yanzu,to nida ba gantalalliya bace nace babu ruwa na da shiga hurumin da banawa ba,nasan ai ba zakai ta ihu kai ɗaya kamar wani zaki ba,to a kan me ma? Su gantallun iyayen naka da suka sallamaka tun kana yaro nike komai naka, nikam tayaya zan bari ka dinga ihu kai ɗaya fisabilillahi?” Miƙewa yay zaune tare ɗura mata rikitattun idanunsa da sauri ta Miƙe tace “kul kul wlh kurwa ta kur,meye wannan kuma?akan wanne dalili zaka kwalalo min ido haka?kai dai jeka can ta masofarka kai ta ihu kai ɗaya kamar doki,Ni kaga tafiya,kuma zan zami uban naka gwamma ka ɗauko ita sallamammiyar yarinya ka zauna da ita,Ni dai da raina da lafiyata ba za’a hanani shiga danki ba,eh to hanawa mana,idan kaja mana abin faɗa ai mun shiga uku gaba ɗaya Masarautar nan sai an sata a bakin Duniya, shiyasa tun wuri na nema mana maganin tsari da kuma ɗan tambura,Ni sai Danoo shawara nake baka wlh wannan ihun bana lfy bane,masifa ce kawai take damunka a rai” shirun da taji yay mata yasa ta juya shi kuma ya gwalo mata jajayen idanunsa waje da sauri tayi waje tana sakin alƙyabbar ta tare da faɗin “A’a wlh kaci kanka nidai nafi ƙarfin ka” bayanta yabi da kallo har ta fici daga cikin bedroom ɗin, miƙewa yay da sauri ya nufi cikin ƙawataccen Bathrobe ɗinsa kai tsaye wajan shower ya nufa tare da sutale shirt ɗin ya saukarwa kansa ruwa, lumshe idanunsa yay ya shiga fesar da ta cikin bakinsa rinannun idanunsa ya ɗago ya sauke cikin makeken mirror’n dake bathroom ɗin, cikin wata dakakkiyar murya yace “Now it’s right time to show them my real face am coming to you Oga Taju” yana faɗin hakan yasa hannunsa ya birkita gashin kansa wanda suka cikurkuɗen kamar wanda aka masa saloon tare da Dada, cikin zafin nama kuma yaja bathrobe ya saka a jikinsa,yana zuwa bedroom ya fara shafawa fresh skin ɗinsa wani versiline mai ƙamshi da laushi,after ya gama ga ɗauki body spray ya fesawa murɗaɗɗan jikinsa,wata riga armless mai shegen kyau ya saka kana ya ɗauki wani half ɗin blue jeans ya saka,ya ɗauki p.cap ɗinsa ya saka sosai kyau kamar Balarabe,ida kaga Deen ba zaka taɓa cewa yasan Muslunci ba bare kai tunanin ya iya wani abu daga cikin karatun Alkur’ani,key car ya ɗauka,da gudu kuma ya fice daga flat ɗin yana jin yadda kuyangi suka biyosa yay masu banza domin tuni yay masu nisa,Ba tare daya kalli flat ɗin iyayensa ba ya nufi can harabar Masarauta yana zuwa fadawa suka nufi wajansa wata gigitacciyyar tsawa yay masu da sauri kowa yaja da baya,kai tsaye ya shige motarsa ya nufi wajan saloon da gyaran ƙumba. Deen ke sauraran abinda Besty ke faɗa masa,da sauri ya ɗago kansa bakinsa har wata kumfa yake yace “Mene? Sarauta fa? Ni na taɓa cewa ina so ne?what the fuck??” Tunda ya fara magana Besty ke kallonsa yana Murmushi gaba ɗaya ya rasa kalar Deen ya iya ruwan masifa akan abu kaɗan,mmkinsa yadda baya iya control kansa kwata kwata,har addu’a yake Allah ya kawo wanda zai iya sarrafa Deen,kuma thank God domin da alama zai iya komai akan his wife, gyara zama Besty yay kana ya kalli Nene ya kalli Yayinda ya kalli Chiroma da kuma Tiraki,kana ya kalli Waziri, numfashi ya sauke kafin yay gyaran murya kaɗan da sauri Chiroma yace “Aliyou kayi hattara,zama Sarki a wannan masarautar wajibi ne gareka,domin tun tuni Sarki yay murabus daman kai ake jira”. wani kallo Deen ya watsawa Chiroma ba tare da yace komai ba ya miƙe zai bar wajan,kasa daurewa Ohinoyi yay hakan yasa yay gyaran murya yace “You can go every where you like to go,but kasan cewa idan har baka yarda zaka zama Sarkin Nufaz to tabbas Auranka da that girl ɗinsa babu shi” cak Deen ya tsaya ba tare daya juya ba yace “what the you mean by that?”. Miƙewa Ohinoyi yay har zuwa inda Deen yake tsaye yay, shoulder ɗinsa ya kama yace “i mean my words Besty,that hausa Fulani girl ɗin can” kallonsa kawai Deen yake with much surprise shi bai taɓa ganin inda aka maƙala wa mutum mulki ba,baya so bashi da interest akai dole ne,fuskar Ohinoyi a haɗe yace “Aliyou Eneye Ahuoyza,bana magana nai karyata billahi indai baka amshi sarautar na ba sai ka saki yarinyar can,na aza zaka min biyayya ko dan farin ciki dana saka na baka abinda yake shirin kai ka lahira,wai ke wacce kalan zuciya gareka heeee??” Ƙasa Deen yay da kansa jikinsa ya ɗauki rawa gashin jikinsa dana kansa duk suka mimmiƙe tsaye, ƙara matsawa kusa dashi Ohinoyi yay can ƙasa yace “BESTY”shiru Deen yay sai fesar da iska da yake,hannu yasa ya rungome sa a jikinsa,kamar zai kuka haka Deen ya kwaɓe fuska yace “i don’t like it Besty,ban so” shafa kansa kawai Besty yake yana faɗin “Sorry!! Nasan isn’t necessary for you,but haka zaka daure,kai fini lfy ƙarfi zuciya jajirr cewa,so kawai yafi can canta daka zama Sarkin Nufaz”shiru kawai Deen da hannu Ohinoyi yaywa su Chiroma alama da suje kawai,gaba ɗaya suka fice daga haɗaɗɗan parlour’n, ɗago kai Deen yay yace “i need a favour” Ohinoyi yay yace “Uhm” Deen yay shiru kamar bazai magana ba sai kuma yace “ina son zuwa wajanta” murmushi Ohinoyi yay yace “who??” Manyan idanunsa ya juya hankali kwance yace “my wife” Murmushi Nene tayi tana jin daɗin yadda ɗan nata yay accepted zama sarki, ko yaya zai gudanar da Mulkin nasa a wannan baƙar zuciyar tasa ohhhhu!? Besty yace “why not? Idan ma tawowa zakai da ita nan ai fine haka nkeso” bayan ya shirya cikin kayan bacci yana kwance yaji wayarsa tana ringing ƙin ɗagawa yay har sai da akai kiran wajan huɗu ana Uku yay answering call ɗin, ajjiyar zuciya Moon ta sauke yana kallon Principal ɗin cikin ƙasa da murya tace “he picked the call” jinjina mata kai yay,shiru tayi tana sauraran yadda yake fidda numfashi kamar,jin shirun yay yawa yasa yace “uhm” sai kuma ya fara ƙoƙarin kashe kiran, Da sauri Moon tace “Daddy!!!” Ware idanunsa yay yana jin muryarta kamar tana gabansa,a ɗan zafafe yace “MAIMOON ALIYOU” kasa magana tayi sai hawayen da yake fita daga cikin idanunsa, miƙewa zaune yay yace “Lolly talk to me” nan ma tai masa shiru cikin tsawa yace “What wrong with you Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen.!!!!”.Mai makon tayi magana duk da tsawar da Deen ya sakar mata,sai kawai ta fashe da kuka iya kar ƙarfinta,baya yay a hankali ya kwanta tare lumshe idanunsa ya shiga fesar da numfashi,shiru yay mata yana sauraren yadda take kuka bilhaƙƙi,sai da tayi mai isar ta dan kanta tayi shiru ta shiga sauke ajjiyar zuciya,kukan a tare suke fidda numfashi domin duk sanda zata sauke ajjiyar zuciya sai yaji shima a lokacin ya sauke tasa,shi yay shiru yana son yaji me zata ce masa,ita kuma tayi shiru sbd bata san mene za tace masa ba,jin shirun yay yawa yasa Deen yay clamly muryars very slow yace “What happened to you Lolly??”kuka ta ƙara saka masa tana ta mutsi da bakinta a ƙoƙarin ta na son faɗin wani abun,but she can’t say anything to her Dad,gaba ɗaya taji ta gaji ta makaranta she need her Dad,runtsa idanunsa yay ya shiga fesar da numfashi da sauri da sauri,da sauri kuma ya zare wayar a cikin kunansa kamar mai neman wani abu haka ya shiga ƙarewa makeken photon Moon dake saman screen ɗin sa ido, cije lips ɗinsa yay kana ya kashe wayar gaba ɗaya ya jefar a saman makeken gadon, bai jira ya kalli lokacin ba ya Miƙe tare da ɗaukan key car ɗinsa ya nufi fita daga flat ɗinsa,wata baiwar sa mai suna Kaltu  tayi saurin shan gabansa kanta a ƙasa tace “Ya shugabana ina dalilin wannan fitar taka??” Ko inda take bai kalla ba ya shige abinsa, Babu kowa a makeken parlour’n dake tsakiyar sides sai ƙarar A.c dake ta kaɗawa ita ɗaya,da sauri yake taka ƙafafuwansa a ƙasa kansa a ƙasa gashin kansa duk ya baje a lokacin idan ka gansa zaka ɗauka wani basamudan ne just like Yayinda’s say, Yana ƙoƙarin fita yaji Muryar Eneye na faɗin “stop here” cak Deen ya tsaya a hankali kuma Besty ya ƙara so inda Deen ke tsaye yana zuwa yace “what are you trying to go?” Shiru Deen yay masa dan shi a yanzu bai jin akwai wanda zai iya hanasa zuwa inda yay niyya,yadda zuciyarsa ke a zalzalashi zuwa gareta ba ƙaramin illa zata masa idan akace za’a hanashi, kafaɗa Besty ya ɗaga yace “anyway idan kaga kamar place ɗin nan toka tabbatar ka zama King of Nufaz” jajayen idanunsa ya ɗaga zuwa ga fuskar Mahaifin na sa,yadda yake kallonsa yasa Besty miƙa masa hannu zai taɓa shi,da sauri yaja baya yana girgiza kansa, cikin ƙara ji yace “don’t ever trying to touch me Abba” waro idanunsa sosai Besty yay sbd sunan Abba da yaji Deen ya ambata,hakan kuma shike nuni da zallar ɓacin ran da yake ciki, ƙara miƙa hannunsa yay zai taɓa shi da sauri Deen ya juya ya nufi flat ɗinsa kamar zai tashi sama,yadda yake fidda numfashi ma kaɗai ya isa mai hankali fahimtar ɓacin ran da Deen ke ciki,kai tsaye side ɗin game ɗinsa ya nufa,yana zuwa ya zare singlet ɗin jikinsa bai tsaya jiran komai ba ya shiga dukan jikin wani ƙaton ƙarfe da iya kar ƙarfin sa. Eki ce tare da Damus zaune suna tattaunawa akan dawowar Deen amma still babu wani impormation daya samu akan yaran da suke da target a kansu, Murmushi Eki tayi tace “wai kayi believe Deen yana aikin da kuka sashi?” Kallonta Damus yay ta ɗaga masa kanta tace “Yeah! Lemme tall you something,Deen ba aikin ku ne gabansa ba,tunda aka gaya masa anyi Missed yarinyar nan,kaga wani action da ya yi akai ne? To Moon she’s with him” Damus da ya kejin abin kamar a mafarki yace “What the you mean by y Eki?” Gyara zama tayi sosai tace bari nai magana cikakken bayani sbd naga kanka babu Uban komai a ciki,daga shisha sai Win, Wannan yarinyar Moon tana wajan Deen,kasan tunda nayi rantsuwa a kansa cewa sai na mallakesa bazan taɓa kaffara ba, muna nan da kai at this week sai kaga Deen yazo,bazan taɓa rabuwa dashi sai na mallakesa,bazan taɓa rabuwa dashi ba sai na rabasa da wannan ƙwailar yarinyar”miƙewa Damus yay tsaye yace “sai yanzu na fahimci abubuwan da nake ta mmki a kansu,Mun saka private investigators,wanda zasu dinga kula da shigensa,to a shekaran jiya yake faɗa min Deen ya dawo gari,na yarda da maganar,kai tsaye na turawa Oga Taju maganar ta email address ɗinsa, nasan bazan taɓa samun magana dashi ko a waya ba ne,amma Oga Taju yace baya son shirme irin wannan,yar dar da yaywa Deen yasan har abada bazai taɓa iya cutar dashi ba,so daga nan ban ƙara magana ba,sbd nasan Oga Taju bazai fahimce ni ba,kaf cikin yaransa babu wanda yafi aminta dashi kamar Deen,tsabar soyayyyar da yake masa fa ya cire gefe guda na sunansa ya bawa Deen,kin san sunansa TAJUDDEEN shi ne ya bawa Deen ƙarshen sunansa, kafin ya yarda cewa Deen yau dararsa yake za’a daɗe,Amma idan har ya san gsky Deen da dukkan family ɗinsa zasu shiga uku tabbas”ya ƙare maganar yana zagaye tsakiyar parlour’n, taɓe baki Eki tayi tace “Wannan matsalarku ce,tawa na riga na shawo akan ta zuwansa kawai nake jira” tana faɗin hakan ta miƙe tsaye tare da nufar ɓangaren en matan gidan,Zau ne ta samesu kowa da abinda yake Salmerh na kusa da Nana wacce take kwance ta lumshe idanunta, Sai kuma Salymat dake zaune tana kallo sai tauna cimgum take,kallon Salymat tayi tace “Saly 2minutes please” tsaki Salymat tayi tace “nifa ba zaki katse min kallo ba,yadda nake masifar son JOHD & AKBAR ɗin nan” kallon cenemar Eki tayi taga yadda Queen Johda da Queen Rakayah,da Queen Salma suke ta fidda makamai suna kaiwa Abu Maleek sara ta ko ina,gefe guda kuma Mahmanga ce da zabgegiyar takobin ta sai sara take kaiwa,gaba ɗaya Masarautar ta birkice,sai ihu Mutane suke an kashe King Akbar,tsaki Eki tayi ta ɗauke kanta tace “Ai ke naga babu tsuntsu babu tarko,lalacewar taki takai kisa Wannan mutanan gaba kina kalla?mai makon kisa romantic film wanda zai kai maki har ka,amma kuma wasting time ɗinki a kan wannan, Allah dai ya kyauta” ta faɗi hakan tana neman wajan zama can kuma tai ƙasa da Murya tace “Wai ya Maganar wajan bokan?anya ba zamu koma ba kowa??” Tsaki Salymat tayi tace “Kina da matsala wlh,da ɗina dake brain ɗinki kamar ta kifi haka take,gaba ɗaya yaushe mukaje? Samnan sati nawa ya bamu yace idan aikin baici ba mu koma?to gaba ɗaya kawo zuwanmu da yanzu ko 4days ba ai ba” lumshe idanunta Eki tayi tace “wlh ba zaki gane ba,a matse nake nafi son ya kawo kansa da wuri wlh” harara Salymat ta fella mata tace “kaji wawiyya,banda hauka gaggawa ai aikin sheɗanne,kawai ki jira soon zaki gansa kamar yadda bokan yace” miƙewa Salmerh tayi tana faɗin “ALLAH ya kyauta” da sauri Eki tace “munafuka ai wlh ko son Deen kike sai dai ki mutu domin na daɗe da fahimtar inda kika dusa”Ita dai Salmerh bata kulasu ta shige part ɗinta, Wayar Nana ce ta fara ihu a hankali ta ɗaga daga can ɓangaren Ovasi yace “Wai Inna ga ta” jin hakan yasa Nana miƙewa da sauri idanunta na kawo ruwa, bakinta na rawa ta shiga faɗin “Innata” da sauri Inna tace “Eh nita walle,Yaya kike?yanzu uban gidanki ya kawo mana kuɗin ai kinki na wannan shekarar,kin san duk shekara sai ya kawo,kedai kiyi masa biyayya babu ruwana wlh sai yay maki baki ya biki tunda matsayin Uba yake wajanki,to ko Ubanki yay maki haka ne??ai baki samu wannan gatan ba” kasa cewa komai Nana tayi sai hawaye  dake bin saman kuncinta,can Inna tace “Ke babu ruwana fa,ko a can kika samu miji kiyi aurenki kawai,to uban me zaki mana idan kin dawo?aikin ƙafa ta ne tuni anyi min nayi rass dani” Ovasi ne ya miƙa hannunsa zai amshi wayar Inna tayi saurin cewa “Nidai idan kika ɓatawa Uban gidanki rai wlh bada yawo na ba” Ita dai Salmerh bata kulasu ta shige part ɗinta, Wayar Nana ce ta fara ihu a hankali ta ɗaga daga can ɓangaren Ovasi yace “Wai Inna ga ta” jin hakan yasa Nana miƙewa da sauri idanunta na kawo ruwa, bakinta na rawa ta shiga faɗin “Innata” da sauri Inna tace “Eh nita walle,Yaya kike?yanzu uban gidanki ya kawo mana kuɗin ai kinki na wannan shekarar,kin san duk shekara sai ya kawo,kedai kiyi masa biyayya babu ruwana wlh sai yay maki baki ya biki tunda matsayin Uba yake wajanki,to ko Ubanki yay maki haka ne??ai baki samu wannan gatan ba” kasa cewa komai Nana tayi sai hawaye  dake bin saman kuncinta,can Inna tace “Ke babu ruwana fa,ko a can kika samu miji kiyi aurenki kawai,to uban me zaki mana idan kin dawo?aikin ƙafa ta ne tuni anyi min nayi rass dani” Ovasi ne ya miƙa hannunsa zai amshi wayar Inna tayi saurin cewa “Nidai idan kika ɓatawa Uban gidanki rai wlh bada yawo na ba” tana faɗin haka Ovasi ya karɓi wayar tare da kashewa yace “Am going Inna” ita dai bata san me yace ba hakan yasa tace “Au har goyo teke Ita Khadii ɗin?”kallonta kawai yay ba tare da yay magana ba ya fice daga cikin ɗan ƙaramin gidan, Durƙoshe wa Nana tayi a wajan tare da rushewa da kuka,bata jin tsanar abinda yake domin komai tayi a yanzu dai-dai ne,haka kuma babu abinda su Damus zasu sata taƙi yi masu, amma me yasa take jin ƙunci da kuma baƙin cikin a cikin ranta? Tana nan zaune har kiran Ammar ya shigo cikin wayarta kasa ɗauka tayi sbd ciwon da kanta yake mata.A can Masarautar Nufaz kam fada cike take da mutane masu yawan gske,manyan mutane na cikin gari Kogi dake wayanta, Tiraki, Chiroma,Sarkin fada,Sarkin aska,Sarkin yaƙi,Waziri,Sarkin ƙofa,Galadima,Hikimai,Dagatai,Masu unguwanni, sa sauransu,sai kuma Bafadawa gefe guda kuma Ex king of Nufaz ne zaune cikin wata iriyar shiga dasu ta IBIRA,Saman wata rantsatsiyyar Kujera wacce aka ƙawata ta da adon ɗanyar azurfa sai walƙiya take tare da sheƙi, ALIYOU ENEYE AHUOYZA shi ne zaune saman kujerar ransa a haɗe,duk yadda ya haɗe ransa amma hakan bai sanya wani sihirtaccen kyau fita daga saman fuskarsa ba, sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda Orange an sanya masa wata Alƙyabba milk sai ratsin Orange a jikin alƙyabbar,ga wani takalmi Kubta mai gashi-gashi wanda ya kasance half covert shoe a ƙafarsa,Gefe guda kuma Sarkin fada ne yake naɗa masa rawani mai bala’in kyau wanda ya kasance mai dai-dai ci,bayan an kammala aka miƙa masa Sandar girma,can kuma aka ɗauko wata zabgegiyar takobi a cikin gidanta, Lokaci da za’a bashi Takobin sai da kowa na fadar ya miƙe tsaye har da Eneye Ahuoyza,cikin girmamawa aka bashi Takobin kansa a ƙasa yasa hannu ya karɓa yana karɓa ya shigar zagaye kansa da ita,sai kuma ya durƙosa har ƙasa tare da miƙa Takobin gaban goshinsa sai kuma ya dawo da ita wajan bakinta ya sumbata,a hankali ya miƙe tsaye tare da komawa wajan kujerar ya zauna, ɗaya bayan ɗaya

Mutane suka dinga zuwa  gabansa suna zubewa tare da kai masa gaisuwar ban girma, lumshe idanunsa yay sbd nauyin da yaji yana masa,ashe haka sarauta take? Haka take sawa Mutum yaji wata izza da girman kai na musamman,sai yaji bakinsa ya ƙara yi nasa nauyi fiye da ko yaushe, ɗan gyaran murya yay kaɗan tare Mutsa sandar hannunsa, Sarkin fada ne yace “Ma sha Allah kamar yadda kowa ya sani yanzu King Aliyou Eneye Ahuoyza shine sarki,kuma nan da wata uku cif za’ai bikin rantsar da shi kamar yadda akewa ko wanne sarki,muna gdy ga dukkan wanda yazo wannan taron sai kuma ALLAH ya nuna mana ranar da Za’ai bikin rantsar dashi tare bashi sandar girma na gold” daga nan zaman fada ya watse, Deen na ganin mutane sun ragu a fadar ya miƙe da sauri kamar zai tashi sama,da sauri shima Eneye ya miƙe yabi bayan Deen, kai tsaye flat ɗinsa ya shige ya shiga fatali da alƙyabbar jikinsa ya shaddar kawai ya bari,bai tsaya ɗaukan komai ba sai A.t.m ɗinsa da abubuwa masu amfani a garesa, kayansa yasa a trolly sannan ya fito Wata Jakadiya sai kirari take masa,a haka ya nufi babban parlour,a tsaye ya samu Nene da Eneye murmushi Besty yay yace “kana tunanin zan habaka hanaka zuwa wajan matar ka ne?tun ka amshi buƙatata zaka iya zuwa duk inda kakeso but make sure ka dawo before 3mouths” jinjina kai Deen yay sai kuma ya nufi wajan iyayen nasa a hankali ya rungomesa yana basu peak,suma peak sukai masa Nene tace “Allah ya ƙarawa Sarki lfy” Fuska ya kwaɓe ya kalli Besty a marai-raice yace “Abba ka ganta ko??” Dry yay yace “rabu da ita ƴar adawa ce Allah ya tsare ya kiyaye, Allah yasa matar kada tayi fushi dakai”shi dai bai ce komai ba ya kama hanya zuwa harabar Masarautar,nan ya samu fadawa tsaye suna jiransa,samun kansa yay da tafiya a hankali amma ba can ba Sannan kuma bai hana fadawan binsa ba,kansa a ƙasa har zuwa wajan motarsa kai tsaye back seat ya shiga sai kuma driver yaja motar suka nufi Airport.

[8/15, 5:17 PM] Nimcyluv📚✍🏻: Moon ce tare da Amira suna tafe a hankali domin zuwa wajan football ɗin su kasancewar yau Sunday shine ranar da suke game, Amira ce tace “Moon ke a tunaninki mene yasa ya kashe maki wayar??” Shiru Moon sbd kukan daya tawo mata,tsaki Amira tayi tace “uhm Allah ya kyauta,komai yay zafi maganinsa ALLAH!” Hawaye ne ya sakko daga cikin idanunta cikin ƙasa da Murya kamar zatai kuka tace “He far away for me Amira,wa nake dashi a duniya sama dashi? sai dai naga a zuwa ganin wasu Amma babu ni,he promised to me zai dawo but he broken his promised Amira,kina ganin Yaya Farouk duk sai yazo ban wani ƙalla halaƙa dashi ba amma baya gajiya da zuwa gare ni,why Dad zai manta dani?” Ta kai ƙarshen maganar tana sakin kuka,tsayawa sukai a wajan dake gaba ɗayan su sanye suke da kayan ball na Amira farare na Moon pink,wando da riga ne sai ƙaramin hijab,ƙafarsu sanye da combus da duguwar Safa mai kauri,gaba ɗaya wandon da ƙyar ya huce cinya,ganin sun tsaya yasa Faizak sakin murmushi a hankali ya ɗauke camerar wayarsa daga kan Moon kai tsaye yaywa Mai martaba sending na vedio’n Moon da yay mata, Juyawa Amira tayi sbd ƙarar camera da taji Maimakon taga Faizak sai idanunsa ya sauka akan Deen wanda yake jikin mota ya harɗe hannayensa a saman ƙirjinsa,gashin kansa ya sauka har gefen fuskarsa yay bala’in kyau sbd saloon ɗin da akai masa,ya ƙara fari da ƙiba ga ƙirjinsa daya ƙara faɗi sosai ya zama wani Jibgege, bakin a Amira har rawa yake wajan faɗin “Moon look your Dad is here look at him” da sauri Moon ta juya nan idanunsa ya sauka akansa akaci Sa’a suka haɗa ido,bata san lokacin data saki dry ba sai kuma hawaye ya shiga sakko mata,da sauri ta yarda ball ɗin hannunta ta nufi inda Deen yake tsaye,shikam idanunsa a lumshe suke yana mmkin yadda a kullum ƙara girma take, ga wani shegen hijab data saka,har wani ball take salon a buɗa masa mata, Moon wani ihu tayi ta shiga faɗin “Dad!!Dad!!” Tana zuwa wajansa ta faɗa jikinsa tana sakin kuka.

Baya Deen yay sbd yadda Moon ta faɗa jikinsa,a hankali ya jingina jikinsa da jikin motarsa yana buɗe manyan idanunsa a kanta Muryarsa dake nuna yana farin ciki yace “Easy,Easy Dolly”  baki ta tura gaba tace “Dad!!” Ware idanunsa yay alamar “what again Wify?” Girgiza masa kai tayi sai kuma tace “I Missed you like a crazy Dad” Kallonta kawai yay ya ɗauke kansa kana ya zare ta daga jikinsa, Amira ce ta ƙarasu wajan su tana kallon Moon tace “Morning sir” idanunsa na can wani gefe yana kallon wani abu yace “Uhm” Amira kuma ta kalli Moon tace “Let’s go dear” maƙe ka faɗa tayi tare da girgiza kai alamar ba zata ba, Amira tace “but we have to win this game” kallon Deen tayi taga waya kawai yake dannawa leƙa fuskarsa tayi ta ƙasa suka haɗa ido,da sauri ya janye idanunsa yana lumshe idanunsa,bata kawo komai a ranta ba tace “Dad za kaga ball ɗin mu yau” haɗe rai yay sosai ba tare kuma da yay magana ya kama hannun Moon ya nufi office ɗin principal da ita,Amira Juyawa tayi zuwa wajan ball ɗin a ranta tana mamaki jijji da kan Deen tare da isa da kuma izzar sa,a bakin ƙofa Deen yaci karo da Principal shida Faizak kallo guda Deen yaywa faizak ya ɗauke kansa, shiru ne ya biyo bayan gaisuwar da sukai a junansu, Faizak kam tuni ya juya ya nufi Ɓangaren sa sbd yau weekend ne babu karatu a yau ma yake son komawa MASARAUTAR TANZAN, Principal ne yace “Ai jiya ta ɗaga hankalinta,ita gida zata ta gaji da zamar makarantar,na lallaɓa ta dai daga ƙarshe kuma ta fara kuka kamar wata yarinya wai ita Dad ɗinta haka dai,bayan ga wani duk weekend sai yazo mata tace min dai Yayanta ne, Finally dai Dad is here congratulations Maimunatou Aliyou Deen” da sauri Deen ya kalli Moon sbd ambatan sunan wani da Principal ɗin yay,ganin ko a jikinta sai ma hawayen shagwaɓa da take ƙara matsuwa yasa ya ɗauke kansa,A karan na farko Deen ya ɗan saki fuska muyarsa can ƙasa yace “Just look at her, she’s crying like a baby” Dry Principal yay yace “Ai Aliyou ma sha Allah! Allah ya baka ƴar a nan kawai taɓara,ranar daka aurar da ita akwai kallo fa,domin ina jin kullum sai an maida ita gidan miji sbd guduwar da zata nayi” ɓoye fuskarta tayi a jikin Deen sbd kunyar daya kamata sosai,  Deen kaman a zuciyarsa cewa yay “She’s mine,komai nata is belong to me ni Aliyou Eneye Ahuoyza the king of Nufaz” a zahiri kuma kallon Principal ɗin kawai yay ba tare da yace komai ba,can kuma ya ɗan saci kallon Moon yace “Hope zaka ban aronta?” Buɗe ido Principal ɗin yay yace “Why not? Ai weekend ne wasu students ɗin har gida suke zuwa ranar Friday Sunday sa yamma su dawo” jinjina kai Deen yay Sannan ya kalli Moon yace “jeki sa veil” marai-raice fuska tayi tace “Dad ba zaka gudu ba?” Kai ya ɗaga mata da sauri tai waje da ido kawai ya bita, lumshe idanunsa yay tare da fesar da numfashi mai zafi, yaushe ƴar rainon tasa ta girma haka? Komai nata ya fito more than his expected her brest waist komai ya buɗe,ga fatar tai wani fresh sai Shinny take, kyanta ya ƙara bai yana, ga wani girman jiki na abun mmki, Tabbas duk wanda ya gansa shi da Moon za’a ɗauka da gaske shine ya haifeta sbd farar fatar su da yazo ɗaya,uwa uba ya bata tazarar shekaru masu yawan gaske,wanda da ace auren yay zai iya haifar kamarta. Moon na fita daga office ɗin ta nufi coner ɗinsu a hanya ta samu su Yasmin tun kafin ta ƙarasa wajan Yasmin tabar wajan,da alama dai barin makarantar zatai domin yau sukai Finally exam ɗinsu, gaba ɗaya ƴan mate ɗinsu sai kukan rabuwa ake Yasmin da Sumy kam na tsaye babu wanda ya tsaya inda suke sai tsohuwar headgril da kuma wasu yara na primary section, ɗauke kanta tayi har zuwa cikin room ɗinsu,Zai ne ta sami Feenerh ganin farin ciki a fuskar Moon yasa Feenerh faɗin “what again? Something new?” Murmushi Moon tayi tace “Guess what?” “Tayaya zan sani? Just tell me” Moon na ware babban veil ɗinta tace “Dad na yazo yanzu fa” buɗe ido Feenerh tayi tace “kai haba? Na tayaki murna kuka ya ƙare” Moon bata ƙara magana ba ta sanya veil tai waje cike da nutsuwa take tafiya,komanta abin sha’awa ne, ta ƙara girma da kyau sai medical glass ɗin ya ƙara mata kyau,a nan ta ƙara shigewa tabar su Yasmin wacce takewa Sumy sallama, tana cikin tafiya taji ance “Maimunatou!!” Juyawa tayi ta buɗe Manyan idanunta tace “Yaya” Murmushi yay mata kafin yace “Cutie ina zaki haka?” Kai tsaye tace “Dad na yazo” taɓe baki yay sai kuma yace “Ina son gaya maki wani abu,ban san yaya zaki fahimta ba,but this is the right time daya kamata ace kin sani,kada ya zamana ina aikin banza” shiru tai masa shi kuma ya ƙara matsawa inda take tsaye idanunsa a kanta yace “Bana sa zaɓin zaɓawa abinda zuciyata keso,ko kuma abinda yafi dacewa da ita,amma zuciyata nada zaɓin son wanda taga ya dace dani” shiru yay sai kuma ya kama hannunta yace “Ina sonki Maimunatou,ina sonki sosai Moon bansan a dadin son da zuciyata take maki ba,na kasa komai sbd soyayyarki ina cikin aiki zan barsa nazo nan dan kawai na ganki,naji sauƙi abinda na keji a raina,bawai dalilin ƙanwata da take a makarantar nan nake zuwa ba, a’a am coming just of you Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza,bazan maki dole ba amma ina jin idan baki amince min Tabbas zan iya rasa raina,kuma na san ba zaki so kiga wani ya rasa ransa sbd ke ba,kina da hankali kina da tausayi nasan zaki zaɓi abinda zuciyarki take so” with much shock Moon take sauraran abinda Farouk yake faɗa mata,banda rawa babu abinda jikinta yake,baya ta farayi yana biyota yana faɗin “No please kada ki barni please Moon accept me as your lover” bata tsaya taji mai zai ce ba ta juya da sauri ta nufi office ɗin principal,Farouk kam idanunsa ne yay jaa kawai ya bita da ido ji yake kamar ya tsaga zuciyarsa ya fito da abinda ya keji game da ita,bazai taɓa give up ba har sai ya mallaketa, da sauri Moon ta shige Office ɗin sai kalle kalle take, Deen dake bakin window ya ɗan kalleta sai kuma ya ɗauke kansa, hanyar waje ya nufa da sauri tace “Dad” cikin tsawa yace “shut up you Mumu!!” Yana faɗin hakan ya fice daga cikin Office ɗin, Yasmin na zaune a cikin mota tana jiran Farouk ya shiga a kasalance Farouk ya fara ƙoƙarin buɗe motar daga bayansa yaji ance “Ohh hello” juyawa Farouk yay domin ganin ai maganar, ganin Deen tsaye yasa ya saki Murmushi tare da miƙa masa hannu,bai musu ba ya bashi hannunsa suka gaisa,shiru ne ya biyi baya kafin Deen yace “Am warning you stop away my Daughter” ware ido Farouk yay yace “ai akwai daughter naka a school ɗin? Ko bayan ka gama aikin gadin ka samu daughter more explanation pls I don’t understand anything” wani mugun kallo Deen yay masa lokaci ɗaya yanayinsa ya fara sauyawa,amma duk da haka he’s trying to control his self bai son abinda zai saka a fahimci wani abu tsakaninsu, Murmushi yay shima yace “Whatever,bana magana ɗaya na maimaita sai dai na ɗauki ma taki akai,Ni abu biyu Ni ruwa ne kuma ni huta ne,lolacin da ban damu da Mutum ba wlh ko inda yake bana raɓa,inuwar dabba tafi min sauƙin gani a kansa, Lokacin da Mutum ya shiga safgata sai fahimci a zaba wacce bai taɓa tunani ba” ware kafaɗa Farouk yay yace “Oh Wow! Lokaci na farko ka birgeni but please do me a favour,ina son ka bani auren ƴar taka” ba tare da yay aune yaji Deen ya sakar masa naushi a baki, kana ya shaƙe wuyan sa yace “you’re mad FAROUK BASHIR YAHYA GIDAN KUƊI you’re so selfish,i told you and i still told you stay away from my Daughter, Maimunatou is belong to not urs dai nai sharini wani da Maimunatou gwamma na kasheta uban kowa ya huta,wlh wlh billahi dalili ɗaya zai saka na barka a nan ba tare dana karya maka wata gaɓa ta jikinka ba,kai kasan wane Farouk idan baka sani ba very soon zaka sani Soon, Ma rantse da zatin Ubangiji uhmm,ka jawa kanka masifa tunda ka shiga inuwar da ba naka ba” yana faɗin haka yay cilli da Farouk jikin mota ya fesar da numfashi duk jikinsa rawa yake,da sauri principal da wasu securities suka ƙarasu wajan, Moon kam jin muryan Dad ɗin nata yana sauke ruwan bala’i yasa ta fito da sauri daga office ɗin zata wajan, Faizak dake tsaye yay saurin kama hannunta yace “wait ina zaki?” Bakinta na rawa tace “Dad na” fuskarsa a haɗe yace “to me zaki masa,ki bari ya gama ihun mana” wani kallon baka da hankali tai masa tace “wake ihun? Ko kai da nake kulaka darajarsa kaci sbd mun haɗa sunan uba ɗaya dakai” Principal yace “Lafiya? Meke faruwa Aliyou” tufar da yawo Deen yay yana nuna Farouk da yatsa sai kuma ya juya kai ya nufi inda yaga Moon tsaye,yana zuwa ya fisgi hannunta zuwa motarsa,da wani irin speed yay mata yabar cikin makarantar,shima Farouk idanunsa yay jajirrr sbd baƙin ciki yama rasa mai zaiwa Deen ya huce,yana ganin yanzu lokaci yayi da Moon zata san komai da haka Farouk ya bar makarantar, Faizak ma office ɗinsa ya nufa yana jin gaba ɗaya zaman makarantar ya fice masa a rai ga wani haushin Moon daya cikasa ace maza har biyu suna faɗa akanta? Mtwsss what the fuck? Kamar wata karya.
+
  *_Albishrin ga masoya littafin Moon,ga dukkan mutanen 10 farko da suka fara siyan book ɗin SIRRIN MU zai kaisu vip kyauta ma dadin nrml grp,wanda suka biya kuɗin vip zan basu littafin UNCLE NE ko THE NEW EMIR a kyauta so karanta, da zarar mutanen 10 sun cika na rufe wannan gara ɓasar🤣 400 for nrml grp 600 for vip account details 0116886423 Sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616_*
Tunda Deen ya fita a cikin makarantar yake sharara uban gudu a cikin motarsa kamar zai tashi tsaye da motar,Moon tsoro da fargabar dake cinta yasa ta kasa magana,babban tashin hankali ta kuma yadda take Dad ɗin nata ya fita daga hayyacinsa sai karkarwa yake yana dukan staring motar,bakinta na rawa tace “Dad!!” Banza yay mata sai ma ƙara giyar motar da yay ganin kamar motar tasu zata kifa yasa ta tura kanta cikin cinyoyinta ta shiga rera kuka da iyakar muryarta, jin kukanta yake har tsakiyar ƙwaƙwalwarsa duk ihun da zatai sai yaji zuciyarsa kamar zata tsaka ƙirjinsa ta fito, hannunsa yasa a cikin tsakiyar sumar kansa ya hargitsa wani ihu yay shi kaɗai kafin ya buga staring motar cikin ɗaga murya yace “Kee!!! dallah  shut up your mouth or else” sai kuma ya girgiza kansa yaci gaba driving motar, kusan motar zaune Moon tai domin bata taɓa tunanin Dad ɗinta zai mata wannan mahaukaciyar tsawar ba,a gaban wani tangameme gida na alafarma yay parking da motarsa,da sauri ya fita yasa key ya buɗe gate ɗin gidan,kana ya komai cikin motar sai da ya shiga yay parking sannan ya rufe gidan, private hause ɗin sa ne babu wanda ya san yana dashi, hasali shi kansa bai taɓa shigarsa ba sai yau, kasa fitowa tayi daga cikin motar yadda yake jin zuciyarsa yasa bai tsaya ce mata wani abu ba yasa hannu ya fito da ita suka shiga cikin gidan, a parlour ya saki hannunta ya haura upstairs tsayawa tayi tana kallon parlour’n wanda yasha kaya na ƙasar waje,komai na parlour’n red and black ne ga wata a.c da ƙamshin airfreshner ɗaya cika parlour’n, Deen na shiga ya fara cire kayan jikinsa ya rage daga shi sai boxer da singlet,saman bed ya faɗa yana lumshe idanunsa,can kuma ya miƙe domin baya jin zai samu sauƙi idan Moon yaje ya tambaye ta, miƙewa yay ya shiga taga stairs ɗin bene,tana tsaye inda ya batar kanta a ƙasa,kai tsaye ya ƙarasu inda take kafin yasa hannunsa a ƙafaɗarta ya juyo da ita gabansa sukai farcing juna sosai lumshe idanunsa yay kafin ya buɗe ido ya sauke a saman fuskarsa,  kamar bazai magana ba sai kuma yace “Why? Why Lolly? Why are you doing this to me Dolly?” Ya faɗi hakan yana zare veil ɗin dake jikinta ƙyakkyawar surar jikinta ya bai yana kasancewar kayan ball ne a jikinta, hanunsa ya ƙara sawa ya ware ribbon ɗin da aka ɗaure mata sumar kanta dashi,Moon shiru tai sbd bugun da zuciyarta ke mata,bata taɓa ganin Dad ɗin nata a cikin wannan halin ba sai yau,mai yasa ya sauya? Mai yasa yake mata tsawa da faɗa? Mai yasa ya sauya daga dukkan abubuwan da yake mata? Baya son ta raɓu dashi ya daina rungome ta ya daina peak na kumatunta he’s changed Yeah he’s changed,mai yasa? Mai tai masa? Shi ɗaya ta sani shine komai nata mai yasa zai sauya daga yadda ta sanshi? Saukar Muryarsa taji inda yake faɗin “You broked my heart Maimunatou,you know I love…” Sai kuma yay shiru kallonsa tayi bakinta ya shiga rawa da kyar ta samu tace “Am sorry Dad please give me please Dad” fesar da numfashi yay yace “Uhm what about that Mumu guy Ahhha Farouk?” Idanunta na zubar da waye kamar yadda idanun Deen yay jajirrr tace “he said  he loves me Me Dad” wata gigitacciyyar tsawa mai tarwatsa zuciya Deen ya sakar mata yana faɗin “Stop stop Saying that to me Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen” firgicin data shiga yasa ta zube a wajan jikinta duk rawa yake,saman kansa ya dafe yana jin kansa kamar zai rabe gida biyu sbd azabar ciwon da yake masa, me yasa zai mata haka? She’s not her fault bata da masaniyar komai,amma mai yasa tai broked promise ɗinsa bayan al’ƙawarin da tayi masa, durƙosawa yay inda tai ya kamata ta miƙe tsaye cikin kuka tace “Am sorry Dad am so sorry” kasa magana yay sai Kallonta kawai da yake,ganin yay mata shiru yasa tace “please Dad” da ƙyar ya samu damar faɗin “It’s okay” kwaɓe fuska tayi tana ɗan buga ƙafa tace “but i need your hug Abba” da sauri ya kalleta kafin yay magana ta rungome sa tana Murmushi, runtsa idanunsa yay sbd wani shock da yaji ya kamasa,da sauri yasa hannu ya cireta a jikinsa matsu da fuskarsa yay dai-dai tasa a hankali yasa yatsarsa guda ya matsar da gashin daya rufe mata gefen fuskarta, idanunsa a cikin idanunta yace “you’ll be with me forever Lolly?” Da mmki take kallonsa inda shi kuma yake kallon bakinta yana jiran yaji me zata ce masa,shi kaɗai yasan zafi da raɗaɗin da zuciyarsa ke masa bai taɓa tunanin zai samu kansa a cikin halin daya samu kansa a yanzu ba,mace na son haukata tunaninsa tana son zama weakness nasa ya amshi sarauta sabida ita,nan gaba bai san abinda zai aikata akanta ba, tsigar jikinsa yaji tana tashi wani sanyi ya shiga ratsa cikin jikinsa, muryarsa na sharking yace “Speak up Lolly” ya faɗa yana ɗura kansa a saman forehead ɗinta tare da ɗura hannayensa a saman waist ɗinta idanunsa cikin nata kamar yadda take kallonsa ta kasa furta komai domin kanta gaba ɗaya ya kulle ta kasa gane abinda yake nufi, “stay with me,loves me, Maimunatou!! Aliyou Eneye Ahuoyza loves you,i love You Dolly and i want to marry you Noor” a rikice  Moon ta ƙara kallan  Dad ɗin nata bakinta ya shiga mutsawa yadda take taune lips ɗin ta da yadda yawo ya jiƙasu yasa Deen jin wani Irin wani abu, bakinta ta buɗe zatai magana deeny zai san lokacin daya haɗe bakinsu waje guda ba..

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *