RAYUWAR CAMPUS CHAPTER 11 BY Fateeyzah mbs✍️
Www.bankinhausanovels.com.ng
*_Marubuciyar_*
*_Gidan nagoggo_*
*_Doctor zahrah_*
*_Yakin Mata (aure)_*
*_Kuda wurin kwadayi_*
_Tukwicine ga daukacin matan jami’a_
*_ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ_*
Ko dana zuge jaka don in dauko masa kud’insa, sai kud’i yace d’aukeni, bazan iya k’iyasta muku tashin hankalin dana shiga ba don ganin babu kud’in nan, nan na birkice komai na jakar amma babu kud’i babu alamunsa, nan na fashe da kuka ina ta surutai, wanda a yanxu ban iya tuna mai nake cewa, haka dai mutane da mai shagon suka yo kaina suna tambayana abunda ya faru, ina kuka ina basu ba’asi, hakuri suka bani, nan dai suka bani kud’in motar dawowa school, tun daga kasuwa nake zubar da hawaye har makaranta, saboda hak’ik’anin gaskiya tausayin kaina nake da iyayena, domin sana’ar nan itace rufin asirin mu, don hatta su ni ke musu sak’o suna toshe wata kafar.
Ko da na dawo meena kad’ai na samu a d’aki, ganin yanayin da nake ciki yasa ta tambayan mai ya faru, a ranar na ma manta da bama magana, nan na kwashe na fad’a mata abunda ya faru, nan ta zauna tana lallashina, sannan ta fice, a tak’aice dai ranar haka na wuni a kwance ina kuka, bacin abinci, sallah kad’ai ke tada ni daga kwance, har bayan isha’i sannan meena ta dawo d’akin, nan ta tarad dani yanda ta fita ta barni, haka ta tasani gaba sai dana ci abinci, sannan ta sani nayi wanka, itama wankan tayi ta shira cikin shigar da ta saba yi in zata fice da daddare, har tamin sallama ta fita sai gata ta dawo take cemin ko zanje inda zata, don in na zauna ni kad’ai damuwa zata kuma min yawa, ba tare da dogon tunani ba na amsa mata da eh zani, nima nan na shirya cikin pencil skirt, sai ‘yar top na bita muka fita.
ko da muka fita, bamu zame ko ina ba, sai sai *BUBBLE PLUS*, wanda shine farkon zuwana club a rayuwata, nan meena ta taja ni har *bar* side dinsu, wanda ta yi mana ordern drinks, duk abunda take da ido nake binta, kamar wacce aka rufe mata baki, a tak’aice dai anan nayi shaye² na na bugu, saboda drinks din da meena ta bani, an masa mixed da alcohol, a lokacin ji nayi na manta da duk wata damuwata, sannan a wannan daren wanda na rad’a ma suna bak’in dare na fara zina da wani had’adden guy, daga rawa abun ya fara, har ta kai da mana da romance daga nan sai ya jani d’aki muka fara sex, duk da a lokacin ban cikin hayyacina, amma naji dad’i, sannan kuma da muka gama sai da ya ajiyemin 100k cash kafin ya wuce, k’arshanta dai anan na kwana, sai da safe dana dawo hayyacina na nemi hanyar school, don kota meena ban biba, sai dai muka had’e a hostel, daga nan na kuma jonewa da meena, wanda shed’an ya dad’a buga mana gangarsa, sex da shaye² mun maida shi kamar wani ado a rayuwarmu.
Duk dana samu jari, bai sa naci gaba da saida kayana ba, sai na maida zina sana’ata, dashi nake ci, nake sha, nake biyan kud’in makaranta, har ma in tura ma iyayena wad’anda basu san sana’ar dana koma ba, don ban tab’a basu labarin b’acewar k’udin sana’ata ba, har yanxu sun d’auka san’ar kaya nake da takalma, tunda in dai naje hutu ina siyosu a lagos, don guje ma zarginsu, shine nake kawo muku ku siya
.
Had’uwarmu da summy kuma shi ya k’ara bud’e mana ido, muka koma bin sugar daddies tare kuma da upgrading d’in club, muka koma zuwa club din *Eleganty*, wanda shine babban club na yaran masu kud’i, summy ita ma course d’inmu d’aya, kuma a hostel floor d’inmu d’aya, nan ta jone damu ta kuma fito damu saboda kud’in da take kashe mana, shine har muka had’u daku wannan shekarar.
Hutun k’arshe da muka koma gidane shine Bukar yazo wurina, yana mai bama iyayena hak’urin abunda ya mini tare da neman gafarata, yana son kuma a kuma d’aura mana aure don yanxu Allah ya d’aura masa masifar sona, su mamana sun yafe masa, sai dai sunce baza su kuma mun dole ba, kakanmu ma haka yace, in na yadda sai a kuma d’aura aure, inje in rik’e ‘yata, shine fa yake ta bina tare da damuna da kira, ko yau ma ya kirani ina tsakar sex call da my sugar, jin muryata ya d’auka banda lafiya ne, shiyasa yace in turo a k’arban mun sak’o don ya riga ya shigo school, shi yasa na tura ku, kun ji tak’aitaccen labarina.
Duk a tare suka sauke ajiyar zuciya, yayin da dukkansu idanunsu ya k’ad’a yayi jajawur, fuskarsu k’unshe da tausayin Hibba, sumy ce tayi k’arfin halin mikewa ta nufi hibba, kama hannunta tayi ta rik’e tare da cewa “Hak’ika Hibba kinga rayuwa, a daa na d’auka ni kad’aice ke da matsala a cikinku, ashe naki ya shafe nawa, amma duk da haka naji ciwon kasancewarki haka, saboda already kin tab’a aure, ga kuma baby kina da ita, ko da yake, ban saka laifin lalacewarki akanki ba, na sakasaa ne akan Meena, don ita ta jaki” ta karashe magana tana mai maida idonta kan meena.
“Ko baki fad’i ba sumy, na riga na d’aura ma kaina wannan laifin, banyi haka da muguwar niya ba, nayi hakane don samun mata salama a cikin zuciyarta, duk dani already a lalace nazo makarantar nan, ban sa ma raina zanyi silar lalacewar wata ba, amma Hibba don Allah kiyi hakuri ki yafemin” cewar meena jikinta a sanyaye.
Dariya hibba tayi mai kama da yak’e sannan tace ” ba komai meena, yanxu dai bamu naki labarin”‘
Murmushin tak’aici ta saki, hade da cewa ” ni labarina bai da dad’in saurare, saboda iyayena sune sillar lalacewata “.
*Wacece meena?*
Sunana Ameena Garba D’an kwarai, hafaffiyar garin zaria, mahaifina garba d’an kwarai shahararren mai kud’ine, tun daga farkon zaria zuwa k’arshenta duk wanda kika tambayesa mahaifina Alhaji D’an k’warai, ba wanda bai sonsa ba, yana da kamfanoni da yawa kamar kamfanin shinkafa, Bread, yoghurt, pure water, sannan da gidajen mai.
Kafin muyi nisa bari kuji kuma wacece mahaifiyata, mahaifiyata Hajiyar Hurera mai dala, itama hamshakiyar mai kud’ice, ‘yar mai kud’i, jikar mai kud’i, wanda suka gada kaka da kakanni, tana da k’aton gidan gona inda take kiwon shanu, raguna, kaji da sauransu, sannan ma’aikaciyace a Jami’ar Ahmadu Bello bangaren *NAPRI*.
Nasan zaku yi mamakin abunda yasa nake b’oye asalina da kuma kud’in gidanmu, wanda hatta hotuna na da kuke gani a gidan ina muku k’aryane da gidan mak’otan mune, ina haka ne saboda duk dukiyar nan dana lissafo muku basu da amfani a wajena.
Nice ‘ya ta farko a wurinsu, don sun dad’e Allah bai basu haihuwa ba, ko ince basu shirya mata ba, saboda dai mummyna ‘yar boko ce, daga ni kuma sai k’anina Alameen, dukiyar da suke dashi bata da amfani a wurin mu, don Daddy irin mutanen nanne da suke bak’in cikin kwandala ta fita daga aljihunsu, wallahi ko zakkah don umurnin Allah ce, shi yasa yake fitarwa, domin kuwa in ma ya fitar, to sai ya d’auki sati yana zazzab’i, cimar gidanmu bata da maraba da ta gidan yari, haka suturunmu basu da maraba data matsiyata, wanda shima suturun sai sallah ake dinka mana, kuma shima kala biyu ne, kuma shima atamfa roba², Alameen kuma shaddar roba, Abu d’ayane zance Daddy ke fitar da kud’i ya kashe mana, shine karatu, don daga primary dina zuwa secondary banyi makarantar k’asa da dubu d’ari ba, ta wannan b’angaren bamu da matsala.
Bangaren mummy kuma……
_In naga comment da yawa, gobe in muku double typing._
*Comment*
*Like*
*Vote*
*Share*
*_Fateeyzah mbs ce✍️_*