SHU’UMIN NAMIJI CHAPTER 10 BY FATYMA SARDAUNA
Www.bankinhausanovels.com.ng
Saida kusan gabaki ɗaya mutanen da suka kawo Zahrah suka soma watsewa zuwa wajen dinner, kafun Husnah ta matso kusa da amarya Zahrah wacce take aikin kuka. Hannayenta takamo haɗe da zama gaf da’ita.
“Please Zahrah kidaina wannan kukan, yanzu haka Doctor yace inkai masa ke yana boys guaters, kuma kinga babu amfanin kije wajensa kina kuka” Husnah tafaɗi haka ga cikin lallashi.
Zahrah dai bata kumace da’ita komai ba bata kuma daina kukan ba,, wayar Husnah ce tayi ƙara alamar shigowar ƙira, sunan Dr.Sadeeq ne keyawo akan screen ɗin wayar,, tana kara wayar akan kunnenta yace
“Yadai Husnah, najiku shiru”
Sake kallon mutanen da sukayi ragowa acikin ɗakin Husnah tayi.
“Gaskiya babu dama Doctor, saboda dazaran anga zamu fita za’ace ina zankaita” Husnah tafaɗi haka cikin ƙasa ƙasa da muryarta….
Ajiyar zuciya Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa
“Okay to bakomai zan san yanda za’ayi, ku shirya me meckup tana nan zuwa”
Cikin matsanancin ciwon kan dake ɗawainiya da’ita tashiga toilet ta ɗauro alwala, kan ƙaton darduman dake shimfuɗe a tsakiyar ɗakin ta hau ta kabbara sallah’n magriba,, tana idar da sallan meyi mata meckup ta ƙaraso, haka tanaji tana gani ta bada fuskarta aka zizara mata meckup wanda yaɗauki fuskarta sosai.. Yauma dai meyin meckup ɗinne ta shiryata tsab cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga (wedding gown) na wani tsadadden leshi me matuƙar kyaun gaske, riga ce doguwa har tana sharan ƙasa yayinda bayan rigar aka sanya wani haɗaɗɗen net me matuƙar kyaun gaske, sosai net ɗin da aka sanya abayan rigan yakuma ƙawata ɗinkin, lace ɗin yakasance light pink colour yayinda kayan ƙyale ƙyale najikinsa yakasance golding ash colour, sosai kayan yayiwa Zahrah kyau,,, haɗaɗɗen ɗaurin ɗan kwali aka tsantsara mata akanta, take tasake yin kyau,,,, yau dai kwalliya da kuma kyawun da Zahrah tayi haryafi wanda tayi a ranan kamu, komai nata yau na musamman ne tasha kyau sosai, ga doguwar riganta me ɗaukar hankali, daddaɗan ƙamshi kawai take fitarwa ajikinta me sanya nutsuwa,, duk da irin wannan kyawun da tayi sai dai fuskarta babu wani wadataccen walwala domin kuwa idanunta sunyi luhu luhu dasu, cikinta kuwa banda kukan yunwa babu abun dayake yi mata, amma kuma saboda masifar taurin kai irin nata taƙi sanyawa cikin nata komai na abinci.. Husnah ma yau zama tayi akayi mata meckup nagani na faɗa, sosai itama tayi kyau, tasha adonta cikin wata doguwar riga na golding white lace, idan ka kalleta dole ka ƙara domin itama tayi kyau sosai dama kuma itaɗin ma ko babu meckup tana da kyau masha Allah….
Yauma dai ango tare da amaryarsa zasu wajen dinner kowa yariga daya tafi harsu Auntie Raliya kuwa….
Husnah ce riƙe da hanun Zahrah suka fito compound ɗin gidan inda motar ango ke jiransu.
Shikam gaba ɗaya kwana biyunnan salon kyawun na Zahrah namatuƙar tafiya da imaninsa babu ma kamar yau, gaba ɗaya komai na surar jikinta ya bayyana bama kamar hips ɗinta yafito raɗau acikin rigan..
STORY CONTINUES BELOW
Husnah ce ta buɗe murfin motar dayake zaune aciki, sai da ta tattaro ƙasan rigan Zahrah’n kafun Zahrah ta’iya shiga cikin motar ta zauna,, lumshe idanunsa yayi haɗe da shaƙan daddaɗan ƙamshin daya kawowa hancinsa ziyara, wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi ya sauƙe,, kallonsa yakuma dawowa dashi kan tauraruwar da haskenta yacika idanunsa,,, murmushi yasakar mata me ƙayatarwa, yayinda ita kuwa kanta ke duƙe aƙasa tama kasa ɗago idanu ta kalleshi,, hanunsa ya sanya ya ɗago haɓarta, sai alokacin ta iya jefa idanunta cikin nasa idon, wani irin abu yaji acikin jikinsa, ita ɗinma hakane, da sauri ta rumtse idanunta,, abun daba ta tsammata ba, sai jitayi ya jawota jikinsa, haɓanta yakuma ɗagowa da hanunsa na dama, haɗe da sanya ɗayan hanunsa yashafi gefen kumatunta
“My Princess!”
yaƙira sunanta cikin wata muryarsa me sanyi. a hankali ta ware idanunta acikin nasa idanun, ƙasa ƙasa yayi da idanunsa haɗe da maida kallonsa ga ɗan ƙaramin bakinta dayasha lipstick, murmushi yakuma sakarmata haɗe da sake jawota ya ɗaurata akan cinyarsa.
“Kinyi kyau fiye da kullum my princess!” yafaɗi haka still yana me shafa gefen kumatunta da hanunsa, wani irin kunyarsane yakamata tunda take dashi baitaɓa yi mata irin kallon dayakeyi mata a yanzu ba, haka kuma baitaɓa jawota yaɗaurata akan cinyarsaba sai yau. Marairaice fuskarta tayi haɗe da sunkuyar da kanta ƙasa,, sweet ɗin dake cikin bakinsa ya cire, haɗe da ɗago fuskarta ya sanya mata acikin bakinta, kallonsa tayi da ɗara ɗara idanunta, kansa ya jinjina mata yana ɗan murmushi, ahankali tashiga juya sweet ɗin acikin bakinta, dama kuma tunsafe babu wani abu daya shiga bakinta inbanda ruwa, sai wannan sweet ɗin daya bata yanzu,, hanunta yakama yashiga murzawa ahankali haɗe da kafeta da idanunsa wanda lokaci ɗaya suka wani marairaice…. Sauƙeta yayi daga kan cinyarsa haɗe da kama hanunta ya buɗe murfin motar riƙe da hanunta haka suka fito daga cikin motar,, kamar wata jela haka take binsa still hanunta na riƙe acikin nasa, direct wani dogon gini dake cikin gidan nasu suka nufa. Ita dai kawai binsa take cikin takunta me ɗauke da nutsuwa yayinda rigar jikinta kuwa ke share wajen, don ma wajen babu datti, wani haɗaɗɗen falo ta tsinci kanta a ciki, suna shiga cikin falon Doctor yatsaya daga tafiyan da yakeyi haɗe da juyowa gareta, murza hanunta dake cikin nasa yayi haɗe da zaunar da’ita akan kujera, kaitsaye wajen wani fridge dake aje cikin falon ya nufa, buɗe murfin fridge ɗin yayi haɗe da ɗauko kwalin fresh milk wanda bashida sanyi sosai, glass cup ya ɗauka ya tsiyaya fresh milk ɗin aciki, saida yakusa cika kofin kafun yamaida sauran cikin fridge ɗin ya aje.. Inda Zahrah ke zaune ta sunne kai ƙasa ya nufo, aje kofin fresh milk ɗin yayi akan ɗan ƙaramin table ɗin dake kusa da kujeran daya zauna, jawo Zahrah yayi jikinsa haɗe da sake ɗaurata akan cinyarsa, kofin da fresh milk ɗin ke ciki ya kawo dai dai saitin bakinta, cikin muryar lallami yace
“Anfaɗamin bakici komai ba tun safe, banaso kina zama da yunwa fa, banso tayi miki illa, kisha ko kaɗanne kinji baby na!”
Tsintar kanta tayi da kasa musa masa, saidai amma kuma gaba ɗaya a tsarge take, bata taɓa zama akan cinyar wani haka ba, hakan yasa gaba ɗaya ta takura,, a hankali take ɗan shan fresh milk ɗin wanda harkusa da bakinta Dr.Sadeeq yake kawo mata kofin, shan fresh milk ɗin take cike da nutsuwa yayinda shi kuma gaba ɗaya idanunsa ke kanta, bakinta kawai yake kallo, karo na farko kenan arayuwarsa dayaji wani irin muguwar sha’awarta na fusgarsa,,, kafun shida ita su ankara tuni hartasha fiye da rabin kofin,, ɗan ya mutsa fuskanta tayi haɗe da sanya hanu ta shafi ɗakalallen cikinta
“Naƙoshi fa!” tafaɗi haka tana me langwaɓar da kanta gefe.
“Um’um ban yarda ba nasan kinajin yunwa sosai, ki ɗan ƙarasha ko kaɗan ne kinji _MY WIFE_!”
Kalmar nan ta_MY WIFE_ daya ƙirata dashi shiyasanya taji gaba ɗaya jikinta yayi mata wani iri,,, bakinta ta turo gaba haɗe da cewa
“dagaske ni na ƙoshi, gashi kuma duk kasa janbakina ya goge!” taƙare maganar akasalance.
Wannan shagwaɓan da takeyi masa shiyake sanyawa yaji gaba ɗaya jikinsa ya mutu, har wani rufewa idanunsa keyi,, yabuɗe baki zaiyi magana kenan wayarsa tasoma ƙara, kobai ɗaga ba yasan dalilin ƙiran, yanzu haka yasan anacan antaru a wajen dinner su kawai ake jira, miƙar da’ita yayi tsaye bayan ya aje cup ɗin dake hanunsa,, amaimakon ya riƙe mata hanu su tafi kamar yanda suka zo sai gani tayi ya ɗagata caɗak yayi hanyar waje da’ita,, a tsorace tanemi sauƙa daga jikin nasa amma kuma kyakkyawan riƙon dayayi mata yakasa bata daman hakan….
Bai direta ako ina ba sai acikin mota, yanashiga driver yaja motar suka fice daga cikin gidan… Kwanciya tayi luf ajikin kujeran motar haɗe da lumshe idanunta gaba ɗaya sanyin AC’n da motar ke busawa ne ke damunta, sam batason sanyi yacika yawa a waje. daga wani ɓangare kuwa amatuƙar takure take, saboda yanayin yanda yake murza hanunta dake cikin nasa. sosai hakan kesawa taji wani iri acikin jikinta, gani tayi gaba ɗaya yau ɗin ya sanja mata, yanayi mata wasu irin abubuwa da baitaɓa ƙoƙarin kwatanta yi mata shiba acan baya, ada sam baya taɓa yunƙurin kama hanunta sai dai idan yazama dole,kuma koda ma ya kama hanunta bawani jimawa zai sake, sannan kuma sam baya yawan jawota jikinsa kamar yanda yakeyi mata ayau, gashi gaba ɗaya taga yanayinsa ya sauya, idanunsa sunyi wasu kala tamkar wanda yakejin bacci… Zuciyarta nayi mata lugude haka suka iso wajen dinner inda mutane suka cika maƙil zuwansu kawai ake jira… Suna isowa waje yaɗauki sowa yayinda mc yasake musu daddaɗan kiɗa me daɗi ta romantic… kamar dai yanda kamu ya ƙayatar haka dinner ma yaƙayatar sosai Dr.Sadeeq yayiwa Zahrah ɓarin kuɗi lokacin da aka ƙirasu tsakiyan fili, sunsha liƙin kuɗi kam sosai, su Auntie Raliya ma sunzo sun liƙa musu, amma duk yanda akaso amarya tayi rawa kasawa tayi, saboda bata iyaba, bakuma al’adarta bane yin rawa agaban mutane, kunya ma bazai taɓa iya barinta ba,, saida Dr.Sadeeq yariƙe hanunta yashiga juyawa da’ita afilin rawan, take aka hau musu tafi yayinda wasu daga cikin abokansa suka ci gaba da yi musu ɓarin kuɗi,, suna komawa kan kujeransu mc yasanya musu daddaɗan waƙar Ed sheeran, shiru Zahrah tayi tana sauraran waƙar sosai dama takeson waƙar domin kuwa duk waƙan Ed sheeran yanayi mata daɗi… Koda aka yanka haɗaɗɗen cake ɗin da aka ƙawatashi da sunan ango da amarya, da ƙyar Zahrah ta’iya bawa Dr.Sadeeq cake ɗin abaki, gaba ɗaya nauyi da kunya sun isheta gawani zazzaɓin daya sake kawo mata ziyara lokaci ɗaya,,, lokacin da aka tashi a dinner tuni amarya Zahrah tayi laushi, hartakai bata iya dogon tsayuwa da ƙafafunta, ƙarfe 10 na dare aka tashi a dinner Aunty Ladi da kuma Husnah su suka sanyata a wata mota, direct aka wuce da’ita asalin gidan da zata zauna wato gidan aurenta…. Gidane me matuƙar kyaun gaske wanda aka kashe kuɗi sosai wajen ƙawatasa, baginin gidan sama bane amma kuma yanayin yanda akayi ginin yayi kyau sosai, wata haɗaɗɗiyar ƙofa suka nufa, suna buɗeta kuwa suka tsinci kansu cikin wani ƙawataccen falo me kyaun gaske. haɗaɗɗen falone wanda yasha kujeru light orange and milk colour, yayinda aka ƙawata jikin ƙofa da window’n da wasu irin haɗaɗɗun labulaye masu kyau, tsakiyar falon kuwa mamaye yake da wani haɗaɗɗen carpet Orange colour,, ga wani irin ƙaton tv plasma dake aje kan wani haɗaɗɗen glass,, falon dai ba’acika masa kayan ado ba amma kuma yaƙawatu sosai komai na falon me tsada ne,, direct wani ɗaki dake cikin falon aka wuce da Zahrah,, ɗakine me kyau wanda yaji royal furnitures milk colour, yayinda aka lailaye kan makeken gadon da wani irin zanin gado pink me kyawun gaske… Akan gado sukayimawa Zahrah masauƙi, Husnah dakanta ta haɗawa Zahrah ruwan wanka, koda tafito a bathroom ɗin hannayen Zahrah dake zaune kan gado ta kamo, haɗe da janta har zuwa cikin bathroom inda ta haɗa mata ruwan wanka…
STORY CONTINUES BELOW
Wani Turare ta bata tace inji Hajiya Shuwa, sannan kuma tayi mata bayanin yanda zatayi amfani dashi…
Zahrah tana fitowa a wanka Husnah ta shafa mata powder haɗe da lipstick, wani riga da sket na material marar nauyi Husnah ta bata tasanya, take tafito ɗas da’ita, a tsakiyar gado Husnah ta zaunar da Zahrah haɗe da rufe mata kanta da wani irin haɗaɗɗen mayafi me sheƙi da walwali, wasu turaruka masu ƙamshi Husnah takuma feshi jikin Zahrah dasu, take ɗakin yakuma ɗumamewa da ƙamshi,, sake matsowa kusa da Zahrah Husnah tayi cikin murya ƙasa ƙasa tace
“Dan Allah Zahrah karkice zaki ci gaba da wannan kukan naki, ki ɗan daure zuciyarki kinji ƙawata, kuma sannan kada ki hana Doctor haƙƙinsa, nasan zakiji tsoro amma please ki daure kinji ƙawata, banaje falo na amsa waya ” Husnah taƙare maganar tana me miƙewa tsaye, idanu tayiwa Auntie Ladi suka fice a tare….
Tun Zahrah na jiran dawowan su Husnah hartasoma jin tsoro, domin kuwa gaba ɗaya gidan yaɗau shiru babu alaman akwai motsin wani mutum bayan ita,,, abun da Zahrah bata sani ba shine su Husnah wayo sukayi mata suka tafi suka barta, sunyi hakanne kuma saboda taƙaitamata wahalan kuka, domin sun san sunace mata zasu tafi zata ƙara fawan kukanta…..
Gyangyaɗine yasoma ɗaukarta, dan haka saita jingina bayanta ajikin saman gadon haɗe da lumshe idanunta da suketa tsiyayar hawaye…
A hankali yaturo ƙofar ɗakin bakinsa ɗauke da sallama, yasake shiga cikin wata farar shadda sabuwa ƙal sai sheƙi takeyi, ƙamshi ne kawai ke fita ajikinsa, daganinsa kasan yana cikin matsanancin farinciki,, ledan dake hanunsa ya aje, haɗe da takowa zuwa wajen datake zaune ta jingina bayanta da saman gado,, zama yayi akusa da’ita haɗe da ƙiran sunanta,, cikin murya me sanyi da kuma alamar bacci ta amasa masa,, ahankali yasanya hanunsa ya ɗan jaye mayafin dake kanta, hawaye yagani kwance akan fuskarta, hanunta yakamo haɗe da jawota jikinsa, hanu yasanya yashiga share mata hawayen dake kan fuskarta.
“Ki daina kuka kinji my wife, bacci zakiyi ne?” yatambayeta yana me ƙaremawa fuskarta kallo,, fuska ta kuma kwaɓewa, haɗe da kaɗa kanta, cike da shagwaɓa tace
“Ina Husnah?”
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da sanya hanu yashafi lallausan gashinta dayasha gyara
“Husnah kuma Zahrah?” yatambayeta cike da mamaki..
“Eh tacemin zata amasa waya tana zuwa kuma haryanzu bata dawo ba!” yanzuma dai asangarce tayi maganar,, murmushi yayi mata haɗe da cewa
“Kada kidamu Husnah zata dawo gobe, taso muje kiyi alwala idan munyi salla saikici abinci ko”
Jitayi gabanta yayi wani irin faɗuwa amma kuma yazatayi da rayuwarta babu yanda ta’iya haka tabisa kamar jela harcikin bathroom,, saida yayi nasa alwalan kafun yabata waje itama ta ɗauro alwala,, tana fitowa daga cikin bathroom ɗin ya miƙo mata wata lufaya, a ɗaɗare tasanya lufayan daya bata, hanunta yakama suka hau kan sallaya, shi yajasu salla raka’a biyu, suna idarwa yayi musu addu’o’i haɗe da kama kanta itama yayi mata addu’a… A tsorace ta zauna akan gado haɗe da sake takure jikinta waje ɗaya…
Wani ɗan madaidaicin carpet Dr.Sadeeq yashimfuɗa haɗe da cika tsakiyar carpet ɗin da kayan ciye ciye, hanu ya miƙawa Zahrah alamar tataho garesa, cikin ɗari ɗari haka ta shiga takowa zuwa inda yake, hanunta yakamo yazaunar da’ita acikin jikinsa, hijabin dake jikinta yasoma ƙoƙarin cire mata, da sauri tasake ƙanƙame jikinta, ganin haka yasanya shi yin murmushi, ya fasa cire mata hijab ɗin,, juice ya zuba acikin kofi haɗe da kai kofin bakinta, babu musu tabuɗe bakinta ta kurɓi kaɗan, aje kofin yayi, haɗe da yago gasasshen nama yakai bakinta,, kanta tashiga girgizawa alaman bazataci ba.
“Kiyi haƙuri kici kinji Baby na, kaɗan zakici bamai yawa ba!” yafaɗi haka cike da lallami,,, shida kansa yake bata kazan, bata wani ci me yawa ba tace masa ta ƙoshi, dakansa yatattara wajen yakai kitchine,, yana dawowa ɗakin yasameta tsaye ajikin mirror tayi jigum,, fargabane yacika mata zuciya, wani irin tsoro ne taji ya ɗarsu acikin zuciyarta wanda bazata iya misaltashi ba,,
STORY CONTINUES BELOW
Kaitsaye drower ɗin dake cikin ɗakin ya nufa, wata doguwar rigan bacci sleeping dress yaciro haɗe da ƙarasowa gareta,, “Kije kiyi brush, wannan kayan kuma kisanya kizo kiyi bacci” hanunta na rawa haka ta amshi kayan sumi sumi ta wuce cikin bathroom, tana kammala brush tasoma cire kayan jikinta, warware rigan da Dr. yabata tayi tashiga ƙaremawa rigan kallo, doguwar rigace na bacci me net, amma kuma tana da faɗin wuya sannan kuma rigan irin me nuna jiki ɗinnan ne,, badon tasoba haka ta sanya rigan ajikinta, hmmm sam bazata iya fita da wannan rigan gaban Dr. Sadeeq ba, saboda gaba ɗaya rigan ta bayyana breast ɗinta, yayinda komai nata yafito fili, hijabin da tayi salla dashi ta ɗauka ta sanya,, a ɗaɗare ta fito daga cikin bathroom ɗin,, zaune tagansa akan gado tuni yasanja kaya zuwa farar jallabiya, murmushi kawai Dr.Sadeeq kejifanta dashi, cikin zolaya yace “Meye narufe jikin da hijabi?”
Ƙasa takumayi da kanta, yanzu kam ko ɗan shagwaɓan ma takasayi masa…
Sarai ya fuskanci halin da take ciki, “Zoki kwanta” yafaɗi haka yana meyi mata nuni da kan gadon dayake zaune,, kamar wacce ƙwai yafashewa haka Zahrah ta zo ta kwanta akan gadon, gaba ɗaya ta takure kanta waje ɗaya,,, miƙewa yayi daga zaunen dayake haɗe da kashe wutan ɗakin ya kunna na bacci, Zahrah najin takusan alamar yakusa zuwa kan gadon taji bugun zuciyarta ya tsananta, yayinda ƙirjinta yashiga wani irin luguden duka,, kwanciyarsa akan gadon yayi dai dai da kusan ɗaukewar numfashinta,,,, da ƙyar ta’iya ƙwato numfashinta, haɗi sa soma sauƙe ajiyar zuciya a ɓoye, kusan minti goma da hawansa kan gadon amma kuma taji baiyi mata wani abu ba, hakan yasa taɗanji zuciyarta tayi sanyi. Shiru tayi tana me jin sauƙar numfashinsa ahankali, wani irin mugun tausayinsa ne taji yaɗarsu acikin zuciyarta amma kuma ita bata da yanda zatayi, tunaninta ne ya katse alokacin da taji sauƙar hanunsa a bayanta,, ahankali ya juyota tadawo tana fuskantarsa,, kallon fuskarta yashigayi batare dayace da ita komai ba, kusan mintuna 4 yayi yana kallonta, cikin wata irin murya wanda batasanshi da ita ba yace
“kicire hijabin nan saboda kiji daɗin baccinki ko”
babu musu ta cire hijabin daga jikinta sai dai kuma bahaka ranta yaso ba, bargo yaja ya rufa musu hanunta yakamo ta cikin bargon yariƙe acikin nasa, “Ki kwantar da hankalinki, nasan kingaji, kiyi addu’a, kiyi bacci me daɗi” yafaɗi haka cikin muryar raɗa, hanunta yasake damƙewa acikin nasa hanun haɗe da lumshe idanunsa, zai bartane kawai saboda tausayinta dayake ji, amma bawai don baya sha’awarta ba, hasalima baita ɓa jin matsanancin sha’awarta irin nayau ba, hakan yafarune kuma saboda baitaɓa samun kusanci me tsanani da ita irin na yau ɗin ba, da wannan tunanin bacci ya ɗaukesa,,,, Zahrah ma dai baccin ne yaɗauketa batare data shiryawa hakan ba,, ƙarfe ɗaya na dare wani irin zazzafan zazzaɓi yarufe jikin Zahrah take tasoma karkarwa haƙwaranta har haɗewa suke, suna ba da wani sauti, hakan yafaru ne kuma sakamakon sanyin AC wanda yayi mata yawa, acikin baccinsa yakejin hucin numfashinta nafita da sauri, a hankali ya buɗe idanunsa ya sauƙesu akanta, da sauri yatashi ya zauna haɗe da kamo kafaɗunta,, “Zahrah!” yaƙira sunanta a hankali,, tanajinsa amma bazata iya amsa masa ba domin kuwa ba iya zazzaɓi ba hatta kanta jinsa take tamkar anɗaura mata gungumen ice, yamata nauyi Da sauri ya sauƙa akan gadon, AC’n yafara kashewa, kana ya buɗe wata ƴar drower maganin ciwon kai da zazzaɓi ya ɗauko haɗe da goran ruwa,, yana zuwa ya ta data zaune, ɓalle maganin yayi yasa mata abaki haɗi da kafa mata goran ruwa, babu musu ta haɗiye maganin, ajiye goran yayi haɗe da hawa kan gadon, hanunsa yasanya akan wuyanta, zafi yaji zau kamar wuta, ajiyar zuciya ya sauƙe, haɗe da cire rigan dake jikinsa, cikin bargon yakoma, haɗe da jawota kusa dashi, ahankali yasanya hanunsa a bayanta yayi ƙasa da zip ɗin doguwar rigan dake jikinta,, cike da nutsuwa ya cire mata rigan,, Zahrah tana jinsa amma kuma ayanzu babu wani abu da zata iyayi wanda zata kare kanta,, bashi kaɗaiba har ita kanta saida ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi alokacin da zallan fatar jikinsu suka samu haɗewa waje guda. lokaci ɗaya yaji tunaninsa yasoma sauyawa, nutsuwarsa tafara gushewa, haka kuma idanunsa sun soma rufewa,, haɗewar jikin Zahrah danasa jikin baƙaramin feeling me girman gaske ya sauƙar masa ba, tunda yake aduniyarsa yau shine karo na farko, da ya fara haɗa jikinsa dana mace haka, yasan yataɓa rungumar Zahrah amma ba runguma irin wannan ba,,,, Zahrah kuwa baƙaramin jin daɗin jikin nasa tayi ba, jitayi gaba ɗaya nutsuwa yasoma sauƙar mata, sake maƙalewa ajikinsa tayi haɗe da cusa kanta acikin faffaɗan ƙirjinsa har yazamana laɓɓan ta suna gogan fatar wuyansa,, jin yanda take ƙara shigewa jikinsa shiya ƙara taimakawa wajen ƙara masa wutar sha’awarta, hannayensa duka yasanya a bayanta yasake riƙeta gam, numfashi kawai yake fitarwa akai akai shi kaɗai yasan meyakeji acikin jikinsa,, yana cikin wannan irin yanayin yaji sauƙar numfashin Zahrah ahankali yana fita da’alama baccine yakuma ɗaukarta,,, haka yarungumeta ƙam acikin jikinsa yayinda yacusa kansa acikin gashin kanta yana shaƙan daddaɗan ƙamshinta dake ƙara rikitasa,, bakaɗan ba ya yi jarumta wajen ganin ya ƙyaleta baiyi mata komai ba, haƙiƙa bakowani irin namiji bane zai haɗa jiki da mace ace ya iya daure zuciyarsa baiyi mata komai ba, balle ma mace irin Zahrah wanda irinsu basu da yawa acikin mata,, da ƙyar bacci ya’iya ɗaukarsa…….
Ƙiran sallan asuban fari akan kunnensa,, a hankali ya ware idanunsa akanta, baccinta takeyi cikin kwanciyar hankali da’alama zazzaɓi da ciwon kan dake damunta sun jima da kama gabansu,, baisan lokacin da murmushi ya ƙwace masa ba, komai na Zahrah me kyau ne, har idan tana bacci kyawunta baya ɓuya, kallon zara zaran eye lashes ɗinta daya kwanto aɗan ƙasan idanunta yayi,, ahankali ya zare jikinsa daga nata jikin, cikin sanɗa yatura ƙofar bathroom yashige, gudun kada motsinsa ya tashe ta daga daddaɗan baccin da take,, saida yafarayin wanka kafun ya ɗauro alwala,, tsayawa yayi yana kallon yanda taketa fidda numfashi a hankali, badon sallah yazama dole akanta ba, to tabbas da babu abun da zai sanya ya tasheta a dai-dai wannan lokacin, zai bartane tasha baccinta ta ƙoshi,, ahankali yashiga girgiza ƙafanta haɗe da ɗan ƙiran sunanta, cikin murya ƙasa ƙasa… Da yake bata da nauyin bacci, ƙira biyu yayi mata ta buɗe idanunta,, da sauri ta sake jawo bargo ta rufe jikinta, kana tasoma raba idanu, murmushi yakumayi mata haɗe da sanya hanu ya shafi gefen kumatunta.+
“Kitashi kiyi sallah, ni na wuce masallaci”
Bata iya amsa masa ba haryafice daga cikin ɗakin,, kallon kanta tashiga yi gaba ɗaya gashinta ya watse yayi buji buji dashi, da’alama dai tasha juyi acikin bacci,,, tana shiga bathroom ta haɗawa kanta ruwa me ɗan ɗumi, wanka tayi itama kana ta ɗauro alwala (🤔Yadai dukanku wanka sai kace 🙊)….3
Tana fitowa daga bathroom ɗin ta zura wata jan doguwar riga marar nauyi, haɗe da zura hijab ajikinta, kan sallaya tahau haɗe da dai-dai ta tsayuwarta…… Koda ta’idar da sallan saida tayi azkar kafun ta miƙe daga kan sallayan,, harta zauna akan gado, maganganun Hajiya Shuwa suka faɗo mata arai inda take ce mata _”Kada ta sake ƙamshi yabar jikinta, sannan kuma idan tayi sallan asuba kullum tana shafa turare aduk wani lungu da saƙo na jikinta”_ batasan mene manufar hakan ba, amma dai ta ɗau maganar kuma zatayi aiki dashi. Gaban mirror tanufa haɗe da ɗaukan ƴar ƙaramar hand bag ɗinta dake aje kan mirror’n wani ɗan kwalban body spray ta ciro daga cikin jakar, haɗe da fesawa ajikinta, daga kan wuyanta har zuwa bayan kunnenta, sosai turaren yake da ƙamshi, take ɗakin ya gauraye da ƙamshin turaren,, tana shirin maida turaren cikin jakarta, Dr.Sadeeq yaturo ƙofar yashigo bakinsa ɗauke da sallama,, cikin murya me sanyi ta amsa masa sallaman nasa,, direct inda take tsaye ya nufo, batayi tsammani ba saiji tayi ya buɗe hannuwansa ya rungumeta ta baya haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta,,,, idanunsa ya lumshe haɗe da buɗe hanci ya shaƙi daddaɗan ƙamshin dake fita ajikinta cikin wata irin murya yace
“Good morning madam!”
Kunyan sane yakamata, saikawai tayi ƙasa da kanta haɗe da cewa
“Ina kwana”
“Lafiya ƙalau, yajikinki?” ya amsa mata yana me cusa kansa acikin wuyanta..
“Da sauƙi”
Ta mayarmai da amsa cikin ƙasa da murya…
“Ƙamshinki yamin daɗi sosai, kinyi sallah ne?”
STORY CONTINUES BELOW
Kanta ta ƙaɗa masa alamar “Eh” hanunta yakama yajata zuwa kan gado… Zama yayi kana ya jawota jikinsa,, ɗago fuskarta yayi haɗe da jefa idanunsa cikin nata. Sunanta yaƙira cikin wata irin murya me ɗauke da nutsuwa..
Kanta ta ɗago ta kallesa, ganin idanunsa tsaye cak akanta yasanya tayi saurin meda kanta ƙasa..
“Meyasa kikejin kunya na sosai ne?”
Yayi mata tambayar da bata tsammata ba,, jijjiga kanta tayi alaman
“babu”
Sake matseta acikin jikinsa yayi haɗe da kwantar da kansa akan kafaɗanta.
“Mallakarki danayi wata babban nasara ce dana samu acikin rayuwata Zahrah, inasonki ne da duka zuciyata, dakuma iya gaskiyata, banda niyar cutar dake acikin rayuwar zaman aurenmu, abu ɗaya nakeso kiyi mini shine, ki rage yawan tunani da kuma kukan nan dakikeyi, inajin tsoro kada su haifarmiki da wata cuta, yanzu nasan kina da buƙatar hutu ko, ki kwanta ki huta, kafun anjima sai kiyi break fast”
Miƙewa tayi daga jikinsa haɗe da hayewa kan gadon ta kwanta, amma kuma bata ɗauke idanunta akansa ba, bayan kamar mintuna biyar da kwanciyarta shima yatashi daga zaunen da yake, kan gadon ya hau, har Zahrah taji bugun zuciyarta yasoma ƙaruwa, sai kuma taga ya lulluɓe mata duka jikinta da blanket, agefe da ita ya kwanta haɗe da juya mata baya… Shiru ɗakin ya ɗauka babu abun dake tashi sai sautin fitar numfashinsu,,, bayansa ta kafe da idanu, yayinda a cikin zuciyarta take wani tunani na daban, haƙiƙa duk duniya babu wani namiji daya dace yazamo miji agareta sama da Dr.Sadeeq, ya cancanta ƙwarai, shi mutum ne wanda zaiyi wahala asamu kamarsa, Dr.Sadeeq kuwa lumshe idanunsa yayi bawai don bacci ya ɗauke sa ba,, shima wani tunanin yakeyi daban, baisan meyasa aduk sanda idanunsa zasuyi masa tozali da Zahrah yakejin matsanancin sha’awarta ba, wanda ada kuma ba haka abun yake ba, bazaice da bayajin sha’awarta ba, yanaji sai dai kuma bakamar wanda yakeji yanzu ba, jiya bakaɗan ba ya’iya daure zuciyarsa, amma daba haka ba tabbas da baisan wani irin aika aika zaiyi mata ba, a hankali yaji idanunsa sun soma rufewa da’alama dai shima bacci bai ishesa ba, ae dole ma jiya sunsha gajiya sosai,, cikin mintuna ƙalilan bacci ya ɗauki ma’auratan biyu, yayinda kowanne daga cikinsu da irin samfurin tunanin dake cikin zuciyarsa….
***1
10:00 am dai-dai ta buɗe idanunta, haɗe da waresu akan haɗaɗɗen zanen POP’n da ya cika saman ɗakin, kallonta ta mayar ga inda take tsammanin ganinsa, amma sai dai taga wajen wayam babu shi babu alamarsa. Da sauri ta tashi zaune haɗe da maida kallonta ga wani ɗan madaidaicin agogon bangon dake saƙale jikin ginin ɗakin.
“ƙarfe 10 nakai ina bacci?”
ta tambayi kanta cikin yanayi naɗan mamaki.. A hankali tazuro ƙafafunta ƙasa, haɗe da miƙewa tsaye, ɗakalallen cikinta daya soma mata kukan yunwa ta shafa, haɗi da ɗan yamutsa fuskarta, direct ƙofar bathromm ta nufa, ɗan tsayawa tayi ta kasa kunnenta ajikin ƙofar, koda zataji ƙaran ruwa, amma saitaji shiru da’alama dai bakowa acikin bathroom ɗin, murɗa handle ɗin ƙofar tayi tashige ciki,, ruwan wanka ta haɗa yayinda ta cika turaren ƙamshi acikin ruwan, wankanta tayi cike da nutsuwa… Sanye da wani ɗan madaidaicin towel pink colour ajikinta tafito daga cikin bathroom ɗin, hatta gashin kanta ajiƙe yaƙe, still ƙaramin towel ne kuma riƙe ahanunta tana goge gashin kanta dayake ajiƙe,, daidai lokacin Dr.Sadeeq yaturo ƙofar ahankali yashigo, suman tsaye yayi ajikin ƙofar yana me ƙare mata kallo daga sama har ƙasanta, yayinda ita kuwa batasan ma da zuwansa ba, kanta kawai take aikin gogewa, saboda bataji motsin buɗewar ƙofar ba, shikuwa dama yabuɗe ƙofar ne ahankali gudun kada ya tasheta a baccin daya barta tanayi,, wani yawu ya haɗiye, haɗe da jan ƙafansa a hankali yafice daga cikin ɗakin batare daya bari ta ganshi ba,, yana fita yajingina bayansa da ƙofar haɗe da sauƙe wani irin ƙaton ajiyar zuciya,, lumshe idanunsa yayi haɗe da sanya hanunsa acikin tulin sumar kansa yashiga shafawa a hankali,, ashe haɗuwar Zahrah yawuce yanda yake zato yake kuma tunani, wannan wace irin haɗaɗɗiyar surace Zahrah’n sa ta mallaka,, lallai Zahrah mace ce cikakkiya tagaban kwatance,, da ƙyar ya’iya jan ƙafansa ya koma cikin falo, kwanciya yayi akan kujera haɗe da lumshe idanunsa da suka sauya launi lokaci guda…
STORY CONTINUES BELOW
Zahrah kuwa tana gama goge gashin nata tayi amfani da hand dryer wajen busar dashi mintuna kaɗan gashin yabushe tashafa masa mai,,, wani lotion me ƙamshi ta shafa ajikinta haɗe da murzawa fuskarta hoda da kuma kwalli, light pink lipstick tagoga akan leɓenta, take fuskarta ta tasake yin kyau,, gaban makeken drower’n dake kafe ajikin bangon ɗakin taƙarasa haɗe da buɗewa, kayane jere reras acikin drower’n kala kala sai wanda ranka yaso zaka saka, wata jar atamfa taciro wacce taji ɗinkin pencil gown,, tana sanya doguwar rigan yayi mata kyau haɗe dayi mata ɗas ajikinta, daga kan guiwanta harzuwa ƙafarta atsage yake ta bayan rigan, tanason atamfar sosai saboda tana ɗaya daga cikin kayan da Maman Husnah ta bata, Husnah ce kuma takai akayi mata irin wannan ɗinkin duk da kuwa irin tsadar da atamfar take dashi, kallon kanta tayi acikin madubi, murmushi tasakarwa kanta saboda ita kanta ta yaba da yanda rigan tayi mata kyau ajiki, wani ɗan madaidaicin vail me kalan ja ta ɗauka haɗe da rufe jikinta, duk da kuwa cewa kayan yana da ɗan kwali, sai dai bazata iya tafiya daga ita sai wannan rigan agaban Doctor ba saboda sosai hips ɗinta suka bayyana, ga shi breast ɗinta sun bayyana kansu ta saman rigar kasancewar wuyan rigan yana da ɗan faɗi. Da turaruka masu daɗi ta feshe jikinta… A hankali ta buɗe murfin ƙofar ɗakin tafito, ɗan tsayawa tayi tana kallonsa,, kwance yake akan kujera yayinda idanunsa ke a lumshe, yasha adonsa cikin wata bugaggiyar shadda blue colour. Murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau, sosai kuma hasken fatarsa yasake bayyana acikin blue ɗin kayan. A hankali tashiga takawa har zuwa tsakiyar falon, ƙarewa falon kallo tashiga yi, ita dai haryanzu bata gamsu da cewa wai nan ɗin falon ta bane, koda wasa ma bata taɓa tunanin zata shiga cikin daula irin wannan ba,, bata ankara ba saiji tayi anriƙe mata hanu, da dauri ta juyo don batayi zaton idonsa biyu ba,, Murmushi yasakar mata haɗe da cewa,
“yaushe kika tashi?” yayi tambayar kamar bashi yaganta ɗazu ba..
Zama tayi akan kujera haɗe da cewa ” banjima da tashi ba”
Tashi yayi daga kan kujeran haɗe da kama hanunta, kaitsaye haɗaɗɗen darny area’n dake cikin falon yanufa da’ita, jawo kujera ɗaya yayi daga cikin kujeru huɗu dasuka ke waye wani babban table, zaunar da’ita yayi haɗe da buɗe wani babban food flask, plate ya ɗauka yazu ba mata soyayyen dankalin turawa’n dake cikin kulan (Chips) wata food flask ɗin yasake jawowa pepper chicken ne dayasha albasa, shima zuba mata yayi haɗe da haɗa tea acikin wani cup, turo mata duka plates ɗin dakuma cup ɗin tea ɗin yayi gabanta,, saurin ɗago kanta tayi ta kallesa, kansa ya jinjina mata alamar koma me take tunani hakane, take ta shagwaɓe fuska haɗe da cewa “Bazan iya cinye duka wannan abincin ba yamin yawa”
“Bakomai kici sosai, nasan kinajin yunwa” yafaɗi haka yana me ƙoƙarin barin wajen.
“Kai kuma fa?” batare da ta shiryawa fitowar tambayarba, saikuma bakinta yayi saurinfurtawa,, tsayawa yayi da tafiyar haɗe da juyowa, murmushi yayi mata haɗe da cewa “Ni bayanzu zanci ba” harya fice daga cikin falon bata ɗauke idanunta daga kansa ba,, ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da ɗaukan fork tasoma cakan chips ɗin tana kaiwa bakinta, dama yunwa takeji sosai,, sosai taci chips ɗin saidai tea ɗin sama sama tasha shi, naman kuwa ko taɓa shi batayi ba, domin ita gaba ɗaya naman kaza baiwani dameta ba, tafison gasashshen naman sa, fiye da na kaza, sai da taji cikinta yayi haniƙan kafun ta kimtsa wajen haɗe da miƙewa takoma cikin falon,, haryanzu dai idanunta basu ƙoshi da ƙarewa falon kallo ba, rayuwa kenan wai yau ita Zahrah ce zaune acikin wannan katafaren gida dasunan gidan aurenta, ita da ko gado bata dashi akan zallan ƴar katifa take kwana sai gata yau ta kwana akan haɗaɗɗen gado harda lallausan bargo da ta rufa dashi,, a hankali ya turo ƙofar falon yashigo, wayarsace riƙe a hanunsa yana latsawa,, gaf da’ita ya zauna har kafaɗunsu suna gogan na juna, hanunsa ya sanya ya shafi ɗa kalallen cikinta, “Wannan ɗan ƙaramin cikin baiƙoshi ba”
Murmushi tayi masa haɗe da waro idanunta “Dan Allah kayi haƙuri wallahi na ƙoshi” tafaɗi haka tana me ɗauke hanunsa daga kan cikinta.. Kallonta yashigayi yana me karantar yanayinta yayinda ita kuma tayi ƙasa da kanta, batason haɗa idanu dashi kwata kwata, “taso muje” yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye, babu musu ta miƙe, hanunta ya kama suka nufi wata ƙofa dake cikin falon, key ya sanya ajikin ƙofar ya murɗa, tura ƙofar ɗakin yayi, still hanunta na riƙe acikin nasa hanun suka kutsa cikin falo’n, falone ma dai-dai ci wanda aka kewaye tsakiyansa, da wasu kujeru dark purple masu kyau, yayinda tsakiyar falon kuwa aka cike sa da wani ɗan madaidaicin chanies carpet dark and light purple colour, wasu labulaye masu kyau kalan light purpule su suka ƙawata jikin ƙofa dakuma windown falon, wani ɗan ƙaramin plasma ne maƙale ajikin bangon falon, su kenan iya abun dake cikin falon amma kuma duk da haka falon yayi kyau, kasancewar kalan kujeru da labulayen kalane me ɗaukar hankali, ga kujerun sunsha pillow ƴan ma dai-dai ta gwanin ban sha’awa, yana riƙe da hanunta suka kuma shiga cikin wani ɗaki dake cikin falon,, gadone me kyau irin na zamani da drower’nsa me ɗauke da murafe shida, sai kuma su dressing mirror dakuma abun aje takalma da jaka,, kayan furnitures ɗin bawasu masu tsada bane daga kujerun har gadon bazasu wuce dubu ɗari huɗu ba, amma kuma anyi kayan da kyau da kuma inganci,, kallon sa Zahrah tayi alamar tanason ƙarin bayani,, murmushi yasakar mata haɗe da sa hanu ya shafa kumatunta, yace da’ita
“Kayan ɗakin da Baffa yayi miki ne”
STORY CONTINUES BELOW
Daɗi da farinciki ne suka cika zuciyar Zahrah take tacigaba da wurga idanunta tana kallon kayan, Allah sarki Baffa ashe haka yayi mata ƙoƙari batasani ba, lallai Baffa yafaranta ranta sosai, bata taɓa tunanin zata samu kaya haka ba, ashe dai Baffa yanasonta yana kuma ƙaunar fitar da’ita kunya, lallai wannan kaya sunfiye mata komai, saboda koba komai zata tsallakewa gorin wasu mutanen, wani irin tausayin Baffan nata ne taji ya sake ɗarsuwa aranta,, duk da cewa shiba mawadaci bane amma yayi ƙoƙari ya wadata ta da kayan ɗaki masu kyau dai dai da me rufin asiri, babu abun da zatace da baffanta sai godiya,, kan gadon taje ta zauna tana murmushin jin daɗi, sai taji tafi ƙaunar ɗakin ma fiye da wanda aka kaita daga farko, duk daɗin kyauta dai baikai ace da kuɗinka kacire ka saya ba.
“Yanaga kin wani zauna madam? taso muje nunamiki kawai nayi, bawai nace anan zaki zauna ba” Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me miƙa mata hanunsa alamar takama sutafi,,
Shagwaɓe fuska Zahrah tayi haɗe da kwantar dakanta gefe
“Nidai nafison nan please kabarni anan!” taƙare maganar cike da zallan shagwaɓa..
Takowa yayi yazo gaf da’ita haɗe da sanya hanunsa ya ɗago kafaɗunta.
“Nan ɗakin hutawan kine, can kuma ɗakin aurenki ne ɗakin dana zaɓa mana ni dake domin muyi rayuwar auren mu, kodai baki yaba da zaɓin nawa bane? kokuma baki amshi kyautar danayi miki bane?”
Ɗara ɗaran idanunta ta ɗago ta sauƙesu akan nasa idanun, kanta ta girgiza cikin sanyin murya tace ” Ba haka nake nufi ba, kuma nayarda da duk inda kazaɓamin zanyi rayuwa aciki, kayi haƙuri idan maganata ta ɓata maka rai ban…..”
“Shiiiiii” ya katseta ta hanyar ɗaura hanunsa akan laɓɓanta, jawota jikinsa yayi , haɗe da sanya yatsarsa yashiga zagaye ɗan ƙaramin bakinta,, ƙasa tayi da’idanunta domin kuwa bazata iya jure kallon cikin idanunsa ba, sake matso da fuskarsa yayi daf da tata har numfashinsu na’iya gauraya waje guda, yayinda dogon hancinsa ke gogan nata hancin, atare suka lumshe idanunsu, ahankali laɓɓansa suka sauƙa akan nata laɓɓan, baikai ga soma yin kissing ɗinta ba ƙaran wayarsa ta karaɗe cikin kunnuwansu, da sauri ya sake ta,haɗe da sanya hanu acikin aljihunsa ya ciro wayarsa dake ta faman ƙara, katse ƙiran yayi haɗe da kashe wayar baki ɗayanta ya kuma maidata cikin aljihun rigansa.
Hannayenta dake cikin nasa hanun ya murza haɗe da ɗanyin ƙasa da murya “Kibani aron 1 hour inaso in ɗan fita”
Batasan lokacin da ta ɗago kanta ta kallesa ba, mamaki ya bata wai ta basa aron 1 hour shida ƙafarsa ae bazata ɗaure saba,
Baijirayi abun da zatace ba yakama hanunta suka fice daga cikin ɗakin, direct asalin falonsu suka dawo, matsawa kusa da’ita yayi ya manna mata kiss akan goshinta, haɗe da cewa “Sainadawo” adawo lapia tayi masa cike da kunyar sunbatar da yayi mata agoshinta,, tanajin tashin motarsa ta sauƙe ajiyar zuciya haɗe da zama akan kujera tamaida hankalinta ga tv, a zuciyarta kuwa hamdala take da Allah yasa bai sumbaceta ɗazu ba, itakam matuƙar kunyarsa takeji, sosai yakeyi mata kwarjini acikin idanunta…..
***
*GERMANY*
Tunda suka iso cikin ƙasar suka kuma sauƙa ababban asibitin dake cikin birnin Germany ɗin Zaid bai buɗe idanunsa ba, duk da kuwa irin kulawan da ƙwararrun likitotin asibiti’n suka basa, bawai baya cikin hayyacinsa bane, sarai yana a cikin hayyacinsa, ƙunci da kuma tarin damuwa me tsanani ne suka hanasa buɗe idanunsa, baison ya buɗe idanunsa kunnuwansa su jiye masa labarin cewa anɗaura auren Zahrah, baya buƙatar yin tozali da fuskar kowa acikin duniyar nan idan ba fuskar Zahrah ba,, yagama yarda da hukuncin da zuciyarsa ta yanke masa, lallai kwanciyarsa haka baida wani amfani, yakamata ne yatashi yayi yaƙi don samo soyayyar Zahrah, idan har bai manta da date ɗin daya gani ajikin katin auren ba, to jiya ne ɗaurin aurenta, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka silalo daga cikin idanunsa haɗe da gangarowa tagefen kumatunsa,, a hankali ya ware idanunsa da suka jima da rikiɗewa suka zama jajur dasu, baya tunanin zaisake samun farinciki acikin rayuwarsa matuƙar yarasa abar ƙaunarsa Zahrah, tashi yayi zaune haɗe da rumtse idanunsa, ƙuna yakeji acikin ƙirjinsa sai dai kuma zafin wannan ƙunan baikai zafin ƙunan da soyayyar Zahrah keyi masa azuciyarsa ba,,, Alhaji Ma’aruf dake tsaye a wajen ɗakin da Zaid ɗin ke kwance, ta cikin makeken glass ɗin daya zamewa ɗakin window ya hango Zaid ya tashi zaune, da sauri yaje ya ƙira Doctor domin kuwa tunda suka zo Zaid ɗin bai motsaba sai yanzu,, ƙa’idansu ne idan zasu duba marar lafiya babu wani me shiga kansu harsai sun ga babu wani matsala sannan zasu bar ƴan uwansa suje kansa,, hakan yasa dole Alhaji Ma’aruf ya dakata daga waje likitan shi kaɗai ya shiga.. Bayan kamar wasu mintuna likitan yafito yabawa Alhaji Ma’aruf daman ganin Zaid ɗin, ae ba’iya Alhaji Ma’aruf kaɗai ba hadda Mum suka rankaya zuwa cikin ɗakin,, har gabansa dukansu suka ƙarasa, hanu Alhaji Ma’aruf ya ɗaura akan kafaɗan Zaid haɗe da cewa “Ya ƙarfin jikin naka?”
Bai amsa musu ba saima kallonsu daya shiga yi kamar wani wawa…
“Ina Zahrah?” shine abun daya iya fitowa daga cikin bakinsa kawai, saboda shine abun dake cikin zuciyarsa..
Kallon Kallo Alhaji Ma’aruf da Mum suka shiga yiwa juna, sukam dai basuda wani amsa da za su bashi domin kuwa sarai labarin Auren Zahrah ya isa ga kunnensu, yanzu haka itaɗin matar wani ce, babu amfanin ɗago zancenta…
Alhaji Ma’aruf ne yayi ta maza haɗe da sauƙe ajiyar zuciya cike da lallashi yakuma dafa kafaɗun ɗan nasa ” Yanzu ba lokacin damuwa bane Zaid, bakuma lokacin daza ka sa kanka acikin ƙunci bane, kabar maganan Zahrah, yanzu samun lafiyarka yafi komai a wajen mu, idan kasamu lafiya sai ayi abun daya dace amma maganar Zahrah abarshi” Alhaji Ma’aruf yaƙare maganar cikin kwantar da murya.
Laɓɓansa ya cije haɗe da girgiza kansa
” Bazan taɓa samun nutsuwa da salama ba Dad har sai Zahrah tazamo tawa, Inasonta Dad, so ba irin na wasa ba, samunta ayanzu yafiyemin komai, taɓa kaji Dad, zuciyata takusa bugawa akan soyayyarta, ba irin bugawan da kasani ba Dad, Bugawa zatayi tayanda bazata sake aiki ba har abada kuwa!” Zaid yaƙare maganar yana me ɗaura hanun Dad ɗinsa akan ƙirjinsa dai dai saitin da zuciyarsa take….
“Baka da hankaline Zaid? ka kosan mekake cewa? wani irin mahaukaciyar soyayya ce wannan? anya kuwa Zaid baka zautu akan wannan banzar soyayyarba?” Mum ta tambayesa cikin yanayi na ɓacin rai, sosai abun nasa yanzu yake sosa mata rai..
“Mutuwa zanyi Mum akan Zahrah zan iyayin komai wallahi dagaske ni mahaukacine akan soyayyarta inason….”
“Kanasonta ko, shikenan tunda baka gujewa saɓon Allah saikaci gaba da sonta idan zaka sameta, domin kuwa yanzu ta riga da tayi maka nisa, saboda matar wani ce!” Mum tafaɗi haka ta hanyar katsesa daga maganar dayake…
Tamkar sauƙar guduma aka haka yaji sauƙan maganganun mahaifiyartasa acikin kunnuwansa,, kallonsa yamayar ga Dad ɗinsa,, kai Alhaji Ma’aruf ya jinjina masa alamar kalaman mahaifiyarsa gaskiya ne..
“Zahrah zata dawo gareka idan har Allah ya rubuta cewa itaɗin matarkace, amma yanzu kacireta acikin zuciyarka, saboda ahalin yanzu Zahrah tajima da zama mallakin wani, kasani kuma tunata da kuma cigaba da sonta zai iya jefaka cikin halaka” Dad yafaɗi haka ga ɗannasa cikin tsananin tausayawa…2
Dafe ƙirjinsa yayi da sauri haɗe da cije laɓɓansa, da ƙyar ya’iya motsa laɓɓansa aniyarsa yafurta wata kalma, sai kuma labari yasha banban, tarine ya sarƙesa, take jini yasoma fitowa daga cikin bakinsa, ƙoƙarin riƙesa Dad yasomayi amma kuma kafun yakai ga riƙesa tuni yafaɗo daga kan gadon, Mum kuwa tuni tafice aɗakin taje taƙira Doctor’s,, kafun Doctors ɗinma suzo tuni Zaid yayi mugun fita acikin hayyacinsa, gaba ɗaya jini ya ɓata gaban rigar dake jikinsa, idanunsa ne suka juye wani irin numfashi yaja me sauti, saikuma komai na jikinsa yasake alokaci guda, daidai lokacin Likitoti suka ƙaraso cikin ɗakin …. Taimakon gaggawa suka shiga bashi don ceto rayuwarsa cikin ikon Allah kuwa suka samu numfashinsa ya dai-dai ta, allurai suka narka masa wanda zasu sanyasa bacci…
Babban likitan dake kula da al’amuran Zaid ɗinne, ya rufe Dad da faɗa akan wai saboda me yasa aka faɗawa Zaid ɗin maganar da zata tada masa da hankali, haƙuri Dad yashiga bawa Doctor ɗin, sharuɗa masu tsauri Doctor ya shumfuɗa musu, akan cewa lallai dole babu wanda zai sake ganawa da Zaid ɗin harsai bayan kwana uku, sannan kuma koda sunkoma gida yazama dole akiyaye shiga damuwa dakuma ɓacin ransa, saboda yanzu zuciyarsa tazama kamar wani ɗanyen ƙwai sai anayi ana lallaɓata, zuwa yanzu abu kaɗan ne zai sanya ta buga, wanda hakan kuwa dai dai yake da rasa rayuwar Zaid ɗin baki ɗaya
***
Bayan awanni 4
Shikaɗai yasan irin raɗaɗi dakuma ciwon dake kwance acikin zuciyarsa, hawayene suke ta fita daga cikin idanunsa suna gangara akan ƙuncinsa,, “Da gaskene Zahrah’n sa tayi aure? me yasa Zahrah zatayi masa haka? Bazai taɓa iya jurwa ba, lallai koda Zahrah tayi aure bazai taɓa daina sonta ba, kuma koda duka mutanen duniya zasu taru akansa bazai sanja ƙudurin dake zuciyarsa na auren Zahrah ba, zaiyi duk wani abu wanda yasan Zahrah zata dawo garesa koda kuwa hakan zaijawo sanadiyar rasa rayuka ne, ZAHRAH kawai yasani kuma itace cikar burinsa”….. (😲karya kasheni nima🏃♀🏃♀)
*NIGERIA*+
Tunda Doctor yafita baisake dawowa cikin gidanba harkuwa Zahrah ta ƙaraci zamanta acikin falon ta koma uwar ɗaka, sai dai kuma yayi mata waya yasanar mata cewa yana gidan Hajiyarsa wani uzuri ne ya riƙesa…
***
Idar da sallan isha ɗinta kenan ta miƙe haɗe da ƙarasawa gaban dressing mirror, lotion ɗinta me ƙamshi ta shafa ajikinta, powder kawai ta shafa akan fuskarta sai kuma man leɓe… Wata rubber pencil gown maroon colour ta sanya ajikinta, rigace irin marar nauyi ɗinnan sannan kuma an cika gabanta da fararen duwatsu wato (stones) wani maroon ɗin mayafi me ɗan kauri ta ɗauka haɗe da kafa ɗaurin ɗan kwalin nan na turban akanta, sosai tayi kyau saikace wata balarabiya, zama tayi akan gado haɗe da jawo wayarta, ajiyar zuciya ta sauƙe, har cikin ranta tana mamaki ƙwarai na rashin dawowan Dr.Sadeeq, tun safe daya fita haryanzu baidawo ba,, tashi tayi ta rage gudun ac’n dake cikin ɗakin, haɗe da ɗaukar wayarta tafice zuwa falo, hankalinta gaba ɗaya ta maida kan tashan MBC Bollywood da suke haska film ɗin nan me suna SANAM TERI KASAM bata taɓa kallon film ɗin ba amma kuma tana da waƙoƙin film ɗin acikin wayarta saboda sosai waƙoƙin sukeyi mata daɗi,, ta shagala a kallon film ɗin har idanunta sunfara kawo ƙwalla saboda tausayi, jitayi ansanya hanu anrufe idanunta , a razane ta ƙwalla ƙara domin kuwa sam bataji motsin shigowan mutum cikin falon ba, da sauri tature wanda yarufe mata idanun gefe haɗe da tashi tsaye,, ganin cewa shine yasanya tashiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai,, murmushi yasakamar mata haɗe da cewa
“Matsoraciya”
Zama yayi akan kujera,, itama zama tayi tana me da numfashi sosai yatsorata ta donkuwa bata tsammata cewa shi bane sam ta manta ma da cewa babu mayafi ajikinta… Kafeta da’idanunsa yayi yana me ƙarewa kwalliyartata kallo,, sai alokacin ta ankara da irin kallon dayake jifanta dashi.
“Sannu da dawowa!” tafaɗi haka cikin sassanyar murya.
“Yauwa, kimin afuwa najima da yawa” yafaɗi haka yana me sanya hanunsa ya kama kunnensa alamar yana neman afuwa, murmushi kawai tayi masa haɗe dayin ƙasa dakanta…
Miƙewa tsaye yayi haɗe da cewa “Bari naje nayi wanka, akwai kayan fruit acikin fridge please kiɗan yanka min kafun na fito”
“To” kawai tace dashi haɗe da tashi tanufi wajen fridge ɗin shikuma direct ya wuce ɗaki donyin wanka…
Tana kammala yanka fruit ɗin ta ɗauko wani plate me kyau tarufe yankakken fruit ɗin, kan kujera ta koma ta zauna haɗe da sake maida hankalinta ga tv.. Sanye da tree guater jeans ajikinsa haɗi da wata farar t-shirt ya fito, ƙamshi kawai yake fitarwa, satan kallonsa Zahrah tayi haɗe da ɗan sakin murmushi, bata taɓa ganinsa acikin irin wannan shigar ba amma kuma yayi mata kyau sosai.. Akan lallausan carpet ɗin dake malale tsakiyar falon ya zauna haɗe da tanƙwashe ƙafafunsa, alama yayi mata da hanunsa cewa ta miƙo masa fruit ɗin, ɗaukan plate ɗin tayi taƙarasa gabansa, durƙusawa tayi har ƙasa kana ta aje plate ɗin,, “Miƙomin wancan ledan” yafaɗi haka yana meyi mata nuni da leda wanda shiya shigo dashi sam ita batama lura ba,, cike da nutsuwa taɗauko ledan kamar yanda ya umarceta ɗan duƙawa tayi haɗe da miƙa masa ledan,, amaimakon yakarɓi ledan sai taga ya jawota jikinsa, zaunar da ita yayi acikin jikinsa haɗe da sanya hanu ya zame ɗaurin turban ɗin dake kanta, take lallausan gashinta ya zubo harzuwa kan bayanta, kansa ya cusa acikin gashin nata yana me shaƙan daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikin gashin nata,, “Kiyi mini afuwa my princess, banƙi dawowa haka kawai ba!” yafaɗi haka yana me ƙara matseta acikin jikinsa.
STORY CONTINUES BELOW
“Ni bakayi mini laifi ba sam sam, nasan ae bazaka ƙi dawowa haka kawai ba” tafaɗi haka cikin zazzaƙan muryarta..
“Yauwa my wife nasanki dama kina da haƙuri, natsaya a wajen ƴar uwarki Salima ne, ina fatan banyi laifi ba?”
Da sauri tajuyo da kanta tana kallonsa, “Salima kuma? bakace tafasa aurenka ba” tatambayeshi fuskarta ɗauke da tsananin mamakin jin abundayace..
Dariya yayi ganin yanda tawani zaro idanu kishi ya bayyana akan fuskarta ƙarara daga ambatan sunan Salima.
“Wasa fa nake miki Madam, miye na wani tsorita haka” yafaɗi haka yana me ƙarewa kyakkyawar fuskarta kallo..
Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da ɓata fuska, ta juya da kanta batace dashi komai ba,, sarai ya lura taji haushi,,, yankakken apple ya ɗauka haɗe da kaiwa kusa da bakinta.. ƙin buɗe bakinta tayi saima daɗa kauda kanta da takeyi jefa apple ɗin yayi cikin bakinsa, haɗe da sanya hanu ya juyo da kanta yazama tana fuskantarsa…
“Fushi kike da mijinki? kiyi haƙuri banfaɗi haka don ranki ya ɓaci ba, wasa nake miki kiyi mini murmushi kinji Zahrah na!”
Hakanan taji zuciyarta tayi sanyi harbatasan sanda tasaki murmushi ba.. Yankakken apple yakuma ɗaukowa yakai bakinta babu musu ta buɗe bakinta yasanya mata… Tana zaune acikin jikinsa haka yaciyar da’ita domin kuwa atare sukasha fruit ɗin haɗe da ɗaura fresh milk akai.. Yana nan azaune ta tattare wajen takai kitchine haɗe da dawowa, miƙewa tsaye yayi haɗe da ƙarasawa gaban tv wanda yaketa ɓaɓatu shikaɗai ya kashe, kallonta yayi kamar zaiyi magana saikuma ya fasa, wutan falon ya kashe kana yakama hanunta suka nufi ɗaki, hmmm tun ɗazu bata ji tsoro ba sai yanzu da ta gansu sun hallara acikin bedroom, janta yayi har cikin bathroom sukayi brush… Da kansa yaciro wani ƴar fingilar rigan bacci wanda take shara shara kamar rariyan tata sai dai kuma tana da ado ata wajen wuyan.. Ganin yanufota kai tsaye ne yasanya tayi saurin saddakanta ƙasa, zuciyarta kuwa luguden duka tashiga yi mata, kamar anka mata tana sata, harga Allah ita tsoronshi take Allah yasa yauma karyayi mata komai.. Tunaninta ne ya katse sakamakon sauƙar hanunsa da taji abayanta, matsowa yayi gaf da’ita harsuna iya jiyo hucin numfashin junansu,, ahankali yayi ƙasa da zip ɗin rigar nata, lokaci guda yasanya hanu ya soma zame rigar daga kafaɗunta, rumtse idanunta tayi ƙam, haɗe da takure jikinta waje ɗaya, bazata iya hanasa ba, amma kuma dazai barta yace ta cire rigan da kanta da hakan yafiye mata komai daɗi, saboda ko bakomai zatayi iyaka ƙoƙari wajen ganin ta kare ƙirjinta, lokacin daya kawo ƙirjinta kasa jurewa tayi, dasauri ta duƙa ƙasa haɗe da cewa “Dan Allah kabarni naje toilet na cire da kaina”
Bai tanka mata ba saima ɗagota daya sakeyi tsaye, rungumeta yayi ta baya haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, hancinsa yasanya yashiga shaƙan daddaɗan ƙamshin da fatarta ke fitarwa, ahankali yake goga mata lallausan sajen sa akan fatar wuyanta yayinda yasanya hununsa duka biyu ya saƙalo ƙugunta, rumtse idanunta kawai tayi tanajinsa, yayinda zuciyarta kuwa ta ke bugawa da sauri. a hankali yashiga kissing ɗin wuyanta haɗe da soma yawo da hanunsa akan cikinta, wani iri Zahrah tasomaji acikin jikinta, yayinda gaba ɗaya tsikar jikinta ya shiga motsawa,, shi ɗin ma hakance ta kasance dashi, baisan sanda yasanya hanunsa yaci gaba da ƙoƙarin zame mata rigar dake jikinta ba,, har rigan tafaɗi ƙasa Zahrah bata ɓuɗe idanunta ba shima kuma baibuɗe nasa idanun ba, hanunsa yasanya akan lallausan fatar cikinta yashiga shafawa, cikin wani irin salo ya juyo da’ita yazamana suna fuskantar juna, dayake ɗakin babu wadataccen haske sosai, hakan yasanya baya iya ganin jikinta sosai, hanunsa yasanya duka biyu ya tallafi bayanta haɗe da kusanto da fuskarsa daf da tata, laɓɓansa yaɗaura akan nata laɓɓan tare da kama leɓenta na ƙasa yashiga tsotsa ahankali,, al’amarin dayayi mugun sanya mata shock acikin jikinta kenan, tunda take aduniyarta wani ɗa namiji baitaɓayi mata kiss ba sai Zaid, shiɗin ma kuma alokacin dayayi kissing ɗinta bata cikin nutsuwa da kuma hankalinta saboda haka babu wani abu da taji game da hakan, Dr.Sadeeq ma hakane takasance dashi saboda a iya tsawon tarihin rayuwarsa baitaɓa yiwa wata mace kiss ba, yau shine karonsa na farko… Ahankali yake shan lips ɗin nata yayinda ita kuma takasa koda ƙwaƙƙwaran motsi ne,, cikin wani irin salo ya soma tura bakinsa cikin nata bakin, harshenta ya laluɓo haɗe da soma yi masa shan lollypop,,, cikin mintunan da basu wuce 8 ba yasoma sauƙe wani irin numfashi, haɗe da sake ƙamƙameta acikin jikinsa, sosai yake kissing ɗinta yana fitar da wani irin numfashi me ɗauke da wani kalan sauti, yayinda itakuwa Zahrah ƙafafunta suka soma ƙoƙarin rugujewa ma’ana suka soma saƙewa da’alama dai abun yafi ƙarfinta,, ɗaukanta yayi caɗak yanufi kan gado da’ita, kwantar da’ita yayi haɗe da sake sanya bakinsa acikin nata,, haɗuwar fatar jikinsu waje ɗaya shiya matuƙar taimakawa kiss ɗin nasu yaƙara armashi a wajen Doctor, dan Zahrah kam tuni tazama statue.. A iya kiss kaɗai Dr.Sadeeq ya ruɗe yakuma sukurkuce, sucking tongue ɗinta kawai yake cike da nutsuwa yana me fidda wani irin numfashi, tuni idanunsa sunkaɗa sunyi jajur dasu, ƙasa yasomayi dakansa harzuwa kan cikinta, kissing ɗinka yashigayi akan cikin nata yana me shafa santala santalan cinyoyinta, hanunsa yasanya abayanta ya ɓalle maɓallin brezian dake jikinta, haba ai tuni hajiya Zahrah ta ruɗe ta sake ƙanƙame jikinta, saida yasamu shiɗewa haɗe da ɗaukewar numfashi alokacin da hanunsa suka sauƙa akan lallausan breast ɗinta wanda suke a tsaye ƙyam babu alamar kwanciya atattare dasu, bakinta yaƙara kamowa yacigaba da tsotsa yayinda yasanya hanunsa yana murza breast ɗinta ahankali, gaba ɗaya ya zauce ya ruɗe yakuma susuce yafita aduniyar mu yashiga wata duniya me cike da wani irin masifaffen sha’awa me matuƙar ƙarfi harji yake kansa nawani irin sarawa,, kuka ta fashe dashi me tsanani alokacin da taji sauƙar bakinsa akan nipple ɗinta, hmmm kukanta bazaiyi aiki ba da dukkan alamu, domin kuwa tsotsar dayakeyimawa nipple ɗin nata ma na dabanne,, da ƙyarma yake iya ƙwato numfashinsa,, duk yanda yaso ya share kukan nata yakasa, dolensa ya tsagaita haɗe da kwanciya akanta, cikin wata irin murya da take a shaƙe yace “Please Zahrah stop craying!” ae kamar cewa yayi ma taƙara volume ɗin kukan nata, kansa dake matuƙar yi masa ciwo ya dafa, haɗe da cije laɓɓansa, wallahi bazai iya jurewa ba komai zai iya faruwa dashi, yakai ƙololuwar sha’awa matuƙa, amma kuma yazaiyi da kukan da Zahrah takeyi masa yanajin tausayinta sosai, yasan ahalin yanzu metake tunawa, wancan mummunar ranan take tunawa, amma kuma haƙƙinsa ne ya mantar da ita komai. (Khair anya ruwanki bazaiyi tafasan banza ba kuwa🤔 naga mutumiyar taki tana neman hana doctor walwala🙊) Sake matseta ajikinsa yayi haɗi da haɗe bakinsu waje ɗaya, sauya salon kiss ɗin nasa yayi, wanda hakan ya tilasta mata dole tayi shiru, sai dai haryanzu jikinta bai daina ɓari ba, idan tace gangar jiki da ruhinta basa karɓan saƙon Dr.Sadeeq tayi ƙarya, amma kuma matuƙar tsoro takeji, ƙwaƙwalwarta azabar da Zaid yajiyar da’ita take tariyo mata, gani take shikenan itakam tata ta ƙare dan kuwa bazata iya jure azaba biyu ba,, salon romance ɗin da Doctor keyi mata yawuce gaban kwatance burinsa shine ya mantar da’ita wannan tsoron, ita kanta ta yarda da cewa saƙonninsa sun ratsata domin kuwa tuni ta gama jiƙewa to amma abun tsoron na gaba,, bai ɗauke bakinsa acikin nata ba haryagama ratsa cikin jikinta, wani irin wawiyar ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da sakin wani irin ƴar ƙaraman ƙara dake nuna alaman cewa mutum yagama lulawa cikin duniyar da babu irinta,, baisan dayaushe yazare bakinsa acikin nata ba, wani irin ƙara ta sake haɗe da soma rusa kuka kamar wanda ake zarewa rai…..*** Bayajinta balle kuma ganinta saboda idanuwansa rufewa sukayi ruf, duk kuka da ihun da takeyi baisan tanayinsu ba, wallahi shikam tunda yake baitaɓa sanin menene daɗi ba aduniya sai awannan lokacin, bazai taɓa iya misalta abun dayaji ba abun yafi ƙarfin tunaninsa ya shammaci hankalinsa, harya manta da cewa ita ɗin ba budurwa bace, baitaɓa kusantar wata mace ba Zahrah itace ta farko, kuma amatuƙar kame yajita gam, sai dai kuma fa har’abada baza’a haɗa virgin da kuma wacce ba virgin ba dole akwai banbanci amma shidai baiji banbancin ba saboda dama baisan kowaba sai ita*** Doctor ya hole iya holewa yayi gurnanin yayi sambatun harsau ba’adadi yayinda ƴar mutane kuwa tayi kuka kamar ranta zaifita harsaida idanunta suka kumbura alokaci guda kanta kuwa ba’a magana wajen yi mata ciwo..
***
After 1 hour.
Shikansa jikinsa zafi zau ya ɗauka yayinda yaji gaba ɗaya duniyar tana juya masa, to inaga kuma wacce ya bawa kaya, da ƙyar ya’iya kwantawa agefenta haɗe da jawota cikin jikinsa, baisan da wani kalma zaifara yi mata magana ba, kyakkyawan sumbata ya bata akan goshinta haɗe da rumtse idanunsa, wanda suke zubar da hawayen tsananin tausayinta,,, kusan 12 minute yana rungume da’ita acikin ƙirjinsa “Me daɗi na!” yafaɗi haka acikin kunnenta da’alama dai sunan daya bata kenan,lol. Zahrah da’idanunta sukayi luhu suna ta tsiyayar da hawaye kasa cedashi komai tayi.. (Su Me daɗi ansha wuya😂🙊🙈)
“I’am so sorry, banyi haka don nacutar dake ba, nakasa control ɗin kainane, Inasonki Zahrah, a iya daren yau soyayyarki ta sake ninkuwa acikin zuciyata, kiyafemin kinji me daɗi na bazan ƙara ba, please for give me!” yaƙare maganar cikin kwantar da murya, da’alama dai har yanzu giyar daɗin baigama sake shiba… Me daɗi dai taƙi cewa komai haka ya sauƙo daga kan gadon rungume da’ita kamar wata ƴar baby, direct bathroom yanufa da’ita, dakansa ya haɗa mata ruwan ɗumi haɗe da zaunar da’ita aciki, duk da cewa ita ba virgin bace amma kuma wannan ɗin ma kusan daidai yake dayinta na farko, saboda ta matuƙar shan azaba sosai, hakan yafarune kuma saboda yanda Hajiya Shuwa ta dinga ɗurka mata magungunan matsi dakuma na ciko da mace, sosai taji zafi aƙasanta lokacin da yazaunar da’ita acikin ruwan amma kuma yazatayi yazama dole ta daure.. Dakansa yayi mata wanka haɗe da naɗota acikin towel like wata ƴar ƙaraman baby, shima wanka yayi kana yafito daga cikin bathroom ɗin, shidakansa ya sanya mata rigan bacci, shima ya jallabiya ya sanya ajikinsa, haryanzu Zahrah bata daina tsiyayar da hawayeba,, new blanket yasanya musu domin kuwa wancan ya ɓaci da sperm ɗin me…. au 🙊Zahrah,, jawota yayi jikinsa haɗe da rungumeta tsam tsam jiyake kamar wani zaizo ya ƙwace masa ita (wai inji nuru ba kama bane Zaid yananan tafe😂 niko nace yayi ƙarya)
Hawayen da suketa ambaliyan sauƙa akan fuskarta yashiga share mata, haɗe da ɓare wani sweet yajefa acikin bakinsa, kwantar da’ita yayi akan ƙirjinsa haɗe da ɗago fuskarta ya tura mata sweet ɗin acikin bakinta, harshensa yasanya yana meyi mata wasa da sweet ɗin acikin bakinta, lumshe idanunta tayi tana me sauƙe ajiyar zuciya, yayinda yake shafa mata bayanta ahankali,,har wani irin nannauyan bacci yazo ya ɗauketa….. Kafeta yayi da idanunsa aransa yana me godia ga Allah daya basa wannan mata me ɗauke da tarin ni’imomi na fili dana baɗini, kai yasha sweet fa yau harwani jin kansa yake a sama.Lol,,, batare da yayi aune ba shima bacci ya ɗaukesa bayan yayi musu addu’a yashafa mata… Good night angon me daɗi…Tun da ta tashi tayi sallan asuba take ta ruskar kuka tamkar wacce aka cewa wani nata ya mutu, ita kanta batasan kukan me takeyi ba, amma dai hakanan takeji zuciyarta babu daɗi, gashi gaba ɗaya jikinta ciwo yake, “Gaskiya Doctor mugune.” tafaɗi haka acikin zuciyarta, gaba ɗaya ya gajiyar da ita, daga ƙasan zuciyarta kuwa wani abune yayi mata tsaye wanda kuma shine sanadiyar kukan nata, wannan wace irin rayuwa ce? wace irin ƙaddara ce wannan? rabonta da tayi farinci me tsayi tun kafun Zaid yashigo cikin rayuwarta, ada tana ganin rayuwar da takeyi acikin gidansu rayuwar ƙunci ce, ashe bata sani ba wannan rayuwar salama ce a gareta, SO baiyi mata adalci ba, so bai kyautawa rayuwarta ba…2
Yajima tsaye akanta yana me ƙare mata kallo, mamakin yanda take kuka tsakaninta da Allah yake, a iya saninsa banda abun daya wakana atsakaninsu daren jiya baiyi mata komai ba, amma kuma sai gashi yanzu tana ruskar kuka, har a ƙasan zuciyarsa bayason kukanta, idan yaji kukanta jiyake gaba ɗaya nutsuwarsa ya ƙaura daga jikinsa,, ahankali yashiga takawa harzuwa inda take duƙe akusa da gado tana kuka, sam batamasan da shigowarsa ba kukanta kawai takeyi…. Hanunsa yasanya ya dafa kafaɗanta, da sauri ta juyo aɗan razane don bataji shigowarsa ba,, idanunsa ya ƙanƙance haɗe da waresu alokaci guda, zama yayi akan gado haɗe da ɗagota zuwa jikinsa…1
“Me yasa Zahrah? me nayi miki? meyasa kike ƙuntatawa rayuwarki akan wani dalili naki? ban aureki don nazuba miki ido kita cutar da kanki ba, please ki daure zuciyarki kidaina wannan kukan banaso!” ya faɗi maganar cikin lallashi… Saurin ɗauke hanunsa dake kan wuyanta yayi, kansa yaɗan ɗafe haɗe da zaunar da ita akan gado, direct wani ɗan madaidaicin drawer yanufa, maganin da yasan zai sauƙar mata da zazzaɓi acikin mintuna ƙalilan ya ɗauko tare da ruwan gora ya dawo zuwa gareta. Maganin ya ɓalla ahanunsa tare da jawota jikinsa, bakinta ya buɗe ya jefa maganin aciki haɗe da bata ruwa, babu musu ta haɗiye maganin bayan ta rumtse idanunta, sai kace wacce aka bawa guba… Aje goran ruwan yayi haɗe da sake jawota jikinsa, kwantar da kanta yayi akan ƙirjinsa, yayinda yake shafa bayanta a hankali. Ajiyar zuciya haɗi da sheshsheƙan kuka kawai take sauƙewa. Shikuwa Dr.Sadeeq wani tunani na daban yakeyi acikin zuciyarsa, hakanan Allah ya halittamasa tsananin tausayin Zahrah acikin zuciyarsa, yana sonta sosai, bayason yaga tana cikin damuwa, bayajin akwai wani abu aduniyar nan da Zahrah zata nema agaresa matuƙar yana dashi tarasa, zai iya mallaka mata komai nasa, matuƙar zataji daɗi, za kuma tayi farinciki, bakinsa ya kawo daf da kunnenta cikin murya me sanyi yace2
“Zahrah!”
Tanajinsa amma kuma saitayi sauri ta lumshe idanunta, tanaso ya ɗauka cewa bacci take.
Jin tayi shirune yasanya yashiga goga mata lallausan sajensa akan fatar wuyanta, yayinda yake yawo da hanunsa akan bayanta a hankali..
Luf tasakeyi acikin ƙirjinsa, tana jin saƙonsa yana tsarga mata hartafin ƙafarta, yayinda daddaɗan ƙamshin turarensa ke ƙara sanyaya mata jiki, batajin bacci ko kaɗan, amma kuma yazama dole ta ƙwaƙulowa kanta baccin dole, kodan ta samawa zuciyarta salama. “Ina laifin Dr.Sadeeq? mene bayi dashi wanda mace takeso tasamu ajikin ɗa namiji? miye laifin masoyin daya nuna maka haƙiƙanin so? ashe wani lokacin zuciya batasan menene halacci ba? me yasa SOYAYYA tazamo guguwa me hargitsa zuciyar ɗan adam tayi fatali da komai nasa?” itakam ko da a yanzu soyayya ta barta haka ta gama iya cutarta, cuta me muni ma kuwa.. Yajima yana shafa bayanta, harsai da ya ji sauƙar numfashin dake nuna cewa da gaske bacci ya ɗauketa. Kwantar da’ita yayi akan gado, haɗe da jawo blanket ya rufe mata duka jikinta, yasani sarai batason sanyi, don haka ya rage gudun A.C, kashe mata fitilan ɗakin yayi, kana ya jawo mata ƙofar ya rufe mata bayan yafita zuwa falo.. Laptop ɗinsa ya ɗauka haɗe da buɗewa, aikinsa ya shigayi cikin nutsuwa, ɗan kwana biyun nan da bai shiga office ba haryatara ayyuka masu yawa, gashi ansanar masa patients suna buƙatar taimakon sa, duk da ya ɗau hutu ma ashe bai tsira ba, ayyuka na nan akansa wanda yazamana dole sai shi zaiyisu…
***16
STORY CONTINUES BELOW
*GERMANY*
Shikaɗai yake rayuwarsa acikin ɗakin, yau kwanansa ɗaya kenan baisanya komai na abinci acikin saba, yayi matuƙar ramewa alokaci guda, yayinda gashi dakuma sajen dake kwance akan fuskarsa suka ƙara yawa fiye da na da, duk da dama cewa shi mutum ne me yalwan suma, kallo ɗaya zakayi mai kasan cewa yana ɗauke da damuwa me tarin yawa acikin zuciyarsa, Zaid ɗin da dana yanzu sun banbanta, wan can Zaid ɗin zuciyarsa cike take da isa, ɗagawa, girmankai, rashin sanin darajan ɗan adam, Zaid ɗin da mashayine, mazinaci, wanda bai ɗauki zina abakin komai ba, haka kuma Zaid ɗin da, baisan menene damuwa ba, baisan menene rashi ba, samu kawai ya sani, sannan kuma baisan menene ƙunci da ɗaci ba, baikuma san menene wani abu waishi soyayya ba. Zaid ɗin daya kasance yanzu kuwa, wani mutum ne dayake cikin ƙunci, zuciyarsa tana cike da tarin damuwa, Zaid ɗin yanzu yarasa duk wani farincikinsa, yarasa jin daɗi, yarasa nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa. “ko wannan baici yasa Zahrah ta tausaya masa ba? shin wai shi kaɗaine yataɓa aikata abun da baidace ba?” yatambayi kansa, abu biyune suke damunsa, zazzafar soyayya dakuma rashin nutsuwa da salama dake damunsa, yanzu shikaɗai yasan halin dayake ciki, baya iya bacci, baya iya cin abinci, bayajin daɗin komai nasa, gaba ɗaya duhu ya mamaye rayuwarsa, yanzu yafara zargin cewa zunubansa ma sunyi masa yawa, yasani ƙwarai, yasan abu me kyau da kuma marar kyau, amma saboda ruɗin duniya gaba ɗaya ya shagala. (Yawancin mutane yanzu rayuwarsu sukeyi saka ka, zasu aikata zina, zasu sha giya, zasu aikata duk wasu aiki dake jawo musu manya manyan zunubai, amma kuma yawancinsu sunfi gudun kunyar duniya data lahira, suna tsoron wani yakamasu suna aikata zina, amma basa tsoron kallonsu da Allah yakeyi, wasu sun maida zina manshafawarsu, suna ganin kamar hakan wayewace, bayan kuma suna sane dacewa aikata ta babban halaka ne, Ya ALLAH kaci gaba da karemu, kakuma tsaremu da sharrin zina, ka rabamu da zama da mazinata, Ameen Ya ALLAH!)4
Yariga daya gama yanke hukunci cewa ko da su Dad ɗinsa basaso saiya koma Nigeria, bazai iya zama anan ba, zafi yakeji acikin zuciyarsa marar misaltuwa idan haryatuna da cewa Zahrah’nsa tana can gidan wani, sai yaji gaba ɗaya nutsuwarsa ta gushe, wataƙila ma wannan banzan Doctor ɗin ya kusanci Zahrah’nsa, ae kuwa baisan sanda ya ƙwalla wata irin ƙara ba, azuciye ya ɗauki wani flower dake gefen gadon, yayi jifa dashi, take kwalbar flower’n ya tarwatse a tsakiyar ɗakin, duk da haka hakan baiyi masa ba, saida yataka ya ƙarasa gaban mirror, da hanunsa ya daki mirror ɗin, take mirror’n ya tarwatse har saida ya yanka masa hanu, amma saboda tsananin kishi’n dake cinsa, ko zafin ciwon baiji ba.
“Hakane ma, yakusanceta” wata zuciyartasa ta faɗa masa..1
“No!!! it will never happen, i Know Zahrah will not do it, bazata taɓa iya bawa wani kanta ba bayan ni, because she know we love each other” yafaɗi haka da ƙarfi cikin wata irin murya, me ɗauke da tsananin ɓacin rai, durƙushewa yayi a ƙasa haɗe da sanya hanu ya dafe saitin zuciyarsa wacce take bugawa da sauri, da dukkan alamu dai ya tsokalowa kansa. Haki yasomayi tamkar wani wanda yayi gudu, tarine ya sarƙesa, take jini yasoma fitowa ta bakinsa, shi kaɗai yayi tarinsa harya ƙare, ya galabaita sosai da sosai, da ƙyar ya’iya jan jikinsa ya shiga toilet, wanke bakinsa yayi kana yafito daga cikin toilet ɗin, numfashi kawai yake maidawa cike da wahala,, wani ɗan abu yadanna, bayan kamar minti 1 saiga wata cleaner tashigo cikin ɗakin, nuni yayi mata da inda jininsa ya ɓaɓɓatata, babu ɓata lokaci ta sanya kayan aiki ta gyara wajen, tana kammala gyaran kuwa wasu likitoti su biyu suka shigo cikin ɗakin.. Duba lafiyar jikinsa suka sake yi haɗe da basa wasu magunguna, wata allura sukayi masa da take matuƙar sa bacci, domin kuwa gwaje gwajen da sukayi masa yasa sungano cewa baya samun wadataccen bacci.1
Suna fita ya lumshe idanunsa, wanda tuni suka zama jan gauta, saboda tsabar tsananin kishi dake cinsa, jiyake ma kamar idan ya ƙara kwana ɗaya ba acikin Nigeria ba ya cutu, gwamma yaje ya ƙwace Zahrah tunkan wanda ya ɗauka bakomai ba ya ɗanɗana masa zumarta. (Hahhh guy ae ka makaro,yasin doctor yajima da ɗanɗanawa🙈) **** Mintuna kaɗan dayi masa alluran, bacci me nauyi yayi gaba dashi…2
STORY CONTINUES BELOW
Dad ne ya nutsu haɗe da dawo da kallonsa ga Mummy. “Inaga abu ɗaya zamuyi masa yamanta da wannan yarinyar, kawai na yanke shawara aure zanyi masa.”
Shaye da mamaki Mummy take kallon Dad. “Aure fa kace Alhaji? wakake tunanin zata iya zama da Zaid, da irin wannan halinnasa? hmmm bana majin cewa Zaid zaiso wata mace bayan wannan Zahrah’n, ni nama fara tunanin cewa asirce masa zuciya tayi, amma inbanda haka taya lafiyayyen ɗa namiji kamar Zaid zai maƙalewa mace ɗaya kamar maye”
Murmushi Dad yayi haɗe da girgiza kansa, “itadai Safara’u haka take, idan ana magana me hankali saikuma tana sako wasu abubuwa kamar na wasa.” dad yafaɗi haka acikin zuciyarsa, afili kuwa gyara zamansa yayi haɗe da sake fuskantarta…
“A wannan karon dagaske aure zanyi masa, saboda aure ne kaɗai zaisanya Zaid dawowa cikin nutsuwarsa, bandamu da ko yanason matar ko baya sonta ba, nasan watarana ahankali zai sota ya manta da waccar”1
“To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma gaskiya nima banjin daɗin ganinsa acikin wannan halin dayake ciki yanzu,ko abincin kirki wallahi bana iya ci” Mum tafaɗi haka cikin tausayawa ɗan nata….. (Team Zaid kunji fa wai aure za’ayi masa me zakuce? wayaga Zaid da auren dole)4
****
NIGERIA
Tunda ta kwanta bacci ba’ita ta tashi ba sai 11:30 am, ko tsayawa nemansa yau batayi ba tafaɗa bathroom, wanka tayi kana ta fito daga cikin bathroom ɗin… Mai kawai ta shafa kamar kullum sai kuma powder, itakam batason cika meckup akan fuskarta.
Riga da sket na atamfa tasanya, wanda yayi mata caras ajikinta, ɗan kwalin kayan kawai ta yafa akanta zuwa kafaɗarta. Direct falo ta nufa sai tashin ƙamshi take, kamar yanda tayi zaton zata ganshi a falo, sai taga saɓanin haka, domin kuwa babu shi babu alamarsa,, kallonta ta mayar kan dinning area saidai taga kan table ɗin wayam babu food flask ko ɗaya,, hahhh take idanunta sukayi raurau dasu, ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro haɗe da shafa cikinta, “Yanzu kenan Doctor da yunwa ya barta?” ta tambayi kanta…
Motsi ta soma ji daga ɓangaren kitchine, tsoro ne yaɗan kamata dan tasan Dr.Sadeeq da kansa kam bazai shiga kitchine ba, “to kodai basu kaɗai bane acikin gidan?” tasake tambayar kanta. Cikin sanɗa take takawa harta isa ƙofar kitchine ɗin, motsinne yasake tsananta, don haka cikin sanɗa ta tura kanta cikin kitchine ɗin.
“Kamata!!!” taji anfaɗa da ƙarfi. Wani irin ƙara ta ƙwalla haɗe da rugawa a guje ta koma cikin falo.. Dariya yashiga yi mata bayan yafito daga kitchine ɗin hanunsa riƙe da plate wanda yake ɗauke da soyayyen chips..
Zamewa tayi aƙasa haɗe da dafe ƙirjinta, nunfashi take fitarwa da ƙyar, da’alama ta tsorata sosai.
Zama yayi akan kujera har yanzu dariya yakeyi mata, yasan zata tsorata amma baiyi tunanin tsoron nata zai kai har haka ba.. “Yadai karfa ki sume min” yafaɗi haka yana me ɗan tsagaita dariyarsa…
Ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro gaba haɗe da miƙe ƙafafunta akan sofa, “Nidai Allah ka tsoratar dani, please kada ka ƙara zan iya mutuwa fa!” taƙare maganar cikin tsantsar shagwaɓa.
“Kindai tsorata kanki, ni bani na tsorataki ba ƴan mata, da wayace ki shigo kitchine ɗin cikin sanɗa?”
“To ba motsi naji ba, na ɗauka ko aljanine!” still cikin shagwaɓa takumayin maganar..
Kallonta kawai yashigayi yana murmushi, a garin gudu harta yada ɗan kwalin dake kanta bata sani ba, hakanne yabaiwa gashinta damar bayyana.
Jingina da kujera tayi, tana me sauƙe ajiyar zuciya, sai yanzu ta fara dawowa daidai.
Ƙaurin abinci yasoma ji da sauri yatashi ya nufi kitchine, aikuwa yana zuwa ya tarar da soup ɗin daya ɗora akan wutane yasoma ƙonewa, da sauri ya sauƙe haɗe da ƙwaɗawa Zahrah ƙira..
STORY CONTINUES BELOW
Saƙare tayi tana kallon yanda yake kwashe soup ɗin ƙwai da albasa yana sanyawa acikin wata ƴar ƙaramar kula, dariya ne ya ƙwace mata, cikin dariyan tace “Doctor dama ka iya girki ne?”
Hararan wasa yayi mata haɗe da cewa “Na bugawa a jarida ma kuwa”
Dariya ta ƙara kwashewa dashi, wai iya girkinnasa har na bugawa a jarida ne hmm. Ɗan matsowa tayi kusa dashi haɗe da leƙa tukunyar da akayi soup ɗin aciki, da sauri ta sanya hanu ta toshe bakinta, dariya ne yazo mata, gaba ɗaya cikin tukunyar yayi baƙi, soup ɗin yasoma ƙonewa..
“Miye wai kikewa dariya? yarinya zaki faɗa wa mutanen garinkune anjima, kin kuwasan daɗin girki na yafi na kowa ko” yaƙare maganar yana me ƙaƙalo ƙasan tukunyar daya ƙone zai zuba acikin kulan. Dasauri ta rike hanunsa haɗe da cewa “Idan kazuba wannan fa soup ɗinnan bazai ciwuba”
“Meyasa, ko hassada kikeminne?”
Yatambayeta yana me ɗage giransa ɗaya..
“Shikenan to, tunda kanaga kamar wasa nake ma, amma kuma idan kasa akan abincinka yayi ɗaci ni ba ruwana” tafaɗi haka tana me sake hanunsa.
Kallonta ya ɗanyi haɗe da marerece fuska. “Yazanyi to Zahrah, banaso kitashi kinajin yunwa banbaki abinci ba, shine na soyamiki chips yanzu kuma gashi nayi soup ɗin kince wai ya ƙone bazai ciwuba, ko zamuje resturant ne?” gaba ɗaya fuskarsa ta sauya da alama shagawaɓa yakeson yi mata..
Wani irin tausayinsa ne taji ya daki zuciyarta Allah sarki, ashe duk akantane yaketa shan wannan wahalan.. “A’a basai munje resturant ba, zan ma iyaci a haka fa ai ba duka soup ɗin bane ya ƙone, kuma ma basai muci da tea ba!” cikin yanayi na kulawa ta ƙare zancen..
Cikin jin daɗi yace “Yauwa tawan to ɗauki soup ɗin kije, bana haɗa mana tea ko”
“A’a kabarshi ni dakaina zan haɗa mana” tafaɗi haka tana me ƙoƙarin fara haɗa musu tea ɗin. Hanunta ya kama ya sumbata haɗe da ɗaukan kulan da soup ɗin ke ciki yanufi falo… Mintuna kaɗan tafito da ɗan wani tray wanda yake ɗauke da kofuna biyu na tea ɗinsu.. Aje tray ɗin tayi akan sofa haɗe da maida kallonsa gareta, gani tayi ya kafeta da idanunsa, wanda suke daɗa sawa tanajin nauyinsa..
Ɗan shagwaɓe fuska tayi haɗe da cewa “To miye kake kallona!”
Murmushi yasakar mata haɗe da tasowa daga inda yake zaune, zama yayi akan sofan, dakansa ya zuba musu soup akan chips ɗin, loman farko Zahrah ta tauna wani Chips da bai gama soyuwa ba, kallonta yayi haɗe da cewa “Ya kikaji yayi daɗi ko? ai nasan ma zaiyi daɗi”
Murmushin dole tayi haɗe da cewa “Yayi daɗi sosai”
Hanu yasanya yashafi kumatunta, “Yauwa My Zahrah ae dama nasan saikin yaba”
Da ƙyar ta’iya danne dariyarta, loman farko da yayi ya ɗago kansa ya kalleta, itama kallonsa takeyi, saitaga ya ɓata fuska kamar zaiyi kuka, bazata iya riƙe dariyarta ba yanzu kam yazama dole saita dara, sake shagwaɓe fuska yayi ganin yanda takeyi masa dariya. Da ƙarfi yajawota jikinsa haɗe da murɗe mata hannayenta “Wakikewa dariya?”
Cikin dariya tace “Kayi haƙuri nifa badakai nake ba, dariyarce kawai tazomin”
“Uhhh aini ba yaro bane nasan ni kikewa dariya, to amma ai balaifi na bane laifin gas ɗinne da bai ratsa kaskon suyan da kyau ba, kuma ko kema ae nasan haka zaiyi miki”
Itadai dariya kawai takeyi masa, gaskiya wannan girkin nasa kam yacancanci abugasa a jarida kamar yanda ya faɗa, onion and egg soup ya ƙone dankali kuma bai soyuba.
Haka suka haƙura da dankalin suka sha tea tare da snacks kawai. Bayan sungama cin abincin ya jawota jikinsa, haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, lumshe idanunsa yayi yana me sauƙe numfashi a hankali, wani abu yakeso daga gareta wanda yasan idan ya nema balallai yasamuba, kuma ma koda yasamu to ba a son ranta ta basa ba, shiyasani matuƙar zasu kasance waje ɗaya da’ita tofa har abada acikin sha’awarta zai kasance.. Jin yanda yake sauƙe mata numfashi akan wuyanta ne yasanya jikinta yin sanyi, ahankali kasala tasoma dirar mata, itama lumshe nata idanunta tayi, tana me yin wani tunani acikin zuciyarta.. Tsawon mintuna 15 suka ɗauka a haka babu wanda yace da ɗan uwansa ƙala, shi dai Dr.Sadeeq tsundum yake acikin kogin sha’awa, yayinda itakuwa take tsundum acikin kogin tunanin wani abu wanda bashida amfani a wajenta, wani abu wanda tunaninsa yazame mata jiki da jini, sai dai kuma tasan abun baidace da itaba, baidace da rayuwarta ba, ƙaddara ce kawai ta haɗasu, sannan kuma zuwa yanzu yakamata ace ta manta da babinsa, takuma daina tunasa, sai dai kuma duk yanda taso hakan yakasance abun yaci tura, dole zata haɗa da addu’a, saboda addu’a yafi gaban komai, duk da cewa dama tanayi amma dole zata ƙara akan wanda takeyi…1
A hankali yajanyeta daga jikinsa haɗe da miƙewa yanufi ɗaki, da kallo kawai tabisa harya shige cikin ɗakin, “Meke damunsa?” tatambayi kanta a bayyane.
Ganin batada maibata amsa, baikuma dace ta zauna batare da taji damuwarsa ba yasanya ta bisa zuwa cikin ɗakin..
Kwance ta iske sa akan gado yayi ruf da ciki yayinda yasanya hanunsa ɗaya akan mararsa, sam bata fahimci wani abu game da hakan ba, ahankali taƙarasa wajen da yake, cikin murya meɗan sanyi tace “Bakada lafiya ne?”
“Lafiyana ƙalau, kawai dai bacci nakeji ne” yafaɗi haka ataƙaice, baison yayi magana me tsawo ta harbo jirginsa, tsakani da Allah bayason yasake takurata, jiyama da yayi, yauda safe da kuka ta tashi masa, saboda haka yanzu baison ya ɓallo liƙi gwamma yabari ko zuwa dare ne ma, amma kuma idan yatuno irin daɗin dayaji jiya, sai yaji kamar bazai iya haƙura ba.. Haurawa tayi kan gadon haɗe da kwanciya a bayansa, ƙurawa kwantaccen gashin kansa ido tayi, abubuwa da yawa nasa suna matuƙar burgeta, babu ma kamar idanunsa, idan yana kallonta harwani mutuwa jikinta yakeyi, babu ta inda Dr.Sadeeq ya gaza, komai nasa yayi 100%.
“Ɓacci bai isheki bane?” yayi mata tambayar batare daya juyo zuwa garetaba.
“A’a kawai dai ina hutawa ne” tafaɗi haka a taƙaice don talura kamar bayason damuwa.
Ƙarar wayartane ta karaɗe cikin ɗakin, da sauri ta ɗauko wayar dake aje kan ɗan ƙaramin drawer’n gefen gado.. Ganin Husnah ce me ƙiran yasanya ta ɗaga wayar da sauri, tana ƙoƙarin yin magana taji muryar Husnah tace “Gani a falo”
da sauri tatashi daga kan gadon haɗe da ficewa daga cikin ɗakin, ko bayani bata tsaya yiwa Doctor ba. Shikuwa da kallo kawai yabita harta fice daga cikin ɗakin, lumshe idanunsa yayi haɗi da sauƙe ajiyar zuciya.
Da gudu Zahrah taje ta faɗa jikin Husnah, rungume juna sukayi ƙam cike da kewar juna.
“Nayi kewarki sosai ƙawata” Husnah tafaɗi haka tana me ƙara rungume Zahrah.
Tureta Zahrah tayi haɗe da ɗan turo baki gaba. “Bawani nan ni ae nayi fushi, tunda ranan nan kin yaudareni kin gudu”
Dariya Husnah tayi haɗe da cewa “Yi haƙuri amaryar likita”
Dariya suka sanya su dukansu, saida Zahrah ta cikawa Husnah gabanta da su drinks kafun tazo ta zauna akusa da ita..
“Gaskiya dole ne nima acikin wannan shekaran nayi aure, kiduba kiga 2 days kacal amma gaba ɗaya sai wani shining kike” Husnah tafaɗi haka tana me ƙarewa Zahrah kallo.
Harara Zahrah ta wurgawa Husnah “Kinganki ko wallahi banason tsokana, ae ko a engine aka sani baici ace zuwa yanzu nafara walwali ba”
“Hahhh kedai faɗi gaskiya don da alama doctor madara na musamman yake shayar dake kullum”
Dariyane yakama Zahrah “wai madara” hmmm itasam bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba..
“Ke dai baki rabo da tsokana, wace madarace zatasa acikin 2 days kacal na sauya” Zahrah tafaɗi haka tana me duban skin ɗinta..
“Hahhhh madara mana irin taku ta masu aure, ae babe kawai ki manta, nasan kinbasa yasha kuma kema yabaki kinsha”
Sai yanzu Zahrah ta gano me Husnah ke nufi, duka ta ɗaka mata abaya haɗe da yin dariya. Husnah ma dariyan tayi, kana taɗauki drinks tasoma sha..
****
Hira sosai Husnah da Zahrah sukayi, duk da Husnah tace bajimawa zatayi ba. Bata jima ba kuwa tayi tafiyarta bayan tabawa Zahrah wasu ingantattun magunguna wanda Hajiya Shuwa ta bata tace takawo mata, har bakin gate Zahrah ta raka Husnah, cike da kewar juna sukayi sallama…
***
Kallon Dad ɗinsa yayi arikice gaba ɗaya idanunsa sun rufe, miƙewa yayi tsaye yasoma takawa ahankali, ganin zaifita daga cikin ɗakinne yasanya, Dad yayi saurin riƙosa, “Bazaka iya kulawa da kanka ba Zaid, badai Nigeria kakeso mu koma ba?” cike da kulawa Dad ya tambayeshi..
Kansa ya kaɗa kamar wani ƙaramin yaro, ajiyar zuciya Dad ya sauƙe haɗe da ƙara riƙe hanun Zaid ɗin.
“Shikenan ka kwantar da hankalinka gobe zamu koma Nigeria”
Wani irin sanyi Zaid yaji acikin zuciyarsa, badon komai ba saidon zaije yaga Zahrah’n sa, babu ruwansa da wani tayi aure, shi so yarufe masa ido, hargidan nata zaije… (🙆♀🙆♀ Anya Zaid bai samu matsala a ƙwaƙwalwarsa ba kuwa? )
Dad kuwa yayanke wannan hukuncinne saboda suna zuwa Nigeria zai ɗaurawa Zaid ɗin aure da ƴar abokinsa, wannan shi kaɗaine zaisanya Zaid ya nutsu yakuma dawo cikin hankalinsa….Tana idar da sallan isha, ta ɗauki wata doguwar riga marar nauyi ta zura ajikinta, rigace irin shara shara ɗin nan, gashi kuma yaɗan kamata ta ƙasa, yayinda saman rigan kuwa ya buɗe, zura rigar kawai tayi batare da koda ta kalli kanta a madubi ba tafice zuwa falo. Sauri take batason Bollywood sufara haska film ɗin Bajrangi Bhaijaan bata kusa, ƙarfe takwas kuma dai dai zasu saka film ɗin, gashi yanzu bakwai ne hadda wasu mintuna, direct kitchine ta wuce taɗauko wani ɗan ƙaramin cup, fridge ta buɗe ta ta ɗauko babban cup ɗin milk shake dake cikin fridge’n ta tsiyaya, ahankali take tafiya tana ɗan zuƙan milk shake ɗin a bakinta, yajima yana jingine jikin ƙofa, kan ƙirjinta kawai yaketa kallo tun fitowarta daga cikin ɗakin, daga kan fatar cikinta har brezia’n dake sanye a jikinta, duk sun bayyana kansu a fili kasancewar rigar bata wani ɓoye sirri, sam bata lura dashi ba, hankalinta yana ga tv, hanu yasanya ya jawota jikinsa, saura kaɗan cup ɗin hanunta ya suɓuce ya faɗi ƙasa. Da sauri ta kalleshi haɗe da ɗan turo ɗan ƙaramin bakinta gaba.+
Ta baya ya rungumeta, haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, cikin wata murya me sanyi yace “Ɗaukar alhaki ne, ko kuma kawai anyi danni ne?”
Cikin rashin fahimtan inda kalamansa suka dosa tace
“Bangane ba”
“Ummmm nima so nake nagane saina baki amsa” yafaɗi haka yana me ƙoƙarin zame wuyar rigar daga kan kafaɗunta.
Dasauri ta nemi matsawa daga jikinsa, amma saidai bata samu daman hakan ba, domin kuwa ya riƙeta gam.. Baidamu da yanda takeyi ba yasanya hanunsa yazame wuyar rigan, dake rigan dama tana da faɗin wuya sai gashi yakawo wuyan har kusan ƙasa da kafaɗunta, bakinsa ya ɗaura adai dai saitin wuyanta ta baya, wani irin lafiyayyen kiss yabata wanda saida yasanya tsikar jikinta suka tashi, da sauri ta juyo tana fuskantarsa, idanunsa da suka koma kamar na mejin bacci, ya ɗago ya watsa mata su, wani dokawa taji ƙirjinta yayi, yanayin da taga ƙwayan idanunsa shiyafi komai sanya mata faɗuwar gaba, har abada bazata taɓa manta mutumin data fara ganin irin wannan yanayin acikin idanunsa ba, kusan nasakamma har yafi na Doctor tsanani, domin kuwa bata taɓa mantawa da yanda idanun suka riƙiɗe suka zama jajaye suke kuma lumshewa alokaci guda ba, Zaid shine mutum na farko da ya fara kallonta da irin wannan yanayin, “mekenan hakan yake nufi? me yasa idanun suka sauya launi alokaci ɗaya?” tayi mawa kanta duka waƴannan tambayoyin da bata da me amsa mata su..
A hankali yake ƙara matseta haɗe da kusanto da fuskarsa daf da tata, burinsa kawai shine yaji bakinta acikin nasa. Kawar da kanta gefe tayi tana me sauƙe numfashi ahankali, gaba ɗaya tunowa da tayi da Zaid ya sanja mata yanayinta, Zaid ba mutum ne da zata manta dashi ba, lallai dole harta mutu yana cikin rai da zuciyarta, kodan abun da ya aikata a gareta.
Hanu yasa ya juyo da fuskarta, yazama suna fuskantar juna, baijirayi komaiba ya ɗaura bakinsa akan wuyanta, kissing ɗin wuyanta yake sosai, wanda hakan ya haifarmata da mutuwar jiki, cikin nutsuwa ya dawo da bakinsa kan nata bakin, ahankali yake sucking lips ɗinta, lumshe idanunta tayi tana me karɓan saƙon sa, karo na farko a rayuwarta da taji hakan dayakeyi mata yayi mata daɗi, batasan lokacin da ta gama sakar masa jikinta ba haɗe da sake buɗe masa bakinta, shikuwa dama abun da yake jira kenan, ba ɓata lokaci ya kamo tongue ɗinta yashiga tsotsa a hankali.. Wani irin numfashi kawai yake fitarwa, ko a iya haka idan ya tsaya yasan zaisamu gamsuwa, har abada shikam yanaji ajikinsa bazai taɓa gajiyawa da tsotsan baki da kuma harshenta ba, wani ɗanɗano na musamman yakeji acikin bakinsa idan yana tsotsan harshenta, yakan rasa duk wata nutsuwarsa idan laɓɓansu suka haɗe waje guda,yakan tsinci kansa cikin matsanancin shauƙi dakuma wani irin yanayi me daɗin gaske.
Ƙafafunta ne suka soma saƙewa, gaba ɗaya tsayuwar ta gagareta, yayinda shikuwa yaketa jifanta da salonsa iri iri, idan zasu shekara a haka sai dai ƙafafunsa su gaji suƙi ɗaukarsa, amma bawai shi ya gajiya da shan tausassun laɓɓanta ba, ƙoƙarin zamewa ƙasa takeyi da sauri ya riƙota haɗe da ɗagata caɗak kamar wata ƴar ƙaramar yarinya… Direct ɗaki yanufa da ita, bai direta ako inaba sai akan gado, ɗan ƙaramin ƙara tasanya haɗe da cewa “Wayyo nauyi!”
STORY CONTINUES BELOW
Dariya yayi haɗe da jan hancinta cikin muryarsa da ta soma sarƙewa yace
“Waye ne me nauyin?”
“Kai mana!” tafaɗa a shagwaɓance. Gaba ɗaya rigan jikin nata ya zame ƙasa, haɗe da soma bin ko wani ɓangare na jikinta da hot kiss, shiru tayi tanajin yanda yake tsotseta kamar wani maye, amma kuma fa saƙon nasa na yau yana shiga inda ya kamata domin kuwa tun ɗazu jikinta yagama mutuwa.
Kissing ɗin bakinta yaci gaba dayi, batasan lokacin da itama ta soma tayasa ba, baitaɓa tunanin zata taya saba, shiyasa sanda takama harshensa tana tsotsa a hankali, yaji gaba ɗaya ya ruɗe haɗe da zaucewa, jiyake kamar awata duniyar aka tsoma shi.. Yanayin yanda yake romancing ɗinta ne yasa har kuka sai da tayi masa wanda batasan na menene ba, jitakeyi kamar kan nipples ɗinta zasu cire, tsabar anbasu kyakkyawan sucking.
“wallahi doctor ma mugu ne” tafaɗi haka acikin zuciyarta….. Yau dai ba iya Dr.Sadeeq bane kaɗai yaji daɗin kasancewarsu tare ba, hadda ita kanta me daɗi’n nasa, sai dai kuma gaba ɗaya zautar dashi takeyi, yauma da ƙyar yasamu ya iya dawowa cikin duniyarmu, bawai don yasoba saidon gudun wahalar da ita… A hankali yasa hanu yashafa gashin kanta, haɗe da manna mata kiss akan goshinta, Zahrah dake kwance luf acikin ƙirjinsa ta lumshe idanunta haɗe da sake cusa kanta acikin ƙirjin nasa..
“I’am sorry me daɗi na na gajiyar dake ko? ba laifi na bane, inata so nayi controlling ɗin kaina amma nakasa, ke ɗince kin cika da….” saurin toshe masa baki tayi haɗe da sake ɓoye kanta acikin ƙirjinsa, kunya takeji tsantsa idan yaƙirata da sunan me daɗi’n nan, sai taji gaba ɗa tazama wata iri da ita.. Tsotsan hanunta dake kan bakinsa yasoma yi, da sauri tacire hanun nata haɗe da tashi zaune, bargo ta rufa ajikinta tayi toilet da sauri gudun kar ya tsaidata, jingina tayi da jikin ƙofar toilet ɗin tana sauƙe numfashi ahankali, gaba ɗaya abun daya wakana a tsakaninsu ne yashiga dawowa cikin kanta, tanaso ƙwarai taga tana farantawa mijinta rai, zatayi iyaka ƙoƙarinta wajen ganin tayi yaƙi da zuciyarta, wajen ganin ta basa farinciki me ɗorewa yanda ya kamata. Wanka tayi haɗe da zura rigan wanka tafito…
Tsaye tagansa daga shi sai 3 guater jeans ajikinsa, kallo ɗaya tayi masa tayi saurin ɗauke kanta, har yanzu bata taɓa amincewa yaga tsiraicinta cikin haske ba, sannan haka itama bata taɓa tsayawa takalli jikinsa acikin haske ba komai sunayinsa ne acikin rashin wadataccen haske, “Jikinsa yanada kyau” tafaɗi haka acikin zuciyarta haɗe da ɗan satan kallon 6 packs ɗin dake kwance akan cikinsa.
Raɓawa yayi ta gefenta yashige cikin bathroom ɗin fuskarsa ɗauke da wani irin murmushi.
Wata ƴar ƙaramar riga wacce ta tsaya iyaka guiwarta kawai ta sanya haɗe da sanya igiyoyin dake gaban rigar ta ɗaure cikinta, haurawa tayi kan bed ɗin ta kwanta.. Yana fitowa yakuma sanya wani 3 guater jeans ɗin haɗe da feshe jikinsa da turare.. Wutan ɗakin yakashe yakunna musu na bacci, hawa kan gadon yayi haɗe da jawota jikinsa, kwanciya ajikinsa yanayi mata matuƙar daɗi shiyasa aduk sanda yajawota jikinsa bata bijirewa. “Kinyi addu’a?” yatambayeta.1
Kai kawai ta ɗaga masa alamar “Eh” addu’a yayi shima ya shafa kana ya lumshe idanunsa, ahankali yake shafa bayanta, cikin mintuna ƙalilan bacci ya ɗauke ta, sannu sannu shima bacci me nauyi ya ɗaukesa….
*****
Washe Gari.
Ƙarfe 5 dai dai jirginsu ya sauƙa acikin Nnamdi Azikwe International airport.
A hankali yake taka matattakalan sauƙowa daga cikin jirgin, sanye yake da riga da wando irin na sanyi navy blue colour, hatta takalman dake sanye a ƙafafunsa navy blue colour ne, yayi kyau sosai yaƙara haske, sai dai kuma sosai rama ta bayyana kanta ajikinsa. Yana gama saƙƙowa daga kan matattakalan yanufi wajen da motocin da sukazo ɗaukarsu ke fake, 4matic yabuɗe yashiga haɗe da hakincewa agidan baya, bayasan damuwa shiyasa bayason shiga mota ɗaya dasu Dad ɗinsa.. Harsuka isa gida tunani yakeyi, maiya kamata yayi? sai kuma yanzu daya dawo yakeji gaba ɗaya Nigeria’n tayi masa ƙunci haɗe dayi masa duhu,daya kulle idanunsa Zahrah kawai yake gani… Yana fita daga cikin motar direct ɓangarensa dake cikin gidannasu ya nufa. Falo’n sa tsab-tsab yake tamkar wanda wani yake rayuwa aciki, bedroom ɗinsa ya wuce, yana shiga yaƙarasa gaban wani tangamemen hotonta da yasa aka masa kalanda (Calender) dashi yakafa ajikin bangon ɗakin, rungume ƙaton kalandan yayi haɗe da lumshe idanunsa.1
STORY CONTINUES BELOW
“I really Miss you My Zahrah!”2
ya faɗi haka cikin murya me sanyi da kuma tsananin rauni, hanu yasanya yashafa daidai saiti laɓɓanta dake jikin hoton calender’n.
“Bana tunanin zan daina kewarki Zahrah na, tunaninki yazama abincin ruhina, inasonki sosai, lokaci yayi daya kamata ki dawo gareni, muyi rayuwar auren mu cike da tarin farinciki, nadaina komai Zahrah shan giya, zina, duk na daina please ke nake jira har yanzu, ina fata baki bawa wanina kanki ba?” yanayin yanda yake magana da hoton idan ka gansa kaitsaye dasunan mahaukaci zaka ƙirasa, domin kuwa me cikakken hankali bazaiyi haka ba.. Wayarsa ya ɗauka yayi dialing number’n Abid, bugu uku Abid ya ɗauki wayar baijirayi abun da Zaid ɗin zaice ba yace
“Wow surprise kenan?”2
Ƴar ƙaraman tsuka Zaid yayi cikin muryarsa me rauni yace “Inason ganinka Abid, yanzu agidan mu please!” baijirayi me Abid ɗin zaice ba ya katse wayar haɗe da cilla wayartashi kan gado, yasan Abid bazaiƙi zuwaba shiasa baijirayi amsar saba yakashe ƙiran. Zama yayi akan wata kujera dake cikin ɗakin, kan ɗan madaidaicin fridge’n dake aje cikin ɗakin ya maida idanunsa, jiyake kamar yatashi yaje ya ɗau wine ɗinsa yasha, sai dai kuma wata zuciyar tana gargaɗinsa da cewa, Zahrah bataso, tun randa ta gayamasa wata baƙar magana akan shan wine da yake, bai ƙara shaba harkuwa rana me kamar ta yau, duk da kuwa irin azabtuwan da yakeyi idan baisha wine ɗin ba, saboda yariga daya saba. Shiru kawai yayi haɗe da kama kansa ya rumtse idanunsa.. Abid ne yaturo ƙofar ɗakin yashigo bakinsa ɗauke da sallama, ciki ciki Zaid ya amsa masa sallaman haɗe da watsa masa idanunsa da sukayi jajur dasu.. Cike da mamaki haɗi da tsoro Abid ya matso kusa da Zaid da ɗan sauri.2
“Zaid meke damunka haka? yaushe kuka dawo? yajikin naka?” duka waƴannan tambayoyin Abid yayiwa Zaid su a lokaci ɗaya kuma duk amsarsu yake nema idan zai samu..
“Abid nakasa mantawa da ita, itace nutsuwar tunani na, banajin zan iya kaiwa lokaci me tsawo batare da na sanyata acikin idanuna ba, Inasonta sosai kai kasani!”
Kallon Zaid kawai Abid keyi yamarasa me zaice masa.. Kallon ɗakin yashiga yi sai alokacin ya Lura da maka makan hutunanta dake manne ajikin bangon ɗakin Zaid ɗin,wasu zane ne wanda Zaid ɗin yayi wasu kuwa hotunanta ne. Wani irin tausayin Zaid ɗinne ya tsirga masa me tsanani, shidai bazaice baitaɓa soyayya ba, amma kuma baita ɓayin kwatan kwacin irin wannan son me tsanani da Zaid keyi ba. Zama yayi akan kujeran dake fuskantar na Zaid, hanun Zaid ɗin yakamo haɗe da cewa “Kazama jarumi Zaid, kada kamanta fa yanzu Zahrah matar wani ce kuma….”
“Ya isheka haka Abid!!” Zaid ya katse Abid cikin tsawa sosai.
“Matar wani, Matar wani, abun da kuke ta faɗa kenan, meyasa ni bazaku duba halin danake ciki ba? shikenan don tana matar wani sai nadaina sonta? kafun wanda kuke ikirarin matarsace yasota nine nan nafara sonta, kada kataɓa tunanin zan daina son Zahrah Abid, bakuma zan taɓa samun nutsuwa ba harsai Zahrah ta zamo mallakina, kataimakeni Abid kazo muje gidanta mu ɗaukota tazo nan mu rayu tare nasan itama tana sona!” cikin murya me tsananin rauni yake faɗan maganar..1
Kai kawai Abid yake girgizawa azuciyarsa kuwa wutar tausayin Zaid ne ta kunno, So yamakantar da zuciyar Zaid yasanya harya kasa tuna cewa Zahrah a yanzu ta haramta a garesa, shi duk iskancinsa baya tunanin Zaiso matar da take da aure, dukansu shida Zaid sunsani cewa shangiya da zina duk haramunne amma kuma saboda son zucia irin tasu suke aikatawa, yanzu kuma ga wani sabon saɓon da Zaid yafito dashi, yana goya masa baya akan komai, amma a wannan karon kam baya tunnin zae goya masa baya yaci gaba da son matar aure, haƙiƙa Zahrah takai macen da kowani ɗa namiji zai sota, amma kuma tunda ayanzu tazama mallakin wani babu amfanin Zaid yata takura kansa akanta. “Zaid!” Abid yaƙira sunansa araunace. Kansa kawai ya ɗago ya kallesa batare dayace dashi komai ba.
“Kada kaga laifina Zaid, mun hau wani mataki da yanzu dole ne mufaɗawa kanmu gaskiya, menene ribar da zakasamu idan kacigaba da dakon soyayyarta acikin zuciyarka? tazarar dake tsakanin ka da Zahrah a yanzu yanada matuƙar yawa, tana tare da mijinta kuma nasan zuwa yanzu tajima da zama shi kuma shima yazama ita, me yasa to kowannan bai isa yasanya kacireta acikin zuciyarka ba, akoda yaushe kada kana tunanin cewa wai Zahrah zata dawo gareka, so ne yasa mijinta ya aureta, kaga kenan haka nan kawai bazai rabu da ita ba, kasa aranka ma idan ƙaddara ta rabasu babu yiwuwar Zahrah zata amince ta aureka, kai da kanka kasan haka amma zuciyarka tana yaudaranka, haƙiƙa nima shaidane akan cewa har yanzu Zahrah tana sonka, amma hakan bawai yana nuni da cewa zata iya kashe aurenta ta aureka ba ne, kai koma da ace tafito agidan aurenta to bana tunanin Zahrah zata amince ta aureka, kamanta da ita Zaid, kasawa zuciyarka salama, akwai mata da yawa acikin ƙasarnan dama sauran wasu ƙasashen kasamu wata kabawa ajiyar zuciyarka, na tabbatar watarana komai zai zamo labari!” Abid yaƙare maganar yana me dafa ka faɗan Zaid almar son ƙarfafa masa guiwa..1
STORY CONTINUES BELOW
Wata tsuka me ƙarfi Zaid yaja haɗe da ture hanun Abid dake kan kafaɗansa… har abada bazai daina yiwa wanda yace yarabu da Zahrah kallon mahaukaci ba, wai Zahrah’nsa ake so yamanta ya daina sonta, sai yaushe mutane zasu gane cewa cire so bakamar cire takalmi bane? miƙewa yayi daga zaunen da yake haɗe da shigewa cikin bathroom ko sake kallon inda Abid ke zaune baiyi ba.. Ajiyar zuciya Abid ya sauƙe haɗe da gyara zamansa akan kujeran, yana nan yanajiran fitowarsa koda awa ɗaya zai share a banɗakin bazai tafiba saiyajirasa, Zaid bayason gaskiya wani lokaci, kuma kozai mutu saiya faɗamai gaskiya, ae soyayya ba hauka bane, son matar aure mezai jawo maka inbanda wahala da ƙarin zunubai….1
Zaid kuwa yajima tsaye ruwa na fitowa daga shower yana dukan jikinsa…. Ɗaure da towel a ƙugunsa yafito daga cikin bathroom ɗin, kallo ɗaya yayiwa Abid yaɗauke kansa, Abid na kallonsa har yagama shafa man lotion ajikinsa…
“Saboda nace kamanta da Zahrah shine kake fushi dani? kai kanka kasan abun da kakeyi ba daidai bane Zaid sannan…..”
“Ya isa Abid!” Zaid ya katsesa aɗan kausashe.
Murmushi kawai Abid yayi haɗe da sa kai yafice daga cikin ɗakin, yasan Zaid ya hau sama bazai taɓa sauraransa ba, wanda yayi nisa bayajin ƙira.
****
Tun fitarsa ta shige cikin kitchine yau bataso ya sayo musu abinci tafiso ta girka musu da kanta, fried rice tayi wanda taji zallan tsokan kaza, da kanta ta haɗa shaka ta sanya acikin fridge, takammala komai yanzu saura kawai tayi wanka.. Ƙaran wayarta take ta jiyowa, da sauri tanufi ɗaki inda wayartata take. Wata number ce special ke yawo akan screen ɗin wayar, ɗan tsayawa tayi tana ƙarewa number’n kallo, har ƙiran ya katse bata ɗauki wayarba, wani ƙiranne kuma sake shigowa…. A hankali ta ɗaga wayan ta kara akan kunnenta.
“Zahrah!!!” taji wata murya wacce bazata taɓa mantawa da itaba ta ƙira sunanta, jikinta ne yasoma rawa yayinda bugun zuciyarta yaƙara tsananta shin dagaske ne kokuwa kunnuwanta ne basuji da kyauba, kusan mintuna biyar ba asake cewa komai daga cikin wayarba haka kuma itama bata ce komaiba..
“Wa….y..e?”
tayi tambayar cikin wararrun kalmomi yayinda tsoro ke sake ɗarsuwa acikin zuciyarta.
“Zahrah na! me yasa zaki barni? kin barni cikin ƙunci da tarin damuwa, yazanyi da soyayyarki ne Zahrah, bazan iya rayuwa ba idan babu ke, please ki taimaki rayuwata dakuma zuciyar da ta jima da matowa akan ƙaunarki!!”
Jikinta ne gaba ɗaya yaɗauki rawa harbatasan sanda wayar ta zame daga hanunta ba, take ta faɗi ta tarwatse a ƙasa. Itakanta batasan sanda ta zame ta durƙusa guiwowinta a ƙasa ba, hawayene suka shiga fitowa daga cikin idanunta. “Zaid” shine sunan da take ta nanatawa acikin zuciyarta, sai yaushene Zaid zai barta ta huta tayi rayuwar aurenta cikin nutsuwa? anya kuwa Zaid baisamu matsalan ƙwaƙwalwa ba? ta tambayi kanta, shiru tayi haɗe da lumshe idanunta ƙirjinta kuwa har yanzu bai daina bugawa da sauri ba.
Cikin tsananin mamaki yake kallonta, da sauri ya ƙaraso inda take durƙushe haɗe da tsugunnawa yaɗaura hanunsa akan kafaɗunta
“Meke faruwa?” yatambayeta cike da kulawa.
Da sauri tabuɗe idanunta da suke a lumshe, batasan yaushe yashigo ba.
Kallonta yakeyi sosai da alama amsa yakeson ji daga bakinta.
Dasauri tashiga goge hawayenta haɗe da tashi tsaye, kallonta yakeyi harta shige cikin toilet, idanunsa yasauƙe akan wayarta wanda ta tarwatse akan tiles gaba ɗaya ma screen ɗin wayar ya fashe, mamaki haɗi da ɗaurewar kaine matuƙa suka kamashi, “Meya faru? yaganta tana hawaye gakuma wayarta daya gani aƙasa a tarwatse” yayi mawa kansa tambayar cike da son sanin amsa. Tattare wayar yayi haɗe da komawa kan gado ya zauna zuciyarsa cike fal da tarin tambayoyi..
STORY CONTINUES BELOW
Zahrah kuwa tana shiga cikin toilet ta soma sauƙe ajiyar zuciya akai-akai, meta aikata hakane, gashi yanzu yazo ya ganta acikin halin damuwa, tasan dole ne shima saiya sanya kansa a damuwa, yanzu idan ya tambayeta metasan zata ce masa, wasu hawayenne suka kuma zubowa daga cikin idanunta, da sauri ta sanya hanu ta share.. Haka tayi wanka duk tanajin zuciyarta babu daɗi, ɗan ƙaramin towel ta ɗaura ajikinta, wanda yatsaya a iyaka cinyarta. A hankali ta buɗe ƙofar bathroom ɗin tafito, karaf idanunsu suka haɗe waje guda, da sauri ta kawar da kanta gefe, haɗe da nufar wajen drawer.. Kallon santala santalan cinyoyinta da suke bayyane a fili yashiga yi, wani iri yaji acikin jikinsa, da sauri ya ɗauke kansa..3
Ganin da tayi cewa baya kallonta ne yasanya tayi saurin zura dogon wando na pencil jeans haɗe da wata farar top shirt me kyaun gaske ajikinta, yaune karo na farko da ta fara sanya irin waƴannan kayan ajikinta, ita kanta saitaga ta burge kanta domin kuwa hips ɗinta sunfito acikin wandon sunyi ɗas dasu kamar wanda aka zana.. Kasa daurewa yayi saida ya kafa mata idanunsa, sosai tayi masa kyau baitaɓa ganinta acikin irin wannan shigar ba, ta ɗau hankalinsa ƙwarai lallai Zahrah macece har mace komai nata me kyau ne… Tana tsaka da shafa turare ajikinta taji yaƙira sunanta. Tsayawa tayi cak daga abun da takeyi haɗe da juyowa sai dai bata kallesa ba ta amsa ƙiran dayayi mata.
“Zonan!” yace da ita ata ƙaice.. Ahankali tashiga takawa harzuwa inda yake, tana ƙarasawa garesa ta durƙusa a ƙasa haɗe da sunkuyar da kanta tana me wasa da yatsun hanunta.. Hanunta yakamo haɗe da jawota jikinsa ya zaunar da ita akusa dashi, cike da kulawa haɗi da lallami yashafa kumatunta yace “Kinyi kyau”
Tsintar kanta tayi dayi masa murmushi kawai…
“Meke damunki? Sannan menene dalilin dayasa naga wayarki a fashe gaba ɗaya kuma tatarwatse?”
Kanta tashiga girgizawa alaman babu
“Kinsan banason ƙarya, menene dalilin da yasa zaki ɓoyemin damuwarki? kada ki manta yanzu bake kaɗai kike iko da kanki ba, nima nan inada iko dake, saboda haka na cancanci ki sanardani damuwarki, ni mijin kine bazan taɓa son naganki acikin damuwa ba!” cike da lallashi ya ƙare maganar.
Mezata faɗa masa? tace masa Zaid ne yaƙirata a waya ko me? ko kuma tace masa hawayen da takeyi duk akan Zaid ne? 1
“Dagaske nake bakomai, na ɗaga wayar hanuna da kumfa shine ta suɓuce ahanuna tafaɗi” tsintar kanta tayi da basa wannan amsar, duk da cewa ƙarya ba ɗabi’arta bane amma yazama dole yau tayi, saboda sanar dashi gaskiyan lamarin daya faru bashida wani alkhairi saidai ma ransa ya sosu.
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da jinjina kansa “Naji amma meyasaki kuka?”
Jitayi gabanta ya faɗi amma saita dake tace “Kuka nake saboda na fasa wayata”
Ɗan guntun murmushi yayi sam bai gamsu da maganganunta ba, amma kuma yazaiyi tunda ta ɓoyemasa gaskiya bazai tursasata ba..
“Saboda wayarki ta fashe kawai shine kike kuka? har yanzu dai ke yarinyace ƙarama Zahrah, amma mene abun kuka, idan kikace na saya miki wata kina ganin bazan saya miki bane?”
Kanta ta jinjina alamar “A’a”
“To indai hakane miye na kukan tunda kinsan zansaya miki wata wadda ta fita, kitaimaki zuciyata ki daina sa kanki acikin damuwa please, inasonki banason naga wani abu ya ɓata ranki!”
Raunannun idanunta ta ɗago ta kalleshi, wannan maganar daga cikin ƙahon zuciyarsa yake fituwa, tabbas ita kanta ta gamsu da ƙaunar da doctor yakeyi mata ɗari bisa ɗari, ya cancanci tasakamai da farinciki ne bawai akasin haka ba..
“Ki kwantar da hankalinki, gobe Insha Allah namiki alƙawari zamuje dake ki zaɓi irin wayar da kike so, shikenan?”
Kanta ta ɗaga tana ɗan murmushi, kamar da gaske maganar wayarce a cikin ranta.. Miƙewa yayi yafaɗa toilet, tanajin sauƙar ruwa aƙasa ta sauƙe nannauyar ajiyar zuciya, bataso doctor yasan cewa Zaid yafara bibiyar rayuwarta. Sumu sumu haka ta fice falo.
Tana zaune tayi jigum ya fito daga cikin ɗakin, sanye yake da blue ɗin wando kalan nata, sai dai nasa na maza ne babu ado kamar nata, saikuma farar polo shirt, murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau sosai, shima murmushin yayi mata haɗe da kashe mata idanunsa ɗaya…
Ita da kanta ta zuba musu abinci, yanaci yanata zuba mata santi, har batasan lokacin da tarin damuwar dake cikin ranta suka kau tasoma ƙyalƙyalewa da dariya ba …
****
Zaid ne zaune agaban Dad ɗinsa ya sunkuyar da kansa ƙasa, magana Dad ɗin keyi masa amma kuma kwata kwata bayajinsa, hankalinsa da tunaninsa sunyi nisa sosai wajen tunanin Zahrah, muryarta dayaji ɗazu shiya kara rikita masa tunani, baisauraran Dad dake yimasa bayani amma duk da haka yaji abun da Dad ɗin yafaɗa na ƙarshe, cike da ƙuncin rai haɗe da tsananin mamaki yake kallon Dad ɗinnasa cikin wata murya me ɗaci yace
“Aure fa kace Dad? ni ɗin, kuma da wata ba Zahrah ba?”
Cikin takaici Dad yake kallon Zaid ɗin, wato tunkan ayi nisa ma yafara nuna masa cewa hakan bazai yiwuba kenan.
“Natabbatar kajini, kuma aure babu fashi!” Dad yafaɗi haka a ƙufule, domin kuwa shima yafara gajiyawa da halayyan Zaid na rashin hankali, taya zaka je kana yiwa matar wani soyayya me tsanani irin haka.
Wani murmushi Zaid yayi me matuƙar ciwo haɗe da sanya haƙoransa ya ciji laɓɓansa.
“Bazan iyaba Dad, kaima kafi kowa sanin hakan, aduniyar nan mace ɗaya kawai nakejin zan iya rayuwar aure da ita, bakowa bace kuma Zahrah ce, saboda haka please Dad maganar wani aure na da wata kabarshi don banaso, idan kuma ka matsa shikenan, amma idan kuka tsinci gawanta nayi mata mugun illa kada ku zargeni kufara zargin kanku” yana kaiwa nan azancensa ya tashi tsaye yafice daga falon mahaifinnasa.. Baki a wangale haka Dad yabi Zaid da kallo har yaɓacewa ganinsa..
“Lallaima kuwa Zaid ya ɗauko babban al’amari, amma kuma wannan karon sam bazai lamunta masa ba aure dole sai yayi masa, acikin satin nan ma kuwa” Dad yafaɗi haka acikin zuciyarsa…
Zaid kuwa yana fita a ɗakin Dad direct motarsa yashiga, dagudun gaske ya ja motar yafice daga cikin gidan, tafiya yake akan titi amma zuciyarsa ƙuna takeyi masa, har wani ɗaci yakeji a maƙoshinsa, wayarsa ce tayi wani ɗan gajeren ƙara alamar shigowar saƙo (Message), da sauri ya ɗauki wayar ya duba, domin kuwa tun ɗazu dama saƙon yake jira, adireshi ne na gidan da Zahrah take aka turo masa.. Wani mugun murmushi naga yayi haɗe da ɗan dukan kan steering motar, lallai dole zai cimma burinsa ne kota halin yaya kuwa…
Faka motan yayi yana me ƙaremawa gaban gidan kallo, gidane me kyau da kuma aji, dagani kasan ankashe kuɗi wajen tsara gidan, amma Zaid dake kishi yacika masa zuciya sam baiga wani kyawun gidan ba, saima ji da yayi ya tsani gidan.. Idanunsa ya tsaida akan tankamemen gate ɗin gidan tamkar wanda yake karantan wani abu, a hankali ya buɗe murfin motar tasa yafito waje, cikin takunsa na isa yashiga takawa harzuwa wajen gate ɗin……. (🤔Anya zaishiga kuwa?hmmm inaga dai yau Zaid aƙasam kanta zai kwana😂)