UMM ADIYYAH CHAPTER 48 BY AZIZA IDRIS GOMBE
Www.bankinhausanovels.com.ng
Inda muka tsaya
Gaskiya hakan bai yi ba sam. Musamman da ya san ga abinda ke hannu. Akwai ma
sha’anin mutuwa ai, wani abu idan ya faru ba a san inda yake ba fa?”
“Ina ga yarinyar nan kawai tayi masa mai zafi ne, ka san yadda yake da gudun
zuciyar mutum. May be ba zai iya ganin su Maami bane ya facia masu duk abinda ke
faruwa. Anyways, na gode. Zan ci-gaba da bincikawa dai.”
“To shi kenan, ni ma a Hangarena zan yi iya KoKarina, akwai Agent Cclinsa na tafiye
tafiye, zan neme shi, na ji.” “To sai na ji ka.”
Suna gama waya. Yaya Saadik ya wuce gidan Abba. Ya facfa masu abinda ake ciki,
Www.bankinhausanovels.com.ng
yana gidan. Adda Zubaida ta shigo da Umm Adiyya, idanunta sun yi jazur! Kamar
mai layi, saboda ba ta da isasshen Karfi a jikinta.
Kanta ya yi a hanzarce, ya Caga hannu zai tsinketa da mari, da sauri Adda Zubaida
ta janyeta, “Yaya meye haka?”
“Meye haka? Ku na kallo, ku ka bar yarinyar nan take zuba iya shegen da take so,
yanzu ga shi nan an nemi Yaya Zaid din, an rasa, na tabbata haka kawai ba zai
Hace Bat ba! Sai idan baya son fuskantar su Baffa. Ke wai dama har yanzu ba ki yi
hankali ba ashe?”
“Don Allah Yaya ka bar ta, yanzu za mu yi magana da ita, shi ya sa ma na zo da ita
mu haclu da Maami mu yi mata magana, ai komai Clan daidaitawa ne ko?” Www.bankinhausanovels.com.ng
“Ke da Asma’ cikinku waye aka taba jin kansa, amma wannan yarinyar kullum
cusawa mutane baKkin-ciki take yi. Wallahi ki ka yarda su Abba suka shiga damuwa a
kanki, sai na gwada misali dake.”
Kanta na Kasa ta wuce ciki zuwa falon Maami, ta san yanzu kam kowa ma laifinta
zai gani, kuma dole a zageta a yi mata komai ma saboda a kansu aka fara auren
Dangi a zuri’ar ga shi abin ya faro a bai-bai.
******
“Ki na jin abinda Yaya Saadik ya fada ko Ummu A? To ina son ki san da cewa
wannan kadfan ne, wannan jininki ne ke fadian hakan a kanki, ke hakan ya fi miki ace
a dalilinki, hankula sun tashi?”
Shiru ta yi tana share hawayenta. Adda Zubaida ta ce, “Kin san dai laifin mace ake
fara gain, muddin aka ce saki ya shigo cikin batu ko?”
“Ni ba ni da matsala da wannan, na san mun dauki matakan da ba su dace ba, mun
dauki hanyoyin da ba daidai ba, amma Adda Zubaida tun farko akan me ya sa zai
dauki wannan matakin? Eh, na san kowa da yadda yake handling matsaloli a
rayuwarsa, amma shi ba zai yi la’akari da sau biyu ina rasa gudan jinina ba?
Babu abu kuma ma fi soyuwa a gareni, irin na samu dana, dan Yaya Zaid dina a
Kasan marata, na riKe shi a hannuna, nayi masa addu’a, na koya masa karatu, nayi
masa tarbiyya. Don me ya sa za a Kwace min wannan damar?Www.bankinhausanovels.com.ng
Idan baya so ya sake fuskantar abin da ya fuskanta na rasa Canmu, ai ba tsarin iyali
bane amsar yin hakan. Likitoci sun facia a duka lokuta biyun ababe daban-daban ne
Hace Bat ba! Sai idan baya son fuskantar su Baffa. Ke wai dama har yanzu ba ki yi
hankali ba ashe?”
“Don Allah Yaya ka bar ta, yanzu za mu yi magana da ita, shi ya sa ma na zo da ita
mu haclu da Maami mu yi mata magana, ai komai Clan daidaitawa ne ko?”
“Ke da Asma’ cikinku waye aka taba jin kansa, amma wannan yarinyar kullum
cusawa mutane baKkin-ciki take yi. Wallahi ki ka yarda su Abba suka shiga damuwa a
kanki, sai na gwada misali dake.”
Kanta na Kasa ta wuce ciki zuwa falon Maami, ta san yanzu kam kowa ma laifinta
zai gani, kuma dole a zageta a yi mata komai ma saboda a kansu aka fara auren
dangi a zuri’ar ga shi abin ya faro a bai-bai.
********
“Ki na jin abinda Yaya Saadik ya fada ko Ummu A? To ina son ki san da cewa
wannan kadfan ne, wannan jininki ne ke fadian hakan a kanki, ke hakan ya fi miki ace
a dalilinki, hankula sun tashi?”
Shiru ta yi tana share hawayenta. Adda Zubaida ta ce, “Kin san dai laifin mace ake Www.bankinhausanovels.com.ng
fara gain, muddin aka ce saki ya shigo cikin batu ko?”
“Ni ba ni da matsala da wannan, na san mun dauki matakan da ba su dace ba, mun
dauki hanyoyin da ba daidai ba, amma Adda Zubaida tun farko akan me ya sa zai
dauki wannan matakin? Eh, na san kowa da yadda yake handling matsaloli a
rayuwarsa, amma shi ba zai yi la’akari da sau biyu ina rasa gudan jinina ba?
Babu abu kuma ma fi soyuwa a gareni, irin na samu dana, dan Yaya Zaid dina a
Kasan marata, na riKe shi a hannuna, nayi masa addu’a, na koya masa karatu, nayi
masa tarbiyya. Don me ya sa za a Kwace min wannan damar?
Idan baya so ya sake fuskantar abin da ya fuskanta na rasa Canmu, ai ba tsarin iyali
bane amsar yin hakan. Likitoci sun facia a duka lokuta biyun ababe daban-daban ne
suka janyo min rasa abin ciki na. Shin ya san abinda Uwa take fuskanta a lokacin
nan? Ban ce uba baya jin zafin rasa dlansa ba, amma ina za a hada biyun?”
Adda Zubaida ta yi tsam, tana kallon ‘yaruwarta cike da tausayawa. “Wata Kila baya
son ya sake ganinki a halin Kunci na ciwo ne. Ba Karamin tabuwa ya yi ba a Darinki
na biyun nan Umm Adiyya, ka na ganinsa ka san yana Clauke da damuwa. Baya nufin wani mugun nufi a kanki.”
“Baya son ya ganni a mawuyacin hali ne, zai hanani abinda na ke so? Ya hanani
zuri’arsa? Kullum a tunanina ni yake so na zama uwar ‘ya’yansa, ki fadla min ta inda
tsarin iyali zai bar mu, mu cimma hakan. Wannan ya sa na gindaya masa sharadii,
kar ya kuskura ya zo inda na ke, in dai sai na amince da batunsa zai kusanceni.”
“Ummu A. Ki na lafiya? Mijinki ne fa! Kin ma san girman miji a gun mace kuwa?”
Umm Adiyya ta claga jajayen idanunta da suka yi luhu-luhu, ta dubi Adda Zubaida,
“Mijina da baya son hada zuri’a da ni, mijina da ya cutar da ni ta hanyar da ban taba Www.bankinhausanovels.com.ng
tsammanin zai cutar da ni ba.”
“Ummu A.?”
“Ku bar shi kawai, ya wuce, ku bar shi kawai, amma kar ku sake cewa na koma
gidan Yaya Zaid.”
“Shi kenan ya isa, ki yi shiru.” Adda Zubaida ta ja ta jikinta ta rungumeta tana shafa bayanta cikin lallashi. “Shi kenan.”” Ta yi haka ne, zuwa anjima ta sake lallaminta har ta fadi wannan dai abin da take Doyewar.
********
Da dare Abba ya shigo, yake ce masu duk su shirya za su wuce Gombe washegari,
daga jin hakan zuwa safiya. Umm Adiyya ta shiga bancfaki ya yi sau shida.
Ta san nata ta Kare, zance ya shiga kunnen su Baffa da Mama da su Hajja Ku. Allah
kacfai ya san watandan da za su yi da ita.
Tunda ta fito da Asuba, ta gayar da su Abba suka amsa mata a ciki, ta san cewa ta
samu matsala, an gama. Inji mai kashi a gado.
Ga shi ta ji suna cewa ba su samu
Yaya Zaid din ba ma, don Yaya Saadik ya zo ya gama dirinsa a daren jiyan, ya Kare
da ce mata, “Sai ki yi tunanin inda ya tafi ai, ki facia mana idan kin damu da inda
yake zuwan ma kenan, na ji labari kin dadfe ki na masa isgilancin da ki ke so, ban
ma san yaya aka yi ya Kyaleki, ki ke masa abinda ki ke so ba.” Www.bankinhausanovels.com.ng
“Yaya, Allah ban san inda ya tafi ba, ni ma ko ranar da abin ya faru ma, saKo kawai
ya turo min a wayata.”
Tafiya ce dai ake yi tamkar an yi mutuwa, koda yake Karamar mutuwar ce ai rabuwa
ta aure, ba Karamin abu bane.
Wannan ya sa lokacin da wayar Saadik take ta Kara, bai daga ba, saboda yana tuKi,
kuma Abba na gefensa, ya damu gaba Claya shi da ilahirin ‘yan motar.
“Haba daga wannan abin don Allah.” Maami ta faca tana zaune a gidan baya,
saboda yadda Karar ta cikasu.
Yayin da Umm Adiyya da Adda Zubaida suke tahowa a motar Baban Walid, su uku
ne a nan dfin ‘yan biyu ba su taho ba, suna can Abuja. Rage gudu ya yi kadcan,
sannan ya daga, “Hello, Assalamu-alaikum.”
“Wa’alai-kumu-Salam, na ji ka na nemana.” Aka fadla a aya Dangaren.
Yaya Saadik ya faKaici idon Abba, sannan ya canza kunnen da yake magana a
wayar. “M… me kace? Ina nemanka? Ka jarraba gaba daya zauri’ar Muhammadu
Nafada na nemanka, ina ka shiga Yaya Zaid?” “Ina lafiya, yaya su Maami?’
“Ba na tsammanin ka na bukatar jin wannan amsar, ka taho Gombe duk inda ka ke
ma kuwa, don Baffa yana nemanku. Baffa MaiKano ma gobe yana hanya.”
“Ya-Salaam! Abinda na ke gudu kenan ai.” Ya fada idanu a runtse daga
Hangarensa. “I’m sorry Bro. Amma dole ka taho.”
“Zan yi KoKari na iso ko nan da kwana biyu ne
Inshaa-Allah.” Kwana biyu? Ka ji me na ke fadla kuwa? Su Baffa ke nemanka fa. Ka na ina ne?”
Daga daya Hangaren Zaid ya lumshe idanunsa, hacfe da shafo kansa. “Ina Chennai.”
******
BABI NA TALATIN DA UKU
Yaya Saadik kam shiru ya yi na tsawon lokaci, sannan ya sulale wayar daga
kunnensa, ya kalli fuskar wayar, ya Kara mayar da ita kunnensa. Www.bankinhausanovels.com.ng
“Sai ka dawo, idan zai yiwu, ka fara neman jirgi yanzun nan ka iso gobe.”
“Ina wai ya shiga? Ya dagawa jama’a hankali.” Abba ya tambaya. Saadik na kashe wayarsa. “Indiya.”
“To ka ji irin abin ai, shi da zai tsaya a san me ake ciki, zai yi taflya ya kuma kashe wayoyinsa?”
“Abba ina ga dai gudun zaman ne ya sa ya tafi.”
“Allah dai ya kyauta. Amma sun tafka wauta ai”
“Umm Adiyya ce ta janyo komai Abba, kuma aka sanya mata idanu.”
“Kai Saadik, ka yi mana shiru, ba ma son zancen wofi.” Maami ta fada rai a bace.
Haka dai aka Karasa tafiyar, rai a dagule.
Gidan Hajja Kubitto suka fara zuwa, aka gaisa, bayan nan ne Abba ya baje bayanin
abinda yake faruwa, nan aka bar tsohuwa da taba hannaye da salati.
“Malam din ne da yin saki? To Allah ya kyauta, to me ake jira ba a mayar da auren ba?”
“Hajja, ana dai jiran dawowarsa, da yake ya tafi ‘yan wasu uzurorin, amma da zarar
ya dawo, za a zaunar da su a ji abinda ake ciki.” “Amma dai Zubairu sakacinku da yawa, yaya
za ayi har a kai wannan matakin kai da
Nahuce a gaza samun wanda zai magance matsalar har a kai ga matakin saki? Ke
Toke me ki ke yiwa Mijin naki?”
Umm Adiyya ko tunda Abba ya fara yiwa Hajja Kubitto bayani, take raba idanu tana
sharara kukan zuci.
“Hajja za ta fada ne? Ni dai in ta ni ne ku yi yadda ku ke so da ita.”
“‘A’a za dai aji koma menene, tunda ba su taba kai Kara gida ba, ai sai wannan.”
“Ko kwanaki ma sun samu sabani, mun zaci abin kacfan ne, ashe bayan sun koma,
haka nan abin ya ci-gaba yanzun kawai sai ga wannan gagarumin aikin kuma.” Abba Www.bankinhausanovels.com.ng
ya Karasa bayani.
“To, Allah hoinu, amma wannan abin bai yi dacfi ba, bari Malam din ya dawo ya zo Www.bankinhausanovels.com.ng
ya tarkata ta su koma kawai, su je su yi ta hakuri, haka duk muka yi muka girma. Iyi ai shi ne girman.”
Da dare suka wuce gidan Abba suka kimtsa. Adiyya kam duniya ta yi mata zafi, don Kiri-Kiri daga Abba har Maami ba mai kula sabgarta, a tunaninta wurin Abban ne ma
HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.BANKINHAUSANOVELS.COM.NG