UNCLE NE CHAPTER 11 BY NIMCYLUV
Www.bankinhausanovels.com.ng
Me yasa kake damun kanka Alhaji khamal?na gaya maka komai ya huce kuma yanci gaba da riƙe Nihila as my daughter”kallonsa kawai Alhaji khamal kafin yace “ina jin kamar ban zame maka amini na gari ba,na cuceka cutar da bai dace amini yaywa amininsa ba,na cuci kaina na cuci baby,dan Allah dan Annabi kayi hqr ka yafemin Wlh bana jin daɗi zcyta babu daɗi,gani nake kamar kana riƙe dani kana jin haushina kamar kana gaba dani” ya faɗa idanunsa cike da hawaye, girgiza kai Abbou yay yace “kada ka damu gareni komai ya huce komai da sanadinsa Allah ya rufa mana asiri baki ɗaya” da Ameen Alhaji khamal ya amsa jiki kuma a sanyaye ya ƙara yiwa Abbou gaisuwa kana ya bar gida zcyarsa babu daɗi,shima Abbou juyawa yay ya shige cikin gida kai tsaye upstairs, Mameey na shiga lambun ta hangesa can kusa da ƙorama ya zura ƙafafunsa ciki yana ɗan wasa da ruwan yayinda idanunsa suke kallon cikin ruwan amma a zahirance bawai ruwan yake kalla ba, tunaninsa yana can wani wajan daban, ƙarasawa wajansa tayi tare dajan wata kujerar ta zauna,bayan ta zauna da kallesa sosai taga gaba ɗaya hankalinsa yana ga wani waje domin ko zuwanta wajan bai sani ba,hannu tasa ta taɓosa da ɗan sauri ya sauke
ajjiyar zcy tare da juyawa sbd yasan shi ɗaya ne a wajan,ganin Mameey yasa ya ɗan saki murmushin gefen baki,kallonsa kawai Mameey tayi kafin tace “meyasa zaka zauna kai ɗaya?”shiru kawai yay mata baice komai ba, Mameey tace “ina lura dakai tun safe ba kaci komai ba,anya zama zai yiwu babu cin abinci?ai saka ɗaurawa kanka wani ciwon nada ban kuma,ohhyaa ga abinci” kallonta yay ya kalli abincin kamar bazai magana ba sai kuma yace “i lost my appetite” Mameey tace “ayaa,dole haka zaka daure kaci ko babu yawa ko kuma a matse maka lemon kasha za kaji dai-dai” baice komai ba ganin ta ɗauki wayarta can kuma ta kara wayar a kunne tace “baby matsewa bobo lemon guda 10 a cup ki ɗan saka suger half spoon” Nihila dake zaune tana kallon Jalilerh wacce take ƙwance tai lamo saman bed ta rungome pillow tana sauke ajjiyar zcy tace “ok Mameey,part ɗinsa za’a kai masa?” Mameey tace “no yana lambu” tana faɗin haka tai rejecting call ɗin, Jalal ne ya fesar da numfashi yace “Mameey bana shan lemon” da mmki Mameey tace “yaushe hakan ya faro,bayan kowa yasan kana sha”lumshe idanunsa kawai yay yace “kawai na daina” gyara zama Mameey tayi cikin serious magana tace” ina tunanin zan maye maka gurbin Oum Jalal,ina tunanin zan baka farin ciki irin wanda kake samu wajan Oum Jalal,amma naga kamar baka nema daga waje na, Muhammad tunda nake da mahaifiyarka Zulfa musu bai taɓa haɗani da ita ba,kusan zan iya cewa nafi kowa baƙin cikin abinda ya faru,Wlh tllh ni kallon su Irfan nake maka gani nake kaima nina haifeka,bana ganin wani banbanci tsakani,dan Allah nima kayi min kallon uwa,bawai ka gayan damuwarka ba domin nasan wannan halittar ka ce ba kowa yake sanin abinda ke ranka ba,amma ko yaya ne ka dinga sharing damuwarka dani in sha Allah zan zame maka madadin abinda ka rasa”ta ƙare maganar tana buɗe wasu warmers,kafin ta buɗe yay saurin riƙe hannunta yana ɗan kwaɓe fuska yace “noo please Mameey, coffee kawai” bata kallesa ba itama tace “eat something than sai kasha coffee ɗin” shiru yay mata harta gama zuba masa Chucus plantain wanda yaji nama, aƙwai kana ta sanya masa spoon ta ɗora masa a cinya tace “eat” bai son musu da ita hakan yasa ya ɗauka ya fara sanyawa cikin bakinsa kamar bai so, yadda yake taunawa kawai zai nuna maka ba daɗin abincin ya keji ba,a haka ya samu yaci rabi kana ya ture plate ɗin, kallonsa tayi tace “meye wannan?” Cikin ƙasa da murya yace “Mameey I’m full” kafin tai magana Nihila ta ƙarasu wajan hannunta riƙe da ƙaramin tray ta ɗura cup a samansa, durƙusawa tayi idanunta akan bobo tace Mameey gashi, girgiza kai Mameey tayi tace “no baida kawai” Nihila ta kalli bobo tace “bobo ya jikin?”idanunsa akan ruwan dake kwaranya yace “Allahamdulillah”zata ƙara magana Mameey tace “leave” komawa tayi da tray ɗin lemon tana tafe tana juyawa,bayan yasha ruwan da Mameey ta bashi ya miƙe tsaye zai fita Mameey tace “koma ka zauna i want talk to you Muhammad” zama yay yana ɗura idanunsa akan Mameey,itama kallonsa tayi tace “mene ra’ayinka akan baby?” With much surprise ya dinga kallonta kafin ta ɗura da faɗin “nasan baka da niyyar aure yanzu,amma yanayin da kake jiki auren shine mafita,kuma kasan idanun jama’a akan ka suke dole ne ka ajjiye iyali ka fara mulkarsu kafin ka mulki jama’ar gari,ban san yaya matsayin baby yake a ranka ba,kana sonta da aure ko akasin haka? duk yadda yake a ranka inma kallon sister kake mata ko baka da feelings a kanta,ya zama dole ka dinga sanya sonta da son kasancewa da ita a cikin zcyarka,nasan bata da wata damuwa komai aka zartai zata amsa,amma ga namiji auren macen da bai so matsala ne,duk da cewa ina da tabbacin ba zaka taɓa yin wani abu da zai cuci Nihila ba,amma rayuwar aure da kuma zamantakewarsa daban yake,dole yadda kuke ada ba haka zaku kasance ba,anawa tunanin ya kamata ka fara jin ta bakinta ma’ana ka fara keɓewa da ita”ware idanunsa wanda suke a rufe yay kafin ya cije lips ɗinsa yace “what about Jafar?” Shiru Mameey itama tayi kafin ta miƙe tace “don’t worry about him, Abbou Jalal zai masa magana ok” tana faɗin hakan ta miƙe tsaye tare da ɗaukan tray ɗin tai gaba da kallo kawai ya bita,kafin ya sauke wasu tagwayen ajjiyar zuciya. Bayan sallar issha’i Jafar yay parking da motarsa kana ya nufi cikin gida,a main parlour ya samu Mameey sai kuma Mama zama yay kansa a ƙasa ya gaishesu kana ya ƙara yi masu ta’aziyya,satar kallon Nihila yay sai kuma ya ɗauke kansa, miƙewa Mameey tayi tace “bari nasa Laure ta kawo maka ruwa”bai ce komai ba sai Murmushi da yayi, Nihila ce tace “Yaya Jafar ina yini?” Murmushi yay wanda yake nuna zallar jin daɗi yace “bana amsawa” idanunta ta ɗauke daga kan littafin da take dubawa tace “why?” Shima ya kwaikwayi muryarta yace “why?” Salati yaji an zabga da sauri ya juya sbd a tunaninsa tuni Mama tabar parlour’n tsaye ya ganta tana tafa hannu tace “huuuu³ yaushe ka zama sallamamme bani da labari,a’a Wlh wannan halin banza ne,ina ruwanka dayin Muryar mace? Banda neman magana, yuuuu ko daudo zaka koma ne bana da labari Jafaru? a’a wlh wannan gantalewa ce yaya ina ya bonka sallah zaka kasa alwala?” Ɓata fuska yay yace “to ina ruwanki ne?” Haɓa ta riƙe tace “Mahadurrasulillah zagina zakai? Daga faɗin gsky sai cin mutunci ya biyo baya? To Allah ya baka hqr tunda ka zama gantalalle” shi dai baice komai ba harta gama surutanta tai gaba,tana barin parlour’n ya koma kusa da Nihila yace “me kike ne?” Idanunta akan littafi tace “study” jinjina kai yay yace “ok you can continue my wife to be soon in sha Allah” ɗago kai tayi ta kallesa suka haɗa ido kasa ɗauke idanunta tayi sbd gabanta daya faɗi taba rasa mene za tace masa,tarin da sukaji yasa gaba ɗaya suka dawo cikin nutsuwarsu,bobo ya fito daga shi sai 3gauter da farar singlet kai tsaye kitchen ya nufa ko inda suke bai kalla ba, duk da cewa shida Jalal abokai ne amma hakan bai hana yaji wata kunyarsa ta kama sa ba,dalilin haka yasa ya miƙe da sauri ya ɗauki key ɗin motarsa yace da Nihila “goodnight wify,luv u Soo much” yana faɗin hakan ya fice daga cikin gidan ya nufi waje,bobo na shiga kitchen yaga da aƙwai ruwan zafi a flast tea ya haɗa a mug ya zuba milk da bonvita da obalti,sai suger guda uku, spoon yasa ya juya tea ɗin, yana kitchen ɗin zaune saman stool kasan cewar ta kashe wutar kitchen ɗin yasa ba kowa zai san yana ciki ba, tun daga bakin ƙofa ya hango ta tana tafiya a hankali kamar wacce ƙwai ya fashewa a ciki,tana tafe hannunta a mararta wacce tun safe take mata ciwo, idanu ta fara rarraba wa sbd duhun data gani a kitchen ɗin, ƙarasa shiga ciki tayi ta nufi inda makunnin ƙwan yake,tsayawa tai cak a tsakiyar kitchen ɗin sbd wani murɗawa da marta tai har sai da ta saki ƙara ta durƙoshe a wajan ta fara kuka,sbd Allah yana gani ciwon ya fara cin ƙarfinta,ga wani amai dake taso mata haɗe da ciwon kai zazzaɓi duk lokaci guda,duk abinda take a kan idanunsa yana zaune yana shan tea hankali ƙwance time to time yana lumshe idanunsa,amma idanunsa ko mutsawa basayi a kanta, lokaci ɗaya kuma ya fahimci abinda ke damunta,ganin bata da niyyar miƙewa ga kukan dake cin ƙarfinta,yasa ya sakko daga saman stool tare da ajjiye cup ɗin wajan sink,kai tsaye wajanta ya nufa yana tafe a hankali sbd bai son taka wani abu ko taka hannunta sbd ba sosai yake ganin komai na kitchen ɗin ba,a haka harya ƙarasa zuwa inda take,fesar da numfashi yay tare da sunkuyawa yasa duk hannayensa biyun ya ɗagota sosai ta tsorata zata saki ihu yay saurin saka hannu ya toshe mata baki, tura ta ya dingayi har zuwa jikin bango kafin ya haɗata da jikin bangon ya ɗan ranƙwafo dai-dai fuskarta yana leƙawa, bakinta kawai yake iya gani suma dalilin jan da sukai ga kuma hawaye da yawon da suka jiƙasa,ita dai Jalilerh sai leƙa fuskarsa take amma ta kasa ganin ko waye sbd duhu ga kuma wani a zaɓaɓɓen ciwo dake cinta hakan yasa ta ƙara sakin wani kukan tana zabewa zata faɗi yay saurin haɗata da jikinsa a tare suka sauke ajjiyar zcya mai ƙarfi,da sauri Nihila wacce take bakin kitchen ɗin ta juya idanunta cike da hawaye,shiru gaba ɗaya sukai sai Jalilerh dake sauke ajjiyar zcy,a hankali kuma ya dinga bubbuga bayanta yana shafa ƙwantaccen gashin kanta,a hankali kuma ta dingani ciwon na sauka sai wani gumi daya dinga sakko mata, idanunsa ya sauke a red lips ɗinsa kafin a hankali kuma ya ƙarasa kusanta bakinsa da nata ya ɗan lumshe idanunsa cikin ɗaukewar numfashi ya sauke lips ɗinsa saman nata kafin ya bata wani special hurt kiss a gefen lips ɗinta,kana ya juya da sauri yabar kitchen ɗin,yana fita ya samu Aryan a parlour ko kallansa bai ba ya ƙarasa shigewa part ɗinta, Aryan kuma kitchen ɗin ya shiga yana shiga yaji bugi abu da sauri kuma yasa hannu ya kunna hasken kitchen ɗin,tsaye ya ganta kanta a ƙasa, ƙarasawa yay inda take tsayen tare da leƙa fuskarta ganin hawaye ƙwance saman fuskarta yasa shi faɗin “Hubby…!!”saurin ɗago kai tayi yayinda zcyarta ta buga da ƙarfi,zallar tsoro ya bai yana a Zcyarta tunaninta shine badai Aryan shine ya rungome ta ba?to idan ba shi bane waye? Tabbas shine tunda gashi taji muryarsa kuma shi ta gani tsaye,to mene yake cikin kitchen ɗin?ganin tai shiru tana kallonsa yasa yace “what wrong?” Nan ma shiru tai masa hannu ya miƙa zai riƙe ta tayi sauri matsawa baya tana girgiza kanta,kallon fararan kayan baccin dake jikinta yay sai kuma ya ɗauke kai tace “You are Staired” da sauri ta kalli jikin ta sai kuma tai waje da gudu bayanta yabi da kallo yana sauke ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya. washegari kamar yadda aka buƙata Jalal ya shirya cikin wata jumper mai shegen ƙyau maroon color ya saka babbar rigar,sai Black hula da black covert shoe,hannunsa ya ɗaura agogon gucci ga farin bluetooth daya saka,da sauri ya ƙarasa fesa parfume ɗin hannunsa,kana ya ɗauki wayoyinsa ya riƙe,fita yay yana fita ya zamu Mameey ita ɗaya a main parlour kowa ya tafi wajan aiki dake Monday ce, Nihila kuma na makaranta Jalilerh na ɗaki tana bacci sbd bata jin daɗi, Abbou yana wajan masu karɓar gaisuwar da suka zo masa,kallon Mameey yay yace “Mameey I’m going,a gyaran part ɗina before I’m coming back” murmushin jin daɗi tayi ganin yay fesa kamar ango sai zabga ƙamshi yake,ga wata cikar zati haiba kwarjini daya ƙara fitowa saman fuskarsa,tace “in sha Allah, Allah ya tsare ya kiyaye” da Ameen ya amsa kana yay waje,yana fita securities suka rufa masa baya,wata lafiyayyiyar mota aka buɗe masa back seat ya zauna kana driver ya shiga,su kuma su shiga taso motar guda biyu,suka saka motar Jalal a tsakiya a hankali motocin suka fara barin gidan,da yammacin ranar Mubarak Yahya cibo ne zaune a gaban boka Saƙib yana sauraran abinda yake faɗa,boka Saƙib yaci gaba da faɗin “kayi kuskure domin abinda mukace ka aikata bashi kai ba,dole ne ka samu matsala akan zaɓen ka,dole ne kujerar tai rawa,kaci Sa’a kazo da wuri banda haka da bazan iya komai akai ba”da sauri Mubarak Yahya cibo yace “Ni dai burina kawai bai huce na Jalal a ƙasa ba, farin ciki na shi ne dukkan abinda ya sawa hannu a harkar mulkinsa ace ya lalace abun bai albarka ba,ai tasa masa ɓarnar kuɗi,idan har zai yiwu ma kawai a sa ya zama Mazinaci..
_End of book 2 Allhamdulillah ³, Allah yasa muga farkon book 3 lafiya,GAREKU masu karanta min littafi ƙyauta dan Allah ku daina,wannan gumi nane idan dole book ɗina kuke son karantawa ga MOON nan shi free book ne wanda nake typing ɗinsa yanzu, littafin UNCLE NE na kuɗi ne akan 300 vip kuma 600 asusun biya 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 NIMCYLUV😍_
Book 3
ma sha Allah littafi ya ɗauko hanyar ƙare wa,ina sane da masu karanta min book ƙyauta bayan kun san na kuɗi ne,duk wannan bai daman ba,irin wanda suka siya suke fidda min amma ka ku damu,duk mai niyyar biyana 300 babu yawa 600 for vip account details 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 081192371616, Duk mace mai aji neman na kanta take kuma halal ɗinta, rashin daraja ne karɓar abin sata😂👌🏼_
Dariya boka Saƙib yayi har wani hayaƙi na fita ta cikin bakinsa,sai da yayi mai isar sa sannan ya tsoke bakinsa kamar bashi ne ya gama dryar ba, ƙasa ya buga ya fara zane a ƙasanta kana ya ɗago kai yace “an gama,amma bisa sharaɗi guda” da sauri Mubarak Yahya cibo yace “mene sharaɗin gaya min?” boka Saƙib yace “dole ne ka saka masa wannan maganin a inda yake zama,ko kuma kasa masa cikin takalmin sawarsa” Mubarak Yahya cibo ya kalli bokan kafin ya yace “Allah gafarta babu wata hanyar da za’a iya wannan aikin dole sai ni?” Boka Saƙib yace “ita kaɗai ce hanyar da buƙatar ka zata biya,da ace aƙwai wata hanyar da tuni na faɗa baka,kuma tunda ka amsa dole kayi,rashin aikata hakan babbar matsala ne kuma komai na iya faruwa dakai” Mubarak cibo yace “menene matsalar kuma?” Boka Saƙib ya ɗago jajayen idanunsa ya shiga kallon Mubarak cibo kamar wanda yake duba wani abu a jikinsa,chan kuma ya ɗauke idanunsa yace “bazan iya gaya maka matsalar ba,amma dai ya zama dole ka aikata wannan abun cikin kwanakin nan”jinjina kai kawai Mubarak cibo yay kafin yace “shkknan I’ll do my best wajan ganin nayi aikin dai-dai”boka Saƙib yace “yawwa ɓatacce wanda ya yarda aikin boka yaƙi faɗar Allah”shi dai jinsa kawai yake domin idan da sabo ya saba da wannan surutan nasa, kuɗi masu yawan gaske ya ajjiye wa boka Saƙib kana ya fice daga cikin ɗan ƙaramin ɗakin bayan ya amshi maganin,nan ya tarar da mutane da yawa ɓatattu irinsa wanda suke jiran fitowar sa,kai tsaye gidansa ya nufa yana zuwa ya tarar da Hajja Ayushert zaune tayi ta gumi kallo guda zakai mata kasan cewa tana cikin damuwa,tana ganinsa ta miƙe tsaye fuskarta babu walwala tace “haba Alhaji wai mai kakeson zama ne?mai yasa mulki ya keson kaika lahira ne? Nina kasa fahimtar abinda kasa a gabanka,baka tunanin komai sai mulki,kamar dashi aka kawo ka duniya?gsky ka nemawa kanka mafita,nifa mulkin nan ya ishe ni kana ganin dalilin haka muka rasa ƴar mu ƙwaya ɗaya tak da muke da ita” tunda ta fara magana yake kallonta harta kawo ƙarshe,hannu ya ɗaga mata yace “yaushe kika zama uwata ban sani ba Ayushert?ko kuma ke kike Aure na bani nake naki ba?to wlh ki kiyaye ne, And mulkin nan ai bake nace kiyi ba,nine nake so kuma ni nake buƙata,ruwanki ki maramin baya ruwanki ne kiƙi i don’t care,kuma ki fita a idona na gaya maki”yana faɗin hakan ya shige part ɗinsa da sauri,da kallo kawai ta bisa yana shigewa ta ɗauki wayarta ta shiga dailing number yayarta Hajja Saudat,tana shiga ta nemi waje ta zauna tare da faɗin “Assalamu alaiki” Saudat dake tare da babban ɗan ta Bashir tace “Wasalamu alaiki Hajja Ayushert” Hajja Ayushert tace “Yaya Saudat aƙwai matsala wlh,dan Allah kina gida ne?”hankalin Hajja Saudat a tashen tace “yasubuhanallah!, lafiya?meke faruwa dake?”cikin kuka Hajja Ayushert tace “Nidai Yaya ki gayamin idan kina gida yanzu zanzo” da sauri Hajja Saudat tace “eh ina gida sai kin ƙarasu”kashe wayar sukai a tare kafin Hajja Ayushert ta miƙe ta fara shiri.bayan sallar magrib Lamir yay sallama cikin gidan Mama ce zaune a parlour sai Jalilerh wacce take ƙwance ta lumshe idanunta tana jin muyarsa ta miƙe da sauri kamar zata kifa tai upstairs,da kallo kawai ya bita yana wani irin Murmushi yana gyara hular kanta, Mama kam tunda ta kansa ta ɗura ƙafa ɗaya kan ɗaya ta shiga girgiza wa,zama yay yace “ina yini Mama?”shiru tai masa ba tace masa komai ba,shima shiru yay mata bai ƙara magana ba,ana haka Jalal ya shigo cikin bakinsa ɗauke da sallama hannunsa riƙe da key ɗin motarsa,a hankali yake tafiya kamar bai son ɗaga ƙafarsa sbd gajiya,tun safe daya fita zuwa gidan gwamnati ana shirye-shiryen Rantsuwa dake saura ƙwana biyu kacal, idanunsa ya ɗan wara jin Muryar Lamir yana amsa masa sallamar,kallo guda Jalal yaywa Lamir ya ɗauke kansa kamar bazai magana sai kuma yace “ina yini?”Lamir na Murmushi yace “lafiya ina tayaka murna fa”kamar ancewa Jalal ya zauna haka ya samu kansa da zama a saman sofar dake kallon Lamir,saurin runtsa idanunsa yay sbd wani abu da yaji ya sari kansa a hankali yaji kansa na juyawa,cikin ransa ya dinga ambatar “La’ilaha illallah Muhammad Rasulullah” haka ya dinga Nana tawa a cikin zcyarsa,da sauri kuma ya buɗe idanunsa jin mararsa na halbawa da ƙarfi tana ƙoƙarin miƙewa tsaye,abun ya keji kamar almara tunda yake haka bai taɓa faruwa dashi ba, cinyoyinsa ya haɗe waje guda yana ɗan maza Babbar rigar sa gudun kasa su kaga yadda mararsa ta miƙe tsaye,duk abinda yake akan idanun Lamir Murmushi kawai yake yana jinjina kansa, Mama ce ta kalli Jalal tace “Muhammadu yaushe ka zama sallamamme bani da labari?idan kai zcyarka mai ƙyau ce an gaya maka ta kowa mai ƙyau ne? Ka manta abinda ya aikata gareka har kake gaishesa,na ɗauka sa tamkar ɗan dana haifa a cikin jikina ban taɓa kallonsa a wanda wani ya haifesa bani ba,kana dai kallo kana jin abinda ya aikata ga gudan jini na,ba tai masa komai ba,babu abinda ta tsare masa tana kallonsa matsayin yayanta,amma yau shine ya nemi tuzarta rayuwata ya sanya akai mata abinda ko maƙiyinka baka son ya kasance da ita,dukkan abinda ya samu Zulfa shine sila,mai makon duk abinda zai yi ya aikata a kaina sai ya nemi tarwatsa farin cikin ƴarta,mai Zulfa tai masa? Me ta tsare masa?idan gadonta yake magana ba ubanta ya mutum ya bar mata ba?ko kuma kuɗin na uban wani ne?wlh wlh tllh da wasa naga ka ƙara gaida wannan mutumin sai ranka ya ɓaci,sai kaga ɓacin rai da baka taɓa ganinsa a waje na ba,tashi kaban waje?”kasa miƙewa yay sbd yadda ya keji baƙon yanayi a jikinsa,ga kuma yadda mararsa take ƙara miƙewa tare da harbawa sai haɗe cinyoyinsa yake,lokaci ɗaya idanunsa suka kaɗa sukai jajirr kamar wanda yaci kuka ya ƙoshi, miƙewa Lamir yay tare da kallon Mama yace “Ni ba tashin hankali ya kawo ni,kuma dukkan wannan abinda kike faɗe na aikata ne?hujja ɗaya da zata nuna ni mai laifi ne baku da ita,ko aƙwai hujja a wajanku ne?” Ko kallon inda yake batai ba,kuma bata tanka sa ba, Lamir yace “ko kuma zargina kike a kan wanda ya tuna asirin mahaifiyar Jalal da kuma Alhaji Kabeeru,to bani da niyar faɗa maku,ni bana da hannu a yaɗa cewa mahaifiyar Jalal mahaukaciya ce,abinda baki sani ba bayan ni Lamir kuma bayan ex Governor Mubarak Yahya cibo aƙwai wanda yake farauta rayuwar Jalal,kuma shi yake da hannu wanda faɗin abinda ya faruwa a ranar zaɓe,idan har zaku tashe tsaye ku tashi ni daga nan garin ma zan bari,kuma ni bani jin tsoran faɗin abinda nayi dukkan abinda na aikata zan iya faɗa a gaban kowa,maƙiyyan Jalal nada yawa na ɓoye dana sarari na jikinsa da kuma wanda bana jikinsa ba ok!” Yana faɗin hakan ya fice daga cikin parlour’n ya nufi waje,da idanu Mama ta bisa tana watsa masa harara kamar ta bishi ta shaƙe haka ta keji,kallonta ta dawo sashi zuwa ga Jalal tace “ka dai ji ko?to ni babu ruwana wlh,idan zakai hankali gwamma kayi niba shasha bace haka nan,kai dai girman kawai Allah ya baka da shekaru amma baka da wayo sam wlh,sai uban tunbi da aka ajjiye gaba kamar mai tsuhun ciki,to Wlh ka nutsu ni babu ruwana wlh na sha ruwan tabara da yasin na shayar da Zulfa dashi dan haka babu abinda zai sameka,wlh lalata ta zamanin yanzu ya lalace,abu daga wannan sai wannan kamar cin ƙwan makauniya”ta faɗa tana ficewa daga cikin parlour’n ta nufi part ɗinta,shi dai Jalal abin duniya ya ishesa abinda ya keji kaɗai ya ishesa,a sanyaye ya miƙe yana baza babbar rigar sa,harya shige part ɗinsa,girgiza kai kawai Abbou yay kafin ya juya ya nufi upstairs,daman ya fito ne domin ya tabbatar Jalal ya dawo kuma yana saukowa yaga abinda yake faruwa da sauyawar Mood ɗin Jalal har abinda Lamir yake faɗa da wanda Mama yake faɗa, Jalal na shiga part ɗinsa ya shige bedroom,kayan jikinsa ya fara cirewa ya sanya cikin datti clothes,yana gamawa ya shiga cikin bathroom ya sakawar kansa ruwan sanyi,iska ya fesar ta cikin bakinsa gaba ɗaya abu ya ishesa baya jin daɗin yanayin daya tsinci kansa a yanzu,yana jin wata kalar a zaba wacce bai taɓa jin ta taba, a gurguje ya kammala wankan,yay brush ya ɗaura alwala kana ya fito daga cikin bathroom ɗin sanye da bathrobe a jikinsa, wajan dressing mirror ya ƙarasa ya ɗauki body lotion ya fara shafawa saman fresh skin ɗinsa,yana gamawa ya ɗauki comp ya taje sumar kansa wacce take ta gyalli, parfume ɗinsa ya ɗauka mai sanyin ƙamshi ya fesa,kana ya je wajan wardrobe ɗinsa ya ɗauki wata maroon color ɗin jallabiya ya ɗauka,sai wani farin boxer ƙarami daya ɗauka ya sanya sosai ya kama waist ɗinsa amma haka yasa dan yafi son ya danne masa mararsa,yana gamawa ya ɗauki wani farin hirami ya ɗura saman kansa lokacin ladan ya fara kiran sallah,yana kammalawa ya fito daga daga cikin part ɗinsa,tsaye ya samu su Imran suna jiransa, haɗa baki sukai wajan faɗin “barka da fitowa”kansa a ƙasa yay gaba ba tare kuma daya amsa su ba,a main parlour suka samu Abbou,gaba ɗaya suka nufi masjid ɗin,bayan Jalal ya kammala jansu sallah ya zauna ya fara gabatar da karatun Alqur’ani ga jama’ar da suke jiransa,bai shigo cikin gida ba sai wajan 9:5 gaba ɗaya ya samesu a saman danning harya shige part ɗinsa sai ya tsaya sbd Muryar Abbou da yaji yana faɗin “Muhammad”tsayawa yay kana ya nufi wajan kujera yaja ya zauna,tunda ya zauna taji Zcyarta na bugawa da ƙarfi ga wani mayataccen ƙamshin parfume ɗinsa daya daki hancinta, lumshe idanunta tayi tana sauke ajjiyar zcya,tsaki kaɗan Nihila tayi sbd taji saukar ajjiyar zcyarta,kansa a ƙasa yace “gani” spoon ɗin hannunsa Abbou ya ajjiye ya ɗauki tissue ya goge bakinsa tass,kafin ya ɗauki gorar ruwa mai sanyi ya sha,samansa ya gyara tare da kallon yaran nasa sosai yace “ku ko shirya ko kada ko shirya na riga na yanke hukunci da zuciyata da kuma mahaifiyarku,bayan rantsuwar Jalal da sati guda duk za’ai bikinku, ni ba wata bidi’a za kuyi min ba,daga ɗaurin aure sai walimar da za’a haɗa bayan ɗaurin aure da sati ɗaya, tsakanin Jalal da Aryan kowa ya san wazai aura daku nake ƴan uku,ko hanzarta fitar da matar aure tun wuri”shiru gaba ɗaya sukai yayinda baby da tsorawa Jalal idanu tana son taji mene zai ce,jin shirun yay yawa yasa abby cewa “ko baku ji abinda nake faɗa bane?” Irfan ne yace “Abbou daman naiwa Mameey maganar ni wacce na keso a familynta ne, mai suna Ikram kuma nan da 2daya zaku ƙarasu”kallon Mameey Abbou yay Murmushi tai masa ta ajjiye cup ɗin hannunta tace “eh tun ranar baƙwan Mummy ya sanar min,daman yau nake son faɗa maka”idanunsa ya mayar kan Imran yace “what about you?”Imran ya sunkuyar dakai yace “a’a ni bana da wata budurwa Abbou duk abinda ka yanke shikenan” Mameey ce kallesa tace “kai sakaran kawai,kace tsoran matan kake,amma duk matan da suke duniyar nan kace ka rasa budurwa?” Abbou ne yace “don’t worry ka shirya gobe kaje gidan Alhaji Zubairu kaga yarinyar wajansa Fatymerh” kallonsa ya mayar kan Jalal yace “ina magana kai baka ce komai ba,ko kuma auren ne baka shirya yinsa ba?” Girgiza kai Jalal yay kafin ya fesar da numfashi idanunsa a kan Jalilerh wacce kanta yake a ƙasa tana cakalkala abincin gabanta yace “Jafar fa?” Murmushi Abbou yay yace “kada ka damu gobe za nemesa,yay hqr ya janye maganar auran baby kai zaka AURETA” da sauri Jalilerh ta ɗaga kanta ta sauke ganinta a fuskar Jalal shima kallonta yayi da sauri kuma ta miƙe ta nufi upstairs tana rufe bakinta sbd kukan daya taho mata,da kallo gaba ɗaya suka bita banda Jalal daya sunkuyar da kansa yana jin kansa na sara masa ga wata azabar da mararsa ke masa,shima miƙewa yay ya nufi kitchen yana zuwa ya buɗe babban fridge ɗin yaga lemon da yawa guda goma ya ɗauka ya shiga matsesu cikin cup sai da ya gama sannan ya ɗan zuba ruwan zafi kaɗan tare da sanya lipton guda biyu,fita yay daga kitchen ɗin ya nufi part ɗinsa, Lamir yana fita daga cikin gidan kai tsaye gidan Mubarak cibo ya nufa a guest room suka zauna,bai jiran gaisuwar da Lamir yake masa ba yace “yaya² ka gama aikin naka?”dry Lamir yay sosai kafin yace “aini abu sai dai idan banyi niyya ba,kana tunanin haka kurum zanje wannan gidan ne,tuni na barba ɗa maganin kai na taƙaice maka a kan idanu abar ta fara tashi.
Dariya Mubarak Yahya cibo yay kana yace “ai karawa dani babu daɗi,tun kafin shi mun kara da manyansa basu ji daɗin,bare shi ƙaramin ƙwaro,yanzu ni kuma lokacin hutawa ta ne,zan zo ba masa idanu yayta min mata hotel² kamar ɗan taure” dry suka tun tsire da ita gaba ɗayansu,kafin Lamir yace “kaga kowa ba ƙaramin jarababbe Za’ai ba,kana ganin yanayinsa kaga….,”sai kuma ya sanya dry, Mubarak cibo yace “kaga hajiri ko?bari ni na ƙarasa maka tunda tsoro kake”da sauri Lamir ya girgiza kai kamar yana gaban kamar ƙaramin yaro yace “kai haba² ni zanji tsoron wata halitta a nan gidan duniya never badai ni ba,kawai wani abu ke ban mamaki”ya faɗa yana kallon cibo domin ,cibo ya tsaya da dryarsa yace “me kenan kuma,hope ba’a a ɓangaren mu yake ba?”numfashi ya fesar, kana yace “no ko ɗaya”yace “to mene?”Lamir yace “kasan cewa bamu kaɗai ke neman Jalal da sharri ba,bayanmu aƙwai wajan mutane guda uku,nayi nayi malam yay min bayanin suwaye amma yaƙi”shiru Mubarak cibo yay can kuma yace “to mene matsalar mu dashi?”Lamir na danna wayarsa yace “matsalar duk abinda zamu jefesa dashi na sharri kafin mu aikata sun riga mu,shi ne kawai”cibo yace “to a ganinka su waye?”Lamir yace “i have no idea,amma duk abinda kake tunanin yiwa Jalal sun riga,dan yadda suke jifansa da sharri yaci ace sunga bayansa yanzu”cibo yace “haka ne,zanje wajan nawa bokan naji daga bakinsa”sallama sukai kana yay cikin gidansa,shi kuma Lamir ya nufi gidansa.tunda yasha ruwan lipton ɗin wanda ya sakawa lemon ciki yay rufda ciki, yana jin wata kalar masifa wacce bai taɓa jin irinta ba,banda sarawa babu abinda kansa ke masa,ya watsa ruwa har babu adadi mai makon feelings ɗin daya keji ya lafa sai abin ya ƙara tsamari,banda zufa babu abinda yake karyo masa,ga wata harbawa da dick dinsay ke masa ta tsaya gam ko mutsi ba tayi,da yaga abun sauki ya shiga kiran sunayen Allah,yana ta tsintiri daga bedroom ɗinsa zuwa parlour,idan yace zai yi sallah a haka tabbas zaiyi rafkanwa domin shi kaɗan yasan abin ya keji a cikin jikinsa, idanunsa sunyi jajir sun ƙanƙance,idanunsa biyu har akai kiran sallar farko,kana ya lallaɓa a hankali ya shiga bathroom, ɗan ƙaramin boxer’n daya saka ya zare yaga duk farin abu ya ɓata wandon,cillashi yay cikin warshing machine kana ya sakarwa kansa shower yana yi yana matsa mararsa a haka har Allah ya taimeksa ya samu sauƙi kaɗan kuma ta saki,alwala ya ɗaura tare da fitowa daga cikin bathroom ɗin sanye da towel,a ɗan gurguje ya shirya ya saka jallabiya ash kana ya ɗaura hirami, prayer mat ya ɗauka tare da fita daga cikin bedroom ɗin,a parlour ya tsaya ya data raka’atul firjir,ya daɗe yana azkar da addu’a akan Allah ya sassauta masa abinda ya keji akan sabun lamarin daya kunnu masa a lokacin dai baiyi tsammanin haka ba,masjeed ya nufa sai da suka zauna zaman jira kasancewar da wuri suke zuwa,bayan ya sallame ya tsaya yay karatu,bai shigo cikin gida ba Sai wajan 7 na safe,yana zuwa ya shige kitchen Laure ya samu tana haɗa breakfast da sauri ta zube ta shiga gaisheta,da ƙyar ya amsa mata,bisa dole yace ta zuba masa ruwan zafi a cup ta matsa masa lemon ta sanya lipton guda biyu,yadda yace haka tai masa kana ta bashi cup ɗin wanda tasa spoon a ciki,a hankali ya dinga shan ruwan lipton ɗin,tun kafin ya gama shanye wa ya fara zufa remote ya ɗauka ya ƙaro gudun a.c,kana ya ajjiye cup ɗin, miƙewa yay saman 3seater cikin ƙaramin lokacin bacci yay gaba da shi,kasancewar kuma weekend yasa babu wanda ya fito daga cikin part ɗinsa,wajan 10 na safe Jafar yay sallama ya shigo cikin parlour’n ganin babu kowa yasa ya ƙara so ciki,sosai yay mmkin ganin Jalal ƙwance yana bacci kamar ba shine ya gaya masa yau da wuri zai fita ba sbd gobe Sunday shine ranar da za’a rantsar da shi ba, ganin ƙafarsa ta zame yasa ya nufesa domin ya gyara masa ƙafar yana zuwa wajan yaga marar Jalal ta ɗaga sosai da sauri ya ɗauke idanunsa,kana ya gyara masa kwanciya shi kuma ya nemi waje ya zauna,Laure ce ta fito ta fara shirya danning,ganin Jafar yasa tace “Barka da zuwa” Murmushi yay mata yace “yawwa yaya aiki?”tace “Allahamdulillah”yace “ma sha Allah” kallon Jafar tai sai kuma ta kalli Jalal wanda yake bacci yana fidda numfashi a hankali tace “ko za’a haɗa maka breakfast ne?” Girgiza kai yayi yace “no bari zuwa anjima,nima wajan Abbou nazo ai” miƙewa tare da faɗin “ai ina jin yanzo mutum gidan zaso fito” bai ce mata komai ba sai wayarsa daya ɗauko ya fara dannawa,yana nan a zaune Mameey ta sauko daga upstairs da sauri,tana sanye da green ɗin atamfa ɗinkin riga da zaki sunyi mata ƙyau sosai,a ɗan gurguje ta nufi kitchen tsayawa tayi sbd ganin Jafar zaune yana danna waya tace “a’a Jafar zuwan yaushe?kazo duk muna ƙwance” Murmushi yay mata tare da rusunawa yace “ina ƙwana Mameey?”tace “Allahamdulillah,ya maman taka”yace “tana lfy,tace ai gaidaki Sai gobe idan tazo”Mameey tana murmushin jin daɗi tace “to ma sha Allah, Allah ya nuna mana gobee”yace “Ameen” kallon danning sai kuma ta kallesa tace “mai makon ka sanya Laure ta haɗa maka breakfast”Murmushi kawai yay kafin yace “daman Abbou yace nazo yana son gani na”kafin Mameey tai magana Abbou ya sauko cikin wani boyal milk tare da babbar riga sai zabga ƙamshi yake,idan ka gansa ba zaka taɓa yadda shine ya ajjiye manyan masari irin su Jalal ba, fuskarsa cike da Murmushi ya ƙara so cikin parlour’n tare da neman kujera ya zauna, idanunsa a kan Jalal domin tunda yake mai taɓa ganinsa yay bacci a parlour ba,kallon Jafar yay yace “wannan kuma lafiya?”Jafar ya durƙosa yace “haka na taddashi Abbou”jinjina kai kawai Abbou yay, Jafar kuma yace “ina ƙwana Abbou?” Abbou ya shafa kan Jafar yace “Allahamdulillah,ya Abban Maman taka?”Jafar yace “tace a gaidaku” gyara zama Abbou yay yace “zauna mana Jafar” a kunyace Jafar ya miƙe ya zauna,domin idan ya tuna Abbou ya kusa zama sirikinsa Wata kunyace take kamasa,wata rana har Jalal kunyarsa yake, Abbou ne ya tattara nutsuwar sa yace “Muhammad Jafar bani hankalinka nan”haka nan yaji gaban sa ya faɗi kansa dai a ƙasa yana sauraran abinda Abbou zai ce masa,kallon Jafar shima Abbou yake kafin yace “nasan kana da hankali,kana da ilimi both sides arabi da boko right? Kuma kasan muhimmanci ƙaddara da kuma wasiyya,alfarma zan nema a wajanka Jafar,ina neman alfarma ka janye maganar auran baby,bawai dan baka cancanci a aura maka ita ba, a’a kana da nagartar sa dukkan wani uba zai so haɗaka da ɗiyarsa,amma dole ce ta sanya nace maka haka,sbd wasiyyar mahaifiyarta ce haka,kuma kusan a akan wannan wasiyyar da kuma burinta komai ya lalace,ta riga ta faɗa tun kafin numfashinta na ƙarshe ya fita a kan tana buƙatar haɗa auran Jalal da Nihila,Nima na shiga tashin hankali da ruɗu sbd Jalal da kansa ya zaɓa maka Nihila matsayin mata,ba komai yasa yay hakan ba sai nagartarka da kuma jajir cewarka,dan Allah a matsayina na uba a wajan Jalal da kuma uba a wajan kayi hqr ka janye maganar auran baby,na maka al’ƙawarin duk yarinyar nan da kakeso zan tsaya maka wajan ganin ka sameta”tunda ya fara magana Jafar yake kallon Abbou,kasa cewa komai yay tunaninsa gaba ɗaya ya tsaya,wani shocked ya shiga wanda bai taɓa shiga irinsa ba,ya hqr da baby?ya janye maganar aurata?ko wannan dalilin ya sanya baby ta sauya masa? Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un,yaya zai yi da zuciyarsa yanzu?tayaya zai cire son Nihila?wacce mace zai samu wacce zartai replaced ɗinta a zuciyarsa?runtsa idanunsa yay da ƙarfi yana jin duniyar na juya masa,gaba ɗaya ya rasa amsar da zai bawa Abbou daya tattaro wata maganar zai faɗa sai ta ƙwance masa, Mameey ce ta zauna kusa da Abbou tace “kayi hqr Jafar,munsan cewa bamu ƙyauta ba,kuma zaka dinga kallonmu a masu son kansu ko ƴar ƴarn su,dakai da Jalal duk ɗaya kuke garemu babu bambanci,amma damu dakai dashi kansa Jalal ɗin babu yadda muka iya,shi kansa ba’a son ransa ba,amma mahaifiyar yarinyar ita ta buƙaci haka da kanta,kuma bamuyi haka da cin ZARAFIn ka ba”kansa ya shiga girgiza wa kafin a hankali ya shiga faɗin “babu komai Abbou,dani da Jalal duk ɗaya ne,zan iya mallakasa masa abinda na mallaka kamar yadda nake da tabbacin zai iya mallaka min abinda yake dashi koda ban nema ba,kuma daman Ubangiji ya ƙaddara ba matata mace,matar mutum kabarinsa, Allah yasa albarka ya masu zama lafiya da zuri’a masu albarka”gaba ɗaya suka amsa da “ameen”kana Abbou ya ɗura da faɗin “Nagode sosai Jafar, Allah yay maka albarka kaima ya haɗaka da mace ta gari wacce tafi baby”kasa amsawa yay sai mikeway da yay zai fita Mameey tace “a’a ka tsaya kayi breakfast mana”girgiza kai yay yace “I’m not hungry Mameey,zanje daman unguwa ne shine na fara zuwa nan,bari naje sai goben”Mameey tace “to Allah ya tsaye kuma ya kaimu goben”da Ameen ya amsa bai tsaya jin abinda zasu ƙara faɗa ba ya fita,tunda gabar gidan yake zagaye a motarsa yay tunani harya gaji yama rasa wacce mafita zai sabawa kansa,bai taɓa tunanin abin zai kasance ba,ya gama sakar jiki zai mallaki baby ashe Abun na haka yake ba,daman ance matar mutum kabarinsa, Jalilerh kam abun Duniya yake mata zafi idan ta tuna maganar Abbou cewa Aryan ne zai aure ta hankalinta tashi yake,gefe na zuciyarta ga wani sabon abinda ta keji game da Uncle ɗinta,yanzo haka bata taɓa yarda ta haɗu dashi,duk sanda ta ganshi gabanta ya dinga faɗuwa kenan,ta rasa nutsuwar ta,hankalin ta ya tashi,musamman shima idan ta tuna baby zai aura,takan shiga ɗaki taita kuka kamar ranta zai fita,Birnin nufar Jabir ne akan tattausan carpet sai Zulfa dake ƙwance ya ɗura kanta saman cinyarsa yana ta mata addu’a,sai ihu take tana zabura take kiran sunan Hubby,tunda suke da ita banda lokacin da bakinta ya buɗe tace sunanta Zulfa,babu abinda take iya faɗa sai ya jabbaru ya rahamanu,sai kuma yau da bakinta ya fara furta Hubby,yasan hakan na nufin bai yanar abu da dama,kuma kullum cikin addu’a yake,abu guda ke damunsa,yadda zata ɗauki teddy ta rungome tai ta kuka ko kuma tace zata fito da brest ɗin ta ta bashi,sai kuma yawan jinin da take zubarwa ga wani zazzafan zazzaɓi dake damunta kullum, lokacin da yaji labarin zaɓen su Jalal da kuma samun nasarar sa sosai yay murna, Abba Papa ya ƙwance wayarsa koda wasa yaƙi bashi bai son kuma dalilin hakan ba, ɓangaren Papa kuma uwa sundu ce ta sanya shi yin haka,ya rasa yaya zai yi idan yace zashi Ibadan ba lalle ya samu ganawa da Jalal ba, musamman yanzu daya samu babban matsayi ganinsa zai wahala,idan kuma ya tafi wa zai barwa Zulfa, Papa ya hana kowa zuwa inda take bare har yay tunanin bada riƙon ta zuwa wajan wani har yaje ya dawo,hatta Katarina Papa ya hanata zuwa wajan Zulfa,shi yake mata komai,dalilin hakan yaso Papa ya sahale masa auran Zulfa,amma yaƙi,yana jin baƙin cikin yadda yake samun kusanci da ita,amma yasan bashi da nufi tunda taimako yaya kuma baiyi da wata niyyar ba, Joshua ne zaune gaban Uwa sundu tana sauraran abin yake faɗa, “Allah ya taimaki Uwa sundu, Uwar mu maganin kukanmu,kiyi min izini naje neman wancan yaron da kaina,nasan zuwa yanzu ya girma,shekara wajan huɗu ai ba wasa bace,na gaji gashi har watan haɗa aure ya kusa kamawa”dry Uwa sundu ta ƙyaƙyace da ita,sai da tayi mai isar ta kafin tace “wannan aiki nane,na kira aljanun da suka shiga jikinta domin su azallata ta dawo garemu,amma sun ƙasa sbd wahalar da wanda take tare dashi yake bata,shiyasa nima na fara lalata masa tasa rayuwar ta hanyar amfani da mazantakarsa,amma maganarka ta sanya naji ina son tura mata da wasu baƙaƙen ALJANU wanda zasu tunzaruta su ɗaga mata hankali taji babu inda take son zuwa sai wannan birnin nawa,a kuma lokacin zamu samu damar haɗaka da ita domin ka amshi budurcinta.dukkan abinda aka sanya rana babu shakka zaizo sai dai idan ba’a sanya masa ba,kamar yau Deen yaci zaɓe gashi yau ake shirin rantsar dashi a matsayin Governor Ibadan,harabar gidan gwamnatin cike da dubban jama’a baƙi da kuma na cikin garin,kowa ka gani yasha sabbin kaya,wasu ma kallar tutar jam’iyyar suka sanya a jikinsu,su Abbou suna can cikin bayan baƙi kowa yasha ado cikin sabbin kaya masu tsadar gske, Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo kowa yana zana saman wata lafiyayyiyar kujera,gabansa da bayansa wasu sabbin securities kuma manya wanda gwamnatin garin ta turosu,sanye yake cikin wata jumper fara tass mai manyan zane, ya ɗura wata baƙar hula a saman sumarsa,ga farin bluetooth daya maƙala cikin kunnansa,yay wani ƙyau na musamman,amma ya faɗa idanunsa sun janye sbd masifar daya tsinci kansa ciki, yanzu haka ma azumi yake,taro yay taro baka ganin komai sai securities da ƙarar jiniya,su Mameey na can ɓangaren manyan baƙi na mata ita da Nihila wacce tasha ado cikin wani Maroon ɗin lace, Jalilerh kama cewa bata jin daɗi, Jalal bai san bata zo wajan ba, a hankali Jalal ya miƙe tsaye sbd umarnin da Cheap joji ya bashi,kana ya riƙe Alkur’anin a aka mashi,cikin harshen turanci Cheap joji ya umarce Jalal ya dinga maimaita abinda zai faɗa,tsaiwarsa ya gyara tare da lumshe idanunsa yana fesar da iska ta cikin bakinsa,kafin ya ware idanunsa ya sauke saman dubban jama’ar da suke sauraransa, idanunsa ya mayar ya rufe kafin ya buɗe bakinsa cikin wani wata iriyar murya mai daɗin sauraran ji yace “Ni Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo nayi al’ƙawarin kare haƙƙin al’ummar da kuma kula da dokiyoyinsu cikin yadda da aminci,na rantse da Alkur’ani mai girma zanyi aiki tsakani da Allah kamar yadda na ƙudiri niyyar yi, zanyi mulki cikin ja..ja.”,shiru yay sabida kasa faɗar kallamar da yay,a Cheap joji yay magana ba tare da kowa yaji mai yace bai ba,kallonsa Jalal sbd still kalmar bata zauna bakinsa ba,sai da Cheap joji ya ƙara faɗin JAJIRCEWA, lumshe idanunsa kana ya buɗe su ya saita bakinsa saman speaker yace…
*Nimcyluv*
Zanyi mulki cikin jajircewa da kuma zaƙwaƙuranci,nayi al’ƙawari da littafin Ubangiji cewa babu wani rai da zanci ZARAFI ko kuma na tauye masa haƙƙinsa,nayi al’ƙawari kuma zancika alfarmar Annabi da Kur’ani”gaba ɗaya wajan aka sanya tafi wasu kuma sukayi kabbara, lumshe idanunsa yay yana jin wani mai girma ya hau kansa,yasan rantsuwarsa bazai taɓa sanyawa yaci abinda yay al’ƙawari ba,sai dai kawai ya roƙi Ubangiji akan ya taimake sa,ya bashi ikon cika al’ƙawarin daya ɗauka akan talakawan sa, Cheap joji ne ya amshi Kur’ani ya miƙawa wani,kana ya rataya wa Jalal wani abu a wuya daga nan aka shiga ɗaukan photonan,gidan TV kuma suka shiga ɗaukan vedio,gidan redio kuma suka shiga ɗanar recording na abinda ake,bayan nan wajan bawa Jalal key ɗin office a tafi,sabbin securities,sabbin motocin,sabbin ma’aikata,sabon gida a cikin gidan gwamnati,sosai akai shagali,kana taro ya watse su Abbou suka dawo gida cike da farin ciki,hakama Jafar da ƴan Uku zana dawowa gida aka fara shirin dinner ɗin da Jafar ya shirya domin taya Jalal murna,sai dare za’a gabatar da dinner ɗin a babban event, shirye-shirye su Mameey suka fara, shigowar ta kenan ta samu Laure ita da Mama da kuma sauran mutane da suka zo tayasu murna,suna zaune sai cin abinci take, Mameey ta kalli Laure tace “Jalilerh ta sauko kowa?”Laure tace “wlh hajia bata sauko ba,sau biyu ina zuwa dubata sai naga ƙofar a rufe”kafin Mameey tai magana Mama tayi saurin faɗin “mu dai har yanzu bamu gama sanin zuciyar yarinyar nan ba,banda baƙin ciki yarinyar ƙirmishishi kije wannan taron nan amma ta murzawa idanunta toka, meye wannan da tayi?yaya sunansa? a’a wlh baƙin ciki kawai takewa Jalalu,yaro ɗan marayan Allah ya ɗauki rimi² domin gyara gobenki,amma ki watsa masa ƙasa a idonu,to Wlh nidai babu ruwana,idan ba baƙin ciki take gwamma musani tun yanzu ko ba haka ba?”Mameey tace “ayyya ba haka bace Mama,kinsan bata jin daɗi ne shiyasa”wani kallo taiwa Mameey sheƙeƙe kafin ta yatsuna fuskarta tace “au haba?” Mameey tace “eh wlh,sai amai take ga zazzaɓi” nama ta tura a bakinta kafin ta haɗiye da ƙyar tace “banda kema kin zama sallamammiya ina ke ina biyewa wannan Salamatu?wlh fita a idona tun tuni na rufe,yanzo dan waye ya kejin daɗi a wannan rayuwar ta yauma ta komu? to ai shikenan nan tunda kema kin zama sakarya,yarinya baƙin hali fal zuciya,ga shegu aljanu irin na gado kai ita dai abu goma da ashirin,bai laifi kuma tana da ƙyau abinta shiru² da ita gwanin sha’awa,to waya sani ko ƙyan ɗan maciji ne?”ita Mameey ba tace komai ba ganin abin na Mama ya fara zama shiririta yasa ta haura sama tana ƙunshe dryar dake cinta,da wani kallo Mama ta bita kafin ta juyo wajan wata ƙawarta tun ta yarinta tace “to ga ta nan dai Asabe,kinga tun daga haihuwar ƴan ukun nan shikenan haihuwar ya tsaya,kila juya da Za’ai sai Allah ya taimaka” tsohuwar da aka kira da Asabe ta ajjiye ƙashin da take ta faman tsotsa tace “na sai wani kallon tara saura take mana ai..” Mama ta miƙe tsaye tace “a’a wlh kedai anyi natsoraciya,me yasa baki gayan ba sai da ta tafi,nidai banji daɗi ba,meye nata da zata yi maki harara?bayan itama aurota a kai,ai anjima ƴan uwanta zaso sauka akan su zan rama maki” haka dai sukaci gaba da surutai irin nasu na rikitattun tsofaffi,kafin su sanya Laure ta kawo masu farfesun kan ragon da akai, Mameey na shiga part ɗin su Jalilerh ta tura ƙofar a hankali,a ƙwance ta sameta ta kifa kanta cikin pillow tana sauke ajjiyar zuciya,jin alamun mutun yasa tayi saurin ɓoye photon Jalal dake hannunta,kana tai lamo kamar mai bacci, ƙarasawa cikin bedroom ɗin Mameey tayi tace “daughter har yanzo jikin ne?”shiru Jalilerh tai mata tai kamar bacci take, ganin haka yasa Mameey taja mata ƙofar ta,tana fita Jalilerh ta sauke ajjiyar zuciya tare da lumshe idanunta wasu hawaye Masu zafi suka shiga fita daga cikin idanunta,a hankali kuma ta zaro photon Jalal wanda ta ɓoye a ƙasan pillow,gaba ɗaya a ɗan kwanakin nan ta rasa mene yake damuwa da ita,bata da aiki sai tunaninsa,a duk sanda kuma akai maganar sai yaji zuciyarta ya buga da ƙarfi,kullum cikin damuwa take,duk sanda ta matsa zuciyarta domin ta gane abinda yake damunta da kuma abinda ta keso,sai taji zuciyarta kamar zata fito waje,abu ɗaya yake sanyawa taji daɗi idan taga photon Jalal, zuciyarta nayin daɗi taji damuwarta ta yaye,tana nan ƙwance lamo har Nihila ta shigo, da sauri ta ɓoye photon tare da lumshe idanunta,kallonta Nihila tai sai kuma ta taɓe bakinta ta nufi cikin bathroom domin sake sabon wanka,sai wajan biyar na yamma sannan motocin Jalal dana securities ɗinsa sukai parking a harabar gidan, buɗe masa ƙofa akai ya fito yana tafe yana baza babbar rigar jikinsa yana ɗan haɗe ƙafafuwan sa,kansa a ƙasa bai yadda sun haɗa idanu da kowa ba,a main parlour ya samu Mama da wasu tsofaffi,kamar bazai magana ba sai kuma yace “sannunku” Mama take faman jan dafaffiyar ganda tace “mene kuma sannu?a gadon asibiti ka ganmu?ko kuma labari ka samu bamu da lafiya? a’a wlh wannan ai gaisuwar raini ce,meye sannu ana zaman lafiya,kama rasa a ina zakimin wulaƙanci sai gaban ƙawaye ne?to uwarka salamutu ita kaiwa bamu ba”Asabe ce tai saurin zungurar Mama tace “a’a wlh babu ruwana yanzu saiya saka a kullemu a bayan sel babu ruwansa,ba gwamna bane?” Shiru Mama tai tana rarraba idanu tace “to me nace kuma? Allah ya baka hqr kada ka ƙullace ni faɗa na nema ba”girgiza kai kawai yay yana shigewa cikin part ɗinsa,yana barin wajan Mama tai ƙasa da Murya tace “yanzu Asabe duk yadda muke da Jalalu sai ya saka a kamani?kinga fa nina haifi uwarsa,uwarsa kuma ta haifesa ai na huce cin mutuncin a wajansa” Asabe tace “kedai bar yaran zamani,yooo ko uwarsa tayi ba dai-dai baya kulleta ba,bare ke kakarsa, Gwamna fa akace maki ba kansila ba”shiru Mama tayi kafin tace “to dai Allah ya basa hqr,Ni banyi da wata manufar ba wlh”Jalal na shiga part ɗinsa ya shiga zame kayan jikinsa na ajjiye su cikin wardrobe a wani side na datti clothes,ya rage daga shi sai boxer,wajan fridge ya ƙarasa ya ɗauki malt, harya juya sai kuma ya koma ya ajjiye sbd tunawa da azumin da yake, parlour ya dawo ya zauna tare da miƙar da ƙafafuwansa,lumshe idanunsa yay lokacin da sanyin a.c ɗin ya rasa cikin saman farar fatarsa, hannunsa yasa ya ɗauki remote kana ya kunna cenema ɗin dake ɗakin, series ɗin Joda &Akbar wanda ake haskawa a zee world,idan kagansa zaka ɗauka da gaske kallon yake, amma a zahirance tunani ne fal cikin zuciyarsa,ya rasa me yake damunsa,duk iya kacan rayuwarsa bai taɓa jin sha’awar kasan cewa da mace ba,bai taɓa damuwa da zama da mace a matsayin mata ba,sbd abinda ake so a auran shi kuma bashi da lafiyar yinsa,tunda yake sha’awa bata taɓa damunsa, sai dai yaji Jafar na faɗa, kasancewar shine kaɗai abokinsa,kuma amininsa bashi da wani sama dashi,amma gashi yau shine yake son kasacewa da mace, yasubuhanallah! Wannan wanne irin abune ya samesa?wacce kalar masifa face haka? kumshe idanunsa yay yana taune lips ɗinsa,yana nan zaune har lokacin magrib ya kusanto,tashi yayi tare da kashe kallon ya nufi cikin bedroom ɗinsa,yana shiga ya huce bathroom ya sakarwa kansa shower,wanka sosai yay tare da ɗaura alwala, fitowa yay sanye da bathrobe a jikinsa,wajan dressing mirror ya tsaya,ya shiga gyara jikinsa sai da ya gama shafa lotion mai ɗan ƙamshi kana ya fesa parfume,comp ya ɗauka ya gyara sumar kansa ta kwanta sosai gwanin sha’awa,ganin yana da sauran lokaci kafin dinner ɗin yasa ya ɗauki farar jallabiya mai ƙyau kuma mai ƙaramin hannu, Wannan ko hiramin da yake sanyawa bai sa ba,haka ya fita daga part ɗinsa yana zabga ƙamshi,a parlour’n ya tarar da Abbou da ƴan uku,kallon parlour’n yay yaga tsaf sai ƙamshi yake a juna borner turare na fita ta cikinta kamar ba wanda su Mama sukaiwa kaca-kaca,kansa a ƙasa ba tare kuma da yay magana ba yabi bayan Abbou ganin yay gaba,suma ƴan uwansa suka mara masu baya,suna zuwa Masallaci Jalal ya tsaya sahun farko mai makon ya ƙarasa wajan da yake tsaiyawa wanda aka tana da domin liman,kallonsa kawai Abbou har zai magana sai kuma ya fasa,wanda yay magana har wani magidancin mutum yazo wajan ya tada sallah,bayan an idar da Sallah kowa ya ƙara taya Jalal murna tare sayi masa addu’a na tsari da kuma fatan alkairi,murmushin dole yake yana amsawa da “Ameen” bai tsaya karatun da yake masu ba yace suyi masa uzuri,suma basu takurasa ba haka ya tsallake su Abbou ya nufi cikin gida,a parlour ya samu Mameey tana ganinsa ta saki Murmushi tace “ur excellence Barka da shan ruwa” ɗan kwaɓe fuska yay ba tare kuma da yace komai ba, Murmushi ta ƙarayi tace “yanzu na kammala yi maka abun buɗe baki,nan zaka tsaya ko part ɗin ka za’a kawo maka?”girgiza kai yay yace “no bada a kawo min” tace “okey!amma baby bata nan,wai taje makeup ne, nace ta bari na kira har gida ai mata daga nan aiwa daughter amma tace a’a”lumshe idanunsa yay kafin ya buɗe yace “no wahala,bawa wacce kike magana ta kawo min” kallonsa tai tace “wa kenan?” Ɗan juya idanunsa yay sbd ciwon da mararsa take masa kafin ya fesar da numfashi yace “ina ba baby ce ɗaya a gidan ba?”Murmushi kawai tai masa kafin tace “daughter bata ta jin daɗi,domin ko dinner tace ba zata ba,kuma yanzo tailor ya kawo masa ɗinkin su”juyawa yay bai ƙara magana ba,har yaje ƙarshe ya tsaya yace “ki bata ta kawo min” yana faɗin haka ya shige cikin part ɗinsa, Mameey upstairs ta haura tana zuwa ta shige part ɗin su Nihila,a a zaune ta sameta tana goge dugun gashin kanta,da alama fitowar ta daga wanka kenan, kallonta kawai Mameey keyi tana mamakin tsarin halitta mai ƙyau da ɗaukan hankali irin na Jalilerh,ko ita da take babba baza ta taɓa nuna mata hips mai ƙyau da girman brest ba, komai nata mai ƙyau ne,ganin yadda take abu a sanyaye yasa ta ƙarasa wajanta tare da amsar handrayer ɗin,da sauri ta juya sbd tsoran da taji, ajjiyar zuciya ta sauke tare da sunkuyar da kanta kuma bai tace komai ba, Murmushi Mameey tayi wanda ya zame mata jiki tace “tubarkallah,wannan gashin kamar ana ƙara masa tsayi halan ke bafulatana ce ko”shiru tayi tana ƙara sadda kanta ƙasa,sai da ta gama gyara mata gashin ta naɗesa kamar alƙaki,kana ta tace “maza shirya bobo na kiranki,kuma zaki tafi masa da abun buɗe baki,kin san azumi yayi” gabanta taji ya faɗi zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske, marai-raice fuska tayi tace “ayya Mameey kin kallo bana da lfy” wata duguwar riga mai ɗan santsi ta ɗauko mata tare da hijab tace “babu ruwana ni,idan baki jeba ki tanadi amsar bashi”tana faɗin hakan ta fita, Jalilerh kamar tai kuka haka ta shiga sanya rigar hawaye na bin fuskarta,bayan tasa rigar harta ɗauki parfume sai kuma ta ajjiye,hijab ɗin ta ɗauka tasa har ƙasa kana ta nufi waje ido duk hawaye sai tura baki take gaba,a hankali take sauka daga benen zuwa downstairs,tana zuwa ta samu Aryan zaune shida Jafar suna magana,gaba ɗaya kallonta sukai, Musamman Jafar rabon daya ganta harya manta,sosai yay mmkin girmanta ta zama cikakkiyar budurwa,ga wani sihirtaccen ƙyau mai ɗaukan hankali data ƙara, chocolate skin ɗinta sai sharning yake yaji mayoka masu ƙyau da tsada, lipstick ɗinta yay jajir kamar ta shafa jambaki, kanta a ƙasa ta nufi kitchen tana zuwa Laure tace “yawwa yanzu daman Hajiya ta gama shirya masa”Murmushi kawai taiwa Laure kana ta ɗauki tray tai waje, shira ta mesu sunayi nan ma bata kulasu ba tai side ɗin samarin gidan, zuciyarta na bugawa ta tura ƙofar parlour’n a hankali ta shiga, lumshe idanunta tayi sbd daddaɗan ƙamshin daya daki hancinta,murya can ƙasa tai sallama,amsa mata yay kana yaci gama da danna system ɗinsa yana matse cinyoyinsa,kamar wacce ƙwai ya fashewa ta fara tafiya zuwa inda yake,tana zuwa taja ƙaramin table ɗin gabansa ta ɗura babban tray ɗin a kai,juyawa tayi zata fita kamar daga sama taji muryarsa yace “nemi waje gida zauna”tsayawa tai kamar ba taji abinda yake cewa, zuciyarta banda lugude babu abinda take,sanin cewa bazai ƙara magana ba kuma bata da ikon fita yasa ta nemi waje kusa da ƙafafuwansa ta zauna saman carpet,tana ta shiga wasa ta yatsun hannunta,duk abinda take yana kula da ita yay banza da ita,tana nan zaune harya kammala abinda yake,kana ya kashe system ɗin bai kula ta ba ya fara buɗe warmers ɗin da aka zuzzuba abincin,sakwara ce da biyar Agushi,miyar tasha nakakƙen agushi,ganyen ugu,(ki wanke,ki yanka) Sai Alaiyahu sai kifi sukumbiya,Tafarnuwa,Attaruhu,Albasa kifi banda,Nama (soyayye)sai maggi, Curry, gishiri,kayan kamshi,manja da man gyaɗa,onga,sune kayan da akai amfani dasu wajan haɗa miyar,a hankali ya sanya yatsun hannunsa ya fara cin sakwarar guda biyu kawai yaci kana ya wanke hannayensa,tare da ɗaukan malt ya fara sha ko takan farfesun da akai masa da kuma dambun naman bai bi ba,yana shan malt ɗin ya ɗan kalleta Kafin ya ɗauke kai yace “zo nan”da sauri ta kallesa sai kuma ya sunkuyar da kanta ƙasa,hawayen daya gani ƙwance a cikin idanunta yasa ya kalleta kana ya Miƙe tsaye a hankali tare da ƙarasawa inda take zaune,yana zuwa ya sanya hannunsa gaba ɗaya ya ɗagota tsaye,kallonta yay tun daga sama har ƙasa,sosai red hijab ɗin yaywa baƙar fatarta ƙyau, lumshe idanunsa yay kafin ya buɗe su a kanta, Murya can ƙasa yace “meye kike kuka?”girgiza kai tayi hawaye na ƙara bin fuskarta, haɗe rai yay sosai kafin ya ƙara saita muryarsa yace “meye?ke dawa?wani abin ke maki ciwo?”kuka ne ya ƙwance mata hakan yasa ta saki kuka ta shiga rerawa kamar ranta zai fita, ƙasa hanata yay sai ajjiyar zuciya daya sauke,cikin sanyin jiki ya saka tattausan hannunsa ya jawota zuwa gabansa a hankali kuma ya sanya hannunsa ya shiga zare zumbulelen hijab ɗin data sanya,cillashi yay saman sofa, kallonta ya shigayi from head to toe,kama ya leƙa fuskarta cikin murya mai sanyi yace “gaya min mene?”kasa magana tai sai jikinsa data faɗa ta shiga rera kuka, lumshe idanunsa yay yana jin kukanta har tsakiyar kansa,jin kukan yay yawa yasa ya sanya hannunsa duka biyun ya rungome ta a jikinsa tare da ɗura kansa a shoulder ɗinta ya shiga sauke ajjiyar zuciya.
Sosai Jalilerh take kuka kamar ranta zai fita,koda wasa Jalal bai yi ƙoƙarin hanta kukan ba,sai ma bayanta da yake bubbugawa yana faɗin “cry.. cry..cry very well Jalery” ai kam kamar ya kunna ta sai da tayi mai isar ta sannan ta shiga sauke ajjiyar zuciya,a hankali ya zare ta daga jikinsa ya shiga kallon jikinta,lura da kallon da yake mata rasa ta fara ƙoƙarin neman inda ya sanya mata hijab ɗin ta, haɗe fuska yay tamkar bashi yake kallonta ba,hijab ta ɗauka zata saka yay calmly yace “kada ki sa”and meye kike ɓoye?tun kan kikai haka na sanki, about 3yrs to 4″turo baki tayi kamar zai tai kuka tace “to stop looking at me” taɓe yay tare da nufar wajan kujera ya zauna,tana nan tsaye bai kulata itama bata zauna ba, hannunta riƙe da hijab tana jujjuyawa, lumshe idanunsa kana ya buɗe ya saukesu a kanta, jikinta yabi da kallo kamar ya samu tv, sosai yake mmkin girmanta lokaci guda ko uwar mata sai haka,ga yanayin shap ɗin mai matuƙar ɗaukan hankali, kwaɓe fuska tai zatai kuka kafin tace “Uncle naje?”waro idanunsa yay wanda suka ɗan janye kafin ya sauke numfashi yace “waya tsaidaki?” Cikin shagwaɓa tace “no body” bai kalleta ba yaci gaba da kallon daya kunna na labaran BBC, juyawa tai zata fita yace “zo nan” kasa musa masa tayi hakan yasa ta nufi inda yake tana zuwa a ƙasan carpet wajan ƙafafuwansa, fuskarsa a haɗe ya zame daga saman kujerar murya chan ƙasa yace “Jalileeeehh” ji tai tsigar jikinta ta tashi zuciyarta ta buga da ƙarfi, runtsa idanunta tayi kasa amsa masa tayi sai ƙasa da tayi da kanta, tattausan hannunsa ya saka ya tallafo haɓarta ya kasance fuskarta tana da kusanci da tasa sosai, ƙara runtsa idanunta tayi sbd saukar numfashinsa da taji,kamar mai kuyan magana yace “me damunki?ba kije wajan taro ba,then yanzo kince baza kije wajan dinner ba,ko baki farin ciki da abinda na samu ne?”hawaye ne suka shiga zubuwa daga cikin idanunta ta shiga girgiza kanta, haɗe fuska yay yace “zaki daina kukan nan ko sai ranki ya ɓaci”saurin haɗiye kukan tai sai ajjiyar zcya da take saukewa, ƙara natsuwa yay kusa da ita yace “to gaya min” muryarta na rawa tace “I’m sacred Uncle” da mmki yake kwallon kafin yace “akan me?” Kuka ta fashe dashi tace “Uncle ban son auren nan dan Allah kace kada ai dani” Murmushi yay kafin yace “why” ƙansa tai da kanta tace “bawai bana son yaya Aryan bane,kawai bana son zama dashi,ni bashi nake so ba” idanunsa ya ɗauke yace “then go and tell Abbou” girgiza kai tayi tace “i can’t” taɓe baki yay kafin yace “ohh ni rainani kikai da kike gayamin yanzo?” Ƙara sautin kukanta tayi kafin tace “a’a Uncle,nasai kai ne kawai zaka fahimce ni,kace ni rayuwarka ce baby kuma ƴar uwarka ce,bazan manta da haka ba,tunda har zan zama rayuwarka kaga babu wanda ya dace yasan abinda yake damuna sama dakai” da idanu kawai yake kallonta kafin yace “to wa kikeso?” Kasa magana tai sai hannunta data shiga wasa dashi, hannayanta ya riƙe a hannunsa then yace “ina tambayarki?”wata kunya ce ta kamata da sauri ta kifa kanta a ƙirjinsa tana ɗan yin dry kaɗan, lumshe idanunsa yay yana jin mood ɗinsa na sauyawa wani a zababban feelings na neman zautar dashi,a hankali yasa hannunsa ya ƙara jawota jikinsa tare dasa hannu ya ware ribbon ɗin kanta ya shiga tura yatsuna cikin sumar kanta,kafin ya ɗura hancinsa ya fara shaƙar ƙamshin ta,kanta ta ɗaga ta shiga kallonsa shima kallonta yake kamar bai taɓa ganinta ba, idanunta ta ɗauke muryarta na rawa tace “Uncle baka da lafiya ne?meke damunka?” Fesar da numfashi yay kana ya copping face ɗinsu yace “so kike kisan meke damun Uncle ɗinki?”da sauri ta ɗaga kanta tana taune bakinta, Murmushi yay yace “ohhyaa open your mouth”batai tunanin komai ba ta buɗe bakinta, hancinsa ya ɗura saman bakinta yaji wani ƙamshi na fita, Murya can ƙasa yace “close your eyes”rufe idanunta tayi a hankali Jalal ya tura hannunsa cikin sumar kanta ta wajan wuyanta hakan yasa fuskarta ta ƙara mannewa da tasa, slowly ya sanya bakinsa cikin nata lokacin da ɗumin bakinsu ya haɗu gaba ɗaya suka sauke ajjiyar zuciya,cikin wani irin yanayi na rashi sabo, da kuma yanayi na buƙatuwa ya kama lips ɗinta ya shiga tsotsa yana lumshe idanunsa, da sauri ta buɗe idanunta tana kallonsa shima kallonta yay yana ci gaba da shan bakinta, lumshewa idanunta tayi hawayen cikinsu ya samu damar sakkowa,da ɗan zafi² ya kama tongue ɗinta ya fara bata wani hot kiss Jalilerh ƙasa ɗaure tai hakan yasa ta fara ƙoƙarin ƙwance bakinta jin kamar zai rabata da harshen ta, ganin abinda take shirin yi yasa yay saurin juyar da ita ta koma jikin kujerar shi kuma yay mata rumfa,da wani irin salo mai tafiya da tunanin wanda akewa Jalal yaci gaba sucking tongue ɗinta yana yi yana tura mata nasa tongue ɗin ko zatai accepting,har cikin ransa baya jin daɗin yadda abin yazo masa,bai kuma san lokacin da zuciya da gangar jiki ta ɗebe sa zuwa gare ta ba,bashi da wani option daya huce haka yana da tabbacin ita kawai zai iya raɓa ya samu sauƙin abinda ya keji,ko wacce akai masa Engagement bazai taɓa iya aikata mata haka,kawai zuciya tafi nutsuwa da Jalery, abubuwa daya keji gama da ita,suna da yawa yasan cewa bawai sonta yake irin so na aure ɗin nan ba,amma yana jinta a jinin jikinsa,ko abune ya sameta kafin a gaya masa jikinsa ya gama bashi, Jalilerh kam ganin abin take kamar amafarki, ƙasa mutsi tai sai Jalal da take kollo jin yana da fidda wani sexcy sounds, zuciyarta kuma banda lugude babu abinda take, tsoro da firgici sun gama cika mata zuciya tsoranta ɗaya kada wani ya shigo parlon ya gansu a haka, musamman Nihila wacce take shirin zama mata a garesa lokaci kawai ake jira,jin hannunsa ya shirin sauka a cikinta tai saurin riƙe hannunta tare da ƙwance bakinta, hannunsa yasa ya dafe kansa yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa ga wani irin azaba daya keji a mararsa,fesar da numfashi yay mai zafi tare da ɗaga idanunsa ya sauke a kanta,kasa daure kwallon da yake mata tayi jikinsa ta faɗa ta sakar masa wani kuka wanda kai tsaye bazai iya fassara kukan nata ba,sai da tayi mai isar ta taji bai kulata ba, ɗagowa tayi ta kallesa taga still ita yake kallo idanunsa sun kaɗa sunyi jajirr, muryarta na rawa tace “Uncle why?”kasa magana yay sai kallonta kawai da yake,kamar daga sama kuma taji yace “ɗaga ni” zamewa tayi daga jikinsa hawaye na bin fuskarta,tana ɗaga shi,ya saci kallonta ganin kanta a ƙasa yasa yay saurin miƙewa tare da nufar bedroom ɗinsa sbd bai son taga yadda mararsa ta miƙe,ta daɗe a zaune kafin ta miƙe tsaye jiki a sanyaye ta kwashi warmers ɗin tayi tare da fita daga part ɗin,a parlour ta samu Nihila wacce dawowarta kenan daga wajan makeup,tana zaune saman sofa tana latsa wayarta,tana sanye da wani blue ɗin lace tayi ƙyau sosai,kallon juna sukai ba tare da kowa yace wani abu,daman ita Jalilerh magana bai dameta ko waye kai sai tai niyyar magana zatai, harta shige kitchen ɗin idanun Nihila na kanta,sosai tai mmkin abinda take a sides ɗin samarin gidan kuma tana da tabbacin part ɗin Jalal taje,tana wannan tunanin Mameey ta sakko dwonstrais tasha ado cikin wata atamfa Holand mai ƙyau,ganin Nihila yasa tace “a’a masha Allah baby, kinga yadda kikai ƙyau kowa?eyeee duk kwaliyyar nan ta bobo ce?”Murmushi baby tayi tace “Mameey ina yaya Aryan ne?” Mameey tace “yaje airport jirginsu Anuty ya sauka,yanzu haka ma suna hanya”miƙewa baby tayi tace “wow can wait to see matar yaya Irfan Anuty Ikram” Mameey tace “ai kam suna hanya, Jalal ya fito kowa? We getting late” girgiza kai tayi tace “bana jin ya fito,coz yanzu naga Jalilerh ta fito daga part ɗin sa”waro idanu Mameey tayi tace “sai yanzu ta fito?”sai kuma ta saki Murmushi tace “ok jeki ce masa duk an tafi wajan dinner shi ake jira”kamar jira take tace “ok Mameey” tana faɗin hakan ta nufi part ɗinsa, Jalilerh tana sane taƙi fitowa daga kitchen ɗin gani take kowa zai iya gane abinda Uncle ɗinta yay mata yau,tana zaune saman kujera taja idanunta ta lumshe,sai a lokacin taji tsigar jikinta na tashi musamman idan ta tuna lokacin daya sanya bakinsa cikin nata,takurewa tai a saman kujerar ta shiga sauke ajjiyar zuciya,a ƙwance Nihila ta samesa yay rufda ciki yana fitar da numfashi a hankali, wato bacci yake nan?ta tambaya a ranta,shine ya sanya tana ta Knocking bai magana ba, ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin tayi tare da bubbuga gefen kanta,shiru yay mata duk da cewa yana jinta amma yay pretending kamar bacci yake, leƙa fuskarsa tayi aikam kamar ance ya buɗe idanunsa nan suka haɗa ido, kallonta kawai yay na ɗan wani lokaci kana ya janye idanunsa daga gare ta,magana ta fara while idanunta na kansa tace “we getting late bobo, Mameey tace ka tashi ka shirya”banza yay mata sai data ƙara magana yace “to bazani ba”zaro ido tayi waje kafin tace “kamar ya?,bobo dinner ɗinka ce fa”haɗe rai sosai kana yace “kee get out,idan zaki adawo lfy nace bazani”fita tai da sauri idanunta cike da hawaye, Mameey na ganinta tace “Mameey wai ba zashi ba”Mameey tace “kamar ya kenan?”baby tace “haka dai yace min,kuma hadda kuruni ai da Jalilerh ce bazai kurota ba”miƙewa Mameey tai tace “ya isa,ban son magana irin wanann, just wait for me”tana faɗin hakan tai part ɗinsa tsayawa tai sbd ganin ƙofar a rufe, Knocking ta shigayi amma akai mata banza,dole yasa ta hqr ta juya abinta, parlour ta dawo a nan ta samu Nihila tsaye idanunta cike da hawaye,tana ganinta tace “wayata na sama,kiramin Irfan” babu musu tai dailing number da aka sawa sweet bro,yana picking ta bawa Mameey,daga chan Irfan yace “en mata kun ƙarasu ne?” Mameey tace “a’a wanann uwar mata ce, Jalal bazai zo ba,but kada ka gayawa kowa har Jafar ɗin sbd kada yaji babu daɗi,idan aka shiru a tashi daga nan Jafar nasan zai zo nida kai na zan masa bayani”Irfan kamar zai kuka yace “but Mameey…,” Da sauri Mameey tace “don’t question me Irfan” da sauri yace “ok I’m sorry” kashe wayar tayi sannan ta kalli Laure dake shiga kitchen tace “ki cewa ta kitchen ɗin nan kada nazo na sameta ciki”da sauri Laure tace “to Hajiya” ana kiran sallar issha’i Aryan yay sallama shida su Ikram da Anty Sajida da kuma Firdausi sai wasu twisn guda biyu duk mata shekarunsu bazai huce 3 ba,sosai sukai murna da ganin ƴar uwar tasu,Anuty Sajida yayace a wajan Mameey, Firdausi kuma ƙanwa, Ikram kuma ƴar gidan Anty Sajida ce wacce Irfan ya keso, twins ɗin kuma yaran Firdausi ne,da gudu baby ta fito tama manta abinda bobo yay mata,tana zuwa ta faɗa jikin Anty Sajida rabonta da ita tun sau ɗaya da da Mameey taje da ita tana ƙarama, buɗe ido Anty Sajida tayi tace “Hajiya Salmerh don’t tell me baby ce wannan,wow ma sha Allah”dry Mameey tayi tace “wlh fa gata nan tana shirin Aure”Anty Sajida tace “kai kice munzo a dai²?” Firdausi ce tai Murmushi tace “Allah dai ya jiƙan Mummy” gaba ɗaya suka amsa da ameen, ƙamshi da kuma alamun tafiyar da sukaji yasa gaba ɗaya sukai kai dubansu zuwa upstairs,a hankali Jalilerh ke sakkowa kanta ƙasa,ta sanya zumbulelen hijab har ƙasa wanda ya kance blue sai fararen idanunta da take juya,ga jajeyen lips ɗinta da suke ta ƙyalli, Firdausi ce tace “tubarkallah bisimillah,ma sha Allah, Anty wannan kyakkyawar fa?kai gsky na daɗe banga beauty irinta ba”Anty Sajida ce tace “Jalilerh right?”Mameey tace “eh kam kin ganeta kenan?” Anuty Sajida tace”gsky ta huce tunani na,hatta ɓakar fata wlh banga mai ƙyan nata ba,ko fari bazai nuna mata ƙyau ba,gashi Hajia Salmerh tana shirin kamaki a halitta” dry sukai Mameey tace “ai tubarkallah ni kina mmkin girman daughter nake,nan fa baby ta girmeta amma Yanzu bata goye baby a baya ba” Firdausi tace “itace wacce Aryan zai aura ko? gsky na tayashi murna ya samu baƙar balarabiya” ita dai tana jinsu bata iya cewa komai ba,sai da taji sun ambaci Aryan sannan ta ɗaga kai aikam ido biyu sukai tashi yana zaune saman kujera ya harɗe hannayensa yana aika mata da wani irin kallo, zamewa tayi a ƙasa cikin ƙaramar muryarta tace “Fatan kun sauka lfy?”gaba ɗaya suka amsa da lfy lou,baki baby ta taɓe kama da haura upstairs, Mameey kuma taja su Anty Sajida zuwa inda zasu sauka, parlour ya rage daga Jalilerh sai Aryan, miƙewa yay tare ƙarasawa inda take zaunan yana zuwa ya ɗuka wajanta yace “meyake faruwa dake ne?”shiru tai masa ba tace komai ba,cije lips ɗinsa yayi yace “ok tashi kije”kamar jira take ta miƙe da sauri tare dayin upstairs ne,iska ya fesar daga cikin bakinsa kafin ya juya ya nufi part ɗinsa zuciyarsa duk babu daɗi, Mama daman tunda taja Asabe ɗakinta tace “yi zamanki a nan,bayan ɗan naki gantalalle ne,yooo banda sallamamme ne tayaya zai zuba ido matarsa tana hulaƙantaki?Keba uwarsa bace?bazan manta ba a haihuwarsa har kusa makancewa kikai sbd wahala,wata rana da kwana tara yana cikin amma dake bashi da liffasi yake bari ana maki haka, a’a dama can dai ba’a san zuciyarsa ba”Asabe tace “kuma kuɗi garesa”a fusace Mama tace “uban me kuɗin nasa ya amfana maki Asabe?kina dai kallo jibi zamu koma gidan gwamnati, sabon gida da motoci da masu tsaro haka aka bawa Muhammad,haba² ai Allah ya ƙara Annabi daraja,shifa jikane a wajena amma ba kiga yadda ya kemin ba,nidai abinda na keso dake kiyi zamanki nan sai ya nemeki,kee ko nan yazo zance masa kawai kin mutu ko?”zaro ido Asabe tayi tace “mutuwa kuma?a’a adai sauya haka nan kuma nazo na mutum?”dry Mama tace “taje ji ido?kai Asabe har yau kina nan da tsoran mutuwa”daga nan kuma suka ɗura da hira suna zaune Mama tasa Laure ta cika mata ƙatuwar warmer da soyayyan naman rago,ga dafaffiyar ganda,ga farfesun kifi,haka suka cika ɗakin da nama sai ci suke,a nan sukai sallar magrib da issha’i a nan kuma bacci ya ɗauke su. Washegari da yamma Jalal da Abbou suna zaune suna maganar yadda za’a koma gidan gwamnati gaba ɗayansu, shi kuma Abbou yace a’a ya koma shi ɗaya sai baby idan an ɗaura masu aure,tunda gaba ɗaya auren saura kwana biyu,kamar daga sama suka fara jiyo ihun Jalilerh, miƙewa sukai a tare,chan kuma sukaji ta ƙara fasa wani ihun ai Jalal bai tsaya Abbou ya bashi umarni ba ya ruga da gudu zuwa upstairs,a hanya sukaci karo da ita daga ita sai wata ƙaramar riga idanunta a rufe bakinta sai kumfa yake fitarwa,tana ganinsa tayi kansa da gudu. ⁹⁸ ⁹⁹