WANI AURE CHAPTER 30

WANI AURE






CHAPTER 30






Ki Ki daina furta kalmar mutuwa nan nablah addu’a kawai shine mafuta .
zeenat wacce gabadaya tagama rudewa sbd ganin halin da nablah take ciki tasoma zariya a dakin tana Kai kawo da furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun.
A rude ummi tace kamamin ita zeenat mukaita dakin kasa .
+

Zeenat dake tsintitin acikin dakin takaraso da sauri .
Takai hannuta jikin nablah ita da ummi zasu kamata.
nablah tayi saurin girgiza kanta tana dukan Tear’s da tafin hannunta .
kibari akai ki dakin kasa nablah zai fi sauki akan nan din.

uhmmmm ummi uhmmmm takasa cewa komai sai uhmmmm da murkususu ciwo .
take wani irin gumi me zafi shiga tsaftsafo mata takoina jikinta.
Jikinta ke wani irin kirma Dan azabar radadin ciwo.
ta dinga cizan lip’s dinta da karfi tsabar tashin hankali .
kuka take da idanunta tana kokarin kamo hannu ummi ‘aiko Allah yabata sa’a ta damke hannun ummi ‘cikin nata da karfi tsiya .
nishi take hankali sbd numfashinta dake sizing yana dawo .
zeenat dibo min ruwa a cup kikawo nayi mata addu’a.

hk zeenat ta fita jikinta Na rawa biyu biyu ta dinga taka step taje takawo ummi ruwa acikin cup .

ummi takarba tayi mata addu’a tabawa nablah tasha Amman still ciwon Bai ragu ba .
Sai abunda ya Karu Na naxaba wani irin murdawa cikin nata yayi da karfi aiko ta saki wata irin razananniyar kara wanda Yasa zeenat fashewa da wani irin matsanancin kuka jikinta yacigaba da rawa .
Tana kuka tace  ummi Dan girma Allah mukai yarinyar nan  asibiti karfa Yar mutane ta mace mana mushiga uku Daga taimako ..

bazata mutu ba inshallahu .

Duk  wani taimakon da ummi tasan anayiwa me nakuda tayiwa nablah shi  Amman Sam bbu wata  alamun zuwan bby wanda hkn ya nuna ummi cewa doguwar nakuda gareta.
Daman km dayawa anasamun hk wani zaga alokacin rainon ciki basashan wahala sai gurin haihuwa wasu km tun gurin daukar ‘cikin suke shan wahala har zuwa haihuwa wasu ma kwata kwata basu San da wannan matsalar ba zasuyi renon ciki lafiya Haka ma haihuwar ‘cikin sauki zasuyi ta .

kuka nablah keyi tana kiran mutuwa zatayi itama zeenat kuka take tana cewa ummi kinga abinda nake gudu da  jin tsoro ko……..
ummi kalli yadda yarinyar mutane ke shan wahala kalli yadda numfashinta keyi ni dai wlh tsoro nake ji wani abu yasameta ‘cikin wani irin kuka zeenat takarashe  zancenta da wallahi ummi  bazan iya haihuwa ba ban zan iya ba wallahi Na hakura da haihuwar gabadaya .

‘Cikin fushi ummi ta buga mata tsawa Dan Allah kiyiwa mutane shr duk kinbi kin cikawa mutane kunne ba’a haihuwa ke uwarki ta  haifeki.
zakizo ki  ishi  mutane da surutan banza da wofi shasha kawai ‘aiko kowace da yadda haihuwa take zuwa mata  kamamin ita ni mukaita kasa .. .

Haka suka  kama nablah zuwa  dakin kasa ummi ta kwantar daita tunda tun dazu a tsugunne take a sama har garin Allah yawaye ciwo yaki ci yaki cinyewa banda murkususu ciwo bbu abinda nablah keyi da ikin kiran sunan mamata da mutuwa zatayi .Wani daren yashigo nablah Na kan  abu daya , tayi firifiri daita tayi mugun fita haiyacinta  iya jigatuwa tayi shi  har tasoma gajiya tana janyo numfashi da kyar tana fitawar da kyar km still  ummi da zeenat Na tsaye akanta  Amman haihuwa shr.
Gashi km  sosai nablah ke  jin wata irin azababen azaba har tasoma fezgar gashin kanta ….
ta daina gane suwaye akanta ta dawo bbu karfin komai ajikinta bakinta ya bushe sannan Yayi fari fat..  idanunta suka bushe .
hawayen dake idanunta suka kafe suka bar xuba  bakinta ne kawai ke motsin ahankali tana karanto duk wata addu’ar tada iya ji taje da zata iya data fizge ‘cikin jikinta ta huta da radadin azabar ciwon datake ji …
Daren ranar bbu shiri ummi ta da zeenat suka cucibi nablah tamkar wata Yar bby suka sakata  abayan mota batare da sanin kowa  ummi ta zauna baya tare da nablah  zeenat ta shiga gaban mota ta  tayiwa motar key sai wani asibiti kudi  me zaman kanshi da shegen kyau. +

  suna xuwa hospital doctor yana  dubata yace haihuwa ce Amman km da saura Dan yanzu ma tasoma nakudar domin har lokacin jikin nablah Bai bude.
ba jin Haka Yasa zeenat sadaukarwa da mutuwa zatayi duk wannan azabar data kwana tana Sha .
Ace km yanzu taka fara nukuda  ita kam tunda take arayuwarta   bata taba ganin irin ciwon nan ba.
shi Yasa tasawa ranta ta nablah   takare ..

Tun daren jiya jikin mahaifiyar nablah yake a tashe takasa runtsawa sakamakon gabanta  daketa aikin  faduwa tamkar ana buga mata guduma wanda batasan dalilin faruwar Hakan ba  Dan Haka ta Mike jikinta a sanyaye Daga kwanciyar datayi tazo ta dauki buta tayi alwala tashiga jero nafiloli da addu’oi neman tsari .

Shi can bangaren   deeni tun daren jiya jikinshi yabashi gidanshi bbu lafiya sbd mafarkin barkatai daya kwanayi   km duk akan nablah ne Dan Haka tun da asuba yashiga   neman layin zeenat dana ummi Amman shr bbu wanda ya dauka acikinsu ,Bai hakura ba Yacigaba da neman layin  Daga karshe ma daya Kira yaji wayar akashe .
nan fa hankalin shi yayi mugun dagawa yakasa yin komai sannan Kuma rasa jin dadin zuciyarsa kawai yaga gara ya dawo gida  .batare da bata lokaci ba yabada Umarni siyan Tiket kawai  yana shirya jikinshi yana neman layin  ummi dana  zeenat Amman har lokaci shr swchoff ake ce masa . Wani tashin hankali ma sai jirginsu ya  sauka a Lagos gabansa ya tsananta faduwa zuciyarsa Na tsinkewa Allah Allah yake yaganshi agida kawai ..

Yana  shigowa ‘cikin gidan da zeenat yasoma cin karo ya sauke ajiyar zuciya da karfi yana dubanta   tana sauri tana hada kayan  bby Na haihuwa Dan jiya daddare basu tafi da kayan haihuwa ba sbd a rude suke. 
tana ganinsa duk ta dabirce tasoma kuka  muryasa Na rawa yace Ina nablah da ummi ‘cikin sharar hawaye tace suna hospital prioucion s .
Tun jiya batada lfy amman doctor yace nakuda ce ….inna lillahi wa inna ilaihi rajiun yana tafiya yana furta hakan acikin zuciyarsa  atare suka shiga mota gabadayansu a rude suke  .sanda ya iso asibiti nablah ta jigata iya jigatuwa bbu kowa agurinta  sai nurse nurse ne tare daita.
deeni ko gaisawa bai tsaya yi  da ummi ba. +

Hankalinsa a matukar tashe  yace Ina nablah  take  ?
Suka nuna mishi dakin haihuwa Kai tsaye yashige ‘cikin labour’ room din wata doctor ce tace please sir kayi hakuri ka Dan jiramu awaje hankalinsa a matukar tashe yace madam Dan girma Allah kiyi hakuri nima Ina son naga matata .
Ai yana dora idanunshi akanta Bai san sanda hawaye suka shiga siyayo masa .
ya mannata   ajikinshi ya rungumeta yana kuka da  aikin jero mata sannu bbu kaukautawa addu’a kawai yake mata yana zubda hawayen tausayinta ya dinga jin daana kar bar wa mutun nakuda daya karbarma ta huta tun daren jiya ake abu daya har yanzu .  tamkar shi nakudar take jira ta tashi zanga zanga  Amman haihuwa shr bbu labari .

Hankali likitoci Suma  yayi matukar  tashi sosai tun daren jiya suke tsaye akanta , zeenat kuwa a ranta tace tun dai shekaranjiya Dan dai bamu gaya muku gsky  bane .
.. likitoci suka tabbatarwa deeni zata haihu zuwa karfe goma shabiyu  ranar Amman gashi har yanzu shr Ga dai  ‘cikin Na motsa alamun bby ‘cikin  Na raye.
Sosai  hankalin deeni yakai karshe gurin tashi tsigar jikinshi har tashi suke tsabar tausayin yarinyar .
ganin har  biyu  tayi ta wuce bbu sauki sai wahala datake Sha Yasa Shi  cewa doctors din suyi mata aiki su cire mata abinda yake ‘cikin ta huta .
tunda sauran karfinta yazamo yanzu ko nishin bata iyawa sai shanyayyun idanunta datake jujjuyawa wal wal dasu .

Hudu daidai aka yi mata shirin aiki sai addu’a ummi keyi ita ko zeenat kuka take sosai har da shesheka .

A dakin tiyata sabon ciwo yatashi ‘cikin zafi zafi ta dinga jin bayanta tamkar ana Sara mata da ada jikinta wani irin  rawa  har gadon datake kwance akai  shima sheking yake .iya wahala nablah tasha sai dai Allah sauketa lafiya ..

Deeni  rike da hanuta yana kuka  yana mata addu’ar .Shi yanzu bata ‘cikin jikinta yake ba ,ita din yafi bukata .domin duk yadda yakai da son haihuwa sai daya ji ta fita aranshi tausayinta da kaunarta ke zariya a gangar jikinshi.
   wani irin uban nishi tayi da karfi  sai Ga kan yaro ya fito fit .
Jim kadan wani kadan wani  yaron ya sake fitowa sororo deeni yayi yana kuka yana kallon ikon Allah Wani sabon kukan farinciki ya kufce masa ya rike hannuta gam yaki saki sai sumar kanta yake shafa ahankali yana mata sannu  can km  sai Ga wani  sabon ciwo  nakuda   take doctors din  suka gane Yan uku ne suka taimaka mata aka fiddota  agalabaice duk tafisu shan wahala Dan ko kuka batayi.
nan suka fita da yaran duka uku Dan gyarasu ummi tayi matukar farinciki da saukarta lfy  an shirya yara ummi nata murna  .Shi kam deeni bbu wanda yake son Gani kmr nablah doctors sukace masa kada ya damu ana kimtsa ta ne suka mata allurar bacci sannan suka kaita dakin hutu bacci take sosai Dan batasan irin hidimar da’akeyi daita ba .koda zeenat taga bbys sai kirjinta ya buga sbd tsabar kamanin da suke da deeni sak sak komai Nasu Na deeni har ma gara ta mace ta dauko kamanin uwarta sai sai farin Na deeni ta debo .’aiko take tasoma yiwa ummi mitar kamanin yaran .Kai zeenat wlh Kin fiyye matsala Wani kama yaran nan sukayi da deeni kawai idanunki ke ganin hk Amman ni Banga hk ba ..
+

Tun asibitin ummi ta dinga kiran dangi tana sheda musu zeenat ta haihu sauka lafiya tasamu yan uku .

Sannan ta tilasawa doctor kan sai ya sallamesu a ranar doctor yace a’a sbd uwar tana bukatar hutu .ummi tace bbu damuwa abar uwar anan zasu wace da yaran doctor yacika da mamaki Amman dayaga ai sune suka kawota yace shikennan .

Suna komawa gida nan dangi sukayi matuka murna da farinciki saukarta lfy kowa sai albarkaci bakinsa yake fada Kai Kai zeenat gsky kin iya haihuwa  tamkar bake ce kika haifi yaran nan ba. 
Kai Masha Allah Yara sak ubansu takoina deeni yaran nan  suka dauko  ita dai sai dai tayi murmushi  kawai tana duban yaran dake kwance masu  tsantsar kamanin da mijinta tun asibitin gabanta ke faduwa sbd tsabar kamanin da yaran ke yi da deeni ..

ita kam nablah tana can hospital batasan hidimar da’ake da bbys dinta a gida  ba.
Dan  batama San yan uku ta haifa ba .

Tana  farkawa idanunta suka sauka akan  deeni ya taso da sauri sannu nablah kin tashi ?
Kallonsa kurum tayi .
Ta kauda fuskarta gefe ya  wanke mata baki ‘cikin wani dan karamin kwanan siliva tare da tayarda ita zaune yaje ya ajiye kwano ya hado mata tea me kwari yazo yana bata da kanshi ..idanunta  kawai ta tsura masa tana kallonsa tana tea din .
ahankali ,shi kanshi yagane mgn take son yi .. ‘cikin sanyi jiki  ta kauda bakinta Daga cup din . alamun takoshi .
Ya ajiye cup ya dawo gefenta ya zauna ya kamo tafin hannunta ‘cikin nashi yana mammatsa mata  magana take son yi Amman bakinta Yayi mata nauyi ..

Ya kafe da rikitattun idanunshi gabadaya  tayi wata irin muguwar rama acikin kwana biyn din datayi tana nakuda muryarsa a sanyaye yace kina son wani abu ne akawo miki ?
Ta girgiza masa kanta. ahankali .

Ok kimin mgn mana  naji muryarki ko wani guri Na miki ciwo ne,?
Nan ma  ta girgiza masa kanta ..can  km muryarta a raunane tace Ina abinda Na haifa ?

Gabansa yayi Wani irin tsalle Dan baiyi tunanin zata tambayi abinda ta haifa ba .take 
Zuciyarsa tashiga harbawa da sauri da sauri muryarsa can kasa kasa yace  Suna gida gurinsu ummi .
ta runtse shanyayyun idanunta da suka sake shanyewa tsabar wahala dataci .
yabita da wani irin kallo tunhuma  Haka kawai yaji gabansa Nacigaba da dukan uku uku sautin muryarta ya sake ji nima Ina son zuwa gida .yace Ok bari nasamu doctor . Ya Mike tsaye ya sumbaci goshinta kana ya fice da sauri yana waigenta .
+

Byn deen  yasamu doctor yayi masa bayanin ko za’a iya sallamarsu bbu wata matsala doctor yace bbu komai ai zasu iya wucewa ..

Sai yamma liss suka shiga estate din ta kofar baya deeni yashiga daita sbd taron mutane dake ‘cike da gidan.
Yan taya murna  bai samu damar kaita dakinta ba .
ya nufi dakinsa na kasa  daita zuwa lokacin da jama zasu tafi ..


misalin karfe tara Na daren deeni  yaje gadon kwanciyar yaran ya dauko mace da namiji ya rungume yaran yana jin matukar son yaran nabin jiki da jinin jikinshi yana mamaye ruhinsa da zuciyarsa .. ummi ta dauko daya suka nufi dakin da nablah take .
Da sallama suka  shigo dakin nablah .
suka zauna tare da saka nablah a tsakiyarsu  muryar deeni cike da farinciki yace nablah kinga arzikin da Allah Ya …wani irin  kallo ummi tayi masa yakasa karasa abin zaice  take km yagane ashe  yaso ya kwabsa ne..kwantar da yaran sukayi akan bed .wayanda suka Sha wasu haddun kaya sanyi  masu shegen kyau da tsada da daukar hankalin farare tas tas dasu tamkar ya’yan turawa ,sosai ta tsurawa bbys din ido tana masu Wani irin.kallo kamanin yaran take kallo ‘cikin tashin hankali taki dauke idanunta akansu yanzu itace ta haifi wayan nan kyawawan bbys din masu kyawun kyau hk ganin yadda yake kallon baby’s din Yasa ummi tashi ta fice shima can deeni ya Mike tsaye yana amsa wayar Yan taya Shi murna ya bar dakin .

Dakin ya saura Daga nablah sai bbys dinta da suke kwance reras akan gado  abin sha’awa. kallon yaran tacigaba tana jin Wani irin sanyi Na bin jikinta  take km taji Wani irin mugun son yaran yashiga ranta tare da ratsa kowane shashi Na gangar jikinta tundaga tafin kafafunta har ‘cikin kwalkwaluwarta nan take taji idan dukiya zata taru bazata iya rabuwa da yaranta ba ,daidai da daya Daga cikinsu bazata iya bayarwa ba ballanantana dukansu kawai ta fashe da wani irin matsanancin kuka tare da rungume yaranta tasoma sabatu , wallahi tallahi bazan iya rabuwa daku ba yarana  Ina  sonku ina kaunarku km zan rayu daku.
koda kuwa duniya zatakini .ta zageni akanku Ina sonku takarasa fadar hkn tana sakin Wani irin kuka me cin rai ahankali take cigaba da kallon baby’s dinta hawayenta Na tsaya ahankali  tasa hannuta ta goge tana sakin ajiyar zuciya ‘ta daura mazan duka a saman cinyoyinta mace km ta daurata akafadarta tana jin Wani irin dadi mara misaltuwa aranta tare da jin duk abinda zai faru sai sai ya rafu Amman bazata rabuwa dasu ba ….’Cikin wannan halin datake  ciki  deeni ya km shigowa dakin fasukarsa dauke da wani irin maganadisun murmushi .ta koina ka kalleshi kasan yana ‘cikin tsantsar farinciki da murna samun wayan nan kyawawan bbys din masu matukar kyawun da daukar hankali . +

Ahankali yakarasa inda take zaune rungume da ya’yanta duka .
ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta  da jin Wani irin mugun sonta da yaran yana tasoma masa .
Yanayin daya ganta ciki  yasashi shan jinin jikinshi .
zama yayi kusa daita sosai  har cinyoyinsu Na gugar juna ya amshi ta mace Daga hannuta  ya daurata saman cinyarsa yana kallonta yana kallon fuskarta nablah dayaga gabadaya ta canza ta dawo wata iri . muryarsa a sanyaye ya Kira sunanta nabeelah ….bata amsa masa  ba sai ma juyo da tayi inda yake zaune  tayi masa kallon second  2 kana ta dauke idanunta Daga kanshi.
ta maidasu  kan yaranta dake cinyarta .
,sautin muryarsa taji a matukar sanyaye fiyye da farkon shigowarsa dakin  .. nablah kinga kyautar da Allah Yayi mana ko?

Adakike ta amsa masa da uhmmmm . gsky kin iya haihuwa.
arayuwata bantaba ganin macce data iya haihuwa  kmr ki ba .
Gsky kinyi kokari sosai . nan ma  tayi masa banza ta sharesa gabadaya ma  taki cewa dashi  komai .
yanzu mekike bukata akawo miki ?
muryarta can kasa kasa tace babu tare da kamo lips dinta Na kasa tana cizawa ahankali ahankali tana Dan jijjiga kafarta daya akasa .

Gabadaya deeni ya rude yarasa abinda ke masa dadi tunda ta haihu yarasa gane kanta sai wani shashsharesa take tana basar dashi  da ciccin magani wanda yarasa dalilinta nayin hk . runtse rikitattun idanunshi Yayi sosai .
ciki Mutuwar jiki  sakamakon tuno da kyawawan bbys dinsu data haifar masa masu tsananin kamadashi  km  yake tare dasu ahalin yanzu.
To  me zai dameshi da duk abinda zatayi arayuwa tagama masa komai tunda tabashi abinda yafi so da kauna a rayuwarsa ta duniya . sumbar bby  girl din  yayi  yana jin wata irin natsuwa ta daban tana ratsa kowane shashi Na gangar jikinshi sosai yake son yaransa Amman yafi jin kaunar mace fiyye da sauran acikin zuciyarsa  .Jikinasa cike da rauni soyayyarta  yakamo tafin hannuta  ‘cikin nashi  yasoma murzawa ahankali ahankali ‘hade  da  shaukin kaunarta yace meke damunki nablah naga duk kinyi wani iri hk ? +

Ki sanar da deeni  abinda ke damunki banason ganinki ‘cikin wannan  damuwa da tashin hankalin  please …
yanzu kin zama wata bangare Na rayuwata da farincikina gabadaya sbd wannan kyawawan  bbys din dakika bani ..

Kimin abinda wata matar  takasa jura ta min arayuwa  .
Kin bani kyautarsu alokacin danafi bukata . akan wayan nan yaran bbu abinda bazan iya miki Shi ba , matukar Bai shafi addanina ba .
ban ji  dadin yadda naganki ba yanzu.
idan akwai wani abu dake damun zuciyarki ki fito ki sanar min.
ni km nayi miki alkwarin zan yi miki maganinsa kowani iri ne .. yakarasa fadar hk yana matse laulausar tafin hannunta ‘cikin nashi yana jin yadda sonta ke fizgar zuciyarsa gareta ..

So take tayi mgn Amman maganar taki fitowa sakamakon wani yanayi data tsinci kanta ciki ,ita fa bbu abinda ke damunta s halin yanzu wanda ya wuce son rabata da ya’ya za’a yi.
ta lumshe shanyayyun idanunta kana ta budesu ahankali ta zubesu ‘cikin nasa still takasa tabuka komai shima lumshe rikitattun idanunshi Yayi sannan yace Ok kingama ganin yaran zan maidasu kasa sbd masu zuwa ganin bby ..
take zuciyarta ta buga da matsanancin karfi har sai data taji zubowar  gudan jini Daga kasanta . afrigice ta zare hannuta ‘cikin nashi tana kallonsa  a tsorace bakinta da alamun son yin mgn .
kanshi ya girgiza mata yana kokarin mikewa tsaye .

Muryarta cike da inn inna ta fizgo mgn da kyar  tace nifa.. nifa ..ban bada ya’ yana.

what ? Bai San sanda yakoma ya zauna ba .yana kallonta da matukar mamaki .Wallahi wallahi deeni idan duniya zata taru akaina idan sama da kasa zata hade idan za’a yi ruwan jini deeni bazan iya bada ya’ya nan ba.
kai ni daya Daga cikinsu ma bazan iya bayarwa ba ballanantana duka .
deeni koda duniya zata kini ciki  kuwa har da mahaifana dakai deeni koda zan dawo kwanan akan  bola Ina tsince tsince in ciyar da kaina da ya’ya Na ,bazan iya bada ya’yan nan ba wlh. duk da Allah yasani bansan waye mahaifinsu ba Amman Ina ji ajikina mahaifinsu ba wulakantacce mutun bane duba Ga yanayin ya’ya.
take gaban deeni ya fadi rassss  rassss rassss yashiga bugawa da karfi karfi .zuciyarsa tashiga   tsalle da kururuwa neman dauki da agaji . +

muryarta ahankali ‘cikin sanyi jiki tacigaba da mgn tunda Na kalli fuskar ya’yan nan narasa meyasa naji Ina mugun kaunarsa wanda bansan dalili ba narasa meyasa tun sanda Na daura idanuna akansu kawai naji bazan iya rabuwa dasu ba .
takarasa mgnr tana fashe masa da wani irin matsanancin kuka me cin rai da Daga hankalin .

Jikinta Na matsanancin rawa  ta kwantar da yaran daya byn daya akan gadon.
da kyar  ta sauko Daga kan gadon datake   ta zube  masa a gabansa  ta dinga kuka Dan Allah deeni karku rabani da ya’yana Ina son su ko zan rasa raina bazan iya rayuwa bbu su ba.
Wallahi  bazan iya rabuwa da yarana ba   aduk yanayin da suke Wallahi azim bazan iya rayuwa bbu su ba ni Ina son su a Haka .
kuka take sosai tana rokonsa akan kada surabata da yayanta .

Gabadaya jikin deeni yayi Wani irin mugun tsayi km  ilahirin jikinshi suka  mace murus yarasa abinda ke masa dadi a zuciyarsa .
Ga koshi Ga kwana yunwa.
hankalinsa ya Kai  kololuwar gurin tashi gabadaya yarasa abinda yakamata Yayi ahalin dayake ciki .
kukan  farinciki zai yi ko haushinta zai ji Na sabon salon iskanci data tsiro  …  sai kallon bbys din yake yana kallonta tsugunne agabansa tana risgar kuka  tana rokonsa . 
shima  ajiye bby’ girl din  dake  hannunshi yayi .
ya tsura mata rikitattun  idanunshi da kyau  yana cigaba da kallonta hade da nazarinta wato dai da gaske mutuwar son yaran take kmr yadda shima yake matsanancin son su .
duk Shi a tunaninsa yafita son su da bukartasu arayuwarsa ..
a zuciyarsa yaji wani irin matsanancin sanyi ya ratsashi tundaga tafin kafafunshi zuwa kwanyarsa , kennan idan yace zai isar da sakon zuciyarsa gareta bazai Sha wata wahalar shawo kanta ba adalilin wayan nan yaran  ..

take  km burin  mahaifiyarsa ya fado masa  .
yaya zaiyi da ummi wace oready  tagama gaya duniya da shelar cewa  zeenat ta haihu ?
..yaya zata ji idan tasamu wannan mummunar labarin ?Kuka take Sosai ta rike kafafunshi gam deeni kayi hakuri nasan ban kyauta ba akan abinda nayi Amman  Ina son ya’yana  duk da  kasancewarsu shegu  wlh  ba zan iya kyauta dasu ba kmr yadda nayi maka.. shiiiiii Karki kara kiran ya’ya Na da  she.. shegu ni..Ni..ne …sai km yayi shr ya datse harshensa da hakorinsa gam  jikinsa Na wani irin matsanancin  rawa idanunta dake cike da ruwan hawaye ta xuba masa tana kallon bakinsa .. zuciyarsa gabadaya gaskiya take son  fada mata Dan ta daina danganta ya’ yansa da kalmar shegu   Amman yana jin matsanancin tsoron tashin hankali dazata shiga fiyye da wanda take ciki ahalin  yanzu.. Shi dai yasan  xuwa yanzu  ya Mika duk  rayuwarsa gareta  sbd kaunar dayake mata ita da yayanta … +

‘Cikin wannan halin zeenat da ummi suka shigo dakin atare turus sukayi ganin nablah durkushe gaban deeni rike da kafafunsa  tana risgar  kuka da iyakacin karfinta .

Da sauri suka karasa garesu suna tmbyr deeni lafiya  meke faruwa ?

‘cikin rawar jiki nablah ta Mike tsaye ta nufi gurin ummi tana layi tana  kuka muryarta cike da kuka tace Dan girma Allah ummi ku  min rai wallahi bazan iya bada ya’yan nan ba  kumin abun alkhari nasani km Na gode da karamcinku gareni Amman kada Ku rabani da ya’yana …..

A zubure zeenat  ta dafe kirjinta tare da cewa what ke kina da hankali kuwa ?

Ke wace irin mahaukaciya  ce yaza’a yi kice bazaki iya bada ya’yan ba …..
take nablah ta fuskanceta sosai  a fusace tace gaki nan babbar mahaukacirya da  batasan abinda takeyi ba  da sanin ciwon Kanta  ba.
ke kinsan zafin haihuwa ne?ko kinsa zafi ya’ya ke kinsa wahalar dana Sha akan wayan nan ya’ya? +

to nace bazan bayar ba km idan sama da kasa zata hade bazan bada ya’ya nan ba ke ni akan ya’yan nan banki duniya takini  ba ciki km har da iyayena wallahi wallahi dana bada ya’yan nan gara narasa rayuwata gabadaya.
ke indai kika ga nabada ya’ya nan sai dai idan bana numfashi a doron kasa .

rassss rassss gaban ummi yayi wani irin matsanancin bugawa da karfi ..Hk ma deeni gabansa ya km bugawa  zuciyarsa tacigaba da rawar datake tun kafin shigiwarsu ummi ..

Zeenat tace Wallahi wallahi  baki isa ba nablah kinyi kadan km  sai kin bada yaran nan tunda tun farko ke kika  amince km kinyi alkawarin  zaki bada su  muryar zeenat  Na rawa takarasa fadar hk  .

Wani irin kallon tababbiya nablah tayi mata sannan muryarta Na rawa rawa  tace to..to.. yanzu nafasa badasu sbd nima  Ina son abuna dama can danayi kyautar su bansan zafinsu bane yanzu kuwa sai dai nabawa wasu labari .
Baki isa ba wallahi sai  dai kuwa ki rasa ran naki dakike ikirarin rasawa akansu Amman kmr kin bada ya’ya kingama ..  Ok zanga wanda ya isa dazai  rabani da ya’yana ..

ke nifa nafiki zafin Kai da rashin mutunci akan yaran nan zan iya miki duk abinda yazo zuciyata inji cewa zeenat .

baki  nablah ta saki tana kallon zeenat da mamakinta  hakan yabawa zeenat damar cigaba da  maimaita kalmar dole abasu yara tunda tun farko an rigada anshirya hk  da surutai kala kala   tayi kan baby’s   cike takama  zata dauka nablah tayi kuka kura ta dire gabanta cike da maseefa tace ubanwa  yabaki damar taba min yara ?

Ubanki  da km uban  Yayi miki ciki  a gidan nan .
a fusace ummi tashiga tsakaninsu tana jan zeenat baya.
ummi ta dinga mamakin abinda nablah tayi duk da tasan Yar tatace da fadan rashin gsky Amman batayi tunani nablah zata  iyawa zeenat rashin kunya da tsiwa Haka ba  .

Ni zaki kawo danyen Kai da ranshi kunya ta fadi Haka tana nuna nablah da yatsan hannuta  Dan girma Allah ummi ki matsa Na canzawa wannan Yar iskar  yarinyar halitata dama Ina da ciki daita Ina takaici ta wlh.

kallon kasa da sama nablah ke bin zeenat dashi ahankali wanda ke nuna alamun bata isa ba .

Kina takaicina ai sai kixo ki kasheni ki huta  banda mijinki daya nace akan zai taimakamin  da tuni ban  san inda dare Yayi min .
zeenat tayi sororo tabi deeni da wani irin kallo tana jiran taji yakarya mgnr yarinyar .
Amman taji Yayi shr yana binsu da idanu kawai .
  my hrt ummi kuna jin fa abinda yar iskar  yarinyar kecewa ko.ummi tace munji  ai zance nata duk shirme ne bakya ganin duk abinda take bata ‘cikin haiyacinta tasoma jijjga zeenat din  kiyi shiru mu yanzu bawannan shirme bane agabanmu yadda yara zasu zama naki shi kawai  .kiyi shr ki  natsu asan abin yi .
+

nablah najin   Haka ta buga kafarta daya   a kasa ta nufi gurin da bbys dinta suke kwance  gadan gadan  tasa wani irin mahaukatan  kuka  tana cewa  wllahi tallahi ban bada ya’ya Na .
ya’yan guda uku ta rungumesu ajikinta tana  sake sakin  wani irin matsanancin kuka  me ban tausayi da taba zuciyar ma aboci  saurare ..

Tashin hankali wanda ba’a saka masa ranar zuwa .
zaune kawai deeni yake yana kallon    sarautar Allah.
Yana mamakin  daman zafin kan yarinyar nan yakai hk Shi Bai sani ba ….abu kmr a film yarinya tana kokarin birkice musu da dagula musu lissafi.
  hatta ummi tsaye kawai take sake da baki tana kallon ikon Allah da yadda nablah ke nuna reaction dinta akan bby din da batasan taka maimain wanda yayi ma ‘cikin su ba .
,to wannan  idan km tasan ya’yan deeni ne km  jikokinta   me zai faru ? Tayi wa kanta tmbyr tana cigaba da kallon nablah rungume da yara tana kuka . 
tamkar wata zautaucciya .
Gabadaya Daga deeni har ummi kasa tabuka komai suka yi sai idanu  da suke bin nablah dashi …

Wani irin  tausayinta ne me gyaraye da tsansar soyayyarta   ke sake huda kirjinsa da  mamaye gangar jikinshi da zuciyarsa .
alahakikanin gaskiya Bai taba tunani yarinyar zata canza salo irin Haka  ba.bai dauka zata so ya’yan da ta dinga hauka akan acire mata su ba .
Wani irin  gumi ne me zafi ya shiga   tsaftsafo masa ta koina ajikinshi yazama tamkar wani mutun mutumi a zaune yana kallon nablah kwakwume da bbys ajikinta duk tayi firi firi tafita haiyacinta   .

Take zeenat ta dinga jin zuciyarta tamkar zata fashe ta tarwatse kan   takaicin nablah.
ita kanta wani irin mugu mugun son bbys din ne yashiga ranta tun sanda suka zo duniya  ta daura idanunta akansu taji sun shiga ranta.
duk da duk  sanda ta kallesu gabanta Na tsananta faduwa akan tsananin  kamanin da yaran keyi da mijinta.
Dan ko mahaukaci ya kalli yaran yasan kamarsu daya da deeni babu wani bambanci launi ko sura  daidai da  yatsun kafafun yaran dana hannusu  irin na deeni  ne sak  .bakinsu da  hanci komai Nasu  irin nasa ne .
sosai take taji wani irin  mugun  son yara Na sake  ratsata  har ‘cikin zuciyarta  tana jin bazata iya rayuwa bbu su ba ….
+

Amman Ga tashin hankali da uwarsu tazo mata  dashi wanda take jin  bazata iya  jurawa ba .. Amman duk da Haka durkusawa wada ….
gabadayan ilahirin jikinta yayi mugun sanyi jikinta banda kirma bbu abinda yake tsabar tsoro da rudani .
Ga mamaki deeni da ummi har nablah.
suka Ga zeenat ta zube a gaban nablah tana kuka tare da  rike kafafunta tana rokonta  Dan girma Allah nablah ki rufa min asiri kada ki min Haka  wannan   ita kadai ce damata da zata min katanga tare da yi min shingi da kishiya arayuwa ta.
  Dan girma  Allah kibar min yaran  wallahi nafiki bukatarsu  zan kular miki  dasu fiyye da tunaninki .
zan basu gatan  duk duniyar nan .
zan kaunace su fiyye da ke kanki da kika kawo su duniya ..
Dan Allah kibar min su Karki fasa kyautar mana dasu kmr yadda kikace  ummi Dan Allah kisa baki tabar min su .. my hrt kaima kayi shr kaki cewa komai please kuyi mata mgn kozataji  nafita bukatarsu takarasa mgnr tana fashewa da wani irin matsanancin kuka.

kuka zeenat take tana rokon nablah akan tabar mata  yaran … ahankalin deeni ya Mike tsaye Daga zaune dayake yaje har gaban nablah ya mika mata  hannunwansa duka  alamun tabashi yaran Amman taki .

Yayi yayi tabashi yayan taki sai ma matsawa da tayi Daga kusa dashi tana jijiga yaran da zuwa yanzu hayaniyarsu tasoma tayar dasu .

da kyar  deeni ya shawo kanta ta hanyar ce mata bbu inda zanje da yaran nan  nablah  zan kwantar dasu ne kawai  ko bakiga yadda kika matsesu ba ajikinki ba kar wani abu yasamesu  .
sannan ta Mika masa mace da Na namiji zuciyarta cike da tsoro da fargaba yaje ya kwantar dasu .
ya dawo ya amshi dayan ma ya kwantar dashi kusa da yan’uwasa  kana ya janyo hannuta ciki sanyi jiki Ya zaunar daita akan gadonta ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kare mata kallon  tsanake .
sannan  yasoma magana ‘cikin sanyi rai da zuciya… Nablah ki natsu ki dawo ‘cikin haiyacinki muyi mgn ‘cikin tsanake da fahimtar juna da farko kin amince da zaki bamu abinda zaki haifa wanda har muka sanyawa rayuwarmu son abinda ke cikinki.
” to meyyasa yanzu kika canza ra’ayinki alhalin duniya tagama sannin wayan nan ya’yan ya’yanmu ne nida matata ? +

Ilahirin jikinta da bakinta wara suke gurin cewa  nidai  kawai ji nake a halin yanzu bazan iya kyautar dasu ba.
. saboda kinsha wahala gurin haihuwarsu shiyasa bazaki iya badasu ko me ?
Kai tsaye taji ya ‘aiko mata da tmbyr datasa ta tsura masa shanyayyun idanunta da suke cike da ruwan hawaye taki ce masa komai sai kallonsa kawai  take ..
“jikin deeni Yayi sanyi sosai sbd ganin yadda  yanayinta ya sauya . yarasa ta inda zai bullo mata.
ta  kalleshi sosai Yayi matukar bata tausayi  Amman har ‘cikin zuciyarta bata jin zata amince tabashi yayanta kyauta .
”  tacigaba da dubansa can km yace kina jina ko kiyi hakuri kibar mana yaran nan nida matata nayi miki alkwarin zan raba tarin dukiya biyu Na baki rabbi akansu kije kicigaba da rayuwarki .
Sosai ta sake  tsareshi da shanyayyun idanunta tamkar zata cinyeshi  tana mishi wani irin kallon rainin wayo.
hakan Yasa gabansa cigaba  da faduwar dayake .
shima kallonta yake yana jira Daga gareta tare da  mamakin canzawarta  a’cikin zuciyarsa .
idan wani ya fada masa zata rikide ta dawo masa Haka wallahi zai rantse da Allah  yace karya ne ranta a matukar bace tace  Kai dukiya ta dama km take rudarka har kake jin Kai wani ne .
Amman ni bbu abinda za’a bani a duniyar nan da zai Saka Na iya kyautar da ya’yana har UKu  ba daya ba.
ko mahaikaciya ce Ni bazan soma yin wannan dayin aikin ba ballanantana Ina ‘cikin haiyacina, yakarasa fadar hk tana nuna brain dinta da yatsan hannuta.
kana tacigaba nidai Dan girma Allah Na rokeku daku barmin ya’ya Na Ina sansu nima a duk yadda suke.

deeni ya runtse idanushi gam tare da furta ya Allah akasan zuciyarsa  ….yasoma cizan lips dinsa da karfi .
gabadaya komai Na ‘cikin duniyar nan yasoma tsaya masa Bai taba tunani sanadiyar yarinyar zai taba  shiga  ‘cikin tashin hankali irin Haka ba.
   ya dauka rashin son ‘cikin jikinta datake tun farko zai tsaya a Haka ne .Amman a kalmomin bakinta na yanzu komai ya sauya agareshi yagane  shi din bakomai bane a duniya nan .
sannan ya soma fahimtar Bai isa yace zai ma kaddarsa wayo ba .
Yau din nan tazo masa da tarin abubuwa da daya farinciki dake  tattare da tashin hankali mara misaltuwa . +

Shin yanzu ya zaiyi da kaddarar data fada masa ?

Ya’yan da zai fara samu a duniya sunzo masa da wani irin salo  na daban .
yanzu mezai cewa danginsa da yan’uwa ?

Hakika Komai yagama dagule masa ahankali ya juya saitin da zeenat take tsaye surusuru tana aikin barin jiki da marairaice wa .
yana aika mata da wani irin matsiyacin kallo me frigita zuciyar wanda akawa  sannan muryarsa a fusace  yace kinga ni ko ?
Kinga  irin abinda sakacinki  ya haifar mana   ko ?
Me kike tunani zai faru gaba  idan har taki amincewa tabada yaranta ?

Zeenat da jikinta ke mugun kirrrrrrma ta sake fashewa da wani irin matsanancin kuka tana yarfe hannuwa .
  yanzu dakin yi hakuri kin haifi wanda Allah yabaki da duk hk Bai faru ba.
da km baki samu ‘cikin tsaka me wuya ba. Amman bbu komai duk ‘cikin wannan lamarin ni akafi cuta yakarasa mgnrsa yana jin kunar rai acikin zuciyarsa yayinda kirjinsa ke wani irin buguwa da karfi .
Shi kanshi  kuka yake son yi ko zai daina jin radadin azabar ciwon zuciyarsa keyi .

banda kuka bbu abinda zeenat keyi ita kanta tasan ta cuci kanta da kanta.
Ta  ruguza rayuwarsu sbd  sakacinta  da  son zuciyarta ta Mike Daga inda take  ahankali tana layi ta rungume ummi ajikinta  tana matsanancin kuka.
Ummi kiyi hakuri a rayuwa nasan Na cutar daku Amman ko daidai rana daya ummi baki taba kina ba .
Sai ma sabuwar kulawa da kike bani hakika ke uwace guda har da rabi samun irin Ku ahalin yanzu zai yi wuya  ummi kiyi hakuri abida nayi  ki ya femin Na cutar dake domin ba irin tarbiyya da kika bani ba kennan ta sake tsanata kukanta.
ummi itama ta rungumeta sosai  tana zubda hawayen tausayin diyarta arayuwa ta tsani abinda zai saka zeenat dinta  zubd hawaye matukar tana da yadda zatayi.
kasa cewa komai tayi Sai aikin  rarrashita datake tana shafa bayanta ..Ahankali deeni ya dauke idanunsa akansu ya juyo sosai tare da gyaran zamansa yana fuskantar nablah da kyau ya kaskantar da kanshi da muryarsa agabanta yana nuna mata shin din bakomai bane facce me nema agurinta  .
a wannan fani har ya mance dako su waye  tsaye akansa.
Domin Bai San sanda ya kamo tafin hannunta ‘cikin sanyi jiki ba yana kallon ‘cikin kwayar idanunta muryarsa cike da rauni zuciya tare  da mayyen sonta ya Kira sunanta.. nabeelah …kiyiwa Allah ki mallaka mana bbys din nan.
badanmu ba Sai saboda Allah  ki duba tashin hankali da zanshiga akan  yaran nan .
sannan ki duba halin da mahaifiyata da matata zasu shiga ki tausaya nablah ki duba yadda mahaifiyata tagama gayawa duniya akan nida matata muka haifi bbys din nan .Kinsa idan akaji sabanin hk zatashiga tashin hankali  da rudin rayuwa ..
nablah nasan kina da saukin Kai  da sanyi hali hade da hakuri akan komai Na rayuwa .
Na rokeki da Allah kibarwa zeenat bbys din nan .
Allah zai duba lamarinki ya sake baki wasu da yardarsa …
a fusace ta fizge hannuta ‘cikin sauri Daga nashi tana jin takaicin mgnrsa .  .. +

Kana ji har mara hankali matarka ta kirani dashi akan ya’yan dani kadai nasan  kalar wahalar dana Sha akansu tunda Daga cikinsu har zuwa haihuwarsu.
idan har nabar mata yaran nan wallahi azim  Na tabbata mahaukaciyar gaske deeni .
zeenat ta bar jikin ummi tamatso gareta sosai tana kuka tana rokon nablah.

ZUCIYAR  deeni tasoma rawa yasoma jin Wani irin ajikinshi hakika ya tausayawa zeenat duk da yasan itace silar rugujewar rayuwarsu da yi musu katangar karfe da burin ransu km farincikinsu  Amman fur nablah taki amincewa tare da cewa aunty kiyi hakuri  wlh nima  Ina son ya’yana.
idan nabaki su ni km yazamanto su kadai ne ya’ya da zan haifa a duniya   ni km Sai  nayi ya’ya ?

Kiyi hakuri kawai kema Allah zai baki naki da yardarsa Amman zance nabar miki ma su  yanzu bbu shi .kibar min nawa nayi rayuwa dasu , sune duniyata  ayanzu bazan iya rayuwa bbu su ba . +

deeni ya juyo a tsukwane ya kafe zeenat da idanushi yana kallon yadda ta dawo wata kala abar tausayi bbu wuya tashin hankali ya canza mata kammani .
Ummi takaraso ahankali itama  ta zauna kusa da nablah ta dinga bata hakuri da yima dabarunsu irin Na manya da siyasa iri iri Amman fur  nablah taki Sai ma fashe musu da sabon kuka datayi ni kibarni  Haka  Dan Allah Dame zanji .
yanzu zan bar muku gidanku akan na bada yaran nan gara na komai
kan bola Na rayu dasu ‘cikin kulawata .

gabadaya deeni yasoma tsorata da yanayinta har yasoma aikawa kwalkwaluwarsa  tmbyr Anya kuwa wani abu Bai samu brain dinta ba kuwa gurin haihuwa ?

Sosai Ya xuba uban tagumi tare da jefa Dan  karamin yatsansa ‘cikin  bakinsa yana cizawa da karfi yana kallonta  yana nazarin reaction dinta ..
sosai ya jima yana kallonta kafin Daga bisani yace first love barta kawai  akawo mata abinci  yaci da alamun tana jin yunwa tun da muka shigo gidan nayi nayi daita taci abinci taki ci a she rigima take ji shiyasa.
jikin ummi a matukar sanyaye tace zeenat goge Hawayenki ki natsu  kada mutane su gane Muna ‘cikin damuwa da matsala.
muje maza  ki kawo mata abinci ni zan Dan tsaya saboda kauda idanun mutane akanmu.

Tare suka fita .
ummi Na sake rarrashinta akan ta kwantar da hankalinta ..

Suna fita deeni ya juyo gareta ya hade da jikinshi ya rungumeta  zuciyarsa Na harbawa da sauri da sauri .
  tare sa sakin naunauyen ajiyar zuciya bakinsa yakai daidai saitin kunneta sosai.
Yace  Na yaba da jarumtarki Na yaba  miki da yadda kike son baby’s dinmu .
daman Haka yakamata duk wata uwa tayi akan yayanta .
km hakan da kika yi ya sa naji kin  birgeni sosai. Sai dai me zai hana ki tausaya kibarwa zeenat dina baby’s din please  zata kular miki dasu ..ki tuna sanda kike kuka kike rokona akan azubar da ciki Na hana batare da saninki ba .
ki tuna irin taimakon dana miki akan ni zan karbi ‘cikin da bansan wanda Yayi miki ba domin gujewa kunyar  duniya 
Da karfina da dukiyata duk sa sadaukar akan Na inganta ‘cikin jikinki da rayuwarki .
Amman kirasa abinda zaki  sakayyar min dashi .
Sai  hanani bbyn dana gama wahala akansu.
Meyasa  zaki min hk ? Yakarasa mgnr da 
Ki bar mata sake of me please  nablah zanji dadi idan har zaki iya min hk .kina jin yadda zuciyarata ke bugawa da karfi  akanki .
,akanki zan iya yin komai ciki har da fallasa sirrin dake  boye wanda hakan bazaiwa first love dadi ba.please nablah sake of me jikinta Sai kirma yake tana zubda ruwan  hawayen tausayinsa muryarta a dashe tace nasani deeni kataimaka min a rayuwa km zan iya yi maka komai a rayuwa Amman bazan iya  kyautar yaran nan  Ga kowa ba ciki kuwa har da kai ..
Ni kaina Haka kawai Na tsinci zuciyata da matsanancin kaunarsu tunda Na daura idanuna akansu .kasa samun natsuwa .
Ya zanyi nabaku kennan ni zauna hk ?
Byn tarin wahalar dana Sha akansu .
ahankali ya sausauta rungumar da Yayi mata ya ciro hanky Daga gaban aljihun rigarsa yashiga goge mata hawayen dake tsiyaya akan kuncinta .
bakinsa ya Kai kan lips dinta ya tsotsa yana kallon ‘cikin idanunta .
Lumshe shanyayyun idanunta tayi tasoma kokari cire bakinta Daga nashi .
Jikinsa a sanyaye ya xuba mata rikitattun idanunshi kawai yana kallonta yana imagine dinta.
har sanda zeenat ta dawo dakin hannuta rike da cool food flasks   da  flasks din ruwan zafi da plate Deeni ya janyo wata Yar karamar stood tsakiyarsu  ya bude cool da  zeenat tashigo dashi.
miyar dayafi tsana arayuwarsa  yasoma cin karo dashi wato miyar kuka wace Tasha  naman kaza da kayan kamshi makewa Yayi  ya ciro karamar ta sama ya ajiye yacigaba da bude cool yaga tuwan samiviter ne aciki Whit lailon ya ciro tuwon yasaka akan plate ita km zeenat jiki Na rawa ta hada mata tea me kauri ta mikowa deeni.
  ” ya karba ya ajiye a gefen plet din.
abin zeenat nabashi mamakin sannan km   yana jinjina girma al’amarin.
lallai sanadin wayan nan baby’s din  Yasa  zeenat dinsa tasoma sauya halinta wanda yajima yanasonta dashi . +

Muryarsa a matukar sanyaye yace Bismillah nablah kici abinci .
taki ci ta xubawa masa  idanunta ya Mika mata cup din tea shima taki karba.
Yayi shr  ya tsura mata rikitattun idanunshi bazaki ci abinci ba ?
Ta girgiza masa kanta alamun eh saboda kina tunani zamuyi poison naki ko ?
Tayi saurin sake girgiza kanta to meyasa bazaki ci ba alhalin nasan kina jin yunwa ?

Muryarta a shagwabe tace nifa bance zakuyi min wani abu ba .. zeenat kawo min spoon. 
.
  Zeenat ta juya da sauri taje takawo masa spoon ta Mika masa .
mamaki ne yakama zeenat Ganin deeni yasoma  tura  tuwon samiviter da miyar kuka  abakinsa the most abincin dayafi tsana kennan arayuwarsa ballanantana dai miyar kuka wanda ko sunan miyar akafada agabansa Sai ya yatsuna fuska tsabar baya sonta .
Amman yau shine zaune yana ci hankali kwance dago rikitattun idanunshi Yayi masu tsantsar cike da tashin hankali  ya daura akan nablah dake zaune tamkar an dasata  tare da yi mata alama da spoon din hannunshi .
, zeenat tasoma itama  sosai ta tsoma hannuta sbd ganowa datayi lallai nablah bata yarda dasu ba.
tasoma ci  Sai da nablah ta tabbatar dayaci sosai hk ma zeenat  sannan ta tsoma hannuta ciki tare da yin bismillah tasoma ci  ahankali aranta tace idan ma mutuwarce ba zan  mutu ni kadai  ba Sai dai abarwa ummi baby’s din .
ko tea din ma kin Sha tayi  Sai da zeenat Tasha deeni yasha sannan Tasha itama .
deeni ya kalleta yana tabe baki girgiza Kai .
sbd muraran km azahirance nablah ke nuna kuruciyarta a filli . Idan har wani abu zasuyi mata .
Ai tayi kadan ta kare kanta .

number wayar ummi deeni  yakira .
Byn kmr minti goma Sai gata tashigo dakin   first love yakama ayiwa yarinyar wanka hk fa  da duk abinda yadace.ko bakace ba deeni duk za’a yi mata daman wannan tashin hankali ne Yasa nakasa samun natsuwa nayi mata ai nablah tamkar diyar cikina Na dauketa . +

Da zai fita ya janyo hannu zeenat ya nufi dakinsa daita ya rungumeta tsam tsam  ajikinshi zeenat yakira  sunanta Ina so ki tattaro natsuwa ki sanyawa gangar jikinki sannan ki kwantar da hankalinki da sannu zan shawo kanta ‘cikin sauki batare da wani hargitse ba har ta amince .
domin wannan harbin iskar da kike da tashin hankalin   ba zai saka tabada ya’ya  ‘cikin sauki ba .
as far as tasan wahalar daukar ciki da radadin haihuwa kema kinsa bazai yiwu a karbi yaran ‘cikin sauki ba.
ki dinga lallabata ta yadda taza yarda ta amince da ba cutar daita da yaranta zakiyi ba  ..

narkewa tayi sosai  ajikinshi , zanyi komai my hrt matukar yaran zasu zamo nawa Dan wlh wani irin mugu mugun  son yaran nake ji ‘acikin zuciyarta .
Nima sun shiga raina zeenat  fiyye da ita kanta uwar data kawo su duniya.
Amman duk da hk ba zai yiwu  muyi mata dole ba .
tana bukatar rarrashi da caring  kema kinsa haihuwar nan  is not easy ballanantana irin nata datayi kwana biyu tana abu daya sosai deeni ya kwantarwa da zeenat hankali har ta Dan samu natsuwar zuciya tare da sake jin kaunar yaran daram acikin zuciyarta ..

Kowajen wanka ma kememe nablah taki yarda ummi ta rufe kofa toilet tayi.
  Dan kofar a bude aka barta tana hango wutsil wutsul din yaranta akan bed  Dan gabadaya atsorace take dasu ummu.
yayinda  zuciyar ummi tashiga watsi watsi datashin hankali  anya kuwa ba wata maseefar ce ke shirin faruwa dasu ba.
duba Ga yadda nablah ke nuna son yayanta mura mutane  da yin  kafa kafa dasu …


Daren ranar  gabadayansu   Daga ummi har oga  deeni da zeenat adakin nablah suka  kwanna  sbd yaran a cewarsu .
bbu wanda ya runtse acikinsu.
yaran Sai kuka suke   nablah zaune tana feeding din mazan duka biyu  zeenat km tana tsaye tana hada abinci yara a fidda.
shi km deeni yana tsaye rungume da bby girl dinsa yana jijigata sbd kukan datake ya saka mata lips dinsa abakinta yana Dan jijjigata har takoma bacci ya mannata ajikinshi  sannan ya koma ya zauna .
Ya jin yadda zeenat ke cigaba da rokon nablah Amman tayi mata banza taciga da feeding din yaranta tana jijiga kafa .zaune kawai deeni yake Dan  Bai San me zaice ba .
  ya kwantar daita zeenat ta karbi bby daya Daga hannu nablah  tashiga  bashi abincinsa.
ita dai ummi zuru tayi tana aikin binsu da ido kawai.
sbd al’amarin yarinyar ya daina bata mamakin ya dawo bata tsoro .
Haka ‘cikin daren ummi da deeni sukayi ta mata naci da rarrashi akan yaran .
nablah kema tamkar diyata nake jinki ‘cikin raina  sannan km bazan iya takuriki ba Amman  idan kinsa yadda  yaran nan  suke ‘cikin zuciyarta dakin mallaka manasu  Kai tsaye bazan taba gajiya gurin rokonki  akan kibar mana  su ba .

nablah tace uhmmmm azuciyarta , ummi kennan bazaki tabagane  value din yaran nan a raina ba  .
ni kaina bantabasani Haka yaya suke acikin zuciyar iyayensu ba Sai dayazo kaina .
wayan nan yaran sune duniya ahalin yanzu .. zeenat ma  sake   saka baki ciki nablah zan kular miki dasu Dan girma Allah kiyi hakuri kibar minsu wlh nafiki bukatarsu sannan Ina rokon ki Dan Allah kibari a dinga sauka da baby’s din nan kasa sbd Yan zuwa barka ..
Wani irin mugun kallo nablah tabi zeenat din dashi sannan tace nifa wlh bazan wani bayar da ya’yana ba .
duk me son ganinsu yazo sama idan ya matsu  Amman wlh  idan kuka takurani zan ban bar muku gidanku Gobe goben nan , Dan  nima wlh atakure nake daku.gaban deeni  ya buga da karfi  ya tsurawa Dan karamin  tsukaken bakinta ido .
  Muryarsa   a sanyaye yace nablah  no  duk zance Bai kai hk ba .
Ba Sai kinje koina ba ke zeenat gobe kiyi zamanki anan dakin kawai  duk me son ganinki da bbys  yazo nan yasameki. jikinta a sanyaye tace to shikennan my hrt.

+

Washegari gidan yacika tap da dangi tana ji yadda kowa yake fadar irin  kyawun yaran Amman wai macce ce  kawai   bata biyo deeni  ba suko mazan tamkar an tsaga kara ne dashi  .
Ita ko  nablah tana kwance su ummi gabadayan sun rasa gane kanta domin ranta a matukar bace yake taki yarda tayi magana da ummi ballanantana wata zeenat.
Barta   deeni ko kallo Bai isheta ba sbd magiyar dayake mata akan yaran aranta kuwa kwata kwata batason ta kara daidai da second daya agidan.
tunanin kawai yadda zata gudu take da yaranta ‘cikin sauki batare anganta ba ..


Tundaga ranar  duk yazo barka  ya nemi ganin baby’s Sai  dai subada uzirin Doctor yace bbys din suna bukatar hutu yawan daukar da’ake musu yana saka su zazzabi dare wasu sun yarda da zance Sai dai wasu basu wani amince ba .
km suka dinga cewa iyayi ne kawai irin Na deeni Dan duk sunsa sharrinsa ne …

Sosai ummi ke bawa nablah kulawa ita da yaranta  .ta gasata  sosai da sosai duk da kasancewar  nabla  irin matan ne  masu tsukaken jiki wayan da da  zarar  anagama cinsu suke hadewa take Amman duk da ummi Na kula da kasanta .domin zuwa yanzu ta hade gam tamkar ba itace ta haifo Yan uku ba .sosai km take da nuna mata yadda zata kula da yaranta.
Itama nablah duk abinda ummi tasanar tana  kiyayewa sbd  daman ita can me kaunar yara ce nawasu ma  ta bauta musu ballanantana nata .ita kuwa zeenat gabadaya fargaba da tunani hade da  tashin hankali ya maidaita wata iri .
tayi wujiga wujiga daita tayi wata irin rama tayi duhu  kallo daya zakayi  mata kasan tana ‘cikin taskon rayuwa da  tsaka me wuya. Yayinda kullun kwana duniya take like da nablah tana yi mata naci da magiya akan tabar mata baby’s din ta .ita km ta rufe idanunta taki wani lokacin idan abun ya isheta tasaka mata kuka .abu goma da ashirin Ga kewa gidansu datake Ga taushin hankali da fitinar zeenat.

Ta fanni deeni ma gabadaya ya susuce ya rame tsaye kawai yake da kafafunsa Amman zuciyarsa cike da rudani .
Tunda akayi haihuwar yagagara fita koina . abokansa sukayita zuwa taya Shi  murna  karuwar daya  samu .
Yayinda ,gida da office takoina ka kalli fuskar jama’a  murna haihuwar  manager  suke .
,sadaka kuwa deeni Yayi shi  har bai San iyakacin abinda ya raba ba .hutu sati guda akabawa ma’aikata companies har sai byn suna .

Fk ma yazo ganin baby’s da kyar deeni yasamu ya  karbi a gurin nablah yakai masa km har yakai su ya dawo dasu kuka take .tana ganin ya dawo mata da yaranta ta bar kuka datake  tana sakin numafashi da karfi da ajiyar zuciya ‘cikin jikin nasa  yakaraso gareta  yana cizan lips dinsa yace yanzu har rashin yarda takai Haka nablah ?Bazan cutar dasu domin nima sune duniyata kalli yadda kika dawo nablah akan yaran da nabaki ba .wata katuwar harara ta zabga masa sannan ta turo masa tsukaken bakinta gaba bangane yaran da  banawa ba? 
Kana ganin duk duniya akwai wanda ya isa Yayi claiming din yaran nan nashi ne ? +

Ya Dan yi murmushin takaici ya zauna gabanta ya tsotse lips dinta cike da shaukinki kaunarta yace akwai ubansu km mahaifi ko ba dade zai bayyana kansa garesu Amman dai kafin zuwansa kiyi hakuri ki bar min su.
Ranar da bbys suka cika kwana hudu da haihuwa  tafiyar gaugauwa taka ma deeni zuwa abuja  tun safe deeni ya tafi abuja amman aranar zai dawo.
,tunda nablah taji zance tafiyar sa .
Ta kasa zaune ta kasa tsaye .
hankalinta Yayi matukar  mugun tashi .
Duk ta frigice ..
taki sakarwa ruhinta salama  .


Karfe shida daidai 
deeni yashigo gidan kai tsaye  dakin jikin nablah ya nufa yana bude kofar yayi turus  jikinsa  a sanyaye  sbd ganin da Yayi nablah tsaye rungume da yaranta biyu akirjinta ,sannan  km dayan na goye abayanta tana jijiga su tana kuka su ummi da zeenat tsaye akanta  sunyi cirkocirko suna dubanta .Dan gabadaya sun rasa yadda zasuyi daita tun barin deeni gidan take a Haka .
baby’s din ma kuka suke sosai  tamkar sun San mamansu Na ‘cikin tashin hankali.

ahankali deeni yakarasa shigowa dakin sosai  yana bin su ummi da  kallo.
kana jikinshi narawa da zuciyarsa gurin cewa lfy ummi naganku hk ?
Ina fa lfy  deeni tun safe daka bar gidan nan  nake fama daita taki cin taki Sha  har zuwa  yanzu.
Yanzu  km mun shigo dakin  munganta goye da ya’yan .
da alamun shirin guduwa take ya runtse rikitattun idanushi dake cike da rudani  yana ambatar sunan Allah .
ya kamota ya zauna daita ya karbi yaya duka  ya kwantar dasu ya riko hannuta’cikin nashi yana kallon ummi da zeenat tare da yi musu alamar su fita.

Byn sun fita gabadayansu  ya Mike yaje ya rufe dakin tare da yiwa kofar key yana dawowa ya rungumeta gam ajikinsa kusan minti goma shabiyar suka dauka haka batare da yace komai ba suna sauke naunauyen ajiyar zuciya da shakar numfashin junansu.cike da tausayinta ya zareta Daga jikinsa yaje ya hado mata tea me zafi yakawo mata ta kar Tasoma sha ahankali Dan yanzu tafi yarda dashi akan zeenat da ummi .
muryasa’cik e da fargaba yace nablah ta dago shanyayyun idanunta tana kallonsa batare da ta  amsa.
Meke damunki ?
Tayi shr taciga da kurbar tea .
Ko wani abu su ummi suka miki ?Ta girgiza masa kanta .
Ya kamo tafin hannunta wanda yake empty yasoma murzawa ahankali ahankali  tare da tsareta da rikitattun idanunshi.
Muryarsa cike da laushi ya sanyaya ta sosai sannan yasoma mgn a tsanake  yace   ba ki min alkwarin zaki bani bby 
ba?
Ba  gori ba  ki tuna abubuwan alkhari dana miki nablah akanki Na mari matata ta sunana akanki Na kewa mahaifiyarta gardama Ya’yanki ba’a San usilinsu ba.
ba’a San tushensu ba Amman  naji nagani nace  karbi ‘cikin jikinki domin Na rufa miki asiri sbd kar duniya ta zage ki . +

,kin  tuna sanda kika yi ‘cikin nan ban Kiki ba nayi rayuwa dake tamkar matata ,Na kula dake da abunda ke cikinki . please nablah kada ki canza ra’ayinki akan alkwarin dakika min akan zaki bani su . jikinsa Na rawa yacigaba da cewa wlh  idan kika yarda kika  amince kika bani baby’s din nan  nayi miki alkwarin   zan mallaka miki gidan glass gabadayansa  zan mallaka miki  gidana  dake  ajawu estate zan maidake makaranta kicigaba da karantunki dakike buri .
zan taimakawa iyayenki Na canza musu rayuwa  zan ingata rayuwarki data ahlinki gabadayansu .
haka ya dinga kwadaita mata abubuwan alkhari  dazai mata .
nablah Ina son kisan wani abu ko matata ta sunnu bata taba zuwa sabon gidana Na glass ba Sai ke.
bantaba yin rayuwa da wata mace a duniya irin yadda nayi rayuwa dake ba .
Narasa tantancewar kaina da zuciyata shin sonki nake ko  km tausayin ne ko km sabo ne Amman mutane da dama idan Na tmbyesu suna gaya min sonki nake.
which’s kema kinsha gaya min haka.
Amman Ina karyata zuciyata nablah ki dubi Allah ki taimaka please ki bani yaran nan sake of me zuciyata tayi rauni dayawa gashi bata iya naci akan abu duk girma Amman yau tsawon kwana hudu Ina binki.
  sanadiyar wayan nan yaran bbu abinda bazan iya miki ba  arayuwa zan miki  komai Na rayuwar duniya r nan .
jan jiyar dake dadin duniya zan saki daukaka acikin duniya.
bazan taba barin ki wulakanta ba.
Duk abinda deeni ya mallaka naki ne hk  zuciyar deeni take ce please please nablah  ki taimaka please Haka ya dinga gaya mata Ward’s masu dadi da sanyaya zuciya as ended.
Ya zube kasa agabanta Yayi mata neildwon tamkar dai yadda zeenat tayi mata.
ya daura kanshi a saman cinyarta sannan ya sakala hannushi ya rungumeta gam ta baya muryarsa a raunane yace mata.
Dan girma Allah kiyi hakuri ki taimakeni ki rufa min asiri ni badan zeenat ba Dan ummi banason ki kunyata ummi sbd ta rigada tagama gayawa mutane zeenat haihu . Yanzu tunda abin yazama hk Kinfa sa kyautar mana da yaran shikennan   ki ba r  ya’ya kawai .
Amman Dan sbd dan kada mutane su farga su gane ba yaranmu bane .Ki aro mana su  Amman agurin ki zasu dinga kwana a lallaba mutane har ayi suna inyaso byn suna Sai a gayawa duniya da  mutane abinda zeenat ta haifa sun mutu har an binnesu ke km kina iya tafiya da yaranki .
Gabanta ya fadi jikinta ya dauki  rawa tace to.. to. shikennan Na yarda da wannan .
zan muku alfarma har ta wata daya a gama rurumar suna da barka Sai dai fa wlh da ya’ya zan dinga kwana kmr yadda kace.
zuciyarsa cike da farinciki samun nasara da Yayi yau  yace Na amince .
to kira  ummi da zeenat ka maimaita agabansu gabadayansu suka shigo dakin byn kiran da deeni Yayi musu  ta waya. +

Ahankali cike da natsuwa  ya maimaita yadda sukayi da nablah ummi zatayi mgn da zeenat Yayi saurin yiwa ummi sigina da idonsa  alamun kada suce komai take kuwa  suka yi shiru.
suka hau  cewa shikennan mun yarda da wannan tsarin … gabadayansu da ummi da zeenat har deeni suka tabbatar mata da sun  Yarda akan tsarin…



Uhmmmm to ko yazata kaya tsakanin deeni da zeenat har uwar gaya ummi 🤔🤔

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *