WAYE ANGON CHAPTER 10 BY MARYAM JAFAR KADUNA

WAYE ANGON CHAPTER 10 BY MARYAM JAFAR KADUNA

 

Imran yake fada, shin cikinsu waye na gaibun waye tabbas?

Zuciyarta ta cunkushe tai mata nauyi har daci-daci

take ji, madadin kalamansa su sanyaya ranta sai ma suka

Kara ingizata har dai suka gama wayar bata samu wata

nutsuwa ba,

Sha daya da rabi na dare Imran ya dawo, sam mutane

basu bar shi ya huta ba tun yau kenan a gajiye ya shigo

gidan kai tsaye dakinsa ya sauka ya rage kayan jikinsa

ya dan watsa ruwa ya dora jallabiya ya sanyo slipas ya fito.

À filo suka ci karo da Momy, ta ce

“Ka dawo

kenan?”

Ya ce yana sosa keya

“Eh shigowata kenan

mutane suka rike ni.”

Tace,

“Akwai haka kam, hidimar kenan. Abinci fa?”

Ya ce,

“Ban ci ba tukunna, yanzu dai zan ci.

» Ta ce,

“Ok, kaje ga shi can a dining naka kadai na ce a aje can.”

Ya ce,

‘«To ya Jama’a sun fara taruwa ko?” Ta ce, “Ai

kuwa an gaji wasu sun kwanta wasu kuma ga su can suna hira,

Ya yi murmushi ya mike ya nufi dinning din yana cewa,

“Daddy fa bai sauka ba?”

• Ta ce, Eh sai gobe,

mun yi magana da shi a waya har ya zo airport kuma ya

koma, amman idan komai yai clear zai taho gobe in

kuma sai jibin to

Ya zauna yana cewa “Ya kamata dai yana nan aka

daura auran, ban so tafiyar nan America ba ko da ya fada

min sai da gabana ya fadi.”

Ta ce, “Ai ko ko shi haka yace bai so ba. Yafi son

yana nan ake hidimar komai, amman ya ce ko bari ne sai

ya yi yazo ranar daurin auren akwai abokanshi da za suZo wasu ma Turawa ne da Larabawa, yana da kyau kuma

suhadu.

Har ya gama dai suna hirarsu, daga bisani suka yi

bankwana ya shige dakinsa ya kwanta saboda gajiya

bayan ya cire jallabiyar jikinsa.

Dare ya fara, sam! Ta kasa bacci, sai juyi take

damuwarta ta hanata bacci da bakin ciki, tuni Rafiatu

tayi baccinta har tana munshari.

Imran shi kadai ya zama matsalarta da babu shi tana

jin bata da damuwa, duk shi ya kunna wannan fitinar, da

bai ce yana sonta ba hankalinta kwance.

Ya zama kadangaren bakin tulu, yanda Momy ke

sonshi da alama ba ta sonta haka, tunda ta zabi farin

cikinsa a kan nata. Yanzu in ban da don ya kona mata rai

meye na wani Kirkirar party?

Bayan ba shi da tabbacin shine angon. Me yasa bai

hana su ba ya nuna ba ya so? Yana son ta ba shi kunya kenan?”

zuciyarta ta bata shawara, don haka bata yi

tunanin komai ba ta diro daga gadon ta fice daga dakin.

Dakinshi ta tunkara sha biyu ta gota, kofar a bude

take tana taba handle din ta bude.

Bai samu ya yi bacci ba a lokacin yana dauke da iPad

suna magana da wani abokinsa ta social network daga kasar Saudiyya.

Kwatsam! Yaga ta shigo masa, abin ya ba shi

mamaki matuka, yarinyar da ta tsane shi ko kallonsa ba

ta yi, to me ya kawo ta dakinsa a wannan lokacin?

Daga shi sai shortniker ba ko singileti. Ya yi saurin

mikewa yana cewa,

‘”Subhanallah! Mabaruka lafiyarki

ki ka shigo min daki babu sallama?”

Ya jawo

jallabiyarsa ya saka don kare mutuncinsa,

Ya ci gaba “Ba kya tunanin a ya za ki same ni wanda ba zai miki dadi ba?”

Ta zumburo baki daga in da take tsaye jikin kofa tace.

«Ni ina ruwana, wannan ba shine gabana ba.”

Ya yi murmushi ya ce,

“Ok! Naji to meye gabanki?”

Tayi mai banza tana turo baki. Ya sake cewa,

“Mabaruka

menene?” cikin kulawa.

Ta ce tana kumburi

“Magana nake so muyi.” Ya ce,

“Da ni kuma?” Ta yi masa banza. Ya sake cewa makiyin naki?

* Yana murmushinsa mai kyau.

Ta ce cikin fada,

“To in ba da kai ba da wa zan yi?

Dakin wa ka ga na shigo?” Ya ce,

“Kiyi hakuri to dakina

ne, naga ko muryata ba kya son ji bare ki ce kina son magana da ni.”

Ta ce cikin Kufula ba tare da ta kalle shi ba. “Ni ba

nazo nan don in ja magana ba da surutai marar ma’ana

bane kawai nazo ne na taimake ka.

Ya kalleta da kyau ya ce, “‘Ok, bismillah zo ki zauna ga kujera.

“Ya nuna mata kujerar da ke facing din shi. Ta

juyo tana harararsa ta ce,

“Ba zama ya kawo ni ba, ka

daina tunanin zan iya zama dakinka Ya yi murmushi yaCe,

“Maganar ba ta da

muhimmanci kenan tunda a tsaye za a iya yin ta. A zatona tana da girman da za a girmamata,

» Yana rufe baki ta dauka.

“Na gaya maka ban zo nan ba don surutai marar ma’ana ba, ka saurare ni kawai

Ya nisa ya ce,

, “Ok, kin ce ni za ki taimaka, to na gode

kije kawai idan har ba za ki iya zama ba, ba zan iya

saurararki ba kina tsaye ina zaune, kin gane ko?”

Ta harare shi cikin tsananin jin haushinsa har ita zai

wa barazana, don haka ta kulu kawai ta juya fuuuu ta fice

HMmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *