WAYE ANGON CHAPTER 4 BY MARYAM JAFAR KADUNA

WAYE ANGON CHAPTER 4 BY MARYAM JAFAR KADUNA

 

daga cikinsu take yi ba. Haka nan dai cikin sanyin jiki ta

danne tare da kaiwa kunne tana sallama.

Daga can ya ce,

“Kina ina ne ba mun yi da ke yau

za ki dawo gida ba?” Ta yatsina fuska tace,

“Ni gaskiya na fasa ba abinda zan yi a gidan.

Ransa ya baci,

“Zan ci mutuncinki fa Mabaruka! Kin

maida ni abokin wasanki ko? Tun yaushe mu kai

maganar nan da ke? To ki maida hankali wallahi ki taho

yanzunnan ga Jama’a nan

sun fara taruwa ana

tambayarki, na fada miki. ” Daga haka ya datse layin.

Zuciyarta ta cunkushe tayi shiru ta rasa me zata yi.

Rafi’a ta ce, «Ya kuka yi da shi?”‘ Ta fada mata komai, Tace,

“Ai ba damuwa sai mu wuce tunda an kusa gamawa.

• Nina ma manta da yau ne wa’azin, duk damuwarki ta rikita ni.»

Sai da suka gama sannan suka fito. A kan hanyarsu

Ne a ka sake kiranta. Wayar na hannun Rafi’atun ta duba

taga Mama (Maman Mabarukan), don haka da sauri ta miko mata tana cewa “Karbi Mabaruka, Mama ce.

Harararta tayi ta Kara yin gaba, har wayar ta yanke ba

su dauka ba. Sai a karo na biyu ganin Mabarukar taqi

karba yasa ita ta dauka. Suka gaisa da Maman ta ce, “Ina

Mabarukanne?” ta ce,

«Gata nan wai taki karba ranta ya

baci.

“Maman ta ce, “Ki bata wayar.” Tace, “To.

Ta mikawa Mabarukan ta amsa tana zobara baki.

Daga can ta ce,

“Zan ci ubanki fa Mabaruka, wacce irin

kafaffiyar yarinya ce ke wai? Kina son ki bani kunya

ko? Jibi daurin aure amman ba kya gida, wacce tsiyar ki

ke yi a waje?”

Mabaruka ta ci gaba da turo bakin ba tare da ta ce

komai ba. Maman ta ci gaba da cewa, “Wallahi, kiyi

marmaza ki taho yanzunnan, tun kafin ranki ya baci.

Zan turo Imrana yazo ya dauke ki, kina gidan su Rafiar?”

Cikin gunguni ta ce,

“A’a muna saloon,

.” Ta ce, “Tò

zai kira ki ki fada masa inda kike.” Daga haka ta yanke

layin.

Haushi, takaici da bakin ciki suka tokare ta. Sakin

wayar tayi tayi gaba abinta cikin tsananin fushi. Rafi’ar ta tsugunna ta tattara wayar ba tare da ta ce komai ba,

sannan ta biyo bayanta. Tafiya kawai suke ba me

magana har suka iso.

A kofar gida suka gamu da Baban, ya fito da butoci

za suyi alwalar sallar Magriba tare da mutanansa.

Ya kirata taje tana bata rai, ya dubeta a tsanake ya ce,

“Menene naga ranki a bace?” Bata jin akwai amsar da

zataiya ba shi. Ya kara nanatawa. Ta ce “Ba komai, kaina

ne yake ciwo.

Ya kalleta tsaf! Ya fahimci ko menene, amman ya ce,

“Ciwon kai kuma a wannan lokacin bai kamata ya dame

ki ba. Ke da ke Kokarin zuwa gidan masoyinki?”

Ta kalle shi kallon bai san me yake ba. Shi a

tunaninsa har wani farin ciki zata yi? Da babu wata

harkalla a daura auren da shine zata yi farin ciki,

amman wannan auren da cikinsa yake da fitintinu.?

Ya katseta “To ki je ki sha magani. Tun dazu a ke jiranki har an gama taron amman akwai sauran Jama’a

cikin gida ki isa kwa gaisa.

.” Bai gama rufe bakinsa ba ta juya ta wuce don ta gaji da maganarsa.

Gidan ya fara daukar harama da ‘yan biki, ‘yan

kauyensu duk cikin mutanen babu dangin Mamanta ko

daya, daga nashi sai na Inna matar Babanta, su ke ta. hidimarsu.

Da shigarta ma su tsokanarta nayi ma su janta nayi,

babu wanda ta saurara suka shige dakinsu ita da Rafia.

Ta fadi zaune jagwab tare da dafe kai ta ce, “Na shiga

uku ni Mabaruka, da gaske dai ne?” Idanunta suka yi

rau-rau zata yi kuka. Kafin Rafiatu tayi magana wayarta

ta hau kuka ta duba, Imran ne. Ta kai kunne tare da cewa

“Hello!”

Daga can ya amsa suka gaisa yana tambayarta

“Mabaruka fa? «Ta ce, “Gata nan kusa.” Ya ce, “Ok! Ki

ce mata gani nan kan hanya ina zan sameta?” Ta ce,

‘Muna nan gidan Babanta.

Ya ce, “Ok, ga ni nan na kusa.” Ta ce,

“To.” Tare da

kashe wayoyinsu, ta dube ta ta ce, “Ga Imran nan kan

hanya ya kusa.”

Ta dube ta da rinannun idanunta ta ce, “‘Wai yazan yine Rafi’a? ina zan sa kaina?”

Tayi shiru tana kallonta cike da tausayinta, ta ci gaba

“Shi ya kira ni lallai in taho nan ita ma ta kira ni lallai in

tafi can, har ta turo shi ya tafi dani wai ya ake son nayi?

Sò suke su birkita min kwakwalwa don Allah??

‘Ta cè, “‘A’a wannan duk mai sauki ne, tunda mun zo

nan din ya gan ki sai ita ma muje can din tunda ita uwa

ce mace, me yiwuwa akwai wasu abubuwan da zata ba

ki daman abin da ya kamata kenan daidai wannan

lokacin kina tare da ita, don yi miki shiri mai kyau

wanda shi Baban ba zai yi ba, ko kin zauna a nan ba abin

da zai miki, to gwanda maki tafi can din kawai.

Ta jingina da bango tare da cewa,

“Oh! Ya Allah ka

kawo min dauki cikin gaggawa, kai kadai ka san me

kenan, kai kadai ka san abin da zai faru. Ya Allah ka

kawo min komai da sauki.”

Gidan a cunkushe yake da Jama’a, daman ga shi a

kuntace. Dakuna biyu ne ko kitchen babu.

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE www.Dailynovels.com.ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *