WAYE ANGON CHAPTER 6 BY MARYAM JAFAR KADUNA

WAYE ANGON CHAPTER 6 BY MARYAM JAFAR KADUNA

 

 

‘saboda ciwo.

Tana kukan ta ce, “Don Allah Momy ki tausaya min

ki janye maganar auran nan, wallahi ina cikin tashin

hankali kar ki sa ni cikin masifa, ban taba son Imran ba

ko sau daya a rayuwata.

Shine mutum na farko da na fara tsana, wallahi ko

muryarsa ba na son ji bare in gan shi, har ta kai ni kuma

ga auranshi. Wallahi zan cutu Momy, don Allah ki janye

ki bar ni da Sulaiman.

Ranta ya baci, ta ci gaba da harararta, taja tsaki

“‘Maganar banza kenan, ni so ki ke in yi magana biyu?

Tun yaushe sadakinki ya zo hannu! Ko so kike girma da

mutuncin da Babansa yake ganina da shi ya zube?

Tun yaushe muke maganar nan? Na fada miki na

nanata miki, wallahi ba ki da miji sai Imran, shi na zaba

miki, ban ga aibunsa ba, nutsuwa, hankali da tarbiyya ga

ilimi, to me kuma a ke nema?

Ina da tabbacin wallahi babu gidan da za ki samu

kwanciyar hankali da nutsuwa sai gidansa. Imran yana

sonki, yana tausayinki, ya kuma damu da ke. To don me

za ki ce ke ba kya sonsa? Alhalin an halicci zuciya da son

mai kyautata mata!

Don haka ki sa shi a ranki, ki so shi ki dauka tuni shi

ne mijinki. Ko yau na fadì na mutu wallahi ban yarda ki

auri wani ba sai shi, shi nake so da shi na yaba

Mabaruka ta zauna rajab! Saman lafiyayyan gadon

mai lallausan zanin gado, ta ce “Ni kuma ba za ki duba

abin da nake so ba, zuciyata take so ba? Taki ki ke

dubawa?

Momy zuciyata zata yi daci, zan dawwama da kunci

karshe ciwo ya kama ni na mutu. Sulaiman shi kadai

nake so, duk abin da ki ka lissafo na Imran, Sulaiman

yana da shi har ya fi shi.

A gidansa ne zan fi samun kwanciyar hankali da jin

dadi, shine kadai zai ba ni farin ciki ba Imran ba.”

Ta kalle ta da kyau ta ce,

“To ni kuma ban amince ba,

idan har ni na haife ki ya zama dole ki bi abin da nake so

kiyi kuma.

.” Ta ce,

“To shi kuma wanda ya za6a min

Sulaiman waye shi gare ni in ke Mahaifiyatace?”

Kai tsaye ta ce,

“Ubanki mana. Hakan yasa ban

yarda da za6inshi ba nawa nake so.

Ta ce, “Shi mahaifina ne shi na saba mishi kenan ke

Nabi abin da kike so?”

“Kwarai kuwa, don ni na haife ki nayi renon cikinki,

nasha wuya wajen haihuwarki ko na mutu ko na rayu,

haka na haife ki naci gaba da renonki ko na ci ko ban ci

ba sai na ba ki kinci kin sha fa.

Duk bai gabansa, sai ya ci sau goma ke bai ba ki kin

ci sau biyu ba, amman ni bani ci ke ba ki ci ba asalima

nafi son ke kici akan ni naci. Nafi sonki a kanshi, yanda

yake sonki nafi damuwa da ke a kan shi.

Koda wasa ma ba za ki hada uwa da uba ba, Annabi

ya ambaci uwa sau uku sannan ya ambaci uba sau daya,

don haka dole ni za ki wa biyayya kafin shi in har kina

neman albarka, kuma zabina ba aibu ba ne alkhairi ne

gare ki, ba make kadai ba har ga mahaifin naki.”

Ta dafe kai ta Kara fashewa da kuka har yanzu ta kasa. fahimtarta, shin ya zata bullo wa al’amarin nan?

Anti Karima ta shigo kanwar Momy ce ta bisu da

kallo, sannan ta ce “Har yanzu dai maganar nan ba ta

kare ba Mabaruka?”

Ta dago tana kallonta da jajayen idanunta, tà ce

“Yaushe za ta kare Anti, bayan ni kadai nake hango

tashin hankalin da za a jefa ni.”

Ta zauna tana cewa,

“‘Auran Imran dinne tashin

hankali? Ke ba ki gani kin san kuwa irin jin dadin da za

ki samu gidansa? Ko kayan da ya hado miki-ya isa ki

sauke makamanki uwa uba gidan da ya kera miki

saboda ke kadai kawai yana sonki yana kyautata miki,

kuyi aurenku ku fita Kasashe jin dadinku da hutu.

Amman duk wanna bakya hangowa kin

gwammace ki auri wancan Talakan Malamin

Makarantar wanda kafin albashinsa yazo ya cinye su da bashi?

To me yaci ya ba ki ya ba abokiyar zamanki? Ga uwarsa ga kanwarsa, to bare mu in muka zo me zamu

samu gidan bushe ke bushe? Duk ba ki duba wannan ko

Mabaruka?”

‘Ta kalleta kamar ta mare ta, ta ce “‘Wannan ni ba shi

ne gabana ba, ba shi nake so ba. Ni shi nake so shi kadai,

shine farin cikina da kwanciyar hankalina.

Arziki kuma wannan na Allah ne, zai iya azurta mu.

Shi Imran din da ku ke magana ba zai iya min abin da

Sulaiman din zai min ba, ba shi da abin da nake so daga

gare shi.

Gidansa zai zame min tamkar akurki, dukiyarsa bata

taba burge ni ba wallahi, don ba za ta bani farin cikin da

nake so ba.

Ta ce,Ke yarinya ce sakarya, za ki gane gaba ba ki

da hankali tukunna, wake kai kansa ga talauci? Kowa

yana neman tsari dashi,

Domin kuwa Annabi (S.A, W) ma yana neman tsari

da shi, kowa inda zai huta yake so. Son banza shirme akwai abin da ya kai kudi? Ai so shi ne kudi, in da kudi

komai lafiya daidai ne, kudin su ne za su bada farin ciki

HMMm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *