ALKAWARIN JINI CHAPTER 11 BY _HAWWA MUH’D USMAN

ALKAWARIN JINI CHAPTER 11 BY _HAWWA MUH’D USMAN


               Www.bankinhausanovels.com.ng 

Har jirginsu ya sauka a New York Sabina bata farka ba kuma still d’in tana cikin jikinsa,sai dai time to time ta sake gyara kwanciya ko shi ya gyara mata,,izuwa lokacin kam duk wani sauran hak’urin da Hammad yake jin yana da shi da y’ar dauriyar data masa saura tuni ya nemi k’arewa,har ta kai shi ga komawa addu’ar su sauka lafiya haka nan,cos shi dai ya sani ba zai iya ci gaba da jurewa ba,kuma har ga Allah yana ji idan aka ce zasu k’ara sama da wasu y’an awanni tabbas zai iya yin abunda ba shi kenan ba.

      Da misalin k’arfe 9:00pm a gogon na Nigeria wanda yayi dai² da 3:00pm a agogon k’asar ta U.S,wanda idan muka lissafa tazarar dake tsakaninmu da su zai bamu adadin rata na awanni shida,jirginsu ya sauka a katafaren filin tashi da saukar jirage na *LaGuardia airport* dake nan cikin New york City d’in,,sannu a hankali jama’ar dake cikin jirgin wad’anda suka farka daga nauyayyen baccin daya d’auke su har zuwa wad’anda suke ido biyu a lokacin sai kowa ya hau kimtsa jikinsa saboda jirgi ya riga ya sauka k’asa har an bud’e k’ofar fita,,sai a lokacin da jirgin ya samu damar isowar sannan ita da kanta ta tashi ba tare daya tada ita ba,,jinta kwance a jikin abu yasa sai ta d’an bud’e idanunta da sauri,kwance ta ganta sadidan a saman k’irjinsa,,tunanin lokacin data shige masa ta fara,sai dai iya son ta binciko lamarin ya gagari tunawarta,d’an motsawa tayi a hankali sannan ta d’ago kanta ta kalleshi,hakan da tayi sai ya tabbatar masa ta farka nd tana so ta tashi,hannunsa daya zagayeta da su ya zare ba tare da yayi magana ba,a hankali itanma sai ta mik’e duk a rikice saboda irin kallon da su Jannat suke binta da shi,zumbur kuma ta wuce ta nufi hanyar toilet d’in cikin jirgin,,a hankali mutane suka fara fita cikin nutsuwa,,Hammad kam tunda ta tashi bai samu damar motsawa ba,sai da yaga fitowarta sannan ya tashi suka kamo hanyar fitowa a taren,a wajen suka iske su duka suna jiran fitowar su,bayan an gama musu duk wani checking sai suka tattara da su da kayansu suka bi cab’s da zasu kaisu gida.

     A cikin mintuna k’alilan suka iso mid Manhattan dake a fifth avenue nan cikin birnin na new York,,tunda suka shigo cikin arean 56th street yanayi yadda tsarin unguwar da gine²nsu suka kasance masu dogayen benaye gwanin burgewa duk sai suka ji suna matuk’ar son tsarin gurin,daga *SABINA* har su kansu duka sauran y’an matan sai suka ji gurin yayi musu sosai,musamman kuma daya zama quite place ne babu ruwan wani da wani kowa harkar gabansa yake,kallon tsarin gurin ta sake yi a hankali sai ta lumshe idanu tana shak’ar sanyayyar iskar dake busawa mai tattare da ni’imomi tana murmushi,lokacin da cab d’insu ta samu damar tsayawa a carline dake gefen k’aton ginin na *TRUMP TAWER* sannan ta samu damar bud’e idanunta suka fita,tana fitowa sai ta sake d’aga kanta tana kallon ginine²n,ita dai tunda take ko da da yake basu cika yin nisa daga cikin skul d’insu ba a iya zuwanta sai take ganin kamar bata tab’a ganin gini irin wannan ba,har bayan an sallami masu cab da suka kawo su bata sani ba,tana can kallon ikon ubangiji da kallon ginin da suke tsaye a gabansa da yake da hawa² masu matuk’ar yawa,nd ya kasance anyi shi ne da wani irin concrete construction na dark glass curtain wall,daga can d’an nesa kad’an ta saman entrance na ginin harda wani design da aka masa ya bada wasu stepped facade,su kansu kuma stepped corners d’in dake jikin ginin sai aka yi filling d’insu da wasu irin shuke² masu kyau,sake d’aga kai tayi a hankali ta kallo can k’ololuwar samansa,tsabar nisan da taga yayi mata sai ta juya ta kalli sauran dake gefe da gefe da basu kai shi ba,kanta taji ya fara neman juyawa a hankali sai ta sauke idanunta k’asa dan kallon gine²n yasa ta fara ganin kamar zasu ruguzo mata a kai,a ranta kuwa tambayar kanta take ko ginin zai kai hawa nawa.? Cos ita dai a iya d’aga kanta da tayi bata iya gane ko hawa nawa ne da shi ba,,security ne a ko ina barbaje suke tsaron gurin suma saboda yawan su har ba’a cewa komai,da yake a cikin ginin akwai gidan shugaban k’asa Donald Trump a mafi k’ololuwar nisa na gidajen,,gaba d’ayan su suka wuce entrance bayan k’ofofin gurin suyi scanning nasu,suka shige zuwa in da elevator da zai kaisu floor d’in da suke yake,su dai duka suna gefe,Hammad da yake shi ne a kan gaba shi yayi komai,su kam suna ta kallon ikon rabba,,sai da suka zo 32nd floor sannan elevator ya tsaya,k’ofa tana bud’ewa suka fice,basu yi wata tafiya mai nisa ba tsakani suka iso inda gidajen su yake,,y’an mata da basu san kan gari ba suna ganin su cikin wannan mansion d’in nan suka tsaya kallon tsare² sai dai gently suke yi ba wai yadda za’a kallesu a matsayin k’auyawa ba,,d’aya daga cikin gidajen dake jere suka tsaya,bayan Hammad ya bud’e k’ofar suka shige d’aya bayan d’aya,k’aton parlor ne suka fara tararwa da ak’alla zai ci saitin kujeru biyu ba tare da wata ta matsi wata ba,daga can gefe guda kuma dining area ne da aka masa wani mugun k’awata,sai 2 bedrooms daga cikin wani corridor da kitchen wanda k’ofarsa take ta wajen dining arean,opposite da k’ofar kitchen d’in kuma wani irin dark glass ne daya mamaye fiye da bango guda na parlor’n wanda mutum zai iya hangen wasu guraren da dama a cikin arean fifth avenue da wajenta ciki kuwa har da apple fifth avenue,yanayin tsarin gurin gaba d’ayansa ya kasance duniya ne,ta ko ina ya gama tsaruwa har ba’a cewa komai,komai na more rayuwa kuma a kwaishi a cikin gidajen.

     Bayan sun gabatar da sallolin da ake binsu cikin jam’i sai da suka huta tukun,a lokacin tuni har su Sultan sun gama shawaran zaman su Jannat a nan gurinsu,ma’ana a d’aya daga daga cikin nasu saboda sun san idan suka barsu suka tafi Sabina ba zata tab’a jin dad’i ba,shi yasa sai suka yi wannan shawaran without ma sun sanar da Hammad,su d’in kuma sai suka tsayar akan sai su zauna a guda d’ayan ciki na Sultan ko kuma na Sadeeq,,shi kuma Hammad dama zasu zauna ne cikin nasan,da yake dama a gidan nasa suka sauka ko da suka zo,bayan sun gama shawarwarin,sai da suka sake tab’a hira,sannan Sultan yace su tafi gida idan sun huta zuwa anjima sai su wuce Market su duba kayan amfani,,sallama suka yi musu sai suka fice kowa jaye da kayansa,,suna fitowa Sultan sai ya bawa su Badra key d’in gidan da zasu zauna wanda yake opposite da na su Sabina,su kuma suka nufi d’ayan da yake gefen nasu,sai da suka sake yin sallama dasu har kamar baza su sake had’uwa ba sannan kowa ya shige gida.+

      A gidan Hammad kuwa lokacin da suka zo tafiya zaraf Sabina tayi zata bisu,shi ko gogan tun da suka shigo bayan da suka yi sallah ko tari bai sake yi ba jira kawai yake su bashi guri,cos shi dama ba mutum ne daya cika son shiga hayaniya ba,shi yasa duk sai yake jin ya takura da zamansu a nan d’in,lokacin da tashi tafiya ma har wani murmushin farin ciki ya ajiye,suka yi sallama da su,har sun kama hanyar fita a lokacin ya hango ta tana niyyar binsu,wani irin kallo ya mata a nutse sai yake raya yadda zai yi da ita idan ta shigo hannunsa dan ya fahimci dole ne sai ya saita mata hankalinta,idan kuma har baiyi hakan ba muddin zai sake mata fuska duk abunda take so tayi tofa lallai ne zata jashi a k’asa,,har suka fice bai yi magana ba sai daya bari duka sun gama fita ita ce a bayan tana k’ok’arin fitar itama sannan yace

      “Ina zaki je ne yanzun.!?”

      Juyowa tayi da sauri tana kallonsa fuskar nan a had’e kamar bai san yadda ake dariya,itama sai ta gimtse tace

      “Binsu zan yi.!”

     Murmushi yayi a ciki da fad’in

   “Idan kin bisu kiyi musu mene ne..!?

  

   “Toh ai gani nayi tare muke ko can a skul ma bare nan..”

   A hankali ya jinjina kai yana sake k’are mata kallo mai tattare da y’an sak’o sannan ya taso ya nufo inda take,tunda ya tunkarota take jin gabanta yana tsananta fad’uwa har ya iso daf da inda take tsaye sai ya rik’o hannunta gently yana cewa

    “Muje.!” Yana sake binta da kallon k’asan ido,k’wace hannunta tayi saurin yi daga rik’on da yayi mata tana fad’in

   “Nifa saina bisu,kawai ka kyale nima na tafi tare da su…”

   Murmushi yayi mai sauti k’asa² sai yace

   “Lallai ke yarinya ce,,idan banda shirme ma irin na yarinta ko cewa nayi je ki,ai kya ce min A’a,amma wai kece har da zak’ewa zaki bisu,to ki bisu kiyi musu mene ne a can d’in.!?”

  

   “Toh ni nan d’in idan na zauna mene ne zanyi.!? Naga dai ai can d’in ya ishemu duka,ba sai na zauna a nan ba..”

   Gira ya d’age sama yana kallonta,deeply maganarta na sake reversing da tace idan ta zauna nan d’in me zata yi.? K’wafa yayi a ciki shi kad’ansa ba tare daya bari taji ba,still sai yayi magana a zuci da fad’in “da sannu zaki ga abunda ya ajiye ki a nan,,zan gwada miki abunda za kiyi min idan kin zauna”,a zahiri kuma sai ya tsinci kansa da fad’in

       “Sure..!?”

     Sai tace masa

      “Ehhh.!”

     Jinjina kai ya sake yi then cikin gatse yace

        “Ok.! U can go..!”

  

     Juyawar tayi kamar yadda yace zata fita,cikin mamakinta yayi saurin fizgota ta dawo,a jikinsa ta fad’o cikin tsoro,shi kuma sai ya kai k’afarsa kan k’ofar ya tura da k’arfi yana sake had’e rai,cos ya fahimci sai ya nuna mata waye shi kafin ta nutsu,a hankali k’ofar ta tafi ta rufe without ta bada sound da zai tayarwa mutum hankali duk da da k’arfi yayi pushing d’inta,idanunta ta fara k’ik’k’iftawa cike da tsoron yanayin da suke,shi kuma ganin duk ta diririce masa sai yasa shi sassauta muryar sa cikin hikima yace

   “Lady.! Kin sallama ni ne da kike k’ok’arin guduwa ki barni ni d’aya.!?”

    Girgiza masa kai tayi alamun “A’a” a hankali ya had’iye wani irin salivary sannan ya sake cewa

       “Me yasa to kike son binsu.!? Ko har kin manta ke matar aure ce yanzun.??”

   

     “Ni ban manta ba,,kawai dai ina son binsu ne na zauna tare da su.!”

   

     “Uhmmm! Me yasa kike tunanin k’aura ce min,al’halin kin san yanzun ne lokacin daya kamata ace mun kasance tare.!?”

      Sunkuyar da kanta tayi k’asa tana d’an wasa da yatsunta,cos bata san takamaiman amsar daya dace ta bashi ba,yana ganin tayi haka yasan da wuya ta sake yin magana,sai shima d’in ya rufe batun da cewa

      “Shi kenan muje na taimaka miki kiyi wanka sai mu kwanta mu huta ko.!?”

      Ya k’arashe batun da rik’o hannunta yana janta suka fara tafiya,saurin k’wacewa ta sake yi tana ja baya,sai ya juyo kad’an yana kallonta kafin ya samu damar tambaya

      “Mene ne kuma.!?”

     K’ik’k’ifta masa idanu tayi tana b’oye hannunta a baya da fad’in

      “Ni ba sai nayi wani wanka ba nayi kafin muzo.”

     Murmushi yayi sannan yace

      “I knew ai,,so nake ki sake yin wani yanzun,cos zai taimaka wajen warware miki gajiya’n da kika kwaso..”

     Kai ta sake girgizawa tana ja baya kamar wacce take shirin zurawa a guje

      “Nifa bana son yi ne,kai dai kaje kayi..”

    Duk iya yadda Hammad yake tunanin shawo kanta da sauk’i sai da abu ya gagara,dole ko da ta kaishi bango ya b’ata rai yana nuna mata inda yake tsayen ya ce

      “Zo nan..!”

      Kafad’a ta mak’ale idanunta duk sunyi rau² tana shirin yi masa kuka,tausayinta gami da tsumammiyar soyayyarta da suka fara neman kama shi,a hankali sai ya tab’e baki kuma,tunawa da cewar idan har ya biye ta tausayi zasu yi ta rayuwa ne a haka,k’arshe kuma shi zai ji jiki ba ita ba,sake kiranta yayi ta kuma mak’alewa wannan karon fuskarta cike da wani mugun pampering,sake had’e rai yayi duk da yasan abunda takewa gudun amma sai yayi kamar bai gane ba duk dan ya samu d’in ta zo

      “Ki zo nace.! Me zan miki ne da kike tsoro.!?”

   

     “Allah ² ni dai bazan zo ba.. Haka kawai sai kace sai na zauna da kai..!”

     Idanunsa ya lumshe ba tare daya bud’e su ba yace

      “Idan kika bari na bud’e idanuna baki k’araso ba,Allah za mu samu sab’ani..”

   

    Bata iya sake yi masa musu ba saboda jin ya rantse mata sai ta matsa d’in kamar yadda yace cos ita duk yau ganinsa take ya zamar mata wani abun tsoro²,a hankali cikin mutuwar jiki bayan ta iso gabansa ta tsaya duk da kamar bata son yin hakan ne,sai kuma ta tsinci kanta da fad’in

        “Gani toh.!”

     Cikin muryar kuka²,ajiyar zuciya ya sauke a hankali sai ya bud’e idanunsa ya sauke su a kanta,hannunsa kawai ya mik’a mata fuska babu wadataccen fara’a,a nutse ta rik’e shi sannan suka juya suka bar wajen,sai da ya kaita bedroom bayan ya sata tayi wanka sannan ya sake fita ya barta,parlor ya koma ya d’auko kayanta da nufin ya shirya mata su cikin closet,tana ganin ya shigo tayi saurin mik’ewa dan tun da ya fita ya barta bata matsa ko nan da can ba,a zatonta ko da taga ya fitan sai bata kawo zai dawo da wuri ba,kallonta yayi ya girgiza kai kawai cikin takaicin ta,ba tare da yayi mata magana ba sai ya wuce zuwa jikin wall d’in d’akin ta gefen dama,itama ko da ya dawo d’in da ta ganshi jaye da luggage’s d’inta sai tayi tunanin  zai ajiye luggage’s d’in ne kawai ya fita,buh sai taga ya danna wani d’an bottom a jikin gurin da yake tsayen,k’ofa ta gani tayi gefe guda wani had’ad’d’en reach-in closet ya bayyana,sakin baki tayi tana kallon ikon Allah dan ita dai tinda ta shigo ta ga gado sai mirror,amma bata tab’a tunanin akwai ma’adanin kaya ba,ganin irin wannan ma’adanin kayan kuma sai ya maida ita y’ar k’auye cos bata tab’a ganin irin sa ba,bisan bed ya d’ora kayan daya fito dasu,tana tsaye tana kallonsa yayi ta mak’ala su jikin jikin hanger,har ya gama shirya su tsaf a ciki,still tana tsaye bata bar gurin ba tana kallonsa,,matsowa yayi inda take tsaye tana kallonsa ya rik’o hannunta zuwa bakin bed,shi ya cire mata vail d’in dake kanta ya ajiye d’agowa tayi tana kallonsa,sai ya sake had’e rai ba tare da ya kalleta ba ya rage tsayinsa yana k’ok’arin d’ago gown da take sanye da shi,saurin rik’e hannunsa tayi tana fad’in

     “Me kake shirin yi min ne wai..!?”

    Hararar ta yayi sannan ya janye hannunta zuwa gefe

    “Me nace kiyi kika tsaya min a nan kina kallo na kamar kin samu cinema.!?”

    K’ik’k’ifta idanu tayi ba tare data bashi amsa ba,shima sai ya tsaya kallonta yana maimaita mata

      “Mene ne nace kiyi..!?”

   Sai data turo masa baki sannan tace

      “Cewa kayi kawai fa nayi wanka..”

    “Uhumm! Kawai ne..? To amma! Ke kuma sai kika yi mene.?”

    Cikin idanunsa ta tsaya kallo tana marairaicewa saboda taga da gaske yake sai ya tub’e ta

   “Dan Allah kayi hak’uri to,zanyi da kaina..”

   Banza yayi da ita ya d’ago rigan zuwa sama da fad’in

     “Zaki cire ko sai na..!”

      Cikin azama ta zare hannunta bata ko bari ya kai aya ba,taimakon da Allah yayi mata ma akwai sleeveless da underwear a ciki kafin bra,da tuni tasha kayan kunya duk da su d’inma jinsu take kamar babu su a jikinta,idanunta ta matse tana k’ank’ame jiki da tsoron abunda zai faru da ita,kusan mintuna biyu idanunta suna a rufen sannan ta bud’e su jin shiru bai kuma yi mata komai ba,ganinsa tayi a tsaye yana kallonta,sai ya d’age mata gira kafin yace

      “Mene ne.!?”

      Saurin girgiza masa kai tayi,sai ya sake harararta sannan yace

      “Ban fad’a bana son girgiza kai ba..!?”

     Kasa magana tayi saboda ita dai a tsorace take da shi,dungure mata kai yayi sannan yace

      “Je kiyi wanka ni ina jiranki,saura idan kin tafi ki sake zama har na zo na iske ki baki yi abunda nace ba..”

      Sai yayi k’wafa kawai ba tare da yace komai ba ya juya ya fice,,wahalallen ajiyar zuciya tayi sannan ta juya da saurinta ta shige bathroom,a cikin bathroom d’inma ko data shiga sai data gama kalle² son ranta sannan tayi wankan ta fito,ita dai sai mamakin gidan take tana jinjina kasancewarsa a cikin wannan gini daya kasance ko ina glasses,a gefen gado taga kayan da ya fitar mata sai ta saka cikin sauri² ta rarumo wayarta,line Jannat ta kira,tana d’auka ta ce

  “Dillah malamai mene to na tafiyar ku barni..!?”

Ajiyar zuciya Jannat tayi sannan tace

  “Taya baza mu barki ba,,ko an fad’a miki matsayin mu d’aya dake ne yanzun..!?”

Tsaki taja sannan tace

  “Ni dai da Allah duk ba wannan ba,ki fito yanzun gani nan zuwa,kin san ban san kan gurin ba..”

  Tana fad’a ta katse kiran,a hanzarce ta fice dan ma kada ya fito ya sameta ko yaji fitarta takalmin kansa duk da ba mai tsini bane sai ta rik’e su a hannu ta wuce a sad’ad’e,tana fita daga gidan ta sake yin ajiyar zuciya,a bakin k’ofa taga Jannat ta coge tana binta da kallon mamaki,bata tsaya kula taba sai ta wuce ciki abunta tana yi tana lek’e² abunta,,komai da yake cikin gidan sak irin nasu,cikin ranta sai take ayyanawa wai shin mutanen dake rayuwa cikin gidajen idan sun fita yaya suke su gane gidan da suka fito.!? Zeeharis ce tayi magana ta inda ta katse mata tunanin da take

   “Princess.! Me kika zo yi ne wai yanzun..!?”

  Juyowa tayi tana aika mata da harara cikin hayaniya tace

   “Ban sani ba.!”

Kallon juna suka yi suka tab’e baki sannan tace

  “Kada Allah sa ki sani d’in,,Allah kuma ya aiko da Yah..!”

  Bata kai aya ba doorbell tayi ring,,juyawa Jannat tayi itama tana fad’in

   “Allah ubangiji kasa Yah Hammad ne.!”

  Bata gama rufe baki ba sai data bud’e k’ofar,shi d’in ta gani tsaye ya zuba hannayensa cikin aljihun trouser d’insa sai k’amshi yake bazawa,idanunta a cikin nasa taga ya aiko mata da kallon zamu had’u,sannan ya juya yana fad’in

  “Mintuna biyu na baki ki same ni yanzun..!”

  Bubbuga k’afa tayi a k’asa ta d’an d’aga murya yadda zai ji me take fad’a

  “Ni gaskiya ba yanzun ba,hira fa nazo muyi..”

  Bai juyo ba yaci gaba da magana

   “Idan kika wuce abun da na fad’a zaki ga mene ne zai faru.”

  Sai yayi shigewarsa cikin nasu apartment d’in ya barta tsaye tana kumburi,sai data d’auki ak’alla mintuna biyun da yace sannan ta wuce tana k’unk’uni ta kama hanyar fita,cikin tsokana kamar wad’anda aka sa su a tare sai suka ce

  “Kuma dole kije ba..!”

  Juyowa tayi cike da masifa ta kalle su sai dai bata iya cewa komai ba ta wuce,kwashewa suka yi da dariya har suna tafawa,wannan dalilin yasa tayi saurin shigewa bata ko sake waiwayon su ba,a parlor ta tarar da shi kwance saman armchair yana kallon sama

  “Minti nawa nace na baki ne ki same ni..?”

  Bata kalli inda yake ba tayi k’ok’arin zama tana fad’in

  “Biyu..!”

  “Nawa ke kuma kika yi..!?”

K’aton wall clock dake wajen arean dining ta kallo sannan tace

  “Nima ban sani ba.!”

Jinjina kai yayi yana rufe idanunsa a hankali ya mik’a mata hannu da fad’in

“Zo toh.!”

Babu musu ta taso tana zuwa gabansa ta tsaya tace

  “Ga ni..”

D’an bud’e idonsa yayi kad’an sannan yasa hannu ya rik’ota zuwa jikinsa,a tsorace ta d’aga kai ta kalleshi

  “Mene ne.!?” Ya tambayeta saboda irin kallon da take masa,har ta fara girgiza masa kai sai kuma tace

  “Babu komai..”

Tab’e bakinsa yayi sannan yace

   “Da kyau to,,,tunda babu let us sleep..”

Kwantar da kanta tayi tana jin k’irjinta na harbawa da sauri² wannan dalilin sai yasa tace masa

  “A haka..!?”

Ba tare daya kula ba yace

  “Uhmmm! Kiyi bacci kawai..”

Wani irin terrify salivas ta had’iye lokacin da taji yo saukar palms d’insa saman spine d’inta,a razane ta sake d’agowa ta kalle shi,sauke idanunsa yayi a kanta fuska cike da mamakin tsoronta yace

  “Mene ne wai kike ta wani jin tsoro..!?”

  Sai ta sake marairaicewa

   “Ni dai dan Allah kayi hak’uri ka daina..”

Sake tsuke fuska yayi dan ganin yadda ta koma wata mashahuriyar matsoraciya a lokaci guda,cikin zuciyarsa kamar zai tuntsire da dariya sai ya dake ya ce

  “Na bar mene ne..!? Wani abu nayi miki..!?”

“A’aahh.! To amma ai..!”

  Sai kuma tayi shiru ta kasa k’arasawa

  “To amma me..!?”

“Babu komai..” Tace,girgiza kai yayi yace

  “Ban yarda babu komai ba,,sai kin fad’a min mene ne matsalarki..”

Sake marairaicewa tayi muryarta da rauni sosai tace

“Idan na fad’a baza kamin komai ba..!?”

  Kallonta kawai ya tsaya yi yana tunanin abunda ta fad’a, a zuciya sai yace

  “Ohh! Kin sanma zanyi wani abu ne shi yasa kike firgicewar..!?”

  A zahiri kuma sai yace

  “Me zan miki ne to..!?”

  “A’a ni dai kayi min *ALK’AWARI* idan na fad’a baza ka min komai ba.!”

  Wani killer smile ya saki yana sake matse ta a jikinsa har sai da tayi y’ar k’ara sannan yace

“Wato dai idan banyi wani abu ba hankalinki ba zai kwanta ba ko..!?”

Saurin girgiza kai tayi da fad’in

  “Nifa ba haka nake nuuffff.!”

  D’if tayi a sakamakon mak’ale bakinta da nasa da yayi ta kasa k’arasa maganar,cikin tsoronsa ta yunk’ura zata sauka daga jikinsa,amma rik’on da yayi nata ya hanata tashi,wani irin mahaukacin french kiss ne ya shiga aika mata da zafinsa ta yadda yasan ba zata tab’a iya jurewa ba dole sai ta sallama masa,,yayin da ya rik’e lip d’inta na kasa sosai a bakinsa,idan ya tsotso shi sai ya laso upper da harshensa,y’ar gwanar duk da a tsorace take jin yadda yake wasan biri da lips d’inta take sak’onninsa suka sa ta birkicewa har ra bud’e masa manhajar bakinta ba tare data sani ba,harshensa ya tura cikin bakinta yaci gaba da masa wani irin juyi a cikin,a haukace sai ta sauke mugun ajiyar zuciya tana sake rik’o shi sosai da tura masa harshenta,cafkewa yayi yaci gaba da masa wani irin tsatso kamar ya samu sweet,,sun jima suna aika ma juna wasu irin amatory signals na zallar kiss,kafin ya tura hannunsa cikin rigarta ta bayan ya b’alle marik’an bra d’inta,ta cikin rigan sai ya zagayo da hannunsa yana matsa zagayen boobs d’inta,wani irin d’agowa tayi tana moving head aside,har bata san lokacin da kalmar “Aarrgghh” yayi escape mata a baki ba,afujajan ya d’ago yana kallonta sai ta k’ank’ame shi da sake mik’o masa su,janye rigan yayi zuwa sama ya fito da su fili,then ya kai duka palms d’insa kai yana ci gaba da mixable nasu,idanunta ta lumshe tana jan baki kamar wacce taci mugun yaji cikin shauk’in salon da yake mata,,sai daya tabbatar ya gama kaita k’ololuwa sannan yayi inserting one teat zuwa bakinsa,while d other one kuma yana tsakanin yatsunsa yana ci gaba da murzarsa,,k’ananun ihu taci gaba da saki,tana sake tura masa su duka,,daga nan ko da yaga zai iya samun mishkila sai ya d’auke ta suka nufi hanyar bedroom d’insa,suna shiga tun bai gama ajiyeta ba,ta rik’o shi cos ji take kamar zata bar duniyar saboda yadda wutar sha’awa take ci a cikin jinin jikinta,kafin ya dumfaro ta sai daya janye musu bedspread,then yayi following nata zuwa saman bed d’in ya rufe su da spread d’in,ta k’asa ya antayo sauran siturunsu sannan yaci gaba da hark’alla abunsa.

Sun d’auki ak’alla wasu mintunan,kafin Hammad ya karanto addu’ar saduwa da iyali,jin kunnena ko da na tsinkayo shi yana biyawa na tabbatar lallai yau mai afkuwa zai afku,still suna a cikin spread d’in,suka ci gaba da gurzar juna,bayan wucewar wasu mintinonin kuma sai ta fasa razanannen ihu,saurin rufe bakinta yayi da nasa,yaci gaba da ragargaje sadakinsa,,bayan dya shafe tsayin lokaci a kanta daya tabbatar duk wata k’ishirwasa ta kau,sannan ya janye musu spread d’in kad’an,uban gumi kawai suke zubawa daga shi har itan,sai dai ita nata ya had’e ne har da ruwan hawayen azabar data sha a hannunsa,yadda fuskarta tayi kaca² still tana ci gaba da d’an kukanta sai ta bashi tausayi,rungume ta ya sake yi tsam a cikin jikinsa,cikin kunnenta yana rad’a mata dad’ad’an kalamai masu sawa zuciya nutsuwa,,ba tare daya bari sun wani b’ata lokaci ba ya tashi ya shige bathroom,ruwan wanka ya had’a musu mai d’an karan d’umi wanda yasan zata ji dad’in sa,sannan ya dawo ya d’agota yana mata rad’a,gocewa tayi daga rik’on da yayi mata zata sake kwanciya yayi saurin taro ta. Ko bayan daya kaita cikin toilet d’in ma shi ya gasata,sannan yayi musu wankan,daga nan kuma ya fita ya barta cikin toilet d’in da fad’in

  “Kiyi wankan tsarki,ina dawowa yanzun..”

Harararsa tayi saboda haushin silleta da yayi a kan gado,sannan ya sake cud’eta cikin bathtub,without yaji tausayinta duk da uban rok’on da tayi masa har,amma ya danne kunnensa sai daya ragargaje ta son ranta sai yanzun kuma yace zai lallab’a ta,yana fita tayi gaggawar yin wankan ta d’aura alwala,duk da yace yana dawowa bata iya bari ya dawo d’in ba,ta fito a daddafe sanye da bathrobe,tana fitowa sai ta iske har ya cire bedsheet d’in ya sauya wasu,a hankalin aai ta ci gaba da tafiya a nutse har ta kai saman bed d’in,kwanciya tayi luf tana jin yadda k’asanta ke mata zafi² duk da tasha gashi kamar tsire,sai tayi k’ok’arin matse k’afafunta ko zata ji dad’i amma me tana janyo k’afarta da nufin yin hakan,wani sabon azabar ya kunnota,babu shiri ta wangale k’afafu gefe tana ci gaba da kuka k’asa².

Shigowarsa ke nan da sauri yana niyyar wucewa zuwa bathroom ya fito da ita sai ya jiyo sheshshek’ar kukanta a saman bed,inda take ya k’araso da sauri,sai ya iske ta tayi d’ai² ko robe d’in bata cireba ta kwanta,kanta ya d’an d’ago yana kallonta cikin shauk’inta yace

  “Helpmate.! Mene ne kuma..!?”

  Cike da d’anyen kai ta bud’e ido ta watsa masa harara,cikin muryar kuka kuma tace

  “Ba dole ka tambayi abunda ya faru ba,tunda kasan kaika janyo komai..”

  Sai ta ci gaba da kukanta,kanta ya shafa a hankali yana k’unshe dariyar da yake niyyar yi

  “Please.! Kiyi hak’uri kinji.. Bazan sake..!”

  Cikin hayaniya ta d’ago ta sake kallonsa

“Ai dama ba sai na yarda za’a kuma ba d’in.?”

Girgiza mata kai yayi alamun haka ne,sai ta koma ta sake kwantar da kai ba tare data sake ce masa komai ba,tana sake matse hawaye da sauke ajiyar zuciya a lokaci guda.

   Rarrashinta ya fara yi ganin ta sake rikicewa cikin k’ank’anin lokaci,da kyar dai da sid’in goshi har ya samu ta dakatar da kukan,sai ya kwantar da ita ya sake fita,coffee ya had’o mata mai d’an karan zafi sai ya had’a mata da french toast,da yayi cikin sauri²,ya d’ora su saman midi ceramic tray,,kamar yadda ya barta haka ya dawo ya tarar da ita,sai dai izuwa lokacin tuni baccin wahala ya jima da sace ta,ajiyewa yayi ya zauna kusa da ita sai ya zuba mata idanu,wani irin sumammiyar k’aunarta tana sake taso masa,yayin da wuyar k’aunarta taci gaba da ruruwa a zuciyarsa,,ajiyar zuciya yayi sannan ya matsa sosai yana shafa fuskarta,saboda taci wani abu kafin ya bata magani,saboda idan yasan matuk’ar ta samu taci wani abu a cikinta zai k’ara taimaka mata ba zata yi saurin farkawa ba ko da baccin ya sake d’aukar ta,zata samu isashen lokaci.

Tana bud’e idanunta da kuka ta tashi dan dama da shi d’in tayi baccin,hankali a tashe ya rik’o ta yana tambaya

  “Helpmate.! Mene ne kuma.!?”

A masife ta d’ago masa kumburarrun idanunta tana fad’in

“Dole mana ka kira ni da helpmate tunda ka gama da ni..!”

  Duk iya yadda yake jin tausayinta sai data sashi sakin murmushi mai sauti,sake d’agowa tayi ta kalleshi while tana fashewa da sabon kuka

  “Kuma Allah tunda kayi min dariya sai na fad’awa Mamma,tunda dama ta ce kada nayi kuka..”

     *(Uhmmm! Lallai za’a kai k’ara fa kam,,,to ku fan’s d’in Hammad kunji,sai ku shirya ma Mamma dan hukunci na tane nd ta kafa doka dama tun farkon,,ni dai real smasher babu ruwa na dan bani da party,ko ina ma ina nan,dan haka babu opposition party a guri na).😁Zaro idanunsa yayi duka yana kallonta rik’e da baki,cikin salon lallashi sai yace

   “Please mana,,kiyi hak’uri to na bari,kinji helpmate..!?”

   

      “Ni ka dena cemin wani helpmate.”

    “Me yasa zan bari..? Bayan kin taya ni taimakon kanmu.!”

    Yayi maganar yana mata winking,mugun kallo ta aika masa sai dai bata ce da shi komai ba taci gaba da kuka abunta

     “Tashi kinji yar albarkata na baki abinci sai kiyi baccin.!”

     Bata tanka masa ba har ya janyo tray d’in sai dai ta gyara zamanta tana yi tana matse ido,,shi ya dunga bata a baki har sai data janye masa hannun gefe sannan ya rabu da ita,bayan ya ajiye kayan ya duba mata painkillers ya bata,tana gama sha ko cikakken mintuna goma bata sake yi ba wani baccin ya sake d’aukarta,ajiyar zuciya yayi sannan ya tattara kayan ya fita da su cikin shauk’inta,,sai daya gyara komai da yayi amfani da su a kitchen d’in kamar ba namiji ba komai ya kammale guri guda sannan ya dawo cikin parlor a dai² lokacin da doorbell yayi ring,duk da yasan ko bai duba ba bazai wuce ace su Sultan bane sai ya tafi kai tsaye da niyyar dubawar,ilai kuwa yana bud’e k’ofa sai ya gansu tsaye cikin shirin fita

       “Dude.! Kazo muje..!”

   Kansa ya d’age da tambayar

      “Ina kenan..!?”

    Yayi maganar cike da rainin hankali kamar bai san zasu fitan ba,kallonsa duka suka tsaya yi da mamakinsa yadda ya nuna kamar bai san maganar da suka gama yi ba d’azun kafin su bar gidan,sai Sultan ya danne yace

   “Malam kafa san ina ne zamu je,kawai ka taho mu fita..”

     Juyawa yayi ciki yana fad’in

   “Sai kun dawo,,ni kam bana jin fita yanzun..”

      Biyo shi Sultan yayi a baya yana magana k’asa²

   “Dan Allah dude ka zo mu tafi.. Mene ne hakan wai kake yi ne..!?”

    Bai juyo ba yayi hanyar bedroom yana fad’in

      “Nace fa baza ni ba.. Kuyi tafiyar ku kawai ina da aikin yi a gabana..”

    

      “Shi kenan tunda baza kaba,turo min ita sai muyi maganar da ita..”

   

     “Ita wa kenan..!?”

   

       “Ur helpmate mana..!”

   

      “Bata nan..!”

   

       “Ina ne taje yanzun..? Kai nema zaka barta zuwa wani gurin.?”

  Juyowa yayi yana murmushi

    “Ni d’in sai aka ce maka bazan iya barinta fita bane..!?”

   “A’a kawai dai na fahimci jarabarka ce ba zata tab’a barinta tayi nisa da kai ba.. Please ina take ne wai..?”

      “Tana bacci.!”

    Yace masa a tak’aice,kallonsa Sultan yayi cike da tuhuma yana maimaita

      “Bacci fa kace..!? Har yaushe ta tashima a baccin da zata koma wani..?”

       Murmushin dai still ya sake yi da fad’in

      “Laifi ne dan mutum yayi bacci.!?”

   

      “A’aahh! Ni bance ba,,amma dai baccin ai yayi yawa,sai kace wanda take fama da sleeping sickness..”

      

      “Uhumm!” Yace kawai,sai ya nemi guri nan a parlor ya zauna ya fasa wucewa cikin kamar yadda yayi niyya da farko,sake kallonsa Sultan yayi cikin nutsuwa sai yayi murmushi kawai sannan yace

      “Dan Allah dude tana ina ne..!?”

     D’agowa yayi yana kallonsa da idanunsa a shanye

      “Baka yarda bane dana fad’a maka tana baccin..!?”

  Girgiza kai yayi sannan yace

   “A’a.! Kawai dai nayi tunanin wasa kake yi ne.”

    Bai jira ya kai aya ba yace

   “Sai ka dena to,tunda kaji na maimaita maka..”

   “Uhumm.!” Shima yace sannan ya juya ya fice yana dariya k’asa²,dan yadda yaga mutumin cikin wannan farin cikin daya kasa boy’ewa yasan tilas akwai abunda ya faru,yana fitowa ko da su Bassam suke tambayarsa ya suka yi da shi,cewa yayi da su kawai suje su d’in ba sai sun je da shi ba,sai suka wuce suka tafi iya su ukun.

    Yana ganin fitar Sultan sai ya shige ciki shima yana sakin murmushin,sai daya d’an zauna ya jiran lokacin sallah ya k’arasa,shi kad’ai yayi sallar sa tunda su d’in da suke jam’i  basa nan,yana zaune yana addu’o’i har lokacin isha’a ya shiga yayi,da yake har lokacin bai ji alamun su Sultan sun dawo ba sai kawai ya fita ya rufe musu k’ofa,yana shigowa sai ya kalli inda take,har a lokacin itama tana ta bacci abunta hankali kwance,ji yayi bazai iya tashinta ba,dan haka kawai sai ya rabu da ita bai takurata tashi tayi sallah a time d’in ba,,rab’awa yayi gefenta ya kwanta yana sake matsarta,zuciyarsa cike taf da tsantsar k’aunarta dake sake masa multiplying a ko wane dak’ik’a ya shiga lumshe idanunsa cikin tsantsar farin cikin daya tsinci kansa a ciki while yana caressing wasu sassa a jikinta,idanunsa har time d’in a rufe saboda cike suke da baccin gajiya,a hakan yana shashshafata da shak’ar k’amshinta baccin ya d’auke shi ba tare daya shirya masa ba.

   

      Sai around 10pm suka farka a tare sanadiyyar doorbell da yake ta k’ara,shi ya fara mik’ewa ya fita da nufin ya duba,while itan kuma sai ta lallab’a zuwa bathroom,, still dai su Sultan d’in ya gani,da alamun ma dawowarsu kenan a lokacin,kallonsu yayi da mamaki yana fad’in

      “Wai tun fitar da kuka yi ne sai yanzun kuka dawo..!?”

   

     “Uhmmm!” Suka ce masa ba tare da sunyi magana ba,sai ya jinjina kai kawai,kayan da ya gani parke a gefensu kamar wad’anda zasu tashi wani k’aramin shop sai ya sake kallonsu da mamakin,da ido yayi musu tambayar kayan na mene ne.?,babu wanda yayi magana cikinsu suka wuce suna shigar da kayan,bayan sun gama kai iya adadin wanda suka ware sai suka juya suka bar wajen suna fad’in

      “Sai da safe..!”

     Jinjina musu kai kawai ya sake yi sannan yace

      “Allah tashe mu lafiya.”

   

     Yana ganin tafiyarsu ya maida k’ofar ya rufe sannan ya koma cikin da nufin dubawa ko ta tashin bayan fitowarsa,a saman pray mat ya isketa tana sallah,sai ya wuce shima ya nufi bathroom,alwala ya d’auro bayan ya fito ya shimfid’a wani pray mat d’in ya kabbara sallah,nawafil yayi bayan ya idar a lokacin itama Sabinar ta idar sai yasa ta suyi nafila,bayan sun idar yayi musu addu’o’i sosai,sannan ya kwashe pray mat d’in ya mayar cikin closet,packages d’in da su Sultan suka shigo musu da su ya koma ya d’auko musu da plate sai glass cup daya had’o da shi guda daya kamar rai,yana shigowa ya iske ta har ta sake komawa saman bed ta sake kwanciya,buh wannan karon a rufe duka jikinta yake except fuskarta data fitar waje,ajiye duka kayan yayi ya nufo inda take,har ya zauna bata san ya iso ba sai k’amshin scents d’insa da suka yi alerting nata,a hankali sai ta bud’e idanunta da har lokacin basu gama komawa dai² ba,hannunsa ya kai jikinta yana tab’awa da son gano ko akwai wani ciwon ne a jikinta da bai fahimta ba,d’an d’umi yaji sai dai ba wai irin wanda za’a ce na wani ciwon ba,idanunta ta sake lumshewa a hankali tana sauke ajiyar zuciya.

    “Akwai inda yake miki ciwo ne yanzun.!?”

   Ya tambaya da tsammanin zata sanar masa,amma sai yaji tayi masa shiru,idanunsa ya zuba mata yana kallonta,sai yayi d’an murmushi ta gefe,ya yanjota jikinsa a hankali,tsabar iya sharri irin nata duk lallab’awar da yake mata sai data sa kuka tana masa shagwab’ar ya famo ta,rarrashin ta yayi bayan ya samu tayi shiru da kyar sai yace ta tashi ya bata abincin,girgiza masa kai tayi ta sake zamewa zata kwanta yayi saurin rik’o ta

    “Mene ne.!? Kina jin ciwo ne har yanzun.!?”

     Kai ta d’aga masa

      “Okay! Sannu toh,,barin canja miki kaya sai ki kwanta ko.!?”

      K’asa² ta ce masa “Toh”,sauketa yayi sannan ya tashi da sauri ya fita,bedroom d’in daya fara kaita ya koma ya d’auko mata wani arnen custom silk night wear mai azabar kyau kalar purple mai haske,shi ya taimaka mata wajen sawan,sai dai bai had’o mata ko da pant ba,iya rigan kawai ya barta,yana sa mata ya sake shimfid’e ta sannan ya tattara packages da komai daya shigo da su tunda tace masa bata ci ya fice da su,,ajiyar zuciya ta sauke a hankali lokacin daya fita sannan tayi luf tana tuno abunda ya gabata cikin tarayyar su acikin room d’in,sumbatun da yayi ta zuba mata da rikicewarsa akanta komai bai goge ba,ajiyar zuciya ta sake yi data tuno irin kalaman k’aunar da yayi ta zuba mata har da d’an murmushi tayi,,lokacin guda wani mugun kishinsa ya turnuk’eta tunawa da yana da wata matar bayan ta,kuma itama ta san yadda yayi mata hakan zai mata,,yanzun kenan duk wannan k’aunar daya gwada mata itama waccen d’in haka zai mata.? Take taji wasu irin hawayen kishinsa sun gangaro mata sai tasa bayan hannu ta goge su,shigowarsa dai² lokacin ita tasa tayi saurin shigewa cikin spread har kanta ta rufe tana gyara fuskarta,da sauri shima ya nufo inda take ya bud’e mata fuskar yana tambayar ta ko tana lafiya.? Sai ta gyad’a masa kai,shafa kanta yayi zuwa fuskarta sannan yace mata bari ya canja kaya yazo,yana fad’a sai ya koma ta wajen closet,tana ganin ya d’auko pyjamas d’insa yana niyyar canja su a gurin tayi saurin sake shigewa,girgiza kai kawai yayi yana dariya k’asa² sannan ya canja dress d’insa zuwa na bacci yayi following d’inta zuwa saman bed,tunda ta ji yo shi a kusa da ita yana k’ok’arin maida ita jikinsa ta fara tsorata cos a tunaninta wani abu zai sake mata,kan kace me tuni har hawaye ya wanke mata fuska,sheshshek’ar kukanta da ya jiyo da sauri ya tashi ya zauna yana kunna haske,hawaye ya gani sun mata kaca² cikin rikicewa sai ya kamota ya d’orata a jikinsa fuskarsa na bayyanar da damuwa yace

      “Helpmate.! What’s going wrong.!?”

     Bata iya yi masa magana ba saboda kukan da yaci k’arfinta sai tayi shiru dan da kunya ta iya ce nasa tsoronsa take ji,lallab’a ta ya sake yi sannan suka kwanta,a hankali sai ya kai palms d’insa saman spine d’inta yana caressing,sake firgicewa tayi saboda tuna d’azun ma abunda ya faru kenan har ya janyo mata shan azaba a hannunsa,sai ta sake k’ank’ame jikinta da yake wani irin vibration guri guda,fuskantar damuwar da take tare da shi yasa sai ya daina shafatan,a hankali har baccin tsoro ya kwashe ta tana ta sakin ajiyar zuciya.

   

     Washe gari da safe ko da su Badra suka yi shirin zuwa Pennsylvania Sultan ne yace su bari zuwa wani week d’in,dan haka sai suka hak’ura akan wani week d’in sa koma,,suma kuma ko da suka je office a ranar basu wani jima ba sosai suka dawo dan ma y’an wajen aikin nasu sun tsayar da su suna ta musu sanyawar albarka na auren da Hammad d’in yayi.

      Sai da yamma sosai sannan su Badra suka lek’o ta dan Sultan ya shaida musu tun kafin su fita office akan kada su damu da rashin ganinta cos bata jin dad’i,su dai suna jin haka sai suka yi dariya,Zeeharis cikin tsokana tace “Allah sarki princess d’in Yah Hammad Allah bata lafiya”,da yamman ma ko da suka shiga apartment d’in nasu,a parlor suka iske ta kwance saman armchair,fuskar nan tayi wani irin fayau kamar ta shekara jinya,bayan sun gaisa da Yah Hammad sai ya fice yana cewa “bari ya lek’a gurin su Bassam” sai ya barsu da ita,yana fita Zeeharis ta dawo kusa da ita ta zauna da fad’in

      “Princess sannu.! Ya jikin.!?”

     Saurin d’agowa tayi tana kallonta fuska a turnuk’eta kamar koko tace

      “Waye yace bani da lafiya.!?”

     Dariya suka d’anyi sannan Jannat ta amshe da cewa

      “Yah Sultan yace kada mu takura ku,kuma shi yace bakya jin dad’i.!”

     Zugum tayi musu tana kallo,cikin zuciyarta da tunanin wato ma zuwa yayi ya fallasata a gurin su Sultan d’in.? Sai kawai tayi y’ar ajiyar zuciya ba ta ce musu komai ba,nan suka zauna mata suna ta hira har kusan isha’a sannan suka mata sallama cike da kewarta suka koma nasu apartment d’in da nufin yin sallah,,cos sun san idan oga yana nan tofa sai dai suyi hak’uri da rashin ganinta,sun san ba ko wane lokaci ne zasu samu damar ganinta ba,,suna fita kuwa babu jimawa shima ya shigo gidan sai ya isketa tana sallah.

     

     Ranar Saturday da safe da yake dukansu suna gida babu mai fita,kuma zuwa lokacin Sabinar ta samu sauk’i sai ya shirya musu fita tare da su Badra gaba d’ayansu cos yasan zata ji dad’i,,lokacin da suka ji batun fitar sosai suka yi murna cos a gurinsu da yake wannan shi ne rana ta farko da za su fara fita tun bayan zuwansu shi yasa suke ta murna zasu ga garin sosai,,around 10am suka fito duka cikin shiri,kada kuso ganin k’auyenci a gurinsu saboda yadda wannan fitowar ya zame musu wani abu na musamman,,nima dai sai lokacin na fahimci ashe wancan zuwan ma dan dai suna gajiye ne shi yasa basu maida hankali kan kalle² ba *TRUMP GRILL* suka fara biyawa suka d’anyi ciye² sannan suka yi guzuri da yake ranar yau duka ya tsara musu yinta ne ba a gida ba,daga nan ko da suka fito sai suka shiga *TRUMP ICE CREAM PARLOR* kowa ya d’auki dangin abunda ransa yake so,gaba d’aya kuma daga nan sai suka bar cikin ginin Tawer d’in suka nufi *CENTRAL PARK ZOO* da yake shima a cikin Fifth avenue d’in yake,,sun yi yawo sosai a cikin zoo d’in sun sha iska,picture’s d’in tarihi kuwa duk inda suka je sai sunyi su,,a gefen yallab’ai Hammad shi dai ko ina aka je yana mak’ale da abarsa baya bari tayi masa nisa,wani lokaci ma da yake har tsokanar sa su Sadeeq suke yi akan ya barta ta sha iska,sai dai ya kalle su ko yace “ba ku da hankali ai,da kun san darajar mata da baku shirya yi min maganar na barta ta huta ba,,daga hutu ina sakinta nayi sake wani d’an baturen ya ganemin ita shi kenan sai dai ku mayar ma dasu Daddy corpse d’ina 9ja” suma kansu suna jin ya ce haka sai suyi dariya kawai suna cewa “Allah dai ya kaimu namu lokacin,maji mene ne kake ji”,,ranar dukanta a wajen yawace² suka k’arar da ita,tun fitar su sai yamma sosai sannan suka dawo gida,shima d’in kuma ko kafin su wuce sai da suka shiga *GUCCI STORE* da yake shima a nan Trump tawer d’in yake amma yana daga b’angaren northeast ta wajen entrance na ginin,sun yi siyayya sosai kama daga kan jakankuna da takalma masu kyau da tsada,sannan suka shige ciki saboda k’uratowar lokacin sallah,shi yasa ma sai basu samu damar shiga Gallery d’in Robert Miller da suka yi niyyar yi ba,sun barshi kan sai wani ranar idan sun sake yin irin wannan fitowar.

    Tunda suka shigo gida da yake apartment d’in su Barda suka baje kowa sai ya hau ihun gajiya duk da sun ji dad’in fitar ba kad’an ba,suna shigowa shi dai Hammad ya wuce yayo alwala a d’aya room d’in da yake duka a room d’aya suke had’uwa su kwana,,itama wucewa tayi da nufin d’auro alwalar,sai duka y’an matan suka biyo ta,cak ta tsaya lokacin data fito daga bathroom ta tarar da Jannat tana bud’e luggage’s tana fitar da kaya,sai ta bita da kallo,bayan ta gama k’are mata kallo sannan tace

      “Wai ku nan kayanku suke har yanzun.!?”

     Da mamaki Jannat ta d’ago ta kalleta sai tace

       “Ehh! Mene ne.!?”

   

      “Babu ma’adanin kaya ne a nan d’in.!?”

     Ta tambaya tana kallon walls d’in d’akin

       “Ina kuwa yake.!? Mu dai tunda muka zo bamu gani ba.!”

      Y’ar dariya tayi musu sannan ta nufi wall d’in yamma da d’akin,ba tare da sun san me hakan yake nufi ba suka ga k’ofa tana bud’ewa da kanta,sakato suka mata suna kallo lokacin da had’ad’d’en reach-in closet dake d’akin ya bayyana,sai suka fasa ihu suna fad’in

      “Allah bar mana ke princess,, aradu kin k’aro yaji..”

     Ihunsu ne yasa Bassam tambayar lafiya.? Sai suka ce babu komai sannan suka nutsu suka ci gaba da hira k’asa²,kafin wani lokaci duka suka shirya kayansu a ciki har luggage’s d’in ma suka yi musu guri daga can k’asa,,bayan sun yo alwalar suka fita parlor,jam’i suka yi bayan sun idar sai suka shige kitchen da nufin nema musu d’an abun motsa baki duk da a k’oshe suke,,sun jima sosai a cikin gidan suna ta hira y’an matan da samarin,,around 9pm sai suka yi sallama duka kowa ya kama hanyar tafiya domin ya samu ya kwantar da hak’ark’arinsa.

     Cikin wad’annan kwanakin da suka gabata a cikin ko wane wayewar gari,suna yinta ne cikin tsantsar so,yarda da juna gami da shak’uwa mai k’arfi da take sake ninkuwa tsakaninsu,da yake tun daga ranar daya ragargaje sadakinsa wani abu bai sake shiga tsaninsu ba,ita kam hakan sai yayi mata dad’i sosai,dan dama ta k’udurce ita da shi in dai a wannan fannin ne sai ta Allah,shima d’in kuma ko da ya fahimci yadda take baya² da shi tun daga lokacin sai yaja baya da nuna mata kwad’ayinsa a filin,k’ark’arinsa da ita wasanni,idan ba su ba kuma tofa sai dai ya rungume pillow,cos da zaran taga zai zarta ta dira masa rikici kenan,har sai ya rabu da ita sannan zai samu nutsuwa ranar ko jikinsa bata yarda ta kwanta,tun da ya fahimci hakan sai ya rabu da ita,amma deeply abun yana ci masa jiki,tun yana dauriya da hakur’in zuba mata idanu har abu ya fara neman fin k’arfinsa,,,da daren ranar bayan sun dawo suna shigowa gidan a lokacin sun baro apartment d’in su Badra kenan,sai ya wuce bedroom d’insa ya barta nan a parlor da nufin watsawa jikinsa ruwa ko zai samu rangwamen abunda yake ji cos fitarsu a yau d’in da kusancin da suka samu yasa damuwa ta rufe shi,,shi yasa ma ko da ya shigo d’in bayan yayi wanka ya shirya cikin pyjamas,sai ya fito ya nemi lime juice duk dan kada matsalar yayi masa nisa,a parlor ya zauna yana kallon kwallo abunsa,while ita kuma ta shige a lokacin,sai da ya d’auki mintuna ak’alla biyar da zama sannan ta fito daga bedroom d’in itama sanye da wasu irin women’s sexy pyjamas,d’ago ido yayi ya bita da kallo lokacin data wuce shi zuwa kitchen tukun ya dawo da hankalinsa kan abunda yake yi,,goran juice d’in daya tsiyaya ta tarar a saman storage closet ya manta bai mayar da shi inda yake ba ya fita,itama ko data gani sai ta manta da abunda ya kawo ta,d’auka tayi tana dubawa zuwa wani lokaci sannan ta bud’e goran had’e da tsiyayawa cikin cup ta dasa shi a bakinta,mugun tsanin da yayi mata a baki shi ne yasa da sauri ta juya gefen basin ta zubar sannan ta wanke bakinta,sai data d’auki lokaci a cikin kitchen d’in tana yamutse fuska saboda tsamin da juice d’in yake da har ya kashe mata baki da saurin sai ta ta fito,cikin parlor’n ta ratso still yana zaunen yana ci gaba da sipping juice d’in yana yi yana matse fuska saboda rashin dad’insa,inda yake ta nufo da zuwa ta amshe cup d’in a hannunsa,saurin d’agowa yayi yana kallonta,a hankali har ta kai cup d’in bakinta ta d’and’ani ruwan da harshenta,yamutse fuska tayi cikin salon rashin jin dad’i ta bar gurin da cup d’in a tunaninta zai yi magana amma sai taga yayi shiru bai ce mata komai ba,har ta kai bakin kitchen sai ta waiwayo tana kallonsa ko da taga hankalinsa duka a kan TV sai ta dawo,a kusa da shi sosai ta zauna jikinsu na gogayya,bayan ta ajiye cup d’in a gefe sai tace

      “Me kake yi da shi ne.!?”

     Yi yayi kamar bai jita ba,ita kuma hakan da yayi sai yasa ta d’an ji damuwa saboda rashin kulawarsa,sake tambayarsa tayi buh still ko juyowa ya kalleta yak’i yi bare tasa ran zai tanka mata,hannunta ta kai saman beard d’insa tana shafawa sannan ta rik’o chin d’insa tana marairaicewa

      “Please.! Kana fa jina amma shi ne zaka min shiru.!”

      Yadda tayi maganar cikin salon d’aukar hankali sai yasa shi juyowa yana kallonta,da yake ita ke son ji sai bata damu ba ta sake cewa

      “Me kake yi da shi wannan d’in..!?”

    Gira ya d’age mata yana tambayarta abunda take nufi,sai ta d’ago masa cup d’in tana fad’in

      “Wannan fa nake nufi..!”

     Ta k’arashe kamar zata rushe masa da kuka

        “Amfani.!”

      Ya bata amsar a tak’aice cos bai shirya yin dogon magana akan case d’in ba,hannunta da take wasa da shi saman beard d’insa ta mayar saman shoulders d’insa tana masa wani irin kallo

      “Amfani fa.!? Na mene ne amfanin..!?”

   

     Kansa ya sake d’aukewa akanta yana had’e rai ba tare daya tanka mata ba,hannayenta tasa ta zagaye shi da su,sai ta kwantar da kanta saman shoulder sa cikin yanayin damuwa tace

      “Ba za ka fad’a min ba.!?”

   

     “Ummm!” Yace sai kuma ya sake d’auke kansa zuwa gefe,sai data had’iye wani irin terrified saliva’s sannan ta iya d’ago kanta ta zuba masa idanu,kamar wacce ta tuna wani abu kuma sai tayi saurin mik’ewa zata bar wajen yayi saurin rik’o hannunta,sai data juyo ta kalle shi then ta dawo a hankali ta shige jikinsa,wani irin ajiyar zuciya suka sauke a taren,fuskarsa ya a saman wuyanta,while hannayensa zagaye da ita,sai ya fara goga tip noise d’insa a jikin wuyanta ya bisu da kiss,wani irin yamm! Taji gaba d’aya jikinta yayi mata,sai ta sake yin ajiyar zuciya tana sake shigewa jikinsa,hannunsa ya kai ya tab’o spine d’inta from da neckline d’inta till yayi reaching asshole d’inta,ta sauke sanyayyar ajiyar zuciya tana rik’e fuskarsa dake gefen wuyanta,d’ago fuskarsa yayi ya sake kallon yadda tayi cikin lokaci kad’an har ta fara yin nisa,slightly,lightly nd gently sai yayi pressing lip’s d’insa kan nata ya bata simple kiss mai wuyar mantawa,wani irin sumammiyar sha’awa ce ta kawo mata ziyara a hankali sai ta mayar da idanunta ta kulle tana sake rik’o shi sosai kamar tana jin tsoron ya kufce mata,,lokacin daya kalleta shi kad’ai yayi magana a zuciya yace

   “Lallai yarinya ai kuma sai kin kawo kanki.!”

   Sai yayi saurin d’agota a jikinsa ya direta bisan k’afafunta,a d’an tsorace ta bud’e idanunta tana kallonsa,juyawa yayi ya maida idanunsa kan TV amma a zahiri itan yake kallo ta gefe yace

    “Je maza ki kwanta dare yayi yanzun,nima ina nan shigowa idan na gama abunda nake yi..”

    Ya wani d’auke kamar ba shi yayi maganar ba,tsaiwa tayi a gurin har ya k’are maganar bata iya motsawa ba tana binsa da kallo mai cike da tsantsar sha’awa,sai ya d’an juyo kad’an ya kalleta,a zahirance komai nata yake,shi yasa baiyi wahalar fahimtarta ba,amma kuma duk da ya gane d’in sai yayi k’ok’arin had’iye nasa kwad’ayin,while a ciki yana mata dariyar halin da take ciki,yadda ya juyar da kansa kamar bai fahimce taba shi yasa ta juyawa a hankali cikin rashin kuzari ta nufi master bedroom d’insa,cos ita dai ta ji a ranta baza ta iya fad’a masa abunda yake damunta bq,,bai fi da mintuna biyar ba shima sai ya kashe duk kayan wuyar yabi sahunta,kwance ya ganta tayi lamo saman bed,ko dai makaho ya shafata a time d’in tilas ya gano manufar ta amma haka Hammad yayi biris ya nuna bai gane ba,ko da ya kwanta saman bed d’in ma sai yayi gefe maimakon yadda ya saba mata,tun data shigo ta kwanta banda juyi babu abunda take cike da damuwa sai wai² take a ranta,gashi ita bata ji zata iya fitowa ta nuna masa abunda take buk’ata daga gare shi,lumshe idanunsa yayi yana murmusawa cos yasan yau dai kam sai ya cimma nasara,sake juyawa yayi ya bata baya,bayan kamar mintuna goma a lokacin tayi zaton yana bacci sai ta matsa jikinsa tana ta sauke ajiyar zuciya,,yayin da a gare shi cikin ransa fal yake da mamakinta,yana ta mamaki wato su dai mata idan zasu mutu baza su iya fitowa su nuna maka abunda suke buk’ata ba,sai shi namiji da idan yaji yana buk’ata shi ne baya iya yin hak’uri,,d’if ya sake yi kamar da gasken yayi bacci,while itan kuma duk k’ok’arin ta shi ne ta samu sassaucin abunda take ji amma hakan yak’i samuwa,juyawa tayi bayan ta sake shi ta koma can angle had’e da fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi tana k’ank’ame jikinta,,tausayinta game da soyayyarta masu girma take suka sashi juyowa cos yasan idan shi ya iya jurewa ba lallai itan tayi haka ba,sai yayi saurin birkitota suka fuskanci juna k’asa² cikin muryar bacci² yace

“What’s ur problem ne..!? Wani abu na damun ki kika kasa fad’a.!?”

  Sake fashewa tayi da kuka while tana shigewa jikinsa sosai,jikinta a lokacin saboda taje mak’ura wajen buk’atuwa har wani irin karkarwa yake saboda masifar dake cin jikinta

  “Sshhhh.! Bari kuka.!” Yace mata yana ci gaba da tab’o spine d’inta,abunda gaba d’aya bai fahimta ba a time d’in shi ne yadda yake mata nan yana sake ruro mata wutar sha’awa yake amma ta gagara fad’a masa damuwar duk tambayar da yake mata,sai daya tabbatar taje inda ko me yace baza tayi musu ba sannan ya d’ago fuskarta,da wani irin salon tada hankali yayi pressing lips d’insa against her,babu musu ko nok’ewa itama take mayar masa,sai da suka gurji juna cikin salon wasanni masu tsumama zuciya,sannan ya turo mata takardun kwangilarsa a take ta masa sign suka lula duniyar ma’aurata.

Washe gari da safe,cike da nutsuwa suka tashi,kowa yana kaffa² da d’an uwansa,haka nan ita kad’ai idan ta tuna abunda ya faru sai tayi murmushi kawai,a lokacin sai take tuna irin yadda yake binta amma tana masa kukan ita a’a da ciwo,sai ta jinjina kai kawai da tunanin lallai Allah ne ya kamata jiyan bisa hak’k’in sa data tauye,wato da haka yake shan azaba amma take nok’ewa.? Sai ta saki ajiyar zuciya kawai ba tare da tace komai ba,,,da daren ranar kuma wajen 8pm sai ga su Sultan cikin shirin fita sun lek’o musu,cos yanzun ba sosai suka cika zuwa ba musamman da dare sun san suna buk’atar kad’aicewa shi yasa,suma kuma Sultan d’in sai dai suyi hirar su a gurin su Badra da sunan sunje zance,,shi ya bud’e musu k’ofa a lokacin itan tana zaune saman armchair har suka k’araso

  “Marhaba.!”

  Suka had’a baki duka y’an matan suna d’ago mata hannu,murmushi tayi da fad’in

  “Ahlain.. Khaifakum..!?”

Sai suka sa dariya da fad’in

    “Nahna bi khair..”

Murmushi ta mayar musu ta juya tana gaida su Sultan da suke kallonsu cike da burgewa,,k’asa² taji yo shi suna magana da su Sadeeq d’in,a lokacin y’an matan sun k’araso kusa da ita,Badra ta rad’a mata a kunne

  “Madam muje ciki ki shirya..”

Sai ta d’ago tana kallonsu dan yadda suka d’auki kwalliya tasan zai yi wahala dama ace ba wani gurin ne zasu je ba a haka nan

  “Ni kuma ina zani.!?”

“Pleasee.! Muje ke dai akwai gurin zuwa ai,muje da sauri ki shirya please kafin Yah Hammad yace baza ku ba..!”

Sai data kallo inda suke sai ta mik’e suka wuce bedroom d’inta,da yake komai akwai shi su Badran ne suka yi mata simple make-up da yayi matuk’ar yi mata kyau,wani irin paperboard bag suka bata da suka shigo da shi mai masifar kyau da fad’in

  “Kisa wannan muyi sauri mu tafi..”

“Toh.!” Tace musu sannan ta tashi da sauri ta zazzage kayan dake cikin bag d’in,wani irin women’s sexy prom wedding attire ne mai deep V-neck lace da off shoulder a ciki,sai wani irin hill shoe da Po’s masu azabar kyau kalar royal blue,d’agowa tayi ta kallesu sai ta sake kallon kayan kamar za tayi magana

  “Please kiyi sauri muje kada suyi ta jira.!”

Kad’a kanta tayi sannan ta ware rigar tasa duk dan kada ta b’ata musu tsari,yadda rigar yabi shape d’in jikinta ya zauna dai² kamar an gwada yasa su fara zuzutata,ita dai tunda tasa sai take jinta wani iri,ba don komai ba sai don long tsagar da rigar take da shi ta gefe guda wanda ya kai mata har cinya,gyara mata gashin kanta suka yi a gefe suka kama mata shi da ribbons masu matuk’ar kyau,yadda ta fito tayi masifar kyau kamar a sace ta a gudu,,sai da suka tsaya d’auke²n pictures sannan suka fito,a parlor suka riske su zaune suna jiran fitowarsu lokacin shima kansa Hammad d’in har ya shirya cikin wani smart royal blue men’s suit mai double breasted,yayi masifar kyau sai wani men’s breathable leather takalma bak’ak’e da yake mak’ale dasu a k’afarsa,beard d’insa daya had’e da mustache ya sha gyara sai kyalli yake,,tunda ta fito ya d’ago ya kalleta sau d’aya wani irin mahaukacin kishi ya mamaye masa idanu a fusace ya mik’e yana unbuttoning suit d’in ya wuce zai bar wajen…..Da sauri suka kalleshi har suna had’a baki wajen fad’in

      “Dude.! What’s going wrong..!?”

    Da yake sun kaishi mak’ura wajen fusata,wani irin juyowa yayi yana binsu da kallo a hargitse idanunsa nan nasa cike taf da kishinta yace

     “Saboda kun raina min hankali a haka zan bari ku fitar min da mata.?! Wato gani sakarai,ban san abunda nake yi ba ko.?”

    Shiru suka yi suna kallonsa dan yadda yaje linter a cikin k’ank’anin lokacin nan sun san komai zai iya faruwa shi yasa suka gwammace yin shirun,a dalilin shi ne zai fi musu zama alkhairi,kuma ba wai dan sun rasa abun cewa ba,a’a sai dan kawai basu san ya akayi hakan ya faru ba,nd basu yi hakan da nufin b’ata masa ba buh yadda ya d’auki al’amarin ya matuk’ar tsoratar dasu

    “Kun yiwa kanku ai,,nd ina tunanin za ku iya tafiya,idan munyi ra’ayin fita zamu iya zuwa mu kad’ai ba wai lallai sai munje tare ba..!”

      Sai ya wuce abunsa cike da b’acin rai,yana zuwa daf da inda suke tsayen,ya sake kallonta cike da bak’in cikin kayan da suke jikinta,yake lissafawa a ransa,shi duk da ace rigar babu wannan uban wuyan da tsagar,sannan hannun ya rufe mata gaba d’ayan wrist d’inta,gashinta da yake waje da sun sakaya da sauk’i² zai iya yin hak’uri ta fitan,amma sun fito masa da ita half naked suce kuma bazai yi fad’a ba,tsabar kishin da yake cinsa ma bai san ya rik’o taba,ya jata suka wuce da niyyar barin gurin,Bassam dake tsaye kamar an sassak’a tun farko sai yayi saurin shan gabansa yana marairaicewa,while su sauran duka suna nan zaune kamar wad’anda aka yi girke,,ba samarin kad’ai ba hatta y’an matan kansu sunji mamakin abunda ya farun,ransa har wani irin suya yake masa ya d’ago idanunsa da suka sauya launi dan b’acin rai ya sauke kan k’anin nasa,cikin hucin masifa yace

      “Kauce min a hanya kafin na mare ka..”

   

      “Please! Broah ya kamata ka d’auki komai a sannu,,duk abunda kaga ya faru muma fa duka bamu da laifi a ciki..!”

      Wani mugun kallon daya masa shi yasa shi saurin sake fad’in

      “Believe me,,kasan bana tab’a maka k’arya,, yanzunma i will explain u how hakan ya faru.”

      Ko a bai ce ba ya rab’e zai wuce Bassam d’in yayi saurin rik’o d’aya hannun nasa

      “Please.! Broah i beg u ka tsaya ka saurari bayanin da zan maka,na tabbata zaka gane muma duka bamu da sani akan komai.”

      Cak ya tsaya a inda yake,itama sai ta tsaya d’in tana kallonsa ta gefe cos a tsorace take da shi,musamman yadda yayi fushin nan,,ba tare da ya ce masa komai ba haka bai juyo ba,buh alamu sun nuna bayanin yake saurare,a tak’aice Bassam yayi masa bayanin alak’ar su da kayan,da wanda ya kawo yace a basu,ma’ana shugaban k’ungiyar su,kuma shugabansu a gurin aiki Moses clinton,tab’e baki yayi bayan ya gama saurarensa yace

      “Can ku kuka sani,ni bana fahimtar ko wane zance  matukar akan wannan ne,,soyayya da kusanci ba haukan bane,nd ni d’in ban kasance kuzarin namiji ba,da zai dunga barin matarsa fita a ko wane yanayi,ina kishin abuna,idan zaku iya tayani to,if not kuma dama babu wanda na rok’a,amma wannan ya zama karo  na k’arshe da haka zai sake faruwa tsakaninmu,,ina fatan kun gane..!? Wannan kadara ce mai daraja a gurina da ba zan tab’a iya yin wasa da ita ba..”

     Ya k’are maganar da nuna Sabina data sunkuyar da kai k’asa,,hak’uri da rok’o suka yi ta basi,amma duk da hakan ya kafe kai da fata akan babu inda zasu,,da kyar bayan sun gama kai ruwa rana suka samu ya hak’ura akan zasu je d’in,amma shima d’in sai cewa yayi sai idan wani kayan aka kawo mata ba wannan ba sannan ne zai iya hakur’in bari su fitan,,Sadeeq da Bassam ne suka amsa da indai ya amince d’in zasu je su kuma za su kawo wani kayan,sai yace ya amince d’in amma sai ya kafa musu sharad’i akan irin kayan da yake so,su tabbatar mai dogon hannu nd su had’a da abunda zai rufe mata gashi in ba haka ba kuma sun fasa sai dai su suje kawai,sun amsa sharad’in sannan suka fice zuwa Robert Miller gallery,a can suka duba mata wasu kayan,cikin mintuna kad’an suka dawo da paperboard bag a hannunsu da aka saka musu kayan,sai daya karb’a ya zazzage su a gurin ya duba su tsaf,exclusive ball wedding dress ne with free accessories,da short V-neck amma kuma hannun d’ago ne kamar yadda yace,d’agowa yayi bayan ya gama kallon kayan yana tab’e baki har zai yi magana Sultan da tunda ake maganar bai ce komai ba ya kalle shi da fad’in

       “Please dude.! I beg u with da name of Allah kada kace wani abu kuma,kayan nan dai yadda kace haka aka kawo su,please dan Allah ka bata tasa muje,bai kamata mu watsawa mutanen nan k’asa a ido ba,sunyi mana abunda ya kamata ace mun gode musu ne,nd u know su al’adarsu da addininsu ya bambanta da namu,so duk abunda za mu gani sai munyi hak’uri,please da Allah ka bata tasa wannan d’in it’s Ok..!”

      Ido ya d’aga ya kalle shi sai kuma yayi shiru bai ce komai ba ya mik’a mata kayan,a d’an tsorace ta kalle shi saboda bata san me zai biyo baya ba,yana kallon yanayinta sai yace

      “Je kisa wannan d’in..”

     Amsa tayi ta wuce a sad’ad’e su Badra suka bita da sauri suna farin ciki,still dai kalar kayan royal blue suka d’auko cos so ake su fito a kala d’aya,yayin da saura suke da black nd white,kuma su kansu su Badran shigar da suka yi kenan na bak’in kayan,,bayan kamar mintuna goma sai gasu sun fito tare tana tsakiyarsu,duk da a wancan shigar na farko ma tayi kyau,amma duk sai suka fi ganin kyaunta a yanzun,sake kallon k’annen nasa yayi a cikin shigar high-end women’s off shoulder na wani long evening dress,kuma duk kawunansu rufe suke sun sha turban,sai kawai ya sake yin k’wafa wato da shi suka raina ma da suka so fitar masa da mata a hakan,sai ya girgiza kai kawai sannan ya mik’e yana kallon su,suma d’in duka suka mik’e kamar yadda yayi,suna k’arasowa gaba d’aya basu tsaya b’ata lokaci ba suka fice suka bi elevator zuwa floor d’in da za’a yi event d’in,duka a tunanin Hammad bai san dinner aka shirya musu ba,sun dai barshi akan program ne za’a yi,amma bai san wa su aka shirya ba har suka sakko floor d’in,, *TRUMP BAR* yaga suna niyyar shiga sai ya ja ya tsaya yana binsu da kallon tuhuma

       “Dude muje mana..”+

    “Ina ne zanje d’in.? Mashayar.!?”

    Wani irin kallon takaici Sultan ya bishi da shi sai dai bai iya magana ba sai Sadeeq daya dafa shi

   “Please aboki,mufa ba abunda ya kawo mu ba kenan,idan dan kana ganin mun zo bar ne,just wait for a short time,ba jimawa za muyi ba zamu bar musu gurin,amma dan girman Allah kada kace wani abu daga hakan,muje kawai.!”

   Tsaki ya ja yana sake cogewa a gurin,sai Bassam ya matso kusa da fad’in

   “Please broah.! Mintuna kad’an zamu tafi,bafa cewa aka yi lallai idan munje sai mun sha wani abuba,if ya zama necessary ai akwai drinks..”

   Wani irin kallo yayi masa a kaikaice sannan ya wuce d’in yana rik’e da hannunta,Sultan da Bassam da yake sune na k’arshen biyo su sai da suka furzar da iska mai cike da damuwa,k’asa² Sultan yace da Bassam

   “Gaskiya wannan yayan naka muna fama da shi,,Allah yasa baya yiwa y’ar mutane wannan iskancin..”

    D’an murmushi Bassam yayi shima k’asan² yace

    “Aifa kam,matar Yaya zata sha fama,mutum sai taurin kai kamar ginin majami’a..”

    Suka sake yin dariya dai² lokacin da suka shigo gurin,yadda suke murmushi yasa suna had’a ido da Hammad ya aika musu da sak’on harara,murmushi suka sake yi masa sai ya d’auke kai bai sake kallon location d’in da suke ba,rantsatstsiyar liyafa ce wacce ba kowa ne zai iya shirya kamarta ba,nd sai karan mutum ya kai tsaiko kafin ya iya had’a kwatan kwacinta,shugaban nasu ya shirya ta taya Hammad d’in murnan auren da yayi,da yake babu wanda ya sanarma batun auren nasa kafin lokacin,sai bayan da suka dawo daya samu labarin yadda komai ya wakana a gurin su Sultan shi ne ya tashi yin dinner cikin k’ank’anin lokaci saboda su da basu samu damar halartar auren nasa ba,da kuma kasancewar yana jin dad’in aikin Hammad d’in a k’ark’ashinsa,,tun shigowarsu da shugaban nasu suka fara cin karo a bakin k’ofar shigowa shi da mataimakinsa sai matansu,bayan sun gaisa da su suka yiwa Hammad d’in murna,sai suka nufi ciki gaba d’aya,yadda aka tsara gurin gwanin burgewa sannan komai sun tsara shi bisa k’a’ida,,duk inda mutum zai hanga iya ganinsa sai dai yaga masu jajayen kunne suna wulgawa,sai bak’ak’en da suke kamar an watsa cubes a tsakiyar fili,,gurin da aka tanada dominsu aka nufa da su saman wasu irin armchairs masu matuk’ar kyau,gurin an k’awata shi fiye da ko wane table,,da yake mafi yawancin mutanen dake gurin y’an wajen aikin sune daga su sai matansu wasu kuma da y’an matansu yasa taron baiyi yawa ba bare ya bada hargitsi,tun da suka shigo d’in kuma ko da yaga mutanen dake gurin sai ya d’an sauke fushin nasa,suka ci gaba da amsar gaisuwa daga abokai,a tak’aice dai anyi dinner mai burgewa a wannan daren mai k’ayatarwa,sun kuma samu kyaututtuka sosai bama kamar Sabina data kasance tauraruwa a gurin,,sai around 10pm lokacin mutane su d’an ragu suma suka yi sallama da sauran suka tafi,a lokacin ya rik’o hannunta kenan suna fitowa a gurin wasu y’an mata dake shirin ratsowa cikin gurin sanye da wani irin mini skirts da y’an b’ingilallun rigunansu wanda da kad’an suka wuce bra sun shigo,biyu daga ciki su kuma sunci long trouser sai dai rigunan ne ba na arzik’i ba suka kusa yin karo,baya yayi kad’an da ita,rab’ewa suma suka yi suka nufi cikin bar d’in suna dariya,while su Badra kuma da baki baya shiru suna kallonsu suka tab’e baki da fad’in

    “Cabb’ d’i jan,gaskiya anyi asarar haihuwa.”

      Kallonsu Hammad yayi sai suka yi shiru basu k’arasa fad’in abunda suka yi niyya ba,suka wuce cikin elevator,girgiza kai yayi kawai sannan ya ja hannunta suka wuce,elevator na fara tafiya suka jiyo shi yana fad’in

      “Idan zaku maida hankalinku jikinku tun wuri ku mayar,nan ba 9ja kuke ba,if not kuma ku zaku ji jiki..”

      Su Sultan da basu san mene ne ya faru ba sai duk basu kawo wani abu ya faru ba,amma su d’in da yake sun san da su yake ko wacce sai ta sauke kai k’asa,har suka kai floor d’insu babu wanda yayi ko tari a cikinsu,a bakin k’ofa duka suka yi sallama duk da har lokacin fuskarsa a had’e take tun bayan fitowarsu daga Bar d’in,sai da yaga shigewarsu Badra cikin apartment d’insu sannan ya bi bayanta dan ita kam tuni yasa ta wuce ciki,gifts d’in da su Bassam suka rik’o musu sai ya jira su suka shiga dasu bayan sun zube a parlor,sannan shima ya wuce cikin,,a master bedroom d’insa ya tarar da ita tana ta kokawar sauke zip sai dai ta kasa,inda take ya k’arasa ya tsaya ta bayanta had’e da janye hannunta a gurin,ta cikin mirror ta kallo fuskarsa tana kallon yanayinsa ta d’an d’auke idanunta a kansa tana kallon gefe zuciyarta fal fargabar abunda zai biyo baya,tana can tunanin bata san ya aka yi ba sai ji tayi yana k’ok’arin zare hannun ta daga cikin rigar,a d’an firgice ta d’ago ta kalleshi,shima d’in sai ya bita da kallon ya akayi.? Ajiyar zuciya tayi sannan ta matsa ta bar gurin da nufin tafiya wanka,har tayi gaba ya rik’o hannunta a hankali ta dawo,a gefen bed ya zaunar da ita then shima ya zauna,sai daya rik’o hannunta sannan yace

      “Me yasa kika sa kayan nan..!?”

     Saurin kallonsa tayi da alamun tambaya a fuskarta tace

       “Wanne.!?”

    Harararta yayi ya d’an matse hannunta dake cikin nasa har sai da tayi y’ar k’ara

       “Arhhg! It’s hot fa..!”

  

     “I knew ai,,zaki fad’a ko saina hukunta ki ne.!?”

   Shagwab’e fuska tayi idanunta sai kyalli suke alamun hawaye har sun kwanta suna daf da fara zubowa  

    “Amma na ga dai ai ni da ka gaisa da mutane bance komai ba,sai nice dan na saka kaya zai zama laifi.!?”

      Idanu kawai ya zuba mata yana kallon yadda ta had’e rai

      “Shi ne mene to dan na gaisa da mutanen..!?”

     D’agowa tayi ta kalle shi idanu taf hawaye tace

      “Har da mata ma ai ka gaisa da su.!”

     Siririn tsaki ya saki yace

      “Mene ne to dan mun gaisa.!?”

     Wani irin kallo ta masa mai cike da b’acin rai da tsananin kishi,a fusace ta fauce hannunta daga rik’on da yayi mata ta mike tana k’unk’uni zata bar wajen yayi saurin fizgota,jikinsa ta fad’o a tsorace ta d’ago tana kallonsa jikinta na wani irin shivering,,idonsa fal b’acin rai yace

     “Ni kike fad’awa wannan maganar..!? Ina tambayarki kina bani amsa a tsaye,saboda kin mai dani abokin wasan ki ko dan mene ne.? Wata rana idan baki yi wasa ba sai na mare ki..”

     Tureta yayi daga jikinsa ya mik’e a fusace ya bar ta a wajen,abunda ta hango cikin idanunsa yasa ko motsi ta kasa yi a gurin,,shima d’in kuma tunda ya shige bathroom sai daya d’auki kusan mintuna sha biyar sannan ya fito sanye da bathrobe,fuskarsa kana kallo zaka san baya cikin yanayin jin dad’i,ba tare daya kalli location d’in da take ba yace

     “Zaki tashi ne ki bani guri ko saina zo kanki..!?”

     A sad’ad’e ta mik’e idanunta suna zubar da hawaye,ta gefensa ta rab’e za ta wuce,sai ya d’an waiwayo kad’an ya sakar mata harara,kallon yadda take hawaye tana tafiya cikin rashin kuzari ne yasa shi cewa

      “Zo nan..!”

    Babu musu ta dawo a hankali ta tsaya d’an nesa da shi kad’an dan ita dai tsoronsa take ji gaba d’aya musamman yanzun nan,ajiye dryer d’in hannunsa yayi da yake busar da kansa da ita sai ya k’araso inda take a tsayen,a hankali ganin ya kusantota ta yi baya ya sake matsowa,ta d’aga k’afarta zata sake matsawa yace

    “Idan kika sake ko taku d’aya kika k’ara Allah zaki gane baki da wayo..”

    Tsayawa tayi a gurin ta kasa motsawa sai hawayen da suke ci gaba da sauka,har ya k’araso daf da ita bata kuma attempt na matsawa ba,palms d’insa ya d’ora saman shoulders d’inta had’e da janyo ta jikinsa,a tare suka yi ajiyar zuciya…..

Wani irin sonsa ne mai had’e da fargabar yadda yake treating d’inta a lokaci guda suka sake shigarta a hankali hawaye sai suka ci gaba da sakkowa saman fuskarta,kula da yanayinta sai yasa shi zagaye ta da duka hannunsa yana sake sauke wahalallun ajiyar zuciya,shi kansa ya sani son da yake mata da kusancin da suke da shi ba zai tab’a iya bashi damar d’aukan wani matakin kirki akanta ba,nd her tears too,it hots him within shi yasa baya jurewa ganinta a irin yanayin,,ita kam jin irin rik’on da yayi mata ne yasa hawayenta k’ara gudu,tsoro da fargaba masu girma suka sake shigarta,sheshshek’ar kukan da take a ciki jinta kwance a jikinsa ya kufce,dama she is in need of arms da zata kwanta tayi kuka,sai gashi ya bata damar kwanciya a jikinsa,luf ta sake yi a jikinsa tana kuka mai tsuma zuciya a hankali sai ya d’ago fuskarta ya zuba mata idanunsa,kafin yasa hannun ya goge mata su yana kad’a mata kai,buh still a gareta hawayen ci gaba suke da sauka uncontrollable,d’an b’ata fuska ya kuma yi kamar can baya kafin ya bud’e baki da kyar yace
      “Stop shading tears..”
    Cak taji komai ya tsaya kamar anyi ruwa an d’auke,sai ta d’ago ido tana kallonsa itanma,ita dai haka nan bata san me yake faruwa ba amma sai take kallonsa da wani irin fuskar mamaki,duk da bata san mene ne yake going through ba amma yadda yake mata a wasu lokutan sai take ganinsa kamar wanda ya had’u da matsalar shafar aljanu,yanzun zai murd’e da fushi amma ana jimawa zai koma tarairayota,”me hakan yake nufi ne.?” Ta tambayi zuciyarta,,sake goge mata fuska yayi sannan ya jata cikin jikinsa yana sake rik’e ta sosai kamar wani zai kwace masa ita,sun d’auki lokaci a tsayen har ta ji a ranta ina ma ace zasu dawamma ne a hakan,amma sai ta ji shi yana k’ok’arin raba gangar jikinsu,saurin rik’e shi ta sake yi cike da damuwa cos gani take yana sakinta zasu koma kamar da,hannunta ya b’are daga jikinsa a hankali sannan ya rik’e hannunta suka wuce bathroom,sai daya goge mata make-up d’in fuskarta da remover sannan ya had’a ruwan wanka,duka tana gefe tana kallonsa har ya k’are bata bar kallonsa ba da tsantsar mamakinsa,inda take tsaye ya k’araso da zuwa bai yi shawara da ita ba ya kwance mad’auran rigar daya sa mata ya jata cikin tube,a bakin tube d’in shima sai yayi detaching nasa ya zubar a gurin,a tare suka yi k’asa suka shige cikin ruwan,cikin zuciyar ta kam zuwa lokacin ta daina mamakin dalilin da yasa shi tarairayota bayan yasa ta kuka,haka nan sai take ganin kamar dama manufar buk’atar tace tasa shi yin hakan,,wanda a tunaninta da zaran ya samu nutsuwa shi kenan,zuwa anjima tayi masa laifi sai yace zai sake hukunta ta. Wasu hawayen taji suna k’ok’arin sauka amma sai tayi k’ok’arin mayar da su,,tana a cikin yanayin alhinin gently ta tsinto palms d’insa ta cikin ruwan suna yawo a jikinta,da sauri ta sauke idanunta a gurin,ilai d’in kuwa sune suke yawo suna mata wani irin cud’ewa da wani soft sponge,shi ba cotton ba kuma ba woolen ba,bata iya magana ba sai ajiyar zuciya data yi tana lumshe idanunta masu cike da bacci,har ya k’are tana mamakinsa da dalilinsa na sake yin wanka bayan fitowarsa kenan ya tarar da ita a d’akin ya fara mata fad’an dalilinta na saka kaya,,bayan fitowarsu daga wankan shiya shirya ta cikin wani sexy pyjamas na mata mai taushi da kyaun tsari,sannan shima d’in ya shirya,after kuma sai suka kwanta nd har a lokacin tun daya mata maganar ta daina kuka ko a bai sake furtawa ba,,a saman bed d’in ma cikin jikinsa ya sata a hankali sai take sauke ajiyar zuciya,duka sunyi wani irin shiru yayin da garin duka ya d’auki shirun,k’asa² har bacci ya fara fizgarta ta jiyo shi yana fad’in
      “Nayi miki tambayan dalilin ki na saka kaya kin maida ni sakarai ko..!?”
     Wani irin fad’uwa gabanta yayi cos a tunaninta tayi zaton zuwa lokacin ya hak’ura da jin amsar ne tunda taga ya jata jikinsa,ashe ba haka bane yana sane da abunda yake,a d’an rikice ta d’ago kanta ta kalle shi,idanunsa a rufe suke amma alamu sun gwada baiyi baccin ba,,maganarsa ta sake jiyowa yana fad’in
      “Am asking kina kallona ba tare da kin bani amsa ba.”
    
       “Amm! Wane kayan wai..!?”
     Ta tambaya saboda rashin bambance d’aya a cikin biyu da tayi,idanunsa ya bud’e ya sauke a kanta da yake itama shi d’in take kallo,sai ya had’e fuska yana fad’in
      “Kada ki rainamin hankali,za ki ce ne baki gane wanda nake magana akansu ba.!?”
     Rau² idanunta suka yi tana shirin fara masa hawaye,da sauri ya tare ta da fad’in
      “Kada ki sake kimin kuka,,tambayar ki nayi,ki bud’e baki ki amsa min idan ba haka ba..!”
      Sai yayi k’wafa kawai ba tare da ya k’arasa fad’ar abunda yayi niyya ba,,marairaicewa tayi cikin muryar kuka tace
     “Amma! Ai naga kai kace na sa su..”
     Kallon k’asan ido yayi mata da fad’in
      “Wanne d’in nace kisa.!?”
     Sai tace “Wanda muka fita da su.”
     Sai daya harareta sannan yace
       “Am i querying about it..!?”
      Shiru tayi tana sake kallonsa sannan tace
     “To ai ni ban san me kake tambaya ba.”
    Kansa ya gyad’a a hankali yace
      “Ban yarda ba,,za ki fad’a ko saina miki wulak’anci yanzun..!?”
    Kuka ta fashe masa da shi,a hankali sai ya saki tsakin takaici da fad’in
   “Rufe min baki,,ko na yi miki wani abu ne.!?”
   Kai tayi saurin girgizawa
   “Toh! Rufemin bakin ki a nan..”
   K’ok’arin had’iye kukanta tayi,sai daya bari tayi shiru sannan yace
  “Oya! Tell me,whom allows u to wear..!?”
     Jikinta har wani irin zillo yayi saboda tsoron abunda zai iya faruwa amma sai ta dake tace
     “Dan Allah kayi hak’uri..”+
   “Uhmm! Zan yi ai,amma first ki fad’a min waye yace kisa su..!?”
  
  “Me d’in..!” Ta tambaya cikin damuwa,lafiyayyen tsaki ya sake yi kafin ya dage ya ture ta gefe,ransa a mugun b’ace ya fara masifa
  “Da Allah kada ki maida ni wani ba gidaje mana,tun d’azun kin sani sai maimaita magana d’aya nake,ina tambayarki kina ta wani neman raina min hankali,i know ai kin san akan abunda nake magana,amma shi ne zaki nuna kamar baki sani ba,,to kayan da kika fara sawa nake magana akansu,waye ya baki permission na sawa har ki fita da su gabansu.? Da a haka zaki ratsa dubannin mutanen can…?”
    K’amewa tayi a gurin daya turata kamar an dasa ta,cikin kuka tace
   “Kayi hak’uri,, Allah bazan kuma sawa bama duka..”
    Tsaki yaja yace “Ni bance ki bani hak’uri ba,all i want to know shi ne ki fad’a min wanda yasa ki sawa.”
    
     “Babu kowa.” Tace
   
     “K’arya ne,,dole akwai wanda yasa ki,idan kin dage akan babu kuma sai ki fad’amin dalilin ki na sawar.”
     Saurin tsallakowa jikinsa tayi cikin kuka ta sake k’ank’ame shi tana bashi hak’uri,amma da yake uban y’an taurin kai ne ko kulawa bai ba,ya dage akan sai ta fad’a masa,k’arshe dai da kyar tayi claiming kanta a matsayin mai laifin,ai kuwa yadda ba ta yi zato ba sai daya nuna mata KUSKUREN ta,bayan ya yanka mata warnings masu zafi akan kada ko da wasa ta kuskura ta sake gangancin sawa matuk’ar ba wa shi kad’ai ba sai ya sab’a mata,tana kukan tayi ta bashi hak’uri,,yadda yayi mata da ganin irin damuwar data shiga k’arshen da yaga tana ta kuka sai ta bashi tausayi,a hankali ya sake janta ta koma samansa,sai daya gama rarrashinta,bayan ya tabbatar tayi shiru sannan yayi preparing masu hanyar samun nutsuwa dukansu,tsakanin miji da mata sai Allah,cikin k’ank’anin lokaci tuni suka manta da abunda ya faru tsakaninsu,suka shiga faranta ran junansu.
      Washe gari da safe kuwa k’in barin kowa ya shigo apartment d’in nasu yayi,,duk wani aiki kuma shi ya taimaka mata suka yi,cikin so da amincewa da juna,,after sunyi wanka sun shirya sai suka kwaso gifts d’in da suka samu jiyan,cikin tsantsar k’auna da kulawa suke bud’ewa,yayin da mafi yawancin kyautukanta suke d’auke da wasu irin necklaces masu azabar kyau cikin tsari mai burgewa da tsada,,washe gari ko da yake Monday ne duka suka shirya komawa skul yayin da Hammad yake hutun angwanci,shi ya kaisu can Pennsylvania d’in,kuma bai dawo ba har suka gama abunda suke suka dawo tare,,yayin da  b’angaren su Sultan kuwa tun daga kan abunda ya faru a daren Sunday d’in da aka yi dinner d’in nan sai ya canjawa musu fuska,magana ko sunyi masa ita a dak’ile yake amsa musu,tun abun yana damunsu har ya zama sun saba da halinsa,shi d’in a nasa gefen duka yana yi musu haka ne ba don komai ba sai don gane illar karb’ar sak’o a hannun wani mutumin ba tare da sun duba ba,a cewarza tunda har suka kasance masu kula da al’amuran da suka shafi bincike dole ne sai sunyi takatsantsan da rayuwarsu gudun wata rana kada a samu damar cutar da su.
*4 month leave..*
        Bayan kimanin wattani hud’u da komawarsu New York,wanda yayi dai² da kwanakin auren su,rayuwa ta ci gaba da tafiya musu,yayin da yanayi yake dad’a sauyawa wata rana jin dad’i wata rana kuma sai yazo a kishiyarsa,dole ne dama kuma a rayuwa sai an samu hakan ya kasance,tunda har tsakanin harshe da hak’ora ma akan samu sab’ani,,a Nigeria kuwa a dai² wannan lokacin tuni maganar auren su Badra tayi nisa,dan Daddy da Abba’nsu Sultan tuni sun tsayar da lokaci nan da watanni biyu masu zuwa auren,,a b’angaren Sadeeq shima da yake tare da su a nan U.S d’in tun kafin lokacin tuni ya sanar da iyayensa batun Zeeharis wacce tun bayan zuwansu bikin Hammad d’in bayan komawarsu New York sai suka mak’alewa juna,kuma shima d’in zuwa lokacin har iyayensa sun je sun nema masa aurenta,,soyayya mai tsafta suke gudanarwa a tsakaninsu wacce bata b’uya,duk yayin da aka ce kayi zama d’aya da su duka sai ka gane asirin zuciyoyinsu,zuwa yanzun kam da komai ya bayyana a gare su sai duk suke mamakin yadda akayi a bayan suka kasa fahimtar soyayyar Sadeeq d’in da ita Zee.
     Lokaci yaci gaba da tafiya,yayin da suke ta shirin komawa 9ja auren su Sadeeq,duka da yake wata d’aya ne ya rage sai suka yanke shawaran tafiya da wurin cos suna so suyi shirye² da dama a bikin,,amma kasancewar a lokacin su Badran suna kan zana exam sai suka d’aga tafiyar tasu,,sai da biki ya rage musu saura sati biyu gaba d’aya sunnan sai suka tattara su ka yo Nigeria,,cikin y’an kwanakin da suka saukan wanda duka sune suka rage musu a fara gudanar da events Mamma ta shiga gyare su babu ji bare gani,kasancewar irin sabon da Sabina tayi da Mamma da yake tun suna U.S kusan kullum ne sai sunyi waya taji lafiyarta,yaaa ko da suka diro k’asar sai tak’i yarda su tare gidansu da tuni ya kammala,acewarta idan za’a kai amare itama sai su tare rana d’aya dan kuwa itama amarya take,,hidima sosai suka shiga yi gaba d’aya tunda suka zo k’asar basu wani zauna ba su ne can su ne nan,kusan kullum idan suka fita basa dawowa sai wajen maghreb,hidimomin biki kuma sai dad’a kusantowa suke.
     Kwanakin su goma duka da isowa k’asar aka fara gabatar da programs,yadda basu zauna ba suma haka su Hammad basa samun lokacin zama,shi yasa ma sai Hammad bai wani damu da takurata ba,dan su kansu suna nan suna can ne,,rana guda aka kawo lefensu su ukun,Badra,Jannat da Zeeharis,ko wacce kuma Alhamdulillah anyi bajinta sosai a lefenta,dan an zuba musu kaya na gani a fad’a,,ita kanta Sabina a lokacin wasu irin fitinannun d’inkuna da tayi ta adana har mamakin kanta take,,wasa² an fara shagali gadan²,ta inda aka fara da kamu a ranar laraba,sannan sauran events suka shiga biyo baya,cikin tsari mai burgewa sai dai duk da kasancewar su y’ay’an gata hakan bai sa su yin k’arya da matsayinsu ba,biki tun daga ranar Wednesday suke yinsa sai da suka shafe kwanaki hud’u,a rana ta biyar data kasance ranar Sunday da safe aka d’aura aurensu su duka a masallacin umar bin khattab dake dangi,inda amare da angwaye suka had’e cikin shiga ta alfarma,Hammad da Sabina ma sai duk suka shige cikinsu shi yasa duk mutanen da basu san sunyi aure ba suke zaton auren mutum takwas ne ake yi,biki yayi kyau Alhamdulillah kuma ya tafi yadda ya kamata,babu hayaniya bare tashin hankali har aka yi aka k’are ba’a yi hayaniya ba,,a cikin wannan tsukin nefa Sabina ta samu labarin abunda ya faru dangane da auren Hammad da Falisha,godiya tayiwa Allah sannan ta sake k’udurcewa a ranta zata zage ta sake yi masa shamaki da duk wata macen da zata yi k’ok’arin rab’ar sa.
    Da dare kuwa ana ta shirin d’aukan amare,su Sabina ana gaba sai tsiya take musu suna kuka Hammad ya kira wayarta,lokacin tana zaune duk ta baje a gefen gado ana k’arasa shirya amare,da sallama ta d’auki kiran,ba tare da ya bari tayi magana ba yace ta same shi a mota,amsawa tayi sannan ta fice ko gyale babu a jikinta,sai data gama ratso taro ta fito zuwa inda yayi parking,motar ta nufa kai tsaye tana tafiya tana murmushi har ta k’araso inda yake,buh da zuwa sai ta tsaya ta wajen daga dai² gefensa,glass ya sauke slowly yana k’are mata kallo cikin d’inkin atamfa da tayi matuk’ar amsarta yace
      “Nan zan biyo ki ne madam.!?”
    Sai data rausayar masa da kai,kafin ta ja k’afafu ta zagaya d’ayar k’ofar,tana k’ok’arin shiga motar ne wata cousin d’in su Hammad ta taho da gudu² tana mata magana,,d’an dakatawa tayi har ta k’araso,sai Sabinar ta d’an kalleta tana murmushinta mai kyau tace
       “Ya aka yine Fauzah.!?”
   Y’ar dariya tayi mata while tana fad’in
     “Dan Allah aunty idan tafiya za kuyi zan biku gidan amarya..!?”
    Y’ar dariya tayi tana fad’in
   “Ehh! Ai nima kinga ban shirya ba,,amma ki bari idan zamu tafin zan miki magana kinji.?”
    Ta amsa tana ta yi mata godiya,sannan sai ta d’an matsa tayi ma Sabina rad’a a kunne,ai kamar mai jira k’amshin scent’s d’inta suna kaiwa hancinta ziyara ta ja baya da sauri tana rik’e hanci,matsowa Fauzah tayi tana k’ok’arin rik’o ta tai saurin d’aga mata hannu tana mata alamun taje kawai,amma sai Fauzar ta kasa tafiya ta tsaya a rikice tana mata magana,hancinta da bakinta ta rufe muryarta da tashin hankali saboda yadda turaren yake hawa mata kai tace
   “Fauzah.! Je ki dan Allah,,zan kira ki idan mun tashi tafiya.”
   Fauzah da damuwa ta bayyana saman fuskarta nd ta kasa gane abunda yake faruwa tace
     “Amma aunty..!?”
   “Jeki please.! Ina lafiya.”
     Saurin fitowa Hammad yayi daga motar yana jifan Fauzah da wani irin kallon tuhuma,cikin sauri kuma ya isa inda Sabina take durk’ushe tana kakarin amai ya d’agota yana tambaya
   “Helpmate.! Me yake damunki ne.?”
   Da hannu tayi masa alamun yace Fauzah taje,cikin damuwa da ganin canjin yanayinta a lokaci guda ya d’ago fuska babu wasa yace
   “Tafi mana,ko saina maimaita miki.!?”
   A ladabce ta amsa sannan ta bar wajen tana tafiya tana waiwayensu duk damuwa ta bayyana akan fuskarta,ko data tabbatar ta bar kusa da su ai ta kasa shigewa ciki ta rab’e tana lek’en abunda ke faruwa,tana tsaye a gurin tana kallon yadda Sabinar ke ta yunk’urin amai amma ta kasa,Yallab’ai hankali a matuk’ar tashe ya d’agota suka nufi mota,da mahaukacin gudu yabar gidan suka nufi asibitin nassawara da yaje shi ne a kusa da su….            Lokacin da Fauzah taga fitarsu daga cikin harabar gidan a sad’ad’e ta iya juyawa ta shiga gidan da fuskar damuwa,,yadda komai ya faru sai yake sake wulgawa mata a ido,har ta nufi masaukinsu da niyyar kwanciya cos a lokacin taji baza ta iya zuwa ko wane guri ba,sai kuma tayi tunanin dole tayi k’ok’arin sanarwa da Mamma halin da ake ciki d’in,,a lokacin har an fito da su Badra ita da Jannat za’a tafi kaisu,sai ta ji ana ta neman inda Sabinar take,kamar dai za ta yi shiru da bakinta sai ta ji baza ta iya rik’e abun a ranta ita d’aya ba,tana kuka ta fad’awa Mamma abunda ya faru tsakaninsu babu jimawa,,duk wanda yake gurin babba babu wanda zatonsa bai kawo kan ciki ne ba,sai duk suka bita da fatan sauka lafiya,,Mamma kuwa rarrashin Fauzah tayi da ta d’ora alhakin faruwar komai akanta,daga nan sai ta bar gurin cike da tsantsar farin ciki ta nufi bedroom d’in Daddy,,shigarta ciki babu jimawa kan wayarta tayi ta soma kiran line Hammad d’in na nan k’asar.+
      Shi kam a nasa gefen ganin yadda take yi kamar zata amayo y’ay’an cikinta ne ya matuk’ar tada masa hankali,a matuk’ar firgice yake jan motar yana jera mata sannu har suka k’arasa asibitin,tuk’i yake amma duka hankalinsa na kanta da wani irin damuwa mai girma shimfid’e a kan fuskarsa cos shi dai bai da sani akan komai bare yayi zaton faruwar wani abun,nd tunda suka taho d’in yunk’urin kawai take ta kasa tin aman,,tafiyar mintuna uku ya d’auke su suka iso cikin asibitin,basu jima da zuwa ba kuma aka karb’eta aka yi cikin emergency da ita,,bayan lokaci mai d’an dama da shiga da ita Dr yasa ayi masa magana da shi,har lokacin Hammad bai ji nutsuwar sa ta dawo masa ba,buh ana isar masa da sak’on likita yayi saurin bin bayan nurse d’in,a saman gadon da yake office d’in likitan wanda yakw duba marasa lafiya ya hangota kwance tayi lamo da drip a jikinta sai dai zuwa lokacin duk yunk’urin da take ta daina,siririyar ajiyar zuciya yayi yana sake k’ureta da kallo mai cike da ma’anoni daban² had’e da tausayawa
       “Have ur sit please.!”
      Dr ya fad’a yana sake  gyara zaman glasses d’in idanunsa,murmushin k’arfin hali Hammad yayi masa sannan ya zauna saman guest chair,buh hankalinsa duka a kashe yake
      “Am Dr JABEER MUHAMMAD.!”
        (of my novel,K’addara koh sakaci)
      Shima Hammad sai yayi masa murmushin amma ya kasa nutsuwa,sai da Dr JABEER yayi masa y’an tambayoyi dangane da itan da alak’arsu duka ta bashi amsa,sannan yayi masa bayanin komai da take faruwan buh sai dai bai riga ya yanke hukunci akan ciwon ta ba a time d’in,duk da yasan ko ya fad’a d’inma zai yi wuya ace ba hakan bane,buh sai ya k’are da fad’a masa yanzun yasa ayi mata test ne,saboda haka za su jira fitowar sakamako,zuwa k’arewar drip d’in daya jona mata,, godiya Hammad yayi masa sosai sai ya juya kad’an inda take yana sauke wasu irin wahalallun numfashi,murmushi tayi masa mai sanyi tana lumshe idanunta,shima sai yayi k’ok’arin k’irk’iro murmushin ya mayar mata,,bayan wucewar wasu lokaci masu d’an dama nurse d’in data d’auki jininta ta dawo da result,ta mik’awa Dr JABEER,kallo daya yayiwa takardar ya sauke ajiyar zuciya mai tafe da kyakykyawan murmushi,then ya mik’awa Hammad d’in hannu suka yi musabaha while yana fad’in
       “Congratulations dude.!”
      Kansa a d’aure yabi Dr JABEER da kallon mamaki kafin yace
       “Akan me kenan Dr.?”
      Takardar Dr ya mik’a masa sai yayi hanyar fita daga office d’in cos akwai round off da zaije yi a time d’in nd yana tafiyar yake fad’awa nurse d’in ta kula da ita,cos yana tunanin kafin ya dawo drip d’in zai iya k’arewa,cikin girmamawa ta amsa masa,sai ya fice ya barsu,itama nurse d’in fita tayi da nufin duba wasu aikin da take kafin ya k’are d’in,,,zubawa takardar ido yayi,zuciyarsa cike da wani irin mix-feelings da suka had’e guri guda suka bada wani irin bold expressions,ko gama nazartarta bai jira yayi ba ya damk’e ta a hannunsa,yana sakin murmushin da shi kansa bai san daga inane yake zuwa masa ba
      “Alhamdulillahillaziiy bii ni’imatihi tatimmus’salihaat..!”
      Yake ta jerawa har ya iso bakin gadon,daga gefenta kad’an ya zauna,while yana rik’o d’ayan hannun nata da babu komai a jiki ya damk’e shi da kyau,cikin k’arajin murna ya furta
      “Thank u helpmate,,thank u so much for making my day extra special..Ana ahabbuk-thtiir.”
     Sai ya sunkuya k’asa² ya bata wani irin light kiss a saman lips d’inta,,murmushi ta sake yi masa mai taushi da fad’in
      “Shhh! Wa’ana kamaan habibiiy,,anaa ahabbak-thtiir,,buh why are u thanking me,,am always ur’s fa ko har ka manta ne.? nd u are mine,,wannan kuma kyauta ne daga ubangijin mu daya azurta mu da shi,so gare shi ne kawai yafi cancanta muyi godiya duka ko ba haka ba.!?”
       Kai ya d’an gyad’a mata yana murmushi,a hankali sai ya d’ora palms d’insa ya shafi gefen fuskarta while yana cewa
      “Allah ya bamu ikon kula da shi,from now till lokacin zuwansa duniya,,nd ya bamu ikon yi masa tarbiyya akan tafarki madaidaici…”
     
     “Ameen” tace tana masa sihirtaccen murmushi before ta sake maida idanunta ta lumshe,from deepest na zuciyarta tana jin wani sanyin rahama na ratsata da yasa take jin kamar tafi ko wace mace sa’a a duniyar..Almost 2 hours suka d’auka a hospital d’in bayan an cire mata k’arin ruwan an sake dubata an tabbatar komai lafiya,sannan Dr JABEER d’in ya sake d’ora su akan shawarwarin yadda zasu kula da cikin,after kuma sai ya sallame su,sun masa godiya sosai sannan suka d’auki hanyar komawa gida,,fitowarsu babu jimawa suna tafiya cikin mota hannayensu mak’ale da juna cos suna cikin farin cikin da baya tab’a misaltuwa nd kanta na kwance a jikin shoulder d’insa,duka sunyi wani irin shiru amma kowa da tunanin da yake a ransa,a hankali murya can k’asan mak’oshi ya d’an kalleta kafin yace
      “Helpmate.! Ina muka nufa yanzun.!?”
     Idanunta a lumshe tace masa “Gida”
      Murmushi yayi yace “kin fasa rakiyar amaren.!?”
   
     “Um’um.! Ai nasan ko naje ma lokaci ya k’ure min,tuni an kaisu ma yanzun kam,,na je musu daga baya..”
     
     “Okay.!” Yace sai yaci gaba da tuk’i abunsa,,daga cikin asibitin Nassarawa sunyi y’ar tafiya sosai,a lokacin jin tafiyar tak’i k’arewa har take masa k’orafin har yanzun basu iso ba.? Sai yace mata “saura kad’an” ba tare data bud’e idanunta ba sai tace “toh”,basu jima da yin maganar ba suka iso bakin get d’in gidan,yana tsayawa da mota a hankali aka yage masa get,ya shige ciki yana d’agawa get man d’in nasu hannu cos glasses d’in motar duka suna rufe,har ya isa carport bata bud’e idanunta ba,sai data ji motar ta tsaya ne a hankali sai ta d’ago kanta ta kalleshi,murmushi yayi mata mai sanyaya zuciya sannan yace
     “Welcome to ur palace my Lady..”
   Y’ar dariya tayi sannan ta juya tana k’ok’arin fita while tana fad’in
      “Baka gajiya da zolaya wollahi..”
     Murmushi yayi yace
      “Kema haka..!”
    Fitowarta daga mota bayan ta kalli inda suke sai ta tsaya cak tana sake k’arewa ilahirin farfajiyar gidan kallo,tabbas ba gidan Mamma bane nan d’in,”shin ina ne to nan d’in ya kawo su.!?” Bata gama tunanin ba taji ya bata wani irin wawan rungumar da sai data so firgita,da yake ta bayanta yake tsayen sai ta d’aga ido a hankali ta kalleshi while tana furta
   “Ina ne nan d’in muka zo..!?”
    “It’s our new home.”
     Ya bata amsa a tak’aice,gyad’a kai kawai tayi sannan tace
      “Toh ai naga ba nan ka d’auko ni ba,,shi ne zaka taho da ni.?”
     Wani irin kallo yayi mata mai d’auke da sak’onninsa sannan yace
      “Da na tambayeki me yasa baki min specifying ba.!?”
     Jimm tayi tana sake bin ilahirin gurin da kallo gaskiya ta ko ina gidan yayi mata ita kam,yadda tun daga haraba gidan ya tsaru tamkar wanda aka kwafo daga k’asar turawa ko aka d’auko hayar masu ginin daga waje,duk inda ta kalla sai ta ganshi gwanin burgewa,duk girman gidan kuma ta side’s dinsa an wani k’awata shi da wasu irin shuke² masu matuk’ar kyau da dad’ad’an k’amshi,,hannunta ya rik’o a hankali sai ta d’aga kai ta kalleshi sannan suka fara tafiya slowly daga carport d’in zuwa ainihin k’ofar da zai sada su da cikin gidan,suna fara tafiya daga gurin da suke tsayen amma ji take inama ya kyaleta ta gama k’arewa gidan kallo,a cikin zuciyarta kuwa banda addu’ah babu abunda take musu da godiya ga Allah akan yaci gaba da kare su daga sharrin masu sharri sannan ya sawa zamansu albarka tare da kad’e musu dukkanin wani abun k’i,har suka iso bakin k’ofar da zata sada su da cikin gidan bata bar kalle² ba,ko bakin k’ofar ma dai shi kansa abun kallo ne,haka taita kalle² abunta yana tsokanarta,nuna masa tayi ko a jikinta,da taje wani gurin tayi gara tayi a nata,a haka har ya janyeta suka shige ciki yana rik’e da ita yana mata dariya,shi kansa parlor’n abun kallo ne dan ta ko ina ya gama had’ewa,fad’ar irin dukiyar da aka zuba a gurin kuwa zai zama kauyanci ne da b’ata baki just imaging,sai da ya d’an zagaya da ita saura gurare daga bedroom d’inta zuwa su kitchen da master bedroom,d’akunan yaransu da suke fatan haifa,,ko ina ya kaita ta gani kuma ta yaba,tsabar murna har kasa magana tayi sai k’ank’ame shi da tayi tana ihun murna da yi masa addu’o’i iri²,bayan d’an lokaci sun gama kewayensu a nan cikin gidan da yake dare ya dan fara yi sai ya janyeta suka nufi master bedroom d’insa,,kada kuso ganin k’auyancin mutuniyar a time d’in da suka shigo,saboda yadda taga an tsara d’akin gaba d’ayansa cikin adon white daga kayan ciki har paint komai fari ne zallah babu sirkin colour,sai ta shagala da kallonsa tana kuma mamakin yadda aka tsara gidan,iskar daya busa mata a fuska ita tasa ta kallonsa da sauri,cos lokacin duka ita har ta manta ma jinya take sai ya kamo hannunta ya zaunar gefen bed sannan ya kwanta a saman laps d’inta,hannunta ta kai saman kansa tana shafa kwantaccen sumarsa da ya d’an d’aga,idanunsa a cikin nata suna kallon juna da wani irin shauk’i a cikin idanunsu,sun d’auki lokaci suna ma juna kallon tsakiyar ido kafin suka sauke ajiyar zuciya,,k’afafunta ta fara motsawa a hankali saboda wani irin yamm da taji suna yi mata sai ya d’ago ya kallota da fad’in
     “Lafiya..!?”
     “Ummm! K’alau.”
    Tace tana ci gaba da motsa k’afar,tashi yayi ya zauna sosai a hankali ya kamo k’afafun ya d’ora saman nasa da yayi flexing ya fara matsa mata su,lumshe idanunta tayi a hankali sau ta zame ta kwanta tayi wani irin luf kamar tana bacci,sai duk d’akin ya d’auki shiru sai kukan A.C dake fita,tafiyar tsutsa ya d’an yi mata a tafin k’afa,sai tayi saurin lankwashe su,tana shirin janyewa ya sake damk’e su da kyau,still yana ci gaba da mata matsar k’afar yana kuma had’a mata da tafiyar tsutsa,dariya tayi tana fad’in
“Please habibiiy.! Ka bari babu dad’i fa.”
    Murmushi yayi mata mai sauti yace
“Babu dad’in kike dariya.!?”
“Ehh! Babu wani dad’i kam,buh kawo k’afarka kaji.”
Sai ya sake yin murmushi kawai yana mak’ale mata kafad’a,cikin salon son ya canja musu hiran kuma sai yace
   “Yaya kika ga gidan naki..!?”
“It was nice nd very massive..”
Ta bashi amsa cike da zumud’i
   “Umm! Yayi miki kyau ne.!?”
  “Ehh! Sosai fa yayi matuk’ar tafiya da ni” har ta yi shiru kuma sai ta kalle shi da fadin “Umm! Shud i ask.!?”
Yace “Mene ne.!?”
  Juyawa tayi ta hango gefen had’ad’d’en reach-in closet d’insu while tana fad’in
   “Waye ne yayi illustrating d’insa.!?”
Murmushi yayi mata da fad’in
   “Ohh.! Yanzun baki san aikin waye wannan ba..!?”
Gyad’a masa kai tayi saurin yi tana kallonsa,sai da sake yin murmushi then yace
  “Sai na fad’wa Bassam nace kin manta aikinsa..”
  Y’ar dariyar tayi irin ta mantawa d’in nan da fad’in
“Please habibiiy banyi tunanin shi yayi bafa.”
Ba tare da ya sake cewa wani abu ba sai ya ci gaba da mata tausar yana yi yana dariya k’asa²,daga nan kuma sai suka zarce da wasanni wanda ya kaisu ga bawa juna kulawar data dace.
  A gidan amare da angwaye kuwa a wannan daren sun raya shi ne da nuna tsantsar godiya ga mahalicci wanda shi ne ya ara musu rana da kuma ganin nasu lokacin suna masu tsayin rai,daga nan kuma sai suka k’arasa raya shi da nunawa juna tsantsar k’aunar da aka jima ana ginawa..Tun daga wannan ranar haka ko wace rana da zata zo ta wuce sai ya zama suna cike ne da nunawa junansu kulawa ta musamman tare da sake k’arfafa alak’ar dake tsakaninsu,,ko wane b’angare dai² gwargwado suna iya k’ok’ari wajen girmama junansu,babu raini bare wulak’anci,a haka rayuwa ta ci gaba da tafiya.
  Bayan wucewar wasu kwanaki da yin bikinsu,tun a gida Nigeria suka gurji sadakinsu son ransu,daga nan sai suka fara shirin komawa bakin aikinsu,cikin d’an tak’aitaccen lokaci da zuwan sun samu damar zagaye dangi yayin da suka cika y’an uwa da alkhairi,bayan nan kuma suka bi jirgi zuwa k’asar ta U.S cike da nasarori da a kullum suke fatan samu,ma’ana su kasance k’ark’ashin inuwa d’aya.
  Tun a Nigeria kafin su koma New York da incidence d’innan ya faru a ranar da za’a kai su Badra,tsakanin Sabina da Fauzah,shi kenan sai ciki ya fallasata,tun daga nan tsurfar yau da ban na gobe da ban,sai dai bata wani laulayi mai zafi,bacci ne dai take yawan yinsa bayan shi ko sai d’an banzan kwad’ayi,idan ta samu lime juice ta tsiyaya shi cikin cup sai ta kawo zuma ta zuba akai,haka za tayi ta shan abunta,yayin da tsamin ke mata dad’i har ranta,Yallab’ai dai tun yana nuna baya so har ya gaji ya rabu da ita,cos yayi ko daya tuntub’i Likitoci da dama suka ce masa babu matsala sai ya zuba mata idanu,wani lokacin ma shi yake had’a mata,tun abun bai shiga jikinta ba har ta saba ko me zata ci sai ta sha had’in lime juice d’inta take samun kwanciyar hankali,,a b’angaren skul ma dai tunda suka dawo d’in suna zuwa babu fashi kuma ko kad’an babu abunda ya tab’a karatunsu,kullum suna kan mai da hankali da duk abunda ke faruwa,,a hankali kwanaki suka ci gaba da tafiya yayin da a kullum take cikin samun kulawa ta musamman daga gare shi dama su Badra da tun bayan da suka san tana d’auke da juna biyun suke kulawa da ita sosai cikinta kuma yana k’ara girma.
A wani wayer gari lokacin cikinta yana da wata biyar dan har ya d’an kumburo ana iya ganewa,kasancewar safiya ce suna kwance manne da juna,tun bayan da suka idar da sallah sai suka koma baccin safe kasancewar yace fad’a mata ranar ba zai fita ba,sai ga kira around 6:00am ya shigowa Hammad d’in daga office d’insu,cikin gaggawa bayan ya amsa kiran ya fara shirin fita,tana daga kwancen ta kalle shi ranta a d’an had’e tace masa
   “Amma fa cewa kayi babu inda za ka yau d’in.! Yanzun kuma fa.!?”
  Waiwayowa yayi yana kallonta shi kansa ba’a son ransa zai je ba,amma saboda ance masa it was urgent,kuma kiran yana da muhimmanci ne yasa zai je d’in
  “Aasiif my Lady.! Ya zama dole ne sai na fita,buh kinsan tunda nace bana fita yau,idan ba irin wannan kiran ba babu dalilin da zai fitar da ni..Zan je na duba naji kiran da ake min,,amma ba zan dad’e ba sosai kinji..!? In sha Allah yanzun zan dawo.!”
Yadda yayi mata magana cikin taushi sai ta d’age zpread d’in da take rufe da shi ta sauke k’afafunta k’asa,a hankali ta taso zuwa inda yake cikin tafiyar ta mai jan hankali,yana tsaye yana buttoning shirt d’in jikinsa har ta iso sai ta rik’e hannunsa,bayan ta taimaka masa ya k’arasa shiryawan sannan cikin sauri tayi making masa 1 cup na coffee da toast,a tsaitsaye ya ci sannan suka yi sallama ta masa rakiya har bakin k’ofar apartment d’in nasu,,yana fita apartment d’in sai ya d’an tsaya a bakin door d’insu yana kallonta da wani irin yanayi masu wahalar fahimta a tare da shi yace
   “Bye Lady,,ki kula min da kanki kinji,,nd kada kiyi aiki mai wahala,in sha Allah i will be back soon..”
    Murmushi tayi masa mai k’arawa zuciya nutsuwa sai ta d’an rausayar da kai cike da kewarsa tace
      “Tamm!”
  Sai yace “kinyi ALK’AWARI baza kiyi ba ko.!?”
    Kai ta gyad’a masa tana lumshe idanunta,a hankali sai ya matso jikinta ya bata warm hug slowly ya had’a da bata peck chicks d’inta zuwa forehead d’inta,stilltana kwance jikinsa ya kai hannunsa ya shafo cikinta yana sauke ajiyar zuciya yace
   “Please Lady,, kada ki bawa baby wahala,idan kinji ba zaki iya zaman ba,please ki nemi su Badra su taya ki zaman kin ji..!? Amma kada kiyi aikin da zai gajiyar da ke.”
    A tare sai suka sake sakon siraran ajiyar zuciya then ya wuce yana waving d’inta,tana tsayen tana kallonsa ya fara tafiya,fitowa tayi kad’an ta tsaya jikin k’ofa tana kallon bayansa har ya kai bakin elevator yana niyyar shiga,,haka nan bata san mene ne ya faru ba taji wani irin mummunar fad’uwar gaba ya ratsa mata zuciya har bata san lokacin da ta kwalla kiran
       *”HAYAT..!”*
     Slowly ya tsaya yana sakin wani irin murmushi mai narka zuciya kafin ya d’an juyo gently,inda yake tsayen ta fara tahowa zuciyarta a raunane har ta iso,tana zuwa sai ta shige jikinsa ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi,haka nan sai take jin cikin k’ank’anin lokaci tafiyar tasa ta tsaya mata a rai kamar tace masa ya fasa zuwan,buh k’arfin hali irin nata sai yasa ta kasa bud’e baki ta sanar masa yanayin da take ciki,,holding d’inta yayi tight suna nan tsaye har wayarsa ta sake yin k’ara,yana dubawa ko da yaga kiran daga Sultan ne,sai ya mayar da wayar silent a hankali bayan sun more tsayawa rungume da junan yayi ta jero mata kalaman da yasan zasu k’ara mata k’warin guiwar zama har yaje ya dawo d’in,sannan ya zareta a jikinsa yana goge mata hawayen,,sai da suka sake yin sallama yana niyyar tafiya ta rik’e shi gam,still tana kallonsa d’in sai ta masa alama ya d’an rage mata tsayinsa,hannayenta ta kai saman wuyarsa bayan ta zagaye shi da su,a habakli sai ta kai bakinta kan nasa,cikin salonta passionately tayi kissing d’insa,almost five minutes suna mak’ale da juna kafin tasake shi a hankali ta koma baya tana masa d’an murmushin k’arfin hali,cikin mutuwar jiki shima yayi saurin shigewa cikin elevator d’in,amma deeply ji yake kamar ya fasa,buhbaabu yadda zaiyi dole ne yaje shi yasa ya bawa kansa k’warin guiwar tafiyar,sai data ga tafiyarsa sannan ta juya a hankali tana sauke nauyayyun ajiyar zuciya,,ko data koma cikin apartment d’in jikin glass curtain wall d’insu ta nufa tana hangen waje,almost 5 minutes da tsayawarta a gurin sai ta hango fitarsa daga cikin Tawer d’in,hannunta ta sauke jikin wall d’in ta dafe sosai while d’ayan yana dafe da cikinta,cikin muryarta mai tattare da rashin kuzari ta furta
     “Good luck for all ur efforts habibiiy,may u get what u truly deserve,,my good wishes are always with u,go for it HAYAT.!”
    Tamkar ya jiyo me tace a dai² lokacin sai ya d’ago kansa slowly ya kallo location d’in da dark glass wall d’in yayi masa shamaki da gano abunda ke ciki had’e da yin kwantaccen murmushi,cikin wani irin sanyin rahama shima sai ya furta
   “U might not be with me,but u are always in my mind..The way u walk,fight,smile nd cry,is all am dying to see…I miss u baby,cos u are my life..”
    Sai daya d’an jima yana kallon gurin sannan a hankali ya k’arasa carline ya shige motarsa had’e da barin harabar gurin….

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *