MISBAH BOOK 3 CHAPTER 8 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 8 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

Nan ya karba yana dubawa sai ya lura hotunansu

ne da Farida suna yara a ciki da irin wasiku da card da suke aika wa juma.

Haka nan ya ji ransa ya baci, ya ajiye su gefe

guda ransa bace, har suka isa suka dauko ta, ta lura

ba walwala a fuskarsa, ta daure ta yi masa magana,

“ba tambayar ya exams din, ko kallonta bai yi ba yace,

“ya exams din? Allah ya ba da sa’a.

“‘Ameen ta masa tana tunanin me ke yawo a

kansa, can dai ta daure ta ce

« Uncle a kai mu yawo www.Dailynovels.com.ng

shopping mana tunda sauran lokaci. Bai yi niyya ba

amma sai yaran suka sa baki

«Eh uncle a kai mu,

please please,

“ba shi da zabi sai ya biye masu, ba

su gama siyayyar ba har karfe biyar, suka dawo

gida saboda yanayin nisa da go slow irin na Lagos,

in yamma ta yi ma’aikata sun taso. Sun shigo gida

suna ta tsalle-tsalle, suka samu Bahijja a falo da su

Baba Audi suna hira, wanda tun karfe uku ta dawo www.Dailynovels.com.ng

nan Farida ta samu dama tana ta kara shisshige

masa don ta ba wa Bahijja haushi, ta ji daci a ranta,

amma sai ta daure ta yi dariya tare da fadin

“sannun ku da dawowa, ya exams din?”

“Lafiya lau,

,” ta amsa kin ga daga nan ma Uncle

Deeni ya kai mu shopping, nan yara kowa ya soma

ciro abin da ya saya ita ma Farida ta ce,

“kin ga na manta ba mu siyo maki komai ba, in

ina tare da Deeni manta komai nake.”

Ta yi murmushi “Ai ba komai kuma duk abin da

kika siyo Deeni ya wadata ni da ninkin baninkin

Su Deeni ya yi murmushi ya matsa kusa da ita yace,

“Ta yiyu a ce Deeni ya fita shopping bai siyo

wa Bahijja komai ba my better half? na siyo maki

abin da kika fi so wanda kuma ba kya gajiya da shi kullum, kuma aka ba ki yana sa ki tsananim farin

ciki favourite dink ma na siyo a ciki, set dinsa

turare hot givincy’ body spray dinsa roll on dinsa

da turarena.

“Wow”! Ta mike da sauri ta yi masa wani irin

kyakkyawar runguma da sumba, ta ce,

“‘na gode

Deeni, really na ji dadi sosai Allah ya bar ni da

MAI SO NA.

“Ameen, ya fada yana murmushi, gaba daya farin

cikin Farida ya dawo bakin ciki, ta ji gaba daya

kokarinta ma aikin banza ta yi, tun daga safe har

yamma, ta harari Bahijja ta ce

“ba zan kyale ki ba,

zan nuna maki in har ina son abu sai na same shi,

ko kina so, ko Deeni naso, ko ba kwa so.”

Deeni ne ya katse ta

‘”zo nan Farida, ina da www.Dailynovels.com.ng

magana da ke, mu je can karamin falo, wannan abu

fa ya tunzura Misbah, duk kokarin ta danne zuciya

ta kasa, musamman da ta ga tsawon lokacin da

suka dauka suna magana ba ta san lokacin da ta

mike a fusace ba ta watsar da su turaren da gudu

tana jin zuciyarta kamar wuta, shi ke nan ya samu

masoyiyarsa, kina da labarinsu ba zai taba daina

son ta ba, ki sa ranki a inuwa, ki dau dangana, ki

bar shi da farin cikinsa, in har kina son sa kina son

farin cikinsa to, ki bar shi da Faridarsa, tsananin

zafin zuciya ya sa hawaye ko digo bai fito a idonta ba ga zafin zuciya ga tsananin fushi, tabbas Deeni

ya shiga a wannan lokaci za su yi ba dadi, dan haka

ta tashi ta sa wa kofar dakinta key ta rufe.

Rana ta farko ke nan da suka fara raba dakin

kwanciya tun aurensu.

A can kuwa Deeni ya kalli Farida cikin zafin

zuciya ya ce

“‘me kike so, me kike nufi?”

ya wurga

mata takardu da hotunan ya ce,

«kina mufin dan kin

tuna min

baya kina wani kirsa da gayu da

kwarkwasa za ki ja hankalina in yi abin da ban yi

niyya ba, ni za ki tuna wa soyayyarmu, ke awa, ke me kika sani game da so Farida? kin canja, ba haka www.Dailynovels.com.ng

na san ki ba, baki san waye Deeni ba ko?.

“Duk ikirarin da kike yi na cewa kin sanni, kin

san ina sonki, har yanzu baki sanni ba, idan ina da

niyyar auren ki ko baki min tayi kin tuna min

wannan shirmen naki ba, ni mai bugan kirji in

aureki ne.

“Wannan shirmen da yarintar da kike yi ba shi

zai sa in aure ki ba; eh naji, na yarda, na amince,

na so ki so na hakika. Sai dai kin manta abu guda,

lokaci ba abin da ba ya mantarwa, ba abin da ba ya

warkarwa, kin iya tuna min soyayyarmu amma ba

ki iya tuna min cin amanar soyayyar ba, baki iya

tuna min halin da na shiga ba, wannan halayyar

naki bai nuna komai ba sai son kai, a neman tuno

min bakin cikin da na manta, dan’uwana dake

kwance cikin kabari kina kokarin tuno min da abin

da ya min, wanda ya wuce na yafe, kullum ina

cikin masa addu’a

da nema masa rahama, mahaifina da na manta abin da yamin, muna zaune

lafiya ina kyautata masa ina neman albarkarsa, kina

nema ki tono min bacin ran da yasa min to, bari in fada maki abu guda,

“ya yan Yaya Shamsu,

“ya ‘yana ne confirm zan rike su, tamkar ni na haife

su, amma fa matarsa ba matata ba ce kuma ba za ta taba zamowa matata ba, a lokacin da kike zaune da

mijinki na taba zuwa gidanki na nemi kashe maki www.Dailynovels.com.ng

aure ko wargaza zaman lafiyar gidanki? dangana

na dauka na yi maku fatan alkhairi, amma ke me ya

sa kike kokarin wargaza nawa gidan da kwanciyar

hankalin gidana?

“Bahijja ba ita za ta hana ni auren ki ba, ra’ayina

ne ba zan aure ki ba, kuma bani da ra’ayin auren

mata biyu kuma babu mai canza min wannan

ra’ayi, gara ki sani, ki bar wani kewaye-kewaye

kamar yadda kika san jiya ba za ta dawo yau ba, HAR ABADA, kai kamar yadda safiyar yau

ta wuce ba za ta taba dawowa da yammacin nan ba,

to yaya kike zaton abin da ya wuce shekaru da

dama zai iya dawowa?

“Soyayyarki ta kare a tun ran da kika auri

dan’uwana, na yarda ba laifinki bane Kaddararmu ce kuma duka mun karbe ta, ta

wuce, a da lokacin da za ki auri dan’uwana ina isa da dagiyar da soyayyar da kike min din take da

ba ki yi protecting ba na yadda, anfi karfinki, kinyi aure kuma kin yi saurin mance ni, kin rungumi

mijinki da ‘ya’yanki, haka nan na yi fama na hakuri

amma ban taba tunanin wargaza auren ki ba.

Dan haka, yanzu kar ki yi wannan kuskuren,

soyayyarki ta wuce shekarun da suka wuce ki cire

wa kanki wannan abin da kika sa wa kanki na cewa

Deeni ya haukace a kan sona, dan haka yanzu zai

dawo da gudu ya sake hankacewa, rayuwata ta kare

a kan mahaukacin Farida ko? Wannan shi ne

tunaninki to, in shine, ki canza saboda Deeni

SHAUKINSA ya sauya na samu sayin shauki na

HAR ABADA.

“Karatu, in ma da niyyar ki shigo gidan nan ne,

to, ki sani ko kin samu ba a gidan nan za ki zauna www.Dailynovels.com.ng

ba, gidan Baba za ki zauna, tunda na lura ke ba

zaman arziki ki ke so a yi da ke ba, kin zama mai son kanki.

” Ya zura mata jajayen idanunsa tare da

watsa

mata takardunta,

“kar ki sake wannan

kuskuren, ni ba irin mazan da kika sani ba ne, ni Deeni daban nake.

Nan ya wuce ya bar ta a

wurin, ta bi shi,

maganganusa sun mata ciwo, ta ce

“to tunda abin

ya zama yar kiri-kiri ya fito na fito to, ina mai

tabbatar maka sai na aure ka, sai na shigo gidanka

kuma sai na tabbatar maka abin da ya shude

shekarun baya yana dawowa, sai na tabbatar maka

shauki baya canzawa, zan shigo gidan ko ta dadi ko

ta rashinsa ko ta tsiya ko ta arziki, nan gidan za mu

zauna da ni da kai da ‘ya’yana matsayin family.

Ya na jin ta amma bai tsaya ba balle ya tamka

mata. Sam, da ba haka Farida take ba, halayyar da

yake son ta dan su gaba daya sun canza, baya ga wanna bai taba ba wa wata mace dama ta shiga

HMMM LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe www.Dailynovels.com.ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *