MISBAH BOOK 3 CHAPTER 10 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 10 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

karkace daga kan daidai ba ko abin da ya kamala,

ko ba komai Farida kamar ‘yar’uwa take a gare ni,

‘ya’yanta da nawa duk mun zama abu daya, Shamsu

kuwa ni mai iya daukar nauyin matarsa da

‘ya’yansa ne har sai randa Allah ya karbi nawa ran.”

“Haka ne Deeni, kai kanka ka san ba abin da

nake nufi ba ke nan, sai dai kawai juya maganar

dan kauce wa manufata, kwarai kana iya rike

yayan yayanka da na kowane, ni ma nawa dan

yana can hannun wasu, ka ga kuwa ba ni da bakin

magana kan ‘ya’yan wasu, ni mai iya rike su ne

tamkar ‘ya’yan da na haila.

“Farida kuwa kana iya kula da ita duk inda take

wannan abu ne mai kyau, saboda ni ma da nawa

mijin ya mutu Allah ya kawo ka kana kula da ni, ka

aure mi ka ba ni mutunci da dangi da komai da ba

ni da shi, ka ga kuwa ba ni da bakin hana ka, kula

da Farida ko a gidansu ko a gidanka ko a matsayin

matarka ko a gadon barcinka, ka yi duk yadda kake

so, wannan halal dinka ne kuma lada za ka samu

mai dinbin yawa, ni kuwa ba zan taba maka bakin

ciki da samun lada ba ko samun abin da kake so ba,

sai dai munafurci da boye-boye ne ba na so, amma

meye na min karyar cewa ni kadai kake so?, tun

farko abin da kake so me ya sa ka yaudare ni da

cewa ni kadai kake son? me yasa ka min alkawarin

da ka san ba za ka iya cikawa ba, me ya sa ka jela

ni a yanayi da halin da nake ciki yanzu, me ya sa

ka jefa ni cikin danginka kana nuna min kabilanci

da nuna min Farida taku ce wani lokacin har a

Kalamanka kana nuna min kafi kusanci da ita

da ni matarka, ka fi ba ta muhimmanci fiye da ni.ka mai da ni sha-sha-sha?

*Ka sani ina sonka ina ganin kimarka da

darajarka kuma inabin ka ina maka biyayya ina gudun zuciya ko wani tashin hankali da zai shiga

tsakaninmu, zaman lafiva da faranta maka rai shi

na fi so da kauna fiye da komai, ina Fatan Allah ya

ba ni aljanna ta hanyar aurena, sai dai ka sani cewa

duk mutumin da ya min karya ya yaudare ni ya

karya alkawarin da ya min, ya ci amanar yardar

dake tsakanina da shi, to ba na sake gain daraja da

kima da mutuncin wanna mutumin ko waye shi.

Ni kuwa ba na iya zama da mutumin da ba na

ganin girmansa da kimarsa, dan haka idan haka ya

kasance tsakanina da kai ban san wane irin zama

zamu yi ba. Na san ni marainiya ce amma ba zan

zauna inda za a dinga nuna min kaskanci da nuna

min cewa ba ni da kowa ba, ba zan iya wannan

rayuwar ba koda ba ni da kowa ba ni da inda zan nuna bani da wata gata ba ni da uwa ko uba ko

dangi ko ‘yan’uwa da zan nufa, kana ganin kamar

ba ni da yadda zanyi ba ni da zabi sai zama da kai

don saboda ba ni da gata? ina so ka sani Allah ne gatana kuma

“‘Muddin ina raye, ba zan rasa wurin shiga ba,

kar ka dauka zan zauna da kai kuna nuna min

kaskanci, ko da ba ni da kowa ina da Allah ina da

sell respect ina da sell confidence, wannan ba mai

raba ni da su, sai Allah da ya ba ni su, kai da Farida

ba ku isa ku cutar dani ta wannan hanyar ba.

“Idan har jarrabawa Allah ya min da kai a

rayuwa insha Allah zan yi kokarin cin wannan

jarrabawar, ka sa ido ka gani, ka yi duk abin da ka

ke so da duk abin da ka ga dama, ba zan hana ka

ba, ba za mu sake jayayya ko musu da kai ba

“‘Ba zan sake cewa komai ba, ba zan sake shiga

maganarka ko rayuwarka ba sai dai zan dauki iya

abin da zuciyata da raina za su iya ne ba zan iya

daukar abin da ya fi karfina ba, ba zan bari har azo

ranar da za ka budi baki ka min gori ba, saboda halayyarka da

aikinka sun fara nuna

min hankalinka da tunaninka da zuciyarka sun yi wani

wurin kafin bakinka ya furta haka, ka san weakness

dima, ka san yadda za ka karya ni, ba zan bari haka

ya faru da ni ba, na ga rayuwa na ga halayyar

mutane da jama’ a da yawa kuma na karance dasu ba

abin da zai sake ba ni tsoro ko firgita ni, ko ya ban mamaki, weakness daya nake da shi, sai dai shi ma

ba zan bari ya ruguza ni ba, ka sani ba zan taba bari

ka ruguza ni ba, Deeni duk abin da zai ruguza ni

Zan yi saurin karkade shi da yakice shi daga gare ni

Tana gama fadi, bata saurare shi ba tayi

tafiyarla ciki, wani irin bakin ciki da bacin rai ya ji a zuciyaRsa ni faruda ke fadama wadannan maganganun tayi masa mummunar fahimta, macen

da yake ganin tafishi sanin kansa da Kansa, gaba

daya ya ji gidan ya masa duhu, ba shi da sha’awar

zama a gidan ma, Bahijja ta karya masa zuciya da

maganganunta, da ma tunaninta a kaina ke nan,

haka ta dauke ni, haka take kallo na? Ya ji ba shi

da sauran abin da zai iya fada mata dan haka ya sa

Kai ya fice a gidan.

Haka nan bangaren Bahijja ta ji zuciyarta ta

tsaurare ba ta da sha’awar sake gain Deeni ko

zama da shi saboda ta gani a zahiri, manufarsa da

abin da yake son yi ta kuma gane da ma can Deeni

karya ya yi mata da yaudara, da ma damace bai

samu ba na auren Farida yanzu kuwa ya samu

damar shine zai zo mata da wasu maganganu to

gara tayi wa kanta gata ta yakice shi a ranta wanda

a yanzu ma take jin ya fita aranta saboda cin amana da ya mata.

Dan haka, tafiyar da ya yi ma bai dame ta ba

kuma hakan ya kara tabbatar mata da abin da take fadi.

Deeni gidan gonarsa ya tare, ba ya zuwa ko’ina,

Yama kashe wayarsa saboda ba ya son sauran

damuwa da bacin rai, maganganun Bahijja ke yawo

a kansa, suna kona masa zuciya, wai Bahijjarsa da

ya sani ce kuwa ta yi masa irin wannan mummunar

fahimta? Ta rufe ido tana gaya masa maganganu da

duk suka z0 bakinta, shin ko harka da marasa lafiya

masu damuwa da matsalar kwakwalwa da take yi

ne ya sa itama ta soma shafar hankalin ta da

tunaninta?

Haka abin nan ya dinga kona masa zuci a

amma duk bacin ransa ya kasa cire ta a zuciyarsa,

tunanin wani hali take ciki musamman da wannan

tunanin a ranta da zuciyarta, tabbas ya san tana

cikin kunci da bacia rai,

“Bahijja, ban ci amanarki

ba, burina in faranta maki, in sanya ki farin ciki, in

gan ki cikin walwala, me ya sa kika bari tunaninki

ya jawo mana rudani cikin rayuwa? Ina son ki, ina

kaunar ki, ina ganin kimarki da darajarki fiye da

komai, ban maki karya ba, ban ci amanarki ba,

haka ban karya alkawari ba, zamanki cikin kunci

da tashin hankali da rashin fahimta yana daga min

hankali. Bahijja, ba wanda ya isa ya wulakanta ki

ko ya maki gori, ke ba abar wulakantawa bace, ke

abar so da kauna ce, halinki da zuciyarki mai kyaune.

“Me ya sa tunaninki da hangenki zai wargaza

mana rayuwar farin cikinmu? A halin yanzu yana

da kyau mu ba wa juna lokaci saboda muna da

bukatar haka, amma insha Allah zan fahimtar da ke

ba haka ba ne

matsayinki da darajarki a zuciyata da

rayuwata ba karami ba ne, bayan iyayena Bahijja

sai ke, ba ni da na biyunki. Haka ya kasance cikin

kewarta da tunanin halin da take ciki ga bacin ran sabani da rashin Fahimta

daYa. singa kwakwalwarta.

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *