MOON CHAPTER 7 BY NIMCYLUV

MOON CHAPTER 7 BY NIMCYLUV

                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

Saurin zare jikinta tayi ta nasa ta shiga haɗe fuska, Murmushi Faizak yay mata yana jin ransa babu daɗi cikin ƙasa da Murya yace “Am sorry,i can’t control myself idan muna tare” banza tai masa sai hawayen da suke shiga zuba daga cikin idanunta zuwa saman fuskarta,da sauri kuma ta fara tafiya tabar masa lambun gaba ɗaya, iska ya fesar kafin yace “what should I do?” Ya faɗa yana dafe kansa dake juya masa,da sauri shima yabar cikin lambun kai tsaye ɓangaren dawakai ya nufa ya samu sarkin dawakai suka fara mgna kafin a ɗauko masa wani farin doki ingarma mai girman gaske,da sauri ya kama silken dokin ya hau cikin sauri kuma ya saki linzamin dokin yay waje da gudu.. washegari ta kama Friday tun asuba ta tashi da wani irin ciwon ciki mai a zabar gaske ga wani kumburi da mararta tayi mata, ciwon kai zazzaɓi duk suka taro waje guda sukai mata yawa, da ƙyar ta lallaɓa tai sallar asuba ta koma ta kwanta a hankali bacci yay gaba da ita sbd baccin da bata samu tayi ba, cikin baccinta taji amai na tasu mata da gudu tai

bathroom ta shiga kwarara amai a cikin sink kamar zata amayar da abinda yake cikinta, Fulani dake bakin ƙofar bedroom ɗin ta tura ƙofar a hankali ta shigo, kamar zata shiga bathroom ɗin kawai saita zauna bakin bathroom ɗin ta shiga bin ɗakin da kallo, tana rawar sanyi ta fito daga cikin bathroom ɗin da sauri Fulani ta riƙeta tana faɗin “dabe careful” kwantar da ita tayi ta rufeta da duvet kafin tace “how long baki da lfy?” Bakinta yana rawa tace “jiya ne” miƙewa tai tace “Am coming” tana faɗin hakan ta fice daga cikin bedroom ɗin. Fulani na fita ta nemi mai Babban ɗaki tai mata iso a wajan sarki, babu daɗewa mai Babban ɗaki tace ta shiga, yana zaune a saman wata ladduma  mai taushi da kuma laushi, sanye da shigar ta Alfarma ga takubin Sarauta a gefensa yay kyau sosai kamarsa da Moon ta ƙara bai yana fiye da kullum, zama tayi cikin ƙasa da murya tace “Salam my king” murmushi yay mata yace “Salam Queen Maryam” kallonsa tayi tana sakin Murmushi shima kallonta yay domin kaf cikin matansa babu wanda yake so sama da Queen Maryan yace “what’s the matter?” Kanta a ƙasa tace “My king Autar ka ce babu lfy,shiyasa na nemi iso domin nazu na gaya maka” da sauri ya mike tare da ɗaukan takubinsa yace “what exactly wrong with you Queen Maryam? Shine tun safe baki faɗan ba sai yanzu, let’s go” ya faɗi hakan yana kama hannunta cike da izza da taƙama yake tafiya zuwa flat ɗin ƴar tasa,tun a hanya ya kira Dr Masarautar ya faɗa masa yana nemensa yanzu, babu jimawa Dr ya ƙarasu har cikin ɗakin Princess Moon or Queen Maimunatou, bayan ta dubata sosai ya tabbatar da abinda yake damunta drip yasa mata bacci ya ɗauke ta, Faizak dake tsaye yace “meke damunta?” Dr yace “time ɗin prioud ɗin ta ne ya fara” da mmki Yakumbo tace “kana nufin bata fara Al’ada ba sai yanzu?” Jinjina kai Dr yay yace “that’s what I mean” tace “da matsala idan haka ne” Dr yace “matsalar me? Bari kiji cikakken bayani akan Al’ada:1

Menene Jinin Al’ada? Jinin al’ada jinine da yake fita da karan kansa daga gaban macan da a al’dance zata iya daukar ciki ba tare da ya wuce kwanaki goma sha- biyarba. Wannan shi ake nufi da jinin al’ada, da akace ‘jinine da yake fita da kansa’ kenan idan ya zamana ba da kansa ya fitaba kamar ace cinnaka ya cije ta a gaba ko kunama sai jinni ya balle mata to wannan bai zama jinin al’adaba. Da akace ‘Ta gaba’ kenan idan ya fita ta dubura ko ta hanci wannan bai zama jinin al’adaba. Da akace ‘Wacce a al’adance zata iya daukar ciki’ kenan idan ya fita daga wacce a al’adance ba zata iya daukar cikiba sabo da yarinta ko girma to wannan shima bai zama jinin al’adaba. Amma da aka ce ‘Ba tare da ya wuce kwanaki goma sha-biyarba’ kenan idan ya wuce kwanaki sha-biyar to bai zama kuma jinin al’adaba. Wadannan nau’uka da akace basu zama jinin al’ada ba kenan hukuncin jinin al’ada bai hau kansu ba za su yi sallah domin jinin ciwone sai a nemi magani, Allah ya sawwake.

Mafi Karancin sa: Malamai sun karawa juna sani kan mafi karancin jinin al’ada, mafi karancinsa shine ‘dugo guda’ kenan idan ya duga sannan ya dauke, shikenan ta yi al’ada kuma ta dauke.

Mafi Yawan sa: Mafi yawan kwanakin jinin al’ada shine kwanaki goma sha-biyar kenan idan ya wuce haka to bai zama jinin al’adaba muddin ba ciki take da shiba.

STORY CONTINUES BELOW

Mata Dangane da Al’ada: anan mun sani mata suna da halaye biyar musamman idan muka yi la’akari da shekarunsu domin auna jinin da ya zo na al’adane ko bana al’ada bane, kamar haka: 1. Kasa da shekara tara: Idan jinni ya zowa yarinyar da take kasa da shekara tara to malamai sun tabbatar da wannan ba jinin al’ada bane, jinin ciwone sai a nemi magani.

2. Tara Zuwa Sama: Idan ya zamana jinin ya zo ne ga wacce ta cika shekara tara zuwa zamanta budurwa, to a irin wannan lokaci sai a tambayi kwararrun mata da likita domin a fayyace jinin na al’adane ko na ciwo. Kada mu sha’afa yanayin abinci da kuma yanayin zafi da sanyi da hutu da wahala suna tasiri.

3. Budurci Zuwa Sheka 50: Idan jinni ya zo daga lokacin da ta zama mudurwa zuwa shekaru hamsin (50) kai tsaye malamai sun tabbatar da cewa wannan jinin na al’adane.

4. Daga 50 – 69: Idan jini ya zowa mace a tsakanin wadannan shekaru wato daga shekara hamsin zuwa sittin da tara (50-69) to malamai sukace za’a tambayi kwararrun mata da likitoci domin sanin wannan jinin na ciwone ko na al’ada.

5. Daga 70: Idan jini ya zo bayan mace ta cika shekara saba’in (70) zuwa sama to malamai sukace wannan kai tsaye ba jinin al’ada bane. Ashe tantance shekarun haihuwa ba karamin abu bane domin tuni musulunci ya gina hukunce hukunce akansu, kuma ana ginine akan tsarin kalandar musulunci, wadannan bayanai na karkasuwar mata har zuwa gida biyar kamar yadda ya gabata haka malam Adawi ya kawo a cikin littafinsa ‘Hashiyatul Adawi’, Allah ya ji kansa da gafara.

Ina dada jadda cewa yanayin abin ci da da abin sha da sanyi ko yanayin zafi suna tasiri matuka, dukkan abinda ba’a fahimta ba dangane da yana yin zuwan jinni ko daukewarsa yarinyace ko babba to kamata ya yi ayi tambaya cikin gaggawa lura da yadda muka yi bayan da cewa yanada alaka da hukunce hukunce, kina yin jinkiri sai salloli su kubuce miki, kuma wannan yana nuna cewa mace da aka saka zata iya kammala idda akasa da watanni uku. Idan yarinya ta ga jinin kuma jinin ya zama shine zuwansa na farko sannan ya tabbata cewa jinin al’adane to ta sani ta balaga, dukkanin hukunce-hukuncen musulunci sun hau kanta, idan ta yi salatin Annabi za’a rubuta bata lada idan kuma ta bari samari suna jagwalgwalata ita za’a rubutawa zunubi, ba wanda yace wai sai ta yi aure sannan za’a fara yi mata rubutu, kenan har azumi sai ta ranka wanda ta sha.

Tabbatuwar Jinin Al’ada: Shifa abinda ya shafi jinin al’ada al’amari da Allah madaukain sarki ya yi bayaninsa a cikin Alkur’ani mai girma, Allah yana cewa: Kuma suna tambayarka dangane da al’ada, Kace: Shidinnan cutane, ku ninci (saduwa da) mata a lokacin al’ada, kada ku kusance su har sai sun yi tsarki (Jinin ya dauke) idan suka tsarkaka (suka yi wanka) to ku je musu ta inda Allah ya umarceku, Lalle Allah yana son masu yawan tuba kuma yana son masu tsarkaka. Bakara, ayata: 222. Haka kuma ma’aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yace; (Wannan) Wani abune da Allah ya dorawa mata ‘ya’yan Adam. Ashe ba shaci-fadin da ake cewa bane ai sanadiyyar da yasa mata suke al’ada shine wannan ganyan bishiyar da Nana Hawwa’u ta ci a gidan aljanna, amma Annabi Adam mala’ikane ya rike masa makoshi (makogaro) sai ya amayar da abin shi yasa maza basa yi. Wannan labarin bashi da kanshin gaskiya domin ayoyin Alkur’ani sun tabbatar da Annabi Adam ya ci itaciyar. Shifa jinin al’ada kada amanta jinine da yake fitowa daga can cikin mahaifa a lokuta sanannu, Allah madaukakin Sarki ya haliccishi domin ya zama abin ci ga yaro a lokacin da yake cikin mahaifiyarsa domin inda zai yi tarayya da mahaifiiyar ta shi a abincin da take ci to da karfinta ya ragu sosai, sa Allah ya sanya shi ya zama abinci ga reshi, shi yasa dakyar kaga mace tanada juna biyu (ciki) kuma tana al’ada. Idan kuma ta haihu sai Allah ya zamar da shi nono jaririn yana sha amatsayin abin ci, shi yasa kadan ake samun matan da suke shayarwa kuma suna al’ada. Idan ya zamana mace bata da juna biyu (ciki) kuma bata shayarwa sai ya kasance ba inda zaii je to shine sai ya taru a mahaifarta, shine mafi yawancin lokuta yake fita a kowanne wata cikin kwanuka shida ko bakwai, ya kan karu ko ya ragu akan hakan kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah- gwargadon yadda Allah ya tsara halittarsa.

STORY CONTINUES BELOW

wannan yadda jinin al’ada yake kwarara kenan daga jikin wata baturiya

Karkasuwar Mata: Mawallafin littafin Akhadari ya kasa mata zuwa kashi uku dangane da jinin al’ada, kashi na farko; itace wacce ta fara, kashi na biyu kuma; wacce ta saba, sannan sai kashi na uku; mai juna-biyu (wato mai ciki), ga bayanansu kamar haka:

ɗigon Jinin al’ada

1. Wacce Ta Fara: Ita wacce ta fara al’ada ya zama yinta na yanzu shi ne ganin al’adarta na farko a rayuwarta, to abinda dake kanta zata zuba idone ta ga kwanaki nawa zauka kafin ya yanke, ta yadda ba zai wuce kwanaki sha-biyarba, idan ko ya wuce sha-biyar to abinda ya doru akan kwanaki sha-biyar bai zama al’adaba, kenan mafi yawan kwanakin da zata saurara sune kwanaki sha-biyar, amma zai iya daukewa kafin hakan, abin nufi in ya wuce to ya zama (Isthala) cuta sai a nemi magani, anan nake cewa iyaye su kara sa ido akan ‘ya’yayansu mata su dungu tuntubarsu suna fahimtar da su tun kafin lokacin ya yi domin kada lokaci ya yi yarinya ta ga jini ta fashe da kuka, ko makamantan haka, wata babbar macece amma bata san menene jinin al’adaba ita dai kawai tace tana ganin jini a wani lokaci bayan wasu kwanaki kuma sai ta daina ganinshi.

2. Wacce Ta Saba: Abinda ake nufi da wacce ta saba itace wacce ta gabatar da al’ada sau uku a adadin kwanaki guda, misali wacce ta yi al’adar farko a kwanaki biyar, da ta sake yi sai ya yi mata kwanaki biyar da ta yi na uku shima kwanaki biyar, to wannan sai muce sunanta wacce ta saba domin ta saba akan kwanaki sanannu. Amma idan ta yi al’adar karo na farko kwanaki uku karo na biyu kuma kwanaki biyar karo na uku kwanaki shida to ba za’a kira wannan wacce ta saba ba, domin ba ta da tsayayyun kwanaki.[5] Ita wacce ta saba wato wacce take da sanannun kwanakin al’ada to wadannan kwanakin sune kwanakin al’adarta, idan kwanakin suka cika al’adar kuma ta dauke sai ta yi wanka ta ci gaba da gudanar da ibada, amma idan kwanakin suka cika al’adar kuma bata daukeba sai ta kara kwanaki uku, haka zata dinga kara kwanaki uku har kwanaki shabiyar su cika, misali idan al’adarta kwanaki biyarne sai kuma jinin bai daukeba a kwanaki biyar din sai ta kara kwanaki uku na sauraron daukewar sun zama takwas kenan, idan ya dauke shikenan sai wanka, idan kuma bai dauke ba sai ta kara uku akan wadancan takwasdin sun zama sha-daya idan bai daukeba sai ta kara uku sun zama sha hudu idan bai daukeba sai ta kara kwana daaya, ya zama goma sha-biyar kenan, sai ta yi wankan kammala al’ada ko ya dauke ko bai daukeba domin kwanakin al’ada makurarsu shine kwana goma sha-biyar kuma sun cika, abinda ya ci gaba da zuwa ba sunan shi jinin al’ada ba sunanshi jinin cuta (Istihadha) sai a nemi magani.

Adukkan wadancan kare-karen kwanaki da aka yi inda ace bayan ta kara kwana uku na saurare sai ya dauke a kwana na daya cinkin hukun shikenen sai ta yi wankan tsarki. Mu sani kamar yadda bayani ya gabata shi jinin al’ada bai wuce kwanaki goma sha- biyar ga wacce ta fara da wacce ta saba.

3. Mai Juna-biyu (Mai ciki): Galibin mata masu juna biyu basa al’ada, sabo da haka da zarar mace tana da juna biyu (ciki) sai kuma ta ga al’ada to kada ta yi sakaci wurin tuntubar likita . Idan al’ada ta zowa mace mai junabiyu to idan cikin ya kai watanni uku zuwa biyar zata iya yin al’ada ta kwanaki sha-biyar zuwa ashirin, idan kuma cikin ya kai watanni shida to al’adar zata iya daukar kwanaki ashirin zuwa ashirin da biyar, kada a sha’afa wurin tuntubar likita idan ana da juna biyu kuma aka ga jini. Tanbihi Na Daya: Idan mace jini yana mata wasa wato ya zo yau gobe sai kuma ya dauke bayan kwanaki uku sai kuma ya dawo to abinda zata yi anan shine, ta tsaya ta yi karatun ta natsu, sai ta lissafa kwanakin da jinin ya zo sune kwanakin al’ada sai kuma ta ware kwanakin da jinin bai zoba sune kwanakin tsarki domin da hakane zata cika kwanakinta na al’ada, misali kwanaki tara; sai ya zo a rana ta farko da ta biyu sai bai zoba a rana ta uku da ta hudu sai ya zo rana ta biyar amma bai zo ba a ta shida da ta bakwai sai ya zo a ta takwas da ta tara. To anan sai muce ta yi al’adar kwana biyar a cikin kwanaki goma, wannan matar ita ake kira (Al-Mulaffiqa) alarabcin mata masu al’ada. Idan ya zama an sami tazarar kwanaki takwas ko sha-biyar tsakanin daukewarsa da dawowarsa to na biyun zai zama sabon jinine kenan, ba na dane ya dawaoba. Alamar Daukewar Jinin Al’ada: idan jinin al’ada ya dauke akwai alama da shara’a ta sanya domin ya zama shine manuniya akan cewar al’adarki ta dauke, wadannan alamu sun kasu gida biyu kuma kowacce tana cin gashin kantane, sune kamar haka:

STORY CONTINUES BELOW

1. Bushewar Gaba: Abinda ake nufi anan shine mace ta shigar da kyalle ko auduga cikin gabanta ta fito da shi busasshe ba wani jini a tare da shi, to da zarar ta ga haka to ta tabbata al’adarta ta dauke.

2. Farar Kumfa: wannan wani ruwane fari mai laushi da yake zuwa karshan al’ada, idan mace ta ga irin haka a karshan al’adarta to ta sani ta kammala. Wadannan alamomi su suke nuna daukewar al’adar mace, idan mace bata taba ganin al’adaba sai a wannan karon sai ta fara ganin bushewar gaba to kai-tsaye ta samu tsarki ba sai ta jira farar kumfaba, amma idan wacce ta saba ganice sai ta ga bushewar gaba to malamai sukace zata zata dan saurara kadan domin jirar faran kumfa, amma jinkirin ba zai kai ga fitar zababban lokacin sallah ba. A dunkule dai kowanne daya daga cikin wadannan abubuwa guda biyu yana nuna samuwar tsarki ba lalle sai sun hadu alokaci gudaba, da zarar alamar ganin tsarki ta tabbata sai ta yi wankan tsarki domin ta ci gaba da ibada, domin idan bata yi wankaba ko da jinin ya dauke mijinta ba zai sadu da itaba ba kuma zata yi sallaba, da dai sauransu. Idan mace ta ga ruwa fatsi-fatsi ko diddiga-diddiga bayan daukewar jinin al’ada to kada ta damu ta ci gaba da harkokinta na ibada, dama matsalar idan ta ganshi a farkon jinine, amma idan a karshen jinine to wannan ba komai, Ummu Atiyyah medakin ma’aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) tace: ((Mun kasance bama lissafa (Ruwa) fatsi- fatsi da diddiga-diddiga bayan tsarki da cewa wani abune)). Abu Daud Hadisi Na: 307, Nasa’i, Hadisi Na: 368, Ibnu Majah Hadisi Na: 647, Darimi Hadisi Na: 865. Mace ta dinga duba samun tsarkinta a lokacin da zata kwanta bacci da kuma lokacin sallar asuba, amma ba’ace ta tashi cikin dareba domin ta duba.

Idan mai al’ada ko mai biki (jinin haihuwa) ta ga tsarki kafin rana ta fadi to sallar azahar da la’asar sun hau kanta, hakanan kuma idan ta ga tsarki kafin hudowar alfiji to tabbas za ta yi sallar magariba da lisha. Abubuwan Da Basu Halatta Ga Mai- al’adaba: Anan za’a lissafa abubuwan da basu halatta mai al’ada ta yi su ba ko ayi mata ba, wadannan abubuwane guda goma:

1. Sallah: Bai halatta mai al’ada ta yi sallaba farilla ko nafila, idan kuma tayi ta yi ba’akarba ba sannan kuma ta yi laifi, sannan bayan ta kammala al’adar ba zata rama sallolinba.

2. Saki: Baya halatta matar da take al’ada a saketa, wannan ya sabawa karantarwar musulunci, saboda haka koda yana son ya saketa to ya bari sai ta kammala al’ada kafin ya sadu da ita sai ya saketa, kuma dai idan ya saketa tana jinin al’adar to sakin ya yi amma za’a tilasta shi ya mayar da ita idan sakin bai kai ukuba.

3. Dawafi: Bai halatta mai al’ada ta yi dawafin Ka’abah, amma zata yi sauran dukkan abinda maniyyaci yake yi, kamar tsaiwar Arafah da kwanan mina dana muzdalifa da jifa da Labbaika, da daidai sauransu.

4. Zama A Masallaci: mai al’adah ba zata zauna a cikin masallaciba, domin sauraron karatu ko karantarwa ko taro da dai sauransu.

5. Azumi: Bai halatta mai al’ada ta yi azumi na farilla ko na nafila, idan ta yi kuma bai yiba, saboda haka zata lissafa azumin da ta sha bayan watan ya wuce sai ta ramasu. Ba’a ajiye azumi domin tsammanin gobe al’ada zata zo, amma dazaran ta zo to dazaran ba azumi, dazaran bata zoba to dazaran akwai azumi, ko da kin ji tafiyar jinin ajiki amma bai fitoba to biki fara al’adaba, sai ya fitane za’a fara lissafi.

6. Daukaa Alkur’ani: mai al’ada bata dauka Alqur’ani kasantuwarsa littafi mai tsarki sannan kuma ita bata da tsarki, amma wannan baya hana idan ta ganshi zai fadi ta daukeshi ta gyara masa wuri.

7. Karatun Alkur’ani: mai al’ada bata karanta Alkur’ani, dudda cewa wadansu malamai suna ganin ya halatta ta karantashi da ka domin kada ta manta sabanin dauka.

8. Saduwa: Bai halattaba saduwa da mace tana al’ada, idan ta ki yadda da mijinta ya sadu da ita domin tana al’ada ba za’ace ta sabawa Allah ba asalima ta yi biyayyane ga reshi, bai halatta a sadu da mace tana al’adaba har sai al’adar ta dauke kuma ta yi wankan tsarki, kenan koda al’adar ta dauke amma batayi wankaba to bai halatta a sadu da itaba. Ya halatta miji ya taba duk inda yake so a jikin matarsa alokacin da take al’ada bayan ta yi kunzugu inbanda daga cikbiyarta zugwiwarta wannan kan bai halattaba har sai jinin ya dauke kuma tayi wanka, hakanan itama ya halatta ta taba ko ina a jikinsa duk da tana al’ada.

9. Tabbatar Da Rashin Tsarki: Al’ada tana tabbatar da wacce take da ita bata da tsarki.

10. Wajabta Wanka: Al’ada tana wajabta wanka, wato dukkan matar da ta yi al’ada kuma al’adar ta dauke to wankan tsarki ya wajaba akanta. Daga wadannan bayanan da suka gabata ya bayyana a fili cewa lalle jinin al’ada bakaramin hukunce-hukunce yake da shi ba, kuma lalle idan aka kyalleshi yadda ake sakaci tsakanin maza da mata akan abinda ya shafi wannan al’amari to lalle abin yanada ban tsoro.

Allah ya datar damu yasa mu dace. Allah shine mafi sanin.

Gaba ɗaya suka jinjina kai alamar gamsuwar da bayanin da Dr yay masu,gdy sukai masa daga nan ya haɗa kayansa yabar cikin gidan. Babban club ne baka jin komai sai ƙarar D.j dake tashi, wasu na karta wasu na shan shisha wasu kuma na rawa haka dai,zaune yake saman wata kujera da kulbar win a hanunsa, yana sanye da wando 3gauther da wata ƙaramar riga sai ƙatuwar sarƙa a wuyansa,ya sanya wani baƙin glass a saman idanunsa, wani dake gefensa yace “Og yanzu mene abinyi tayaya ka tabbatar Deen yana raye?” Dry Farouk yay yace “kana wasa dani, Deen yana raye bari kaji abinda baka sani ba, akwai wata yarinya mai suna Salmerh ɗaya daga cikin yaran dasu Oga Taju sukai safarar, tana son Deen sosai kasan akwai yarona a cikinsu wato Ovasi, shike gayan komai, to a lokacin da bom ɗin ya kusa tashi ita Salmerh ta fita daga cikin ɗakin da aka ɓoyesu da gudu ta fita ta shiga cikin tana shiga ta samu Deen ya lumshe idanunsa banda kalmar shahada babu abinda yake, tana zuwa ta fara ƙoƙarin ɗauke dutsen cikin Sa’a kuma ta zare dutse miƙewa Deen ganin saura 50seconds bom ɗin ya tashi yace “let’s go Salmerh” Murmushi tai masa bata nuna masa ƙarfen ɗaya riƙe mata riga ba tace “i love You so much ban san yaya zan gaya maka son da nake maka ba, kullum ina ƙoƙarin danne abinda ke zuciyata a game dakai,hakan yasa yau na yanke nuna maka tsantsar soyayyar da nake maka,babu lokacin ya kamata kamar wajan nan” kafin yay magana tasa hannu ta hankaɗa sa ta cikin window’n dake kusa dasu a dai-dai lokacin kuma bom ɗin ya tashi da Salmerh dukkan wani part na jikinta sukai pecies….Jan gemunsa Farouk yay yana sakin Murmushi wanda kana ganinsa kasan na mugunta ta ne kana yace “Lokacin hutawarsa ne yanzu, kaje ka huta King Aliyou Eneye Ahuoyza Deen”Wanda ke kusa dashi yace “Oga yanzu yana ina? Babu da sauran time kafin ace ya dawo gareta yana da kyau musameta ko?” Baya Farouk yay idanunsa akan wata budurwa dake rausayawa yace “A.j kasan dole zan san inda Aliyou yake,banyi niyyar kashe fa shiyasa har na bari aka taimakesa,a lokacin da bom ɗin ya tashi ni masa Ovasi ya ɗauke sa sbd duguwar sumar da yay,abinda basu sani ba duk wannan faɗan da ake nima ina cikin ƙasar, bayan Ovasi ya ɗauke sa ne ya kaisa can bakin ruwa inda manyan masu kuɗi suke hutawa,amma inda ba za’a a ganshi ba, bayan ya kaisa ya dawo yake faɗa min ya kaisa to a nan Ovasi ya kamamu nida budurwa sa ganin babu yadda zanyi kawai ɗauke masa numfashi da bindigar dake jikin, to kafin na ƙarasa wajan Deen wasu Mutane sun ɗauke sa a mota,nabi diddigi kuma na gane inda suke” murmushi A.j yay yace “gsky Oga kana da brain ba duk kai ba serious” murmushi Farouk yay yana jin daɗin ƙudirinsa na shekara da shekaru na gaf da cikawa, gyara zama yay yace “bari na baka labarin waye Farouk Bashir Yahya gidan iko..+

#flash back.

Sunana Farouk Bashir Yahya gidan iko, nine frist Born wajan iyaye na sai ƙanwata Yasmin,daga nan iyayenmu basu ƙara samun wani ɗa/ƴar ba,ina da Shekara goma a duniya a primary school muna zaune bayan an fita breakfast, wani abokina mai suna Khamis ya bani sweet, girgiza masa kai nayi nace “No thank you!” Ɓata fuska Khamis yay yace “why” nace “haka nan” kamar zai kuka yace “please kasha ko sau ɗaya ne” ganin yadda ya sauya fuska yasa na amsa na sha,tofa wannan wannan sweet ita ce silar jefani halin da nake ciki a yanzu,ashe mahaifin yaron ɗan mafiya ne shike bashi alawa yana rabawa friends ɗinsa,kwana nayi kai na nayi mani ciwo cikin dare zanji shawo na yawo saman bedroom ɗina yana kiran sunana, na shiga tashin hankali sosai sbd ban saba dajin hakan ba, kwanci tashi naje makaranta Lokacin ina ss3 bayan an tashi wata mota tai parking gaba na, banyi wani musu ba na shiga motar daga nan kuma ban ƙara fahimtar komai ba sai farkawa nayi na ganni a cikin wani babban ɗaki tare da tarin maza da mata sanye da jajayen kayan  ga wasu manyan ƙoƙona a hanunsa ɗauke da jini.

Wani babbansu wanda yake saman kujera yay dry tare da faɗin “wlcm Farouk Bashir Yahya gidan iko” nidai tsaye nai ina kallonsu kafin na kalli aboki na Khamis da sauri ya janye idanunsa,a nan dai suka faɗa min abinda suke so kasa yi masu nai a take a wajan kuma nace na bada cikin dake jikin mahaifiyata.

Tun daga nan komai ya lalace kusan rabin familyn mu na bada jikinsu mugwayen kuɗi nake samu bana wasa ba, kuma kai na ya ƙare wayewa,bayan kamar shekara huɗu haka aka ƙara kiranmu meeting, nan dodo ya bada izinin a samo masa wata yarinya kuma babu wanda aka bawa aikin sai ni, photon yarinyar aka ban tare sunanta a jikin photon aka rubuta MOON da jan jini, aikin da hatsari da kuma sharaɗi dole ni zan kawota idan har ban kawota ba za’a fanshi jinina bisa nata da aka rasa, idan na sameta san zama shugaba gaba ɗaya a nan jahar Kano, a lokacin kusan 100.m aka bani..,” murmushi Farouk yay yace “Tayaya kake ganin zanbar wannan dabar da barni,abun mmkin yadda mahaifina bai taɓa tambaya ta komai ba,hakan yasa wata rana da aka kira meeting na gayawa dodo damuwata,dry yay sosai tare da yin wani ihu,cikin ƙaramin lokaci ya buga wani abu sai ga vedio’n Abbana ya bai yana a tsakiyar wasu mata suna ta shafasa,mmki ya cika ni,ban bar wajan ba sai da aka gayamin dukkan abinda Abbana yake,sai naji farin ciki shima yana aikata hakan bare ni,san da su Moon suka tare a gidan dake farcing namu farin ciki ya kamani sai ban nuna sosai ba sbd nasan mahaifina nada buri a kanta, infact bai san nasan na ganta ba,haka akai lokacin da Deen yazo kallo guda nai masa nadan cewa ba asalin aikinsa kenan ba,akwai manufar data kawosa gidanmu,yin duniya Abbana yaƙi korar Deen, Aliyou Eneye Ahuoyza yana da kaifin basira fiye da tunanin mai tunani, duk yadda kakai da gane mutum da wahala ka fahimci inda Deen ya dusa gane asalinsa da abinda yake shirin yi shine Abu mai wahalar gaske tabbas, wannan dalilin yasa na ƙara sanya idanuwa na a kansa, nasan soon or later I know everything about him tabbas,dalinsa na ƙarar da dukkan familyn namu domin duk sanda aka buƙaci Moon nace a ƙara min lokaci to dole sai na bada jinin wani matsayin toshiyar baki”.

Jinjina kai A.j yay yace “tabbas abun babba ne basan san lamarin ya kai haka ba wlh”  ka faɗa Farouk ya ɗaga irin whatever ɗin nan… Yakumbo ce ta kalli Sarki Aliyu Al’amin tace “nikam gani nake yarinyar nan kamar bata son haɗin da kakeso kayi na shekara da shekaru” gyara zama Sarki Aliyu Al’amin yay tare da sakin lallausan murmushi kana yaja numfashi yace “Na lura da wannan amma yaya kikeso naiwa Faizak kina sane da irin son da yake mata ai?” Yakumbo tace “Allah ya ƙarawa Sarki lfy, amma ya kamata aji ta bakinta domin ba za’ai mata auren dole ba, ko Fulani?” Girgiza kai Fulani tayi tace “A’a Yakumbo duk abinda kuke dai-dai ne” Murmushin jin daɗi Sarki Aliyu Al’amin yay domin ya yarda da karamcin matar tasa, miƙewa Fulani tayi tace “Na barku lfy” daga nan ta bar turakar Sarki,ganin babu kowa yasa ta nufi ɗakin Moon zaune ta sameta a gefen gado tana taje sumar kanta, Murmushi tai mata tace “wanka kikai?” Kanta a ƙasa tace “Eh” shiru Fulani tayi can kuma tace “kin gama prioud ne?” Kasa bata amsa tayi hakan yasa fulani yin Murmushi tace “look! Am your mother babu buƙatar ki ɓoye min wani abu, idan ban san abinda ke ranki ko yake damunki ba wane ya dace ya sani? So sharing your feelings with me kin gane, kin gama al’ada? Ma’ana farin ruwa ya biyo bayan jinin?” Kai Moon ta ɗaga kamar zatai kuka duk ta marai-raice fuska tace “eh” “ok kwana nawa kikai? Kin iya wankan ai?” Kwaɓe fuska tayi tace “Ammi” haɗe fuska Fulani tayi tace “bana son shashanci Maimunatou” da sauri Moon ta runtsa idanunta sbd sunan Maimunatou da Fulani ta ambata, duk sanda akace Maimunatou sai ta tuna gwarzon jaruminta wanda ya salwarta da rayuwarsa a kan tata, hawaye ne suka fara taruwa a cikin idanunta, lokaci ɗaya taji zuciyarta ta fara zafi da raɗaɗi haɗi da ƙona, shiru Fulani tayi domin tasan abinda yake damun yarinyar ta ta, numfashi ta sauke tana gyara zaman Alƙyabbar ta tace “Yayinda kike jini ki kiga kumfa wata farin Ruwa ya fito Wannan alama ce take nuna jinin ya tafi saura wankan tsarki, idan kin iya wankan to idan ba kiyi ba yanzu dai zan maki bayani;

STORY CONTINUES BELOW

YADDA AKE YIN WANKAN HAILA DANA JANABAH

Idan Mutum ya shiga Ban-‘daki (bathroom) Zai fara ne da wankewa Najasar dake tare dashi.

Ma’ana, Zai Fara wankewa Al’aurarsa. Da kuma duk Guraren da Maniyyi (ko jinin) ya taba ajikinsa.

(Misali tun daga Cibiyarsa har zuwa cinyoyinsa).

* Kuma Zai Qulla niyyah ne yayin da yake wankewa Al’aurarsa.

* Sannan Sai ya wanke Dukkanin Gabobinsa na Alwala. Amma sau dai-dai.

* Idan kaga dama zaka bar Qafafunka, Sai akarshen wankan.

* Sannan Sai Wanke Kayinka Sau Uku. (tare da Wuyanka da Fuskarka gabadayanta).

* Sai ka Wanke Tsagin Jikinka na Dama. Har Zuwa Kafarka ta dama.

* Sai kuma Tsaginka na Haggu, ka hada har Qafarkata haggu din.

* Ya zama ka chire zobe daga hannayenka (Idan ya matseka) kuma dole ka Tsetsefe Dukkan yatsunka na hannu da na Qafa.

* Ka chuda Kafarka sosai. Musamman ma in har kanada kaushi.

* idan kazo wankewa kowanne tsagi, ka tabbatarda cewa kana Chutchuda Bayanka sosai.

* Idan kuma hannunka baya iya kaiwa, sai ka samo wani Tsumma ko Kyalle mai tsafta, Ka Jiqa-shi, Sannan ka Chutchuda dashi.

* dole ne ka chutchuda Ko ina ajikinka. Musamman ma idan kana da Qiba.

* Dole ne Ka wanke Duburarka sosai tun farko. Kada kayi la’akari da cewar”Ai ba ba-haya kayi ba”.

A’a. Ai nan dinma jikinka ne. Idan baka wanke ta ba, to wankanka bai yiwu ba.

* Ka kula da Ramin cibiyarka. Ka tabbatar cewaRuwa ya shiga har nan.

* Ya zama dole ‘yan uwa mata su tabbatar cewa Ruwan ya ratsa har cikin Kitsonsu yayin wankan.

* idan kuma kana da gemu, to lallai ne ka tabbatar cewa ka Tsetsefe shi komai Kaurinsa da duhunsa.

~~ ~~ ~~ ~~ ~~ ~~ ~

NOTE: Zaka iya amfani da wannan alwalar wacce kayiyayin wankanka. In dai har baka sake ta’ba al’aurarka ba bayan kayi alwalar.

HAKA AKE YIN WANKAN JANABA, HAILA, NIFASI, DA KUMA WANKAN SHIGA MUSULUNCI.

“Daga nan saiki fara sallah azumi riƙe Kur’ani, tana faɗin hakan ta miƙe har taje ƙofa ta tsaya tace “Abbanki yace ki shirya za’a fita ran gadi dake”. Tana faɗin hakan ta fice zuciyarta cike da tausayin ƴar ta…. Tsaye yake da shadda ruwan madara yay kyau ba kaɗan ba, ya ɗura jar dara a saman kwantacciyar sumar sa wacce ya ɗaure ta da ribbon, hanunsa sanye da agogo Patek philippe, lumshe idanunsa yay tare da jin gina da jikin dressing mirror a hankali kuma ya sanya hannunsa a saman forehead ɗinsa yana ƙoƙarin tuna wani abu mai matuƙar muhimmanci a rayuwarsa amma ya kasa, jin kansa na sarawa sosai yasa ya fesar da numfashi a hankali kuma ya juya a tsaye ya ganta tana sakar masa Murmushi, Kallonta kawai yake yana ganin kamar akwai abinda bai gama cika a jikinta ba,farin glass ɗin daya gani yasa ya ɗauka tare da maƙala mata a fuska, sakin murmushi yay wanda ya haddasa bai yanar dimples ɗinsa, can ƙasa yace “kinfi kyau a haka Maimunatou” dry tayi tace “No ban so” juya fararan idanunsa yay yace “basshi sbd ni,kuma ai kin saba sawa ko?” Kallonsa tayi tace “eh yanzu ne kawai naji bana so,but zan barshi sbd kai” Jinjina kai yayi hannu ta miƙa zata riƙe nasa yay saurin yin gaba yana sakin Murmushi mai sauti…. Shirye shiryen tafiyar Moon Paris ya kan kama, domin ya gama shiri tsaf yau jirginta zai tashi da Misalin biyar na yamma..biyar dai-dai kuma suka isa airport Sarki Aliyu Al’amin Yakumbo, Mai babban ɗaki, sai Faizak idanunta cike da hawaye ta maƙale jikin Sarki Aliyu Al’amin sai shasshekar kuka take,kanta ya shafa yace “Afuwa Mamana Soon Zaki dawo ai” kuka ta sanya masa da ƙyar ya lallashe ta, Faizak kam baka gane halin da yake ciki domin harga Allah baya ƙaunar tafiyar Moon, kallonsa tayi yay saurin ɗauke kai, itama batai yunƙurin zuwa wajansa ba, a haka ta shiga cikin jirgi ya tashi da ita zuwa Paris.

Paris

Paris, France’s capital, is a major European city and a global center for art, fashion, gastronomy and culture. Its 19th-century cityscape is crisscrossed by wide boulevards and the River Seine. Beyond such landmarks as the Eiffel Tower and the 12th-century, Gothic Notre-Dame cathedral, the city is known for its cafe culture and designer boutiques along the Rue du Faubourg Saint-Honoré.

Ƙasa ce ta ƴan gayon gaske masu ji da kuɗi ilimi,sun haɗa komai da komai, alrdy an gama mata dukkan wani cike cike, hatta hostel an kama mata..washe gari da safe misalin 10:30 ta fito sanye da wata shiga ta alfarma green ɗin lace ne a jikinta na ubansu kana ganinsa kasan an kashe kuɗi wajan siyansa, yana da milk ɗin torch ta sanya veil milk sai flat shoe milk hannunta riƙe da wayar da faizak ya siya mata, kai tsaye cikin makarantar ta nufa Université de Cergy-Pontoise,tana zuwa ta nufi office ɗin exam officer,a nutse take tafiya tai kyau kamar ka ɗauke ta, a sanyaye ta tura ƙofar ta shiga, wata budurwa ta gani wacce zasu iya zama age mate, Murya a sanyaye ta gaida Exam officer ɗin,shiru tayi kafin tace “Sir yau zan fara ɗaukan lectures” jinjina kai yay yace “wanne cous kenan?” Shiru tayi tace “Low” abubuwa ya fara dubawa yace “your name please” kaita ɗaga tace “Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen” da sauri budurwa dake kusa da ita ta ɗaga kai sai kuma tace “wlcm takwara am Maimunatu Khalid” Murmushi kawai Moon tai mata, exam officer ɗin ne yace “Top 10 Best Pre-law Majors (see also: what did most law school students major in?)

Political Science – 9,612 admitted. …

Other – 2,917 admitted. …

Psychology – 2,960 admitted. …

Criminal Justice – 2,220 admitted. …

English – 2,564 admitted. …

History – 2,657 admitted. …

Economics – 2,373 admitted. …

Philosophy – 1,858 admitted.” Moon na  gyara saman glass ɗin idanunta tace “okey! Sir” daga nan ta miƙe bayan ya gama yi mata bayani, tare suka fito da Takwararta Maimunatu Khalid, tana mata hira ƙasa², tunda suka fito Moon taji gabanta na faɗuwa sai rutsa idanunta take, suna gaf da shiga hall ɗin da zasu ɗauki lecture a ciki taga Maimunatu Khalid ta tsaya, itama tsaya tayi kafin ta lumshe idanunta sbd ƙamshin daya daki hancinta,can dai ta buɗe ido slowly idanunta ya sauka a kansa wata gigitacciyyar ƙara ta saka tare faɗuwa a wajan….

_RANAR KUKE JIRA YAU GASHI TAZO💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽INA MASOYA LITTAFIN MOON INA MASOYA NIMCYLUV YAU RANAR KU CE TA NUNA MIN ƘAUNA, DUKKAN WANI MASOYA MOON YANA DA KYAU YAY PAYMENT SABON LITTAFI NA *SIRRIN MU* NASAN DA YAWA KUN FARA KARANTAWA KUNJI YANAYINSA TO BA KUJI KOMAI BA DOMIN KO RABIN LABARIN BAMU SHIGA BA,SOYAYYA YAUDARA CIN AMANA ZANMA CIKIN AMINCI DUK ZAKU SAMU A LITTAFIN_

Ware idanunsa Mutumin dake tsaye gefen Maimunatu Khalid yay, a hankali ya ɗan lumshe idanunsa ya shiga fesar da iska, kamar a mafarki ya fara jin kansa na juya masa ga wata sarawa da kan ya fara yi masa, ja baya yay sosai yana dafe da kansa gently ya jikin motar tare da jin gina bayansa da jikin motar shiru yay sbd abubuwan da suka fara yi masa yawo a cikin kansa zuwa cikin idanunsa, a hankali kuma ya kifa kansa a jikin motar, Maimunatu da sauri ta fara neman ruwan da zata yayyafawa Moon,ita kanta a firgice take tama rasa mene ya sameta, tunawa da tayi akwai gorar a cikin mota yasa ta nufi motar da sauri, ba’a ɗauki lokaci ba ta dawo hannunta riƙe da gorar ruwa kai tsaye ta ɓalle murfin tare da sheƙawa Moon wata duguwar ajjiyar zuciya ta sauke, cikin motar ya shiga bai tsaya jiran ta ba sbd yadda ya kejin wani iri a cikin brain ɗinsa, da gudu yaja motar ya fice daga cikin makarantar baki ɗaya.
A gigice Moon ta buɗe idanunta dukkan jikinta rawa yake ta shiga dube dube,cikin zafin nama kuma ta miƙe tsaye idanunta har wani juyawa yake sbd medical ɗin ta daya zame daga saman idanunta, ciki ƙarfin hali da murya a sanyaye tace “Where is he? Where is my Dad? Ina Dad ɗina please ki numanin shi” ta ƙare maganar tana riƙe hannun Maimunatu Khalid, mmki ne ya kashe M.k tace “Waye Dad ɗin naki?” Abinka da mai aljanu da kuma rashin lafiyar idanu ta wani kaɗawa M.k idanunta tare da riƙe wuyanta tace “Dad ɗin nawa ne baki sani ba? Bayan yanzu na ganshi dan Allah dan Annabi ki nuna min inda yake shine Rayuwata” abubuwa suka haɗewa m.k ga shaƙar da Moon tai mata ga kuma wata banzar tambaya da Moon ke jifanta dashi, kasa mata amsa tayi sbd riƙon da Moon tai mata bana wasa bane,cikin ƙaramin lokaci Moon ta fita daga cikin hankalinta da alama mutananta ke son kawo mata ziyara a lokacin, few minutes mutane suka ɗan taro a wajan aka shiga kwatar Moon wani ne yace “to ke waye a tsaye tare daku harta ke tambayarsa?” M.k tace “he’s my husband to be, he’s name is Imam not Aliyou” da ƙarfi Moon tace “wlh ƙarya ne Dad ɗina na gani my King Aliyou Eneye Ahuoyza Deen” sai kuma ta zube a wajan a karo na biyu..Bayan an tashi daga last lecture nasu kai tsaye hostel ɗin data sauka ta nufa, da ƙyar take tafiya idanunta har wani duhu² take gani a cikin su, komai na duniyar ji take yay mata zafi to ko dai ba Dad ɗinta ta gani ba? Ko mafarkin data saba yi da shine yasa ta kejin kmar shi ta gani? Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un kawai take ambata harta samu  ta shige cikin bedroom ɗin ta,kai tsaye saman bed ta faɗa tare da jan pillow ta rungome a ƙirjinta a hankali ta saki kuka mai cin rai ita kaɗai ta san zafin da zuciyarta keyi mata, bata jin daɗin duniyar gaba ɗaya ji tayi makarantar ma ta fice mata a rai…Imam kam da ƙyar yake sauke ajjiyar zuciya juyi kawai yake saman bed daya rufe idanunsa sai ya fara ganin wata ƙaramar yarinyar a maƙale a jikinsa tana tsotar yatsarsa, wani lokacin kuma sai yaji kamar ana masa ihu a kunne haka yay ta juyi ya rasa abinda yake masa daɗi… Washegari kamar yadda ta saba bayan ta shirya tsaf cikin riga da zani na Holand ɗin atamfa mai ruwan huda ta ɗauki hijab ta sanya, da ƙyar ta samu tai breakfast kafin ta ɗauki komai nata ta nufi cikin makaranta,tana zuwa m.k na sauka daga cikin motar gabanta taji ya faɗi tuna abinda ya faru jiya yasa tai saurin ɗauke kai domin bata son ƙarayi masa wani kallon da za’a samu matsala, bayan ta gama frist lecture ɗinta ta fito ita ɗaya domin m.k nada abinda zatai can ta samu wani private waje a ƙasan bishiyoyi mai ƙyau ta zauna, wayar hannunta ta fara operating kafin tai darling number Jakadiya, babu jimawa akai answering call ɗin, cikin sanyin murya tace “i want to speak to Abbi” Jakadiyar tace “girman kine princess Allah ya ƙara maki lfy ƴar sarki jikar sarki matar sarki kuma in sha Allah!” Moon ji tayi ranta ya ɗan ɓaci domin bata son wannan abun calmly tayi tace “Ohh! Ya Allah!” Da sauri Jakadiyar tace “afuwa tuba nake,ban ƙarawa” daga ta kashe wayar, not long time wayarta ya fara ƙara a sanyaye tai picking idanunta kuma a lumshe tace “Abbi..” gyara zama Sarki Aliyu Al’amin yay yana sauke numfashi cikin izza da kuma izzar data gama ratsa jikinsa yace “Mamana,yaya karatun?” Tace “Allahamdulillah! Abbi nai missed naka” juya ido yay yana fesar da yace “i also missed my Princess” murmushi tayi iya saman leɓe tace “Dad when za kazo” baya yay tare dasa hannu ya kama hannun Fulani ya shiga murzawa ido suka haɗa ya kashe mata ido ɗaya tare da ɗaga mata gira Murya can ƙasa yace “Ohh Princess rigima har yaushe kika je” ya ƙare maganar yana sauke ajjiyar zuciya, kuka ta sanya masa tace “Abbi I saw my Dad wlh shi na gani amma ace wai sunansa Imam” buɗe ido yay yace “kai! Kaji wani Shirme wato Mamana ba zaki ajjiye abin nan ba, ina jiya kin gayan ƙilan mai kamarsa ne,amma tayaya mutum zai mutu kuma ya dawo,ki ɗauki komai matsayin ƙaddara kuma ai mutuwa ya huce ƙaddara abune daya zama dole,dukkan mai rai mamaci ne, kiyi masa addu’a kawai!” Kasa cewa komai tayi sai kashe wayar da tayi ta shiga rera kuka ita ɗaya, haka ta ƙare hunin ranar a makaranta ranta babu daɗi,a jere suka fito ita da m.k suna mgna ƙasa² ita dai Moon jinta kawai take domin bata fahimtar komai dan gane da zan can da m.k (Maimunatu Khalid)a tsaye suka samu Imam sanye da Maroon ɗin yadi mai manyan zane, kansa babu hula sai ƙwantaccen gashin kansa wanda ya sha saloon yay kyau an ɗaure masa da ribbon daga ƙasa, hannunsa riƙe da waya yana operating ɗinta, tsayawa Moon tayi hakan yasa m.k tace “muje mana,ai hostel ɗin da tafiya sai mu sauke ki a hanya mu huce” girgiza kai Moon tayi tace “A’a jeki kawai” ɓata fuska m.k tayi tace “please Kinga ruwa za’ai fa” ganin ta kurar da take mata yasa tace “ok” gaba sukai Moon ta zauna baya m.k ta shiga gaba, ba tare daya kallesu gaba ɗayansu ba ya nufi side ɗin driver yana zuwa yaywa motar key tare dayin reverse ya jata da gudu, idanunsa ya ɗaga a hankali cikin Sa’a ya sauke su a kanta ta cikin mirror’n dake maƙale a jikin motar, saurin runtsa idanunsa yay tare da riƙe kansa ya shiga faɗin “Yasubuhanallah!” Fesar da iska daga cikin bakinsa yay a hankali kuma ya ƙara ɗaga idanunsa a wannan karan idanunsu ne ya harɗe waje guda, lokaci ɗaya kuma zuciyoyinsu suka fara harbawa da sauri,a tare dukkan su suka miƙa hannu zuwa saitin zuciyarsu suna sauraran yadda take bugawa kamar zata faso ƙirjinsu tayo waje, ɗauke idanunsa yay tare da kallon gefen m.k kaɗan ƙaramin tsaki yaja murya can ƙasa yace “where is your glass Dolly?” Da sauri Moon ta runtsa idanunta sbd sunan Dolly daya ambata, har gaban abada ba zata taɓa mantawa da wannan sunan ba, babu wanda ya ƙara mgn har yay parking da ɗan zafin nama kuma ya fito daga inda yake zuwa side ɗin baya, hannu yasa ya buɗe mata jiki a sanyaye ta fito idanunta a kansa yama za’ai ace wannan ba shine Dad ɗinta ba,idan har bashi ba ne meyasa take jin bugun zuciyarta na ƙaruwa a duk sanda ta ganshi, bata ankara ba taji hannunsa a saman fuskarta ya zare glasa ɗin dake idanunta take fararen eye balls ɗinta suka bai yana wanda suka ɗan juye kaɗan, kallon kallo suka shiga aika wa junansu lokaci ɗaya kuma hawaye ya wanke fuskar Moon ta sauri ta ƙanƙamesa tana faɗin.
+
*SIRRIN MU today promo #300 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ƴan Niger suyi mgn ta nan 84506476 littafin nada banne tabbas ki zama classes woman wacce ta huce kayan sata wannan promo ɗin iya gobe zai tsaya*
“I knew you zaka dawo gareni nasan kai ne Dad ɗina dan Allah kace kai ne Aliyou Eneye Ahuoyza Deen ba Imam Khalid ba, Dad please” ware idanunsa kawai yay yama rasa mene zaice mata gaba ɗaya baya fahimtar abinda take ce masa, wacece ita ma?? Waye kuma Dad ɗinta? Tayaya zai zama wani Aliyou bayan yasan shi Imam yake, lumshe idanunsa yay haka nan ya samu kansa da jin zafi a ransa sosai yake jin kukanta yana taɓa masa zuciya,baya yay zai shige mota tayi saurin riƙe masa hannu tana faɗin “Noo! No please Dad please come back to me,am your wife your Lolly look at me your Dolly, dan Allah kada ka tafi zan mutu” da sauri yasa hannu ya dafe kansa ganin yadda duniyar take juya masa ga wani sauti dake masa yawo a kunne, duk wannan abun da suke m.k bata san komai ba tana cikin mota ta sanya airpies a kunanta, da sauri da sauri ya shiga fesar da numfashi ganin zai shige mota ya barta tsaye a wajan yasa da sauri ta riƙe yatsarsa wacce ta saba sha bata tsaya jiran komai ba ta tura yatsarsa a cikin bakinta…Dafe kansa yay sbd yadda yake feeding yatsarsa har tsakiyar kansa yake jin abun, da sauri da sauri kuma ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa.

Gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa a saman kansa, cikin zafin nama kuma ya zare yatsarsa daga cikin bakinta, tare da shigewa mota ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa bai tsaya jiran wani abu ba yaja motar da gudu yabar wajan ba ki ɗaya, zubewa tayi a wajan ta shiga rera kuka iya kar ƙarfinta, jin an dafa ta yasa ta juya wanda ta gani tsaye a kanta yasa ta saki wata gigitacciyyar ƙara….

Dafe kansa yay sbd yadda yake feeding yatsarsa har tsakiyar kansa yake jin abun, da sauri da sauri kuma ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa.
Gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa a saman kansa, cikin zafin nama kuma ya zare yatsarsa daga cikin bakinta, tare da shigewa mota ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa bai tsaya jiran wani abu ba yaja motar da gudu yabar wajan ba ki ɗaya, zubewa tayi a wajan ta shiga rera kuka iya kar ƙarfinta, jin an dafa ta yasa ta juya wanda ta gani tsaye a kanta yasa ta saki wani kuka mai taɓa zuciya, shi ne dai ya dawo inda take durƙoshe har ya huce yaji bazai iya ba shiyasa ya nemi excuse wajan m.k yay parking motarsa ya fito, tunda ya tawo gareta yaji gabansa na faɗuwa har ya iso inda take durƙoshe tana kuka kasa ce mata komai yay sai dafa shoulders ɗinta da yay.
Kallon kallo aka shigayi tsakanin Moon da Imam, ajjiyar zuciya ya sauke a hankali kuma yace “who are you? Who is that Dad are you talking about?” Moon ji tayi kamar ta sume a wajan domin sai yau ta taɓa jin maganar sa, jikinta ne ya ɗauki rawa ta kasa tsayawa waje guda sbd ruɗu da fargaba, lura da hakan yasa a sanyaye ya miƙa hannunsa tare da zare glass ɗin idanunta jajayen ƙwayar idanunta ya ƙurawa ido kamar mai na zarta wani abu daga gare ta, cikin Muryar kuka ta kama hannunsa tace “Please you’ll my Dad pls” kamar bazai magana sai kuma yace “ok! Okey stop cry” girgiza kai tayi tace “pls go with me ka tafi dani wajanka” kallon motar dake tawowa wajansu yay yace “Enough, kije gida zuwa gobe” da sauri tace “zaka dawo?” Shima yace “why not?” Yatsarta ta miƙa masa tace “promise” hannunta yabi da kallo musamman Ring ɗin hannunta, da sauri ya dafe kansa yana faɗin “promise” yana faɗin hakan ya juya ya nufi wajan motar domin yasan m.k ce ta gaji ta jira ta biyosa, ganinta mazaunin driver yasa ya shiga seat ɗin gaba batai masa magana ba yaja motar suka bar wajan.Yasmin ce ta kalli yayan nata tace “bro yaushe zaka dawo gida da zama ne,wlh gidan ba daɗi tun bayan rasuwar Daddy, ga Umma kullum bata sakewa” mug ɗin hannunsa ya ajjiye yace “don’t worry soon komai zai zo ƙarshe” tace “Allah yasa” Kallonta yay yace “baki gayamin furniture ɗin da kikeso ba, na kusa barin ƙasar kuma sai gaf da bikin ki zan dawo” dry tai tace “kai bro duk wanda ka zaɓa yayi but color ɗin ya kasance ash and milk” jinjina kai yay yace “ok”. Karatu ya ɗauki zafi babu laifi ta saki ranta sbd suna ɗan gaisawa da Imam, gefe guda kuma ana zuwar mata daga gida, gidansu m.k duk an santa tashin hankali ta ɗaya da taji wai Mai kama da Dad ɗinta shine zai auri m.k takan shiga ɗaki tai ta kuka ita ɗaya,wani lokacin ma har mutananta su tashi ita ɗaya zatai ta bige bige harta dawo dai-dai, sunyi Exam ɗin frist samister result ya fita yadda take so, haka masa second samister komai yay mata dai-dai, a lokacin ta ƙara buɗewa sosai fiye da da, farinta da asalin kyanta na fulani sun fito,ga diri mai ɗaukan hankali ta zama kamar wata labarabiya, abu guda ke damunta wanda yake ɗan zata rama shine Dad ɗinta komai take cikin dauriya take yinsa.
After 7mnt.
Tana zaune riƙe da system ɗinta a hannu daga ita sai 3gauter da vest dake weekend ne bata zuwa makaranta, wayar hannunta ce ta ɗauki ƙara Kallonta dake zuwa ga number ganin number ƙasar ce yasa tai ta mmki, har wayar ta gama ringing tana zaune tana kallon wayar, wani kiran ne ya ƙara shigowa a hankali ta answering call ɗin tare da saita bluetooth ɗin kunanta, cikin ƙaramar muryarta tace “Assalam alaika/ki” daga can ɓangaren aka sauke ajjiyar zcy kana akai shiru kamar ba za’ai magana ba sai kuma akace “uhm”  number ta ƙara dubawa taga dai Tabbas ta ƙasar ce can ta kuma cewa “Hello!” Ƙara sauke ajjiyar zuciya akai da ƙarfi sai kuma aka katse kiran, kasa ci gaba da abinda take tayi hakan yasa ta kwanta lamo zuciyarta cike da tunani bacci yay gaba da ita. The next day ya kama Sunday tana zaune a parlour hannunta riƙe da mug tana speeding tea sanye take da riga half body ta tufke gashinta wanda ya tsaya har bayanta, wayarta ce ta fara ƙara da sauri ta duba sbd tana tunanin ko m.k ce domin sunyi zata so anjima, again number ta gani ta ƙasar sharewa tayi har kiran ya katse a kira na wajan uku ta ɗaga, Ajjiyar zuciya ya sauke yace “na kusa mutuwa cutie, sarautar sai a kaina kuma zata tashi sbd Allah?” Kwaɓe fuska tayi tace “Yaa Faizak” murmusawa yay yace “en matan Yaaya” tace “wannan number b” dry yay mata yace “Malama come and open the door” ware manyan idanunta tayi tace “Serious?” Shiru yay sai kuma yace “kedai buɗe” miƙewa tayi gaba ɗaya ta manta da kayan dake jikin ta rabon da taga wani nata harta manta, wayar tana maƙale a kunanta ta isa wajan ƙofar ta buɗe tsaye ya ganshi a doorway kafin yay mgna tai saurin bashi side hug tace “wlcm Yaa” Kallonta ya shigayi frm head to toe yana mmkin yadda lokaci ɗaya ta ƙara buɗewa ta zama babbar mace, gsky Allah yay halitta a nan ga wani beautiful shape mai ɗaukan hankali,boms ɗinta kan kamar zasu tsaga riga su fito, haka nan waist ɗinta yay mahaukacin buɗewa,ganin kallon da yake mata yasa tai saurin Juyawa tare da ɗaukan hijab ta sanya a saman jikinta, lokacin data juya kusan mutuwar tsaye Faizak yay domin bai tsammaci tsarin halittar ta ya kai haka ba, sauke numfashi yay kafin ya ƙarasa shiga cikin parlour’n, a saman sofa ya zauna yana lankwasa ƙafafuwansa like Prince did, a hankali tace “Evening Yaah” hular kansa ya zame kaɗan sumar kan ta bai yana yace “Evening, how are you cutie?” Kanta a ƙasa tace “Allahamdulillah!” Yace “wunya na keji fa” dry tasu kamata tace “Yaah! Yaushe kazo ne har kake jin wunya” shima dryar yake yace “ban wani daɗe ba,daman wunyar tun a gida na kwaso ta” “wajanwa kazo?” Kallonta yay yaga da gaske dai tambayarsa take “Amayarta nazo zaɓawa kayan ɗaki da lefe” shiru tai bata ƙara mgna ba, sai shine yace “yanzu a sama min abu nacin ko kizo muje Restaurant” miƙewa tayi tana ɗan haɗe fuska ba tare kuma da tace komai ba ta shige kitchen, babu wani jimawa ta haɗa masa fried indomie with fish sai lemo, zama yay a ƙasan carpet ya fara ci a hankali, turo baki tayi ta shiga buga ƙafa tana faɗin “Yaah nifa?” Yace “kaji fa? Keda akazo gidanki meye dan kinyi abinci sai kinci” turo baki tayi ta shiga kwaɓe fuska zatai kuka yace “ohhh ni ɗan gidan Abbana sakko to” da sauri ta sauka ƙasa tare dayin bisimillah ta fara ci da yatsunta guda huɗu, Kallonta Faizak yay yace “why hannu?” Lumshe idanunta tayi sbd tunawa da abubuwa da tayi tace “Haka Dad ɗina ya kuyan shima haka yake” shiru yay mata domin ya fahimci wanne Dad ɗin take nufi,a haka suka gama cin abinci sukai shira har magrib yana nan sannan yay mata sallama ya nufi hotel ɗin daya sauka. Washegari kamar yadda yace ya shirya cikin manyan kaya masu kyau kasancewar yau Monday yasa kai tsaye ya nufi cikin makarantar zama yay har ta gama second lecture ɗinta suka fito tare da m.k suna tafe suna shira kusan rabin shirar  m.k ce keyinta,tun daga nesa yake kallonta harta ƙarasu wajansa tace “wlcm”  m.k tafe “mrng Yayanmu” idanunsa akan Moon yace “ykk?” Tace “Allahamdulillah!” Miƙewa yay yace “Am coming” ya faɗa yana nufar cikin motar da yazo,bayan tafiyarsa suka koma ƙasan wata ƙaramar bishiya mai kyau suka zauna, abu ne ya faɗo mata aka kai tsaye kuma ya shige cikin rigar ta, da sauri ta miƙe tsaye tana karkaɗa  rigar jikinta, da gaske taji abu yana binta a dai-dai kuma lokacin motar Imam tai parking da dukkan muryarta ta shiga ƙwala masa kira “Dad!! Dad!! Dad!!” Gaban sane ya faɗi sai ya kejin kamar an taɓa masa irin wannan kiran a baya,da sauri ya buɗe motar ya fito yana nufar inda suke jakar hannunta ta saki ta nufi wajan da gudu,kansa ya shiga girgiza mata musamman da yaga kallon da m.k take masa ga kuma mutanan da suke wajan, tana zuwa wajansa ta faɗa jikinsa dukkan jikinta rawa yake lokacin abun dake mata yawo har ya zo ƙirjinta.
   *Show me some love to pay my book SIRRIN MU it’s 300 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger suyi mgn ta nan 84506476, kada ki bari ayi babu ke za kiji yadda uwa take son ɗan CIKINTA🙇🏻‍♀️*
Dafe kansa yay yana sauke ajjiyar zcy da sauri Moon ta kama hannunsa tana faɗin “Dad zai cire min nipples, Dad cizo na yake” ta ƙare mgnar tana sakin kuka mai ratsa zuciya dukkan jikinta kuma rawa yake tsoro da fargaba sun gama shige mata, ganin yadda numfashinta ke  sama Alamar gaf take da sumewa yasa hannunsa gaba ɗaya ya ɗauke ta cak zuwa cikin motar kafin m.k ta ƙarasu tuni yaywa motar key ya fita da gudu..
Tsayawa tai tama rasa mene zatai dan baƙin ciki yana fita motar Faizak na shigowa a rikice take faɗa masa abinda yake faruwa motar ya koma yace “enter”  tana shiga yaja motar da gudu, wani mutum ne a can gefe ya ɗaga waya yana faɗin “lokaci yayi saka iya farawa” yana faɗin haka ya kashe wayar baki ɗaya shima ya shiga mota ya mara masu baya mota uku kenan suka hau tsere a tsakiyar titi.
Faizak ta madubi yaga mutumin dake bin bayan motarsa sosai gabansa ya faɗi da ganin mutumin hakan yasa ya ƙara gudun motarsa, fesar da iska yay lokacin daya samu damar tura hannunsa cikin rigar ta tare da ciro abun da yake ciki,wani ɗan ƙaramin maciji ne green sai ɗaga kai yake sama cikin ɓacin rai yay wurgi dashi ta cikin glass ɗin  motar, cikin nutsuwa kuma ya shiga shafa masa wajan daya karceta, Ajjiyar zuciya ta sauke tana jin wani iri kamar lokacin da take tare da Dad yana shafa mata nipples ɗinta, duk abinda yake dauriya kawai yake kansa sosai yake sarawa masa yana jin wani iri a lokacin kuma gani yake tamkar ya taɓa kasancewa da ita, Lumshe idanunsa yay and he try to remember something past.
Bayan motarsa da yaji an buga da ƙarfi yay saurin dawowa hayyacinsa tare dakai Kallonsa ga madubin motar,tsuro yaywa mutumin da sukai ido biyu dashi, da sauri Moon ta miƙe daga jikinsa fargaba tsoro ya saukar mata, murmushi cin nasara Mutumin yay tare da zaro bindiga ya saita ƙirjin Imam, da sauri Moon ta faɗa jikinsa ta rungomesa cikin rashin Sa’a bullet ɗin ya sauka a bayanta, wata firgitacciyar ƙara ta sanya sbd zafin daya ratsa ta nan take kuma jini ya fara zuba a jikinta, kafin yay wani abu an ƙara sakar mata wani harbin a hannunta ko mutsi ba tai ba, ana shirin yin wani harbin aka hankaɗa motar Farouk can gefe ta gangara, driving kawai yake a hankali kuma abubuwa da yawa suka fara dawowa cikin brain ɗinsa idanunsa ya runtse tare buɗe baki da ƙarfi yace “Queen Maimunatou!!….
Na faranta baku??? T

Da sauri yake taka ƙafafuwansa a ƙasa yana tafe yana fesar da iska daga cikin bakinsa, idanunsa ya kaɗa yay jaa sbd tension ɗin da yake ciki, cikin isa da gadara da kuma zallar izzar daya samu kansa da ita a lokaci yake tafiya a cikin Maison Santé Rémusat zuwa ward ɗin da aka kwantar da ita, yana tafe Ammar da Faizak na biye dashi gaba ɗaya cikin babu wanda zaka iya tantance abinda zuciyarsa take faɗa masa akan sabon al’amarin daya samesu, har suka isa ward ɗin babu wanda yaywa ɗan uwansa mgna, a  bakin special female surgical room ɗin da aka kwantar da ita suka samu Nene da Besty sai kuma Yakumbo, Waje yaja ya tsaya yana lumshe idanunsa tare da fesar da numfashi cikin ƙasa da Murya yace “BESTY!”  Ware ido Eneye Ahuoyza yay yana ƙara kallon ɗan nasa wanda yar yanzu mmkin bai yanarsa bai sakesa ba, miƙewa yay tare da ware masa hannayensa, cikin nutsuwar data fara samunsa ba kamar da ba ya fara jan ƙafafuwansa wanda ya kejin sun masa nauyin gske ya nufi wajan mahaifin nasa, jikinsa ya shige yana ƙara maƙale sa, bayansa Besty ya shafa tare da bubbuga bayansa yace “Don’t cry my King” cikin sabuwar shagwaɓar data samesa ya sauke numfashi tare dayin ƙasa da Murya very slow yace “Besty! Queen Maimunatou” kansa ya shafa cikin kwantar masa da hankali yace “just pray for her, in sha Allah! Ubangiji na tare da ita matarka zata samu lafiya anyi theatre an cire all bullet ɗin daya taɓa mata jiki, na bayanta ne kawai matsala,na hannunta kuma bai sameta sosai ba” shiru yay kawai yana fidda numfashi kafin ya zare jikinsa cikin nutsuwa ya nufi cikin room ɗin da take, gaba ɗaya suka bi DEEN da kallo kowa yana jinjina ƙarfin soyayyyar da Aliyou ya kewa Maimunatou. Slowly ya sanya hannunsa a saman handle ɗin ƙofar tun a bakin ƙofar ya fara jiyo fitar numfashinta dake fita da sauri², ga kuma ƙarar computer da akai using dashi wajan maƙala mata oxygen ɗin dake taimakawa numfashinta wajan samun damar fita yadda ake so, hannunsa duka biyun ya zuba a jikin aljihu yana ƙarewa innocent face ɗinta kallo wacce ta faɗa lokaci guda, gently ya fara takawa zuwa wajan gadon gadon tare da ɗaukan chair  ya zauna kusa da kanta, lumshe idanunsa kana ya buɗe ya fara bin blood dake maƙale a hannunta yana shiga cikin jikinta, a karo na biyu kenan jininsa na shiga jikinta, ɗaya hannun kuma drip ne ki shiga a hankali, hannunta ya kama ya riƙe a hannunsa ya fara murzawa a hankali yadda bazai dameta, Ring ɗin hannunta ya gani wanda ta mai da shi ƙaramin yatsarta sbd kaɗan din yay mata, a hankali kuma ya sumbaci hanunu yana faɗin “Wake up My Queen Maimunatou, nothing will happen to you again, nothing   my Shona my Moonlight, no more separate My Lolly am with you forever and ever always Darling Habibaties, kin daina kukan rashin mijinki I’ll make you happy zaki alfahari da samuna zan mai daki Shalelen King Aliyou Eneye Ahuoyza Deen” ya ƙare maganar wasu hot tears na bin fuskarsa, soyayyarta shine weakness nasa ya gama tabbatar da hakan, babu wanda zaice yaga kukansa sai ita,to yaya zai yi ta riga ta zama jinin jikinsa ta zama bugun zcyarsa, kanta ya shafa yana ƙara gyara mata kwanciyar da akai mata ta rufda ciki sbd harbin da akai mata a baya. Wayarsa ce ta shiga ƙara screen ɗin wayar yabi da kallo ganin number na yawo yasa yaja tsaki domin yasan m.k ce tuni ya bata waccan wayar ya amshi asalin tasa a wajan Ammar daman tana nan babu abinda akai da ita. Miƙewa tare sumbatar forehead ɗinta kana yay waje yana tamkar ya dawo da ciwon kansa, Ammar kawai ya gani a wajan a tsaye sai kuma m.k da zuwanta kenan, kallo ɗaya yay mata ya ɗauke Ammar ne yay ƙasa da Murya yace “Sarki Aliyu Al’amin ne ya ƙara su shine suka tafi airport daga nan kuma zasu huce hotel ɗin da suka sauka, shiru yay ko tari bai ba sai da wani Dr ya ƙarasu wajan yace “Wannan patient naku he’s in critical condition” tsaki Deen yaja yay gaba abinsa yana tafe yana duba Rolex ɗinsa dake maƙala ne a hannun Patek philippe, da idanu m.k ta bisa da kallo tana jin zuciyarta babu daɗi, fatanta ɗaya kada ya rabu da ita domin soyayyarsa ta gama ratsa zuciyarta. Ammar ne yabi bayan Dr Salamon har zuwa cikin wani room ɗin tun daga baƙin ƙofa yana jiyo surutansa  da yadda yake bige² shi ɗaya, ƙarasa shiga yay ciki a hankali ya bisa da kallo musamman ƙafar data fita da kuma hannunsa daya cire sakamakon accident ɗin daya faro lokacin daya kaiwa Deen hari, yana tsaka da harbin kuma wata motar ƴan kwana kwana tai gaba da motarsa zuwa cikin wani rami, nan take motar ta kifa ta ƙara kifawa sai data kifa sau uku sannan ta tsaya, tashin farko gaba ɗaya yaransa sun mutum shi kuma a take a lokacin ƙafarsa da hannunsa suka fita, yanzu ma tsananin azabar dake cinsa yasa yake ta ihu shi ɗaya anyi masa injection domin ya samu bacci ya ɗauke sa amma ina ko gyan gyaɗi bai ba sbd karfin da jininsa yake dashi. Washe gari aka ƙara yi mata treatment ɗin wajan, har yanzu bata farka ba amma kuma tana cikin hayyacinta kawai allurar hutu ake mata.
STORY CONTINUES BELOW
A one week later
Dukkan wanda yake dasa hannu a harkar dasu Farouk suke an kamsa yawanci duk ɗaurin rai da rai akai masu shima Farouk ɗin jira ake ya samu lafiya, a wannan lokacin ne Nana khadii tazu dubiyar Moon ita da Ammar sai ƙaramin ɗan ta mai sunan Deen suna ce masa jeniour, gaba ɗaya suna zaune sai Deen da kuma Faizak dake cikin room ɗin, tana jingine da jinin gadon asibitin, ta lumshe idanunta sai tura ƙaramin bakinta gaba take, shiru kawai Deen yake sbd ganin Faizak kusa dasu, gane hakan kuma yasa Faizak ya fita jiki a sanyaye, Moon kallon jeniour tayi dake miƙa mata hannu, yaron ƙyakkyawa dashi gwanin sha’awa, hannu ta miƙa zata karɓe sa Deen yay saurin karɓar sa yana faɗin “Madam wannan ba aikin ki bane,salon ya walar min dake” ya faɗa idanunsa akan jeniour kai ka rantse bada ita yake maganar ba,shi kuma yay hkne domin bai son suga sauyawar da idanunsa sukai, Ammar yace “Eyee kaga mai mata,to mugani a ƙasa mana duk zumuɗin ka aika bari sai anyi bikin” taɓe baki Deen yay kana yace “riƙe ɗanka dan Allah ka fita kaban waje” Ammar na dry yace “idan anƙi fa?” Kafaɗa Deen ya ɗaga yace “Olright saiku zauna kuga haramun” Ammar nayin waje yana faɗin “Banza ɗan iska” Moon kam zuciyarta tace ta fara bugawa da ƙarfi tsoro ya shige ta hakan yasa tai saurin kwanciya tare da juya baya, baiko kalleta ba yaci gaba da operating wayarsa, almost 10mins kafin ya ajjiye wayar yana haurawa saman gadon kwanciya yay a gefenta yana ɗaukan duvet ɗin zai shiga ciki tai saurin riƙe wa tana tura baki tace “Stop please Dad!” Haɗe rai yay yace “i can’t how long na kasance babu ke banji ɗumin jikinki ba, banga big twins naba na duba naga how was it, yaya suka koma i knew sunyi missed nawa” Shiru tai tare da runtse idanunta, sai da ya shiga cikin duvet ɗin kana yasa hanunsa ya zagaye waist ɗinta ya shiga fesa mata numfashi sa mai zafi, runtse idanunta tai sbd tsoran daya cikata, a hankali ya juya ta zuwa gabansa sukai farcing juna, wata wahalalliyar ajjiyar zcy ya sauke yana ƙara matseta a faffaɗan ƙirjinsa yace “How you Sarauniya ta?” Shiru tai tana ƙara tura kanta a tsakanin wuyansa tsoransa ya gama cika mata zuciya, yana jin yadda ƙirjinsa ke bugawa da ƙarfi, wani tattausan murmushi ya sakar kafin ya mirgina da ita ta kalli sama shi kuma ya ɗan ran ƙwafa samanta yana kallon yadda take runtsa idanunta, numfashinsa na fisga da ƙarfi  ya fara janye duvet ɗin dake samanta wanda shine ya rufe ƴar ƙaramar rigar dake jikinta, bakinta na rawa tace “No please Dad, I’m scared, dan Allah ka bari” idanunsa lumshe yace “me zan bari? Taɓa halaliyar tawa? You’re miss taking My Queen nasan kinyi missed ɗina koda bai kai yadda zuciyata ga azabtu da rashin ki ba, dan haka leave me Madam Allowed to enjoy myself” ya ƙare maganar yana sauki wani sexcy sounds  tare da riƙe dukkan shoulders ɗinta bayan yay ƙasa da rigar dake jikinta, Numfashinsa ne ya ɗauke na wani lokaci sbd arba da yay da tsayayyun brest ɗin ta wanda suke tsaye cirrr ga yadda nippy ɗinta sukai wani tsini ga wani fresh da sukai wani kurjanani yaja shi kansa yasan mayen nono ne kamar wanda nono bai ishesa ba aka yaye shi haka yake jin kasan, cikin rawar muryar yace “hold me tighter My Queen My Everything saurauniyar masarautar Nufaz, Uhm!! You’re amazing perfect Moonlight” ya ƙare mgnar yana manna lips ɗinsa a saman ƙirjinta.

Topic👇🏾
*Idan soyayyar Moon da Deen na birgeka to tabbas ba kaga komai idan ka karanta SIRRIN MU💋❤️ daga jin sunan kasa akwai zabba cikin aminci kada kai ƙasa a guiwa domin mallakar naka akan 300 tarayyya mai ban mamaki suna aikata abu ba tare da sanin muhimman alaƙar dake tsakaninsu ba, koda ya yaushe ya hjyarsa ta ratsa jikinta yana jinsa wani nada ban da sauran mazan,amma mene yasa baya iya gane abinda yake ba dai-dai ba ne??? Uhmmmm tashin hankalin an sauya mata fuska zuwa wata daman a yayinda da yake mata kallon biri ita kuma take masa kallon… Ya kasance ta alhalin ita ɗin like mother take a wajansa😫 kai SIRRIN MU daban yake ysin kada kuyi missed posting kullum babu fashi it’s 300 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 idan ta bank zaka tura 300 idan airtime ne 400💃🏽*
Saurin banƙaro masa ƙirjinta tayi sbd sabon abun da taji ya ratsa jikinta, a hankali tana lumshe idanunta ta kama kansa ba tare sanin abinda take ba kuma ta ƙara danna kansa a saman ƙirjinta, sai a lokacin kuma ta ƙara tuna yadda Muhammad Jalal Kabeer bobo na cikin littafin *UNCLE NE* yake suck ƴar riƙon sa JALILERH, lumshe idanunsa cikin ƙwarewa ya fara jan nippy ɗinta yana cijawa kamar yadda Irfan yaywa jidda a cikin littafin JIDDA, baza iya jure yadda yake Shansu ba sbd zugin da raɗaɗin da take ji suna mata, ga wani abu mara daɗi dake mata yawo a jiki sai a lokacin da tuna da  yadda Saif yaywa Zarina ta cikin littafin THE NEW EMIR ba zata iya jure wannan abun ba sam idan LAMRAT ta jure yadda Captain Yisham ke mata ba zata iya ba wlh, hakan yasa ta sakar masa marayan kuka tare dukan bayansa ta shiga ƙoƙarin zare bakinsa daga kan nippy ɗinta duk tsigar jikinta tashi take sam sam ba zata shiga iya jure wannan rashin kunyar ta Dad ɗinta ba, zare bakinsa yay ya shiga fisgar numfashinsa hannunsa dafe da mararsa, jikinsa duk rawa yake wai iya brest kawai daya sha take wannan abun to duk sanda akazo yin kai gaba ɗaya kuma yaya zata kasance? Hannunsa ya miƙa ya riƙe macijiyarsa dake halbawa da kyau baya son taga girmanta bare ta ƙara tsorata da shi, door aka fara bugawa yasa tai saurin tura kanta cikin duvet ƙirjinta na mugun ɗagawa, tsaki Deen yaja a ransa yana jawa mai bugun ƙofar Allah ya isa. Jikin Moon ya warware tass sai abunda ba za’a rasa ba, kaf family babu wanda baizo dubata ba sbd abune na kuɗi jet kawai ake tasa hatta shugaban ƙasa sai da yazo dubiya,m.k kowa tuni ta sallama ita ɗaya zatai ta kuka iyayenta kuma sun fahimci mgnar da Sarki Aliyu Al’amin yay masu kuma ya buƙaci su bawa ɗan sa aurenta babu musu suka amince kuma aka sanya rana da komai, dake Moon sunyi resuming na school yasa gaba ɗaya suka tattara suka koma masarauta yin duniya Deen yay abashi matarsa amma aka ƙi wai san ta kammala makaranta, hakan ya shi ba gantalalle ba ne da lfyarsa da komai yana da mata ba babu bazai zauna har kusan shekara 4 babu mata ba, dan haka yay cancelled ɗin makarantar da take da paris ta dawo Naija akwai makarantun masu kyau idan a nanne, bai fi tai shekara biyu ba ta gama. Kuka Yasmin take mijinta na rarrashinta tace “Dan Allah yay kada ka barmu babu kai babu Abba yay zamuyi?” Umma ma hawayen take sosai ta kasa cewa komai sai faɗin take “Farouk kai ka jama kanka dukkan masifar data sameka nima da nake mahaifiyar ka baka barni ba kullum ina mafarkin samun ƙarin yara ashe kai kake kashesu wacce irin rayuwa ce wannan dan Allah? Ni bazan maka baki wannan abunma daka samu kanka kaɗai ya isheka, wlh da zamanka haka babu ƙafa babu hannu gwamma mutuwar ka” ta ƙare mgnar tana sakin kuka mai ciwo, Aman jini ya shigayi ya nayi yana faɗin “ƙaddara ce Umma babu wanda ya isa ya tsallake ta kuma nima bayin kai na ba ne,dan Allah ki yafe min Umma kada na mutu da fushin ki” cikin kuka tace “na yafe maka,idan mutuwa ce sauƙi Allah ya amshi ranka cikin salama” idanunsa ya runtse yana fisgar numfashinsa yace “Ummu ki neman min yafiya wajan Maimunatou da iyayenta” da sauri tace “ai duk sun yafe maka” idanunsa ne suka fara ƙafewa computer ta hau ƙara da sauri Umma ta shiga faɗin kalmar shahada, yana Kallonta amma ya kasa faɗin ko kallama ɗaya daga cikin abinda take faɗa kuka tasa tace “na shiga uku na mezan gani dan Allah kada ka mutu a haka” Kallonta kawai yake kafin ya samu damar faɗin “La’ilaha illallah Muhammad Rasulullah…” Cak numfashinsa ya tsaya.. After 2yrs Moon ta kammala makarantar ta cikin kwanciyar hankali ta zama cikakkiyar lawyer mai zaman kanta, kuma an sanya ranar Aure nan  da 2week an fara shirin haɗa gagarumin biki na Manyan ƴaƴan sarakuna guda biyu, Moon da Deen, Faizak da M.k hadda taron event wanda aka gayyata domin ya waƙe ango da amarya Arman Maleek ne, jet na musamman aka bashi, anyi anko kala daban daban dangin amarya dana ango abokan Amarya irin su Nimcy’s library Moon fans, Moon comment section nasu ankon daban ashobe suka fitar mai tsadar gaske shine na event na mother’s day kuma color of the day aka bada blue da milk, nan da nan Sapna manya aka fara buga invitation venue Nimcy’s library wajan haɗuwa Moon fanse,  manyan baƙi irin su NIMCY real Smasher m.shakur da sauran su, wajan 4mnt rabon data saka Deen a idanunta, tana zaune saman stool daga ita sai towel tasha gyara babu ƙarya ko ina na jikinta fidda ƙamshi yake, amma duk gyaran da akai mata bata kai Fannah ba ta SIRRIN MU, turo ƙofar akai a hankali bata kawo komai yasa ta shiga shafa mai a saman fresh skin ɗinta, miƙewa tai tana ƙoƙarin zare towel ɗin ya saki ajjiyar zuciya yace “Noo! Please” sbd tsabar rikicewar da tayi bata san lokacin da towel ya zame yay ƙasa ba gaba ɗaya tai naked lokaci ɗaya idanunsa suka sauya idanunsa manne akan ƙirjinta ba tare da wani samaki ba ya fara takawa zuwa inda take kwasa tayi da gudu zata shige bathroom yay sauri cafke ta tare da haɗata da jikinta ya shiga sauke numfashi yana ƙara matseta a jikinsa…
Idan ba ki karanta SIRRIN MU Tabbas anyi babu ke
08119237616

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *