SADAUKIN SADAUKAI CHAPTER 1 by Nura Muhammad

SADAUKIN SADAUKAI CHAPTER 1 by Nura Muhammad

                    Www.bankinhausanovels.com.ng 

Azamanin Da Kusan Shekara1000 Dasuka Shude

Anyi Wani Babba Kuma Shahararren Gari Mesun “DARUL-SHU’UM.  Darul Shu’um Yashahara Tafannin Mayaqa, Dakaru, Manya Manyan Gine Gine Da Shahararrun Matsafa. 

Sarkin Dake Mulki Agarin Wani Axxalumin aljanine, Babban Matsafi, Sadauki Kuma GagaraBadau Afannin Yaqi Me Suna “DAWWAM, 

Sarkin Yanada Wani Shaharren Boka Me Suna “Boka Balbalin Bala’i” Sbd tsananin san duniya irin na sarki DAWWAM yatara dukiyarda shikansa besan adadintaba.

Sarki Dawwam Yanada Wata Kyakkyawa Kuma Jarumar Yarinya Mesuna “SAFRAH”

Gimbiya SAFRAH batabar komaiba awajan ubanta tafannin jarumta da tsafi, abu dayane yabambantata dashi shine ita batasan zalumci shikuwa yakasance azzalumi nagaban kwatance. 

wannan dalilinne yasa sarki DAWWAM bayasan ganin SAFRAH kokadan akusa dashi. 

Sarki DAWWAM Yanada wani buri wanda cikar burinnan tamkar yakin duniya ne.

bakomai bane burinsa face ya mulka dukkan aljanu da bil’adaman duniya suxama suna mulki aqarqashin mulkin zaluncinsa. sakamakon hakane bokansansa yacemasa dolene saiya kashe yarsa domin indan da’ita burinsa baxai ta6a cikaba. 

nanfa hankalin saki DAWWAM yatashi matuqa domin duk abinda ya mallaka natsafi itama tanadashi ko fiyeda shima. hakama afannin jarumta. 

boka “balbalin bala’i” yagayamai cewa baxai ta6a samun nasarar kashetaba saiya mallaki takobin mutuwa wandakecan kulle acikin ‘darul ahbab” dajin wannan xancen sarki DAWWAM yayi matuqar raxana, idonsa suka xaxxaro waje gashin jikinsa suka tattashi tsaye cak domin shiga birnin ‘baitul ahbab’ tamkar yasewa kansa tikitin mutuwane.

 domin atariyi bawanda yata6a shiga yafito garin daransa se dancan garin. bokansa yace masa zeshiga halwar tsafi nakwana arba’in dan nneman mafita tayadda zasu samu damar tinkarar DARUL’ABAB.

sarki DAWWAM Besamu sukuniba wanda mutanen garin sun huta nakwanakinnan. GIMBIYA SAFRAH seda tafara tantamar cewa akwai abinda kedamun babanta domin taga hartsawon kwana40 beyi wani xaluncin dayasababa. tadau alwashin seta nemo menene sirrin. sakamakon hakane tatafi can gefen garin wajan wani qaton dutse inda ta ambaci wasu kalmomin tsafinta. nantake kogon yabude setashiga. 

nanfa sega wani shirgegen aljani mematuqar raxanarwa mesuna BOKA KIRYAN, Ataredashi akwai wasu shahararrun ifritan aljanu guda biyu a dama da hagunsa. Da shigarta sai ifritannan cikin tsananin mamaki sukayi wata qara wadda seda BOKA KIRYAN yadaka musu tsawa mekamada faduwar aradu, sanadiyyar daya janyo girgizan kogon kenan dukda akwai bakaken aljanu guda Dari uku wa’inda suke rike dashi sannan ifritan sukayi shuru.
 Ahankali taqarasa cikin kwarjini atsayuwar sadaukan aljanu. 
sannan taxauna akan wata sihirtacciyar kujera wadda tabaiyana agefenta. da xamanta sai BOKAN ALJANIN wato BOKA KIRYAN yace maraba da xuwanki jaruma uwar jarumai.
 nanfa SAFRAH ta murtuke fuska. se BOKA KIRYAN yace uwar gijiyata karki damu domin nasan abundake tafe dake. kinxone domin jin abunda mahaifinki ke shirin aikatawa na dalilin rashin yin zaluncin daya saba aikatawa.
To kisani cewa mahaifinki nashirin mulkar dukkan wasu aljanu dake yawo aduniyarnan.
kuma babban boka wato yayana (boka balbalin bala’i) kuma babban maqiyina yayimai bincike cewa baxaita6acikar burinsaba saidai inbakya raye domin aduk duniyar aljanu kekadaice metaka masa birki.
 kuma abinda baki saniba shine babanki wato sarki DAWWAM baxai iya kasheki da tsantsar tsafinsaba ko qarfin damtsensaba domin haka yayanke neman ‘takobin mutuwa’ domin da takobinnanne kadai zai iyacin galaba akanki harki mutu.  
Yakara da cewa Yake uwar gijiyata kisani wannan babban al’amarine domin akwai hatsari awannan tafiyar. amma akwai mafita guda daya… 
boka kiryan yace mafitar itace dole saikin nemo aljani MARKAHUL NAR sannan kunemo #SADAUKIN SADAUKAI Wato Sadauki SHAHYAT.
 dajin wannan xancen saitai shuru domin tasan nemo wa’innan tankar nemo allurane acikin tafki bama ace ruwaba.
 boka kiryan ne yakatseta yace mata kisani cewa yanxu xakije neman aljani markahul nar ne kumashi yana can tsakiyar dajin WAQQAS kuma kisani akwai ababen hari dadama abakin dajin. kisani babu mahalukin aljani ko tsuntsun daxai iyabi tasaman dajin face yafado matacce saidai ataka aqasa domin  akwai maridan dake gadin dajin sekunyi yaqi kunci galaba akansu sannan xaki iya shiga waajan dakarun aljanun sannan kiyaqesu harki qarasa wajan kejin da aka kulle aljani markahulnar sannan kusulhunta harku budeshi sannan kudawo mutafi wajan sadaukin sadaukai wato jarumi SHAHYAT……..           
gimbiya safrah tai dariya domin tinaninta duk duniya alokacin ba aljanin daxai iya karawa da ita inba babantaba. sai boka kiryan yace yake gimbiya kisani dajinnan yanada nisa gareki domin atafiyarki xakiyi kwana15 kafin kije. amma inada bawan daxai iya kaiki akwana3. Kafin gimbiya Safrah tayi wata magana tuni boka KIRYAN yatafa hannunsa kafin dakika biyu kogon yafara girgidi Nantake saiga wani shirgegen aljani wanda yake bakikkirin ga manyan damatse daukeda kanbunan sihiri nadaban ya bayyana agabansu.
koda gimbiya safrah taganshi saitai zumbur tamiqe domin yaninkata agirma da kwarjini kusan sau biyu. koda ganin haka saiboka kiryan yaqyalqyale dadariyar mugayen matsafa sannan yace wannanne xe daukeki yakaiki bakin dajin sannan yatemakeki. 
saiya kalli aljanin  yace aljani durfan ka amshi umarni daga uwargijiyarka. saiya durkusa yayi gaisuwa ko amsawa bataiba. 
Tunkafin tazo tashirya da komai, SBD aljanune basajin yunwa (kamar mutanen kano hhhh) sannan tayi tsalle tahau bayansa saiyayi farat ya6ace domin tafiya inda zasuje. 
Aljani durfan yakasance yanada fukafuka guda goma shabiyu kuma duk adakika yakan kada fukafukansa sau ishirin, hakance tasa suka dunga gudu cikin kankanin lokaci……..    
a6angaren sarki DAWWAM kuwa kwana arba’in suncika saiyaje wajan boka ‘balbalin bala’i’ yana xuwa yatarar dashi yafito kenan sannan yace masa yakai shugaba, kasani nayi dogon bincike sannan naga hatsarurrukan dake cikin dajin amma akwai qa’idoji wa’inda xa’abi agujewa 6acin rana
Saiya dauko madubin tsafinsa sannan yashafa saiga wasu aljanu kamar guda 250 sunbayyana agabansu, koda sarki DAWWAM yagansu saiyadan raxana azuciya domin kamarsu daya da  aljaninda gimbiya SAFRAH tagani taraxana. saiyacewa sarki kasani ga xa6abbun dakarunan nabaka guda 250 , to acikin nakama kaxa6o guda 250 sannan kaxo sai ingayama mataki nabiyu sannan kuwuce. karkayi jinkiri domin gobe nakeso afara tafiyarnan. Dakomar sarki dawwam yatara dakarunsa yaware guda 250 sannan yadawo wajan bokansa.
 itakuma gimbiya Safrah tuni sunata tsala gudu cikin sarararin samaniya abayan wannan gansamemen aljanin wato Durfan xuwa DAJIN WAQQAS. arana ta ukunne suka gabato dajin. tinkafin yaxo saiyafara tangal tangal, agalabaice yasauko sannan duka tsaya a bakin dajin suna tinanin mafita..
yayin da sarki DAWWAM yakoma wajan bokansa sai bokan yayi murna sannan kuma yayi wata mahaukaciyar kururuwar firgitarwa.
sannan yacewa sarki, ya shugabana kasani gimbiya SAFRAH ayanxu haka tasan duk abinda kake shiryawa kuma tana hanyar neman mafita wadda inbaka mallaka takobin nanba to dole zaka mutu ahannun jarumi SHAHYAT dominshi tsafi baya tasiri ajikinsa saidai tsagwaran jarumta wanda afanninnan babu sadauki kamarsa…..
 da isar aljani durfan bakin dajin waqqas saiya durkusa gimbiya safrah tasauko abayansa. saiyacemata yake shugabata kisani munxo wajan daxamuyi yaqi iyaka qarfinmu domin wa’innan maridan tsafi baya tasiri ajikinsu. saiya ambaci wasu kalmomin tsafi nantake saiga shirga shirgan aljanunan irinsa sunbayyana guda249 shine cikon na 250din. 
saiyace yake shugabata kisani ga abokan tafiyatanan wato sune zasu taimakamana wajan yaqi da maridannan. nanfa sukafara shawarar waxefara shiga cikin dajin kafin su’ankara saiganin gimbiya safrah sukayi tayi wani tsafi nantake wani haske talullubeta sannan tashige dajin. da shigarta saisuka biyo bayanta duk afirgice. 
sunyi tafiyar rabin sa’a basuji komaiba domin harwasu daga cikin aljanin sunfara tinanin cewa babu wata halitta me rai a cikin dajin.
Saidai maridan aljanunnan suka tabbatar sunzo tsakiyar dajin. kwatsam sesukaji kururuwa daga bayansu. suna waigawa saisukaga wani shirgegen maridi wanda yayi girman katon kogon dutse………. 
cikin tsananin raxana aljani durfan yayi wata kalmar tsafi sewata takobin haske ta bayyana ahannunsa sauranma haka. itakuwa gimbiya safrah tsayawa tayi kallan maridin nan, 
Alokacin  dasuka hada ido shima yayi matuqar mamaki domin yaga batawani raxana kokadan daganinsaba. carab yadamko wani aljani yamatse kansa sannan yawullasa cikin dumbarun bakinsa. 
nanfa kowanne yafara kukkukcewa yana kaimai sara amma abin mamakin shine aduk lokacin da wuqar tata6ashi saitayi tsalle kamar ta daka dutse. 
ita kuwa gimbiya kallansa kawai takeyi.  saiya matso kusa da ita danufin yafyaudeta. Cikin tsananin zafin nama tabude fukafukai tayi sama sannan ta ciro wata sanda tadaka kansa nantake saiya fadi matacce. 
Alokacin dayaje KASA SBD tsananin nauyinsa gabakidaya dajin saidai yayi girgiza nantake sauran maridan kuwa kusan guda 500 duk suka tinkarosu dagudu dansuyi musu zobe su kashesu gaba daya. 
 nanfa aka fara sabon yaqi naban al’ajabi wanda sekace maridannan zasu cinye aljanumnan⁴
08108488607

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *