TSINTACCIYAR MAGE CHAPTER 8 BY AUFANA

TSINTACCIYAR MAGE CHAPTER 8 BY AUFANA

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Dik wani lungu da sak’o na k’asar kebbi ba’inda ba’asaka matakan tsaro ba, hanyoyin shiga da fice filayen jirgi tashoshi dakuma hanyoyi ba’inda ba’asaka tsaroba ko’ina police ne da sojoji,, bincike ake sosai ko’ina da ko’ina ba kama hanun yaro domin kamo momy da mubina,,,,”….

+

Zaune suke suna firan irin k’ok’arinda Rayyan yai, acikin zuciyoyinsu kuwa farinciki ne fall yanzu abu d’aya suke jira shine kotu ta wanke MUFIDA daga zarginda ake mata koma ba’akamo su momy ba tinda dai antabbatar ba’itace ta aikataba to Alhmdllh,,,….

Cikin ikon Allah ana tsaka da bincike sai aka kira D.I.G daga office d’in masu tsaro na filin jirgin Ahmadu Bello International Airport wa’enda ake nema suna daya daga cikin basinjojin jirginda zai d’aga 2pm, nantake aka k’ara tsaro acikin filin jirgin lungu da sak’onsa,,,…

Cikin nasara kuwa Allah yasa akaga momy da mubina da mustapha zaune acikin office din d’aya daga cikin ma’aikatan wajen nan akamasu sannan aka daukesu aka wuce dasu izuwa court,,”….

3pm dot aka koma kotu akacigaba da gudanarda shari’a, bayan mai Shari’a ya’iso sai aka fito da momy da mubina aka kai musty gun momyn su faruk sukuma aka gurfanardasu agaban kotu sai rabon idanu suke dakagansu kaga marasa gaskiya,,,….

Bayan mai Shari’a yagama abunda yake saiya dago yadubesu sannan yacire glass d’in idonsa yafara magana “tabbas kwararan shaidu sun tabbatarda mubina kece kika kashe faruk saidai shaidu basu tabbatar da kece kika Nashe Alhj Ahmad ba amma dole kinada masaniya akan Wanda yakashesa saboda haka kotu na sauraronki daki fad’amata waya kashesa?” dube dube tafara nantake kwallah suka fara zubomata takalli momy wacca itama kwallan take sannan tafara magana “eh ni nice nakashe faruk amma banice nakashe dady ba momy ce” tana fad’a nantake motanen kotun kowa yace “SUBHANALLAH WA’IYAZUBILLAH” nanfa surutu yafara cika kotun saida mai shari’a yai magana “order order  is ok” sannafa akai tsiitt,,,…..

Y’an rubuce rubuce mai Shari’a yai sannan yasake d’agowa yace “mubina meyasa kika kashe faruk meya maki akan wane daliline yasa kika kashesa?” Tsuru tai da idanu tana sai kwallah take zubarwa, ahankali tafara magana “Mahaifina shine silar canzawar halayyata wacca natashi bada itaba sakamakon nunamana fifiko dayake a tsakaninmu da wacca ba y’ar uwarmuba, tinda muka girma muka mallaki hankalin kanmu nafara sanin bambanci tsakanin farinciki da bak’inciki dad’i da d’aci fari da bak’i tin lokacin tsintsar tsanar MUFIDA tafara Shiga acikin zuciyata sakamakon fifiko da mahaifinmu ke nunawa a tsakaninmu da ita, tin muna yara dady yafison MUFIDA akanmu komai zai siyamana sai nata yafi namu kyau da tsada tin bama magana harmuka fara amma idan munyi sai mahaifiyarmu tace ai itace babba akanmu, a makaranta ma idan MUFIDA tai ta d’aya saiyamata kyauta amma ni idan nai bayamun, lokacinda mukaje university sainasamu wani saurayi Wanda nake matuk’ar so najima sosai atare dashi, kwatsam sainagansa da MUFIDA danamasa magana saiyamun tozarci ya wulak’antani a saboda ita, nahak’ura dashi nafara son yayanmu wato hamma faruk, nayi nisa sosai cikin soyayyarsa wacca takaiga harnakasa b’oyewa nafad’awa dady da momy sai dady yace najira harmugama karatu saboda so yake yahad’ani tareda MUFIDA da munira ya aurardamu atare, jin hakan yasa nakwantarda hankalina tinda shi dady yasanda zancen,, kwatsam wani lokaci munyi Hutu muna gida sainaji wai anyiwa MUFIDA baiko da hamma faruk, nayi kuka nayi kuka kamar raina zai fita lokacin ne nafara tinanin kashe faruk zuciyata take ingizani tinda narasasa to itama bazata auresaba” share kwallanda suka zubomata tai sannan tacigaba,,,….

Lokacinda natinkari momy da zancen lokacinne take fad’aman ai MUFIDA basu suka haifetaba, naji dadin hakan ba kad’anba sai momy tahanani d’aukan matakinda nai niyar d’auka tafad’aman tsarinda tai akan dady da MUFIDA, natsorata sosai saida tak’araman kyakkyawan bayani sannan hankalina ya kwanta na’amince da tsarin nata”,,,,….

STORY CONTINUES BELOW

Munjima sosai muna tsara yanda zamu kashe dady da faruk da MUFIDA, kwatsam munacikin wannan tsarin sai dady yake shaidamana yaraba dukiyarsa biyu yabama MUFIDA rabin to tindaga lokacin muka fara farautan rayukansu, Aranarda MUFIDA tazo gida sai mukai amfani da wannan damar bayan tafito daga d’akin dady momy tashiga yana a kwance kan kujera ta baya ta caka masa wuk’a a zuciya, saida ta tabbatar yamutu sannan tafito Wanda nikuma dai dai lokacin nariga nasami faruk a buge yanacikin halin maye nacaka masa wuk’a acik….I” kuka yacik’arfinta saita tsaya,,”….

Saida ta tsagaita sannan tacigaba “acikin tsarinmu hadda MUFIDA zamu kashe amma kasancewar tariga data gawar faruk shine tsarin ya sauya kada asirinmu ya tonu saikawai muka d’oramata kisan akanta, wannan shine abunda yafaru amma wallahi ahalin yanzu munyi nadama munyi ndamar abunda muka aikata muntuba dan Allah a yafemana wallahi sharrin shaid’an ne da binsan zuciya dakuma kwad’ayin abun duniya” acikin kuka take maganar”,,,….

Shuru yaratsa kotun sai sheshekar kukan MUFIDA da munira, mubina da Amira dakuma momy kakeji, su hajiya ma kukan suke amma baka jiyo nasu kukan,,,….

Tsawon mintina aka d’auka ahaka saida mai Shari’a yagama sannan yad’ago yafara magana “to Alhmdllh acigaba da sauraron k’ara da akayi dakuma kwarewa da gogewa had’eda jajircewar lauyoyi yasa muka samu kwararan hujjojinda suka taimakamana wajen kai k’arshen wannan shari’a, kotu tagama tattara hujjojinta kuma tayanke hukunci akan waenda suka aikata laifi wato Fatima da mubina, a saboda laifinda suka aikata kotu ta yankemasu hukunci daidai da laifinsu,,,, kotu tayankewa Fatima Alhassan da mubina Ahmad shitu hukuncin kisa ta hanyar rataya kamar yanda yazo a aya dakuma hadisi dik Wanda yakashe akashesa, sannan a k’ark’ashin kundin tsarin hukunci na Shari’a shima yace dik Wanda yakshe akashesa, wannan kotu kuma tana aikine da Qur’ani da hadisi dakuma kundin tsarin doka”,,,…..

Kotu tawanke MUFIDA Ahmad Shitu tass saboda ya tabbata ba’itace ta aikata laifinda ake zargintaba sannan kuma kotu namaibata hak’uri akan b’atamata suna da’akai kan cewa ta kashe mahaifinta da mijinta, da wannan ne kuma muka kawo k’arshen wannan shari’a sannan inaso nayi amfani da wannan damar wajen tinatarda al’umma”,,,,…..

Iyaye yakamata musan yanda zamu tarbiyyantarda y’ay’anmu idan d’a yawuce d’aya yakai biyu har yawuce to dole ne kasan yanda zaka nunamasu so dakuma k’auna karkace zaka nuna fifiko a tsakaninsu saboda zuciya batada k’ashi tabbas dole asamu zuciyarka tafi son daya daga cikin y’ay’anka to idan kasami hakan saikai amfani da tinaninka karka bari zuciya tafi k’arfinka,,,

           Sannan mudingayin k’ok’ari wajen fin karfin zuciyoyinmu dakuma neman tsari akan shaid’an musani dukiya fa bakomai bace face turd’a abun shek’ewa iska ce ita kokamalleka watarana dole zaka barta wata dukiyarma bala’i ce ga mai ita saboda ko a gobe k’iyama sai talaka yariga mai kud’i shiga aljannah wani talakama saiyayi shekara d’ari uku kan mai kud’i yashigo saboda haka dan Allah
mudinga addua sannan mudinga kokari wajen fin karfin zuciyoyinmu Allah yak’ara tsaremana zuriyarmu yasa mufi karfin zuciyoyinmu yakuma karemu daga bin tafarkin shaid’an ameen,, Fatima Alhassan da Mubina Ahmad shitu sunada damar d’aukaka k’ara izuwa wata kotur daban nanda sati d’aya kan a zartanda hukunci akansu” yana gamawa yamik’e tsaye nankowa yamik’e tsaye,,,….

Tin kan mai shari’a bak’arasa fita ba Amira da munira sukazo da gudu suka rungume MUFIDA suna kukan farinciki nansuka durk’usa sukai sujudul shukru wato sujadar godiya ga ni’imar ubangiji, Rayyan ne yazo yanafad’in “Congratulation sister’s inatayaku murna sosai Allah kuma yak’ara tsare gaba” cikin farinciki Amira tace “Congratulation too Barrister Rayyan tabbas kacika cikakken lauya Wanda ya cancanci lambar yabo muna godiya sosai akan namijin kokarinda kai Allah I sakamaka da mafificin alkhairinsa” yai murmushi yace ameen,,,”…..

Kallonsa MUFIDA tai cikin tsintsar farinciki tana zubda kwallan farinciki tace “THANKS Barrister” yai murmushi yace “ur always wlcm MUFIDA” munira ma godiya tamasa sosai,,, momyn faruk da hajiya da Abbu da Abban ammar suma tasowa sukai sukazo gun MUFIDA kowannensu nazubda kwallah nan taje ta rungume hajiya tana kwallah kowa sai farinciki yake yau gaskiya ta bayyana su momy anji kunya sund’ora hanu a ka sai kuka suke rusawa police sunzo zasu wuce dasu gidan kaso kan lokacinda aka d’iba na zartarda hukunci yayi,,,”….

Atare suduka suka fito jami’an tsaro na bayansu suna fitowa kuwa yan jaridu sukayo Kansu da tambayoyi kowa da tasa kalar tambayar su Amira kuwa farinciki yacikasu harsunkasa amsa tambayoyin sai fara’a suke suna dariya, dakyar sojoji suka samu suka rakasu suka shiga motocinsu tareda escort d’insu suka wuce izuwa gidansu hajiyar dady saboda Abbu yace bazasu zauna sukad’ai acikin wannan k’aton gidanba,,”….

A canma koda suka isa cike yake taff da mutane nanma saida securitys sukai dagaske sannan akashigadasu cikin gidan, suna isa tashiga toilet tai wanka sannan tafito bayan tafito sannan tasaka kayanta tai sallar la’asar, bayan tagama sai baba mai aikin hajiya takawomata abinci, kad’an taci saboda cikinta batajin dad’insa kasancewar tajima batasakamasa abincin kirki acikinsaba,,,…..

Dakyar taiya cin rabinsa shima dan Amira tamatsane nan tasha ruwa sannan ta kwanta nantake bacci mai nauyi yai a won gaba daita, Amira tini nakira ummin ta tafad’amata nasararda suka samu sannan tafad’amata waenda suka aikata laifin, ummi tajinjina lamarin sosai daga bisani sukai sallama,,,”….

Tanacikin bacci saitai mafarkin dady ita da shi suna zaune suna fira wai sai kawai taga yatashi yana d’agamata hanu alamar bye bye yashige acikin wani haske mai haske sosai saikuma yai sama, dagudu taje tana kiransa yadawo yatafi da’ita tana fadin “dady dady dadyyyy” sai kawai tafarka dakarfi tana dube dube, Amira dakammala sallar magrib tana a gefenta takalleta tace “yanzu nakeda niyyar natasheki kiyi sallah nasan mafarkin dady ne kikai ko” hmmm….!!!  tasauke numfashi mai nauyi tareda shafa fuskarta sannan tace “eh ko a prison ma sau biyu ina mafarkinsa kuma dik acikin fararan kaya daga karshe kuma sai munacikin fira saikawai yatashi yatafi yabarni ina kuka koda zan farka sainaga hawaye facha facha a fuskana”,,,,……

Hmm….!!! Amira ta sauke nannauyan numfashi sannan tace ” MUFIDA yanzu ba abunda dady yafi buk’ata agareki face addu’a itace abunda yake buk’ata agareku Allah yamasa rahama ya gafartamasa ya haskaka k’abarinsa” ta amsa da ameen sannan tamik’e tsaye tawuce toilet tad’auro alwala tafito,,,”…..

                 *****  ****

Yau kimanin kwana biyu kenan da dawowar MUFIDA, xaune take akan gado tana rik’e da hoton dady a hanunta sai zubda kwallah take, munira ce tashigo ta taddata acikin yanayin, zama tai tareda dafa shoulder d’inta saita d’ago ta kalleta idanuwanta cike da kwallah, cikin muryar kuka tace “munira yanzu shikenan munrasa dady shikenan bazaya sake dawowaba har abada” saikuma tamaida kallonta kan hoton “Allah sarki dady na I really miss u, I hert u so so much my dad bansan izuwa wane lokacine hawayena zasu daina zubowaba tinda narasaka my dady, Allah yamaka rahama I hert u so much my dady” tak’arasa bakinta na rawa tana kuka,,,…..

Rungumeta munira tai itama tana kukan sannan tace “Aunty MUFIDA idan baki daina kukaba to mu yaza’ayi mudaina dady yatafi har abada saidai in mun cimmasa a can” ahankali munira ta d’ago tashare kwallanda suka zubomata tai murmushi tace “kinga nama manta Abbu ne yace nakiraki yana parlonsa”  nansuka tashi sannan takai hoton ta’ajiye suka fita,,,”….

Cikin sallama suka isa kowa ya hallara acikin parlon harsu Abban ammar hajiya da Abbu suna daga gefe, k’arasawa sukai suka gaishedasu sannan suka zauna, Abbu ne yad’ago yafara magana “to Alhmdllh kowa ya’iso, bakomai yasa nataraku anaba saidan nasan  gaskiyar zancenda nakeji akan MUFIDA” jin ya ambaci sunanta yasa tad’ago ta kallesa tace “Ni kuma Abbu menayi ne” kallonta yai sannan yajuya fuskarsa yacigaba “Fatima tace basune suka haifi MUFIDA ba bayan kuma bantab’asanin wasu iyaye waenda akace na MUFIDA bane saboda haka yau inabuk’atar sanin gaskiyar wannan lamarin”,,,….

Shuru yaratsa d’akin nawasu y’an dak’ik’u can Abban ammar yad’ago yafara magana…………..

Shuru yaratsa d’akin nawasu y’an dak’ik’u can Abban ammar yad’ago yafara magana “hak’ik’a yau itace ranarda yaya Ahmad yace zatazo kuma yai bak’incikin zuwanta saidai naji dad’i da Allah yasa koda tazo baya raye bare ya zubda kwallah” hankalin kowa akansa yake domin sauraron abunda zai fad’a, saida ya kalli MUFIDA cikin yanayin tausayi yace “MUFIDA dan Allah inaso ki d’auki wannan al’amarin a matsayin k’addara kibarsa a matsayin *KUNDIN K’ADDARA* ki tabbas komai yasami bawa to *MUK’ADDARI* ne daga ubangiji dolene saiya sameka” Sam bata fahimci abunda yake nufiba danhaka saiyacigaba da maganar,,,….+
“Tabbas MUFIDA ba y’arsu bace basune suka haifetaba” dasauri MUFIDA ta d’ago kanta ta kalli Abban ammar nantake idanuwanta suka cicciko da kwallah, cigaba yai da magana “MUFIDA y’ar amininsace Alhj TAJUDEEN ABDUSSALAM d’an d’an’uwanka Abbu sarki Abdussalam tsohon sarkin k’asar BAGDAAZ yankin Arab’s,, shekara ashirin da biyar da suka wuce a makarantar TURKEYSH INTERNATIONAL SCHOOL dake k’asar TURKEY wato makarantar yaya Ahmad yakammala karatunsa nazama cikekken likita, anan ne yahad’u da abokinsa tajudeen, cikin k’nk’anen lokaci shak’uwa tashiga tsakaninsu kasancewar abu d’aya suke karanta, sun shaku sosai dik inda kaga yaya Ahmad to zakaga tajudeen anan idan kana neman d’aya kaga d’ayan to kamar kaga d’ayan ne saboda komai nasu d’aya ne saidai inda sukeda bambamci shine tajudeen yana neman mata sab’anin Ahmad, yaya Ahmad yayi iya k’ok’arinsa dan yaga tajudeen yadaina neman mata amma yak’i gashi kuma gida anyi anyi yafitarda mata yai aure kuma yace saiya kammala karatunsa sab’anin yaya Ahmad dahar ansaka masa rana”,,,,…..
Suna cikin karatu akai auren yaya Ahmad da Fatima idan baku mantaba ma har tajudeen yazo shine yamasa babban aboki a auren kuma su sarki dik sunzo, bayan angama shagalin bikin suka koma school suka cigaba da karatunsu,,,, suna gab da kammala karatun tajudeen yahad’u da wata budurwa mai suna SHAHIDA it’s shuwa Arab ce amma mahaifiyarta yar turkey ce, yafara soyayya da’ita kasancewar tajudeen akwai wayou yasan dik yanda zaiyi yaja hankalin yarinya nantake yasiye zuciyar Shahida tafad’a tarkonsa saidai ita son aure takemasa sab’anin shi dayake mata son sha’awa, ahankali ahankali yafara Jan hankalinta harta amince dashi yafara kusantarta batareda sunyi aure ba, lokacinda yaya Ahmad yaji zancen nanfa yai cikinsa yanamasa masifa meyasa shi baya tinani meyasa bazaiyiwa kansa wa’aziba yadaina wannan banzar rayuwar k’azamar rayuwa idan dai har dagaske yake toya aureta mana, amma kasancewar tajudeen yariga yai nisa bayajin kira saiyai banza dashi yawatsarda zancensa”,,,…..
Haka sukacigaba da wannan bak’ar rayuwa batareda sunyi aure ba
, Shahida bata ankaraba kwatsam saiga ciki ya bayyana a jikinta, hankalinta yamatuk’ar tashi nantake taje tasami tajudeen tafad’amasa, shima hankalinsa yatashi sosai saboda dik y’ammatanda yake mu’amala dasu gwangwazajjin matane basa yarda su d’auki ciki amma ita wannan shine ya tirsasat dole badan halayyarta bane to yanzu yazaiyi da’ita, nantake dabara tafado masa saiyacemata kawai a zubda cikin daga baya saisuyi sure nanfa tace ita wallahi ita tinda tasab’awa Allah nafarko bazata sakeba bazata zubda cikinba saidai yasan yanda zaiyi saboda idan gidansu akasani wallahi tashiga tara mahaifinta ko kasheta zaiyi, hankalinsa yatashi sosai dan shid’inma tsoron nasa iyayen susani yake musamman dayakasance gidansu gidan mulki da sarauta ne sarki mahaifinsa sarki zai iya korarsa”,,,….
   Nadama iya nadama Shahida tayita ta d’ora hanu a ka tana kuka sosai saboda tasan tariga data rusa kyakkyawan ginin rayuwarta, tashi tai tafita batareda sungama yanke hukunciba saidai itakam tariga tayanke nata hukuncin,,”….
Yaya Ahmad na zaune tajudeen yazomasa da zancen nan yaya Ahmad yaketinamasa maganarda yamasa a baya amma yaki yanzu gashi tace bazata zubda cikinba kuma tabbas idan tahaihu shi zata kawowa jinjirin,, tin ranar basusake ganin shahida ba har saida suka kai saura sati d’aya suyi graduation sannan tazo da katon cikinta tafad’amasa yazama da shirin karban babynsa dan bazai tafi yabarta dashiba,,”…
STORY CONTINUES BELOW
Bayan sunyi graduation batareda sanin yaya Ahmad ba tajudeen yawuce abunsa saima wata letter kawai daya barmasa shidai yaya Ahmad murmushi kawai yai, bayan sunyi graduation sai yaya Ahmad baiwuce gida ba yana jira ya karb’i notification d’insa sannan yawuce, kwatsam wata rana yana zaune saiga shahida tazo tana Neman tajudeen saboda ta haihu zata bashi y’arshi tawuce nan yaya Ahmad yakefad’amata yawuce garinsu shima baisan lokacinda yawuceba sai yar k’aramar letter daya barmasa, kuka tadingayi sosai tana tsinewa tajudeen Ahmad yadinga bata hakuri”,,,…..
D’agowa tai tana share kwallah tacemasa yunwa takeji dan Allah yabata abinci taci nanyatashi yashiga kitchen domin d’ibomata abinci, koda yad’ibo yafita saiyaga ba’ita ba labarinta tagudu ta’ajiyemasa baby akan kujera, a rikice yafita yana nemanta amma harya zagaye school d’in baigantaba dole yadawo yad’auki babyn wacca taketa baccinta, hankalinsa yatashi sosai yarasa yazaiyi da babyn cikin ikon Allah dabara tafad’omasa nan yashirya yad’auki babyn yadawo gida”,,,….
Kasancewar lokacin ba’a kebbi yake zaune da matarsaba yasa plan d’insa yai dai dai, lokacinda yakawowa Fatima jinjiran kuka tadingayi wato ita tana nan tana killace kanta tana daraja aurensa ammashi yanacan yanacin amanarta to wallahi bazata karb’i yarkowa ta rainaba kasancewar har lokacin basusami haihuwaba, dakyar da sud’an goshi yasamu yashawo kanta takarb’i jinjiran suka fara rainonta suna shayarda’ita da madara,, bayan sati d’aya sai kawai suka kira a gida Fatima ta haihu tasafka lafiya tasamu y’a mace,,,….
Abun yamatuk’ar bama kowa mamaki saboda bawanda yasan tanada ciki kasancewar tayi kusan wata shida rabonta datazo gida ashe baiwar Allah cikine da’ita, nan Ahmad yake fad’amasu ai surprising nasune sukayi saidai shi bayason bidi’a kawai aturomata tsohuwarda zatazo takula tasu amma baza’ayi bikiba zai turamasu kud’i su sayi sa ko saniya su yanka suyi sauran kayan yarkacen shi dagananma Australia zaitafi da matarsa da babynsu saboda su huta, gida basu yarda daba haka itama Fatima iyayenta basuyardaba nan hajiya tace yamaidota gida idan tagama jego saiya d’auketa sutafi nanfa yakafe yace inba hakaba saidai surabu, dole badan sunso hakanba suka kyalemasa matarsa aka tura baba maituwo garin Abuja domin takula da babyn da mai jego”,,,…
Yana kawowa nan yad’ago yakalli su Abbu yace “bayan ni baba mai tuwo ma tasan da wannan Sirrin saboda dataje yaya Ahmad yafad’amata gaskiyar zancen, kasanvewar baba mai sauk’in kaice tace ” insha Allah bawanda zaitab’a jin wannan zancen a bakinta, haka sukacigaba da binne wannan al’amin inda yaya Ahmad da Fatima da baba sukacigaba da bama baby *MUFIDA* cikakkiyar kulawa, wata d’aya kacal baba tai acan yaya Ahmad yakwashesu suka wuce kasar Saudi Arabia suka gudanarda umrah dik saboda MUFIDA, acan ne yarok’i Allah daya tayasa rik’on wannan yarinyar saboda yai alk’awarin bazai tab’a Neman iyayentaba harsai su sunnemeta da Kansu zai cigaba da kula daita kamar yanda zai kula da y’ay’ansa waenda zai haifa nangaba zaikuma rik’eta tamkar y’ar cikinsa”  yana kawowa nan yakalli Abbu da zufa ke ketomasa ta’oina na jikinsa sannan yace “to kaji gaskiyar wannan lamarin” MUFIDA ce tamik’e tsaye kwallah na xubadaga idanuwanta tamkar an bud’e famfo bakinta na rawa tace “wannan wace irin k’addara ce yanzu kenan ni shegiyace wacca aka Haifa batareda aure b…a” bakinta na rawa takarasa maganar tareda fashewa da matsanancin kuka, munira ce tajanyota ta zauna tafara rarrashinta itadinma dai kukan take,,,….
Shuru yaratsa parlon nawasu y’an mintina can Abbu yad’ago yafara magana “tabbas wannan wani al’amarine mai cike da ban al’ajabi saidai babu abunda zamuce sai addu’a dakuma fatan samun kyakkyawar lahira ga Ahmad saboda badik mutum ne zaiyi abunda yaiba kuma insha Allah idan ita MUFIDA tagama takaba zamuje BAGDAAZ domin taga mahaifinta sannan yafad’i inda mahaifiyarta take itama taganta” dasauri MUFIDA tad’ago tamik’e tsaye tace “ni ba’inda zanje Abbu tinda su basunemeni ba nima bazanje gunsuba” tana fadar haka tawuce dagudu tana kuka Abbu yai murmushi sannan yace “kowa zai iya tafiya” nan kowa yatashi yawuce yana jinjina wannan lamarin,,”….
Wunin ranar gaba daya MUFIDA acikin d’aki tayisa tana kuka datagadai wannan bashine mafitaba saita tashi tai alwala tazo tad’auki Qur’an tafara karantawa nantake taji zuciyarta tafara sanyi, saida taji tasami nutsuwa sannan tarufe nantafara korawa dady addu’a tana nemamasa gafara a gun ubangijinsa, tad’auki tsawon lokaci tana yiwa dady addu’a sannan tashafa taje ta kwanta,,,….
               *****  *****
Rayuwa tacigaba da tafiya inda MUFIDA kecigaba da takabar mijinta faruk, yanayinda yanda take saka damuwa a ranta yasa dikta rame yanzu daga d’aki sai parlor kawai take zama saikuma cikin lambu tai karatun Qur’an, munira takoma school ga bilkis itama tana school ga Amira takoma Abuja tini danhaka yasa batajin dad’in gidan sai idan su musty sundawo daga school shikuma batason zama dashi saboda saiyaita tambayanta momy yanacewa takaishi gun momy, tin tanamasa karya yanzu hartarasa mezatace masa idan yatambayeta saidai taita kwallah tarungumesa tana rarrashinsa,,,….
Haka rayuwa tacigaba da tafiyarmasu cikin k’unci da kad’aicin rashin iyaye,,….
              *****  *****
Alhmdllh yau itace ranarda MUFIDA tagama takabar faruk nan momyn su faruk tasaka akaimata kitso da lallen Hausa bak’i hajiya tasiyamata sababbin kaya Abban ammar yabata kud’i da wata abaya mai shegen kyau taitamasu godiya tanamasu kyakkyawar addu’ah,,,”…
Sati biyu da gama iddarta takoma aiki inda Abban ammar yabata matsayin mijinta tamaye gurbinsa wato manager,,,…..
Tini akafara shirye shiryen tafiya kasar BAGDAAZ saidai itakam MUFIDA sam batason tafiyar hakan yasa batawani shiri saima harkan gabanta take, tana zaune saiga kiran Amira yashigo nanta d’aga cikin murna suka gaisa nan Amira take cemata tashirya jibi tananan zuwa tanaso tarakata wani waje ne, kamar Amira tasan MUFIDA neman abunda zaisa tak’i tafiya BAGDAAZ take nantake cikin murna tace mata “ok Allah yakawoki lafiya” tace ameen sannan sukacigaba da firarsu,,,….
Ranarda Amira tazo washe garine tafiya izuwa BAGDAAZ yankin Arabs danhaka zancen tafiya aka fasashi saima akai shirin tafiyar da’ita tinda tazo, saidai batasan wace iriyar tafiyace za’ayiba danhaka ta tambayi MUFIDA shin inane zasuje, nan MUFIDA tafad’amata komai bats b
‘oyemata ba saboda yanzu Amira tawuce k’awa aminiya tazama y’aruwa agunta, Amira tayi mamaki sosai saidai ta jinjinawa dady matuk’a saboda abunda yai badik mutum ke iyayinsaba, nantake tafara shirin tafiyar itama,,,….
Washe gari 8am drivers d’in gidan da bodyguards d’insu suka d’aukesu izuwa airport, 10am jirginsu yad’aga izuwa k’asar BAGDAAZ,,,…
     *MASARAUTAR BAGDAAZ*
Sai kusan 2:30pm sannan jirginsu yasauka kasancewar saida jirgin yabi ta Jidda yasauke fasinja sannan suka wuce, koda suka isa kuwa tini aka aiko da driver’s da hadimai su d’aukesu jirginsu na sauka kuwa suka d’aukesu izuwa masarautar kasancewar hadiman sunsan Abbu yasa suka durk’usa suna kwasan gaisuwa, kai tsaye masarautar suka wuce dasu,,”…..
Masarautar Bagdaaz babbar masarautace babbar daulace wacca aka gina tin kakannin kakanni,,….
Suna isa a k’ofar shiga masarautar hmm baki na sake ina kallon ikon jallah hausawa sukace jaka cikin jaka, wani katafaren ginine akayiwa masarautar Wanda dakagansa kasan tsohon ginine amma ginin ya karb’i sunansa na gini, k’ofar gidan dik dakaru ne zagaye daita kowanne rik’e da bindiga wasu na zarya suna dube dube wasu kuma tsaye suke kawai wasunsu kuma suna zaune gefe d’aya,,,….
Sunaganin motocinsu Abbu nantake da sauri suduka suka taso suka durk’usa suna gaida Abbu sunkumayiwa su MUFIDA barka da sauka lafiya nan cikin sauri aka bude gate motocin suka danna ciki, ko acikin filin gaban gidan saida sukai yar tafiya mai nisa sannan suka isa gunda ake ajiye motoci saboda girman gidan, bayan motocin sun tsaya sannan suka fito suna fitowa saiga dakaru sunzo suna welcoming nasu suka kwashi kayansu suka wuce dasu izuwa masaukinsu, tinda suka iso su MUFIDA ke ware dara daran idanuwansu suna basu hakkinsu gaba d’aya tsarin masarautar yatafi da tinaninsu kaikace masarautar k’asar ingila ne iya kallonka bazakaga karshen gidanba,,,…..
Kai tsaye hanyarda zata sadasu da fadar sarki akawuce dasu, kamar ancewa MUFIDA waiga aikuwa tana waigawa saita zaro daran daran idanuwanta takafe Wanda tagani da mayun idanuwanta…………..
Kuyi hakurin jina shuru 2day’s NEPA namune yasami yar masala amma yanzu Alhmdllh komai normal zakucigaba da jina akai akai kamar da insha Allah ngd ❤👏Kai tsaye hanyarda zata sadasu da fadar sarki akawuce dasu, kamar nacewa MUFIDA tawaiga tana waigawa kuwa saita zaro dara daran idanuwanta takafe wanda tagani da mayun idanuwan nata,,,…..
Tsintsar mamakine ya bayyana k’arara a fuskarta ganin Rayyan tsaye tareda wasu kyawawan y’ammata twin’s larabawa shar dan ko hausardasuke ma dakaji kasan basu iyataba, kasancewar baigantaba yasa tajuya fuskarta tacigaba da tafiya,,,,”…
K’ofar shiga fadar ma tsare take da dakaru hud’u kowanne rik’e da bindiga nan Abbu yashiga gaba sukuma sunabin bayansa, cikin sallama suka shiga ciki mutanen fada suka amsa masu cikin sauri sarki yataso yazo yadurk’usa cikin fara’a yakwashi gaisuwa gun Abbu nan Abbu yad’agosa suka rungume juna sannan abbu ya sumbacesa a goshi nansuka gaisa cikin yarensu na larabci,,,…..
Bayan sungaisa da Abbu sannan yajuyo yabama Abban ammar hanu sukai musabaha sannan suka sumbaci juna a kunce, bayan sungaisa yajuyo yakalli su MUFIDA yafara masu magana cikin harshen larabci nanfa su MUFIDA akai tsuruu ana kallon juna, Abbu dariya yai sannan yafad’awa sarki ai su basajin yaren saidai hausa yai dariya sannan yamasu hausa nansuka gaidasa, tinda MUFIDA taga sarki taketa kallonsa a zuciyarta tace “wannafa mai kama da mr man d’ina kaddai ace shine mahaifinsa kuma shine mahaifina wayyo Allah Allah yasa bahaka bane dansuma twin’s d’inda nagani a waje kamarsu d’aya da mr man to kodai nanne gidansu” hakadai taita sak’e sak’e a zuci,,”….
Bayan sungama gaisawa sai aka masu iso izuwa cikin gida, sashen tsohon sarki da matarsa wato d’anuwan Abbu aka wuce dasu, suna isa sarki yataso yana dariya yazo suka rungume juna shi da abbu suna gaisawa bayan sungaisa sannan su Abban ammar dasu MUFIDA suka durk’usa suka kwashi gaisuwa, bayan sungaisa saiga gimbiya matarsa hajiya zainab tafito nansuka gaisa da abbu sannan su MUFIDA suka gaidata,  suna anan sashen saiga wata kyakkyawar mata tareda kyawawan y’ammatanda MUFIDA tagani tareda Rayyan sun shigo dakaru mata guda hud’u suna bayansu,  nansuka shigo suka gaisa, y’ammatan nan sukazo sukaja hanunsu MUFIDA suna dariya suka fita itakuma momyn faruk sarauniya Sainah tawuce da’ita izuwa sashenta su abbu da abban ammar kuma aka kaisu masaukinsu,,,…..
Sai dare sannan su MUFIDA suka dawo masaukinsu nan sukai wanka sukai sallah suka sauya kaya sannan suka kwanta, around 8pm aka aiko da wasu hadimai hud’u suka kawomasu abinci, girke girke ne kala kala sai wanda kakeson ci hadda na gida Nigeria, 9pm sarki mai ci yanzu yashigo suka gaisa sannan yace sufito sashen sarki za’ayi magana nansuka shirya sannan suka fito atare,,,,”…..
Kai tsaye sashen sarki tsoho suka wuce, suna isa MUFIDA tahango wani mai kama da sarki na yanzu nantake taji gabanta ya fad’i, bayan sun isa sunzauna sai Abbu yafara magana “to Alhmdllh kamardai yanda kukaji tajudeen shine mahaifin MUFIDA kuma shi kansa yasani saidai asakamon wani laifi daya aikata shiyasa bai fad’amaku yanada ita ba kuma yamanta da’ita dikda kuwa da tsawon shekarunda yakwashe bai haihuba, MUFIDA” Abbu yakira sunanta wacca kwallah sukariga sukagama wankewa fuska tad’ago ahankali takallesa yace “wannan shine mahaifinki doctor tajudeen”,, taju ne yace “Abbu kana nufin kace wannan y’atace” murmushi abbu yai sannan yace “tabbas kuwa y’arkace MUFIDA wacca ka haifa da shahida kukagudu kukabarta” duk’arda kansa yai kasa nantake kwallah suka fara zubomasa, mai martaba ne yace “mufa kunsakamu acikin rud’ani kumana kyakkyawan bayani saboda mufahimta” abbu yace “yanzu kuwa zakuji” nantake yabasu labarin komai tin had’uwarsa da shahida har girman MUFIDA da irin rayuwar jin dadinda tai a hanun dady,,,”….
Labarin yamatuk’ar bama su sarki mamaki da al’ajabi dan tinda suke da taju baktab’a basu wannan labarinba, shikuwa banda zubda kwallah ba abunda yake hakama MUFIDA kuka take sosai,sarki mai martabane yafara magana “hak’ik’a tajudeen kayi abunda yamatuk’ar b’atamin rai sannan ka aikata babban kuskure wanda badan MUFIDA tasami kyakkyawar rayuwa ba da bazan tab’a yafemakaba amma yanzu zakaci darajar Ahmad” abbu ne yaisaurin karb’an zancen “yanzudai ai Alhmdllh dama abunda mukeso kusanta kusan jininkuce sannan shima yasan yanada y’a itama kuma tasansa sannan yafad’amana inda mahaifiyarta take domin akaita taganta dikda basunemetaba”,,,….
STORY CONTINUES BELOW
    Taju ne yad’ago fuskarsa yace “hak’ik’a nai nadamar abunda na’aikata kuma natabbata abunda na’aikatane yake biniyana tsawon shekara ashirin da wani abu dasuka wuce, tinda nai aure bansami haihuwaba matana biyu uku muka rabu saboda bana haihuwa amma kowaccensu bata tab’a yin b’ariba har izuwa yanzu, naje school d’inda mukai karatu naita neman shahida amma harnadawo bangantaba kuma bansami wanda yace yasantaba haka nagama yawona nadawo, MUFIDA dan Allah kiyafeman ki yafemana dan Allah” MUFIDA kasa cewa uffan tai saboda kukanda takeyi, Abbu ne yace “kadaina kuka yarona komai yawuce ai Allah dai yak’ara shiryarmana da zuriyarmu” suka amsa da ameen, d’agowa taju yai yace “abbu to ina doctor Ahmad ne bakuxo atareba” duk’arda kai abbu yai sannan yasauke nannauyan numfashi yad’ago yace “Ahmad Allah yamasa rasuwa Ahmad yarigamu gidan gaskiya asanadin matarsa data kashesa” nanfa Abbu yabasu labarin komai har irin wahalarda aka ganawa MUFIDA, sun jinina lamarin sosai taju hadda kwallah saida yaita zubarwa saboda tsintsar tausayin halinda MUFIDA tashiga asanadin laifinda bata aikataba,,,”….1
Tajudeen yad’ago yashare kwallanda suka b’atamasa fuska sannan yafara magana “Shahida mahaifiyar MUFIDA bansan asalin gidansuba ammadai nasan ita y’ar k’asar Turkish ce sunanta kuma Shahida Safraz shik’adai nasani agameda ita” abban ammar yace “insha Allah zamusameta inada wani abokin
business d’ina dayake k’asar zannemesa namasa magana” daganan dai sukacigaba da tattaunawa harsuka yanke MUFIDA zata zauna anan BAGDAAZ izuwa wani dan lokaci saboda tasan y’an uwanta suma su santa,,,”….
Wasu hadimai mata mai martaba yakira su hud’u suna zuwa sai yace “kukaisu sashen gimbiya Zainab gunsu Nasma da Nasmat akaita gun Biryama shima tagansa tasansa takuma gaidashi da jiki gobe saisuje suzaga gari suje gidajen sauran y’an uwa” nan hadiman sukace amsa sannan su MUFIDA suka mik’e tsaye suka fita,,,….
Kai tsaye sashen gimbiya suka wuce dasu bayan sun isa su MUFIDA suka durk’usa suka gaidata nan dasauri su Nasmat suka taso suna murmushi suka kamasu MUFIDA suka wuce d’akinsu MUFIDA sai kallonsu take itadai suna mata kama da mr man d’inta, Amira tace “waye biryama hala” Nasmat tace “yayanmu ne shi” kasancewar tafi y’ar uwarta jin hausa sosai sai Amira tace “to sarki yace kukaimu gunsa mugaidashi” sukai murmushi saisuka mik’e tsaye suka fita hanun Nasmat nasakad’e dana MUFIDA,,,,….
Cikin sallama suka shiga tareda bud’e k’ofar parlon, wani katafaren parlor ne naji da gani daka gansa kasan bana k’aramin mutum bane kodai yarima kokuma shi kansa sarkin, atare suka kutsa suka shigo yana a zaune kan kujera 3seater kafafuwansa kan matashi Rayyan kuma na gefensa yana b’are masa aiba yanabashi yanaci a hankali, Rayyan ne yakab’a sallamarsu saboda yasan bazaiwuce twin’s din sarki bane, cikin fara’a sukaje suna masa magana cikin harshen larabci suna fad’amasa waiga wasu y’an uwansu sunzo daga Nigeria zasu gaidasa, Rayyan yafara d’agowa yagansu tsaye suna kallonsa wani irin murmushi yai sannan yace “a,a kai maraba manyan bak’i mukai ashe sannunku da zuwa” Amira ce tace “Barrister sannu dai ya aiki” yace “Alhmdllh MUFIDA yakike” murmushi tai tace “lafiya k’alau Barrister ya aiki” yace Alhmdllh,,,…
Jin an ambaci sunan MUFIDA yasa yad’ago tareda juyoda fuskarsa ya kallesu yanayin tozali da kyakkyawar fuskarta yatashi zaune dasauri, tanayin tozali da fuskarsa itama tai saurin ja da baya tareda zaro dara daran idanuwanta cikin tsintsar mamaki tace “mr man” wani zama yai tareda kwantarda kansa saman kujera fuskarsa na kallon sama yafara magana cikin wani irin yanayi mai cike da tsintsar ban tausayi “MUFIDA kin wahalardani kin wahalarda zuciyata meyasa kika tafi kikai nisa dani meyasa kika bar zuciyarda take cike tsintsar so da k’aunarki” wasu zafafan kwallah ne suke zubomata ahankali tanatso kusa dashi sannan tafara magana cikin muryar kuka bakinta har rawa yake,,,….
“kaine yadace nayiwa waennan tambayoyin MUJAHID shin kakuwasan halinda katafi kabar zuciyata aciki lokaci d’aya zuciyata takamu da tsintsar k’aunarka saidai ina kariga dakamata nisa tashiga had’aruruka ba adadi dik a sanadin sonka” tasowa dakyar yasaukarda k’afuwansa k’asa ganin haka Rayyan yazo da sauri zai rikesa saiya dakatardashi yakama dakyar yamike tsaye Nasmat da Nasma suka zaro idanuwansu suka firfito dasu waje saboda mamaki mutuminda yake kwance tsawon shekara amma yau gashi yamik’e tsaye, ahankali ya tattako yazo kusa da’ita Rayyan nakusa dashi yakalleta yace “kinga waennan k’afafuwan yau kimanin shekara d’aya da wata bakwai kenan rabonsu dasu taka k’asa dik a sanadin sonki” kamo hanunta yai suka kama hanyar wani d’aki, suna isa Rayyan yasaka key yabude d’akin suka shiga, suna isa first abunda tafara tozali dashi shine wani k’aaaton hotontane manne a bagon d’aki tana sanye da abaya wankanda tai ranarda akai graduation d’insu MUJAHID a k’asansa kuma anrubuta My smole baby, k’arasawa tai ciki tana kallon bangon ginin d’akin koina da koina hotunantane dik waenda tai ranar wasuma batasan lokacinda tayisuba wasunsu a k’asansu anrubutu my JERRY wasu kuma my smole baby wasunsu kuma my one and only wasu kuma my MUFIDA, waigowarda zatai sai taga wani wanda yahad’a hotonta danasa k’asa yarubuta TOM AND JERRY,,,….
Waigowa tai ta kallesa tareda rufe bakinta da hanunta d’aya tana murmushi kuma tana kwallah sannan tace “nadade da d’aukan nikadai ce ke haukana nikadaice ke fama da d’awainiyar son ka ashe kaima hakane” baiyi maganaba murmushi kawai yai,,”….
Amira ce tamatso kusa da’ita tadafa shoulder d’inta tace “bakekad’ai bace Jerry, tin lokacinda kika kamu da son MUJAHID kuma kike shan fama da k’aunarsa nai alk’awarin saina had’aki da MUJAHID har kuyi aure, nafara shirin yanda zanyi nashawo kan MUJAHID ya’amince yakarbi soyayyarki, bayan mungama karatu mun rabu sainafara naman Rayyan saboda nasan zanfi samun sauki idan nahad’a baki dashi, cikin ikon Allah kuwa nasamu ganin Rayyan wani abun mamakin danasamu agun Rayyan shine, shima Rayyan din burinmu d’aya dashi nanyake fad’aman shima MUJAHID yakamu sonki, nantake mukafara shirin had’aku saidai kash koda nakiraki saikike sanardani ansaka ranar aurenku da faruk, nayi bak’inciki sosai saboda naso MUFIDA ku mallaki junanku kodon kuci ribar k’aunarda kukeyiwa junanku amma ina abun yafu karfinmu”,,,…..
Lokacinda naji labarin faruk yamutu naji dadi saidai kuma dadin yakoma ciki saboda cewarda akai kekika kashesa, lokacinda nake neman lauyanda zai tsayamaki sai kwatsam Rayyan yazo yace indai zan amince nataimakasa wajen shawo kanki ki’amince bayan kingama idda ki auri MUJAHID to zai tsayamaki harsaiyatabbatar anwankeki daga zarginda ake maki yakuma bani labarin halinda MUJAHID yake ciki dik asanadin sonki har yakaiga baya iya tafiya da k’afafuwan sa yakasa auren kowacce mace dik wacca aka kawomasa saiyace batamasa ba, nan take na amince kuma Alhmdllh sai mukai nasara, shekaranjiya dana kiraki nace zaki rakani bikin k’awata bawani biki dazamuje dama nanne zan kawoki kiga irin halinda MUJAHID yake ciki dik a saboda sonki”,,,,…..
Wani irin nannauyan numfashi MUFIDA ta sauke sannan tad’ago ta kallesa wanda yakafeta da mayun idanuwansa tai murmushi tajuya fuskarta sannan tafita, suma murmushin sukai Nasmat tace “dama yaya ciwonka ciwon so ne shine aka kasa samun maganinsa” dariya suka kyalkyale da’ita yajanyota ya rungume tareda mata rankwashi sannan suka fita parlor,,,….
Tindaga ranar wasan b’uya suka fara tak’i yarda su tsaya suyi magana wai kunyarsa takeji irin abunda tamasa a baya, saidai tsohuwar zumar soyayyarsu ta taso tadawo sabuwa gall yanzuma saitafi ta da d’in saboda wannan kunyar tata saima yaji k’aunarta tak’ara shigarsa……….

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *