YAR LEKEN ASIRI CHAPTER 8 BY ANUP JANYAU
(_SPY_🎥)
Www.bankinhausanovels.com.ng
Wani irin dirowa Saimah tayi daga kan kujerar da take zaune, saboda ba kâaramin tsorata da ganin Binta tayi ba, don tunda ta shigo bata lura da ita ba sai yanzu. Saurin kallonta Kuzeem tayi sannan ta maida dubonta wurin Binta. Dâan guntun tsaki taja tare da bâalla ma Saimah wata uwar harara tace;
âTou shugabar matsorata, mutum ce ba aljana ba, tunda kika shigo fa take dâakin nan amma mitar da kike bata baki damar ganinta baâ.
Wata nannauyar ajiyar zuciya Saimah ta sauke tare da kâyalkâyalewa da dariya sannan ta koma ta zauna tace;
âYoo ai tsoro halas ne, ya zaâayi inga mutum bansan daga ina ya fito ba in rasa tsorataâ.
Murmushi kawai Kuzeem tayi bata ce mata komai ba, sai mamakin tsoro irin na Saimah take.
âAunty fitsari nake jiâ.
Binta ta fadâa tana isowa wurin Kuzeem, jin hakan yasa Kuzeem ta mikâe tare da rikâa hannunta suka nufi dâakin da ta shiga dâazun, saida ta duba bathroom dâin taga akwai ruwa a ciki sannan ta barota ta dawo palor, tana zama Saimah tace;
âKuzeem wannan yarinyar fa?â.
Dâan lumshe idanuwa Kuzeem tayi kamar ba zatayi magana ba sai kuma can tace;
âKi ajiye maganar wannan yarinyar a gefe, zamuyi ta daga bayaâ.
Gyadâa kai Saimah tayi alamar gamsuwa kana tace;
âTou amma me kika zo yi a RADDAL haka?, harda su kama gida sai kace wacce batada kowa a cikin garinâ.
Guntun murmushi Kuzeem tayi ba tare da ta budâe idanuwanta ba tace;
âNa samu aiki neâ.
Cike da tsantar mamakin jin furucinta Saimah ta gyara zama tana fuskantarta da kyau sannan tace;
âHajiyata ban gane kin samu aiki ba?, fahimtar da niâ.
A hankali Kuzeem ta budâe lumsassun idanuwanta kana tace;
âShima zan miki bayani daga bayaâ.
Saimah da haushin halin Kuzeem ya cikata bata sake cemata komai ba ta maida hankalinta kan wayarta, daidai lokacin Binta ta dawo palorn, kallonta Kuzeem tayi tare da fadâin,
âKinyi breakfast?â.
Saurin girgiza kai Binta tayi tace;
âAâahâ.
Kuzeem bata ce mata komai ba ta maida dubonta kan Saimah tare da fadâin,
âDr please ki kai yarinyar nan eatery taci abinciâ.
Dâagowa Saimah tayi ta kalleta tace;
âTou ke kinyi breakfast dâin ne?â.
âKarki damu bana jin yinwaâ.
Kuzeem ta bata amsa, tare da maida dubonta kan wayarta da kira ya shigo, da hanzari ta dâaga kiran tare da karawa a kunnenta.
âBarka da warhakaâ.
Kuzeem ta fadâa tare da yin shiru tana sauraren abinda ake fadâa mata, bayan kamar 5 minutes tace;
âOkayâ.
Tana gama fadâin haka ta ciro wayar daga kunnenta ta katse kiran. Car key dâinta ta dâauka ta mikâama Saimah tace;
âKi fita da motar da kika gani waje, nima zan fita da taki akwai inda zanje, ina so ki wuce da yarinyar nan wurin aikinki, idan na dawo zan biya in dâaukotaâ.
Kai kawai Saimah ta gyadâa mata, tana mamakin Kuzeem a ranta, don ta kasa gano komai tattare da ita, karbâar key dâin da Kuzeem ta mikâo mata tayi kana ta mikâa mata nata Car key dâin motarta tare da mikâewa ta kalli Binta tace;
âTashi mujeâ.
Ba musu ta mikâe tare da bin bayan Saimah da ta nufi hanyar fita kana suka fice daga palorn. Kuzeem kuwa kallon agogon hannunta tayi taga har 11:20am tayi, mikâewa tayi ta nufi wurin trolleyn ta dake ajiye a palorn, tare da budâe zip dâin sama ta ciro wani file mai dâauke da tarin takardu ta ajiye gefe, sannan ta budâe ainahin babban zip dâin trolleyn ta ciro wata maroon satin silk gown, da wani glass golden wanda cikinsa yake orange, daga haka ta rufe trolleyn.
Wasu maza biyu dake tsaye a dâan nesa da Estate dâin na ganin fitowar su Saimah, sukayi saurin fadâawa cikin motarsu tare da bin bayan su cikin dubara yanda wani ba zai fahimci su suke biya ba.
Dâan kallon jikinta tayi, Allah ya sani tana bukâatar tayi wanka saidai babu lokacin da zatayi wankan da zai gamsar da ita a halin yanzu, a gurguje ta tubâe abayar dake jikinta sannan ta zura rigar da ta dâauko, ba kâaramin kyau tayi mata ba, veil dâin rigar tayi rolling kanta da shi tare da kafa tsadadden glass dâin a idanuwanta wanda yayi azabar yimata kyau, ya kâara fiddo da karan dogon hancinta sosai, duk da bata fesa turare ba amma hakan bai hana ma jikinta fitar da sanyayyen kâamshin turarenta ba mai shegen dadâi.
Dâaukar file dâin tayi tare da nufar wurin da wayarta da Car key ke ajiye ta dâauka, sannan ta fice daga dâakin, kai tsaye wurin da Saimah tayi perking motarta ta nufa tare da budâe kâofar motar ta shiga sannan ta tada, a hankali ta fara yin baya kana ta juya motar cike da kâwarewa, tare da nufar hanyar get, daidai lokacin wata arniyar mota ta kunno kai cikin get dâin, hakan yasa Kuzeem dakatawa har saida motar ta shigo sannan taja motar ta fice daga gidan.
A harabar wani tsadadden eatery Saimah tayi perking sannan ta budâe kâofar motar ta fita tare da zagayawa ta budâema Binta ta fito, kana ta rikâa hannunta suka nufin cikin wurin. Fuska dâauke da mamaki mutanen da ke biye da su suka kalli juna sannan dâayan yace;
âMun samu matsala ba yarinyar ba ce a cikin motarâ.
Dâan shiru dâayan yayi sai can yace;
âTabbas ba ita ba ce, amma kuma ai a airport munga lokacin da ta shiga cikin motar kuma tunda suka baro airport dâin baâa tsaya da ita ko ina ba sai cikin Nagarta Estate balle muyi zaton ko ta fita daga cikin motar neâ.
âGaskiya da sake bari mu kira Alhaji mu shaida masa, domin mu samu mafita don wallahi da zaran munyi sake wannan aikin ya wuce mu tabbas mun tabka babbar asaraâ.
âKaji shirme, kai a tunaninka in mun kirashi zamu samu wata mafitar ne?, tou bari kaji wallahi bamu gayawa Alhaji, tsayawa zamuyi a nan har sai wannan yarinyar ta fito mu bita muga inda zata komaâ.
Tafiyar kusan 40 minutes Kuzeem tayi sannan ta iso cikin wata area da shirunta yayi yawa, saboda jefi-jefi mutane ke gilmawa, kuma babu gine-ginen gidaje a wurin saidai manyan gini masu kama da Companyâs. Gaban wani tafkeken gini Kuzeem ta tsayar da motarta tare da dâan sauke glass dâin gefenta tana kâarema wani symbol dake gefen wurin kallo, wanda aka rubutama *MCTV RADDAL*
Mayar da glass dâin tayi sannan ta fara danna horn, cikin sauri get dâin wurin yayi wani irin zugewa gefe tamkar an turashi saidai babu kowa a wurin, ba bata lokaci Kuzeem ta cillah kan motar cikin farfajiyar hadâadâdâen gidan talabijin dâin, wanda yayi mugun kâayatuwa duk inda ka kalla saika sake kallo, komai a tsare yake gwanin birgewa, babu kowa a wurin saidai tun kallon farkon wurin zaka sha jinin jikinka saboda naâurorin dake wurin ba ma gaskiya ba ne.
Kai tsaye perking lot ta nufa tare da tsayar da motar, sannan ta dâan jingina bayanta ga kujerar da take zaune tare da fara danne-danne a wayarta, cikin Email dâinta ta shiga tare da dâaukar wata Special number da aka turo mata, sannan ta kira number, tana jin an dâaga kiran tace;
âHey Iâm Kuzeem Yusuf Garba, gani na kâaraso a cikin wurinâ.
âOkay mun ganki, yanzu zaâa zo a shigo da keâ.
Abinda aka fadâa mata kenan, dâan murmushi Kuzeem tayi tace;
âAlright!â.
Daga haka ta katse kiran sannan ta dâau file dâin gefenta ta budâe motar ta fita tare da dâan jingina da jikin motar tana kâarema tsarin wurin kallo don ba kâaramin birgeta yayi ba, tsawon 3 minutes sannan ta hango wani babban mutum ya fito ta cikin wata kâofa, kallo dâaya tayi mashi ta dâauke kanta ta mayar kan naâurar da mutumin ya bayyana a cikinta. Fuska dâauke da murmushi ya iso wurinta tare da fadâin,
âYouâre welcome Kuzeem Yusuf Garbaâ.
Dâan murmushi Kuzeem tayi masa bata ce komai ba, daga haka yace ta biyosa, hakan yasa Kuzeem ta bi bayansa suka nufi kâofar da ya fito.
Tun Mom Eshmal na zuba idanuwan ganin dawowar Binta harta cire ranta, sai mamakin take meyasa takâi dawowa, tunda ta san ba yau ta saba cin ubanta ba kuma bai hana ta dawo. Shigowar mijinta ya sanyata saurin mikâewa tana kallonshi, da mamaki tace;
âHoney lafiya ka dawo?â.
Kan kujera ya zauna tare da dâan shafa kan Eshmal dake bacci kan kujerar kana yace;
âTafiya ce ta kamani shiyasa na dawo in sake dâan watsa ruwaâ.
âIna kuma zaka je?, duka yaushe ka dawo RISAM zaka wani ce tafiya ta kama kaâ.
Wani kallo yayi mata sannan yace;
âTou zan miki kâarya ne?â.
Saurin gayyato murmushi tayi akan fuskarta, tace;
âBa haka nake nufi baâ.
âOkay, ina Binta?â.
Wani irin bugawa kâirjinta yayi, tayi shiru tana kallonsa ba tare da ta bashi amsa ba.
âWai bakiji ina tambayarki Binta ba?â.
Ya fadâa a dâan fusace ganin Mom Eshmal tayi shiru, gefenshi ta zauna tare da dâan hadâe rai ta cinno baki gaba sannan tace;
âHoney sai faman tambayar yarinyar nan kake, sai kace dafata nayi na cinyeâ.
Wani kallo ya watsa mata kana ya maida dubonsa saitin dâakin da Bintar ke zama, cikin dâan dâaga murya yake fadâin,
âBinta!, Binta!!â.
Dakâyar Mom Eshmal tayi kâokâarin daidaita nutsuwarta, tare da yakice tsoron da ya mamaye zuciyarta, tace;
âHoney bata nan faâ.
âTana ina?â.
Murmushi tayi mishi tace;
âWallahi ta raka Mom Arif unguwa ne, ka san Binta mutuniyarta ceâ.
âOkay!, dama naso kira mata Nafisa ne su dâan gaisa, tunda kwana biyu bataje wurinta ba, jiya ma muke magana da ita akan batun School dâin da nace miki zan sanyataâ.
âAllah ya taimaka Honey, gaskiya samun irinka zaiyi wuya a wannan lokaciâ.
Inji Mom Eshmal har lokacin fuskarta na dâauke da murmushi.
âAmeen Ameen ai yiwa kaine, ko kin manta kirkin Nafisa ne?â.
âAâah ina kuwa zan manta?, tunda ga âyarta nan ta bamu sukutumâ.
âTou kin gani, ai saidai kawai fatan mu rikâe amanar da ta bamu, ko don maraicin yarinyarâ.
Dâan kawar da kai gefe tayi tare da tabâe baki sannan tace;
âHakane kamâ.
âYawwa, tashi ki hadâamin ruwan wankan, in kama jikiâ.
âAngama mai martabaâ.
Mom Eshmal ta fadâa kana ta mikâe ta bar wurin tana sauke ajiyar zuciya.
******
Kuzeem na biye da mutumin har suka iso cikin wani babban office mai kyan fasali da tsaruwa, wanda mutane hudâu ke zaune a gaban wani dogon table, kowanensu na danna laptop dâin gabanshi, shigowar su Kuzeem ya sanyasu dakatawa daga abinda suke. Gefen macen cikinsu mutumin ya nuna ma Kuzeem alamar ta zauna, babu bâata lokaci ta isa wurin tare da jan kujera ta zauna fuskarta a sake. Yayinda mutumin ya iso wurinta ya dâauki file dâin da ta ajiye akan table dâin, sannan ya nufi gefen dâaya daga cikin mutanen wanda da alama shine babbansu, ya ajiye masa file dâin a gabansa kana ya koma ya zauna.
********
âKin kâoshi da abincin ne?â.
Saimah ta tambayi Binta, ganin ta daina cin abincin ta rafka uban tagumi.
âEhâ.
Binta ta fadâa a hankali, Saimah na kâokâarin sake magana wayarta ta fara ruri hakan yasa ta dâaga kiran tare da fadâin,
âHello Sis Hananâ.
âWai ina kika tafi ne tun dâazun?, gashi zaâa shiga meeting baki nanâ.
Daga can bâangaren wata mace ta fadâama Saimah, cikin sauri Saimah tace;
âOh ganinan kan hanya Sis Hanan, thanksâ.
Tana gama fadâin haka ta katse kiran tare da dâaukar Car key ta mikâe tana kallon Binta, tun kafin tace da ita wani abu itama ta mikâe sannan suka fice daga wurin.
âYawwa gata nan ta fitoâ.
Inji dâaya daga cikin mutanen dake biye da su, da kallo suka bi su Saimah har suka shige cikin mota, nan suma suka shiga tasu motar tare da rufa musu baya, sunyi tunanin Estate dâin Saimah zata koma sai sukaga ta sanja wata hanyar, suna biye da ita har ta iso Hospital dâin da take aiki, hakan yasa suka dakata daga biyarta don sunsan bazasu samu damar bin ta har ciki ba saidai suyi zaman jiran fitowarta.
********
âWell done Kuzeem Yusuf Garbaâ.
Suka fadâa mata fuskokinsu dâauke da murmushi, itama murmushin tayi musu tace;
âThank youâ.
Wata doguwar takarda macen dake kusa da ita ta mikâo mata, tace;
âKi duba dakyau duk abinda baki fahimta ba zaki iya tambayaâ.
Kai Kuzeem ta gyadâa mata alamar gamsuwa tare da karbâar takardar ta maida hankalinta akanta, ta dâau tsawon wasu mintuna tana duba takardar kana ta dâago tace musu duk ta fahimta, ba kâaramin dadâi sukaji da hakan ba, saida suka kâara tattaunawa kana suka ba Kuzeem damar tafiya sai kuma Monday wato ranar da zata fara zuwa aiki.
Driving take cike da kâwarewa, bâangare dâaya tana kâarema yanayin garin na RADDAL kallo, saboda yana dâaya daga cikin garuruwan da take jin dadâin kasancewa a cikinsu, musamman ma da ya kasance nan ne mahaifarta, daga baya kuma ta tattara hankalinta wuri dâaya ta shiga nazartar wasu muhimman abubuwa. Saida ta tsaya wani tsadadden restaurant tayi take away abinci, sannan ta nufi asibitin su Saimah, tana isowa bakin get dâin asibitin tayi wani murmushi mai tarin maâanoni ko mai ta gani?, oho, har tayi perking a harabar asibitin bata daina murmushin ba, tana fitowa ta wuce office dâin Saimah, saidai Binta kawai ta tarar don su Saimah sun shiga meeting, da wannan damar Kuzeem tayi amfani da ita wurin yima Binta tambayoyi, inda ta bata hadâin kai dâari bisa dâari ta amsa mata duk tambayoyin da tayi mata, dâan shiru Kuzeem tayi tana nazarin abubuwa da dama a ranta, sannan ta dâago ta kalli Binta tare da fadâin,
âAmma meyasa baki tabâa fadâama Mijinta ba ko Mamanki?â.
Wani irin zaro idanuwa waje tayi tace;
âHaka tace idan na sake na fadâama wani saita yanka ni, kuma dagaske takeâ.
Kuzeem bata san lokacin da murmushi ya subâuce mata ba ganin yanda Binta ta zaro manyan idanuwanta, sai kawai Saimah ta fadâo mata a rai.
âKina son na mayar dake gida?â.
âEh Aunty, dan Allah ki maidani wurin Mamanaâ.
âTou zan mayar dake gobeâ.
Cikin tsananin murna Binta tayi tsalle ta rungume Kuzeem tace;
âNagode Aunty, zan fadâama Mamana ke mutuniyar kirki ceâ.
Ba kâaramin tausayi yarinyar ta ba Kuzeem ba, hakan yasa taci alwashin saita koyama Mom Eshmal hankali. Suna nan zaune Saimah ta dawo, gefen Kuzeem ta zauna tana mata sannu da zuwa sannan suka fara dâan tabâa fira, wanda yawanci duk Saimah ce kâarfin firar don Kuzeem ba wani amsata take ba saboda hankalinta na kan wayarta tana duba wani abu. Sai misalin 2:30pm ta mikâe tace ma Saimah zasu wuce, nan kowacensu ta karbâi Car key dâinta, har harabar asibitin Saimah ta rakasu, sallama sukayi sannan suka shige motar, yayinda Kuzeem taja motar suka nufi get dâin asibitin na baya wanda ba kowa ya san akwai shi ba.
âMiswar kaga motar dâazuâ.
Hisham ya fadâa yana nunama Miswar motar Kuzeem da ta kunno kai cikin layin, fuska a dâan tamke Miswar ya dâago ya dâan kalli motar yana kâokâarin dâauke kansa yaga motar ta tsaya a dâan nesa da inda suke.
Kuzeem kuwa hango wani dâan tsoho zaune a gefen titi ya sanyata tsayar da motar domin ta bashi sadaka, a hankali ta budâe kâofar motar sannan ta fito. Wani irin bugawa zuciyar Miswar tayi har saida ya lumshe idanuwansa, yanajin yanda bugun zuciyarsa ke kâara tsananta, wanda tunda yake bai tabâa tsintar kansa cikin irin wannan yanayi ba sai a yau, sakamakon arba da yayi da Kuzeem, wacce baima gama tantance ya yanayinta yake ba, saboda akwai âyar tazara a tsakaninsu.
âSubhanallah!â.
Inji Hisham yana cigaba da kallon Kuzeem da ta nufi wurin dâan tsohon, sai kuma ya dâan kalli Miswar yaga idanuwansa a lumshe.
âAbokina kar in gani ni dâaya, budâe idanuwanka kaga wata kyakkyawar halittaâ.
Saurin girgiza kai Miswar yayi tare da fadâin,
âBa bukâatar hakanâ.
âMtssww kai ka saniâ.
Hisham ya fadâa yana maida hankalinsa kan Kuzeem da har ta mikâama tsohon sadaka ta dawo wurin motarta, shiga tayi tare da jan motar ta bar wurin, Miswar kam ya kasa budâe idanuwansa har lokacin don shi kadâai yasan me yake ji.
âWai Miswar lafiya kuwa?, meyake damunka ka wani lumshe idanuwa?â.
Cewar Hisham yana kallon Miswar dâin cike da mamaki, ba tare da Miswar ya budâe idanuwansa ba yace;
âBabu komai Abokinaâ.
Kuzeem na shigowa cikin Estate dâin wayarta ta hau ruri, ganin Bilal ne ke kiran nata ya sanyata dâagawa, a hankali tace;
âBilal ya ake cikiâ.
Daga can bâangaren Bilal yace;
âDaidai Kuzeem, ya yanayin gidan da kike?â.
Bata bashi amsaba saida tayi perking motarta kana ta sauke wata ajiyar zuciya tace;
âBabu dadâi sam, naso in bar gidan a gobe saboda wani dalili, saidai akwai abinda nake son aiwatarwa tukunaâ.
Murmushi mai sauti Bilal yayi kana yace;
âDa fatan dai bai shafi mutanen cikin gidan ba?â.
âInhar abinda hasashenka ya baka kenan, to tabbas yayi gaskiyaâ.
Inji Kuzeem tana budâe kâofar motar ta fita, âyar dariya Bilal yayi yana mai kâara jin zazzafar kâaunar Kuzeem a ransa, ina ma ace zuciyarsa nada kâarfin halin tunkarar zuciyar Kuzeem ta sanar mata sirrin da ke tattare da ita.
âSai anjimaâ.
Sassanyar muryar Kuzeem ta tsamoshi daga duniyar bege da shaukâinta da ya fadâa, saidai bai koyi yunkâurin magana ba, har Kuzeem ta katse kiran, budâe back seat tayi tare da ciro ledodin take away da tayo.
Cikin sauri Mom Eshaml da tun dazun dake tsaye bakin windown palorn ta tana zaman jiran dawowar Kuzeem ta fito daga palorn, tana isowa wurin su Kuzeem tasha gabanta tace;
âKe kâaramar âyar iska ce, amma zan nuna miki nawa iskancin yaci uwar naki gaba da bayaâ.
Tana gama fadâin haka ta cafko hannun Binta da nufin janta su wuce, saurin sakin hannun tayi jin azababben cizon da Bintar ta gatsa mata a dâayan hannunta, yayinda Bintar ta koma wurin Kuzeem da gudu.
âKam ubanchan, ke Binta ni zaki ciza?, lallai..â.
Maganarta ta sarkâene ganin sun shige cikin gidan sun barta tsaye a wurin, cizon yatsanta tayi sannan tabi bayansu saidai jin kâofar a kulle yasa jikinta yayi sanyi, bubbuga kâofar ta shigayi tana surfama Kuzeem zagi kamar wata hauka sabon kamu, da dai taga alamar Kuzeem bazata budâe mata kâofar fa ta bar wurin.
Kuzeem kuwa saida ta watsa ruwa ta sanja kaya sannan ta zauna cin abincin don ba kâarya yinwa ta tasota a gaba, ko don jiganiyar da tayi, tunda ta saba da rashin cin abinci da wuri, barinma yau ko breakfast bata yi ba, shiyasa abun yayi mata yawa.
Kusan mayar Mom Eshmal biyar tana bubbuga musu kâofa akan Kuzeem ta bari Binta tazo, amma sukayi uwar shegu da ita tamkar basu san tanayi ba, dole ta hakâura don kanta.
******
âRabson wallahi na gaji, haba sai kace wasu âyan iska tun dâazun muna kime wuri guda kamar wasu kayan wanki, kawai mu fadâa masa bamu ganta baâ.
âMatsalata da kai kenan Bash mugun dâan ujila ne kai wallahi, dama ba sai an wahala ake samu ba?, naga dai halas dâin mu ne muke nema tunda dai uban yarinyar nan ne da kansa ya sanyamu mu rikâa bimasa diddiginta, ai ko kaga ya yarda damu dâari bisa dâari to meyasa mu bazamu basa hadâin kai ba?, kaga inkai baka iyawa kawai ka kama gabankaâ.
Yana gama fadâin haka ya tada motar, âyar dariya Bash dâin yayi yace;
âNa fahimce ka abokina, ya kuma naga ka tada motar?â.
âZamu tafi sai kuma gobe, tunda safe zamuje wurin Estate dâin mu tsaya, daga bisani mu dawo nanâ.
âTou shikenan hakan ma yayiâ.
Inji Bash dâin, daga haka suka bar wurin.
*The following day*…….✍️
#Anup💋â·â¶ âžâ°