DANGIN JUNA BOOK 1 CHAPTER 2 BY SA,ADATU WAZIRI GOMBE

DANGIN JUNA BOOK 1 CHAPTER 2 BY SA,ADATU WAZIRI GOMBE

 

 

bakaken maganganun da ta gayawa Faruk ya

fado mata, ta tuna yanayin fuskarsa lokacin da

take gaya masa. Take ta ji wani gumi yanko mata, tuni ta yaye bargon duk da haka gumin bai bar diga mata ba tamkar wanda take labour room, duk da A.C da fanka da ke aiki amma gumi sai Karuwa yake.Kuka take shabe-shabe da hawaye,

“Yaya faruk ka yi hakuri, wallahi ina sonka! Wallahi ina sonka’Idonta a rufe suke hawaye ko sai Bul bula suke tamkar an Balle famfo.

Duk da dare ya yi amma ya kasa hakura

sai gobe ya z0 yaga Fatin, a wannan tsohon

Daren ya kamo hanya, abunka da dan gida kai

saye ya wuce dakin Fatin.Sai ya ci sa’a Kofar ba a sa mata key ba,Bude Kofar ya yi ya hango ta kwance rigingine’ a tsakiyar gado idonta a rufe, ga kuma hawaye ya wanke mata fuska,

sunan shi kawai ke fita a bakinta,. Kura mata ido ya yi, Subhanallahi!” A gaskiya ba zai iya hakura da Fati wani ya aure taba, kyan jikin Fati ba Karamin ruda shi ya yi ba,duk yadda yake tunaninta ta wuce nan.Bai san lokacin da ya isa kan gadon ba, kwanciya ya yi kan cinyarta, a hankali ya soma shafar lallausan jikinta.

“My dear please ki aure ni, wallahi ba zan

iya rayuwa da kowacce mace a rayuwa ba sai ke,

duk kokarin da na yi don in iya hada jiki da

Maryam na kasa Nan ya yi ta fadan maganganu

cikin shauki, so, Kauna da sha”awa, daga ganinshi ka ga wanda ya kamu da ciwon so.

A firgice ta bude ido cikin matsanancin tsoro

Da fargaba, ganin Faruk din bai ba ta mamaki ba kamar yadda ta ganshi kwance kan

cinyar ta yana aiwatar da abin da bata zata ba.

“Faruk kana da hankali kuwa?”Fati ni mahaukaci ne bani da hankali ko kadan, na haukace a ciwon sonki, Don Allah ki taimaka ki warkar dani, don Allah Fati ki aure ni, wallahi in ban aure ki ba ina ga mutuwa zan yi,in kuma ban mutu ba zan gwammace mutuwa da rayuwar da zan yi.

Ki taimaki dan’uwanki ki aure shi”

Ta riga data san maganar Faruk ba wasa,ya riga da ya gama haukacewa, don haka inba

dabara tai mishi ba yadda za a yi ya tashi a

kanta.Ta ce,To Yaya Faruk na ji tashi muje

falo ka ga in Umma ta z0 ta ganmu a haka zatayi fada Cikin hanzari ya tashi, “To muje Fatina,

wallahi dama na san kina sona kuma za ki aure

Ni Gaba ya yi tana binshi a baya, sai da taga

ya fita ta yi sauri ta rufe Kofar tasa key. Da karfi

ya juyo ya turo kofar yaji ta rufe, bugawa ya yi

ta yi tamkar zai Balla kofar.Kasancewar Kofar gilas tana ganin shi shima yana ganin ta, tsugunawa ya yi yana hawaye shabe-shabe.

“Fatina don Allah ki bude, Fatina rayuwata zata nakasa in bake, don Allah ki taimake ni ki bude Ita ma kukan take amma sai ta tashi ta ja

labule ta rufe. Ya yin da ya ci gaba da magiya

Fati kuma sai kuka. Umma dake daki ta fito ta samu Faruk cikin mummunan hali, don kuwa

ya dawo tamkar tababbe, sai surutai yake.

*Fatina without u life is impossible to

spend my love. I found it very tough, I can’t

even breath properly. Please do me a favour”.

Ki bude kofar nan ki z0 muje ai mana aure

Umma ta dafa shi,Haba Faruk, me yasa

baka da hakuri da kuma tawakkali?”

“Umma ya zan yi da sonta, nima ban san

ya zan yi in daina sonta ba. Umma ko kina min

addu’ar abin da ya fi alheri. kar ki min

addu’ar Allah yasa in daina sonta, don wallahi

bana so in daina sonta. Wallahi Umma ina sonta

da yawa,ina sonta sosai. Ummana inason

Fatina”Umma ita ma hawaye take na tausayin

danta, bare uwa uba Fati da ta rasa yaza ta yi a

daki, don a gaskiya yadda ta dauka Faruk na

sonta har ta wuce yadda take tsammani.

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *