GIDAN ƘWARATA CHAPTER 22 BY MAMAN teddy🧸
Www.bankinhausanovels.com.ng
Bismillahir rahmanur rahim”.
______________________________
“My name is Aliyou Muhd….endigin in Adamawa State,Son Of Africa,Origin In nigeria…i did my Pri&junior School in Abuja Tk School…popularly name As Turkish”. Ba Daliban kadai ba,har ta Aunty Florence Yaron ya tafi da imanin ta,sosai Aliyou Haidar ya burgeta,mussaman dangane da yanda yake Maganan tasa so fluently,hakan yasa ta ta Fara tafa masa,kamin duka sauran daliban su hau masa tafi”. Komawa yayi ya zauna,Rufaida ce ta kalli Deen dake a gyefe kana tace”Deen ba’ancen Haidar dan Familyn Dan Larabawa neba? Meyasa bai fadi mana daga Cikakken Inda ya fito ba? Kallon Rufaida Deen yayi kan yace’Kin san kowa da kalon sa,musamman dabi’ar Haidar tasha banban dana Saura,baya son mutum mai fahari,bare kuma shi yy fahari da Gidan da ya fito! Jin hakan yasa Rufaida jan bakin ta tayi shiru,don ta fahimci daga Haidar din har Nuradeen ba kirki ne dasu ba!
“wata dalibar ne ta kuma mikewa hadi da isa gaban daliban…. Tafara bayani kamar haka ni Sunanan Hauwa Adam”. Haifaffiyar Kano ce ni,amma muna zama anan Kaduna….Sbd aikin da ya kawo Mahaifina nan”. Abunka ga Yaran masu kudi babu kirki komai yin shi suke kwar,nan suka hau meye Aikin Daddyn ta? Murmushi Hauwa jidda tayi,kana tace”Mahaifina Police ne,Yanxu haka shine Commissioner of police na kd state”. Wow…..Kikaji Ajin ya dauka,hadi da tafi…komawa tayi ta zauna bb yabo babu fallasa,don haushi ma suka bata Students din”.
Nan Deen ya mike shima yy bayanin kanshi,kana ya koma ya zauna,Kirar Wata Dalibar akayi daga Office din Principal,wanda yasa Anty Florence bata Excuse tayi waje……… Kamin ta dawo yawan ci Sun kammala Gabatar nawa Yan Abokan nan nasu da sunan su,wanda cike da Harkar ta da ya xamamata jiki a kullum fuskar nan nata na cikin kwantacciyar,kuma sanyayyiyar murmushi…(smilling face) shigowa class din tayi Kamin Anty Florence ta dakatar da ita tana cewa”saura ita ne ta yi masu introducing din kanta”.
Murmushi Ne kwance saman fuskarta,wanda A hankali cike da salbin ta tafara takawa,har saman inda Antyn nasu take tsaye”. Cike da Confidence din t,da yakasance a jinin jikin ta yake ta fara cewa”My name is Hafsat Attahir,Frm Kaduna state,Zongo road”. I came from Public School! Kamin ta kuma wani magana ne Duka ilahirin daliban suka sheke da Dariya harda masu buga desk,suna nanata Kalmar Public School…Tom meya kawota cikin su ayamxu,matan da tayi makarantar gomnati tun daga Pri har Secondary?. Haushi ne ya kama Hauwa Dake a gyefe,ganin Yanda Duka daliban ke dary,Dogon tsaki tajah kana ta buga Desk tana Fadin one Classs…Whats Noncense is dis? Ibeg Ss1 Student Will you Shutup???? Tayi mgnar a kufule da kuma karfi,wanda yasaka Anty florence daka masu tsawa,duk da yasaba ma Dokan makarantar yin hakan da tayi”.
Nan gabaki ďaya Class kowa ya dauke wuta,Murmushi Anty florence tayi kana tace”U are Wlcm dear”. Nan Hafsat ta bata amsa da tnx….sannan ta koma wurin Zaman ta”.
Tana Tfya wasu a dalban sun guntse dariya….Ciki kam harda Gank din su Aliyou Haidar,Da shi idan ka ganshi bakace wai yasan da akwai abun dake faruwa a Class din ba,sbd miskilancin sa”.
Dan tsaki yajah kamin daga jin Haka,sukayi tsit don sun san shi sam bayason damu Hayaniya”. Zaman da xatayi ne yasa Hauwa tasowa tsam tana xama gyefen ta,don sosai Hafsat din taji tabata tausayi,don ko ba afadi mata ba,tasan ita din ba yar gidan kowa bane face talakawa”.
Ahaka ne Antyn tasu tafara masu Abunda ya kawota,kamin lokaci kadan aka fita break”. Mikewa Hafsa tayi don komaawa Office din principal,don har yanxu cuku² n ta akeyi”. Don tabbas tasha Wuya kamin ta samu schoolarship a makarantan nan”. Sosai akaso murdewa,wanda har da ta cire rai,kuma Sai Allah ya kuma dawo mata dashi.
Mikewan da xatayi ne yasa Hauwa Mikewa tana cewa”Muje na rakaki! Tom tace da ita kimin sufara Kokarin barin Class din,tsit daluban sukayi,don bb wanda yy dariya a wannan karon,don Tsoron Hauwa da sukeyi,A haka suka fice gank din su Aliyou ne da yake tabatattu ne sune suke sa Dry still”.
Office din principal suka nufa,wanda matame karamci sosai take nuna kaunar ta gaHafsan,wanda anan ta kammala mata komai,sannan suka fito tare”.
Tun da Suka fita daga upstairs din suka hango Su Aliyou Haidar,a saman benan kome ya kawosu oho”. Tsaki Hauwa tayi,kamon tace Su Aliyou basa da Kirki,amma dai dai nake daku,dadin Abun kunsanni sarai”. Ta fadi mgnar suna takawa don sauka Stairs din”. Kee…? Muryar Wani daga cikin Su ya doki dodon kunnenta…wanda kaman baxasu tsaya ba,sai kuma su jah suka tsaya”. Takawa yy har xuwa inda suke tsaye”. Kana ya kalli Hafsat yana cewa”Aliyou Haidar ke son mgn dake”.
Binsa da kallo sukayi,kamin Kaman wanda suka yi shawara wurin yin Abu guda,kawai sai suka hada baki wurin jan tsaki,Hauwa ta kama Hannun ta suka barshi nan tsaye……..
Sakin baki daliban dake kallon komai dake faruwa sukayi,wanda basu kadai ne ke mmkin wulakanta su Aliyoun da tayi ba,aa har Da su kansu Gank din nasu”.
Waye Ubanta??? Tambayar da yayi mawa Su Nuradden kenan?
“Bamusan ta ba,bamu san ma daga inda take ba,Amma Ko a mgnar data fadi Class yaci mu fahimta ita din ba yar uban kowa bace face yar talaka. Deen yayi mgnar cike da kara jin haushin Hafsa da tuni sunyi nisa,bama sa ta kansu”. Wani ne A cikin su yace dasu”Kuma shine har ta kalle mu ta wulakantamu? Itaba kowa ba? Haka ma Uban ta? . takaici ne duk ya rufe Aliyou,Kawai sai cewa”Yayi ya isa haka,banason wani bayani ya biyo baya! Da jin haka nan duka sukayi shiru don fahimta da sukayi a harxuke yake da Yarinyar”.
Deen ne yace”Aiko taci banxa,kuma a yau sai munyi maganin ta”. Lukman da tuni bayaice Ufun bane yace dasu”Ai kila daga yau tabar makarantar nan har abada,ku muje Class suna can!
Nan sukayi gaba yuuu xa’aje acima Hafsa mutunci,wanda Nan Haidar yakai hannun shi yana riko na Lukman kamin yace dashi” me zakayi mata? Me kuma tayi? Cike da mamakin tambayoyin shi nama bacin rai Lukman yace”Kama manta abun da tayi kenan,yanxu ace taxo kana kirar ta tawulakanta mu dakai duka,amma wai kana tambayar me tayi ne?. Tom ai ni naga ni tayi mawa,baku ba…kawai ku kyeleta! Yana fadin haka ya fara takawa hadi da nufan Student cantin na Makarantar,yabar su dabin bayan sa da kallo”.
Wow mekyau nan! Cewan Rufaida Tana nuna shi ga kawayen ta da suka lullubeta”. Kara murtike fuska Aliyou yayi,don Bayason mace mai shegen iyayi kaman na Rufaida,Hyy Aliyou ykk? Tayi mgnar tana daga masa hannu”. Wanda sai da ya juyo ya kalleta,kan ya kauda kansa gyefe,yana mgn da mai shagon da Yaje sayayya,Wato uncle Anabeth”.
Tsayawa Sukayi suna binsa da kallo,kamin ya gama abun da zaiyi ya fice yabar su nan…
Haka Har aka tashi gida,Kowa nason tmbayar Aliyou Ba’asin da yasaka shi kin hukunta Hafsa,amma sun kasa,sbd bb fuskar yin hakan! A washe gari ne da misalin Break kaman na jiya…suna a tsaitsaye Sai ga Hafsa da Hauwa Sun taho wucewa,Kurr Aliyou yayi mata da ido,kaman bazai sauke kallon daga gareta ba,har sai da Deen ya tabashi yana fadin wao.me kk kallo a jikn Wannan kucakar yarinyar ne? mganar yy yana sauka a kunnen su Hauwa,Amma sam basu tankasu ba,don ba Hafsa ba,itakan ta Hauwa ta ji tsoron kar yaxo Alyou Talala yy masu,don sarai tasan Halinsa”.
Bai basa amsa ba,illah cigaba da Kallon Students da yy abun shi. haidar Way meyasa jiya kace arabu da Wannan yarinyar ehh? Lukman Yayi mgnar yana taboshi”. Kaman baxai basa amsa ba,sai kuma yace”I just fail in love! Love??? Duka suka hada baki wurin nanata kalmar! Yeah”. Yabasu amsa a dakile”. Waye kk son? Lukman yakuma tambayar sa cike da mmki”. Gata can! Yy mgnar yana nuna inda Hafsat da Hauwa suke a zaune”. Ya juyo ga Lukman yana sakin masa murmushi,amma dai wasa kakeyi ko? Lukman din yy mgnar yana cin Seriuos”.
Na taba yi maka Wasa ne,yy mganar kaman shine gaba da Lukman din,Ina sonta,kuma ni tun a jiya na fadi ma Ammie,na samu matar da zan Aura! Ohh Allah! Aliyou na fahimci haukar yarita ke damunka”. Wacece matar Auren naka? Wancen Yarinyar da kk Age mate ne xaka Aura? Nan deen ya amshi damgnar Lukman yana cewa” Rabu dai Da Aliyou,kila Ma Kamin yy Aure ita tayi har ta haihu da Jikoki”. Nan kaji sun kwashe da Driiya…wanda yabata ran Aliyou Haidar”. Tom se mene? Ni Ita din nakeso,kuma mgnar agemate dina,ai Atarihi ma yaxo mana dashi,Annabin mu Ya auri Nana khadija da ta girme masa,bare kuma ni da take aagemate dina, Inna Aureta sai Ku Hana!.
Jin yanda ya bude masu witar Fada yasa su jahn bakunan su sukayi shiru,Deen zo muje wurin Hafsa,na fada mata ina sonta! Aliyou ka tsaya muyi tunani”. Baxan tsaya ba,idan xakaxo muje malam kaxo mu wuce,idan baxaka…aa muje tom”. Deen yayi saurin katse sa yana takawa hadi da nufar inda Su Hauwa suke a zaune”.
Kirjin Hafsa ne ya buga,ganin Aliyoun da Aminin shi Wato Deen,babu Fara’a ko kadan saman fuskar shi … Deen ne yayi mawa Hauwa mgna da cewa”Hauwa’u Muna son mgna da Hafsa”. Kallon su Hauwa tayi cike da mmki,sai kuma tace”Tom me zakuyi mata? Murmushi Deen yayi kamin yace”Boss ne ke Son mgna da ita😂 . ieem nan ta yatsina baki kamin tace”Ok Hafsa ina jirar ki a kofan Class…ta mike tabar Hafsa da ta tagaxa cewa komao,Hankalin ta ya dan tashi,don ta lura Haidar baya da mutunci sam”. Mikewa tayi daga tsaye kaman yanda yake”. Kamin tace”Ina jinka”. Hmmm shiru yayi na en seconnni,kana yakalleta ido cikin ido,bb kunya yace da ita” Hafsa Ina sonki,Inason zana Aure ki..kefah?
Mamaki gami da haushi Ne duka suka rufeta,lallai wannan yaron ya raina ta,abun da take cewa”kenan A xuciyarta da take wani irin tafasa,wanda kamin ya ankare Yaji saukar ya tsunta biyar a saman kuncin shi”. Tasssss… Wannan marin yasaka Gabaki daya ilahirin daliban Side din suka juyo da hankslin su a kan Aliyou da Hafsa”.
Amaimakon yayi wani abu,ko bata ranshi kawai sai yy murmushi yana shafa saman kuncin sa,kana ya kuma maimata mata,I really luv u”. Ba da wasa ba,Zan Aureki kod…Kuma wanka masa wani bahagon marin tayi,kamin ta fara mgna a zafafe,don itama batasan ta iyashi ba,Kai wani irin yaro ne,ni sa’ar kace? Kana kanin bayana kaxo kana cemun Kanaso na! Hauka kakeyi ne? Mgnar take jero su dika a one sentence,kamin Hauwa taxo tayi saurin jan Ta suka nufi Class… Taana mmkin Tsaurin hali irin na hafsa da har ta iya marin Aliyou Haidar”.
Sukam abokansa,wani iri kiyayayyan Hafsane ya lullubesu,duk da basa da Halin nunawa sbd Gaba dya idon Aliyou Haidar ya rufe a sonta”.
Tun daga wannan Rana Baki daya Class din suka chanja mata banda Hauwa bb mai kallon ta,run da ta taba Shalelen su abunso Aliyou Haidar”. Kowa Tsaksnin ta dashi sai harara da yada mgna”. A wannan satin kam su Rufaida har a salinta sai da Suka kwakwulo dabata san ta inda suka sani ba…
Kinsan mene Ne Naima? Aa sai kin fada rufaida,wlh Shi idan akace maka mutum Ďan kauyen Bafulkatani ne,tom baya taba wayewa har ya mutu,don sai yy shekara arbain a binni kamin nan”. Nan suka kwashe Da dariya har suna tuntsirawa…shiru Hafsat tayi kana ta wuce su batare da tace”Komai ba”.
Tundaga Ranan Kaman ance Aliyou Haidar ya kuma takura mata da damu ne,Don Tun tana marin shi har ta daina tabarsa da halinsa don ta lura shi irin mutanen nan ne idan suna son abu,idon su rufewa yake sukoma kaman mahaukata”. Hakan yasata rabuwa dashi duk wacce hanya da xai hada su bata son haduwar tasu”.
A haka dai yau dadi gobe akasin hakan….a haka take ta gungurawa tana kokarin kauce mawa Aliyou da nacin shi”.
Ammie Kin san ina son Hafsan sosai kuwa?
Allah dai Haidar? Ehhh Ammie yabata amsa tana kokarin Hada masa Ruwar wanka….Ammie Tom tayaya Daddy Zai amince mun na Aureta?
Tofah Aliyou Wannan wani irin mgna ce haka? Na dauka dai Kawai Abun na ka schl friend ship ne… Aa Ammie nifah Auren ta xanyi. Ganin Abun nashi yana shirin samata Rigima,yasata cewa”Tom shikenan Haidar,allah ya nuna mun lokaci…Sosai yaji dadin mgnar Ammien nashi,Don haka ne A washegari Har ita hafsan sai da ya samu ya fade mata abun da Ammien shi tace,amma sai ta mayar dashi Sakarai”. Ana haka sukayi hutu,wanda sosai Hafsa taji dadin hakan,don ta huta Da damun Haidar….Sai dai Hauwa da take zuwa gida suna taba zumunci”.
****************************
Hafsa…Hafsa…. Inna ce tayo kirar diyar nata,wanda yasa Hafsa Saurin fitowa tana amsa kirar Innan nata daga wajen soron gidan nasu”. Kicibus sukayi da Shi hannun ta dauke da manjan da Inna ta aiketa sayowa….aiko sam bata san lokacin da Ta juye masa manjan a jikin shi ba”. Gaba daya yar farar shaddan tasa ta rine da manja dama ana kafulle an shigo binni daga ruga”. A zuciye ya daga hannun shi yana shirin wanketa da mari,aiko nan Yy saurin rike hannun nasa,kana suka hau kallon kallo”. Cike da xafin murya Maccido ya kalli Aliyou Haidar yana cewa”kai wanene? Da xan hukunta kanwata kaxo ka rike ni”.
.murmushi Aliyu yy kana yace mai sonta! Mene? Ehh yanda kaji”.
Zaro ido hafsa tayi,tana ta’ajibi yaakayi Ya taho gidan su,har ya sani….muryar Umar ne taji yana cewa”Aliyou yayan mu ne,xo mu tafi laifi tayi masa,shigo ka gaida inna!
Jin ance ya taho ya gaida inna yasa shi kutsa kansa cikin soron gidan nasu da yakasance tun daga farkon sa har karshen sa ginin jar kasa.
Tab dijammm Hafsa,yaudara takkyi dama? Budan bakin maccido abun da yace mata kenan,wanda cikin sauri tayi wajen gidan don tsoron xuciya irin na Maccido”.
Mmn teddy🧸⁸² ⁸³