MISBAH BOOK 3 CHAPTER 6 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 6 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

murya kasa-kasa sai dai fa dakakkiyar murya

wadda ba wasa ciki ta ce,

“Deeni ina son wannan daddadar rayuwar

tamu ta ci gaba, ina son wannan wutar soyayyar da

kaunar ta ci gaba da ruruwa a zukatammu, ina son

wannan shauki ya tabbata a tsakaninmu wannan

fahimta da jin dadin juna da muke ya ci gaba HAR ABADA

“Deeni ba na fatan abin da zai taba raba ni da

kai, kana fahimtar me nake fadi ko?”

Ya sa hannu yana shafarta tare da jin sabon

shaukin son ta a ransa ya ce,

“Ni ma abin da nake

so ke nan Bahijja.

Tsam ta mike ta tsame jikinta ta fita, tare da

goge jikinta ta daura towel din tana fadin,

“ina son

ka dinga tuna haka kullum, kuma kamar yadda

kullum ba a shiga tsakaninka da duk wani effort

dinka a rayuwa, ni mana roki wannan alfarmar,

karka shiga tsakanina da duk wani Hakkina.

Bata saurari amsarsa ba ta fita ta nufi daki, ya

bita da ido ya yi murmushi tare da fadin, “Allah ya

bar min Misbah na.

.” nan shi ma ya mike ya fita ya

ga determination a idonta da actions dinta.

Bayan ya kimtsa ya same ta wurin da suka saba

cin abinci, sun ci abincin sama-sama suna yi wa

juna kallon kallo kowa da abin da ke ransa, shi dai

bai son tashin hankali da ita don ya san a dane take

dan haka ya danne tashi zuciyar ya kyale ta.

Alkawarin cin abinci da wurin kwana ba sa raba

shi, duk runtsi duk fushin da suke da juna, in daya ya hau daya na sauka, don haka da suka gama cin

abincin suka dare gado tare da ba wa juna baya,

duk da shauki da son da ke cin su a zuci, da jiki

kowa ya danne, ya ba wa dan uwansa baya,

dukkansu kowa da irin tunanin dake zuciyarsa da

hakan har barci ya yi gaba da su.

Washe gari Farida ta yi sammako ta shirya ta

nufo side din su Bahijja sabod ta kudiri aniya a yau

sai ta yi magana da Deeni, sai kuma ta tada masa

da tsohuwar soyayyarsu. Wanda ta tabbatar daga

shi har ita ba su manta ba, sai dai kash, wai

hausawa suka ce, “in sammako ka yi wani a hanya ya kwana’ don kuwa ta tarar da Bahija da Deeni

sun fice a gidan, a bakin Baba Audi take jin wai

sun fita tun karfe bakwai da motar Bahija, don

kuwa ta ga motar Deeni a gida shi ya sa ta yi

tunanin yana nan, wannan lamari. ba karamin

bakanta ran Farida ya yi ba.

Bahijja tana nufin za ta dakile

duk wani

kokarinta da take yi na ganin ta cimma burinita

kan Deeni, abin da ya kawo la garin Lagos ke nan

na musamman, “ba zai yiyu ba, ki ci gaba yanzu.

“Idan har kika kifar min da duk wani kokarina

to, nasan ta inda zan bullo maki. Wanda ina da

tabbas a kan wannan kudirin, a duk randa kuwa na

shigo gidan Deeni nawa ne, aronsa kaddararki ya

baki na wani lokaci Deeni nawane ni kadai.

Baba Audi ta katse ta “Hajiya ta bar sallahu in

kuna son zaga gari ga driver da mota zai kai ku duk

inda kuke so, sannan ga karin kumallo an shirya

muku.

Ta kalli Baba Audi, ta ji kamar ta falla mata

mari don haushi ta ce,

“ba mu da bukatar zuwa ko

ina break fast kuwa ko ba a mana tayi ba mun san

hanyar inda za mu samu, don mu ba baki ba ne,

nan gidanmu ne da ni da yarana.”

Baba Audi dai bata ce mata kala ba, ta tafi ta barta wurin. Bayan gama karyawarsu, yara suka rikice

mata, su fa yawo za su fita, dole ta bar su driver, ya

Fita da su, yayinda ta zauna ita daya a gidan, ta kai

Ta kawo tana saka wa tana kwancewa, ta wuni cikin

takaici da bacin rai

Lokacin da Bahijja tayi wa Deeni tayin fita a

motarta bai yi mata musu ba saboda ba ya son

fitina da tashin hankali, hakanan ta sha yi masa

hakuri da daga masa kafa a kan lamura da dama,

wannan ne karo na farko da ta tada kayar baya.

kiris take nema su yi tashim hankali, shi kuwa ba

zai bye mata ba, haka nan ya fahimci (cars dinta,

sai dai da la san me ke zucivarsa da bata daga

hankali ba, ita kadai dim nan ta ishe shi rayuwar, ha

shi da kuma niyya ko sha’ awar kara aure, ba Farida

ba ma ko da wala mace ce sai dai fa in ta kai shi

bango zai nona mata ba tsoronta yake ko shakkarta

ba, amma ya sa mata ido ya ga gudun ruwanta.

Yana kallon ta tana tuki tana wani cim magani

kamar mai fada da motar, ya kalle ta ya yi

murmushi, mata da kishi, amma shi ya tabbatar

kishin Bahijja daban yake da na sauran mata. Allai

ya sani Misbah na ce farin cikina kuma SANYIN

IDANIYATA “duk yadda Kika kai ga bata min rai,

wannan soy ayyar ba za ta taha gogewa a zaciyata

ba, Allah ya ha ki wata baiwa da kullum in na kalle

ki kara sonki nake, kara burge mi kike, addu ‘a nis da

fatana, Allab ya sa ki haifa min yarinya irinki.

Allah ya min baiwa ya kuma azurta ni da samun

irinki Mishah na. Allah ya bar mu tare har karshen

rayuwa.”

A jikinta ta dinga jin idon Deeni na kanta.

hakan ya sa ta juyo la zuba masa manayan

idanuwanta, tuni ya ji tana tsuma shi da kallonta.

ya vi saurin dage kai, ita ma ta dage kai har suka

isa gidan gonar nasa, ba wanda ya ce wa kowa kala

har sai da ya sauka, ta dage kai ba tare da tana

kallonsa ba ta ce,

*Zan dawo in dauke ka, karle biyar kafin nan ni

ma na gama da asibiti, ina fata za ka jya jira na, in

kuma kana hanzari ka koma gida ne to.

Ya yi murshi yadda take maganar ya ba shi

darya ya ce,

*My Misbah, ba ki sun sauka gida

kuwa, me zan je in yi tun da sarauniyar zuciyata ba

ta gidan,

a dadim gidan sai da Misbah ciki,

wannan gata da kike min, a kai ni wurin aiki a

dauko mi, ai jin dadi ne, ba ko wane namiji ke da

wannan galar ba, sai ni mai gimbiya Misbah.

Ta juyo ta mai wannan kallon nata na isa da

kasaita, la juya ta ja mota ta tali, ya jima a tsaye a

wurin yana kallonta yayin da wannan kallon ya

tsaya masa a zuciya. Lumshe ido ya yi yana jin son

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *