RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 26 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 26 BY HALIMA K/MASHI

 

 

 

Amna ta ce, “in Na yi magana sai ya ce shi bai san ya ce ba, mantuwa ce

“Tabdi yarinya ta tsare muku Maman Jafar

bacci ku ka yi ne haka! In fada miki ni nan ba ni da kishiya, amma na yi kishiyoyin waje. Da baban su Afra kwararren dan neman mata ne, ni ma farkon haduwarmu da haka ya zo na nuna mishi ni fa ina da

tarbiyya, shine ya Billo da batun aure, da yake ina sonshi ban Qi ba na amince.

In fada miki anyi aure muna ta soyayya daga

samun cikin Afra sai wulakanci ya shiga. Ai ko ya shiga neman matanshi har ba ya shakka in sani. Ina haihuwa Yayata ta hadi ni da wata mai saida maganin mata a Kaduna. Kafin in yi arba’in ta yi min gyara tare da shawarwari yanda ya kamata.Ranar ko da ya dawo ban da tona sirrin aure babu

kyau da na ba ki labarin yanda muka kwashe kin sha dariya.

Mutum ya koma tamkar soko, ko inCe bawana, Ni ina sonsa tsakani da Allah haka bai sa na

wulakanta shi ba. Cikin hikima dubara da addu’a Allah ya taimake ni ya bar duk wata macen waje,sannan in na yi magana yana karba, duk abin da nace ina so in yana da hali yana mana. Daraja da Kima

ta ta dawo idanunsa, Ke shawararsa wadda ba ta shafe ni ba ma sai ya kawo min ita. Ni ko in ba shi iya fahimta ta sakamakon ina karance-karance

littafan Hausa ina samun kaifin basira”Amna ta tabe baki

“Ni fa duk wannan

karance-karancen na Hausa bana yin su, gara English Novel, sannan wadannan abubuwan ban yarda da su

ba. Ga likitoci kullum suna gargadin shaye-shaye da matse-matsen nan”

Maman Afra ta ce,

“Ina mamakin irinku”yan

gayu masu karatun al’adun wasu ku bar naku.

Hikima da basira ai tanaga marubutanmu cikin

hikima da basira, kuma kin san wannan matsalar da ki ke fadì da kina karatun da tuni kin magance ta batare da kowa ya sani ba kuma game da kayan gyaran

jikin nan, sai dai in ba ki nemi ingantattu ba kuma basu baki shawara daga masu saida kayan ba. Kin san cewa ni ma na yi irin abin da ki ka yi?”Amna ta tabe baki,

“Ni fa ban iya wannan

aikin, ko da aurena ban sha sosai ba, ko yanzu na fi ga dan irin na waje din nan Maman Afra ta ce,Ai wannan ba su zama a

jiki in za ki dawo hanya ki dawo kawai”

Amna ta ce,Mu bar wannan zancen, ni muyi wanda nike miki

Maman Afra ta ce,

“Mun bari. Amma in kin

canza shawara kina iya tuntuba ta zan kuma hada ki

da ita. Don kullum ina fada ma mata sai sun gyara zasu ga daidai Amna ta ce,

“Yanzun ni ya zan magance

wannan matsalar, yanzu haka fa ita tana Abuja gaba daya mu sai dai ya zo ya yi mana kwana daidai don ita Karamarmu ma da yake ya maida ta sakara, sai yayi zuwa ka ga bai kwana gurinta ba

Maman Afra ta sheke da dariya tareda fadin,

“Lallai na jinjina ma wanna Nafisar, har ta burgeni” Amna ta ce

“To mene ne abin dariya a nan.

Maimakon ki taya ni bakin ciki miji yana tare da ni,kuma yana ambatar kishiya. Akwai ranar da har kuka na yi saboda kiran sunan Nafisan, na yi wai sai ya ce

min wai sun yi fada ne shine abin yake ransa

Maman Afra ta sake shekewa da dariya har

da kwalla. Amna ta mike za ta tafi tana fadin,

“Tunda abin dariya ne bari kawai in tafi”

“. Ta yi maganar cikin fushi.

Maman Afra ta riko ta,

“Tsaya ki ji kawata,

rainin hankalin da namiji nike yi wa dariya. Ya rasa lokacin da zai tuna sun yi fada da ita sai irin wannan lokacin mai tsada a gurinki?”

Maman Afra ta dafa kafadar Amna,

“Yi tunani da kyau ki gani. Yarinar nan tana matukar gyara jikinta, inda za ki tambayi sauran kishiyoyinki

Kila su ma yana kiran sunanta a gurinsu. Ai bai san lokacin da zai yi barin ba

Amna ta ce,

“Kin ganta ne, busasshiya. Na fi

ta komai fa! Har na fara zargin ko ta yi masa asiri ne” ta ce,

“Ba wani asiri in fada

miki isassun mata yanzun ba sa zuwa gurin bokaye, kayan gyara suke siya suna gyara jikinsu, ki ga mace

birtintin amma ta isa’ a gurin miji, kuma ita ma har bushewarta ta fi ku a idonshi. Shawara ta daya ku dage kawai ki gyara, amma fa tushi babu inda zai kaiki”

Ita dai Amna har ta tafi ba ta gamsu ba. Cikin dare nakuda ta kama Aliya, ranar

asabar ce Shatima yana dakin Amna, Aliyar ta yi ta kiran layinshi ba a daga ba. Haka ma layin Amna tayi ta kira, wayoyin duk suna falo su kuma suna cikin

daki, sam ba su ji kiran ba. Karfe biyar na asubahi Aliya ta haifo danta santalele shi ma mai kama da

Babansa. Cikin bacci Shatima ya yi mafarki wai Aliya ta haihu. Da sauri ya farka, falo ya nufa ya ciro

wayarsa a caji da nufin kiranta tunda likita yace

lallai tana fara nakuda a kai ta asibiti, domin ta gota lokacin da ake saka ran za ta haihu. Adadin kiran daya gani nata a wayarsa shine ya sa shi ficewa daga

dakin babu shiri, ya nufi sashen Aliyar, Ya same ta tana numfarfashi a gefe ga da

yana ta tsala kuka. Da alama ba ta jima da haihuwar ba. Ya kai hannu ya kama ta tare da fadin, “Tashi”Ta ce.

“Ka bani reza a cikin can in fara yanke

mishi cibiya”

Ya dubo ya ba ta, ta yanke cibin, sannan ta ce

ya ba ta zani. Ta nannade yaron, sannan ta ce ya kwantar da shi. Ta ce ya taimaka mata ta shiga wanka. Ya tara mata ruwan zafi ta shiga wanka, layin Amna ya kira da wayar Aliya, ba ta daga ba ya

Nufi dakin da sauri ya tashe ta, ya fada mata

haihuwar Aliya.Juyi ta yi tar da fadin, Allah ya raya Ta maida kai ta kwanta.

Yace Ki tashi ki taimaka mata’ Amna ta ce, “Me ni gaskiya ba zan iya zuwa wani taimako ba Ya ce, “Ita kadai fa ta haihuTa ce, “Ina asibiti ne Can ya kamata ka kai ta Ya nufi dakin Salma da sauri, ya taso ta, ya

“ce ta zo ta taimaka wa Aliya. Suna shiga suka samu° Aliyar zaune tana goge jiki, ta fito wanka. Salma ta ce, “Sannu Anty Ya nuna mata gurin jinin, “Ki gyara nan  Salma ta nufi gurin zuciyarta ta tashi, amma

haka ta daure ta kwashe ta kulle uwar a ledar da Aliyar ta ce ta dauko a store, ta goge ko ina tsaf da Detol sannan ta fesa turaren daki; ta koma dakinta zuciyarta a tashe, ta shiga ta yi wanka, sannan ta yi sallah,”Da safe Shatima ya dauki maijego da danta ya kai su asibiti don likita ya duba lafiyarsu. A ranar

– dangin Aliya suka cika gidan daga Zaria, Amna sai da ta tashi fita zuwa shago sannan ta shiga don yi wa

‘Aliya barka. Kusan tunda take a gidan wannan ne karo na farko da ta shiga gurin Aliya, gara ma gurin

HMmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *