UKU BALA’I CHAPTER 8

UKU BALA’I CHAPTER 8

                    Www.bankinhausanovels.com.ng 

Juyi kawai yake yi saman faffaɗar gadonsa da ya kusan cinye rabin dakin numfashi yake ja a hankali zuciyarsa na wani irin kartawa.

A hankali ya mike yana kai kawo a tsakiyar dakin gumi  mai tsananin zafi sai tsantsafo masa yake yi a goshi lokaci-lokaci yake runtse idanuwansa ba abin da yake hangowa sai Huzaif da ya rike hannun Mariya sosai yaji zuciyarsa na zafi da zugi wani katon abu mai nauyi yaji ya zo masa zuciya ya tsaya cak!.

Bai san abin dake damun sa ba a daidai wannan lokacin zuciyarsa sosai take son firgita masa tunani game da Mariya sosai yake jin wani fili mai girma ya buɗe a zuciyarsa ba abin dake yada zango a cikin sa sai lamarin Mariya sosai yake hangowa a ranar da ya fara ganinta bayan shekaru hudu da suka shuɗe ba tare da ya sanyata a idanuwansa ba.

Runtse idanuwansa ya sake yi a karo na ba adadi kafin ya shiga taka kafafuwansa a hankali yana mai isa toilet din sa ruwa ya watsa domin ko zai samu sa’ida a zuciyarsa dama gangar jikinsa gabadaya.

Yana cikin goge sumar kansa da shawul wayarsa dake yashe gefen gadonsa ta dau Ringing ya tsine fuska yayi kafin ya dubi wayar cikin halin-ko-in-kula yana mai jan guntun tsaki sai da wayar ta tsinke sau biyu kafin a na uku ya kokarta zuwa ya dauka new number ga ni kuma bata najeriya bace shiru yayi yana tunanin inda number din ta fito amma ya kasa cankowa yayi kamar zai katse sai wata zuciyarsa ta bashi damar dagawa a hankali ya latsa madannin yana kaiwa kunnansa mai makon ya rike da hannunsa sai ya ƙi sai ya makale ta a kafaɗarsa.

“Dr.Karami”.

Yaji muryar ta doki dodon kunnuwansa da sauri ya yarda shawul din dake hannunsa ya dago wayar daga kunnansa yana duba number din sosai mamakin murya da yaji yake yi sosai gabansa ya buga kadan don yasan shi mai laifi ne sau ba adadi yana kiransa yana kin dauka wanda bai san dalilin ba a hankali ya ciji laɓɓansa yana mai da wayar kunnansa.

“Uhmm!”.

Ya fadi da dan sauti a muryarsa.

“Ka kyauta kaji Dr.Karami…”.

Runtse idanu yayi kafun ya motsa laɓɓansa.

“Please Sorry My Dr.Vijay kasan dai ba haka kawai zan shan yaka ba dole sai da dalili”.

“Ban yarda ba kawai kace mani wulakanci ne ya tashi ko abin da ba halayyakar baka…wai shin ma me ya zaunar da kai ki dawo wa aiki ne har yanzu 3weeks left fa haba mana ya kamata ace duk abin da kake yi izuwa wannan lokaci ka kammala shi ka dawo”.

Runtse idanu Dr.Karami yayi yana jin yarda zuciyarsa ke sake hautsinewa da wani irin yanayi mai girman gaske na tashin hankali ba ya zaton zai koma aiki ba tare da komai ya daidai ta ba, ba ya zaton zai koma Delhi a yanayin da yake a yanzu ko yace zai koma to tabbas karya yayi domin kuwa ko yaje din ganga jikinsa ne kawai zata je can din amma zuciyarsa da ruhinsa suna nan nisawa yayi kafin ya fesar da huci mai zafi.

“Ina cikin wani yanayi ne mai matukar girma Dr.Vijay a halin da ake ciki yanzu ban san ranar dawowa ta aiki ba in har ba wai komai ya zama Normal bane”.

“What?!. Me kake kokarin cewa dani Dr.Karami anya kana hayyacin ka kuwa aikin naka kake mai dawa haka kana masa halin ko in kula meye ya same ka har da kake wannan ikirarin haka ya kamata gaskiya ka sauya tunani tun wuri kuma ya kamata ace ka dawo aiki at this time domin ana bukata ka”.

“Ba zan iya ba”.

“Kan wani dalilin?”.

“Kawai dai ba zan iya dawowa a yanzu ba domin akwai abu mai girma da nake so ya zama normal in har ba wai ya zama normal din bane to gaskiya bana tunanin ko na dawo zan iya wani abun kirki”.

STORY CONTINUES BELOW

“Shikenan Allah ya kyauta”.

Abin da Dr.Vijay ya fadi kenan da damuwa a muryarsa shi kansa Dr.Karami ya lura da haka sai dai ba yarda zai yi a matakin da yake a yanzu ba ya tunanin zai iya komawa Delhi sauke wayar yayi bayan sun yi Sallama jiki a mace ya zube bakin gadon kamar wani kayan wanki hannunsa ya saka ya dafe kansa da yake jin yana yi masa wata irin sarawa kamar zai rabe gida biyu runtse idanuwansa yayi kafin ya buɗe su a hankali.

Sosai yake jin zuciyarsa na sonta sosai yake ji duk jikinsa na aiki ne da sosai yake jin zuciyarsa nayi mata ya jima yana karyata kansa akan cewa son ta yake yi ya jima yana jin zuciyarsa na sanar dashi amma ya ki ansar lamarin sosai yayi kunnan uwar shegu da komai ba tun yau ba lokaci mai tsayi da ya shuɗe zuciyarsa tana kawo masa abubuwa masu matukar girma a game da ita amma bai yi AMANNA ba.

Bai san ya zai yi ba bai san ya zai fuskance ta da wannan lamarin ba sosai yake jin wani iri a zuciyarsa sosai yake hango rashin nasara baya tunanin in ya tunkare ta da wannan lamarin zata ansheshi har ta bashi fili a zuciyarta.

Fushi take yi dashi fushi na sosai da sosai bai san mai yasa ba ya sani har da laifin sa laifin sa mai girma ne a gareta wanda bai san ya zai wanke kansa ba a idanuwanta ta ki yarda dashi taki bashi lokacin ta su zanta gudun sa take yi sosai ta ke kin haɗa ko da hanya dashi ne sosai yake bibiyarta amma bata bashi lokaci yayi iya yin sa saboda ita ya baro aikin sa saboda ita ya zauna har tsayin wannan lokacin tun da ya fara aiki bai taba zuwa ya zauna a kasar nan ba mai tsayi sai a dalilinta a dalilinta komai nashi yake canzawa wanda bai yi zato ko tsammani ba zuciyarsa ta dade da narkewa da duk wani lamarinta ruhinsa ya jima da daskarewa da duk wani abu nata kwanyarsa ta jima da buɗe fili mai girma na tunaninta.

A tunaninsa ba ta kai matsayin da zai so taba, a tunaninsa ba ta kai matsayin da zai tsaya ya nuna yana son taba, a shekarunsa gani yake yi kamar ba su dace ba, gani yake yi kamar sun bambanta a wajaje da dama sai dai wani abu da yake kokarin ruguza duk wani tunaninsa a lokaci kankani ganin yarda ta canza komai na ta ya sauya ta koma masa mace mai ansa sunanta mace ta ko wani fanni sosai yake ji a ransa yayi wauta a can baya tunaninsa bai yi masa adalci ba da ya tunano masa rashin dacewa tsakaninsa da ita sai yau ya kara tabbatar wa SO SHU’UMI NE so ba ruwansa da girma ko yarinta a ko wata zuciya zai iya sauka ya buɗe filinsa yayi yarda yake so da zuciyar.

Numfashi ya ja mai tauri kafin ya fesar da huci mai zafi a hankali ya mike ya shiga shiryawa cikin riga da wando rigar mai dogon hanni Milk-colour sai blue din wando mai haske kayan sun yi matukar ansarsa suka kara fito da tsarin halittarsa ta mazantaka kallo daya zakayi masa ka gane Allah yayi halittar ɗa namiji a wajan mai ji da kansa ta ko wani fanni.

Sosai ya feshe cikin sa da turare mai dadin kamshi dakin kansa sai da ya dauki kamshi na ban mamaki kamar anyi barinsa.

Bayan ya kammala ya dauki Key din motarsa da wayarsa ya fice can parking Space ya nufa ya fiddo motarsa sai da ya gama kare mata kallo kafin ya buɗe ya shiga yayi mata key a hankali ya ja ta ya fice daga harabar gidan ya cilla titi.

London Streat unguwar ya nufa in da gidan mahaifiyarsa yake tuki yake yi a hankali a jikinsa yake ji kamar bashi da lafiya sosai yake jin ko wani sashi na jikinsa kamar an doddoke masa cikin wannan yanayin ya isa gidan Horn yayi mai gadi ya buɗe masa Get Babban gida ne sosai kallo daya zaka yi masa kasan masu gidan akwai farcen susa ko wani sashi ka kalla tsaf yake Parking yayi ya fito bayan sun gaisa da Malam Audu mai gadi sannan ya nufa hanyar Falo din da sallama a bakin sa ya tura ya shiga ba kowa a falon sai Tv dake ta faman aiki yawatawa ya shiga yi da idanuwansa cikin falon da yake ta faman tashin kamshin turaren wuta a hankali ya ja numfashi yana mai sakin yak’e kamar wanda akayi wa dole da sauri yayi hanyar dakin mahaifiyar tasa don ya tabbata tana ciki.

STORY CONTINUES BELOW

Zaune ya tadda ita bayan yayi mata sallama ta ansa shi fuskarta da murmushi mai girma kallo daya zakayi mata ka tabbatar da ita ce mahaifiyar tasa suna kama sosai sai dai shi Dr.Karami ya fita hasken fata saboda hasken fatar mahaifinsa ya biyo kama ce dai ya dauko ta uwa sak!

A hankali ya isa gareta shi ma fuskarsa da murmushi kan salayar da take kai ya samu guri ya zauna ya na daura kansa a kafadarta shafar kansa tayi kafin ta rufe littafin Husnul-Muslim dake hannunta.

“My Son ya akayi ne?”.

Margaya kai yayi kamar wani karamin yaro kafin ya dago kansa ya dubeta.

“Ba komai Mami kawai dai yau bana jin dadin jikin nawa ne sosai”.

Zaro idanu waje tayi kafin ta furta.

“Yaa Allah da fatan dai ba wani abu bane yake damun ka”.

Girgiza kai kawai yayi kafun ya mai da kan nasa jikin kafadarta.

Wani numfashi taja mai kwari kafin ta dubi Dr.Karami sosai fuskarta da wani irin yanayi mai girma na damuwa.

“Hisham”.

Ta furta kamar bata so ba da hanzari ya mike yana dubanta jin ta ambaci sunansa sak! Wanda ya manta rabon da yaji ta kira shi da hakan sosai yake kallon ta jikinsa da wani irin yanayi gabansa ya ji yana bugawa a hankali.

Kau da kai tayi daga kallonsa.

“Na fara gajiya Hisham abin dai da baka so shi zan fadi ban san adadin lokutan da nake zaunar dakai muna irin wannan maganar ba ban san adadin lokacin da na dauka wannan lamarin na damuna ba abin ya fara shanlake tunani tun kafin rasuwar mahaifinka ake abu daya amma har yau babu wani lamari to maganar gaskiya in har ba so kake yi nima na mutu da wannan burin ba to ya kamata ace kayi wani abu akai ba wai takura maka nake yi ba abin da zai kuftar da kai daga fadawa halaka nake gujewa ba wai ina zargin ka bane da komai Hisham amma ya kamata ace a irin wannan shekarun naka yaci ace kana da mata har da ‘ya’ya duk da dai komai na rayuwar nan sai Allah ya sa zai tabbata san nan yake tabbata”.

Shiru yayi kansa na wani irin juya masa gabadaya yake jin komai na kara hargitse masa musamman yanayin da ya ga mahaifiyarsa a ciki a yau din nan ya san ta kai makura amma shi kam bai san ya zai yi akan maganar auren nan har yanzu bai jin akwai wacce zai iya zama da ita a filin duniyar nan a matsayin mata ba shi akaran kansa yana mamakin rashin aurensa bai san dalili ba bai san mai yasa sam a shekarun da ya kwashe na girman sa bai ji yana da muradin aure ba domin zuciyarsa har yau bai ji ta kamu da son wata ‘ya mace ba…

Shiru yayi jin zuciyarsa na karyatashi da abin da yake fadi wanda ya tabbata a yanayin da yake ciki yanzu komai ya sauya komai ya canza sosai yake jin so a cikin zuciyarsa son ma akan wanda bai taba tsammani ba.

“Hisham kai kadai ne ɗan mu a duniyar nan kai kadai Allah ya ba mu duk da muna son ‘ya’ya haka muka hakura da hukuncin Allah kai ya kamata ka share mana hawaye na ‘ya’ya bila adadin amma kuma ya kamata ace kai a bangaren ka kayi aure ka hayayyafa domin Ubangiji yayi alfahari da kai nima nayi alfahari da kai mu ba muyi ba ya kamata ace kai kayi Hisham a maganar gaskiya shekarun sun kai matakin da ya dace ace ka ajje iyali in har ba so kake yi ka koma ga mahaliccin ka a haka ba ba abinda ka rasa kana da arzuki daidai gwargwado kana da aikin yi ba rashin muhalli kana da lafiyarka ko mace fiye da daya Hisham kana da halin riketa to don Allah ka duba Hisham ba wai takura maka nake yi ba a,a so nake yi kai ma ace ko ka bar duniya to ka bar wanda za a gani ace naka ne wanda hakan ba zai sa a manta da kai ba a lokaci kankani”.

Dago kai yayi ya dube ta da damuwa kafin ya saki fara’a.

“Mami na! Shikenan naji in Allah ya yarda ba zan baki kunya ba a wannan lokacin kin san mi ma kawai ki nemo min matar aure kawai…”.

STORY CONTINUES BELOW

Wani kallo ta watsa masa.

“Ban yarda ba ai bani zan zauna maka da matar ba don haka da kanka zaka zaɓo matar auren ka don haka maza tashi ka bani waje na baka lokaci kayi abin da ya dace”.

Kokarin kwanciya yake yi da dariya a fuskarsa ta dube shi.

“Me zakayi kasan Allah ba yarda za ayi kana katoto da kai ka karasa ni maza tafi gidan ka kaje can ka kwanta ba wai ka zo nan ka isheni ba…wai shin sai yaushe zaka koma wajan aikin ka ne Hisham lokaci fa naja kuma nasan za su ne meka ban son abin da zai zo ana dana sani”.

“Na kusan komawa”.

Ya fadi yana mai mikewa domin a halin da yake yanzu sam bai so ayi masa maganar kin nan nasa sam ba ya gabansa wannan tashin hankalin da yake ciki ya ishe shi Sallama yayi wa Mahaifiyar tasa yayi tafiyarsa ita kanta ta lura da sauyin ɗan nata a lokaci guda sai dai fatan ta Allah yasa lafiya littafin Husnul Muslmin din ta dauƙa ta cigaba da dubawa.

*******

Ya tsine fuska ta shiga yi ganin wanda yake kiranta sai da ta gama kare masa kallo kafun ta isa gareshi shikuwa sai faman yashe baki yake yi kamar wanda aka ce an bashi ita kyauta.

Gaidashi tayi ba tare da nuna masa komai ba ta lura da Dr.Aqeel sosai yake son bata matsala a duk lamarinta sosai yake so yake haifar mata da tashin hankali lokaci da yawa yana zuwa amma sai yaji labarin Dr.Karami ya zo sannan zai fara mata zarya kamar wacce yake bi bashi a cikin satikan nan da Dr.Karami yayi Dr.Aqeel ya zo yafi a lissafa ta rasa mai yake nufi da haka sosai take hango kamar akwai wata manufa ta daban a zuciyarsa duk da ya nuna yana sonta din ta yarda amma ita halayensa ne ba su mata ba ya fiye zafin rai da mai da karamin abu babba ita kuma abin da ta ki jini a filin duniyarta zafin rai da sauri hassala…

“Mariya ban san ta ya ya zan billo miki ba iyakar bakin kokarina nayi amma abin har yanzu dai ba canji ya kamata izuwa wannan lokaci kin bani matsaya domin ni dai da gaske nake ba karya nake miki ba ni ba karamin yaro bane da za ai ta kai kawo akan abin da bai fi shan ruwa wuya ba”.

In akwai abin da ta tsana a filin duniyar Dr.Aqeel to rashin iya kalamai sam magana yake yi kamar saukar markaɗe ga shi murya ba kadan ba gabadaya sai ta cika mata kai ba wai bata son sa bane a,a sosai take jin sa a ranta amma ba ta tunanin za ta iya zama dashi a inuwa daya.

“Kice wani abu mana”.

Dago idanuwanta tayi ta dubeshi sosai Dr.Aqeel ba shi da makusa ko ta miskala zarratin amma bata san mai yasa zuciyarta har zuwa wannan lokaci ta kasa amanna dashi ba.

Horn din da ya doki kunnuwansu ya sanya su gabadaya suka juya kallo daya Mariya tayi wa motar ta gane wanene wani irin bugawa taji gabanta yayi da karfi idanuwanta suka yo waje wani matsanancin tsoro taji ya ziyarce ta nan ta shiga kallon kallo tsakanin Dr.Aqeel da Motar Dr.Karami yanayin da Dr.Aqeel ya ganta aciki ya tabbatar masa da akwai wani abu domin shidai bai gane waye ma a cikin motar ba.

Numfashi ta shiga ja a hankali ji take yi kamar ta kwasa da gudu sam bata so ace sun hadu da juna domin rabon dasu tsaya a tsakaninsu tun ranar da rigima ta kacame tsakanin Dr.Karami da Huzaif shikenan ta shiga wasan buya ko ya zo wajan ta sai ta san yarda tayi ta guje masa.

“Zan shiga gida Sai anjima”.

Mariya ta fadi muryarta na rawa da sauri Dr.Aqeel ya dubeta cikin mamaki da tuhuma kafin ya motsa laɓɓansa yana cizansu.

STORY CONTINUES BELOW

“Idan kika yi mani haka kina tunanin kinyi mani Adalci kenan Mariya me yasa wai baki son tsayawa ki fuskanci in da na dosa ne mai yasa kullu yau min in na zo wajanki baki taba bani lokacin ki…”.

Numfashi mai zafi ya fesar kafin ya sake kallon motar wacce har zuwa wannan lokacin ba alamun za a buɗe ta.

“Ina son ki Mariya so mai tsanani kuma na san ke ma kina sona ko baki so ni dan komai kin so ni taimako…”.

Ware idanu tayi sosai tana duban Dr.Aqeel da take jin kalamansa na saukar mata kamar aradu aka jin in da ya dosa ya sanyata daga masa hannu.

“Ban yi zaton haka daga gareka ba ban taba tsammanin zan ji haka daga gareka b Dr.Aqeel me kake son ce mani kana nufin ba saboda Allah ka taimaka mani ba ko me kana nufin dama akwai wata manufa a tsakanin taimakon da kayi mani”.

Lokaci guda idanuwansa sukayi ja bacin ranta ya bayyana sosai bakin ta na rawa ta sake dubansa kafin ta kau da kai.

“Kenan ba don Allah kake so na ba kenan dama can kana da wata manufa ta daban a haka kake so na so ka a haka kake so mu zauna inuwa daya da kai a haka kake son ko mun zama ma’aurata ba zaka mance taimakon da kayi mani ko da laifi nayi maka goranta min zaka din ga yi kaico!”.

Ta fadi tana mai dauke kwallar da suka zubo mata a fuska a hankali ta shiga takawa tana barin wajan zuciyarta na wani zafi da raɗaɗi kirjinta take ji yana kartawa kwanyarta na hautsine wa.

Gabanta ya sha cikin matsanancin tashin hankali idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir.

“Mariya me kike nufi da haka mai yasa zaki yi saurin yanke min hukunci akan abin da ba haka bane mai yasa kike kokarin fuskantata a hagunce  na rantse miki da…”.

Da sauri ta daga masa hannu izuwa wannan lokacin idanuwanta sun kawo ruwa.

“Ba abin da zaka ce mani Dr.Aqeel ba maganar da zaka sake fadamin na yarda na sani ni talaka ce wacce bata dashi wacce ubanta ya kawo su asibiti ya gudu ya bar su ba tare da komai ba…”.

Wani murmushi mai ciwo ta saki kafin ta dora da cewa.

“kana da damar fada min komai ko mai kace ban ga laifin ka ba ni ce mai laifi mu muka zo wajan ka mu muka nemi taimako zaka iya fada mana komai amma ka sani a duniyar nan hanyoyin da Allah ya buɗe su da yawa suke domin wani ya zo ya nemi wani abu a wajan dan’uwansa ka sani komai yake faruwa dani da sauran iyayena ba mu muka daurawa kan mu ba ka sani ALKALAMIN ƘADDARA ne ya zana mana kuma ka sani duk wani dangin rai a duniyar nan ba yarda ƙadddararsa bata zuwa masa domin kuwa ba komai bane bawa ke nema ya samu Dr.Aqeel…”.

Runtse idanu tayi jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi a duniyar nan in akwai abin da ta tsana shine ayi mata gori tana jin zafin hakan sosai a ranta shiyasa ta kullacin hakan a ranta cewa duk yarda zatayi rufawa kanta asiri zata yi domin ta lura a duniyar nan ba abin da yafi bakinciki da takaici shine ka nema wajan wani ya dizga ka ko kuma yayi maka bayan idonka ya zo yana zaginka ko yana goranta maka a duniyar nan ba abin da yafi kwanciyar hankali da gujewa wulakanci kamar DOGARO DA KAI.

“Mariya don Allah kiyi hakuri wallahi tallahi ba haka nake nufi”.

“Don Allah Dr.Aqeel ka rabu dani in har ba so kake yi zuciya ta buga ba ka barni haka ka sani ban ga laifin ka ba don ka fadi haka maganar so kuma Dr.Aqeel ka sani ina son ka amma halayenka ne na tsana ba zan boye maka ba a yau na kara gasgata abin da zuciyata ta ɗade tana sanar dani bana tsammanin inuwa daya da kake kwadayin mi zauna a tare zai yuwu”.+

STORY CONTINUES BELOW

Ta karashe tana mai kaucewa tana wucewa da sauri ya shiga kokarin shan gabanta wani kallo tayi masa hakan ya sanyashi tsayawa cak! Yana dubanta har ta karasa cikin sauri-sauri gudu-gudu.

Zubewa ne kawai Dr.Aqeel bai yi ba a kasa domin zuciyarsa yake ji tana wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zata faso kirji ta fito duniyar yaji tana juya masa bai san abin da ya kai shi yin wannan maganar ba bai san mai ya kai shi ba gashi yanzu bakin sa ya yanka masa wuya yankan da bai san ko zai warke ko ba zai warke ba yanayin da ya ga Mariya a ciki ba karamar kiɗima yayi ba a hankali ya fara taka kafafuwansa hannunsa rungume da kansa har isa wajan motarsa ya shiga kafun ya dago ya dubi Motar da tun dazu take tsaye ba tare da mai ita ya fito ba sosai yaji zuciyarsa tana azalzalarsa da ya tsaya ya ga kowa waye amma a halin da yake jin kansa a yanzu ba zai iya ba yana bukatar ya gansa a gida yana bukatar ya kebe kan sa waje daya domin yin tunani da samo mafita da za ta haifa masa da ɗa mai ido.

A hankali yayi wa motar key kafun yayi ribas ya fizge ta da gudu ya bar unguwar zuciyarsa a jagule.

Dr.Karami da zuciya ta kwasoshi tun dazu yana dannewa duk abin da ya wakana yana kallo ya dade yana zargin Dr.Aqeel akwai wani abu a tsakaninsa da Mariya bai gasgata ba sai yau da idanuwansa suka gane masa zuciyarsa yaji tana zafi da wani irin turiri sitiyarin motar ya buga tare da buɗe murfin motar ya fito sai faman  huci yake yi kamar wani kumurci fuskarsa har ta canza launi saboda tsananin bacin rai ya shiga kai wa iska naushi kafin ya ja kakafuwansa zuwa cikin gidan da Sallama ya shiga ba kowa tsakar gida sai muryar Mu’azzam dake tashi cikin kuka  sake sallamar yayi a lokacin Umma ta ansashi kafin ta bashi izini ya iso daga kofar dakin ya tsaya suka gaisa da Umma abin da bai saba yi ba yau yayi shi kansa sai da yaji wani bambara kwai wai namiji da suna Hajara ita kanta Umma sai da tayi mamaki amma ba ta nuna masa ba.

“Mariya na ciki Umma ce ina son ganinta”.

Ya fadi murya a sake amma a zuciyarsa shi kadai ya san abin da yake ji

Mariya dake dunkule waje guda tun dazu dama take jiran tsammani da sauri ta mike ta zauna tana rarraba idanu alamun rashin gaskiya sosai Umma ta shiga dubanta tana karantar yanayinta kafin ta wurga mata harara lokaci guda.

“Tashi ki fice mani daga daki sakayya”.

Rau-rau tayi da idanu kamar zatayi kuka don yarda Umma tayi maganar ya tabbatar zargin da take yi yiwa Dr.Karami laifi tayi shi shi haifar da komai.

“Tashi nace tun kafin na kwaɗe ki wallahi”.

Zabura tayi tana mike tana tura baki gaba har sai da ta ga Umma ta mike sannan tayi saurin ficewa daga cikin dakin bata same shi a tsakar gida ba hakan ya tabbatar mata yana waje a hankali ta fara takawa gabanta na faduwa a har ta isa cikin soron gida tana kokarin ficewa daga cikin sa sam bata lura da mutumin da ta wuce ba sai ji tayi ya kira sunanta a firgice ta waigo tana kokarin kwasa da gudu ya sha gabanta saura kadan ta fada jikinsa runtse idanu tayi jikinta ya shiga rawa sosai ta firgita da yanayin sa a hankali taji yayi gyarar murya.

“Buɗe idanunki”.

Ya fadi ba yabo ba fallasa jin abin da yace ya sanyata buɗe idonta daya tana kallonsa harararta yayi da sauri ta mai da ta rufe kafin ta bude su gabadaya a firgice.

“Ke kina tunanin wannan halin da kikeyi shine mafita a gareki ko a yarda kike a matsayinki na ‘ya mace kina tunanin abin da kike yi mutuncin kine na lura Mariya gabadaya kin canza halayenki ba yarda na san ki a da ba wai har kece kullum baki wajan wannan saurayi ba ki wajan waccan kuna rigima a matsayinki na ‘ya mace anya kuwa bana tunanin wacce ta san mutuncin kanta da darajar ta zata kasance a haka”.

Wata katangar tashin hankali taji ta rikito mata lokaci guda kanta ya shiga sarawa lokaci guda idanuwanta suka kawo kwalla ta shiga dubansa shikuwa nuna wa yayi ko a jikinsa amma can kasar zuciyarsa ji yake yi kamar ana hura masa wuta.

“Duk mace mai daraja ba za ta taba kasancewa a haka ba Mariya kin bani mamaki kin canza  mani ban yi tsammanin haka kika koma ba…ba ma wannan ba tun yaushe nake garin nan amma daidai da rana daya kin ki bani lokacin ki amma kin iya baiwa wanda zaku tsaya layi kuna rigima da su saboda ni bani da wata daraja a idanunki ban cancani ki tsaya dani ba shikenan na gode amma ki sani in har kikace haka za ki cigaba da rayuwa da samari kina da katon aiki a gabanki”.

Yana gama fadin haka ya fice daga cikin soron zuciyarsa na suya sosai yaji ba dadi a ransa da maganar da ya gaya mata amma haka kawai yake ji a zuciyar tasa ita kadai hanyarsa ta samu sauki duk da dai bai san ya zata dauki lamarin ba.

Idanuwanta da suke zubda hawaye ta kure kofar da su tana jin wani tashin hankali mai girma yana wanzuwa gareta a hankali taji kafafuwanta na kokarin kasa daukarta zubewa tayi kan gwuiwowinta lokaci guda ta na sakin wani kuka mai ciwo da taba zuciya…A hankali take taka benan har ta isa bakin kofar tana jin yarda gabanta ke dokawa ba ta san ya zai kalleta ba bata san ya zai karbeta ba ita dai  ta san tana son sa so mai tsanani wanda tun da take a filin duniyarta bata taba jin son wani ɗa namiji ba kamar Dr.Erena zuciyarta da ruhinta sun jima suna kai kawo akan son shi ta dalilin son sa ta zo aiki cikin Company sa saboda burinta ya cika take zaman aiki a company ba wai saboda kudi ba amma ta rasa ya zatayi ta rasa mai ya dace tayi a gareshi domin ya amince da ita har ya so ta sosai ta lura sam! baya kula duk yanayin da take nunawa don ya sota amma hakan sam ba ya wani tasiri akansa ba ta san ya za tayi ba abin da ya ke kara tayar mata da hankali yarda lokaci guda  wata ta shigo cikin Company din take kokarin bata mata duk wani shirinta ta lura Dr.Erena son ta yake yi so kuwa mai tsanani abin da ta lura dashi ita Areefa ba son sa take yi ba shi yake kiɗin sa yana rawar sa ga inda ake son sa amma ya kwashi jiki ya tafi in da ba a son sa.

Ita dama tun da Areefa ta shigo cikin Company nan gabadaya taji bata kwanta mata ba sosai take ji a ranta akwai abin da zai faru don ta lura ita ma Areefa ba wai aiki ne kawai ya kawo mata ba har da wani KUDIRI nata na daban.

Tsaki taja kadan kafin ta gyara zaman rolling din da tayi wa dan kwallin jallabiyar dake jikinta  sosai ta gyara zaman glass din dake fuskarta kallo daya kayi mata ka san ita ma ba baya b wajan kyau da kirar jiki fara ce amma ba can sosai ba.

A hankali ta turo kofar Office din ta shiga zuciyarta na bugaawa da halin tsoro don bata san abin da zai je ya dawo ba bata san yarda Dr.Erena zai karbeta ba ta san ya zai anshi abin da za taje masa dashi ba.

“…Bobby karka sake ka bata min rai kayi kawai abin da nace da kai ba wai ka kai shi can in da ba a dawowa ba a,a kawai so nake yi yaji a jikinsa  ya san har yanzu Dr.Erena yana nan a yarda ya sanshi ba wai canzawa yayi ba”.

Tana kokarin buɗe baki tayi sallama ta tsinkayi muryar Dr.Erena ya na fadin haka ai mutuwar tsaye tayi idanuwanta a warwaje lokaci guda jikinta ya shiga ɓari kamar wacce akayi wa wankan ruwa mai tsanani sanyi gumi ya shiga tsantsafo mata a jiki lokaci guda duk taji jikinta ya shiga narkewa da duk wani kudiri da buri da ta zo don cimmawa a hankali ta shiga jan numfashi tana mamakin kalaman Dr.Erena bata taba zaton haka yake ba bata taba zaton akwai rashin imani har haka ba a ransa.

A hankali ta shiga kokarin juyawa don ficewa amma zuciyarta tana hanata akan kudirin da ta zo dashi sosai taji komai ya fara canzawa tsoro da fargabar da take yi ya ragu sosai zuciyarta na kara mata jarumta akan kawai taje ai mai nema ba ya rasawa ita fa abin da ta zo yi daban maganar da yake yi bai shafe ta ba kuma ba ta san abin da yasa yace haka ba.

Da wannan tunanin ta shiga saita kanta gabanta na faduwa kadan kadan.

Sallama tayi tana mai cusa kanta cikin Office din tsaye ta hangeshi yana kai kawo fuskarsa da murmushi wanda daka kallashi zaka gane na mugunta juyowa yayi jin sallamar da kayi dubanta yake yi cikin wani irin yanayi kafin ya kau da kan sa.

“Sannu Sir”.

Ta fadi da kokarin dauko jarumta ta azawa kanta ansawa yayi a ciki kafin ya dube ta ba yabo ba falla sa.

“Lafiya me ke faruwa ne Mufeeda?”.

Sosai taga yayi mata kwarjini a idanunta gabanta taji yana bugawa wata irin burgewa take jin lokaci guda tana karuwa akan Dr.Erena juya idanunta ta shiga yi tana faman yak’e kamar wacce bata da gaskiya.

Dubanta ya shiga yi da wani irin yanayi na tuhuma kafi ya tako inda take tsaye.

“Akwai wani abu ne?”.

STORY CONTINUES BELOW

Ya fadi yana kureta da kallo da ya kusan narkar mata zuciya da gangar jiki. A hankali ta shiga motsa baki zuciyarta na tsallen tsoro akan yarda zai anshi lamarin.

“Sir, dama akan maganar Areefa ce”.

Dan yatsine fuska yayi kafun yace.

“Me ya faru da Areefa din wani abu tayi miki ne?”.

Girgiza kai tayi kafun ta ja numfashi mai tauri tana jin yarda wani abu da ya tokare mata kirjiya ya sauka.

“Gaskiya Sir. Ban yarda da ita ba jikina sam! Bai kwanta da ita ba tun da ta zo Company din nan sosai nake ji ajiki kamar ba alheri bace a gareka da ma mu kafatanin ma’aikatanka…”.

Hautsine wa fuskarsa ta shiga yi da wani irin bacin rai idanuwansa suka shiga kaɗawa da tsananin haushi kafin ya dube ta sosai da sosai yana faman hirji kamar wani kumurci.

“Me kike cewa Mufeeda Areefa din ce ba alheri ba Areefa ce kike jifa da wadannan kalaman naki kina da hankali kuwa anya ba wani abu kika sha ba wanda ya rabaki da duniyar hankali gaskiya bana zaton kina cikin hayyacinki na lura ke ma kin fara yan kurɓe-kurɓen nan na yan matan wannan zamani in ba haka ba ina ruwan ki da ita mai ya shafe ki da ita rayuwarki daban ta ta daban don haka tun wuri tun muna kallo juna a mutunce ki fice mani daga Office tun kafin na keta miki rashin mutunci.”.

“Am…amma Sir. Daka tsaya ka fuskance ni gaskiya ce fa nake sanar da kai…”.

Wani kallo ya watsa mata kafun ya shiga nuna ta da hannu.

“I Say Get Out! tun kafin nayi miki abin da baki taba zato ba”.

ware idanu tayi sosai jin furucinsa ya taba mata zuciya amma sai taki barin haka yayi tasiri a zahirancen cikin jarumta ta sake dubansa murya alankwashe.

“Sosai na fuskat kamar akwai wata alaka a tsakanin kai da ita Sir hakan kuma bai dace ba sam ya kamata ace ka nemi mace mai daraja mutunci a matsayinka na mutum mai daraja da mutunci mutane da yawa yanzu kallon wani daban suke yi kamata ganin alakarka da Areefa…”.

“Mufeeda! Which can of nonsense kike kokarin gaya mini me kike nufi dani me kike so ki ce da nine akan Areefa ya kamata tun wuri ki gyara kalaman ki kuma ki sani indai akan Areefa ce kika zo kina yi mani wannan haukar wallahi tallahi gaf! kike da barin Company din nan”.

Gwalo idanu tayi waje sosai zuciyarta na wani irin raɗaɗi da zafi komai take ji na jikinta yana canzawa sosai take jin komai nata kamar ba nata ba kalaman Dr.Erena ba karamin taba mata zuciya sukayi ba ji take kamar ta daura hannu aka ta kurma ihu bata san ya zatayi ba bata san me zatayi Dr.Erena ya kalle ta a mutunce ba bata san hanyar da za ta bi ba domin ya kulata ya anshi tayin da take masa ya sota kamar yarda ta kamu da son sa a filin duniyar zuciyarta sosai take son sa so bana wasa ba tana kishinsa ba ta son duk wata mace ta ga tana kusantarsa sosai tashiga tashin hankali lokacin da ta ga Areefa ta fado rayuwarsa.

Wasu kwalla taji suna neman zuba mata da sauri ta dauke su ba tare da  Dr.Erena ya gani ba amma sai dai tayi shuka a idon makwarwa domin kuwa duk motsinta akan idonsa take yi da mamaki yake dubanta sosai hawaye da ta shafe ya kara sanya shi a mamaki sosai sakanni ya dauka yana kallonta kafun ya ce da ita cikin muryar tuhuma.

“Hawaye Kuma me yayi zafi shi ba wuta ba Mufeeda me yake damun ki wani abu akayi miki ne Pleaae Leave my Office ba zan dauki wannan haukar taki ba kin ji ko I need to be alone ba na son abin da zai kawo mani ciwon kai don ba dauka zan yi ba”.

STORY CONTINUES BELOW

Murmushi tayi wanda ya fi kuka ciwo sosai take jin bakin ciki da takaici na rashin darajawa da Dr.Erena yake nunawa akanta sosai take ganin rawar kanta da gangacin da zuciya tayi mata na son wani wanda bai son tana yi ba ga ta yanzu a gaban shi amma yana nuna ita da banza duk daya bata san mai ya sa haka ba ta san dai SONE SILA wanda bai yi mata adalci ba bai dace ace yayi mata haka ba bai kamata ace AKAN SO tana kuka ba kukan ma akan wanda ba tayi tsammanin zuciyart za ta so shi ba ko a mafarkin ta ba ta taba zaton zuciyarta zata dauko mata son Dr.Erena ba ta kawo mata tun da ta fara aiki a Company tun ranar da ta daura idanuwanta akan sa taji ta kamu da son sa amma bata san ta yaya zata bayyanar son da take masa ba a gareshi domin sosai da sosai yake mata girma da kwarjini a idanunta.

Ba ta zaton za ta iya barin nan batare da ta amayar masa da abin da take ji game dashi ba bata zaton zata iya daukar  gangar jikinta ta fice daga cikin Office din nan batare da ta bayyana son da take masa ba ko da kuwa hakan zai sanya ya kore ta daga Company din nan. Ba za ta iya cigaba da dakon son sa ba tana bukata zuciyarta ta sarara mata da tashin hankali da take samun kanta kullum a ciki runtse idanuwanta tayi kirjinta cike fargaba da tashin hankali mara musaltuwa tana jin yarda kirjinta ke bugawa da sauri-sauri motsa laɓɓanta ta shiga yi kanta take ji yana juyawa amma haka ta kinkimo jarumtar duniya ta daurawa kanta.

“Dr.Erena…”.

Ta fadi tana jan wani numfashi mai tauri gaske shi kuwa dubanta yake yi da mamaki cike da fuska jin a RANA DAYA Mufeeda ta kira sunansa abin da bata tabayi ba tsayin lokacin da ta fara aiki sosai ya natsu yana dubanta kafin ya ja kujera ya zauna.

“Na jima a duniyarka ina shawagin son ka amma sam baka lura da haka ba, na jima ina jiyar zuciyata da tayi gangancin daukar sonka ta azawa kanta, na jima ina kwaɓarta amma ta ki ji tayi nisa a sonka, na jima ina sanar da ita cewa ba mu dace ba amma bata ga hakan ba ta nuna min so ba ruwansa da haka, Dr.Erena naji ma ina son ka so mai tsanani sosai nayi zaton za ka gane in da na dosa amma ina sam hankalin ka bai kai nan ba maganar gaskiya ina son ka kai ne namiji na farko a filin duniyar nan da zuciya ta tayi amanna dashi a fannin so ban san ya zan kwatanta maka ba amma ka sani ina son ka so mai ansa suna so”.

Zabura yayi daga kan kujerar da yake zaune idanuwansa cike da tulin mamakin maganganun Mufeeda hannu ya shiga nuna ta dashi yana jan numfashi kafun ya saki wata dariya wacce ta kaɗa ‘yan hanjin Mufeeda sosai lokaci guda taji gabanta ya yanke ya fadi runtse idanu tayi wasu hawaye suka zubo ta kasar Glass din da ke fuskarta kafin ta shiga haɗe hannayenta waje daya tana Rolling din su.

“You Love Me? For God Sake! Mufeeda kina cikin hayyacin ki kuwa kin san waye Dr.Erena kuwa da kike daukar wa kan ki wahalar son sa to maganar gaskiya ba zan boye miki ba bana tunanin zan iya zama nayi soyayya dake bake ba ma hatta WATA MACE daban bayan Areefa bana zaton ko kallon arzuki zan iya yi mataa ya kamata ki san wani abu mace bata gabana mace daya na taba so kuma nake burin zama da ita ita ce Areefa ita ma ban san ya akayi zuciyata ta kamu da son ta ba a RANA DAYA ba zato ba tsammani naji KIBIYAR AJALI ta son ta ta cakar min zuciya wanda har zuwa wannan lokaci na kasa zareta sai kara lumewa take yi cikin zuciyata da duk wani gurbi na cikin ta”.

Dubansa take yi da duk idanuwanta da suka kaɗa sukayi jajir fuskarta har tana canza kala izuwa ja sosai take jin duniyar nayi juya mata da duk wasu kalaman Dr.Erena da take jin su kamar saukar garwashin wuta.

Numfashi take ja da take jin sa kamar ta na jan barkono izuwa  kanta dama cikin ta sosai take jin duk wani sashi na jikinta na narkewa kamar zata watse a kasa  dan yatsanta daya ta kai baki tana cizawa domin tabbatar da abin da yake faruwa da ita gaskiyane ba a mafarki bane yau ta kara tabbatar wa da maganar hausawa na cewa SON MASO WANI koshin wahala ne ta tabbatar da yau Dr.Erena baya tare da ita At All baya gayyatarta a filin duniyarsa bai ma san tana yi ba.

STORY CONTINUES BELOW

“Na lura da abin da kika zo dashi akan Areefa duk kishi ne kina tunanin son da nake yi mata zai bari na dauki abin da ki ka zo mani dashi a gaske to ko da kuwa gaske ne ba zan dauka ba Areefa mace ce da nake so so mai garman gaske wanda bana zaton a filin duniyar nan akwai macen da zan iya yiwa ko da kwatar son ne don haka fice mani daga cikin Office”.

Ya fadi yana mai yi mata nuni da hannu fuskarsa a murtuke kamar bakin hadarin da ya gangamo yake kokarin zubda ruwa.

“Dr.Erena MENE NE LAIFIN ZUCIYA don ta nuna so da kulawa akan abin da take so bana zaton son da nake yi maka zaka yi masa fatan KARKON KIFI ka sani so nake yi maka son da ban taba yi wa wani ɗa namiji ba a filin duniyar nan ya kamata ace ka girmama son da nake yi maka ka dauke shi da daraja ka killace shi a zuciyarka a wani fili ko ya ya ne…”.

“Are U At Of Your Sense Mufeeda kina da hankali kuwa wacce irin magana ce haka kike fadi wani irin hauka ne haka ina so dole ne nace bana yi na ce bana sonki leave alone mana”.

Murmushi ta saki mai ciwo kafun ta zare Glass din dake fuskarta idanuwanta da suke rine suka bayyana sosai take duban Dr.Erena da yake mata kallon wulakanci da raini laɓɓanta ta ciza.

“Karka yi tunanin don na furta kalmar so a gareka zai baka lasisin wulakanta ni, karka yi tunanin don buɗe baki na sauke aji na da daraja ta ta ‘ya mace za ka wulakanta ni ka sani ba aibu bane san nan ba zubda mutunci bane don mace ta buɗe bakinta ta fadiwa ɗa namiji tana son sa ba san nan haka ba yana baiwa ɗa namiji dama bane don ya wulaƙanta ‘ya mace don ta nuna tana ta son sa ba duk macen da zata iya buɗe baki tana cewa namiji tana son sa ba abin kunya bane kuma ba abin a wulakanta ta bane domin tayani don ceto kanta da halin da zata fada ka san wannan Dr.Erena karka yi tunanin son da na nuna ina yi akan ka zai baka damar tozartani ka wulakanta ni daraja da martaba ta tana nan ba abin da ya ragu sannan ko a duniyar masoya na san nayi abin kwarai wanda da yawan mata ba sa yi sannan kuma kamar yarda mata suke tsoro halin da ka nuna min da tozarci da wulakanci don kawai na nuna ina son ka ba laifi na bane laifin zuciya tane wacce ba ƙashi gareta ba”.

Dubanta ya sake yi a wulakance domin sosai zuciyarsa tayi zafi da kalamanta motsa baki ya shiga yi yana kokarin magana ta daga masa hannu.

“Ba sai ka daka min tsawa koka koreni kamar wata mara ‘yanci kai ba yanzu zan bar maka Office din ka”.

Tana fadin haka tayi hanyar fita daga Office har ta rike Handle din ta juyo ta dube shi sosai kafun ta kau da kai tare da ficewa daga cikin office din tana kokari hau benen da zai kai ta kasa ita kuma Areefa na sako kai saura kadan suyi gware nan suka shiga kallon kallo a tsakanin juna su fuskar Mufeeda cike da kunci da bakin ciki kallon Areefa take yi da wani irin yanayi kafun ta kau da kai gami da jan tsaki ta wuce ita dai Areefa bin ta take yi da kallo ganin yanayin da take ciki kamar akwai abin da take damun ta musamman idanuwanta da suka kaɗa sukayi jajir kafaɗarta ta daga cikin nuna halin ko in kula kafin ta isa ta tura kofar cikin Office din.

Tsaye ta same shi yana kai kawo hannayensa goye a bayan sa motsin shigowar tane ya sanya shi tsayawa yana jan numfashi fuskarsa a daure kamar hadari.

A hankali ta isa ta zauna tana mai daura kafa daya kan daya bakinta dauke da cingum tana faman taunawa idanuwanta akan Dr.Erena kallon sa take yi da wani irin yanayi mai haifar mata da ɗaci a zuciyarta sosai take dubansa da damuwar da take fuskarsa a ranta take fata dama ya dauwama a haka yaƙe ta saki kafun ta kaɗa idanuwanta.

“Me ke faruwa ne Dr.Erena?”.

Sai a lokacin yaja numfashi mai girma ya na huci gami da runtse idanuwansa dubanta yayi kafun ya ja kujera ya zauna.

STORY CONTINUES BELOW

“Wannan mai kalar haukar ne za tayi mani akunyanci bata san na fita da duk tashencin ta ba”.

Cikin rashin fahimta ta yatsine fuska cikin son karin bayani.

“Wai fa zuwa tayi tana sakin wasu banzayen kalamai kafun daga karshe ta dire da cewa wai ni take so ki ji fa wata wauta da kalar hauka”.

Fakare tayi tana kallonsa tana karantar yanayin sa mamaki ya cikata ta yarda Mufeeda ta iya jefa kanta son wannan mugun mutumin mara tausayi da imani ita kam bata ga abin so a jikinsa ba bata ga abin burgewa a gareshi ba har da Mufeeda zata zo tana fada masa tana son sa har ya samu damar ci mata mutunci ya wulakanta ta ko da yake kila kudin da yake dashi ya ruɗeta in kuwa haka ne Mufeeda bata yi wa kanta adalci ba da tayi sake ta fada motar kwadayi ta dire a tashar wulakanci da cin mutunci.

“Ni ban ga abin ta da jijiyoyin wuya ba don tace tana son ka ai ta dace ace kai ma ka anshi son da take yi maka duk macen da zata iya zuwa ta ce tana son ka ai bata cancanci wulakanci da tozaryawa ba duk da dai ku mafiyawancin maza haka kuke in har kuka ga mace ta mutu akan son ku shikenan kun samu hanyar wulakanta ta da cin zarafin ta iri-iri”.

Murmushi yayi lokaci guda kafun ya motsa laɓɓansa.

“Bana tunani haka zata kasance tsakani na da ke Areefa so daya nake yi kuma akan ki yake bana zaton akwai wata mace da zan so bayan ki akan ki na fara  so kuma akan ki zan gama so ki san wannan”.

“Uhmm haka dai kace aiku dama haka kuke maza akan mace akwai iya dadin baki musamman in duniya na yi muku biyayya ba abin da ba za kuyi wa mace ba”.

“Areefa na lura kamar kina goyon bayan Mufeeda da ne ko baki jidadin abin da nayi mata ba”.

“Ko daya wallahi amma dai ka sani mace mace ce ko min lalacewarta don haka ka kula mace ba yar wulakanci bane ita mai daraja ce da kima duk da dai wasun mazan ba su dauki mace a bakin komai ba sun mai da ita kamar riga lokacin da suke ra’ayin ta za su saka ta da sun gama kuma su cire su ajje ita da banza duk daya”.

Mikewa tayi tana mai daukar jakarta ta dubi Dr.Erena da ya saki baki yana ta faman murmushi idanuwansa akanta kafun ya mike shima.

“Ya haka Areefa ina zaki daga zuwanki kuma Please ki zauna mana akwai maganar da nake so muyi dake mai muhimmanci ce”.

“At this Time bana tunanin zan iya zama kuma ina da abin yi gaskiya”.

“Please mana Areefa”.

Juya idanu tayi kafun ta dube shi cikin gyaɗa kai ganin haka ya sanya shi komawa ya zauna yana mata nuni da ta zauna ita ma ba musu ta zauna yana ma kallonta kallo na sosai da sosai kafun ya ja mumfashi.

“Areefa maganar gaskiya ya kamata ace kin ce wani abu akan alakar dake tsakaninmu ya kamata ace kin motsa motsawarki kawai nake buƙata a yanzu”.

Ci rashi bawa zancen nashi muhimmanci ta dubeshi kafun ta motsa laɓɓanta cikin ɗacin zuciya

.

“Ina jin ka me kake nufi?”.

Sai da ya sosai ƙeyarsa kafun ya saki murmushi na sosai da sosai.

“Maganar aure mana ya kamata ace mun tsayar da magana a wannan lokacin…”.

Da sauri ta daga masa hannu tana mikewa kan kafafuwanta zuciyarta take ji tayi wani bugawa da tashin hankali mai girman gaske jin zantukan nashi take yi kamar saukar aradu ƙwanyarta taji tana juya a hankali ta dube shi.

STORY CONTINUES BELOW

“Please ka bari za muyi waya in na koma gida kaji komai zai yi settling a cikin kan kanin lokaci”.

Tana gama fadin haka ta fice daga Office din cikin sauri kamar wacce zata kifa haka take ji komai taji lokaci guda ya canza mata da tashin hankali mai girma kunnuwanta take ji ba za su iya daukar kalamansa ba masu dauke da kunci da bakin ciki tafiya take yi har ta sauka kasa ta isa in da sashin ta yake komai ta kammala a hanzari ta zare key din motarta ta fice daga cikin reception din tun kafin ta isa in da motar ta take tayi mata key ta buɗe baya ta isa ta shige ta haɗe kanta da sitiyari tana mai da numfashi a hankali kanta take ji yana sarawa da karfin tsiya kamar zai rabe gida biyu sai da ta shafe lokaci mai tsayi kafin ta yiwa mota key ta fizge ta cilla ta saman titi ta shiga zabga gudu kamar wacce zata tashi sama burin ta kawai ta ganta a gida ko ta samu tayi saita kanta sosai take jin tashin hankali na tunkaro ta sosai take jin ranta na kara baci duk lokacin da suka hadu da Dr.Erena don dole kawai take zama dashi da umarnin Hajiya Layla.

*********

Tun da ya doso Muhabbir Coffee yake jin gabansa na yankewa yana faduwa lokaci lokaci hakan na karuwa sosai yaji a jikinsa akwai abin da ke kokarin faruwa dashi.

Parking yayi bayan yashiga wajan yayi oda din duk abin da yake bukata ka kawo masa a hankali yake kai Coffee bakin sa yana kurba har zuwa lokacin jikinsa bai daina sanar dashi wani abu dake kokarin faruwa dashi ba tun yana daukar lamarin da sauki har yaji zuciyarsa tana kara azalzalarsa da yabar wajan  A hankali ya mike ya dauki wayarsa da key din sa bayan ya biya kudin abin da yayi oda ya doshi in da motarsa take ajje ya bude ya shiga ya zauna bayan kulle yana kokarin yi mata key yaji an dorasa masa bakin bindiga ta bayan kansa zare idanu yayi a firgice yana kallon mutane biyun da suke bayansa zaune ta glass din gaban motar.

“ja motar muje”.

Daya daga cikin su yace dashi murya a buɗe gabadaya kamar saukar markaɗe.

Jikin rawa ya shiga yi jin abin da suka ce dashi ware ido yayi yana kokarin juyawa ya dube su laɓɓansa na motsi daya daga cikinsu ya daka masa tsawa cak! ya tsaya da maganar da yake kokarin yi jikin sa na ƙyarma sai faman ambaton sunan Allah yakeyi.

A hankali yayi wa motarki bayan ya yi ribas ya fice daga cikin wajan. In ba wai kasan abin da yake faru a cikin motar ba ba zaka iya cewa komai ba dubin gabadaya glass din motar mai duhu kuma a zuge yake.

Suna fita daga cikin wajan suka shiga nuna masa hanyar da zai bi a hankali a hankali suke tafiyar har suka fara ficewa daga cikin gari nan Alhaji Abdulwahaab ya kara ruɗewa ganin suna tun karar daji da sauri yayi kokarin taka burki amma jin bindiga a keyarsa ya sanya shi kara wuta cikin hanzari jikinsa na rawa domin ya tabbatar wadannan mutanan barayi ne ko kuma yan satar mutane.

Daji sosai suka yanka sai da  yashiga cikinsa sosai sannan suka ce yayi parking a hanzarce yayi sannan ya juya yana kokarin kallon su daya daga cikin su ya buga masa kan bingida a gefen fuska wanda hakan ya sanya shi sakin kara gami da yin lif! jikin kujera kamar wani mara lafiya wajan da suka dokar masa lokaci daya ya fara fiddo jini.

Gabadayan suka buɗe suka fito dayan su ya ja kofar gaban ya buɗe ya fizgo Alhaji Abdulwahaab zuwa waje ya baje akasa kansa na buguwa da gefen motar wata irin kara ya saki gami da ambaton sunan Allah numfashi kawai yake ja a hankali gabadaya ya gama shiga tashin hankali mai tsanani dagowa yayi cikin matsanancin yanayi yana duban su ganin su yake yi suna kasuwa bibbiyu idanuwansa suna lumshewa a hankali yana buɗe su bai ankaraba ya sake ji an kai masa wani wawan naushi a fuska an daki goshinsa da kan bindiga nan ya baje a sume bai sake sanin in da kan sa yake ba.

Duban juna sukayi suna masu sakin wata mahaukaciyar dariya kafin su tafa hannayensu a hankali suka fara tafiya suna ficewa daga wajan shikuwa Alhaji Abdulwahaab bai ma san in da kan sa yake ba.

Ya dauki lokaci mai tsayi can wajan magrib sanyin yamma ya kaɗashi ya farka a wahale yana kokarin buɗe idanuwansa amma jin su yake yi kamar ba a jikinsa suke ba dafe kan sa yayi sosai yana mai kara runtse idanuwansa lokaci daya ya buɗe su duhun daren da ya fara shigowa shi ya an karar dashi da sauri ya tashi zaune ya juya yaga motarsa hannu ya saka ciki Aljihu wayarsa yaji da sauri ya zaro yana dubawa 6:50pm shida da minti hamsin ya gani a hankali ya shiga kokarin tashi amma tsamin da jikinsa yayi ya hana shi kokarin da yake yi rarrafawa yayi har ya isa wajan motar ya dafata sannan ya mike yana faman cizon laɓɓansa buɗe motar yayi ya shiga a hankali yana faman numfarfashi yakeyi zama yayi sosai yana jin yarda bayansa ke amsawa da ciwo mai tsanani cikin dauriya yayi wa motar key Allah ya taimake shi ta ta shi ajiyar numfashi yayi mai karfi a hankali ya shiga yin ribas har ya juya hanyar da zata fiddo shi daga cikin daji.

Sosai ya fita daga cikin daji ya shiga gari daidai wani Super-Market ya tsaya ya daga kansa sama daidai wani shago da yake zaton clinic ne haka kuwa akayi KAMALA CLINIC ya ga an rubuta da dan hanzarin sa ya buɗe ya fito ya doshi wajan bayan yayi sallama ya shiga nan ya yi musu bayanin abin dake faruwa wani daga cikin ma’aikatar wajan ne ya zo yayi masa komai da ya dace har da allurai sai daya sha

Kafun ya fito ya dauki hanya zuwa gida zuciyarsa cunkushe da godiyar Allah da lamarin ya tsaya a haka ba tare da sunyi masa wata illa sosai ba.Wata alkarya.

10-July.

Ihu sukeyi gabadaya sun karaɗe wajan sai cukuikuye junansu sukeyi a waje daya cikin matsanancin tashin hankali kallo daya zakayi musu ka tabbatar suna cikin tsaka mai wuya gabadaya sun jeme sun yi baki kayan jikin su gabadaya sun gama fita hayyacin su wasun suma ko kallabi babu akan su.+

Janta yake yi yana faman dukanta da bakin bindiga itakuwa sai turjewa take yi tana janyon yan’uwanta suma sunan janta kallo daya zakayi mata ka gane tana cikin galabaitaccen yanayi idanuwanta gabadaya sun gama rufewa kawai fizgar ta yake yi har zuwa lokacin da ya fidda ita daga cikin wajan sai numfarfashi take yi can ciki tsakiyar rana yaja ta ya watsar da ita ga ranar ta kwala sosai kamar zata darkar da mutum.

A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta jin zafin ranar na dukanta ta ko ina gashi ba wata wadatacciyar suttura bace a jikinta wando ne dogo sai riga ita ma doguwa iyakar gwuiwa da guntun hannu amma yanayin da kayan su ka koma sai ka ka rantsee yagaggune daga bola aka tsinto su kanta kuwa ba kallabi wasu hawaye suka zuba daga cikin rufaffun idanuwanta kafin ta tashi zaune tana faman cizon laɓɓanta.

Wani irin murɗawa taji mararta tayi lokaci guda kamar yan hanjinta da mararta za su zazzage wata kara ta saki mai razanarwa kafin ta kai hannayentala duk biyun cikin galabaitaccen yanayi tana dafe wajan zubewa tayi gabadaya a kasa tashiga murkususu da shure-shure kamar kazar daka yanka take kokarin mutuwa cikin lokacin kankani ta fice daga hayyacinta ko motsi bata yi kafin can kuma jini ya balle ya shiga kwararowa ta kasanta mai dauke da gudaje-gudaje numfashi take ja jin komai na duniyar take kamar ba nata ba duniyar take ji tana canza mata da tashin hankali mai tsananin gaske zafin da take ji tun daga cikinta har zuwa mararta ya tabbatar mata da lokacin mutuwarta yayi sosai taji dumin da ke bin kafafuwanta hakan ya kara tsinkar mata da zuciya.

Tsaye yake kanta yana kallon duk abin da ke faruwa amma ko motsi bai yi ba sai  faman murmushi yake yi kafin ya juya ya dubi gabadayan alkaryar tasu sannan ya juya ya dubi sauran yan’uwan nata da ke kargame ko wacce da sakar a hannayenta da wuyanta sai faman zubda kwalla suke yi suna gunjin kuka hannu suke miko mata amma ina bata san ma a ina take ba lokacin da suka lura da abin da ke faruwa da ita ba su san lokacin da suka kara sautin kukansu ba cikin matsanancin yanayi.

Bindigar da take hannunsa ya daga  ya saita in da suke ji kake daram! ya sake nan take albushiri yayi fitar burgu ya sauka cikin wajan a saitin goshin daya daga cikin yan matan wani razanan nan ihu ta saki lokacin da kanta ya tarwatse kwanya ta watse duk ta bata yan uwanta kafin gangar jikinta ya zube kasa warwas.

Ganin abin da yake faruwa ya ka sanya su cikin matsanancin rikici lokaci guda duk su rikice suka shiga kai kawo cikin wajan ko wacce hannunta akanta suna faman kankame junansu.

Ihun da yake tashi ne a wajan yana ansa kuwwa ko ta isa ya sanya shi dago tambol din sa ya fito fuskarsa a murtuke kam! ya tsaya a tsaye yana faman bin filin wajan da kallo kafun ya sauke wajan yan matan da yake hangowa sun faman rusar ihu wata razananniya tsawa ya doka lokaci guda sautin tsawar ya karaɗe wajan ƙafin ya shiga takawa cikin matsanancin zafin rai idanuwansa da wani irin yanayi na tsananin rashin imani da tausayi idanuwansa na kan su sam bai lura da abin da yake gabansa ba sai da yaji yaci karo da mutum sannan ya tsaya yana duban wajan shame ya ganta ko alamun rai babu a jikinta da sauri ya daga kansa yana duban sa.

“Ita kuma wannan fa?”.

Ya tambaya cikin yanayi na halin ko in kula kafun ya sake dubanta iya zuwa lokacin tana fidda numfashi a hankali hankali.

“Shiga nayi na bukace ta shine ta saka min hakora a jiki”.

Ya fadi yana mai nannaɗe hannun rigarsa wani wawan cizo ne ya bayyana har fatar wajan ta dauke sosai.

STORY CONTINUES BELOW

Ji kake kau ya dauke shi da mari kafi ya tsartar masa da yawu cikin tsananin dacin rai.

“Mai ya hanaka rabata da filin duniyar nan tun da har zata yi maka taurin kai har haka”.

Yana gama fadin haka ya zaro wata karamar bindiga fisto ya saita ta lokaci guda ya sakar mata albushiri a kai shurawa daya tayi daga shi bata sake yin wani ba.

“Wa ya fada maka ana jayayya da su ai duk wacce ta tsaya tsaiko a tsakanin ku kawai dauki ranta don ba su da wani amfani a gare mu”.

Ya fadi yana mai tsartawa gawan dake yashe tana zubda jini daga kanta yawu kafun ya juya cikin takun isa yana mai juya bindigar  dake hannunsa har ya isa garesu tun da suka ga ya tunkara garesu suka shiga haɗewa waje daya suna cakume junansu numfashin su na fita da sauri-sauri cikin matsanancin faduwar gaba da tsoro mai tsanani jikin kofar ragar da aka rufe su da ita ya tsaya yana mai yawatawa da idanuwansa akan su kafin ya saki wata mahaukaciyar dariya mai matukar razana su ya shiga sakin albushirin bindiga wajan na ansa sautin fitar albushirun hakan ya kara firgitar da su kafin lokaci daya ya daka musu tsawa da ta sanya su yin shiru wasun su har da sakin fitsari.

A hankali ya shiga kaucewa daga wajan yana faman cilla bindigar sama yana caɓewa har ya isa ga tambol din sa can nesa ya hangota tana ta faman kyalaye amai kamar zata amayar da kayan cikinta gabadaya ta gama galabaita numfashi kawai take saki cikin tsananin zafi da raɗaɗi gabadaya jikinta take ji ya canza komai nata jin sa take yi kamar ba nata ba a hankali ta shiga kokarin tashi amma jirin da taji yana dibarta ya sanyata komawa tayi zaman daɓaro idanuwanta sai faman shatatar da hawaye sukeyi gabadaya ta gama figewa ta rame kamar ba ita ba idanuwa duk sun zurma ga wani mahaukacin duhu da tayi kamar wacce ta shekara ba ta ga ruwa ba.

A hankali ya tako ya iso gareta yana bin ta da kallo kafin ya dan ranƙwafa sosai ya tallabo haɓarta a dan razane ta dago kai ganin waye ya sanya ta buge hannunsa tana mai jan jikinta can nesa dashi zuciyarta na kara cushewa waje daya ta wani tarin bakinciki da takaici mai yawan gaske kallonsa take yi kallo na tsana da kiyayya fuskarta a murtuke sai faman huci take yi ji take kamar ta cafko shi ta shake shi ya mutu ko ta huta da wannan bakar izaya da ukuba da take ciki a filin duniyar nan bata san yarda zata kira wannan lamarin ba bai ta san mai zata ce da wannan al’amarin ba bata san ya zata kwatanta rayuwar kaskanci da take cika ba ta rashin yancin da mutunta kallon kanta take yi a wata banza wacce bata da saura galihu tun da ta fado filin duniyar  azzalumin mara imani wanda ba abin da ya saka gaba sai daukar rai da bai ji bai gani ba.

Murɗawar da cikinta yayi ne ya sanyata dafewa tana runtse idanu hadi da tura laɓɓanta duka cikin baki tana cizawa wata irin azaba ce taji tana kartar mata ciki da bayanta ji take yi kamar zata mutu don azaba da take ji hawaye suka shiga zuba wanda bata san ma suna zuba din ba kawai dumi take ji a sama kuncinta har zuwa kirjinta buɗe idanunta tayi ganin mutum tsaye akanta ya sanyata saurin matsawa tana watsa masa wani matsiyanci kallo mai cike da tsana da kiyayya mai girman gaske kafun ta shiga motsawa laɓɓanta suka shiga motsi hawaye sai faman ambali suke yi.

“Ka sani wannan dariyar da kake yi akwai ranar da za ta zame maka kukan jini, karka yi tunanin wannan rashin imanin da kake nunawa ba ranar da zai zo karshe, karka yi tunanin cin zarafi da keta haddi da kake yi ba zai zo karshe ba, ka sani duniyar ma gabadaya sai ka barta kamar yarda kake zama SILAR AJALI ga wasu to ka tabbata yarda ko wani dan aike yake zuwa ya dawo to  ka tabbata kai ma dan aiken ka yana nan dawowa kuma duk abin da kake aiken sa yayo kai ma sai ya zo ya yi akan ka”.

Numfashi taja tana jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi da tashin hankali mai girman gaske.

“Ka kashe mani iyaye na ka rabani da gari na ka keta min haddi ka zaja min UKU BALA’I bala’in da bai taba rabuwa dani ba ka ja zamanin bala’in da ba zai taba canzawa ya koma alheri da yake kamar da ba amma ka sani shi sharri dan aike ne wallahi”.

STORY CONTINUES BELOW

Mikewa ta shiga kokarin amma har lokacin jiri take ji wani fizga taji yayi mata ya watsar da ita kasa ya taka mata ruwan ciki da kafarsa mai dauke da wani kafcecen takalmi wani irin nishi ta saki hawaye suka zubo mata idanuwanta a runtse.

“Ina so ace na mutu amma abu daya zan roki Allah ya banni nayi rayuwa har zuwa lokacin da zan ga karshen ka zan fi kowa farin ciki da murna a filin duniyar nan mutane da yawa na san za suyi farinciki duk da dai baya in ta tafi bata taba dawowa amma ina so ace mutane da ka saka wa ciwon rai ka saka su a BALA’I zan so ace sun ga karshenka Malik”.

Buɗe idanu tayi tana jin yarda zuciyarta take kara kekeshewa da rashin tsoronsa yinkurawa tayi zata tashi tana mai ture kafarsa daga ruwan cikin ta.

Duban gawarwakin da ake kokarin dauka guda biyu na yan’uwanta tayi kafun ta dube shi fuskarta da murmushi mai ciwo.

” ‘Ya’ya Mata kayi wa haka ka sani komin daren dadewa wallahi sai hakkin su ya hanaka sukuni ba ganin ka na shiga rigar mutanan adalci kana nuna kai na Allah ne kana yaudarar mutane ta wannan hayar Uhmm…”.

Taja numfashi kafin ta girgiza kai.

“Lokaci ne ba wanda yake hanyar sabawa Allah ya samu nasara komin lokacin kuwa da ya dauka yana cin nasara to akwai RANA DAYA tak! da zata zo ta rushe duk wannan nasarorin da yake zaton ya samu”.

Sosai ya har zuƙa jikinsa har rawa yake yi wani wawan cafka ya kai wa wuyanta nan ta shiga kakari idanuwanta sukayo waje sun kaɗa sunyi jajir wani huci ya shiga fetar wa kamar zai ci babu kafin yayi cilli da ita can gefe guda ta hadu da wani katon dutse ta gaban goshinta lokaci guda gun ya tsage ya shiga zubda jini sosai ta ji zafin wajan amma ba ta nuna hakan ba tashi tayi ta sanya hannunta ta na dauke jinin a hankali a ko ina na sashin jikin ta azaba take ji amma jarumar zuciyarta ta kiyin rauni.

“Kisan kai da kakeyi ka dauka kuma aikin yi a filin duniyarka na rantse da Allah wata rana kai ma zaka mutu mutuwa kuwa ta wulakanci sai ka raina kan ka BAR GANIN ALLURA wallahi karfe ce bar ganin abin da kake yi kamar abun burgewa ne wallahi kai ma sai wannan hanyar ta zama silar barinka duniyar nan”.

Kallonta yake yi da wani irin yanayi na mamaki tun da yake bai taba gani mace mai taurin rai kamar ta ba tun da yake bai taba ganin an kwaso yan mata an kawo masa ya samu mai taurin rai haka ba har zata iya dubansa ta gaya masa magana son ranta ba tare da fargaba ko tsoro a fuskarta ba gyaɗa kai yayi kafin ya bar wajan yana faman dukan iska.

Ita kuwa kuka ta saki mai taba zuciya da soya ruhi sosai ta durkushe hannayenta saman kanta ji take yi kamar ta hadi zuciya ta mutu ta bar wannan duniyar komai na cikin ta ba dadi sai yau ta kara tabbatar da cewa DUNIYA BA ALJANNA BACE ta tabbata bakomai cikin duniyar na sai ta shin hankali da rashin imani kaicon wannan rayuwa kaicon wannan zamani.

*****

Numfashi take ajjewa kyar idanuwanta sun kaɗa sunyi jajir hannunta dafe da cikinta da take jin sa yana ta faman juyawa sosai ta shiga tashin hankali sosai tayi kuka kuka wanda har zuwa yau take yin sa kuma bata san ranar daina shi ba ta shiga kunci da ukuba da bala’i ta sani bata da wata dama da za ta sake zuwa mata ta dadin rayuwa ta sani ita kam rayuwarta ta gama karewa tunda ta fado hannun wadannan azzaluman mutanan maras imani da tausayi maras ganin darajar ‘YA MACE ba su dauke ta a bakin  komai ba ‘Ya’ya Mata sun mai da su kamar Toilet din su na duk lokacin da suƙa bukata za su je su biya bukatar su ko hali ƙaƙa ne ba sa ganin darajar koma waye bata san wasu irin mutane ba ne su bata san wata alkibla suke bi ba har ga Allah zata iya cewa ba musulmai bane domin bata ganin su da suffar ni’imar musulci ba duk da dai suna ikirarin su din haka amma ita kam bata taba yarda ba.

STORY CONTINUES BELOW

Nisawa ta sake yi Hawaye na kwaranyo daga idanuwanta kamar daga sama taji ana dauke mata su firgigit tayi ta dawo hayyacinta dubansa tayi kafun ta kau da kanta zuciyarta nayi mata zafi da raɗaɗi ji take yi kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu da wannan bala’in da take ciki bata son ganinsa ko muryarsa bata son ji domin ganinsa kamar ganin bala’in rayuwa ne.

Murmushi yayi yana sake kai hannunsa bisa kuncinta.

“Ki yarda dani ki zauna dani mu rayu tare dake a filin duniyar nan ki yarda mu zama abu daya har gaban abada ni dake da abin da ke cikin ki”.

Wani irin zillo taji cikinta yayi kafun idanuwanta suyo waje sosai fargaba da tsoron da take ji a zuciyarta akan abun da take zargi shi ne ya tabbata tabbas haka ne maganar sa gaskiya ita kanta ta sani akwai abin da ke damunta sosai taji a jikinta komai ya canza sosai take jin motsi a cikin cikinta runtse idanuwa tayi duniyar taji tana juya mata kanta yana komawa kasa kafafuwanta na dawowa sama zuciyarta take ji tana yayyagewa muryarsa da bakaken kalamansa take ji suna ansa kuwwa akan ta da cikin kunnuwanta tartsatsi da rugugi take jin kwanyarta nayi.

“Ban san ta zan sanar dake ba amma ki sani ina cikin yanayi na bukatarki a gareni ina so ki kasance dani har karshen numfashina sosai nake ji a zuciyata sosai da sosai nake jin zuciyata ta baki wani fili mai girma kina rayuwa ki sani ban taba kaunar wata mace ba ban ta taba son wata mace ba iyakata da mace na biya bukatuna da ita domin ni ban dauki mace a abun darajawa ko girmamawa ba amma akan ki ina ji a zuciyata ke ta daban ce”.

Numfashi ya ja mai tauri kafun ya kureta da idanuwansa masu firgitar da ita a ko wani lokaci.

Bata san ya zata dauki wannan lamarin ba bata san a wani mizani zata ajje shi ba sosai take cikin wani mataki na rashin nasara a rayuwa sosai ta hango kaifaffan ALKALAMIN ƘADDARA ya daura tsininsa akan rayuwarta yana rubuta rubutun da take gani a matsayin ajalinta a duniyar nan rubutun da take ganin shine sanadin afkawar wannan rayuwar mai cike da tashin hankali da bakin ciki da ukuba sai yau ta kara tabbatar wa bata da sa’a ko daya a duniyar nan bata da sa’a matsayinta na ‘ya mace bata da duk wasu ababe da mace zata yi alfahari da shi a duniyarta komai ya ruguje komai ya lalace wai ita ce yau dauke da juna biyu, juna biyun da ba ta hanyar aure ta same shi ba junan biyun da ya kasance ta same shi ta hanyar bala’i da masifa da jafa’i juna biyun da zata iya kiransa da shine ajalin rayuwarta

.

‘Yaa Zuljalali wal-Ikram’.

Ta ambata a zuciyarta da take ji tana yayyagewa tana fadowa kirjinta da tashin hankali mai girma ga wani abu mai girman gaske da take jinsa tsakanin makoshinta da kirjinta ya tsaya cak!.

Bata san me zata ce ba ita dai ta san rayuwarta ta kare rokon Allah take ya dauki ranta a filin duniyar nan rayuwar take ji gabadaya ta ishe ta bata son ta bata son komai na cikinta komai baki ne take gani bata burin sake maimaita WATA RAYUWA a duniyar nan burinta kawai numfashinta ya dauke a daidai wannan lokacin lokacin da take ji yafi komai zama bala’i a gareta.

Hawaye suka cika gaba da zuba a idanuwanta shi kuwa sai hannu yake kai wa yana dauke mata su.

“Ki ce wani abu ina son abin da yake cikin ki ina kaunarsa har dake kan ki ki yarda mu rayuwa a inuwa daya a tare har zuwa numfashin mu na karshe”.

Daga idanu tayi ta dubi sashin da yan uwanta suke gabadaya sun gama mutuwa yawancin su da sunyi musu fyaɗe suke kashe su wasu kuma in suka ki yarda da bukatarsu suke kashe su su jefa gawarwakin a ruwa tana kallo bata da damar hanawa a gabanta sun kamo mutane masu yawa suna yin yarda suke so da su tana kallon yarda ake nunawa yan uwanta mata zallar rashin imani da tausayi amma bata san yarda zata yi ba agabanta an kashe har bata san a dadi ba an sha daukar bindiga ana bata ko wuka da sunan ta kashe wani amma bata tunanin zuciyarta zata iya zama mara imani da tausayi har haka yan uwanta musulmai ake kashewa har ake bata damar ta kashe batare da laifin komai ba.

STORY CONTINUES BELOW

Ruwan hawaye suka zuba mataa ta daga kai can nesa ta hango Baaba BG na kallonta tun da ta zo shi kadai ne mutumin da take kallo a mutum wanda ba irin su ba tana zaton shima kamar sato shi akayi kamar yarda suma aka sato su bata taba jin yayi magana ba bata taba jin ya buɗe baki ya furta kalma daya ba tausayinsa take ji mutum har mutum amma izayar da yake sha in da wahala na kisa da tuni ya mutu sosai ta fuskanci hakan bai son aikin da suke saka shi a lokuta da dama tana kallon yarda Malik yake basu umarnin aiwatar da wani aikin na mugunta amma shi sam ba yayi Malik lokuta da dama ya sha daura masa bindiga da sunan zai harbeshi amma sai ya fasa amma fa izaya ya na shanta ko yanzu da yake cikin razana tsaye sai faman gumi yake yi idanuwansa a sama yana kallon ranar da ta kyalla sosai idanuwansa sai faman zubda hawaye suke yi.

Malik ya sanya shi akan idonta yake bashi wannan azabar don kawai yaki yin mubaya’a akan abin da ya saka shi…

Karar albushirin da yaketo cikin dajin ne ya firgita su da sauri Malik ya mike yana kai kawo a tsakiyar wajan ita kuwa gabadaya ta firgice tashima ya gagare ta.

Yaran Malik ne taga suna ketowa kan baburansu a guje kamar za su tashi sama gabadaya wajan ya kaure da karar albushiri sosai  da sosai Malik ya nufi cikin Tamfol din sa cikin hanzari lokaci guda kuma ya fito jikinsa da wata riga baka wulik mai kauri ga wasu igiyoyi da suke barbaje a jikinta da hanzari ya keta hanyar da ya ga yaransa na shigowa gudu yake yi kamar zai tashi sama can nesa ya hango bataliyar sojoji sun tun karo wajen bindigogin sa kirar Ak47 ya ya cilla sama tare da caɓe su a hannayesa ya shiga gudu yana sakin wuta ko ta ina cikin dajin sai da yayi tafiya sosai yana zubda sojojin da suka tunkaro alkaryar tasa albushiri ko ta ina amma shi ko a jikinsa domin albushiri da ta fado kansa yake watsewa kasa batare da ya bula jikinsa ba sai dai rigarsa ta dau hayaki a daidai inda albushirin ya sauka sosai ya cigaba da tafiya yana kallon yarda ake ta kashe masa yara hakan ya kara harzuka shi matuka lokaci guda zuciyarsa ta shiga tururi fuskarsa na kara hautsinewa idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir a daidai lokacin da ya tun kari inda yake hango bataliyar sojojin adaidai kuma lokacin albushirin bindigun nasa suka kare watsar da su yayi tare da yin wata uwar sufa ya yi kasa ya tura hannayenssa cikin ciyayin da ke wajan lokaci guda ya dago wata bingida mai saffurin mai jigida ya cilla sama kafin ya sake mai da hannunsa cikin ciyayin ya fizgo albushiri mai matukar tsayin gaske ya mike kan kafafuwansa da wani irin karfi gaske domin inda yayi tsalle ya dire sai da ciyayin wajan suka yi sama bindigarsa da ta shilla sama a daidai lokacin tayo kasa da hannu daya ya caɓe ta tare da zura mata albushirin nan ya shiga sakin wuta ko ta ina yana faman juyi kamar wanda yake amfani da wani maganakisun majajjawa.

Abin da Malik bai sani ba shine sojojin sosai suka shirya domin kuwa ƙawayansu kayi wa dajin can bangaren alkaryar tashi tuni sojojin sun isa cikin ta suka shiga sakin wuta ga duk wani yaransa sosai yan matan suka firgita suka shiga ihu saboda sautin tashin albushiri da suke ta faman ji ko ta ina ba su tsinke da lamarin ba sai da suka mazaje na bajewa a kasa matattu Mubeena dake cikin Tamfol din Malik tana kai kawo hannuwanta saman kai sai faman du’a’i take yi da fatan Allah yasa masu Ceton Rai ne a garesu.

Wani albushiri ya ratso ta ciki wajan ya gogi kafatarta wani zafi ne mai cike da raɗaɗi ya ziyarce ta kwalla kara tayi da kafin gaske tare da zubewa a kasa ji take yi kamar hannu aka fizge daga jikinta zafin jinsa tayi a ko ina na sashin jikinta kararsa kuwa amsa kuwwa yayi cikin dodon kunnuwanta a hankali ta shiga jan numfashi da take jin sa kamar zai fice daga jikinta saboda tsabar azaba da raɗaɗi runtse idanuwa tayi a daidai lokacin aka banko tamfol din aka shigo sojoji ne guda biyu ko wane dauke da hula irin ta su ta sojoji hannayen su dauke da jibga jibgar bindigogi a resting din ta sukayi lokaci guda cikin cikin raɗaɗi ta buɗe idanuwanta ta kalle su lokaci guda ta mai da ta rufe tana jin suna surutunsu akan ta amma ko motsin arzuki bata iyayi ba daya daga cikin su ne ya lura da kafataɗarta da sauri yayi wa dan’uwansa alamu hakan ya tabbata masu alburushin ya same ta da sauri suka cinciɓe ta sukayo waje da ita gabadaya wajan ya zama fili sai gawarwaki dake baje can gefe kuma yan matan ne aka tare su waje guda sai faman rusar kuka suke yi gabadaya sun gama ficewa daga hayyacin su can suka nufa da Muneeba yan uwan naganinta da sauri su suka taso suka ansheta ganin halin da take ciki ya sanya su kara sautin kukan su kukan nasu ya farfado da ita daga sumar da tayi na wucin gadi a hankali ta shiga buɗe idanuwanta wanda hasken rana ya saito fuskarta komar da su tayi ta rufe kafin ta ciji laɓɓanta ta sake buɗe su sosai cikin karfin hali sosai ta shiga juya idanuwan nata tana kallon yarda sojoji sukayi wa wajan ƙawanya gabadaya numfashi taja mai tauri kafun ta dubi wanda suka riketa ganin yan uwanta ya sanya ta rushewa da wani irin kuka mai tsuma rai sosai da sosai jikinta har karkarwa yake nan suka sake buɗe babin kuka a tsakanin su sojojin sai bin su da kallo suke yi kafin su cigaba da shiga duk wani sashi na wajan.

A bangaren Baaba BG kuwa lokacin da sojojin suka fara sakin alburushin ba zato ba tsammani yaji saukarsa a hannunsa na hagu da hanzari cikin wahalallen yanayi ya saki wani nishi kamar ransa zai fita ya saukar da kansa daga kallon ranar da yake yi wanda suka gama wahaluwa jijiyoyin kansa sun fito sun burɗun-burɗun da su kwayar idanuwansa sai faman zubda ruwa suke yi.

Zubewa yayi a kasa yana kai hannun damarsa yana rike da hagun cikin wani irin yanayi mai matukar wahala sosai yaji kansa da duk jikinsa sun ansa da alburushin da ya fasa masa hannu runtse idanunsa yayi sosai kafun ya bude su dishi-dishi yake gani duban hannunsa yayi da yake ta faman zubda jini dafe wajan yayi sosai amma hakan bai hana jinin cigaba da zuba ba da hanzari ya shiga kokarin mikewa jiri na dibarsa sautin albushiri ne kawai yake ji ta ko ina zuciyarsa yaji ta kawo masa wani karfi mai girma gaske da hanzari ya tashi yana tangaɗi ko gani sosai bai yayi ya yanki daji yana jan jikin sa zafin raɗaɗi sai kara hauhawa yake yi tafiya ya yanka sosai sai yayi ta har kafafuwansa na kokarin kasa daukarsa amma zuciyarsa bata yi rauni ba karfi yake ji yana kara zuwa masa tun yana cijewa har ya fara gudu yana yankar daji numfashin sa na sama da kasa tafiya mai nisa yayi cikin wannan matsanancin halin har sai da sautin alburushirin dake tashi ya ragu yana jiyo sa daga can nesa bai ankara ba ya gashin gaban wani tafkeken kogi dake gudu cak! ya tsaya da tafiyar da yake yi yana mai da numfashi kafin ya zube kasa yana mai lumshe idanuwansa ko ina na jikinsa yake ji yana masa wani irin ansawa da ciwo mai tsanani buɗe

idanuwansa yayi ya kalli hannun nasa da yake digar da jini ganin jinin ya fara bushewa hakan ya tabbatar masa ba karamar tafiya yayi ba ga hannunsa ya kumbura sosai ko ya ya taba shi zafi da radaɗi yake jin suna ansawa a jikinsa.

A hankali ya tashi yana tangadi ya tunkari kogin sosai idanuwansa suna lumshewa bai san lokacin da ya isa bakin kogin ba har ya tsoma kafafuwansa kawai ji yayi ruwan ya fizgeshi da wani irin karfi ya antayashi ciki gudu kogin ya shiga yi dashi ba k’ank’autawa shi kansa bai sam ba a wani hali yake ba sosai ya mika dashi hanyar da kogin yake bi yana faman sama da kasa dashi.

A bangaren su Malik kuwa abu ya kacame fada sosai ake yi ba abin da ke tashi sai sautin albushiri gawarwaki kawai zaka ke gani ko ta ina ta sojoji da ta alkaryar Malik wanda suka rage kalilan ne wuta kawai Malik yake tafiya yana yi idanuwansa a rufe ba zato ba tsammani yaji saukar wani katoton abu ya daki goshinsa ya cilla dashi can gefe ya bugu ta wata katuwar bishiya mai matukar girma kafin ya sake cilla wa wani wajan can daban ya fada cikin ciyayi har sai da ya shiga cikinta sosai da sosai runtse idanuwansa yayi kafun ya bude su sun kaɗa sun yi jajir yinkurin mikewa yayi amma ina bayansa yaji yayi wani irin amsawa kamar an karya

bushesshen ice da sauri ya koma ya kwanta yana mai sakin numfashi ga wasu hawaye da suka shiga zubo masa a fuska ba kankautawa.

hannayensa duk biyun ya cusa cikin ciyayin wajan ya damka kana jin sautin yardda suke rumurmushewa da yake sun bushe wani bakin ciki yaji ya tokare masa kirji ga wani abu mai girma ya tsaya masa a makoshi da k’yar yake jan numfashi komai.

A karo na biyu ya sake buɗe idanuwansa jin motsi ta ko ina sojoji akansa sun yi masa ƙawanya sosai da sosai ko wannan su hannunsa dauke da bindiga sun saita shi wani takaici ne ya sake kume shi ya kurma wani irin razanan nan ihu da ya ansa sauti sosai cikin dajin…

Juyi kawai take yi zuciyarta na zafi da wani irin raɗaɗi mai girman gaske sosai take jin komai ya sauya mata sosai take jin duniyar da abin da ke cikinta sun zame mata kunci da ukuba komai take kallo a mara dadi zuciyarta da ruhinta suna wani+
mataki na tashin hankali ba abin da take tunawa sai kalaman Dr.Karami sosai suka taba mata zuciya da ilahirin jikinta bata taba zato ko tsammani ba ko a mafarkinta bata taba zaton Dr.Karami ya dube ta ya na gaya mata magana son ransa har haka ba ko da yake bata ga laifinsa ba har da ita da ta tsaya tana kai kawo akan sa ashe duk kulawa da yake nuna mata a zahiri ba haka bane zuciyarsa sam bata tare da ita.
Wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata da saurin ta kai hannunta ta shafe su don bata so Umma ta lura da halin da take ciki yau kusan sati uku kenan amma ta kasa manta kalaman Dr.Karami sai faman kuwwa suke yi mata akai da kunnuwa ta rasa mai yake yi mata dadi a filin duniyar nan bata san abin da ke kokarin faruwa da ita ba ta ji zafin kalamansa amma kuma zuciyarta taki bashi laifi taki yarda da laifin da take dorasa masa bata ma san mai haka yake nufi ba tun da abin nan ya faru ta kasa sukuni tunanin Dr.Karami ya sha mata kai ko barci take yi shine dai take tadda cikin barcin nata.
Mikewa tayi daga shingiɗen da take ta shiga safa da marwa a cikin dakin domin samowa kanta mafita sosai take jin ciwo mai girma a zuciyarta sosai take jin gangar jikinta na kawo mata bakutan wani yanayi mai girman gaske wanda ta rasa yarda zata kwatantashi sosai Dr.Karami yashiga yin tasiri akanta da kalamansa da suka hanata sukuni.
Bata san mutum na tsaye ba kuma za ta iya cewa ga lokacin da ya shigo yana jima yana dubanta da yanayin ta kafun ya motsa laɓɓansa cikin wani irin yanayai.
“Ya jikin naki?”.
A firgice ta juya jikinta har rawa yake yi jin sautin muryarsa lokaci guda ta dube shi da idanuwanta da suka kaɗa sosai shima ita yake kallo da wani irin yanayi mai girman gaske kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu da wani yanayi wanda suka kan su ba su san haka na faruwa a garesu ba sun jima a wannan halin kafun Dr.Karami ya kau da idanuwansa jin zuciyarsa na bijiro masa da wasu lamura da ya tabbata ba za su haifa masa da ɗa mai ido ba numfashi yaja mai tauri yana jin yarda zuciyarsa ke buɗewa da wani yanayi akan Mariya sosai yake jin ko wani sashi na jikinsa na ansa amon tausayawa da yanayin da ya ganta a ciki bai yi tsammanin lamarin ya kai har haka ba nisawa ya kuma yi yana fesar da wani zazzafar huci kafin ya dago idanuwansa da suke lumshewa kamar mai jin barci.
“Uhmm jiya munyi waya da Umma take sanar dani wai baki da lafiya”.
Ya fadi yana mai yawatawa idanuwansa akan fuskarta da wani irin yanayi mai taba zuciya yatsine fuska ta shiga yi tana kau da kanta gefe kafun ta motsa laɓɓanta kamar wacce akayi wa dole.
“Ni ba abin dake damu na”.
Ta fadi da yanayin fushi a muryarta murmushi yayi kafun ya taka ya karasa shiga cikin dakin hannayensa sarƙe a kirjinsa ya zuba mata idanuwansa sosai yana mata kallon tuhuma kallon da take ji har cikin jikinta yake shiga ji take yi kamar zata narke ta watse a wajan.
“Kin fiye gardama wallahi kenan Umma karya take yi miki  ko? Sau nawa ina kiran wayar ina cewa a baki amma bakya ansa na sani ba wai rashin lafiyar ta hanaki ansar kirana ba fushi kike yi dani ko  akan abin da na san na fada miki gaskiya ko”.
Da sauri ta dube shi idanuwanta a warware kafin ta tura baki gaba.
“Fushi fa kace kai din ne zan yi fushi da kai akan wani dalili saboda ni kuma gani wahallaliya ko bani da aikin yi”.
STORY CONTINUES BELOW
Tun da ta fara magana yake kallon ta da mamaki mai girma a ransa dubanta yake yi har ta dire kafun ya ja wani numfashi yana jin yarsa zuciyarsa ke wani irin juyawa a mataki na wahala runtse idanu yayi kafun ya sake buɗe su kalaman nata yake jin su kamar saukar ruwan zafi a dukkan sassan jikinsa takawa ya shiga yi yana isa gabanta ganin haka da tayi taja baya da sauri shikuwa bai bar takawa gabanta ba har sai da ya kusan mannuwa da jikinta sannan ya tsaya.
“Me kika ce maimaita ban ji ba”.
Ya fadi yana mai karkaɗe kunnuwansa fuskarsa a daure tamau hakan ya fadar mata da gaba don ta tabbata maganarta ta bata masa rai sosai don ga fuskarsa nan ta nuna.
“Maimaita mana ina jinki”.
Ya sake fadi yana watsa mata wani kallo da ya razana mata zuciya  da sauri tayi baya har tana kokarin faduwa kasa.
“Ni kike fadawa haka ko Mariya  Good kin kyauta”.
Yana fadin haka ya juya yana kokarin fita juyowa yayi ya dubeta sosai.
“Dr.Aqeel da Huzaif ba zan hanaki tsayuwa da su ba don na lura su ne kika mai da abokan zama har kuna SA’IN SA amma ki sani ko samarinki ne ko auren su zakiyi dole ki fidda daya domin kuwa maza biyu ba auren su ake yi ba gabadaya kisan da wannan”.
Yana gama fadin haka ya dage labulan ya fice daga cikin dakin.
Sosai ta ware idanu waje jin maganar da yake fadi mata sosai taji zuciyarta ta tabu ta rasa mai Dr.Karami yake nufi da haka ta rasa mai ya mai da ita da yake fadi mata irin wadannan kalaman wayace masa son su take yi wa yace masa samarinta ne har yake gaya mata magana har haka.
Dafe kanta tayi da take jin yana barazanar tarwatsewa ta runtse idanu tayi tana jin wani zuki da raɗaɗi na taso mata tun daga kasar ruhinta
yana direwa a dukkan jikinta sosai taji duniyar na juya mata komai take ji yana kara hargitsewa sosai kalaman Dr.Karami suke taba ta don ta lura kallon wata mace daban yake yi mata mai wani hali na daban…
“Ke Mariya wai shin meke damun ki ne? na rasa gane kan ki gabadaya kin daurawa kan ki wani bakin hali da ZURFIN CIKI wanda ban san ki dashi ba”.
Maganar Umma ce ta katse mata dogon tunani da ta afka da firgice ta juyo tana duban Umma da ke tsaye bakin kofa tana watsa mata wani irin kallo.
“Na gaji nagaji da halin ki Mariya haba mana ke kenan kullu yau min ki hana kan ki sukuni ki hana wasu kuma haba mana ai wannan shiga Hakki ne an tambayeki me ke damun ki kin ki fadi to ya kike so kiyi yanzu shima Hisham din ya zo daga yanayin da ya fita na san ke ce kika bata masa rai ko shikenan ki cigaba da yi abin da ranki ke so karki daina kin jiko”.
Tana gama fadin haka ta juya ta fice daga cikin daki ranta a matukar bace.
Mariya da tayi mutuwar tsaye ta shiga duban kofar kanta na kara rikicewa da sarawa sosai taji komai ya sake kwance mata wani abu mai nauyi take ji ya zo kirjinta ya zauna sosai kwallar da take makalewa taji sun zoba mata akan kuncita kafafuwanta taji suna kokarin kasa daukarta da sauri tayi kasa ta zube wani kuka taji ya zo mata ba zato ba tsammani kanta ta tura cikin cinyoyinta jikin har k’yarma yake yi hawaye suka balle mata kamar an buɗe famfo ita kam bata san yarda zata cakuɗa wannan lamarin ba komai ya kulle na kanta sosai take jin tashin hankalin na daɗuwa a filin duniyarta.
********
A hargitse ta fado cikin gidan bayan mai gadi ya buɗe mata Get din sam ba ta lura da wanda yake gabanta ba sai da taji ta daki mutum tayi taga taga kamar zata fadi da sauri ya riko mata hannu idanuwanta a rufe don ta sadakar ta je kasa jin an riketa ne ya sanyata saurin buɗe idanuwanta ta sauke su a cikin nasa da suke zube akan ta.
STORY CONTINUES BELOW
“Tareeq”.
Ta furta tana mai zare idanuwanta sosai kafun tayi hanzari fizge hannunta taja da baya.
“Yi hakuri don Allah wallahi ban gan ka bane…”.
Hannu ya daga mata idanuwansa na kan wayarsa ba tare da yayi mata magana ba ya rabata ya wuce abin sa wani takaici ya kule ita kam bata san wani irin hali wannan mutumin gareshi ba na shariya da kyaliya tun da ta fara ganinsa a hakan dai yake jiya iyau ko muryarsa bata taba ji ba sosai hakan ke taba mata rai ta ki jinin mutum mai irin wannan hali shiyasa Dr.Karam…
Shiru tayi da sauri jin tunaninta na kokarin canza jaha da sauri ta figi kafarta tayi cikin gidan.
Abin da bata sani ba shi Tareeq ko da ya tafi makalewa yayi yana kallon ta da wani yanayi wanda shi kadai ya barwa ransa tun ranar da ya fara ganin Mariya yaji gabadaya ta tafi da imaninsa amma ya rasa ya zai yi kuma gani yake yi kamar da raini ace k’awar kanwasa yake bibiya shiyasa ke ta faman tsare gida shi ala dole girma ne nan yake dauka bayan kuma zuciyarsa ta jima a wani fanni na rashin wannan girman don tuni ta yasar dashi akan abin da tajima tana so.
Numfashi ya ja yana fesarwa kafin ya fice daga cikin gidan.
Ko da tashiga cikin falon ba kowa sai karar Tv kawai dake tashi numfashi taja kafun ta ja kafa da sauri ta haye saman bangaren Baseera kofar a buɗe ta same ta don haka da sauri ta tura ta shige kwance ta hango Baseera tayi ɗai-ɗai saman gado sai faman zabga murmushi take yi kamar wacce aka zunduma gidan aljanna kunnan ta dauke da waya alamun wayar da takeyi mai muhimmanci ce turjiya Mariya tayi ta harɗe hannayenta a kirjinta ta zuba mata ido cike da mamaki kafun taja kafarta da sauri ta isa gareta duka ta daga mata ganin yarda ta saki jikinta har rigar ta na tattarewa cinyoyinta sun bayyana a firgice ta tashi ta zunduma ihu ta cillar da wayar can gefe idanuwa warwaje Mariya da ke tsaye bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba tana dubanta ita kuwa Baseera nar-nar tayi da idanu kamar zata yi kuka kafin ta yi hanzari sankowa daga gadon ta cakumi wuyar Mariya.
“Idan kina da mutunci in nitse wallahi baki da mutunci sam!”.
Ta tureta can gefe tayi tana susar cinya inda Mariya ta dake ta.
“Ai ke za a kira haka wannan ai rashin hankali ne kina waya har baki san kayan suna kokarin bayyana jikinki ba yanzu in da wani ya shigo ya ganki a haka fa me kike tsammani”.
Gefen gado ta koma ta zauna tana faman turo baki gaba tana rarraba idanu in da zata ga wayarta can gefen gado da hango da sauri ta rarrafa ta dauko kafin ta shiga kaɗa idanuwa.
“Yo ba dole na fada cakwalkwalin nishadi ba ni da mai kaunata  ne fa rabin raina sakata zuciyata jinin jikina…”.
“Ke dalla jaye ki bani waje mara kunya kawai”.
Baseera ta kwashe da dariya tana tafa hannaye.
“Ba maganar rashin kunya akan me zan cuci akai na haka kawai ai dole na tattali kayana ke kin san kuwa yarda nake son wannan gayen kuwa ya hadu iya haduwa ko ta ina ke dai kawai bari sai kin ga Fine Bobo dina sai kin kusan mutuwa ke dai yi ta zama a haka ba ki ga tsuntsu baki ga tarko yan maza sai gwara kan ki suke yi kin kasa fahimtar komai ki kasa sanin komai AKAN SO wallahi tun wuri ki koyi soyayya malama ki ji yarda ake fadawa cakwalkwalin nishadi wayyo Allah sahibi na mai sona  ina son ka”.
Wani tukukin bakin ciki ya turnuke Mariya ganin yarda Baseera ke wani narkewa tana bin lafiyar gado sai wani lumshe idanu take yi mamaki ne ya cikata har yaushe Baseera ta koyi soyayya har haka ita bata sani ba ko WUKA A MAKOSHI zata gani bazata iya cewa ta taba ganin Baseera da saurayi ba amma yau RANA DAYA wai soyayya take yi ta gani kashe har tana koranta mata tsaki taja kamar harshenta zai tsinke kafun ta mike tana hararar Baseera kamar idanuwanta za su zubo kasa.
STORY CONTINUES BELOW
“Wayyo Allah My Dr.Hisham”.
Baseera ta fadi tana kara rungume fulo sosai sai narkar da idanu take yi.
Sunan da ta kira ne ya sanya  Mariya firgita tana dubanta bata san lokaci da ta isa bakin gadon bata zauna idanuwanta a warwaje.
“Me kika ce Baseera wani suna naji kin kira”.
Sake narkewa tayi kafun ta mike zauna tana sakin wani lallausar murmushi.
“Abin da kunnuwanki suka jiye miki mana masoyina nakira ko saɓo nayi ne nayi saurin tuba”.
Girgiza kai Mariya ta shiga yi cikin wani irin yanayi sunan da Baseera ta ambata ba karamin tayar mata da hankali yayi ba in har ba kuskure tayi ba kamar sunan Dr.Karam ne takira ko da sunan masoyin ta anya kuwa ko dai ba shi bane ai masu sunan da yawa a filin duniyar nan zuciyarta taki gasgata haka ta fi yarda da Dr.Karami ne masoyin Baseera wani irin bugu taji kirjinta yayi da sauri ta dafe tana faman jan numfashi kadan-kadan duban Baseera tayi wacce sai faman danne-danne takeyi a waya fuskarta da murmushi.
“Cikin raina na sanyoka ka bani guri nima in shigo naka”.
Baseera ta fadi tana rungume wayar a kirjinta idanuwanta a lumshe kafun ta buɗe su akan Mariya da tayi fakare tana dubanta kirjinta sai faman lugudan bugu yake yi.
Tsaki taja na karo ba a dadi kafun ta ja numfashi.
“Wai meke damun ki ne haka wajan ki fa na zo amma kin tsaya kina raina min hankali in ba zaki kulani ba malama na tashi na san in da dare yayi mani”.
Ta karashe a hassale kamar zata kife Baseera da mari.
“Haba my Besty ina ni ina raina miki hankali kawai dai kisan in mutum ya tsunduma cikin kogin love din nan ne abun ne ba sauki walla…”.
Tun kafun ta karasa Mariya ta mike kan kafafuwanta sai faman huci take yi kamar zata hadiye Baseera wani kallo tayi mata kafun ta ja kafa da sauri tana kokarin barin dakin ganin haka da Baseera tayi da sauri ta mike ta riko hannunta sosai.
“Yi hakuri mana mai yayi zafi shi ba wuta ba haba mana Besty bai kamata kiyi mani haka ba zo muje ki gaya min abin da ke faruwa na lura da yanayin ki kina cikin damuwa sosai”.
Fizge hannunta tayi rai bace kafun ta dubi Baseera.
“Ni ki rabu dani kawai tafiya zan yi…”
.
Ware idanu tayi sosai ta sake riko hannunta murya a kasa cikin rarrashi.
“Zo muje na baki labari kin ji san nan ki sanar dani abin da ke damun ki a duniyar nan besty baki da wata k’awa wacce tafi ni nima kuma bani da wata k’awa wacce ta fiki mu rufe MATSALOLINMU a tsakaninmu tare da samun mafita ba tare da kowa yaji ba don Alalh zo muje mana”.
A hankali taja hannunta ta kaita bakin gado ta zaunar kafin taje ta dauko mata ruwa mai rangwamin sanyi tare da lemon Exotic ta dire mata a gabatan amma Mariya ko kallo ba su isheta ba halin da take ciki a yanzu ji take yi kamar zuciyarta zata kama da wuta don bala’in da take ji a ranta komai take ji ya rikice mata kwanyarta ta tsaya cak! da aiki.
“Ban san me zance miki ba Mariya akan wannan lamarin amma ba karamin taba min zuciya yake yi ba na rasa yarda zan kama domin samo mafita na rasa gane kan ki kin ki sakin jiki ki fayyace abin da ke damun ki sannan in aka ce ga abin da ke damun ki baki daukar haka ne sai ki nuna kin amincewarki zuciyarki na wahalar dake sosai da sosai akan abin da kika san gaskiya amma kin ki amsa”.
STORY CONTINUES BELOW
Baseera ta fadi fuskar da yanayi na tausayi kafun ta mike kan kafafuwanta da wani irin yanayi na sanyi jiki taku tayi daya biyu kafun ta juya ta dubi Mariya wacce zuciyarta gabadaya ta gama sakin wannan layin da Baseera ta dauko maganar soyayyar Baseera ce yake kai kawo akan sa wanda ke fadar mata da gaba baka dan ba tagumi tayi hannu bibbiyu idanuwanta cikin yanayi na tsananin damuwa.
“Kullum abu cigaba yake yi na rasa in da kika sa gaba na lura kina jin dadin rayuwa a haka ne shiyasa sam baki damu da kan ki ba baki damu da matsalar da kike ciki ba ZURFIN CIKI da kike yi wallahi ba zai kai ki ko ina ba zuciyarki ne zata haifar miki da matsala tun da kin kasa gasgata abin da take zuwa miki dashi”.
“Baseera wai da gaske soyayya kike yi?”.
Mariya ta fadi cikin yanayi na faduwar gaba da ansar da Baseera zata bata akan hakan kallon sosai Baseera ta shiga yi mata jin ta saki layin da ta dauko mata na matsalar ta ta dauko wani na daban murmushi tayi kafun ta juya idanuwanta sosai
.
“meye abin yi mani wannan tambayar Mariya ya za ayi muna wata magana ki na dauko wata kum…”.
“Tambayarki nayi ansa nake bukata kawai”.
Mariya ta tare ta a hassale kamar zata fizgota daga tsayen da take.
Juyawa tayi kamar zata fice daga cikin dakin kafun ta sake juyo ta koma cikin dakin sosai tana bin Mariya da kallo murmushi dauke a fuskarta.
“Bana tunanin wani mugun abu nake yi bana tunani saɓo nayi don na fara soyayya lokaci nane yayi na kai matsayin ace ina da saurayi kamar yarda ake bukatar ko wata ‘ya mace ta kasance da saurayi in har lokacin ta yayi…ko da yake naga kamar mamaki kike yi ko Mariya amma ban san dalilin ba”.
Wani irin zillo taji zuciyarta tayi gabanta ya buga da karfi a hankali ta shiga rintse idanuwanta tana tura laɓɓanta cikin bakinta da wani irin yanayi mai girman gaske a zuciya mai tattare da kunci buɗe su tayi akan Baseera da take kai kawo a tsakiyar dakin fuskarta da annuri na farinciki so take yi ta tambayeta da wa take soyayya amma tana tsoron ansar da zata bata domin kuwa sosai gabanta ke dokawa da tashin hankali mai girman gaske akan Baseera sosai zuciyarta take gasgata zarginta sosai take jin gangar jikinta na amanna da lamarin mikewa tayi kan kafafuwanta da yanayin na karfin hali domin har wani jiri-jiri take gani taku tayi daya kafun ta sauke kanta kasa tana ambaton sunan Allah ya tsareta da mugun ji.
“Uhmm naji kamar kin ce Dr.Hisham ko”.
Ta fadi dak’yar kamar wacce zata fashe da kuka gabanta na dokawa da tashin hankali.
“Yarda kika ji haka lamarin yake ba kokwanto kike yi ba shine mai kauna ta din”.
Baseera ta fadi a iyakacin gaskiyarta ba alamun wasa wani irin zubewa Mariya tayi bakin gado numfashinta na fita a hankali-hankali kamar wacce tayi gudun CETON RAI idanuwanta ta runtse da karfin tsiya ji take yi kamar ba ita ba komai take ji na jikinta yana narkewa da wani irin tashin hankali wanda tun da take bata taba jin zuciyarta ta kawo mata haka ba jikinta har ɓari yake yi ta buɗe idanuwan nata da suka fara kaɗawa cikin karfin hali ta shiga saita kanta tana kalato murmushi mai sanya ciwo a zuciya mikewa tayi kan kafafuwanta tana kallon Baseera da ta zuba mata idanu da wani irin yanayi kafun tace.
“ba laifin kaddara a lamarin nan naki Mariya har da laifin ki komai ke faruwa ya kamata ki sassautawa kan k…”.
Daga mata hannu tayi cikin karfin hali ji take yi kamar zuciyarta zata tarwatse jikinta take ji yana wata irin k’yarma kamar wacce aka jonawa wutar nepa.
STORY CONTINUES BELOW
“Wai kina nufin Dr.Karami dai Baseera”.
Ware idanu Baseera tayi sosai lokaci guda yanayin ta ya sauya kafun ta motsa laɓɓanta idanuwanta aƙan Mariya tana karantar yanayin da take ciki.
“Kin san dai a filin duniyar nan tamu ba wani Dr.Hisham bayan Karami ko…”.
Ai bata kai aya ba tuni Mariya ta fice daga cikin dakin cike da tashin hankali mai tsananin girma da kokarin yayyaga zuciya da jiki baki daya kafafuwan kawai take dorawa a duk in da taji sun sauka har ta isa cikin falon ba kowa hakan ya sanyata ficewa da sauri hannayenta saman kirjinta idanuwanta sai lumshewa suke yi a hankali kamar wacce ke jin matsanancin barci haka ta isa bakin Get ko maigadi batayi wa magana ba ta buɗe kofar ta fice cikin hanzari hanya ta dauka sosai tana tafiya idanuwanta da wasu zafafan hawaye da suke ambaliya so take yi ta karya abin da kunnuwanta suka jiye mata so take yi ta karyata zuwanta gidan su Baseera a zahiran ce so take yi ta karyata kanta da kan ta ba taji
wannan furucin ba so take yi ace ma a tashi duniyar baki daya ba tare da tabbatuwar wannan lamarin ba baza ta iya dauka ba zuciyarta baza ta iya daukar wannan lamarin ba  ina! ba zata iya ba so take yi a tashi duniya so take yi a ce  tashin alkiyama ne so take yi komai ya zama tarihi kamar ba ayi shi ba.
Wasu hawaye masu kokarin dauke fatar fuska suka sake balle mata zuciyarta take ji na kara kamawa da wuta ji take yi kamar narkewa take yi ji take yi kamar ba ita bace ji take yi kamar ba a halicce ta ba a filin duniyar nan.
Sam bata lura ta kai bakin titi ba har ta hau tsakiyarsa ihun mutane da Horn din motoci ya fargar da ita cikin razana zare idanu tayi waje ganin irin Go-Slow din da ta hada mutane wasu na ganin kamar bata da hankali wasu kam danna mata ashar kawai suke yi gaɓadaya ta firgice ta rasa ina zatayi hayaniyar mutane ya kara razana mata kwakwalwa hannu ta daura akai tana kokarin kurma ihu taji an ja hannunta anyi gefe da ita runtse idanu tayi jin wani irin Shock da ya ansa duk kan sassan jikinta da sauri ta buɗe idanuwanta buɗe baki tayi tana kokarin kurma ihu ganin wanda ke rike da ita da sauri ya sanya dan yatsarsa akan laɓɓansa fuskarsa ba wasa alamun tayi shiru tsit tayi amma har lokacin fuskarta da tashin hankali jikinta sai k’yarma yake yi fizge hannunta tayi tana faman ja da baya shi kuwa bin ta yake yi da kallo cikin tsananin mamaki da tu’ajibi hannayensa harɗe a kirjinsa ganin dai tana kokarin komawa kan titin da sauri ya fizgota ya ja ta kamar zata kifa can inda yayi parking din motarsa ya isa ya buɗe gidan gaba ya bata umarnin shiga amma taki sai faman tirjewa take yi tana faman wurga masa mugun kallo take yi kamar idanuwanta za su fado kasa.
Shi kan sa sai da ya ji gabansa  ya fadi da kallon da Mariya take yi masa kallon da ya tabbatar akwai abin da yasa take yi masa shi kallo ne na tuhuma kallo ne kuma na ka yaudare ni kallo na kayi mani ba daidai ba.
“Please Mariya shiga daga ciki mana…”.
Fizge kanta tayi tana kokarin raɓashi ta wuce batare da ta shiga motar ba amma ganin irin tsayuwar da yayi babu wasa ga wani girma taga yayi mata da kwarjini wani irin bugu taji gabanta yayi lokacin da taga
rinannun idanuwansa ta kalle shi kallon da taga yana jifanta dashi da yanayin da taga kwayar idanuwansa na canzawa gabadaya ya firgita ta da sauri tayi kasa da kai.
“Muje nace”.
Ya fadi da wata murya wacce ba wasa a cikinta dubansa ta sake yi cikin nuna son yin gardama amma yarda taga ya tsare gida sosai ya sanya jikinta mutuwa murus ta tokare bakin kofar ita bata shiga ba ita kuma ba ta wuce ba.
“Yaa Allah! Mariya kina da matsala sosai a rayuwarki  kin fiye taurin kai”
.
Ya fadi yana dafe kansa da wani yanayi na damuwa kafun ya sake dubanta wacce ita ma a lokacin ta dago kanta ta watsa masa kallo.
“Nifa ba zan shiga ba kawai ka rabu dani kayi tafiyarka ba abin da ya dame ka dani ba abin da ya dame ka da yanayin da nake ciki don haka Leavea Alone Please”.
Da mamaki yake dubanta jin maganar da take fadi wanda suka kusan tarwatsa masa kai amma sai ya maze cikin tsare gida sosai ya nuna rashin wasa.
“Kisan Allah ki shiga motar nan tun kafin raina ya baci don na lura sai na nuna miki kala irin taki sannan zamu zauna lafiya dake ban san abin da yake hawa miki kai ba ban san mai yasa gabadaya kike kokarin sanya kan ki cikin matsala har haka b…”.
“Wannan ba damuwarka bace kawai ka rabu dani nayi tafiya…”.
Ai ba ta kai ga dire zancenta ta ji ta saman set din motar baje numfashin da take ji na sauka akan fuskarta ne ya sanyata saurin dubansa  kallonsa tayi shima ita yake kallo da matsanancin bacin rai sai faman huci yake yi tana jin yarda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri sosai take kallonsa ta kasa dauke idon ta kamar yarda shi yake kallonta da wani
yanayi wanda ya shiga haifar mata da kasala mai tsanani gabadaya taji duk wani tashin hankali da take ji da bacin rai game dashi yana kaucewa a hankali wasu kibiyoyi take hangowa suna fitowa daga cikin idanuwansa suna sauka ana ta sosai taken jin zuciyarta na buɗewa da wani lamari mai giraman gaske kallon Dr.Karami take yi kamar bashi ba kallonsa take yi a wani mutum mai kwarjini da haiba gami da cikar zati wani kallo take jifansa dashi kamar tun da take bata taba ganin mai kyau da k’yan kallo kamar sa ba.
Hure mata idanu da yayi ne ya dawo da ita  hayyacinta ba tare  da yace da ita komai ba ya juya dayan barin na zaman direba ya shiga yayi wa motar ki har zuwa lokacin fuskar tashi ba alamun wasa sai ma kara tsare gida da yake yi ita kuwa gabadaya ta gama narkewa sai faman juyi take yi ta kasa zama sosai a kujerar da take duk yana kallon yanayin ta har ya yiwa motar Key ya cillata saman titi yana mai kara sautin wakar ‘Because Of You’ ta Amande Mena. dake tashi a cikin motar…Sosai take kai kawo cikin dakin gabadaya ta kasa zaune ta kasa tsaye tunda Dr.Karami ya zo ya ajje ta a kofar gida ya juya ya tafi ba tare da ya dubeta ba balle yace da ita k’ala hakan ba karamin taba mata zuciya yayi ba duk da tana jin wani iri a game dashi na bacin rai duk da ta san dai fushin da take yi dashi ba ta san ya yake ba amma ta tabbata halin ko in kula da ya nuna mata a yau yayi matukar sanyata cikin wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske sosai take jin zuciyarta da ruhinta suna faman kai kawo dauke da lamari mai matukar girma na tashin hankali.
Hannayenta ta daura bisa goshinta tana dafewa gabadaya take jin duniyar na sauyawa a gareta gabadaya take jin komai na kara cakuɗe mata sosai take jin lamarin da Baseera ta sanar mata ya samu gurbi mai girma a sassa na zuciyarta wanda sam ba kwanciyar hankali a cikin sa.
Numfashi take ja a hankali kafun ta ja jiki ta zauna bakin katifarta idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce aka zubawa barkono.
Bata san me zata yi ba, bata san mai ya dace tayi ba, ta tabbata lamarin nan zai iya narkar mata da zuciya har ma da gangar jiki sosai ta kasa gasgata abin da take ji a zuciyarta sosai take karyata kanta wanda bata san mai yasa haka ba ta tabbata zuwa yanzu ya kamata ta yarda da komai ta anshi komai a yarda ya zo sai dai kuma hanzarin da tayi ba gudu bane domin kuwa tana kallo kwaɗo yana shirin yi mata kafa kafar da take zaton in har yayi mata ita to komai ma ya rigaya ya gama faruwa.
Mikewa tayi cikin rashin kuzari tana faman sakin huci mai zafi da take jin sa tun daga kasar zuciyarta yake busowa bakin kofa ta tokare Umma da take kallo dake zaune tana gyarawa Mu’azzam riga gefe guda ta zauna tana mai duban su amma a badinance zuciyar ta can wani waje ta cilla ta mai nisan gaske tana gayyato abubuwa masu yawa tana ajje mata a filin zuciyar tata.
Umma ta lura da ita amma bata nuna ta ganta ba sosai take jin tausayin ‘yarta ta a zuciyarta sosai yanayin da take ciki yake taɓa mata zuciya amma ta rasa ya za tayi ta rasa wani irin hali Mariya ta daukarwa kanta wanda ba a iya gane me ke faruwa da ita ba nisawa tayi bayan ta saki Mu’azzam yayi hanyar waje domin yin wasa ta dubi dakin su Goggo Marka kafun ta juya da hankalinta sosai kan Mariya da tayi tagumi da hannu daya idanuwanta akan Umma wanda sam ba ita kuma hankalin ta yake kai ba.
“Mariya”.
Umma ta fadi murya a kasa cike da natsuwa da nuna rashin wasa kafun ta nisa ba tare da Mariya ta ansata ba.
“Ban san ya zan dubi lamarin ki ba, ban san a wani mizani zan ajje komai naki ba, amma sosai zuciyata ta cilla wani bigire mai girma akan yanayin ki. Kin boye abin da yake damunki kina kiɗin ki kina rawar ki ke da zuciyarki a tunanin ki hakan shine daidai ko?”.
Girgiza kai tayi kafin ta nuna da hannu a lokacin Mariya ta dago idanuwanta ta na sauke su akan Umma kafin daga bisa ta kau da su.
“Ban san mai ya canza miki halin ki ba, ban san mai ya sauya miki rayuwa ba, nidai na san ba haka kike ba, ni dai na san ba wannan halin kika ta so dashi ba, amma lokaci guda kin sauya komai na ki ya canza kamar ba Mariya ba. Zuciyarki…ina Zargin Zuciyarki da kuma abin da ke cikinta don na tabbata akwai abin da ya shigar miki zuciya ya canza miki komai na ki na tabbatar da hakan a raina, amma ki kasa faɗi mani a matsayina na uwa gareki baki da wata shaƙiƙiya wacce ta dace ki kai wa kukan ki da neman mafita kamar ni baki da kowa ba ki da wanda zaki kai wa kukan ki kamar ni amma Mariya kin yi watsi da wannan damar wanda ita kadai ce hanya mafi dacewa dake a filin duniyarki”.
Nisawa tayi kafin ta dubi in da take jin motsi a bayan ta Hafsat ce tsaye ta tokare bakin kofa ta zuba masu idanu kafin ta kau da kai gefe guda ita Umma nuna wa tayi kamar bata ganta ba Mariya dake zaune itama sun ga juna a tsakaninsu su zubdawa junansu kallo raini kafin Mariya ta kau da kai tana mai kokarin mikewa kan kafafuwanta.
STORY CONTINUES BELOW
Bata hanata b domin ta sani ganin Hafsat ne ya sakata mikewa ta shiga daki ita ma mikewa tayi ta bi bayanta.
Zuciyarta taji tana sanar da ita da ta fadi abin da ke cinta a rai amma tsoro da yarda Umma zata dauki lamarin ya hanata motsawa sai gyaɗa kai take yi kamar wata kadangaruwa Umma na binta da kallo.
“Ba zan takura miki ba domin bana son nima a takura min bana son takura ga kowa domin takurawa tana iya sawa kiyi mani karya ki fada min abin da bashi ne ba ni kuma ba zan so hakan ba na barki har zuwa lokacin da kikayi ra’ayi don kan ki”.
“Ehem…Umma…”.
Da sauri ta daga mata hannu ganin yarda ta fara kalato furucin da zatayi kamar wanda akayi wa dole ganin yanayin da Umma tayi ya sanya ta tsuke bakinta waje daya idanuwanta su tara kwalla kadan.
******
Kallonta yake yi da wani irin yanayi mai haifar masa da wani lamari mai girman gaske tun daga tushen zuciyarsa da ruhi yake jin yanayin gangar jikinsa da jijiyoyin jikinsa gami da ɓargo suna ansar wani sako mai girman gaske.
A hankali idanuwansa suka shiga lumshewa kamar wanda barci yaci karfinsa kafin ya sake buɗe su sosai akanta kafin ya kau da kai yana jan numfashi yana haɗiyeshi da kyar.
“Mariya…”.
Kau da kai tayi daga kallon da take masa tun dazu mai cike da tuhuma da zargi kafin lokaci guda ta galla masa harara wacce ta sanya shi shanye abin da yayi niyar fadi.
Jikinta sosai ya ansa da yanayin muryar da yayi amfani da ita wajan ambaton ta amma bata bari hakan yayi tasiri a zahirin ta ba.
Juya tayi da zubar kowa gida zuciyarta da bugawa da yanayi na fargabar abin da zai je ya dawo ta san bata yiwa kanta adalci ba ita akaran kanta ta san haka amma bata san mai yasa komai take kasa saita shi ba ita da zuciyarta. Zuciyarta sosai take kara buɗewa da lamarin amma ita taki ba da kai bori ya hau numfashi take ja tana jin yarda kamshin turaren jikinsa ke bula ko wani sashi da lungu na cikin hancin ta yana haurawa cikinta yana hautsina mata kwanya da guntun tunanin da take ta kokawa dashi tun dazu.
Bata san shi ne ba da ba abin da zai sata fitowa har ta dubeshi har yayi kokarin kara rikita mata lissafi duk da tana kaunar sanyashi a idaniyarta amma kuma kuncin da take ji game dashi yafi garwashin wuta a gareta zafi.
” A tunani na ban yin tsammani na kai har haka a wajan laifi ba a wajan ki ko da yake ban yi mamaki ba tun da duniyarki ta kubuce ta daina tunanin wani mai kama dani komai sunana”.
Numfashi taja gami da tsayawa daga takunta da take yi wanda take jin jikinta kamar yana narkewa yana watsewa a kasa juyawa tayi idanuwanta na sauka a nasa da wani irin yanayi wanda lokaci guda ya haifarwa da zuciyoyi biyu abu iri guda har ya kusan tona sirrin da yake a ko wani dayan su.
“kana kokarin daura min laifin da ban san dashi ba kana kokarin hukuntani akan abin da ban sani ba…”.
“Ba magana bace wannan ya kamata ki daina yin ta kin ji ko!”.
Ya fadi muryarsa da sauti a ciki yana takowa gareta sosai numfashin su yake dukan juna kafin Mariya ta kau da kai cikin kasalallan yanayi.
“Akan mi zaka ce ba magana bace kai ne dai kake raina ta amma ni abin da na fadi shine daidai!”.
Ita ma ta fadi da zafi a muryarta kamar zata shako wuyarsa wani irin zafi da raɗaɗi take jin zuciyarta na haifarwa mai girman gaske. da mamaki yake dubanta jin yarda take masa magana murmushi yayi mai ciwo kafun ya kara kusanto ta.
STORY CONTINUES BELOW
“Mariya”.
Ya kirata bata ansa shi ba illa dubansa da ta sake yi tana jan numfashi.
“Kace ban cancanta da na tsaya ina kula samari ba har su zama abokan rigima ta yanzu kai mai ya kawo ka nan har ka tsaya a nan kake magana dani har kake daga min murya kenan kai ma kana sahunsu?”.
Runtse idanu yayi kafun ya buɗe su lokaci guda sun kaɗa sun yayi jajir.
Bai san ta wacce hanyar zai dubi Mariya ba bai san mai ya dace yayi mata ba da zata gane in da ya sanya gabansa take ganewa taki fahimtarshi shi kuma ya rasa gane ta ina zai bi domin fahimtar da ita komai bai koma ya sanar da ita bai san ta yaya zata fuskance shi ba yana tsoron abin da zai je ya dawo.
Takun da suka ji na takalmi ne duk ya dawo dasu daga dogon nazarin da su ka fada su duka dubanta suke yi da mamaki Baseera ce tsaye hannayenta sarke a juna fuskarta sanye da bakin glass No respect wanda ya hana tonuwar asirin yanayin da kwayar idanuwanta suke ciki amma daka kalleta zaka hango wani kwantaccen murmushi mai girman gaske a fuskarta ta a hankali ta shiga takowa har ta iso in da suke tsaye sai da tayi musu kallon tsaf! kafin tayi kasa da glass din tana duban Mariya wacce ita ma ita take kallon da wani yanayi wanda ba yabo ba fallasa.
Murmushi tayi mata kafun ta dubi Dr.Karami da yayi fakare yana kallonta kashe masa ido daya tayi wanda komai da tayi din akan idon Mariya ne hakan ya sanya ta juyar da idanunta jin yarda kirjinta ke ansa sautin bugu kamar zuciyarta zata faso kirji ta yo waje wani tukuki bakin ciki da takaici taji yana taso mata yana turkewa a makoshi numfashi ma daƙyar take jan sa idanuwanta lokaci guda sun kaɗa sun yayi jajir.
Motsa baki ta shiga yi kamar zata yi magana amma ina! ta kasa zuciyarta da take jin tayi nauyi kamar zata tarwatse ta hanata aiwatar da komai takun da taga Baseera nayi zuwa ga Dr.Karami yakara hargitse mata tunani da sauri ta fara ja da baya tana kokarin kwasa da gudu kuka ne take jin yana zuwa mata mai karfin gaske wanda ta tabbata in har ta cigaba da tsayuwa a wajan ba kuka kadai ne zata samu zarafin yi ba har zubewa akasa sumamiya sai tayi.
“Mariya”.
Baseera tayi saurin kiranta ganin tana kokarin barin wajan ta juya tana takowa inda ta tsaya cak! fuskarta da murmushi kafaɗarta ta dafa kafun ta kure da idanu sosai.
“Uhmmm…”.
Hannu ta daga mata a zafafe tana turen hannunta da ta daura mata kan kafada.
“Bana muraɗin jin komai daga gareki kin ji ko don Allah ki bar naji da abin dake damuna a zuciyata bana son karin wani Tension din a wannan lokaci…”.
“ki daina fadin haka domin duk maganar da kikeyi karya ce kawai zalla a cikinta kuma bata kai zuciyarki ba ni nasan haka idanuwanki gashi nan kuma suna karya taki da kan su don haka Tell me the trut I don like joking Mariya in kuma ba zaki iya fadi ba ni zan fadi a yanzu nan ba sai kin bata min lokaci kin bata naki ba”.
Gyaɗa kai Mariya ta shiga yi idanuwanta na kawo kwalla ji take yi kamar ta kurma ihu don takaici komai na Baseera haushi yake bata ta tsaneta tsana mai tsanani bata taba zaton zata tsani wani bawa a filin duniyar nan ba amma a yau ta tsani Baseera Babbar ƙawarta da take ji da ita a filin duniyar nan wanda bazata ce ga dalili ba.
“Of couse in ba zaki iya fadi ba ni ina damar da zan iya fadi”.
Juyawa tayi ta dubi Dr.Karami da ya gama shiga wani hali na ruɗani musamman yanayin da ya ga Baseera tayi masa ba karamin tayar masa da hankali yayi ba ya jefa zuciyarsa cikin tsanani ruɗani mai matukar firgita kwanya.
STORY CONTINUES BELOW
“Ta kasa fada maka abin dake damun zuciyarta, ta kasa fuskarta ka ta sanar da kai komai ko da yake kai ma da naka kunshin na sirrin zuciya a tsakaninku ban san waye ya dace na dora a mizanin masu cutar kai ba”.
Baseera ta fadi fuskarta ba wasa tana kai komo a tsakaninsu sosai dukkannin su suka shiga ruɗani in maganarta wanda suka rasa in da ta dosa sosai zuciyoyinsu suka shiga harɓawa da lamari mai girma akan maganar sosai suka shilla duniyar nazari ko za su kwato kansu daga duhun da suka faɗa akan zancen nata amma sun kasa sai watsa mata idanu suke yi suna faman jan numfashi kwakwalansu na kara cakuɗewa da lamari mara sauki a zuciya da ruhi.
Taku tayi a hankali ta isa wajan Dr.Karami da ya saki baki da idanu yana kallon ikon mai duka shi dai aka ran kansa bai san ina ta dosa da maganarsa ba amma zuciyarsa nayi masa zargi akwai wani sirri da ta sani a tsakaninsu.
“Zuciyarka zata cuce ka in har baka yi wasa ba”.
Ta fadi tana dubansa tsakar idanu kafun ta murmusa da wani irin yanayi.
“Kana sona Dr.Karami amma ka kasa sanar dani har ni akaran kaina na fahimta ya kamata ace baka yi wannan saken ba domin kuwa bana tsammanin zan soka domin ina da wanda nake so”.
Runtse idanu yayi lokaci guda yaji wasu kibiyoyin tashin hankali sun cakar masa zuciya kafun lokaci guda yaji duk wani sashi na jinin jikinsa yana tsayawa cak! da gudana komai na jikinsa yaji yana narkewa da tashin hankali buɗe idanuwansa yayi lokaci guda ya sauke su wajan da Baseera take tsaye wacce a wannan lokacin ta rigaya ta juya ta doshi inda Mariya take tsaye tana kokarin mutuwa zuciyarta na ta faman kai kawo wasu kaifaffun wuƙaƙe taji suna soke mata kirji da zuciya da ruhinta take ji su na babbakewa lokaci guda.
Tsoro ne ya saukar masa lokaci guda ganin yarda Baseera ta doshi Mariya ya tabbatarwa kansa maganar da ta sanar dashi ita zata sanar mata tsoronsa daya taki fahimtarsa tsoronsa daya tayi masa fahimta ta baibai tare da yanke masa hukuncin akan wannan lamari ya tabbata komai kara kwaɓewa zai yi da hanzari ya fara kokarin takawa domin isa wajan domin sanin abin yi amma ina kafin yayi taku biyu ta isa wajanta har ta fara magana da ita mutuwar tsaye yayi lokaci guda zuciyarsa ta buga da wani tashin hankali gumi ya fara karyo masa mai dumin gaske komawa yayi da baya ya jingina da motarsa a daidai lokacin ya hango mota kirar Benz tayi Parking kuri yayi wa motar yana kallonta haka kawai yaji motar bata kwanta masa ba a zuciya har da mai ita karan kansa kafin ya gama guntun
tunaninsa ya ga Dr.Aqeel ya bayyana ware idanu yayi sosai yana dubansa da mamaki wani kunci ne yaji ya zo masa wuya lokaci guda ya tsaya kafun zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri-sauri kamar zata yo waje.
“Kin ka sa fahimta,na fada ki kina cikin yanayi na so amma kin ki yarda sai faman wahalar da zuciyar ki kikeyi na tabbata ba zaki taba samun WALWALAR ZUCIYA ba har sai ranar da kika gasgata na sani Dr.Aqeel kike so amma kin kasa sanar dashi hakan”.
Wani irin duba Mariya tayi ma jikinta har rawa yake yi yana karkarwa bakinta ya shiga motsi ji take yi kamar ta shako wuyar Baseera ta turmushe ko ta samu sa’ida da wadannan banzayen lafuza da take fada mata bata san ya kayi ta san Dr.Aqeel take so ba bata san wa ya fada mata shi take so ba bata ya akayi har bakin Baseera ya iya tafka wannan saɓon mai girman gaske ba.
Numfashi ta ja mai tauri kafun ta dube ta sosai da idanuwanta rinannu.
“ya kamata kiyi saurin tuba ga Ubangiji tun kafin ya hukuntaki akan wannan saɓon da kikayi”.
Ta fadi tana faman nishi numfashinta take ji yana fizga kamar zai rabu da gangar jikinta gabadaya duban Dr.Karami tayi lokaci guda taji zuciyarta ta sake bugawa kafun ta dubi Baseera da take faman kallonta fuskarta da murmushi.
STORY CONTINUES BELOW
“Karki sake zuciyata tayi gangancin fara ci miki mutunci karki ga laifina tun wuri ya kamata ki sauya maganar domin ba haka take ba”.
Dafa kafaɗarta tayi tana faman sauke numfashi ita jarumtar ta fara rauni bata san ya zata sauke lamarin nan da ta dauko ba mai girman gaske kwakwalwarta ta fara kamawa da wuta batayi zaton abin ba zai zo mata da sauki har haka ba ta dauka lokaci guda komai zai sauya za su karbi muradan zuciyoyinsu ashe fatanta ba zai tabbata ba burinta zai nakasa a wannan matakin tun kafin aje ko ina kau da kai tayi wasu kwalla suka taru mata kafin ta mai da su daƙyar tana faman jan numfashi duban Mariya tayi sosai har yanzu tana kan bakarta taki yarda da burin zuciyarta.
Da dan hanzari Baseera ta juya ta koma inda Dr.Karami yake tsaye gabadaya abin duniya ya ishe shi tsoro yake yi yaji inda zance zai kwana shi da Mariya.
“BAR RAINA ALLURA…”.
“…Domin kuwa karfe ce”.
Kamar daga sama Baseera taji muryar ta sauke zancen da ta dauko da sauri ta juya Dr.Aqeel ne yake takowa a hankali fuskarsa da yanayi na ba yabo ba fallasa hannunsa da Key din motarsa ya faman kaɗawa sosai ya tunkaro su kallan kallo suka shiga yi shi da Dr.Karami kallo ne na wani irin hali mai kama da ‘a cike nake da kai, kana son kawo mani tsaiko a lamari na.’
Harɗe hannayensa yayi a ƙirji lokacin da ya iso yana mai dubansu daya bayan daya kafin ya dire akan Mariya da tayi wujiga-wujiga da ita kamar wacce ta kwato kanta daƙyar daga bakin kura.
“Bana tunanin wannan tsayuwar da kukayi akwai mafita a cikin ta maganar gaskiya ya kamata ku sani ni Mariya take so domin duk abin da kuke zantawa da yarda ke Baseera kike yi na san so kike yi ki hada tsakaninsu amma kin kasa to ki sani Mariya bata da wani wanda yake son ta take sansa tamkar yani…”.
“You don get Sense At All Dr.Aqeel ya kamata ka iya bakin ka tun kafin ya kai ka ga dana sani”.
Cewar Dr.Karami yana faman hirji jin abin da Dr.Aqeel yake fadi gaba gaɗi cikin gadara da isa.
Murmushi ya saki yana mai watsa hannu sama kafun ya dubi Baseera.
“Bana zaton Mariya zata so Dr.Karami domin kuwa bai nuna son ba ni na fara nuna mata so don haka ni zata ansar wa so”.
“Ba dole bane ka fara furta kalmar so ka yi tunanin kuma za a anshi naka son akan wanda ya so daga baya so ba ruwansa sai wanda ya burge zuciya ta aminta dashi zata so dadewa a so ba shi yake sanya a so mutun ba so a RANA DAYA yana iya samun gurbi sannan so yana iya wanzuwa zaman shekaru amma bai samun gurbi don haka ka sani GURBIN SO ba a ko wani waje ake samun sa ba sai inda ya dace”.
Gabadayan su suka juya in da suke sauraron zantukan na fitowa Huzaif ne tsaye harɗe da hannu yana faman dariya mara sauti har da ‘yar kwallarsa a idanu a hankali ya shiga takowa yana mai cigaba da cewa.
“Bana tunani don ka zo ka furta so kayi tunanin zaka samun GURBIN SO a zuciyar da ka furtawa so lokaci guda so daban yake sannan so sai inda ya ga ya dace zai shiga duk da dai shi kan shi so din ba ya lura da dacewa ko matsayi ko wata daukaka kafin ya farwa zuciya kana ganganci da kace so sai ya tsufa a in da ake furta shi yake samun gurbin zama ya kamata ka sauya tunaninka”.
Ya fadi ya mai duban su kafun ya dubi Mariya da tayi firgai-firgai da ita kamar wacce take jira ace kes ta kurma da gudu bata san lokacin da hawaye suka fara zuba a idanuwanta ba dumin su kawai taji tunda Huzaif ya tunkaro ta take jin gabanta na tsananta faduwa da tashin hankali mai girma so take yi ta saki ihu ko zuciyarta ta daina tsalle tsalle da babbakewa da take yi zuciyarta ta take ji tana kumbura cikin kirjinta komai na jikin ta take jin yana daukar zafi kamar roba cikin wuta ji take yi tana narkewa da tashin hankali mai girma gaske bata san wani bala’i bane kuma yake kokarin samun gurbi a yanzu bata san wani irin tashin hankali bane zai sanyota gaba a wannan bigire ta shiga uku ita a duniyarta.
STORY CONTINUES BELOW
Saukar hannu taji a fuskarta ana dauke mata hawaye wani numfashi taja mai karfi kafin ta runtse idanuwanta ta buɗe su Huzaif ne yake dauke su da hankicif dake hannunsa dubansa take yi da idanuwanta masu kokarin rufewa da kwalla dubansa take yi gabanta na kara tsananta buguwa komai take ji ya kwance mata bata san ya za tayi ba zuciyarta take so ta buga ko zata mutu ta huta da wannan bala’in da take ciki kau da kai tayi lokaci guda ganin irin kallon da Huzaif yake jifanta dashi mai kokarin rikitata ta tsane shi tsana sosai amma bata san abin da yasa lokaci guda zuciyarta ta tuna mata da babinsa ba ta tuna mata da GURBIN da ta bashi a zuciyarta har yake kokarin buɗewa.
“Yaa Rabbi”.
Ta furta can kasan makoshinta kafin ta dago kanta ta sake dubansa Dr.Aqeel ta hango ya tunkaro wajan kamar wani mayunwacin zaki sai faman hirji yake yi yana kara hura iska a hancinsa idanuwansa sun kaɗa sunyi yayi kamar anyi masa surace da Barkono hankali ta fara kokarin ja da baya amma ina kafafuwanta take ji kamar an turkesu a waje guda ko motsi basa yi.
“Wai kai ba wani iri mutum ne? shin baka san in da so ya dace bane da yarda bai dace ba na lura kai ma dan takife ne a harkar so ka daina tunanin za kayi wani tsawon rai a harkar so tun wuri ka tattare tashin balagar kyankyasan ka da kake ji dashi sannan kake ganin karan ka ya kai tsaiko har kake tunanin TASIRIN SO zai zauna akan ka ni ne nan wanda so zai yi wa rana ba kai ba”.
“Me yasa kafi ye kaunar kan ka ne mai yasa kake son cutar da zuciyarka ne mai yasa kake son ajje GURBIN SO a zuciyarka bayan ka san wauta kake yi wa kan ka bana tunanin ka san meye so kafun ka shige shi a filin duniyarka…”.
Duban junan su suke yi kamar wasu mayunwatan zakuna sai faman kallon kallo sukeyi wa juna mai cike da tsananin rigima da tsanar juna.
Bige hannun da Dr.Aqeel yayiwa Huzaif ne ya sanya shi tsagaitawa da maganar da yake yi yana mai murmushi a hankali kuma ya shiga duban Mariya kamar zai shige jikinta idanuwansa sarke da nata.
“Kice baki Kaunata ki fadi su ji ba kya sona”.
Runtse idanu tayi tana jin zuciyarta na kara buɗe wasu kofofi har kashi uku wanda ta jima da kullesu gabadaya take jin su suna buɗe kan su da kan su dubansa tayi kafun ta daura hannu aka tana kokarin kurma ihu amma ina ihun ma yaki zuwa hawaye kawai suke mata ambaliya a daidai lokacin Baseera ta iso tana faman duban Mariya fuska a raunane.
“Da matsala Mariya ban san ya zan sanar dake ba amma maganar gaskiya Dr.Karami ba so na yake yi ba ke yake so nayi wannan shirin ne akan cewa ko za ki nuna kishi ki fito ki sanar masa shi kike so kika kasa fadi masa…”.
Ji kake kau! hannun Mariya akan kuncinta ta shiga nuna ta da hannu tana faman tangaɗi kamar wanda ta sha barasa tayi makas gabadaya ta fice daga cikin hayyacinta.
“Kina tunanin zan so shi ne bayan kin ce mani kuna soyayya kina tunannin maganar da kika fadi mani zatayi tasiri akai na ne ki bar ni kawai naji da bala’in da kuka jefa ni a ciki na san dama duk ba kwa kaunata dama na sani rakiya nayi duniyar nan na zo ne don kawai a tarwatsa min zuciya na mutu kowa ya huta burin ku ya cika Shikenan..Shikenan zan mutu yanzu zan mutu yanzun nan…”.
Kawai fadin maganganun take yi tana dariya idanuwanta na zubda hawaye da sauri Baseera ta isa gareta ta riketa sosai tana faman hade jikinta da nata wani kuka mai zafin gaske ta saki zuciyarta na faman a zalzala da zafin mai girman gaske.
“karki yi saurin yanke tsammani Mariya so ya gaji haka…”.
Da sauri ta kwace kanta tana faman ja da baya tana sakin huci.
STORY CONTINUES BELOW
“So ya gaji haka fa kika ce dama haka so yake da bala’i a cikin sa dama haka so yake da kayan guba a cikin sa dama haka so yake da masifa a cikin sa tabbas na yarda SO DA RAININ HANKALI yake na tabbata so akai na ya fara haifar da masifa na tabbata akaina so ya fara haifar da bala’i na tabbata akai na so ya fara haifar da cuta mara magani tun kafin aje ko ina so ya fara min haka to ina kuwa in na fara zama ina yiwa so biyayya…”.
Goge fuskarta tayi kafun ta dubi Dr.Aqeel da Huzaif da suka zuba mata idanu cikin halin ta shin hankali.
“Kace kana so, kai ma kace kana so sannan kuma shima…”.
Sai kuma tayi shiru tana duban Dr.Karami da ya zama wani butum butumi gaɓadaya ya kasa motsi a yarda yake tsaye kawai numfashi ke fita a jikinsa amma ya tabbata ba abin da yayi saura mai motsi a ko ina a jikinsa bai taba tsammani zai shiga tashin hankali irin na yau ba bai taba zaton zai ga bala’in rayuwa ba irin na yau sai yau ya kara ganin wautarsa da gangancinsa ya kara tabbatar da maganar hausawa nacewa ‘BAR RAINA ALLURA ƘARFE CE’ in ya cire rashin dacewa ya cire ganin kankata ya dauko ma’aunin so a yarda yake ya ajje a zuciyarsa da duk haka bata faruwa ba ga shi yanzu abin da ya raina yana kokarin haifar masa da CIWON RAI mara magani.
“Baseera ban san wata ƙaddara bace ta jingino mani wadannan mutanan ban san mai yasa ALKALAMIN ƘADDARA da ya tashi rubuto min tashin hankalin rayuwa ba ya jehomin ta hanyar so…”.
Da sauri ta iso gareta tana mai rufe mata baki.
“Karki ce haka ki dauki komai a matsayin jarabawa sannan kuma ƙaddararki ta rayuwa…”.
“zan dauki komai a matsayin ƙaddara amma ban da lamarin na domin na tabbata bala’i ne bala’i mai ansa suna bala’i domin na tabbata duk ikirarin da suke yi suka ce suna sona ba wanda yake tausayi na a cikin sun in da suna sona ba za su so su gannin cikin bala’i ba amma da yake su masu son kai ne ko wanne ya dauko tawagar rigunan bala’in sa ya jinginawa rayuwata”.
A hankali ta fara taku tana kokarin barin wajan kafin ta tsaya ta juya tana duban su.
“UKU BALA’Ikuka dasa min a rayuwa domin ba zan kira shi UKU ALHERI ba kuma ina so ku sani dukkan ku ina son ku ko wannan ku na saka shi a zuciyata yanzu abin da ya rage a tsakanin ku sai ku zo ku dandatsani kowa ya dauki kason sa”.
Ta na gama fadin haka ta juya cikin sassarfa kuka na kara tunkodo mata zuciya hannayenta ta saka ta toshe bakin ta har ta fada cikin gida a zaure ta durkushe tana faman jan numfashi hawayen da take so su zubo mata sun ki zuwa kukan ma lokaci guda ya tsaya cak! kanta ta daga sama ta runtse hannayenta duk biyu ta dora a saman kirjinta tana faman haki kafun lokaci guda numfashinta ya dauke idanuwanta suka ƙaƙƙafe.
Ihu Baseera tayi lokacin da ta biyo bayanta taga halin da take ciki da sauri ta isa gareta ta kai hannu tana kokarin jinjingata amma ina lokaci guda ta bingire kasa ba alamun numfashi hakan ya kara sanyata sake kurma wani uban ihu tayi waje da gudu a daidai lokacin su su duka ukun sukayo cikin soro Dr.Karami har yana cin karo da Baseera da sauri ya rikota tana kokari faduwa ya fada cikin soron a daidai lokacin kuma Umma da Goggo Marka gami da Hafsat suka duro cikin soron ganin Mariya asheme ba alamun rai ya sanya kowa sakin salatin Dr.Karami yayi kanta yana kokarin daukarta Dr.Aqeel yayi saurin riko shi fizge kansa yayi yana yin kurin sake kaimata sura Umma dake tsaye ta shiga duban su su duka ba wanda bata sani ba da sauri ta isa wajan da Mariya take yashe ta durkushe tana mai dundubata kafin da dago ta dube su da hawaye a fuskarta.
“Yaa Allah!”.
Ta fadi tana mikewa kafun ta dubesu ba tare da wani firgici ba.
“Sai ayi kokarin yi mata suttura a kai ta gidanta ko saboda Allah yayi mata cikawa”.
Ba wai Dr.Ƙarami da su Dr.Aqeel ba kadai ba hatta Baseera sai da numfashinta ya dauke.
Saukar ruwan da suka ji ne ya dawo da su hayyacin su Hafsat ce dauke da rusheshen baho tsaye tana faman yatsine fuska sai faman kallon uku ahu take jifan su dashi take yi gabadayan su a firgice suka dawo hayyacinsu sai faman kara kaina sukeyi a tsakanin su sun rasa abin yi ma Dr.Karami ya ja tunga ya tsaya yana mai da numfashi kafun ya dubi in da Mariya take yashe har zuwa lokacin dai jiya-i-yau ƙura mata idanu yayi sosai yana kallonta tun daga babban dan yatsanta har zuwa kanta gata nan sambal! Kansa ne ya shiga juyawa yana dawo masa da maganganun da Umma tayi da karfin gaske ya toshe kunnuwansa yana furta.
“Nooo!!!”.
Kafin lokaci guda ya sureta kamar wanda ya dauki ‘yar tsana ya fice da ita daga cikin soron gidan dukkan su suka goya masa baya illa Goggo Marka da Hafsat dake tsaye suna duban su da wani irin yanayi da nuna halin-ko-in-kula ga lamarin Umma kuwa cikin gida ta koma ta dauko mayafinta ta yo waje ko kafin ta iso ba wanda ta tadda nan ta jin gina da bango tana faman ajiyar numfashi mai zafi kafin ta rintse idanuwanta ta buɗe su.
“Allah ga bayinka kai ka san abin da yake damun su a filin duniyar nan kayi musu maganinsa”.
Tana gama fadin haka ta juya cikin gida cikin yanayi na rashin tabbas din ‘yar ta ta domin kuwa ta san ko sun kaita asibiti sai dai su dawo da ita domin tuni ta tabbbatar Mariya ta shuri burji rai yayi halinsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *